ce To. Sun isa asibitin tana
wanka, sun gaisa da Inna Saratu ta fada musu
tana wanka, sannan likitan ya sallame su amma
sai sha biyu za su tafi gida, lokacin an karasa
mata allura. Abba can baya ya tsaya kusa da
kofar shigowa ya jingina da bango idanunshi suna
fuskantar kofar bayin, matuka ya kosa yaga
Ummi. Sanye da hijabi da zani daurin kirji ta fito,
da Abba suka soma hada ido, bai ta6a kallon
Ummi da sha'awa ba sai yau. Kamshin turaren
Abba ya ratsa ko'ina a dakin, ta zare idanunta
daga nashi, ta kalli Ummanta sannunku Umma.
Suka ce Yauwa. Ta gaida su sannan ta zauna
bakin gado tare da sunkuyar da kai, Alhaji Karami
ya ce, "Uwata jiki kuma ya yi sauki ko? Kanta na
kasa ta ce, Eh, ta kasa dago kanta, gani take
Abba ya cika dakin. Abban ya ce, "To ni zan tafi
don lokacin aikina ya kusa, Alhaji zamu je ne in
sauke ku? Suka ce To, Umma ta ce In an yi mata
Allurar anjima ma nemo mai Taxi. Alhaji ya ce, To
shi ke nan. Umma ta dubi Ummi ba za ki gaida
Yayan naki ba? Ta saci kallon Abban tare da
cewa, Au, ban ganshi ba. Ina yini? Ya ce, Umma
me yasa za ki rokar min gaisuwarta? Inna Saratu
ta ce, Kai Ummi da iya shege take, ina kallonta
shi ta fara kare ma kallo sannan ta kalli kowa
amma wai bata ganshi ba. Su Alhaji dai 'yar
dariya suka yi sannan suka fita, Abba ya bi su
tare da yi wa su Umma sallama. * 31. Bayan
fitarsu, Umma ta dubi Ummi fuska daure, ina
fatan baki nuna damarar nuna kiyayya ga Abba
ba ne? Ummi ta sunkuyar da kai, a ranta ta ce,
"Kin ji Umma da wani zance, ai ina zaton nafi
Mahaifiyarshi sonshi ma bare ku. "Amma a fili sai
ta ce, To Umma shi ma fa Ya Abban bai ce yana
sona ba, Umma ta ce Saratu ji ta da wani shirme.
Ina ce ita ce zata janyo ra'ayinshi gareta? Inna
Saratu ta ce, Kwarai kuwa, ta hanyar ladabi,
biyayya da girmamashi, musamman shi da ke da
matsalar mata. Ummi ta ce, Kuma ina tsoron
masifar matarsa ba dai guri daya zamu zauna ba
ko? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Kada ma in ji kin kuma zan nan, Ummi dai
tayi shiru. Da dare Alhaji ya tasa Abba zuwa
gidan su Bishira, zuwan su ne ma Alhajin yasan
'yarshi tayo yaji, cikin 6acin rai ya kira wayar
Hajiya Zainu ya ce su zo ita da Bishira. Ba tare
da ya jira amsarta ba ya aje wayar, ba tare da
yasan abinda ya faru ba ya shiga ba su hakuri.
Hajiya Zainau taje dakin su Bishira ta kira, suka
nufi sashen Alhajin tana mitar cewa munafukai
sun zo kenan, ai za'ayi ta bari muje mu ji. Suna
shiga Alhajin ya kalli Bishira, "Me ki ka zo min ki
yi a gida? Ta ce, Daddy cin amanata ya yi, aure
fa ya yi da yarinyar da suka tsane ni. Alhajin ya
daukin da ke gabanshi na plastik ya jefe ta da
shi, auren shi ne cin amana don uwaki? Hajiya
Zainu ta ce, "A'a Alhaji, zan cen gaskiya a duba
hakkinta itama, ya ya za a dau 'yar da bata
kaunarta, iyayenta basa kaunarta a ba shi.
Sannan ta yi magana ya hauta da zagin iyaye?
Ya ce, "Ke yi min shiru ban tambaye ki ba". Ya
kalli Abba, Ya abin ya faru? Ban ji ta bakinka ba?
Nan dai Abba ya fadi komai har ta taho, daidai da
cewa tazo ya rage mata haya da abin da ta ce
duka. Alhajin ya yi tsaki ya dubi Alhaji Babba, irin
wannan ai ba a biyo su, tayi ta tafiya sai dai
nima in ba zata koma gidanta ba, to ba gidana
ba. Ya zura hannu cikin aljihu ya ciro rafar 'yan
dari bibbiyu, Ga shi Abba, dama nayi maka
alkawarin baka sadaki duk lokacin da ka nemo
aure. 57..... Abba ya ce, "A'a ka bar su ai an riga
an yi. Mahaifin Bishira ya ce, "Ni nayi alkawari.
Suka yi godiya. Ya kalli Bishira, Ko ki bi mijinki,
ko ki bar gidana. Hajiya Zainu ji take tamkar ta
shake Abba. Ta ce, "Haba Alhaji, gaskiya ban
yarda da wannann hukuncin..." Ya katse ta da
cewa, Ke! Da Allah fita anan. Su Abba suna shiga
mota Bishira na fitowa da kukanta, dole ta zo ta
shiga motar. Alhaji Babba ke ta bata baki har
suka kai gida, shi kam Abba da suke sauke Alhaji
ya yi nasu gidan, suna shiga ta soma zantuka. Ba
za ka ta6a samun kwanciyar hankali ba a gidan
nan har abada, ba dai ka matsa an dawo da ni
ba? Abba ya yi murmushin mugunta, ai ni
wannan yajin naki naji dadinsa, gashi har na
samu gudunmawa, kin ga sai naje kasuwa in
soma darzo wa Amarya zannuwan lefe. Ya nufi
dakinshi ya barta nan tsaye tana zage- zage,
lefen banza, in ma uban lefe ne kai da ita sai na
koya musu hankali. Kusan goman dare Ummi
tana kan doguwar kujera, addu'a take yi Allah
yasa Abba yazo ta ganshi kafin tayi bacci. Can
kasan zuciyarta kuma kishi ne don tasan sun je
gidansu Bishira ne biko ganin Alhaji ya shigo shi
daya sai ta debe tsammani da zuwanshi. A ranta
take raya cewa yanzun haka suna can suna cin
soyayyarsu, kamshin turaren shi ne ke mata gizo
a hanci. Amma sai kunnuwanta suka tsinkayi
sallamarshi, a hankali tamkar ba ya son a san ya
shigo. Umma tana ciki? Tambayar da ya yi kenan
ba tare da ya jira ta amsa sallamar ba, ta tashi
zaune da sauri a'a tana gurin Alhaji. Ya shigo ya
zauna ta ce, "Sannu da zuwa". Ya amsa yana
kalonta, ta sunkuyar da kai, gabanta ke wata irin
faduwa. Shi kam ji yake tamkar ya manne ta a
jikinshi, sai dai yana jin nauyin hakan tunda ba
suyi wannan sabon da ba rin haka zata faru
tsakaninsu ba. Dakin yayi shiru, ita tana wasa da
yatsunta shi kuma yana kallonta, can ya ce
"Ummi". Ta dube shi "Yaushe za ki tare? Ta ce,
Nima ban sani ba, sai yanda su Umma suka ce.
Ya dauko kwalin wayar da ya sai ma Bishira ta
jefe shi da shi ya ciro wayar ya hadata da batir
din bayan ya 6are sim din ya saka. Ummi dai
tana ta kallonshi, ya manna chajar a jiki, ya mika
ma Ummi jona min can, ya nuna mata soke din
da ke bayanta. Ta amsa cike da sha'awar wayar
duk da bata nuna hakan ba sannan ba ta ce kala
ba. Ya ci gaba da cewa, "Karfe nawa a ke kashe
inji? Ta ce, har yanzu ba a canza daga yanda ka
ke kashewa ba. Ya ce, "Sha daya zuwa sha biyu?
Ta ce, "Eh, ya ce in har zuwa wannan lokacin ba
kiyi bacci ba to ki cire in an kashe, ki kunna ko da
yake in dai ke ce ba sai na ce ki kunna ba. Ta
dago ido ta kalle shi, ya ce, Eh kunnawa za ki yi
ko za ki musa ne? Don kin fi ni ma sanin kan
waya. Ta ce, Wayar Umma kadai na iya kunnawa,
sai taka. Ya ce, Oho, cikin dan murmushi, na za
ci ba za ki fadi tawa ba in tuna miki lokacin da
kika kunna tawa. Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. * 58....Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. Ta zuba fuskarta cikin tafukan
hannayenta, sam bata son Ya Abba yana tada
wannan zancen, Umma ta shigo da sallama tana
cewa, Yuwa Ummi, ina ki ka sa min 'yar kwalbar
turaren nan? Ummi ta dago fuska, "Cikin jakarki
ta rataye. Umma ta dubi Abba, "A'a ha, yaushe
ka shigo? Ya ce Ban jima sosai ba. Ta zauna ya
gaisheta, sannan ta ce masa dama Alhaji yanzu
yake ce min zaman me Ummi ke yi a gidan nan?
Ya zaci tun daga asibitin zata wuce dakinta,
Ummi ta turo baki. Umma Alhaji ya gaji da ni
sosai, suka kalle ta, Umma ta ce, Ji wani shirme,
me ya yi na gajiya? Ta ce To dubi fa daga cewa
an fasa aurena sai da ya matsa ya daura min
aure. Sannann kuma yanzun wai ya zaci daga
asibiti zan tare? Abba ya ce, Ai yana daki yi
hanzari ki same shi don shi ya san amsarki ba
Ummata ba. Umma ta ce, "Wallahi daga nan suka
share Ummi. Ta kalli Abba ta ce, "To kawai
yanda za a yi gobe ka kwashe kayanka daga
dakinka sai a kai na Ummi din kawai. In yaso
zuwa yamma ko Saratu da sauran makota sai su
rakota. Abba ya kalli Umma, ni da so nayi a dan
yi kwaskwarima a gidan kafin sannan na dan
samu na sai ma Ummin Zannuwa. Umma ta ce,
"Zancen wofi, yanzun tsirara take yawo? Kawai in
kana da fenti a hannu a goga a kawo ta haka, in
babu ma dai goben nan zata tare don ba zan
amince ran mijina ya 6aci ba. Abba ya yi
murmushi, to shi kenan Umma da safe kafin na
fita zan nemo masu aiki ina da fenti da siminti
sai ayi 'yar kwaskwarima shi ke nan. Dama ga
kudi nan da Mahaifin Bishira ya bani, wai dama
ya yi min alkawarin biya min sadaki. . 59...
Umma ta ce, "Yanzun Alhaji ya gama bani labari,
Mahaifin yarinyar nan mutumin kwarai ne, don
Allah Abba ka rike yarinyar nan ko don darajar
mahaifinta. Ummi ta ta6a baki, kishi ya motsa.
Abba ya ce "In sha Allahu Umma nima abinda
nike dubawa kenan, ni ke hakuri da ita. Ta ci
gaba da cewa, Sannan kada kaga Ummi yar
uwarka ce ka ce zaka fifitata, sam ba zan yarda
da haka ba. Kayi adalci a tsakaninsu ka dinga
addu'a Allah ya hada maka kansu. Ya ce, "In
Allah ya yarda Umma zan kula. Ta ce, "To maza
ka tashi ka tafi gurin iyalinka. Sam bai ma dace
ka fito ba, kamata ya yi a ce ka zauna gida ka
kara ba matarka baki, ya cee To Umma. Ta mike
tana cewa, tashi maza. Ya mike yana kallon
Ummi, yayin da ita kuma ta juya fuskarta cike da
6acin rai. Ya ce, Ummi ki fa kunna in an kashe
injin? Sam ba ta tanka ba don haushi, sai da ya
tafi sannan Umma ta dubi Ummi. Ki tashi ki
kwanta don gobe ki tashi da wuri, kiyi duk shirin
da ya dace saboda babu daga kafa a tarewarki
gobe. Ki ta fasha-fishenki ba zamu kuma yarda
da kalace-kalacen ciwonki ba, ta tafi abinta. A
zaton Umma, Ummi tana fushin ba zata tare ba
ne, ita ko haushinta korar mata miji da Umma
tayi ya tafi gurin kishiyarta. Koda ta kulle kofar
ba ta shiga uwar dakin ba, nan kan doguwar
kujeta ta mike abinta. Jira ta ke a kashe Injin ta
kunna waya. Abba ko kafin ya isa gida sai da ya
fita titi ya fanshi kaji guda biyu da madara mai
tsafta.I novels / ZURFIN CIKI book 3 part 8
ZURFIN CIKI book 3 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:37
Jira ta ke a kashe Injin ta kunna waya. Abba ko
kafin ya isa gida sai da ya fita titi ya fanshi kaji
guda biyu da madara mai tsafta. 60...Sai dai
yana shiga gidan ya iske mahaifiyarshi da matar
tashi suna ta zage- zage. Ya nufi gurinsu, Sahura
ta ce, Sai yanzun suka barka ka taho? Ya ce,
"Umma dama ban dade da zuwa ba". Ta ce, "Ina
ta aiken kazo ina nemanka shi ne ka 'ki zuwa
saboda ka maida ni 'yar iska ko? Ya ce, A'a
Umma ba a fada min ba. Sannan aiki ne yasha
kaina... Ta ce, "Rufe min baki, ai baka daga kafa
da zuwa gun Suwaiba. To saurare ni da kyau ka
ji, nazo ne in fada maka cewa ka rubuta saki ka
ba wannan 'yar iskar yarinyar. Ya ce, Kiyi hakuri
Umma, ki bari sai a hankali. Bishira ta ce, Umma
yana sonta fa, jin ku kawai nake. Maganar Bashir
gaskiya ce da ya ce da shi a ka shirya hakan.
Umman Bashir ta ce, "Dama Abba kaima son
Ummi ka ke yi? Ya ce, Umma ba zan ki Ummi ba,
in kun yi la'akari da kaunar da iyayenta suke
nuna min. Amman wallahi ban san komai game
da auranmu ba, ta ce kana nufin kan dole a ka
daura muku aure ba don kana sonta ba? Abba ya
yi dan jim, ta ce kai nake sauraro, don ta tafi sai
ya ce kusan haka dinne, itama kuma ba sona take
ba. Umma ta ce, Ina ruwana da bata sonka, in
bata so iyayenta ai suna so. Ni dai bukatata
yanzun kada ka bari ta tare, sannan ko kusa kada
taga fuska a gurinka. 33. 61... Umma ta ce, "Ina
ruwana da bata sonka, in bata so iyayenta ai
suna so. Ni dai bukatata yanzu kada ka bari ta
tare, sannan ko kusa kada taga fuska a gurinka".
Ya dan yi shiru yana tunanin wannan irin lamari a
zuciyarshi ya ce, bari kawai in lalla6ata, zan yi
yanda ki ka ce sai dai kuma in su Alhaji suka sa
kawo ta ni ba zan iya ja da su ba. Sannann ke
kanki bana so a ce ke ki ka sa ni in ma Ummi
rashin mutunci, amma ki bar ni da ita in har ta
yarda ta tare a nan gidan. Bishira ta ce, "Tab, ba
ko zata tare a nan gidan ba". Umma ta ce "A'a ki
bari in sun matsa ta tare a nan din ta tare, gara
suna kusa muna kallon irin zaman da za su yi.
Can gefe ba sai su rinjaye shi ba". Bishira ta ce,
"Umma na tsani shegiyar yarinyar nan ne, bana
son in ganta ko cikin mafarkina, bare a zahiri".
Sahura ta ce, "Bishira na ce ki nutsu ki bar komai
a hannuna, in ma zan hada da Bokaye ne ba
Malamai ba in sha Allahu sai kin dara a gidan
nan. Ta ce, "To Umma, Sahura ta ce, Yauwa ke
dai ki zuba ido, Abba dai yana tsaye yana
kallonsu. Sai lokacin yayi magana, Umma dare fa
yayi, ta ce to muga ledar hannunka, ya mika
mata. Ta buda ta gani, "A'a kaza? To ku zuba
min nawa". Ya mika wa Bishira, Ki dibarwa
Umma. Ya nufi dakinsa yana jin sallamarta tana
fadin ta wuce, ya fito ya ce "To Umma sai da
safe, ya rufe gidan ya koma dakinsa. Da ya shigo
gidan ne da niyyar lallashin Bishira, amma yanda
abubuwan suka zama sai ya ji ba ma ya son
ganin Bishiran. Zantukan Bishiran da na
Mahaifiyarshi sun saka shi cikin tunani, lamo ya
kwanta a kan katifa yana ta harsaso irin zaman
da za a yi a gidan. Anya kuwa ba zai kama wa
Ummi haya ba? Cak! Hasken wutar dakin ya
dauke tare da tsayawar Injin. A fili ya futa, Mai
ya kare kenan, sai da ya yi shirin bacci ya
kwanta tare da manne filo a kirjinshi, sannan ya
dauko wayarshi ya kira layin da ya hada cikin
sabuwar wayar da ya ba Ummi. 62.. Gabanta ne
ya fadi, lokacin da taga lambar Ya Abba suna
rawa a fuskar wayar, ta haddace lambobinshi tun
shekarun baya. A fili ta ce, kenan ma ya hada
wayar ba yau ya soma hada ta ba, ta sake yin
lamo a kan gado tare da janyo filo ta manna a
kirjinta. Ta daga wayar lokacin tana daf da
tsinkikewa, can cikin makoshinta tayi sallama. Ya
amsa, tsigar jikinsa a tashe sakamon jin muryarta
tana ratsa jikinshi, ya ce "Ummi, ta ce Na'am Ya
Abba. Ya ce, "Kina son ki tare goben? Ta lumshe
ido, ba ni da za6i Ya Abba, duk yanda ku ka ce.
Dadi ya cika zuciyarshi. To shi kenan ki tare
goben, zan yi parking tun Asubahi sai in sa mai
fenti yayi kafin in tafi aiki. Ta ce, "Ba an ce in
mutum ya yi aure ana ba shi hutu ba? Ya yi 'yar
dariya, "To ni ba ki ga yanda auren nawwa yazo
daga sama ba? Amma duk da haka in na nemi
hutun za a bani, ta ce kayi aikin kama kawai ba
sai ka nemi hutu ba.. Ya katseta, "Don ba a sona
shi yasa ba a damu na amshi hutu ba? Ta ce,
"Ba nufina kenan ba, naga kana matukar son
aikinka ne". Ya yi dan murmushi "Kin dai
wayance kawai, to yanzun haka zaki tare babu ko
dan kunshi bare gyaran kai irin na Amare? Koda
yake ba aure so ba ne. Cikin muryar shagwa6a ta
ce, "Ya Abba ka daina, ya ce me zan daina? Kana
cewa bana sona, ai kai ma ba ka sona... Ya dan
yi shiru, yanda ta ke shagwa6ar ne ta tsuma shi.
Ya ce, ok, to goben sai kije ki gyaranki ko? ta ce,
"Umma ba za ta bari in fita ba, amma me yin
fulawa za ta iya ta mini". Ya ce, "To ina ne a ke
gyaran gashin? Ta ce, "Cikin gari ne, ya ce kin
san gurin? Ta ce, "Eh, amma ban ta6a yi ba, ya
ce to ki bari zan shigo gidan kafin na tafi aiki zan
ce Umma ta bar ki, ta ce "To." Suka dan yi shiru.
Can ya katse shirun da cewa, "Me ki ke tunani?"
"Yaushe?" "Yanzun." Ta dan musukuta, "Ina
tunanin yanda abubuwan za su kasance gobe.
Yanda har za'a yi fenti, sannan a jire kuma in tare
duk a gobe". Ya ce "Duk mai sauki ne, ni kuma
kin san tunanin da nake yi yanzun? Ta ce, "A'a,
ya ce gobe kamar yanzun muna tare... da sauri ta
katse wayar, me Ya Abba ke son fada? Ta kashe
wayar sannan ta kudundune. Ita ma yanzun ya
jona mata wannan tunanin, a fili ta furta gobe
kamar yanzun me ya ke faruwa? Shi kuwa sai ya
ji haushin kansa sakamakon furucin da ya yi har
ta yanke wayar, wani gefen kuma sai ya ga kila
don bata sonshi ne shi yasa har ta ji haushin
furucin nashi. Kila ma yanzun tana can tana kuka
in ta tuna gobe tana gidansa, dare ya tsala amma
ya kasa bacci, don haka sai ya mike yayo alwala.
Sallah ya shiga don kara nuna godiyarsa ga Allah
da ya bashi Ummi tare da rokon Allah ya kimsa
mata sonshi, daga karshe ya roki hadin kan
matansa. 34 63..Yana wanka da safe ya jiyo
muryar mum dinsa harta zo gdn, a zuciyarshi
yace innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yana fitowa
tace wurinka nazo, Bashir yazo ya fada min cewa
yau za'a kawo fitsararriyar yarinyar nan ko? Abba
cikin damuwa yace umma nima bansani ba, tace
munafiki kasani, bari kaji ko an kawota ko
magana bance ta hadaku da ita ba, kai in ma
kaje girin munafukan iyayen nan nata su ka ce
yau zata tare kace saika shirya. Bishira tace
umma bazan yarda ta tare ba, bai sai min komai
ba, ya kalli Bishira to itama na sai mata wani
abun ne? Sahura tace to ina ruwan wani da baka
sai mata ba? Abba yace toni bani da kudi ma,
Bishira tace to kudin jiya da babana ya baka fa?
Umma tace fito dasu, yace umma dama fa kudin
sadaki ne ya biya min, kuma naba alhji karami
waliyyinta sai dai ki je gun shi ki amsa, tace don
kasan bazan tunkareshi bane shi yasa to tana
binka bashi, zaka chanza mata kayan daki, ka sai
mata zannuwa sannan ka bata jari, yace umma
banyi alkawari ba, in dai
Showing 33001 words to 36000 words out of 41322 words
wanka, sun gaisa da Inna Saratu ta fada musu
tana wanka, sannan likitan ya sallame su amma
sai sha biyu za su tafi gida, lokacin an karasa
mata allura. Abba can baya ya tsaya kusa da
kofar shigowa ya jingina da bango idanunshi suna
fuskantar kofar bayin, matuka ya kosa yaga
Ummi. Sanye da hijabi da zani daurin kirji ta fito,
da Abba suka soma hada ido, bai ta6a kallon
Ummi da sha'awa ba sai yau. Kamshin turaren
Abba ya ratsa ko'ina a dakin, ta zare idanunta
daga nashi, ta kalli Ummanta sannunku Umma.
Suka ce Yauwa. Ta gaida su sannan ta zauna
bakin gado tare da sunkuyar da kai, Alhaji Karami
ya ce, "Uwata jiki kuma ya yi sauki ko? Kanta na
kasa ta ce, Eh, ta kasa dago kanta, gani take
Abba ya cika dakin. Abban ya ce, "To ni zan tafi
don lokacin aikina ya kusa, Alhaji zamu je ne in
sauke ku? Suka ce To, Umma ta ce In an yi mata
Allurar anjima ma nemo mai Taxi. Alhaji ya ce, To
shi ke nan. Umma ta dubi Ummi ba za ki gaida
Yayan naki ba? Ta saci kallon Abban tare da
cewa, Au, ban ganshi ba. Ina yini? Ya ce, Umma
me yasa za ki rokar min gaisuwarta? Inna Saratu
ta ce, Kai Ummi da iya shege take, ina kallonta
shi ta fara kare ma kallo sannan ta kalli kowa
amma wai bata ganshi ba. Su Alhaji dai 'yar
dariya suka yi sannan suka fita, Abba ya bi su
tare da yi wa su Umma sallama. * 31. Bayan
fitarsu, Umma ta dubi Ummi fuska daure, ina
fatan baki nuna damarar nuna kiyayya ga Abba
ba ne? Ummi ta sunkuyar da kai, a ranta ta ce,
"Kin ji Umma da wani zance, ai ina zaton nafi
Mahaifiyarshi sonshi ma bare ku. "Amma a fili sai
ta ce, To Umma shi ma fa Ya Abban bai ce yana
sona ba, Umma ta ce Saratu ji ta da wani shirme.
Ina ce ita ce zata janyo ra'ayinshi gareta? Inna
Saratu ta ce, Kwarai kuwa, ta hanyar ladabi,
biyayya da girmamashi, musamman shi da ke da
matsalar mata. Ummi ta ce, Kuma ina tsoron
masifar matarsa ba dai guri daya zamu zauna ba
ko? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Umma ta ce ina ruwanki da matarsa?
Sannan in ba ku zauna guri daya ba haya zai
kama? Kada ma in ji kin kuma zan nan, Ummi dai
tayi shiru. Da dare Alhaji ya tasa Abba zuwa
gidan su Bishira, zuwan su ne ma Alhajin yasan
'yarshi tayo yaji, cikin 6acin rai ya kira wayar
Hajiya Zainu ya ce su zo ita da Bishira. Ba tare
da ya jira amsarta ba ya aje wayar, ba tare da
yasan abinda ya faru ba ya shiga ba su hakuri.
Hajiya Zainau taje dakin su Bishira ta kira, suka
nufi sashen Alhajin tana mitar cewa munafukai
sun zo kenan, ai za'ayi ta bari muje mu ji. Suna
shiga Alhajin ya kalli Bishira, "Me ki ka zo min ki
yi a gida? Ta ce, Daddy cin amanata ya yi, aure
fa ya yi da yarinyar da suka tsane ni. Alhajin ya
daukin da ke gabanshi na plastik ya jefe ta da
shi, auren shi ne cin amana don uwaki? Hajiya
Zainu ta ce, "A'a Alhaji, zan cen gaskiya a duba
hakkinta itama, ya ya za a dau 'yar da bata
kaunarta, iyayenta basa kaunarta a ba shi.
Sannan ta yi magana ya hauta da zagin iyaye?
Ya ce, "Ke yi min shiru ban tambaye ki ba". Ya
kalli Abba, Ya abin ya faru? Ban ji ta bakinka ba?
Nan dai Abba ya fadi komai har ta taho, daidai da
cewa tazo ya rage mata haya da abin da ta ce
duka. Alhajin ya yi tsaki ya dubi Alhaji Babba, irin
wannan ai ba a biyo su, tayi ta tafiya sai dai
nima in ba zata koma gidanta ba, to ba gidana
ba. Ya zura hannu cikin aljihu ya ciro rafar 'yan
dari bibbiyu, Ga shi Abba, dama nayi maka
alkawarin baka sadaki duk lokacin da ka nemo
aure. 57..... Abba ya ce, "A'a ka bar su ai an riga
an yi. Mahaifin Bishira ya ce, "Ni nayi alkawari.
Suka yi godiya. Ya kalli Bishira, Ko ki bi mijinki,
ko ki bar gidana. Hajiya Zainu ji take tamkar ta
shake Abba. Ta ce, "Haba Alhaji, gaskiya ban
yarda da wannann hukuncin..." Ya katse ta da
cewa, Ke! Da Allah fita anan. Su Abba suna shiga
mota Bishira na fitowa da kukanta, dole ta zo ta
shiga motar. Alhaji Babba ke ta bata baki har
suka kai gida, shi kam Abba da suke sauke Alhaji
ya yi nasu gidan, suna shiga ta soma zantuka. Ba
za ka ta6a samun kwanciyar hankali ba a gidan
nan har abada, ba dai ka matsa an dawo da ni
ba? Abba ya yi murmushin mugunta, ai ni
wannan yajin naki naji dadinsa, gashi har na
samu gudunmawa, kin ga sai naje kasuwa in
soma darzo wa Amarya zannuwan lefe. Ya nufi
dakinshi ya barta nan tsaye tana zage- zage,
lefen banza, in ma uban lefe ne kai da ita sai na
koya musu hankali. Kusan goman dare Ummi
tana kan doguwar kujera, addu'a take yi Allah
yasa Abba yazo ta ganshi kafin tayi bacci. Can
kasan zuciyarta kuma kishi ne don tasan sun je
gidansu Bishira ne biko ganin Alhaji ya shigo shi
daya sai ta debe tsammani da zuwanshi. A ranta
take raya cewa yanzun haka suna can suna cin
soyayyarsu, kamshin turaren shi ne ke mata gizo
a hanci. Amma sai kunnuwanta suka tsinkayi
sallamarshi, a hankali tamkar ba ya son a san ya
shigo. Umma tana ciki? Tambayar da ya yi kenan
ba tare da ya jira ta amsa sallamar ba, ta tashi
zaune da sauri a'a tana gurin Alhaji. Ya shigo ya
zauna ta ce, "Sannu da zuwa". Ya amsa yana
kalonta, ta sunkuyar da kai, gabanta ke wata irin
faduwa. Shi kam ji yake tamkar ya manne ta a
jikinshi, sai dai yana jin nauyin hakan tunda ba
suyi wannan sabon da ba rin haka zata faru
tsakaninsu ba. Dakin yayi shiru, ita tana wasa da
yatsunta shi kuma yana kallonta, can ya ce
"Ummi". Ta dube shi "Yaushe za ki tare? Ta ce,
Nima ban sani ba, sai yanda su Umma suka ce.
Ya dauko kwalin wayar da ya sai ma Bishira ta
jefe shi da shi ya ciro wayar ya hadata da batir
din bayan ya 6are sim din ya saka. Ummi dai
tana ta kallonshi, ya manna chajar a jiki, ya mika
ma Ummi jona min can, ya nuna mata soke din
da ke bayanta. Ta amsa cike da sha'awar wayar
duk da bata nuna hakan ba sannan ba ta ce kala
ba. Ya ci gaba da cewa, "Karfe nawa a ke kashe
inji? Ta ce, har yanzu ba a canza daga yanda ka
ke kashewa ba. Ya ce, "Sha daya zuwa sha biyu?
Ta ce, "Eh, ya ce in har zuwa wannan lokacin ba
kiyi bacci ba to ki cire in an kashe, ki kunna ko da
yake in dai ke ce ba sai na ce ki kunna ba. Ta
dago ido ta kalle shi, ya ce, Eh kunnawa za ki yi
ko za ki musa ne? Don kin fi ni ma sanin kan
waya. Ta ce, Wayar Umma kadai na iya kunnawa,
sai taka. Ya ce, Oho, cikin dan murmushi, na za
ci ba za ki fadi tawa ba in tuna miki lokacin da
kika kunna tawa. Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. * 58....Haka nan don tsabar iya sarrafa
wayarki tun kina 'yar karama ki ka tura ni garin
Kaduna. Ta zuba fuskarta cikin tafukan
hannayenta, sam bata son Ya Abba yana tada
wannan zancen, Umma ta shigo da sallama tana
cewa, Yuwa Ummi, ina ki ka sa min 'yar kwalbar
turaren nan? Ummi ta dago fuska, "Cikin jakarki
ta rataye. Umma ta dubi Abba, "A'a ha, yaushe
ka shigo? Ya ce Ban jima sosai ba. Ta zauna ya
gaisheta, sannan ta ce masa dama Alhaji yanzu
yake ce min zaman me Ummi ke yi a gidan nan?
Ya zaci tun daga asibitin zata wuce dakinta,
Ummi ta turo baki. Umma Alhaji ya gaji da ni
sosai, suka kalle ta, Umma ta ce, Ji wani shirme,
me ya yi na gajiya? Ta ce To dubi fa daga cewa
an fasa aurena sai da ya matsa ya daura min
aure. Sannann kuma yanzun wai ya zaci daga
asibiti zan tare? Abba ya ce, Ai yana daki yi
hanzari ki same shi don shi ya san amsarki ba
Ummata ba. Umma ta ce, "Wallahi daga nan suka
share Ummi. Ta kalli Abba ta ce, "To kawai
yanda za a yi gobe ka kwashe kayanka daga
dakinka sai a kai na Ummi din kawai. In yaso
zuwa yamma ko Saratu da sauran makota sai su
rakota. Abba ya kalli Umma, ni da so nayi a dan
yi kwaskwarima a gidan kafin sannan na dan
samu na sai ma Ummin Zannuwa. Umma ta ce,
"Zancen wofi, yanzun tsirara take yawo? Kawai in
kana da fenti a hannu a goga a kawo ta haka, in
babu ma dai goben nan zata tare don ba zan
amince ran mijina ya 6aci ba. Abba ya yi
murmushi, to shi kenan Umma da safe kafin na
fita zan nemo masu aiki ina da fenti da siminti
sai ayi 'yar kwaskwarima shi ke nan. Dama ga
kudi nan da Mahaifin Bishira ya bani, wai dama
ya yi min alkawarin biya min sadaki. . 59...
Umma ta ce, "Yanzun Alhaji ya gama bani labari,
Mahaifin yarinyar nan mutumin kwarai ne, don
Allah Abba ka rike yarinyar nan ko don darajar
mahaifinta. Ummi ta ta6a baki, kishi ya motsa.
Abba ya ce "In sha Allahu Umma nima abinda
nike dubawa kenan, ni ke hakuri da ita. Ta ci
gaba da cewa, Sannan kada kaga Ummi yar
uwarka ce ka ce zaka fifitata, sam ba zan yarda
da haka ba. Kayi adalci a tsakaninsu ka dinga
addu'a Allah ya hada maka kansu. Ya ce, "In
Allah ya yarda Umma zan kula. Ta ce, "To maza
ka tashi ka tafi gurin iyalinka. Sam bai ma dace
ka fito ba, kamata ya yi a ce ka zauna gida ka
kara ba matarka baki, ya cee To Umma. Ta mike
tana cewa, tashi maza. Ya mike yana kallon
Ummi, yayin da ita kuma ta juya fuskarta cike da
6acin rai. Ya ce, Ummi ki fa kunna in an kashe
injin? Sam ba ta tanka ba don haushi, sai da ya
tafi sannan Umma ta dubi Ummi. Ki tashi ki
kwanta don gobe ki tashi da wuri, kiyi duk shirin
da ya dace saboda babu daga kafa a tarewarki
gobe. Ki ta fasha-fishenki ba zamu kuma yarda
da kalace-kalacen ciwonki ba, ta tafi abinta. A
zaton Umma, Ummi tana fushin ba zata tare ba
ne, ita ko haushinta korar mata miji da Umma
tayi ya tafi gurin kishiyarta. Koda ta kulle kofar
ba ta shiga uwar dakin ba, nan kan doguwar
kujeta ta mike abinta. Jira ta ke a kashe Injin ta
kunna waya. Abba ko kafin ya isa gida sai da ya
fita titi ya fanshi kaji guda biyu da madara mai
tsafta.I novels / ZURFIN CIKI book 3 part 8
ZURFIN CIKI book 3 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:37
Jira ta ke a kashe Injin ta kunna waya. Abba ko
kafin ya isa gida sai da ya fita titi ya fanshi kaji
guda biyu da madara mai tsafta. 60...Sai dai
yana shiga gidan ya iske mahaifiyarshi da matar
tashi suna ta zage- zage. Ya nufi gurinsu, Sahura
ta ce, Sai yanzun suka barka ka taho? Ya ce,
"Umma dama ban dade da zuwa ba". Ta ce, "Ina
ta aiken kazo ina nemanka shi ne ka 'ki zuwa
saboda ka maida ni 'yar iska ko? Ya ce, A'a
Umma ba a fada min ba. Sannan aiki ne yasha
kaina... Ta ce, "Rufe min baki, ai baka daga kafa
da zuwa gun Suwaiba. To saurare ni da kyau ka
ji, nazo ne in fada maka cewa ka rubuta saki ka
ba wannan 'yar iskar yarinyar. Ya ce, Kiyi hakuri
Umma, ki bari sai a hankali. Bishira ta ce, Umma
yana sonta fa, jin ku kawai nake. Maganar Bashir
gaskiya ce da ya ce da shi a ka shirya hakan.
Umman Bashir ta ce, "Dama Abba kaima son
Ummi ka ke yi? Ya ce, Umma ba zan ki Ummi ba,
in kun yi la'akari da kaunar da iyayenta suke
nuna min. Amman wallahi ban san komai game
da auranmu ba, ta ce kana nufin kan dole a ka
daura muku aure ba don kana sonta ba? Abba ya
yi dan jim, ta ce kai nake sauraro, don ta tafi sai
ya ce kusan haka dinne, itama kuma ba sona take
ba. Umma ta ce, Ina ruwana da bata sonka, in
bata so iyayenta ai suna so. Ni dai bukatata
yanzun kada ka bari ta tare, sannan ko kusa kada
taga fuska a gurinka. 33. 61... Umma ta ce, "Ina
ruwana da bata sonka, in bata so iyayenta ai
suna so. Ni dai bukatata yanzu kada ka bari ta
tare, sannan ko kusa kada taga fuska a gurinka".
Ya dan yi shiru yana tunanin wannan irin lamari a
zuciyarshi ya ce, bari kawai in lalla6ata, zan yi
yanda ki ka ce sai dai kuma in su Alhaji suka sa
kawo ta ni ba zan iya ja da su ba. Sannann ke
kanki bana so a ce ke ki ka sa ni in ma Ummi
rashin mutunci, amma ki bar ni da ita in har ta
yarda ta tare a nan gidan. Bishira ta ce, "Tab, ba
ko zata tare a nan gidan ba". Umma ta ce "A'a ki
bari in sun matsa ta tare a nan din ta tare, gara
suna kusa muna kallon irin zaman da za su yi.
Can gefe ba sai su rinjaye shi ba". Bishira ta ce,
"Umma na tsani shegiyar yarinyar nan ne, bana
son in ganta ko cikin mafarkina, bare a zahiri".
Sahura ta ce, "Bishira na ce ki nutsu ki bar komai
a hannuna, in ma zan hada da Bokaye ne ba
Malamai ba in sha Allahu sai kin dara a gidan
nan. Ta ce, "To Umma, Sahura ta ce, Yauwa ke
dai ki zuba ido, Abba dai yana tsaye yana
kallonsu. Sai lokacin yayi magana, Umma dare fa
yayi, ta ce to muga ledar hannunka, ya mika
mata. Ta buda ta gani, "A'a kaza? To ku zuba
min nawa". Ya mika wa Bishira, Ki dibarwa
Umma. Ya nufi dakinsa yana jin sallamarta tana
fadin ta wuce, ya fito ya ce "To Umma sai da
safe, ya rufe gidan ya koma dakinsa. Da ya shigo
gidan ne da niyyar lallashin Bishira, amma yanda
abubuwan suka zama sai ya ji ba ma ya son
ganin Bishiran. Zantukan Bishiran da na
Mahaifiyarshi sun saka shi cikin tunani, lamo ya
kwanta a kan katifa yana ta harsaso irin zaman
da za a yi a gidan. Anya kuwa ba zai kama wa
Ummi haya ba? Cak! Hasken wutar dakin ya
dauke tare da tsayawar Injin. A fili ya futa, Mai
ya kare kenan, sai da ya yi shirin bacci ya
kwanta tare da manne filo a kirjinshi, sannan ya
dauko wayarshi ya kira layin da ya hada cikin
sabuwar wayar da ya ba Ummi. 62.. Gabanta ne
ya fadi, lokacin da taga lambar Ya Abba suna
rawa a fuskar wayar, ta haddace lambobinshi tun
shekarun baya. A fili ta ce, kenan ma ya hada
wayar ba yau ya soma hada ta ba, ta sake yin
lamo a kan gado tare da janyo filo ta manna a
kirjinta. Ta daga wayar lokacin tana daf da
tsinkikewa, can cikin makoshinta tayi sallama. Ya
amsa, tsigar jikinsa a tashe sakamon jin muryarta
tana ratsa jikinshi, ya ce "Ummi, ta ce Na'am Ya
Abba. Ya ce, "Kina son ki tare goben? Ta lumshe
ido, ba ni da za6i Ya Abba, duk yanda ku ka ce.
Dadi ya cika zuciyarshi. To shi kenan ki tare
goben, zan yi parking tun Asubahi sai in sa mai
fenti yayi kafin in tafi aiki. Ta ce, "Ba an ce in
mutum ya yi aure ana ba shi hutu ba? Ya yi 'yar
dariya, "To ni ba ki ga yanda auren nawwa yazo
daga sama ba? Amma duk da haka in na nemi
hutun za a bani, ta ce kayi aikin kama kawai ba
sai ka nemi hutu ba.. Ya katseta, "Don ba a sona
shi yasa ba a damu na amshi hutu ba? Ta ce,
"Ba nufina kenan ba, naga kana matukar son
aikinka ne". Ya yi dan murmushi "Kin dai
wayance kawai, to yanzun haka zaki tare babu ko
dan kunshi bare gyaran kai irin na Amare? Koda
yake ba aure so ba ne. Cikin muryar shagwa6a ta
ce, "Ya Abba ka daina, ya ce me zan daina? Kana
cewa bana sona, ai kai ma ba ka sona... Ya dan
yi shiru, yanda ta ke shagwa6ar ne ta tsuma shi.
Ya ce, ok, to goben sai kije ki gyaranki ko? ta ce,
"Umma ba za ta bari in fita ba, amma me yin
fulawa za ta iya ta mini". Ya ce, "To ina ne a ke
gyaran gashin? Ta ce, "Cikin gari ne, ya ce kin
san gurin? Ta ce, "Eh, amma ban ta6a yi ba, ya
ce to ki bari zan shigo gidan kafin na tafi aiki zan
ce Umma ta bar ki, ta ce "To." Suka dan yi shiru.
Can ya katse shirun da cewa, "Me ki ke tunani?"
"Yaushe?" "Yanzun." Ta dan musukuta, "Ina
tunanin yanda abubuwan za su kasance gobe.
Yanda har za'a yi fenti, sannan a jire kuma in tare
duk a gobe". Ya ce "Duk mai sauki ne, ni kuma
kin san tunanin da nake yi yanzun? Ta ce, "A'a,
ya ce gobe kamar yanzun muna tare... da sauri ta
katse wayar, me Ya Abba ke son fada? Ta kashe
wayar sannan ta kudundune. Ita ma yanzun ya
jona mata wannan tunanin, a fili ta furta gobe
kamar yanzun me ya ke faruwa? Shi kuwa sai ya
ji haushin kansa sakamakon furucin da ya yi har
ta yanke wayar, wani gefen kuma sai ya ga kila
don bata sonshi ne shi yasa har ta ji haushin
furucin nashi. Kila ma yanzun tana can tana kuka
in ta tuna gobe tana gidansa, dare ya tsala amma
ya kasa bacci, don haka sai ya mike yayo alwala.
Sallah ya shiga don kara nuna godiyarsa ga Allah
da ya bashi Ummi tare da rokon Allah ya kimsa
mata sonshi, daga karshe ya roki hadin kan
matansa. 34 63..Yana wanka da safe ya jiyo
muryar mum dinsa harta zo gdn, a zuciyarshi
yace innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yana fitowa
tace wurinka nazo, Bashir yazo ya fada min cewa
yau za'a kawo fitsararriyar yarinyar nan ko? Abba
cikin damuwa yace umma nima bansani ba, tace
munafiki kasani, bari kaji ko an kawota ko
magana bance ta hadaku da ita ba, kai in ma
kaje girin munafukan iyayen nan nata su ka ce
yau zata tare kace saika shirya. Bishira tace
umma bazan yarda ta tare ba, bai sai min komai
ba, ya kalli Bishira to itama na sai mata wani
abun ne? Sahura tace to ina ruwan wani da baka
sai mata ba? Abba yace toni bani da kudi ma,
Bishira tace to kudin jiya da babana ya baka fa?
Umma tace fito dasu, yace umma dama fa kudin
sadaki ne ya biya min, kuma naba alhji karami
waliyyinta sai dai ki je gun shi ki amsa, tace don
kasan bazan tunkareshi bane shi yasa to tana
binka bashi, zaka chanza mata kayan daki, ka sai
mata zannuwa sannan ka bata jari, yace umma
banyi alkawari ba, in dai
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12 Chapter 13Chapter 14