To Abba ayi ta hakuri". Ya ce, Ba
komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana
kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta
kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin
mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar
aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.
71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana
'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke
tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi
cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har
suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina
zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko
Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon
din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta
zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce
a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan
kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,
domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya
saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a
dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai
kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya
ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.
Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?
Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana
tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai
'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi
da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka
ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja
baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,
ya bude mata baya ta zauna tana rike da
yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya
kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.
Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne
don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko
Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya
dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar
yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi
Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya
soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in
ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai
mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi
kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan
tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a
gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin
da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta
matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna
kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana
kishinshi sannan bata masa raini ko rashin
kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da
ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira
Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita
ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta
waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata
fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa
nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki
min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina
ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai
dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma
ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina
sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?
Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka
yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.
Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan
batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.
Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke
ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a
kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba
ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru
ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...
tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba
ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki
ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki
yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar
Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su
Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo
gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.
Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli
Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta
cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana
tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da
tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin
Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi
na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin
ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida
Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin
manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.
Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma
Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa
Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan
maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya
kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma
bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro
wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba
ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da
kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya
ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata
tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba
yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce
matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai
tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta
kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin
kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana
ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an
shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da
ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda
bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki
tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida
katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.
Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce
kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare
data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake
ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don
tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin
'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar
kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma
yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya
zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin
nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin
murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya
ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.
Ko damata uku a ka daura min aure da su bare
daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke
kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina
manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan
soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina
sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo
baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana
cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To
tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya
ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba
Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,
kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina
min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira
taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci
namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai
da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce
in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai
in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.
Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata
uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai
ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya
rungume da kyar dai ya samu yadan rage
matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing
dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura
tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi
bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka
sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai
dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi
lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya
farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta
daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata
doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma ki ke
alhalin na ce zan kira ko? Ta ce, "Amma ka san
bacci ba ya jira in ya zo,ni kuma ba zan iya yiwa
bacci gardama ba". Ya ceto sarkin iya zance, yayi
nufin zolayar ta. Yanzun dai na soma tunanin kin
soma sona, gabanta ya fafi, sam bata son ya
gano hakan yanzu. Tafi son sai lokacin da shima
ya soma sonta. Ya katse mata tunani, hasashe
na haka ne? Ta ce, ko kusa, mene hujjarka da
fadin haka? Ya gyara kwanciya. Na farko naga
ana ta kishina, sannan tun da a kadaura aure da
ni sai ciwo ya kame kansa, kuma nalura kina ta
zumdin tarewa a gidana.Ya saki 'yar dariya,
yasan ya cika mata ciki da takaici, shiru tayi
nazari take wacce amsa zata bashi, ko dai wayar
zata kashe? Tamkar ya shiga zuciyarta, sai ya
ce.... 41 Tamkar ya shiga zuciyarta sai ya ce,
"Koda wasakada a kashe waya. Ranta ya sake
6aci, ta ce Ya Abba ka tafka kuskure da kayi
zaton ina sonka,sam ni bana wani kishinka. In
don ka ce wayar matarka ce na ce ka rike abinka,
sanin kanka ne ba ma shiri da matarka, kuma duk
abinda ka ce nata ne dole na guje shidon ba zan
dauki wulakanci ba. Batun ciwo kuma daka ce
tunda aka daura mana aure ka neme shi ka rasa
dama bani na dora makaina ba, kaima ina naka
hawan jinin ya tafi? Sannann kuma wane zumudi
na nuna na tarewa a gidanka, Ya Abba ka sani
yanda a ka tilasta maka aurena, to ni ma fa dole
tasa na hakura. Amma ka rike a ranka bana wani
sonka bani kamarina ina sonka, kalaman nata na
karshe sun burgeshi har sun sa shi yin da ya
sanin tsokale zancen. Sai kuma ya canza salo da
cewa, haka dai ki ka ce amma ina da ja mu dai
bar zancen, shin dazun kafin ki soma wannan
tunanin me ki ke yi? Ta danyi shiru tana
tambayar kanta. Dama mutumin nan haka ya ke?
Oh yanzun dabara zai min sai ya gano ko ina
sonshi dole, to kuwa bazai ji ba, ya katse ta da
cewa ban san ki da karya ba. Ta ce, ina tunanin
irin ukubar da zan sha a gidanka ne ta
wulakancin da zaka min, ya yi shiru zuciyarshi
tana cewa yarinyar nan ba ta san irinson da ka ke
mata ba ai ta ma dauke ka mugu kenan. A fili sai
ya ce, "Kuma fa kin yi tunani, Allah yabaki ikon
daukar ukubar da zaki sha tare kuma dajure
wulakancin da na tanadar miki goben Ummi. "Ya
fadi, wai dama da gaske wulakancin zai mata.
Gyara kwanciya kawai tayi bata kara cewa komai
ba, kuma bata da nufin cewa wani abu, yasa taji
haushi sosai, don haka sai ya tausasa muryarshi.
"Ummi kina ji na?" Uhm" Kurum ta ce, don ya
gane tana jin shi. Alkawari ta dauka ba zata sake
cewakala ba, tunda ya hanata kashe wayar. "Ba
ni da nufin miki..." Sai layin ya yanke daga
gefanshi, ta ce, "Gara ma haka". Tana kokarin
kashe wayar gaba daya kiranshi ya sake shigowa.
Tsaki taja kafin ta daga, kuma a ciki ta amsa
sallamarshi, sannan cikin murya mai kamar zata
rushe da kuka ta ce "Ya Abba ni fa bacci nake
son in yi". Ya ce, "Sam ba wani bacci da za ki iya
yoa sai tunani". Ta ce "To na ji, ina son yin
tunanin please".Ya ce, "Tunanin me za ki yi".
Cikin gundira ta ce,"Dole in yi tunanin yanda zan
kare kaina daga wulakancinka, don bana
tsammanin zan dauka" .Ya ce, "Wasa nake miki
fa." Ta ce, "Uhum, ban amince da cewa wasa ka
ke min ba, don na tabbata mu ba abokan wasa
ba ne".Ya ce, "To shi ke nan bari in bar ki kiyi
tunanin, amma tunanin yanda za ki faranta min
za ki yi". Muryar Bishira ce ta katse shi. "Oho! Ai
tun da na farka ban ganka ba na san ana nan
ana cin amanata". Ya kashe wayar da sauri, duk
da dai Ummi ta riga ta jiyo muryar Bishiran. Sai
dai bata fahimci me Bishirar take cewa ba,
ringingine tayi tare da dora filo a kirjinta, tunani
take yi wane irin zama za su yi? Koda bata da
amsa ta kudurce har abada ba za ta dauki
wulakanci ba, a shi ko a matar shi. Sai dai
alkawari ta dauka ba za ta musu raini ba,
matsawar ba su suka 6ullo da hakan ba. *
************************************** Shi ko
Abba rigima suka dinga yi da Bishira cikin tsohon
daren wai ya cuce ta ya kwanta da ita yazo yana
hira da wata banza. Kila ma ya saba kwanciya da
Ummin ne yau bai samu dama ba, Abba ya ce kin
so kanki in ki ka yimin wannan zaton, don ban
ta6a nemanki ba, kafinki shigo gidana, ko na
ta6a?"Ta ce, "Don ka san dai ni ba fuska". Da ya
gaji da iya korata ya rufe kofar ya koma can
dakin. 40. 74... Washegarin ranar, ga mamakin
Ummi tun misalin karfe goma jama'asuka cika
gidansu, a ka dora abinci. Can kuma saiga yaran
shagon Abba da dinkunan zannuwan daAlhaji
Babba ya sai mata.Ranar Abba bai shigo gidan
ba a waya ya kiraUmma suka yi magana, zuwa
karfe uku angama yiwa Ummi jeren dakin da yake
yana da girma yacinye komai tsaf.Fitar 'yan jere
babu jimawa sai ga Anty Farida dakannasu motar
tana da kaya tana biye da su, gadoda kujeru a ka
canzo mata.Suka jera mata sannan suka lodawa
motar na dasuka dauki hanya suka koma, Abba
kam yana gurinaiki amma zuciyarshi tana
gida.Fatanshi Allah yasa yana zuwa ya tarar an
kaimishi Umminshi, kawayen Bishira da
makotansu'yan jam'iyyarta duk sun shigo gidan
sun hadu saizugata suke yi tare da nuna mata
koda wasa kadata sakar ma Ummi fuska, kuma in
ta mata takamata ta duki 'yan kayanta.Suna
gidan a ka kawo Ummi, 'yan kawo Amaeyakam
suna jiyo habaici da zagin da su Bishira ke yi,don
haka suka ce kada a kai musu yarinyar.Inna
Saratu da Inna Harira suka ce ai kuwa sai
ankaita.Ba ko kunya Bishira ta zabga musu
harara lokacinda suka fada mata cewa ga
kanwarta sun kawomata, don Allah su zauna
lafiya tare da Aminci.In yarinyar tayi ba daidai ba
ta sata a hanya... takatse su cikin tsawa da
mikewa tsaye. "Don Allahku fice min daga daki
amanar kishiya? Har wai muzauna da aminci ku
ke cewa?Tayi 'yar dariyar yake "Kun yi kuskure,
ai batacanza daga sunan ta na kishiya ba, kuma
kowa yasan kishiya abokiyar gaba ce."Inna
Saratu ta ce, "Baiwar Allah jahilan mata sunesuke
yin irin wannan tunanin, amma ga masu ilimisuna
koyi da gidan mai tsira da Aminci
(S.A.W)ne".Bishira ta ce, "To kawai dai ki ce min
jahila ki huta,bari ku ji ba za n ba ku a 6oye ba,
zama ne za muyi shi na rashin mutunci, na kowa
ya iya allonshi. Don ina kishin mijina, kuma zan
nuna". Tirkashi! Lallai akwai daru kenan. To
masu karatu ku biyo ni cikin littafi na 4, kumana
karshe domin jin yadda za ta kasance atsakanin
Bishira da Ummi da kuma Oga kwata-kwata wato
Showing 39001 words to 41322 words out of 41322 words
komai, Insha Allahu. Suka biyo shi a baya tana
kara jawa Bishira kunne kan cewa in har ta
kuskura ta ji wata magana ta 6ullo ta rashin
mutunci sai ta fasa tsaya mata a kan maganar
aikin Hajji ko Dady ya amince sai tasa ya janye.
71.... Sun shigo mata Muhibba tana baya tana
'yanwutsil-wutsil dinta tamkar kurame, haka suke
tafiyar. Ta zaci su nufi gida sai taga sun nufi
cikin gari. Bata tambaye shi ina za su ba, har
suka isa inda yayi parking ya dubeta, Madam ina
zuwa, hum kawai ta ce. Ya bude baya ya dauko
Muhibba ya sa6a a kafada ya nufi shagon saloon
din. Daidai lokacin sun kammala komai, Ummi ta
zari hijabinta da niyyar rufe kanta, Yagana ta ce
a'a kanwata bari ya gani don ya biya ni 'yan
kudina. Abba bai zaci Ummi tana da gashi ba,
domin dai acikin Hausawa 'yan Arewa za a iya
saka Ummi acikin ma su gashi. Yayi laya-laya a
dokin wuyanta baki sidik. Yayi murmushi, lallai
kin gyara da kyau. Nawa ne kudinki? Ta fada ya
ciro ya bata, sannan Ummi tazari hijabinta.
Mamaki take, Gida ya koma ya dauko Muhibba?
Yamiko mata ita, Ga 'yarki. Ta amsheta. Yagana
tace, yarinyar tana kama da ku. Abba ya ce, "Ai
'yarmu ce, suka yi mata sallama suka fito. Ummi
da Bishira a tare gabansu ya fadi lokacin da suka
ga juna. Bishira ta kauda kai yayin da Ummi taja
baya daga mazaunin kusa da direban da ta nufa,
ya bude mata baya ta zauna tana rike da
yarinyar. Ya tada motar suka dauki hanyar tafiya
kowanne zuciyarshi da abinda take karantowa.
Ummi tunaninta Abba ya je ya zo da matarshi ne
don yanuna mata shi fa matarshi yake so. Ita ko
Bishira nata ganin wulakanci ne na karshe da ya
dauko ta yazo da ita gurin wannan karamar
yarinyar. Shi ko Abba addu'a ce a zuciyarshi
Allah ya hada masa kan matansa, sai kuma ya
soma tunanin ina zai soma zuwa? Nashi ganin in
ya kai Bishira gida ya sauke ya tafi kai Ummi bai
mata adalci ba. Amma ya kula Ummi tana fushi
kuma yaso ya lallasheta, yana cikin wannan
tunanin ya tuna dawayar nan. Ya kalli wayar a
gefanshi. Dan murmushi yayi da ya tuna lokacin
da ta dangwarar masa da wayar don ya ce ta
matarsa ce. Yanayin yanda Ummin ke nuna
kishinta yana birge shi, koda bata sonshi tana
kishinshi sannan bata masa raini ko rashin
kunya. Kofar wani gidan saida gasassun kaji da
ire-iren kayan kwalam ya tsaya. Ya kalli Bishira
Madam mu shiga ko? Ta ce, "A'a ni fa ba zan fita
ba, ya ce To bari in dawo, ya nufi ciki. 72.. Ta
waiwayo ta dubi Ummi, ta ce "Ba ni 'yata
fitsararriya. Ummi ta mika mata tare da cewa
nima ai ba cewa nayi a bani ba, ta ce "Kar dai ki
min rashin kunyaki bar ganin an jona ki da mijina
ki zata za ki hada sahu da ni. Ummi ta ce, "Sai
dai kada a kuma in dai batun hada sahu ne, kuma
ban damu don mijinki ba bai sona ba, tunda ni ina
sonshi. Bishira cikin daga murya ta ce, oho?
Dama sonshiki ke yi? Yanzun na gane da nufi aka
yi. To ki sani kin sai ma kanki masifa da bala'i.
Ummita ce, "Kin ga bala'inki can, daga nan
batakara magana ba ta bar Bishira na ta masifa.
Tundaki ka za6i ki auri mijina zan shayar da ke
ruwan dana sani. Sai kin gwammace zama a
kurkuku fiye da gidan mijina, daidai lokacin Abba
ya dawo da ledoji guda biyu. Bishira bata yi shiru
ba sai zagin Ummi take yi,"'Yar iska, 'yar daba...
tsawa Abba ya daka ma Bishira, tare da cewa ba
ki ji kunya ba da ki ke zaginta amma bata kula ki
ba? "Ta ce, "To ka ji abin da ta ce min ne? Tsaki
yaja tare da daukar wayar da ta aje yasa a ledar
Ummi, sannan ya tada motar. Kofar gidan su
Umma ya tsaya, Ummi wadda dama ta kosa tazo
gida, ta bude motar ta fada gida cike da takaici.
Ya kashe motar sannan ya dauki ledarta ya kalli
Bishira, Ina zuwa. Kala bata ce ba. Illa baki da ta
cije, kirjinta na yin wata irin suya. Ban da tana
tsoron Anty kada ta fasa zuwa gurin Dadynsu da
tuni ta shago Ummi ta nadi 'yan kayanta. Dakin
Umma ta shige, Ummar tana shirin fitowa Ummi
na shiga, ta ce kun dawo? Ummin ta hadiye 6acin
ranta."Eh, mun dawo Abba a ya shiga gaida
Umma sannan ya mika ma Ummi ledar, gashi kin
manta Ummi ta amsa tare da cewa, an gode.
Umma ta ce, "Me ku ka siyo in ce dai ka sai ma
Bishira? Ya ce, "Eh na sai mata, kaza ce fa
Umma ba wani abu ba". Ta ce, "To shi ke nan
maza ka koma gurin su, yace "To. Tana fita ya
kalli Ummi akwai waya a cikin zan kira ki, kuma
bana bukatar ki kashe min waya. Ummi ta ciro
wayar da sauri, ta dibe shi ba wayar matarka ba
ce? Ya ce, "Eh tata ce, ta mika mishi cike da
kunan rai, ga abinku ka kira ni da layin Umma. Ya
ce, "Ke ce za ki cigaba da rike ma mata
tawayarta, ba tare da ya jira jin me za ta ce ba
yana murmushi, Ummi ta kasa gane cewa ita ce
matarta shi. Ko kallon kazar bata yi ba illa dai
tayi duk wasu abubuwan da ta saba yi kafin ta
kwanta, sannan ta kunna wayar tana tsammanin
kira. 73..... Shi ko Abba koda yazo Bishira tana
ta mitar don tsohon wulakanci an zo da ita an
shanya ta, bai ce mata kala ba illa dai motar da
ya tada suka nufi gida. Gidan duk kaya saboda
bai maida ba da a ka gama fentin, ya dauki
tsintsiya ya share dakin, sannan ya shimfida
katifa ya fito inda take zaune bakin Rijiya.
Muhibba tayi bacci tana rungume a jikinta, ya ce
kawo ta, ta mike a fusace ta nufi dakin ba tare
data bashi 'yar ba. Ya bi bayanta, so kurum yake
ya lallasheta ba wai don tsoronta ba sai don
tausayinta, yasan mata kan kishi za su iya yin
'yar karamar hauka. Wasu ma sai sun yi babbar
kuma bai dace ana nuna kishinsa ba, shi kuma
yana nuna ko 'in kula a gare ta, gefen katifar ya
zauna ya lalubo hannunta ya rike cikin
nashi."Bishira!" ya ambaci sunanta cikin sanyin
murya, bata amsa ba kuma bata dube shi ba, ya
ci gabada cewa, "Bishira ban ga abin damuwa ba.
Ko damata uku a ka daura min aure da su bare
daya, inkin yi la'akari da irin son da nake miki ke
kin san Bishira ba kiyayya ta hada mu ba. Kina
manta wannan ne? Ta dago ta dube shi ta dan
soma saukowa, yayi murmushi har yau ban daina
sonki ba, ta sauke ajiyar zuciya, sannan ta turo
baki sai kace 'yar yarinya. To ai na sha jin a ana
cewa so daya ne tak, ya cehaka ne, ta ce "To
tsakanin ni da Ummi wa ke keyi wa? Da sauri ya
ce ke, ta ce Allah?Ya sake tausasa murya, haba
Bishira ya ki ke wannan zancen kema kin sani,
kuma don Allah na roki ki in muna tare ki daina
min zancen Ummi, ke kadai ce za6i na. Bishira
taji dadin wannan kalamai, don haka sukaci
namansu suka kwanta, ya bukace ta a nan masai
da ta ce kaje gurin Ummin mana. Ya ce, "Na ce
in muna tare bana son kina min zancenta. Sai dai
in kina son ci gaba da horon daki ke min ne.
Haba Bishira, ko tausayina bakya yi?An fi wata
uku kina haramta min halas dina. Kullum sai dai
ina azumi sai ka ce gwauro? Yajawota jikinshi, ya
rungume da kyar dai ya samu yadan rage
matsala, sai dai ita ma ya lura tayi missing
dinsa. Suna kwance har kusan sha daya saura
tuni ita tayi bacci, shi kam daman so yake tayi
bacci yakira Ummi. Ya mike yaje yayo wanka
sannan ya nufi dakinshi. Yaja katifarshi ya kai
dakin, sannan ya kwanta akai, ya kira Ummi
lokacin bacci ya soma figarta. Ringing din ne ya
farkar da ita, sai da ta kusa tsinkewa sannan ta
daga, kafin ta amsa sallamarshi sai da tayi wata
doguwar hamma.Ya ce, "Ke baccin ki ma ki ke
alhalin na ce zan kira ko? Ta ce, "Amma ka san
bacci ba ya jira in ya zo,ni kuma ba zan iya yiwa
bacci gardama ba". Ya ceto sarkin iya zance, yayi
nufin zolayar ta. Yanzun dai na soma tunanin kin
soma sona, gabanta ya fafi, sam bata son ya
gano hakan yanzu. Tafi son sai lokacin da shima
ya soma sonta. Ya katse mata tunani, hasashe
na haka ne? Ta ce, ko kusa, mene hujjarka da
fadin haka? Ya gyara kwanciya. Na farko naga
ana ta kishina, sannan tun da a kadaura aure da
ni sai ciwo ya kame kansa, kuma nalura kina ta
zumdin tarewa a gidana.Ya saki 'yar dariya,
yasan ya cika mata ciki da takaici, shiru tayi
nazari take wacce amsa zata bashi, ko dai wayar
zata kashe? Tamkar ya shiga zuciyarta, sai ya
ce.... 41 Tamkar ya shiga zuciyarta sai ya ce,
"Koda wasakada a kashe waya. Ranta ya sake
6aci, ta ce Ya Abba ka tafka kuskure da kayi
zaton ina sonka,sam ni bana wani kishinka. In
don ka ce wayar matarka ce na ce ka rike abinka,
sanin kanka ne ba ma shiri da matarka, kuma duk
abinda ka ce nata ne dole na guje shidon ba zan
dauki wulakanci ba. Batun ciwo kuma daka ce
tunda aka daura mana aure ka neme shi ka rasa
dama bani na dora makaina ba, kaima ina naka
hawan jinin ya tafi? Sannann kuma wane zumudi
na nuna na tarewa a gidanka, Ya Abba ka sani
yanda a ka tilasta maka aurena, to ni ma fa dole
tasa na hakura. Amma ka rike a ranka bana wani
sonka bani kamarina ina sonka, kalaman nata na
karshe sun burgeshi har sun sa shi yin da ya
sanin tsokale zancen. Sai kuma ya canza salo da
cewa, haka dai ki ka ce amma ina da ja mu dai
bar zancen, shin dazun kafin ki soma wannan
tunanin me ki ke yi? Ta danyi shiru tana
tambayar kanta. Dama mutumin nan haka ya ke?
Oh yanzun dabara zai min sai ya gano ko ina
sonshi dole, to kuwa bazai ji ba, ya katse ta da
cewa ban san ki da karya ba. Ta ce, ina tunanin
irin ukubar da zan sha a gidanka ne ta
wulakancin da zaka min, ya yi shiru zuciyarshi
tana cewa yarinyar nan ba ta san irinson da ka ke
mata ba ai ta ma dauke ka mugu kenan. A fili sai
ya ce, "Kuma fa kin yi tunani, Allah yabaki ikon
daukar ukubar da zaki sha tare kuma dajure
wulakancin da na tanadar miki goben Ummi. "Ya
fadi, wai dama da gaske wulakancin zai mata.
Gyara kwanciya kawai tayi bata kara cewa komai
ba, kuma bata da nufin cewa wani abu, yasa taji
haushi sosai, don haka sai ya tausasa muryarshi.
"Ummi kina ji na?" Uhm" Kurum ta ce, don ya
gane tana jin shi. Alkawari ta dauka ba zata sake
cewakala ba, tunda ya hanata kashe wayar. "Ba
ni da nufin miki..." Sai layin ya yanke daga
gefanshi, ta ce, "Gara ma haka". Tana kokarin
kashe wayar gaba daya kiranshi ya sake shigowa.
Tsaki taja kafin ta daga, kuma a ciki ta amsa
sallamarshi, sannan cikin murya mai kamar zata
rushe da kuka ta ce "Ya Abba ni fa bacci nake
son in yi". Ya ce, "Sam ba wani bacci da za ki iya
yoa sai tunani". Ta ce "To na ji, ina son yin
tunanin please".Ya ce, "Tunanin me za ki yi".
Cikin gundira ta ce,"Dole in yi tunanin yanda zan
kare kaina daga wulakancinka, don bana
tsammanin zan dauka" .Ya ce, "Wasa nake miki
fa." Ta ce, "Uhum, ban amince da cewa wasa ka
ke min ba, don na tabbata mu ba abokan wasa
ba ne".Ya ce, "To shi ke nan bari in bar ki kiyi
tunanin, amma tunanin yanda za ki faranta min
za ki yi". Muryar Bishira ce ta katse shi. "Oho! Ai
tun da na farka ban ganka ba na san ana nan
ana cin amanata". Ya kashe wayar da sauri, duk
da dai Ummi ta riga ta jiyo muryar Bishiran. Sai
dai bata fahimci me Bishirar take cewa ba,
ringingine tayi tare da dora filo a kirjinta, tunani
take yi wane irin zama za su yi? Koda bata da
amsa ta kudurce har abada ba za ta dauki
wulakanci ba, a shi ko a matar shi. Sai dai
alkawari ta dauka ba za ta musu raini ba,
matsawar ba su suka 6ullo da hakan ba. *
************************************** Shi ko
Abba rigima suka dinga yi da Bishira cikin tsohon
daren wai ya cuce ta ya kwanta da ita yazo yana
hira da wata banza. Kila ma ya saba kwanciya da
Ummin ne yau bai samu dama ba, Abba ya ce kin
so kanki in ki ka yimin wannan zaton, don ban
ta6a nemanki ba, kafinki shigo gidana, ko na
ta6a?"Ta ce, "Don ka san dai ni ba fuska". Da ya
gaji da iya korata ya rufe kofar ya koma can
dakin. 40. 74... Washegarin ranar, ga mamakin
Ummi tun misalin karfe goma jama'asuka cika
gidansu, a ka dora abinci. Can kuma saiga yaran
shagon Abba da dinkunan zannuwan daAlhaji
Babba ya sai mata.Ranar Abba bai shigo gidan
ba a waya ya kiraUmma suka yi magana, zuwa
karfe uku angama yiwa Ummi jeren dakin da yake
yana da girma yacinye komai tsaf.Fitar 'yan jere
babu jimawa sai ga Anty Farida dakannasu motar
tana da kaya tana biye da su, gadoda kujeru a ka
canzo mata.Suka jera mata sannan suka lodawa
motar na dasuka dauki hanya suka koma, Abba
kam yana gurinaiki amma zuciyarshi tana
gida.Fatanshi Allah yasa yana zuwa ya tarar an
kaimishi Umminshi, kawayen Bishira da
makotansu'yan jam'iyyarta duk sun shigo gidan
sun hadu saizugata suke yi tare da nuna mata
koda wasa kadata sakar ma Ummi fuska, kuma in
ta mata takamata ta duki 'yan kayanta.Suna
gidan a ka kawo Ummi, 'yan kawo Amaeyakam
suna jiyo habaici da zagin da su Bishira ke yi,don
haka suka ce kada a kai musu yarinyar.Inna
Saratu da Inna Harira suka ce ai kuwa sai
ankaita.Ba ko kunya Bishira ta zabga musu
harara lokacinda suka fada mata cewa ga
kanwarta sun kawomata, don Allah su zauna
lafiya tare da Aminci.In yarinyar tayi ba daidai ba
ta sata a hanya... takatse su cikin tsawa da
mikewa tsaye. "Don Allahku fice min daga daki
amanar kishiya? Har wai muzauna da aminci ku
ke cewa?Tayi 'yar dariyar yake "Kun yi kuskure,
ai batacanza daga sunan ta na kishiya ba, kuma
kowa yasan kishiya abokiyar gaba ce."Inna
Saratu ta ce, "Baiwar Allah jahilan mata sunesuke
yin irin wannan tunanin, amma ga masu ilimisuna
koyi da gidan mai tsira da Aminci
(S.A.W)ne".Bishira ta ce, "To kawai dai ki ce min
jahila ki huta,bari ku ji ba za n ba ku a 6oye ba,
zama ne za muyi shi na rashin mutunci, na kowa
ya iya allonshi. Don ina kishin mijina, kuma zan
nuna". Tirkashi! Lallai akwai daru kenan. To
masu karatu ku biyo ni cikin littafi na 4, kumana
karshe domin jin yadda za ta kasance atsakanin
Bishira da Ummi da kuma Oga kwata-kwata wato
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14