ba, da mutuwa ya yi tazo ta min
gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke Abba, da yake
sarkin dankara magana ne, sai ya ce "To ita ta
kashe shi da zata miki gaisuwa?" Ta kule da
bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai kasan ni
na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ahankali yake tukin, kira'ar Ahmed
Suleiman ce ke tashi wadda ya yi murya biyu
cikin sanyin murya. Wayarshi d ake gefe ta soma
ruri. Ya kali fuskar wayar, Hajiya Nina ce, don
haka ya ci gaba da tukinshi, kusan kira na bakwai
sannan ya daga. Ta ce, "Lokacinka ne za ka iya
yin duk yanda kaso, amma kafin kazo hannuna
wacce shawara ka yanke?" ya ce, "Ta me?" Ta
ce, "Au, ka manta kenan? To ba damuwa za ka
zo yau ne ko sai an dauko ka?" 2.... 'Yar dariya
ta kufce masa, "Ki sa a dauko ni sai ka ce wani
karamin yaro? In kin ci gaba da bibiyata za kiyi
nadamar hakan." Ta ce, "Ko kuma kai kayi ba, na
baka awa goma ka kawo kanka in ko ka 'ki, hum!
Za a kawo ka." Abba yaja tsaki "Yanda ki ke
zatona na wuce haka". Ta ce, "Idris Aminu Idris
raina ya biya da kai, kuma dole sai na cimma
hakan, jarumtarka din nan ta sake bige ni, kasan
dalilin da yasa na ce nan da awa goma? In ka
lissafa zai baka bakwai na yamma. Daidai lokacin
da ake watso mana labarai ina kwadayin ina tare
da kai, lokaci guda kuma ina kallonka cikin TV
kana feso turanci, kasan ina son muryarka ga shi
ka gwanance da iya tsara turanci, sai ka ce
yarenka. Kada in cika ka da surutu sai mun hadu
anjiman". Ta kashe wayarta. Abba yayi kokari ya
tsaida motar shi a gefen titi a hankali ya furta
"Allahumma ajir ni fi musibati..." ya kifa kansa a
jikin sitiyarin motar, yana tunanin wai shin ba za
ta sauya masa a halin da yake ciki ba? Wata
zuciyar ta ce in tasan kana cikin wani halin ko? A
haka ya isa gurin aikinsa, tunda suka shiga dakin
daukar labarai, abokanshi suka gane yana cikin
wani hali duk da bai kasance mai yawan magana
ba, amma yau ba kamar kullum ba. Salis ne ya
kasa hakuri, don haka bayan an gama daukar
labarai da kyar sun je su yi sallar Azahar suna
zaune wata Bafulatana da ke kawo musu fura ta
kawo. 3..... Dama shi Abba bai cika shan fura da
rana ba, yafi shanta da dare, don haka siyan
kurum yake yi. Bayan yaje gida sai yasha, amma
ranar ya ce mata ta bar shi kawai, ta jiya ma
tana nan bai sha ba. Da ta tafi Salis ya dube shi,
"Idris ba ka da lafiya ne?" Ya ce, "A'a me ka
gani?" Ya ce "Ba yanda ka saba ba, duk kwanakin
nan na lura kana cikin damuwa". Abba ya dube
shi amma ai kasan nayi rashin lafiya ko? Salis ya
ce dakata Idris kada kaga kamar na matsa maka
sai na ji cikinka, ko kusa ba haka ba ne. Ni
mutum ne mai saurin karantar duk dan Adam din
dana zauna kusa da shi na awa daya bare kai da
na zauna da kai tsawon lokaci, muna kuma ci
gaba da zama. Idris na fahimci kana da matukar
'ZURFIN CIKI' dalili kenan da yasa ban ta6a
damuwa da in tambaye ka matsalarka ba.
Sannan dalilin 'ZURFIN CIKIN' da naga kana da
shi ne yasa har kwanakin baya na kawo maka
matsalata da iyalina. Alhamdulillahi ka bani
shawara kuma nayi amfani da ita, kuma naga ci
gaba, matsalolina sun ragu". Abba yayi dan
murmushi. "Wai kana nufin saboda ina da
'ZURFIN CIKI' ne kaga ya dace ka sanar da ni
sirrinka?" Salis ya ce "Kusan haka ne, don me
Zurfin Ciki ya iya hadiye magana, sai dai a ganina
zurfin ciki wataran zai iya fadawa halaka, ko
wata gagarumar matsala". Abba ya dube shi,
"Wace irin halaka? Salis ya ce, "Me zurfin ciki sai
ciwon zuciya ya kama shi yana muku-muku da
matsalarshi, wani ma har ya mutu da ita ba
wanda ya sani. Amma in abu na cinka ka samu
wanda ka yarda da shi mai amana ka fada masa
zaka ji dan dadi". Abba ya ce, "To kai tunda baka
da zurfin ciki, kenan bai dace ka ji matsalar ba?"
4....Salis ya tuntsire da dariya, "Ta nan ka 6ullo?
Ai dama ka sani ba ina son yabon kaina ba ne,
a'a duk surutuna nasan abinda nake fadi". Abba
ya ce, "Salis na gode da kulawarka, matsalata ko
ka ji ta nasan shawarar da za ka bani bata wuce
ka ce in yi hakuri ba, ni kuma ba wannan ni ke
son ji ba. Salis ba komai nake yiwa 'ZURFIN CIKI'
ba, yawanci in ina da matsala nakan tunkari
Ummata ne kuma ta warware min komai. Saboda
na taso da wannan koyin da ta min, yanda na
shaku da ita ko su Alhajina ba mu shaku haka
ba". Salis ya ce, "To me ya hana ka fada mata
wannan karon?" Abba ya ce, "Ba zan iya ba, sai
dai in za ka samo min mafita ban da hakuri, to in
fada maka". Salis ya ce "In sha Allah ba za arasa
mafita ba". Nan Abba ya bai wa Salis labarinshi
da Ummi tun farko har zuwa yau. Salis ya
numfasa, sannan ya ce "Kaga illar 'ZURFIN CIKI'
ko? Ummin ma taka ce amma kana nema ka
rasata, ai ba mafitar da ta wuce ka samu
Ummarka ko Alhajinka ka fada musu muradinka".
Abba ya ce, "Tabbas haka ce mafita, sai dai idan
na aikata haka abu biyu za su faru, na farko na
zubar da mutuncin Alhajina, domin babu girma,
sun ba da 'ya ba tare da wani dalili ba ya ce ya
fasa. Sannan haramun ne neman aure cikin aure".
Salis ya ce, "Haka ne, to hakurin kawai zaka yi".
Abba ya ce "Ai mun yi ban da bada hakuri ko?"
Salis ya saki dariya, sannan ya ce "To kayi
addu'a". Abba ya mike tare da fadin "Ka tayani
da addu'a". Daga nan ya shiga dakin, Filin Don
Matasa na Hausa, don likkafar shirin tayi gaba
yanzu har na Hausa yana gabatarwa. Kullum
sake kar6uwa shirin yake a gurin Jama'a.
5......UMMI Tana kwance kan doguwar kujera,
yau kwana hudu kenan bata saka Abba a idonta
ba. Tamkar Umma ta san abinda ke ranta, sai ta
tsinkayi Umma na cewa "Yau kwana uku ne ko
hudu rabon Abba da gidan nan, sai dai ya kira mu
a waya. Alhaji dai ya ce, yana zuwa gunsa
kasuwa". Ummi ta ce, "Nima yanzun nake tunanin
haka". Ta miko ma Ummi wayarta da ke gefenta.
"Lalubo min shi in ji". Da ta soma /ringing/ sai ta
mika mata. Ya dauka suka gaisa ta ce "Abba ko
dai na maka laifi ne?" Ya ce, "Umma me a ka yi?"
Ta ce, "Tsaf, ka dauke min kafa, wanda kullum
komai saurinka sai ka biyo". Ya ce, "Ina nan
zuwa Ummata, kina raina duk inda nabi, harkoki
ne suka taru suka sa ni gaba". Ta ce, "Ni kuma
sai na ke ganin kamar don ba mu dauki
shawararka ba ne ta game da karatun Ummi shi
yasa ka". Ya ce, "Umma ba haka ba ne, zan shigo
da zarar na dawo". Ta ce. "To". Sam shi batun
shi yayi ba, sai dai baya son yazo ya ga Ummi
domin da ya ganta yake neman kwanciyar
hankalinsa ya rasa na tsawon lokaci. Amma
yanzun kalmar Salis ta karshe daya fafa masa da
za su rabu a gurin aiki ita yake tunawa. Dafa shi
ya yi tare da cewa "Miste Man shawara ta
karshe, ka nunawa kanwarka kana sonta a fili".
Ya ce "Tab, wannan shi ne me wahalar ai,
furtawa Ummi kalmar so. Zubar da kai kenan".
Ga shi ba sonsa take ba, duk yanda mace ke
girmamaka da zaran ka ce kana sonta shi kenan
ka zube a idonta. Musamman in kai ke sonta ita
ba ta sonka, wata ma har da rashin kunya zata
tsula maka, a fili ya ce, "Ina, ai ba zan ta6a gigin
bari ta san ina sonta ba". Daga kasan zuciyarshi
yaji an ce za ko ka sarata. Sai da ya yi sallar
Isha'i sannan ya yi wanka ya saka kananan kaya,
ya fito da nufin gidan su Ummarshi. Bishira ta
bishi da kallo, daga ganin fita zai yi ta fito da
saurinta tana cewa "Baban Walid! Baban Walid!!."
Ya tsaya, ta dube shi "Ina za ka?" Ya ce "Gidan
su Umma". Ta ce, "Ba wani gidansu Umma, kai
dai kurum tadi za ka je". 6.... Dariya ta su6uce
masa, sai da ya dara sannan ya ce "To in ma
tadin zan je ya za ki yi dani?". Ta ce, "Tab!, ai na
rantse maka kayi kadan. Kullum kuma ina 'kara
fada maka kai mijin mace daya ne rak!" Ya ce, "In
ji ki ko?" ta ce, "Eh." Ya ture ta gefe tare da cewa
"Da sauki tunda ba fadin Allah ba ne". Yayi
ficewarsa ya barta nan tana ta masifarta. Kan
dakalin kofar gidan, Ummi ce zaune da Sahabi
suna hira, duk da cewa Sahabin shi kadai ke ta
surutanshi Ummi na can duniyar tunanin abinda
zuciyarta ke so. Tun daga nesa ta shaki kamshin
turaransa, zaraf ta mike tsaye. So take ta kalli
fuskarshi amma ya dauke kanshi daga gare su.
Haka nan ya share sannun da zuwan da ta ke
mishi tare da shigewa cikin gida abinsa. Sahabi
ya ce, "Ya Abba na nan kuwa kwana biyu na rabu
da ganinshi?" Ta dauke kai sannan ta ce "Zan
tafi gida". Ya ce, "Haba Ummi, zuwana fa
kenan?" Ta dube shi. Ji take tamkar ta sheka
mishi mari, ta ce "To kaina ciwo yake yi, sannan
kuma ga Ya Abba yazo baya son ina dadewa a
waje". Ya ce, "To shi kenan sai gobe?" Ta ce,
"Don Allah kada kazo gobe, ka bari sai jibi". Ya
ce "Za ki azabtar da ni, ba zan iya kwana biyu
ban gan ki ba." Maimaikon taji dadin kalmar, sai
taji takaici ya mamayeta. A ranta ta ce,, "Tunda
ga gyatumarka ba". Ya ce, "In zo goben don
Allah?" Cikin muryar tausayi yake maganar, ta ce
"To shi kenan". Ta soma tafiya, ya dan tako ya
biyo ta tare da cewa "Sahibata mu kwana lafiya"
A kagare ta ce "Uhum". Ta samu Abba suna hira
da Umma, ta tura mishi kular birabisko tana
lallashinshi ya ci, tayi sallama Umma ce ta amsa.
Ta shiga idanunta kan Abba, ta zauna a kujerar
da ke fuskantarshi. Umma ta ce "Har Sahabin ya
tafi?" Ummi ta ce "Eh". Ta tsura ma Abba ido
tare da cewa, "Ina kwana Ya Abba?" Umma ta ce
"Wane irin kwana kuma Ummi da wannan daren?"
Ta ce, "Au, zan ce ina yini?" Ya amsa tare da
kallonta, "Lafiya". Ya mayar da dubanshi ga
Umma. "Umma Matar Ahmad fa ta haihu". Ta ce,
"Eh, ba jiya ka fada min ba a waya? Me ta samu
ne?" Ya ce, "Mace ta haifa, gashi ta sha wuya".
Umma ta ce, "Allah Sarki, to Allah ya raya mata,
zan je in dubota in mata barka gobe". Ya ce,
"Allah ya kai mu, ai Ahmad yayi dacen mata ba
kamar ni ba. A da Umma bana tunanin sake aure,
amma yanzun ina ganin dole sai nayi mata biyu".
Umma ta ce, "To ba dai yanzun ba duk nawa ka
ke kuma yaushe kayi wancan?" Ya ce, "Umma ke
dai ki min addu'a, ban samu irin macen data dace
da ni ba". Ta ce, "Ina maka addu'a, Allah ya
shirya maka matarka." Abba ya ce, "Ko ta shiryu
sai nayi aure insha Allahu". Ta ce, "Abba ni ko
gani nake ba ka san wadda za ka aure din ba
itama da nata kalar halin zata zo, sai su taru su
ruda ka". Ya kalli Ummi wadda ya lura da kallon
da ta tsare shi da shi kamar tana son jin abin da
yake fada ne. Ya maida idanunshi kan Umma.
"Na yarda da tarbiyar wannan yarinyar da nake
son aure yanzun, duk da yarinyar bata sona tana
girmamani". Umma ta ce, "Har ka samu kenan,
'yar gidan waye? Ummi kuwa tuni makoshinta ya
bushe, ta zaro idanu tana son ji wa kuma Abba
ke so? 7:....Ya kalli Ummi ganin yadda ta zaro
ido ya ce "Ke ni ke fadama wa ki ka zaro ido ki
ka tsare ni da su?" A hankali ta lumshe idanu
sannan ta maida kanta kan hannun kujera, ya
fuskanci Umma "Ba 'yar unguwar nan ba ce",
matsalar da yarinyar bata sona". Umma ta ce,
"To ka bar ta mana ka samu mai sonka? Yo in
haka ne ma ka ce gara matar taka ta gida, don
ita tana sonka". Yayi shiru zuwa can ya ce
"Umma in dai zan sameta zan aureta a haka".
Umma ta ce, "Kayi addu'a, ina ko mamakin mene
ne ta gani na 'ki a tare dakai Abba?" Ya ce cikin
'yar dariya "Umma ai ba dole ba ne sai ka birgke
kowa". Ummi ta mike jiri na dan dibanta ta shige
ciki. Zance ya dada watsewa, ta furta bayan ta
fada kan gado, ni ina son shi shi kuma ashe yana
can ya zarme da son wata. Ranar ta raba dare
tana kuka daga karshe ta soma ba kanta
shawarar ta samu Abba ta ce a fili dama
shisshigi ne irin na zuciyata Ya Abba ba irina
yake so ba. Shi kuwa zuciyarshi ta soma zargin
wani abu a kan Ummi, irin yanda ya ga tayi
kamar hankalinta ya tashi da batunsa. In ko haka
ne zai fi kowa murna, wata zuciyar ta ce ka sani
ko tsabar jin gulma ne yasa ta kafa maka ido duk
da haka yasha alwashin bibiyarta. Sun taso daga
sallar Juma'a shi da su Ahmad gidan budurwar
Tukur suka dosa, wayar Salis ta katse shi. Wani
aiki ne ya taso dole ya koma gurin aiki. Ya sauke
su a unguwar shi kuma ya nufi gurin aikinshi.
Karfe biyar ya baro gurin aikin da nufin yada
zango gidan Ummanshi. 8.... Yasan yau juma'a
duk yanda aka yi zai samu abinci na musamman,
don al'adarta ce girkinta na juma'a daban ne,
tana girmama ranar da abincin da ta san mijinta
zai yi farin ciki da shi. Haka nan ta kan yi
kwaliyyar musamman, shi yasa yake kara
kwadayin aura Ummi, ya san zata dauki wannan
tarbiyyar. Matasa guda uku a tsaye gefen titi cikin
fara'a da murna suka tsaida shi, ya saba kusan
kullum sai irin haka ta faru. Matasa kan tsaida
shi suna ma su nuna jin dadi da ganinshi, a gaisa
su wuce. Wasu kuma su amshi lambarshi har da
ma su son adireshinsa, yanzun ma sai ya tsaya
zai fito, tsum! Yaga sun bude motar sun shigo.
Biyu baya daya gaba, ya ba su hannu suka gaisa
su duka. Na gaban ya ce. "Mai matasa ai muna
jin dadin taimakon da ka ke mana. Ya kamata a
baka Sardaunan Matasa". Daya daga baya ya ce
"Sarkin Matasa gaba daya zamu ba shi, don yana
kokarin gurin binciko matsalolin matasa". Abba
ya yi murmushi tare da cewa, "Na Gode". Dayan
da bai yi magana ba sai ya ce "Amma mai
Matasa ka san da wannan matsalar?" Abba ya
waiwaya da nufin jin karin bayani, sai ko ya fesa
mishi wata farar hoda a fuska. Take nan atishawa
da tari suka tirnike shi. Ya soma mutsuka
idanunshi bakinshi na furta "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raji'un". Kafin 'yar sakwanni kanshi yayi
din, kuma ya fita daga hayyacinsa. Suka tuka
motar suka tashi dashi. * Farkawa ya yi tamkar
wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude ido
tangaran a kan silin, irin na masu hali. Kwan
lantarki irin na kasaitattun gidaje ya daki
hancinshi. Nan take ya shiga tunanin me ya kawo
shi nan? ba 6ata lokaci ya tuna duk abinda ya
faru, da sauri ya tashi zaune yana fadin "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raji'un". Ya ci gaba da kallon
dakin, cikin tangameme ne yana dauke da
tafkeken gado da sauran saitin shi. Sai kafet din
tsakar daki da kayan kallo, ga kuma kofofi guda
biyu. Ya tambayi kanshi da cewa me ya kawo ni
nan? me matasan suke nema a gurina?" Take
muryar Hajiya Nina ta fado masa, inda take cewa
"Za ka zo yau din ne ko sai an dauko ka?" ya
girgiza kai tare da cewa, Lallai wannan makirar
matar ce tasa aka mi shi haka". 9... Nan take ya
soma karanta addu'ar neman tsari. Daya daga
cikin kofofin ta bude, ya kure idonsa gurin da
kallo, matar ta shigo sanye cikin doguwar riga
baka mai ma6allai a gaba. Fara ce kyakkyawa,
shekarunta suna tsakanin Talatin da takwas zuwa
arba'in da biyar, domin kyawun nata sun 6oye
shekarunta, ta baza gashi a kafada. Tsura mata
ido yayi yana son tuna inda ya ta6a ganinta,
domin tabbas yasan fuskar. Muryarta ce ta katse
shi,"Dama nasan zuwa yanzun ka farko, kuma ka
gama nazarin yanda aka yi kazo nan. Kila ma
tunda kana da kamannin ma su basira ka hararo
wadda tasa a ka dauko ka". Ya ce, "Kwarai
kuwa". Lokacin ne ya tuno inda ya santa, wato
Hajiya Zabba'u ce matar shaharraran Attajirin nan
Alhaji Uzairu wadda a ke nuno ta a TV da Jaridu
tana taimakon talakawa da Marayu. Wadda ake
labarin tsoron Allahnta da gudun duniyarta,
wadda ta gina Masallatai da Makarantun Addini
ma su dama. Ya girgiza kai cikin matukar
mamaki, ta ce "Ka gane ni kenan?" Ya ce (Cikin
karfin hali) "Lallai mutum mugun ice. Wannan shi
ne Allah a baki shaidan a zuci". Ta ce "Kai ne na
biyu da ka furta wannan kalmar, sai dai bana fata
ka zama na biyu da ya bakunci inda na farkon ya
tafi. 10.... Ta tako a hankali ta dunfaro shi, ya
matsa baya cikin zuciyarshi yana korar shaidan,
'yar dariya tayi. "Nutsu Idris ko ince Abba. Ba
fyade zan maka ba". Ya dubeta da sauri, "Eh haka
nace, in na son hakan zan maka, amma ba
hakanne burina ba". Ta zauna bakin gadon, "Ka
zo mu daidaita, in kana tsoron ciwo zan baka
makari, sai dai ina so ka sani bana dauke da
wata cuta". Ya ce, "Karya ki ke, kina dauke da
mummunar cuta". Ta ce "In ka tashi daga dan
jarida ne, ka koma Likita zan baka dama ka
gwada ni". "Ya ce ba ki bukatar gwaji don ga
ciwonki nan a fili ciwon zuciya". Ta ce, "Sam ba
ni da ciwon a zuciyata, to in ma ina da shi me zai
dameka tunda ba dauka za ka yi ba". Ya sake ja
da baya ya ce, "Zuciyarki ta kamu da ciwon zina.
Ta yi duhu dumdum! har bata iya ganin
gaskiya...". "Ta daga mishi hannu, "Dakata min,
ban tambayeka labarin wa'azi ba, domin in shi
nake son ji ina da kaset-kaset kala-kala zan saka
na ji". Ta mike zuwa wata durowa ta bude, dauri
uku ta dauko ta aje gaban madubi na 'yan dari
biyar-biyar sababbi dal! Ta ce, "Wannan za ka
sha mai ne sannan kasa kati, kuma in ka kwantar
da hankalinka zan canja maka mota, zaka je
Makka. 11.... Sannan idan naga kana bin
umarnina zaka yi suna a aikin jarida fiye da duk
wani dan jarida da ka sani a kasar nan. Kai zaka
taka duk wani matsayi da dan jarida ke takawa".
ta sake nufoshi da tausasa murya. "In kabi yanda
nace ba kai ba sake kwana a talauci..." Ya
katseta da fadin, "In naki fa?" Ta hade rai tare da
zuba mishi ido, "Shima kallonta yake, sai a
lokacin ya ga tsufanta ya bayyana. Ta juya mishi
baya tana 'yar tafiya, sannan ta ce "Am sorry to
say". Ta juya ta dube shi "Za ka mutu". Gabanshi
ya fadi, amma sai ya yi karfin hali ya ce "In na
mutu sai me? Dama can mutuwa zan yi ko ba ki
kashe ni ba. Kuma ni na san ba zan wuce iyakar
ajalina ba, murnata daya zaki sauke min nauyin
zunubaina". Ta matso kusa da shi "Ka san
matasa nawa
Showing 18001 words to 21000 words out of 41322 words
gaisuwa?" Takaici ya turnu'ke Abba, da yake
sarkin dankara magana ne, sai ya ce "To ita ta
kashe shi da zata miki gaisuwa?" Ta kule da
bakin ciki ta zabga mishi harara "To ai kasan ni
na dora mata ciwon, don haka dole in je
gaisheta." Ahankali yake tukin, kira'ar Ahmed
Suleiman ce ke tashi wadda ya yi murya biyu
cikin sanyin murya. Wayarshi d ake gefe ta soma
ruri. Ya kali fuskar wayar, Hajiya Nina ce, don
haka ya ci gaba da tukinshi, kusan kira na bakwai
sannan ya daga. Ta ce, "Lokacinka ne za ka iya
yin duk yanda kaso, amma kafin kazo hannuna
wacce shawara ka yanke?" ya ce, "Ta me?" Ta
ce, "Au, ka manta kenan? To ba damuwa za ka
zo yau ne ko sai an dauko ka?" 2.... 'Yar dariya
ta kufce masa, "Ki sa a dauko ni sai ka ce wani
karamin yaro? In kin ci gaba da bibiyata za kiyi
nadamar hakan." Ta ce, "Ko kuma kai kayi ba, na
baka awa goma ka kawo kanka in ko ka 'ki, hum!
Za a kawo ka." Abba yaja tsaki "Yanda ki ke
zatona na wuce haka". Ta ce, "Idris Aminu Idris
raina ya biya da kai, kuma dole sai na cimma
hakan, jarumtarka din nan ta sake bige ni, kasan
dalilin da yasa na ce nan da awa goma? In ka
lissafa zai baka bakwai na yamma. Daidai lokacin
da ake watso mana labarai ina kwadayin ina tare
da kai, lokaci guda kuma ina kallonka cikin TV
kana feso turanci, kasan ina son muryarka ga shi
ka gwanance da iya tsara turanci, sai ka ce
yarenka. Kada in cika ka da surutu sai mun hadu
anjiman". Ta kashe wayarta. Abba yayi kokari ya
tsaida motar shi a gefen titi a hankali ya furta
"Allahumma ajir ni fi musibati..." ya kifa kansa a
jikin sitiyarin motar, yana tunanin wai shin ba za
ta sauya masa a halin da yake ciki ba? Wata
zuciyar ta ce in tasan kana cikin wani halin ko? A
haka ya isa gurin aikinsa, tunda suka shiga dakin
daukar labarai, abokanshi suka gane yana cikin
wani hali duk da bai kasance mai yawan magana
ba, amma yau ba kamar kullum ba. Salis ne ya
kasa hakuri, don haka bayan an gama daukar
labarai da kyar sun je su yi sallar Azahar suna
zaune wata Bafulatana da ke kawo musu fura ta
kawo. 3..... Dama shi Abba bai cika shan fura da
rana ba, yafi shanta da dare, don haka siyan
kurum yake yi. Bayan yaje gida sai yasha, amma
ranar ya ce mata ta bar shi kawai, ta jiya ma
tana nan bai sha ba. Da ta tafi Salis ya dube shi,
"Idris ba ka da lafiya ne?" Ya ce, "A'a me ka
gani?" Ya ce "Ba yanda ka saba ba, duk kwanakin
nan na lura kana cikin damuwa". Abba ya dube
shi amma ai kasan nayi rashin lafiya ko? Salis ya
ce dakata Idris kada kaga kamar na matsa maka
sai na ji cikinka, ko kusa ba haka ba ne. Ni
mutum ne mai saurin karantar duk dan Adam din
dana zauna kusa da shi na awa daya bare kai da
na zauna da kai tsawon lokaci, muna kuma ci
gaba da zama. Idris na fahimci kana da matukar
'ZURFIN CIKI' dalili kenan da yasa ban ta6a
damuwa da in tambaye ka matsalarka ba.
Sannan dalilin 'ZURFIN CIKIN' da naga kana da
shi ne yasa har kwanakin baya na kawo maka
matsalata da iyalina. Alhamdulillahi ka bani
shawara kuma nayi amfani da ita, kuma naga ci
gaba, matsalolina sun ragu". Abba yayi dan
murmushi. "Wai kana nufin saboda ina da
'ZURFIN CIKI' ne kaga ya dace ka sanar da ni
sirrinka?" Salis ya ce "Kusan haka ne, don me
Zurfin Ciki ya iya hadiye magana, sai dai a ganina
zurfin ciki wataran zai iya fadawa halaka, ko
wata gagarumar matsala". Abba ya dube shi,
"Wace irin halaka? Salis ya ce, "Me zurfin ciki sai
ciwon zuciya ya kama shi yana muku-muku da
matsalarshi, wani ma har ya mutu da ita ba
wanda ya sani. Amma in abu na cinka ka samu
wanda ka yarda da shi mai amana ka fada masa
zaka ji dan dadi". Abba ya ce, "To kai tunda baka
da zurfin ciki, kenan bai dace ka ji matsalar ba?"
4....Salis ya tuntsire da dariya, "Ta nan ka 6ullo?
Ai dama ka sani ba ina son yabon kaina ba ne,
a'a duk surutuna nasan abinda nake fadi". Abba
ya ce, "Salis na gode da kulawarka, matsalata ko
ka ji ta nasan shawarar da za ka bani bata wuce
ka ce in yi hakuri ba, ni kuma ba wannan ni ke
son ji ba. Salis ba komai nake yiwa 'ZURFIN CIKI'
ba, yawanci in ina da matsala nakan tunkari
Ummata ne kuma ta warware min komai. Saboda
na taso da wannan koyin da ta min, yanda na
shaku da ita ko su Alhajina ba mu shaku haka
ba". Salis ya ce, "To me ya hana ka fada mata
wannan karon?" Abba ya ce, "Ba zan iya ba, sai
dai in za ka samo min mafita ban da hakuri, to in
fada maka". Salis ya ce "In sha Allah ba za arasa
mafita ba". Nan Abba ya bai wa Salis labarinshi
da Ummi tun farko har zuwa yau. Salis ya
numfasa, sannan ya ce "Kaga illar 'ZURFIN CIKI'
ko? Ummin ma taka ce amma kana nema ka
rasata, ai ba mafitar da ta wuce ka samu
Ummarka ko Alhajinka ka fada musu muradinka".
Abba ya ce, "Tabbas haka ce mafita, sai dai idan
na aikata haka abu biyu za su faru, na farko na
zubar da mutuncin Alhajina, domin babu girma,
sun ba da 'ya ba tare da wani dalili ba ya ce ya
fasa. Sannan haramun ne neman aure cikin aure".
Salis ya ce, "Haka ne, to hakurin kawai zaka yi".
Abba ya ce "Ai mun yi ban da bada hakuri ko?"
Salis ya saki dariya, sannan ya ce "To kayi
addu'a". Abba ya mike tare da fadin "Ka tayani
da addu'a". Daga nan ya shiga dakin, Filin Don
Matasa na Hausa, don likkafar shirin tayi gaba
yanzu har na Hausa yana gabatarwa. Kullum
sake kar6uwa shirin yake a gurin Jama'a.
5......UMMI Tana kwance kan doguwar kujera,
yau kwana hudu kenan bata saka Abba a idonta
ba. Tamkar Umma ta san abinda ke ranta, sai ta
tsinkayi Umma na cewa "Yau kwana uku ne ko
hudu rabon Abba da gidan nan, sai dai ya kira mu
a waya. Alhaji dai ya ce, yana zuwa gunsa
kasuwa". Ummi ta ce, "Nima yanzun nake tunanin
haka". Ta miko ma Ummi wayarta da ke gefenta.
"Lalubo min shi in ji". Da ta soma /ringing/ sai ta
mika mata. Ya dauka suka gaisa ta ce "Abba ko
dai na maka laifi ne?" Ya ce, "Umma me a ka yi?"
Ta ce, "Tsaf, ka dauke min kafa, wanda kullum
komai saurinka sai ka biyo". Ya ce, "Ina nan
zuwa Ummata, kina raina duk inda nabi, harkoki
ne suka taru suka sa ni gaba". Ta ce, "Ni kuma
sai na ke ganin kamar don ba mu dauki
shawararka ba ne ta game da karatun Ummi shi
yasa ka". Ya ce, "Umma ba haka ba ne, zan shigo
da zarar na dawo". Ta ce. "To". Sam shi batun
shi yayi ba, sai dai baya son yazo ya ga Ummi
domin da ya ganta yake neman kwanciyar
hankalinsa ya rasa na tsawon lokaci. Amma
yanzun kalmar Salis ta karshe daya fafa masa da
za su rabu a gurin aiki ita yake tunawa. Dafa shi
ya yi tare da cewa "Miste Man shawara ta
karshe, ka nunawa kanwarka kana sonta a fili".
Ya ce "Tab, wannan shi ne me wahalar ai,
furtawa Ummi kalmar so. Zubar da kai kenan".
Ga shi ba sonsa take ba, duk yanda mace ke
girmamaka da zaran ka ce kana sonta shi kenan
ka zube a idonta. Musamman in kai ke sonta ita
ba ta sonka, wata ma har da rashin kunya zata
tsula maka, a fili ya ce, "Ina, ai ba zan ta6a gigin
bari ta san ina sonta ba". Daga kasan zuciyarshi
yaji an ce za ko ka sarata. Sai da ya yi sallar
Isha'i sannan ya yi wanka ya saka kananan kaya,
ya fito da nufin gidan su Ummarshi. Bishira ta
bishi da kallo, daga ganin fita zai yi ta fito da
saurinta tana cewa "Baban Walid! Baban Walid!!."
Ya tsaya, ta dube shi "Ina za ka?" Ya ce "Gidan
su Umma". Ta ce, "Ba wani gidansu Umma, kai
dai kurum tadi za ka je". 6.... Dariya ta su6uce
masa, sai da ya dara sannan ya ce "To in ma
tadin zan je ya za ki yi dani?". Ta ce, "Tab!, ai na
rantse maka kayi kadan. Kullum kuma ina 'kara
fada maka kai mijin mace daya ne rak!" Ya ce, "In
ji ki ko?" ta ce, "Eh." Ya ture ta gefe tare da cewa
"Da sauki tunda ba fadin Allah ba ne". Yayi
ficewarsa ya barta nan tana ta masifarta. Kan
dakalin kofar gidan, Ummi ce zaune da Sahabi
suna hira, duk da cewa Sahabin shi kadai ke ta
surutanshi Ummi na can duniyar tunanin abinda
zuciyarta ke so. Tun daga nesa ta shaki kamshin
turaransa, zaraf ta mike tsaye. So take ta kalli
fuskarshi amma ya dauke kanshi daga gare su.
Haka nan ya share sannun da zuwan da ta ke
mishi tare da shigewa cikin gida abinsa. Sahabi
ya ce, "Ya Abba na nan kuwa kwana biyu na rabu
da ganinshi?" Ta dauke kai sannan ta ce "Zan
tafi gida". Ya ce, "Haba Ummi, zuwana fa
kenan?" Ta dube shi. Ji take tamkar ta sheka
mishi mari, ta ce "To kaina ciwo yake yi, sannan
kuma ga Ya Abba yazo baya son ina dadewa a
waje". Ya ce, "To shi kenan sai gobe?" Ta ce,
"Don Allah kada kazo gobe, ka bari sai jibi". Ya
ce "Za ki azabtar da ni, ba zan iya kwana biyu
ban gan ki ba." Maimaikon taji dadin kalmar, sai
taji takaici ya mamayeta. A ranta ta ce,, "Tunda
ga gyatumarka ba". Ya ce, "In zo goben don
Allah?" Cikin muryar tausayi yake maganar, ta ce
"To shi kenan". Ta soma tafiya, ya dan tako ya
biyo ta tare da cewa "Sahibata mu kwana lafiya"
A kagare ta ce "Uhum". Ta samu Abba suna hira
da Umma, ta tura mishi kular birabisko tana
lallashinshi ya ci, tayi sallama Umma ce ta amsa.
Ta shiga idanunta kan Abba, ta zauna a kujerar
da ke fuskantarshi. Umma ta ce "Har Sahabin ya
tafi?" Ummi ta ce "Eh". Ta tsura ma Abba ido
tare da cewa, "Ina kwana Ya Abba?" Umma ta ce
"Wane irin kwana kuma Ummi da wannan daren?"
Ta ce, "Au, zan ce ina yini?" Ya amsa tare da
kallonta, "Lafiya". Ya mayar da dubanshi ga
Umma. "Umma Matar Ahmad fa ta haihu". Ta ce,
"Eh, ba jiya ka fada min ba a waya? Me ta samu
ne?" Ya ce, "Mace ta haifa, gashi ta sha wuya".
Umma ta ce, "Allah Sarki, to Allah ya raya mata,
zan je in dubota in mata barka gobe". Ya ce,
"Allah ya kai mu, ai Ahmad yayi dacen mata ba
kamar ni ba. A da Umma bana tunanin sake aure,
amma yanzun ina ganin dole sai nayi mata biyu".
Umma ta ce, "To ba dai yanzun ba duk nawa ka
ke kuma yaushe kayi wancan?" Ya ce, "Umma ke
dai ki min addu'a, ban samu irin macen data dace
da ni ba". Ta ce, "Ina maka addu'a, Allah ya
shirya maka matarka." Abba ya ce, "Ko ta shiryu
sai nayi aure insha Allahu". Ta ce, "Abba ni ko
gani nake ba ka san wadda za ka aure din ba
itama da nata kalar halin zata zo, sai su taru su
ruda ka". Ya kalli Ummi wadda ya lura da kallon
da ta tsare shi da shi kamar tana son jin abin da
yake fada ne. Ya maida idanunshi kan Umma.
"Na yarda da tarbiyar wannan yarinyar da nake
son aure yanzun, duk da yarinyar bata sona tana
girmamani". Umma ta ce, "Har ka samu kenan,
'yar gidan waye? Ummi kuwa tuni makoshinta ya
bushe, ta zaro idanu tana son ji wa kuma Abba
ke so? 7:....Ya kalli Ummi ganin yadda ta zaro
ido ya ce "Ke ni ke fadama wa ki ka zaro ido ki
ka tsare ni da su?" A hankali ta lumshe idanu
sannan ta maida kanta kan hannun kujera, ya
fuskanci Umma "Ba 'yar unguwar nan ba ce",
matsalar da yarinyar bata sona". Umma ta ce,
"To ka bar ta mana ka samu mai sonka? Yo in
haka ne ma ka ce gara matar taka ta gida, don
ita tana sonka". Yayi shiru zuwa can ya ce
"Umma in dai zan sameta zan aureta a haka".
Umma ta ce, "Kayi addu'a, ina ko mamakin mene
ne ta gani na 'ki a tare dakai Abba?" Ya ce cikin
'yar dariya "Umma ai ba dole ba ne sai ka birgke
kowa". Ummi ta mike jiri na dan dibanta ta shige
ciki. Zance ya dada watsewa, ta furta bayan ta
fada kan gado, ni ina son shi shi kuma ashe yana
can ya zarme da son wata. Ranar ta raba dare
tana kuka daga karshe ta soma ba kanta
shawarar ta samu Abba ta ce a fili dama
shisshigi ne irin na zuciyata Ya Abba ba irina
yake so ba. Shi kuwa zuciyarshi ta soma zargin
wani abu a kan Ummi, irin yanda ya ga tayi
kamar hankalinta ya tashi da batunsa. In ko haka
ne zai fi kowa murna, wata zuciyar ta ce ka sani
ko tsabar jin gulma ne yasa ta kafa maka ido duk
da haka yasha alwashin bibiyarta. Sun taso daga
sallar Juma'a shi da su Ahmad gidan budurwar
Tukur suka dosa, wayar Salis ta katse shi. Wani
aiki ne ya taso dole ya koma gurin aiki. Ya sauke
su a unguwar shi kuma ya nufi gurin aikinshi.
Karfe biyar ya baro gurin aikin da nufin yada
zango gidan Ummanshi. 8.... Yasan yau juma'a
duk yanda aka yi zai samu abinci na musamman,
don al'adarta ce girkinta na juma'a daban ne,
tana girmama ranar da abincin da ta san mijinta
zai yi farin ciki da shi. Haka nan ta kan yi
kwaliyyar musamman, shi yasa yake kara
kwadayin aura Ummi, ya san zata dauki wannan
tarbiyyar. Matasa guda uku a tsaye gefen titi cikin
fara'a da murna suka tsaida shi, ya saba kusan
kullum sai irin haka ta faru. Matasa kan tsaida
shi suna ma su nuna jin dadi da ganinshi, a gaisa
su wuce. Wasu kuma su amshi lambarshi har da
ma su son adireshinsa, yanzun ma sai ya tsaya
zai fito, tsum! Yaga sun bude motar sun shigo.
Biyu baya daya gaba, ya ba su hannu suka gaisa
su duka. Na gaban ya ce. "Mai matasa ai muna
jin dadin taimakon da ka ke mana. Ya kamata a
baka Sardaunan Matasa". Daya daga baya ya ce
"Sarkin Matasa gaba daya zamu ba shi, don yana
kokarin gurin binciko matsalolin matasa". Abba
ya yi murmushi tare da cewa, "Na Gode". Dayan
da bai yi magana ba sai ya ce "Amma mai
Matasa ka san da wannan matsalar?" Abba ya
waiwaya da nufin jin karin bayani, sai ko ya fesa
mishi wata farar hoda a fuska. Take nan atishawa
da tari suka tirnike shi. Ya soma mutsuka
idanunshi bakinshi na furta "Inna lillahi wa'inna
ilaihir raji'un". Kafin 'yar sakwanni kanshi yayi
din, kuma ya fita daga hayyacinsa. Suka tuka
motar suka tashi dashi. * Farkawa ya yi tamkar
wanda ya tashi daga bacci, a hankali ya bude ido
tangaran a kan silin, irin na masu hali. Kwan
lantarki irin na kasaitattun gidaje ya daki
hancinshi. Nan take ya shiga tunanin me ya kawo
shi nan? ba 6ata lokaci ya tuna duk abinda ya
faru, da sauri ya tashi zaune yana fadin "Inna
lillahi wa'inna ilaihir raji'un". Ya ci gaba da kallon
dakin, cikin tangameme ne yana dauke da
tafkeken gado da sauran saitin shi. Sai kafet din
tsakar daki da kayan kallo, ga kuma kofofi guda
biyu. Ya tambayi kanshi da cewa me ya kawo ni
nan? me matasan suke nema a gurina?" Take
muryar Hajiya Nina ta fado masa, inda take cewa
"Za ka zo yau din ne ko sai an dauko ka?" ya
girgiza kai tare da cewa, Lallai wannan makirar
matar ce tasa aka mi shi haka". 9... Nan take ya
soma karanta addu'ar neman tsari. Daya daga
cikin kofofin ta bude, ya kure idonsa gurin da
kallo, matar ta shigo sanye cikin doguwar riga
baka mai ma6allai a gaba. Fara ce kyakkyawa,
shekarunta suna tsakanin Talatin da takwas zuwa
arba'in da biyar, domin kyawun nata sun 6oye
shekarunta, ta baza gashi a kafada. Tsura mata
ido yayi yana son tuna inda ya ta6a ganinta,
domin tabbas yasan fuskar. Muryarta ce ta katse
shi,"Dama nasan zuwa yanzun ka farko, kuma ka
gama nazarin yanda aka yi kazo nan. Kila ma
tunda kana da kamannin ma su basira ka hararo
wadda tasa a ka dauko ka". Ya ce, "Kwarai
kuwa". Lokacin ne ya tuno inda ya santa, wato
Hajiya Zabba'u ce matar shaharraran Attajirin nan
Alhaji Uzairu wadda a ke nuno ta a TV da Jaridu
tana taimakon talakawa da Marayu. Wadda ake
labarin tsoron Allahnta da gudun duniyarta,
wadda ta gina Masallatai da Makarantun Addini
ma su dama. Ya girgiza kai cikin matukar
mamaki, ta ce "Ka gane ni kenan?" Ya ce (Cikin
karfin hali) "Lallai mutum mugun ice. Wannan shi
ne Allah a baki shaidan a zuci". Ta ce "Kai ne na
biyu da ka furta wannan kalmar, sai dai bana fata
ka zama na biyu da ya bakunci inda na farkon ya
tafi. 10.... Ta tako a hankali ta dunfaro shi, ya
matsa baya cikin zuciyarshi yana korar shaidan,
'yar dariya tayi. "Nutsu Idris ko ince Abba. Ba
fyade zan maka ba". Ya dubeta da sauri, "Eh haka
nace, in na son hakan zan maka, amma ba
hakanne burina ba". Ta zauna bakin gadon, "Ka
zo mu daidaita, in kana tsoron ciwo zan baka
makari, sai dai ina so ka sani bana dauke da
wata cuta". Ya ce, "Karya ki ke, kina dauke da
mummunar cuta". Ta ce "In ka tashi daga dan
jarida ne, ka koma Likita zan baka dama ka
gwada ni". "Ya ce ba ki bukatar gwaji don ga
ciwonki nan a fili ciwon zuciya". Ta ce, "Sam ba
ni da ciwon a zuciyata, to in ma ina da shi me zai
dameka tunda ba dauka za ka yi ba". Ya sake ja
da baya ya ce, "Zuciyarki ta kamu da ciwon zina.
Ta yi duhu dumdum! har bata iya ganin
gaskiya...". "Ta daga mishi hannu, "Dakata min,
ban tambayeka labarin wa'azi ba, domin in shi
nake son ji ina da kaset-kaset kala-kala zan saka
na ji". Ta mike zuwa wata durowa ta bude, dauri
uku ta dauko ta aje gaban madubi na 'yan dari
biyar-biyar sababbi dal! Ta ce, "Wannan za ka
sha mai ne sannan kasa kati, kuma in ka kwantar
da hankalinka zan canja maka mota, zaka je
Makka. 11.... Sannan idan naga kana bin
umarnina zaka yi suna a aikin jarida fiye da duk
wani dan jarida da ka sani a kasar nan. Kai zaka
taka duk wani matsayi da dan jarida ke takawa".
ta sake nufoshi da tausasa murya. "In kabi yanda
nace ba kai ba sake kwana a talauci..." Ya
katseta da fadin, "In naki fa?" Ta hade rai tare da
zuba mishi ido, "Shima kallonta yake, sai a
lokacin ya ga tsufanta ya bayyana. Ta juya mishi
baya tana 'yar tafiya, sannan ta ce "Am sorry to
say". Ta juya ta dube shi "Za ka mutu". Gabanshi
ya fadi, amma sai ya yi karfin hali ya ce "In na
mutu sai me? Dama can mutuwa zan yi ko ba ki
kashe ni ba. Kuma ni na san ba zan wuce iyakar
ajalina ba, murnata daya zaki sauke min nauyin
zunubaina". Ta matso kusa da shi "Ka san
matasa nawa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7 Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14