ya yafito shi da
hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce
Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba
ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan,
unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan.
Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya
kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira
a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn
Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau
dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin
yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun
zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar
masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke
giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan
mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba
shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama
zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma
ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da
akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan
karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan
aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike
da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa
samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe
wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d
wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko
ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna
shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna
shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna
da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai
gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr
kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma
kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya
wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko
me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za
ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake
ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam
in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu
bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn
Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta
sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na
tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin
motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora
tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda
ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta
mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su
xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi
dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi
ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa
aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su
aka shaida musu cewa mai wannan layin sun
samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm
aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun
rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma
xagawa bandaki tana kuka tana face
majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina
suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in
qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne
sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan
kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta
cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma
shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar
tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe
ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban
sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa
me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na
tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka
hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan
shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san
ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana
kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu
a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta
tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka
nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira
su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta
xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa
hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka
da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa
asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka
shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba
dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba
karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe
su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin
alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a
ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa
stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan
suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma
da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu
ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah
gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma
tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi
da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin
wayar,sai dai bata san inda ta saka sim din ba
sai wanda ta tsinto ne a ciki.ummi dai tayi shiru
ta miqa ma umma waya. kusan qarfe goma sha
daya wayar abba da umma ta taho da ita ta
soma qara,umma ta dauka.alhj ne ya ce ina
wayarki ina ta kira ana cemin a kashe?una tace,
a ku6e take gata ma a hannuna.yace to inata
kira.tace qila faduwan da tayi daxu ne ta samu
matsala.yace to dama zance ne ki dafa masa
ruwan xafi a xuba a flask dan uwan matansa xai
kawo mu yanxun a mota xai amsa ya kai.ta ce to
alhj wayn xai kwana gunsa?yace bashir na nan
kuma matarsa anyi anyi ta qi tafiya shi yasa na
haqura xan dawo dan ba na xauna gun su ba ko?
umma tace amma yaya jikin nashi?ya ce da sauqi
yanxu ma yana son shan tea ne.tace to xan hada
harda wayar tasa inya so ma dunga kiran shi
kafin gari ya waye.ya ce yauwa ki
bada.Alhamdulillah abba jiki ba matsala. Don hk a
ka sallamo shi zuwa gd.kai tsaye gdn su umma a
ka wuce d shi. A salin dakinsa a ka gyara a cikin
kwana nan 3 ya yi ras sannan ya koma shago.
Bishira kuwa lkcn mahaifinta ya ce maza ta koma
dakinta,tunda ga abn d ya samu mijinta.Sun
dawo hr da tafkeken injin Janareto wai yaron ba
ya son duhu. Sannan ga kayan kallo d
saraunsu.TabbasAbba ya ji dadin dawowar
iyalanshi,dn dama yana cike d bukatarsu. Ranar
yini suka yi gyaran gd ita da 'yan uwanta,sai byn
magrib sannan ya shigo d tsarabobi.madara
tatacciya da kaji. Ya dauki dansa cikin jin dadi
yana kallonta cike da so da kauna,Nayi missing
din ku da yawa.URFIN CIKI book 2 part 3
ZURFIN CIKI book 2 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:08
Ai bama shiri. shi ne fa ya kawo ni mkrntr kwana
dn kawai baya son ganina. Suka yi ta mamaki.
Can jimawa ya dawo, sun fito rakiyar 'yan
uwansu Safiyya da na Khadija, suka ganshi tsaye
yana danne- dannen waya. Ya taho ya gaida
iyayensu duka,sannan suka koma gefe d ummi,
ya ce Ni ma zan tafi. Ta ce, Ya Abba ko fa
gaisawa ba mu yi ba. Ta karkatar da kai,Cikin
raunin murya tamkar mai shawagaba,ta ci ga ba
da cewa Ya Abba su Umma ba wanda ya ce a
gaishe ni? Sai hawaye suka soma zuba.
Hankicinshi da ke hannunta tasa tana sharar
kwalla.Abba yana da matukar tausayin mace. Don
haka duk da tsanar da ya yi wa Ummi sai da ya
tausaya mata.Ya tausasa Murya. Sun ce in
gaishe ki sosai, za ki ga gyada mai gishiri,
Tsohuwa ta ce a ba ki.Umma ta miki miya, ta
kuma daka miki yaji. Ta ce Na gode, Alhj me
yasai min?ya ce kayan tea ne da lemun kwali. Ta
ce Na gode. Tana ci gaba da share hawaye. Ya
mike Zan tafi. yasa hannu cikin aljihu ya ciro kudi
ya mika mata, ta ce A'a ya Abba ka bar kudinka.
Ya ce Ba ni ne na baki ba,Alhj Karami ne ya ce in
ba ki. Ta sa hannu 2 ta amsa tare d godiya.Sun
raka shi kusa da Gate ita da su khadija,sai kuka
Ummi ke yi. Bayan sun dawo dakinsu ne ta zauna
tana duba kayan da ya lissafo mata,duk ta gani.
Sai kuma saitin sabulun wanka da manshi da
turaransa da hodarsa duk na (Aloe vera.) Shi
kuma bai fada mata ko daga wa ba,ko ba komai
ta dai yi murna sobada tana da 'yan kuraje a
fuska,tasan kuma za su mutu. Sai kuma audagar
mata,tayi dan murmushi. . Tunda Umma taji
sallamar Abba ya shigo dakin ta bar komai tazo
ta zauna tana son jin lbrn Ummi. Abba ya fahimci
Haka,dn haka sai ya boye mata cewa, Ummi na
kuka hr yanzun. Ya nuna mata ai Ummi ta
kwantar da Hankalinta,km tayi hnkl dn ya bincika
ya ji ana ta yabonta. Umma taji dadi Sosai,Sai da
ya fara zuwa gurin Ummu,sannan ya je gida.Ya
samu Bishira tana zaune tana aikin nata,wato
Kallo. Tun da ta dawo daga wankan gida tazo da
janareto da kayan kallo,shi kenan ta sanu abn
yi.Kullum tana gabn (TV)da ta shi da safe in ta
kokarta shi ne ta dafa ruwan tea ko wanka ba za
ta yi wa dan ba,sai lkcn d man injin ya kare. Ya
nufi gurin injin ya kashe,dif din da ta ji komai ya
tsaya shi ne yasa ta zabura ta mike tana fadin
Ba dai har man nan ya kare ba? Ta fito da niyar
dubawa.Abba ta gani tsaye gabn injin yana bn
tsakar gidan da kallo cikin takaici. Ta ce Baban
Walid kashe min injin kayi??Ya ce Eh na kashe dn
Allah dubi gidanki?kalli wanke-wanke kuda na bi
dubi tulin wankin kayan Fitsarin yaronki. Dubi
kicin dinki,kuma ko da bn shiga dakinki da
wannan falon da ki ke kallo ba.na tabbata da
wanda ki ka dauke ko tsinkw a cikin sa.Kila ma
ba ki yi Sallah ba. Ta ce Dan karashe ne fa ya
rage min in gama kallon in zo in yi aikin.Haushi
ya sake kana shi,Sai kurum ya shige daki.
Tsakuwar da ya dora kafa a kai tasa tsigar
jikinshi tashi,sam ya tsani ya shiga daki ya dora
kafa kan datti. Ya dawo yasa takalmanshi ya
shiga da su,Walid yana kwance tun kayan da ya
bar shi da su da safe sune a jikinshi yana ta
bacci cikin fitsarin da ya shafka wanda ba wata
leda da zata hana katifar ta jike. Ko wankan safe
ma ba a mishi ba kenan.A fili ya ce,",Inna lillahi
wa'inna ilaihinr raji'un. ya juya ya nufi shagi. Ita
kam sai ta kunna injinta ta karasa kallonta,
sannanta tashi ta dora girki.sai lkcn ta ma Walid
wanka. Ta dan dauraye kwanukan da za su ci
abnci,wai ta gaji sauran wanke-wanken sai gobe.
Fati ta shigo,Bishira ta ce Yauwa Fatima naji
dadin zuwanki.shuga dakina ki gyara min gado,ki
dan yo min shara. Fati ta ce To. Ta shiga ita ma
duk shegiyar darin ce gurin kuiyar aikin,dn haka
ta dan birbira ta fito ta ce ta gama. Bishira ta ce
Yauwa dan dauraye min kaya can na Walid. Nan
ma tasan sama ta shanya. Bishira ta ce Yauwa
ta ga abnci nan kici.sai ki dauki na Ummarku ki
kai mata. Har Fati ta kai waje,Bishira ta kwala
mata kira. ta ce,Zo ki tafi da wannan galan din
na man fetir kije shagon Babn Walid kice ya taho
mana da shi,dn man ya kare. Koda Fati ta same
shi da galan ta fada mishi sako ya ce Ba zan siya
ba,Maida mata galan din. Ta tafi,Shi kuma ya ci
gaba da mita a zcyrshi. Yana fadin Na daina
sayan man tunda ba za a bari sai dare a kunnan
ba.Gidan Ummanshi yaje,ba ta nan ma taje
barkar Haihuwa. Ko dakin Tsohuwa bai shiga
ba,ya zauna nan falonta.Ya za kula ya zuba
abncinshi ya ci.sannan ya dan huta sai ya fita
zuwa gidan su Ahmad. Cam ya samu wasu daga
cikin abokanshi suka shiga hira. Ranar dai Abba
bai je gida ba sai misalin sha daya ko daya shiga
bai nemi matar gidan ba,ya dibi ruwa ya yi wanka
sannan ya shiga dakin. Ya lalibo makunnan wuta
ya kunna,dn Nefa sun kawo wuta. Tana kwance
irn banzan kwanciyarta da ta iya,dakin sai tashin
wani irin wari yake kamar na ruma,kamar na
fitsari ko na datti.Ya kalli ko'ina kullin kaya ne na
wanki ne,na gaga ne ciki da guri.Ranshi ya
baci,Ya kuma dubanta ga wata kiba da ta tafka.
Tun da ta haihu ta zama rusheshiya,gashi bata
son kama jikinta.Tsaki yaja,sannan ya dauki fiko
ya fita. kan doguwar kujera ya jefa filo,ya kwanta
a gajiye.Amma me?sai ya ji dora gadon bayansa
acikin lema.Da sauri ya mike ya kunna wuta.Duk
fitsarin yaron ne a kan kujerun dakin,dn haka sai
ya nufi dakin da takw aje tarkace ya kunna
wuta,shi ma dai duk shirgi. . Ya share Ya
shimfida ta barma ya kwanta,a ranar ya dauri
aniyar maida dakin ya zama nashi din-din-dn.
Don haka washegari yasa a ka zo a kayi masa
fenti,ya siyo kati fa ya yar da zanin gado,dk wani
abu nashi sai da ya kwashe su. Kafin wata guda
ya maida dakinshi cikakken daki,ya zuba dk wani
abu da yake bukata. kafin ya fita kullum sai ya
gyara dakinsa fes. ita kuma sam bata zuwa
dakin,sai dai in yana da lalura yaje can ya sauke
ya dawo. kazantarta kam ta kai in da ta kai,tunda
hr kayan kashi tana zube su a cikin daki. Ya gaji
yaje ya samu Anty ya fada mata,hr gidan Anty
tazo ta zazzageta,ta tasata suka gyara gidan,
amma ko a jikinta.Washegari ta ci gaba da in da
ta tsaya. Sam babu wanda zai ganta ya ce
haihuwarta daya. ¤¤¤¤¤¤ ¤¤¤¤¤¤ UMMI yau
ba wanda ya kaita murna,domin yau dai an basu
hutu..Sai dai tunaninta zata ko iya kai kanta
gida? Sunyi ban kwana bata da kudin mota, dan
duk tayi taba su safiya kudin gurinta, amma ta ce
yau ko da qafa ne xata gida.sun fito wajan mkrt
wata maryam tana cema,ki tsaya mota xato da
xata kaimu cikin kn.ummi tace baxan jira ba.sai
ga abba kamar daga sama,tsoro ya kamata karya
ce ta xauna gidan abokin sa da yace.hanka linta
ya tashi cikin in ina ta gaida shi ya amsa.ya
shiga mkrtn jim kadan ya dawo.hakan ta sha
alwashin yau ko da shiya saita je gida.shi kam
ma ya manta yai mata wannan maganan ma.ya
sabi akwatinta suka je suka shiga mota. abba
mamakin natsuwan ummi yake yi, ko da yake
baxai ce ta natsu ba, qila lafawa tayi.tundaga
soro ta saki jakanta da bokin tayi ciki da
gudu,cikin kuka tana kiran ummanta.umma ta
share do min tsohuwa tana cikin gida,kada tace
tayi rashin kara,sai tsohuwa ne ta tashi da sauri
tana fadin oyoyo takwara.suka qungume juna
tace to menene kuma na kuka?umma ta fito nan
fa ummi taje ta rungume ta.sai umma ta doje
tace bubi shirme,sakar ni ni.tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin, . Tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin ganinki amma ki
gwasale ta? abba ya ce daman nasan ba
natsuwan da yarinyan nan tayi,har ina
yabonta.dubi yanda ta xubarda kayan a soro.to
xaki debo su.tsohuwa tace bari ni in debo mata
tunda kai baka da tausayi.laile umma taga
canji,do min ummi dai tunda ta dawo ko qofar
gida bata fita ba,sai ko in an aike ta.sannan
yanxu ba gudu da tsalle tsalle bare tsokana.ga
aiki har girki ita kema umma komai.alhj yana
shan shayi da safe,ummi ta yi sallama ta shiga.
can gefen su umma ta xauna,sannan ta gaida alhj
ta gaida umma wanda ta saka alhj agaba tana
masa fira.wannan qa'idan umma ne bata barin
mijinta shi kadai,in har yana gida.alhj yace
suwaiba kinga ummina ko?laile abba yayi namijin
qoqari. yarinya ta natsu.umma tace Allah ya
amsa addu'an mu ka duba tsayuwan daran da
muka dunga yi bayan tafiyan ta kan cewa Allah
ya kintsa mana ita.alhj yace hakane,ummi dai na
jinsu tana murmushi.can tace alhj anjima xanje
gidan inna saratu in gaishe ta. qanwan sahura ce
da ke aure a kabuga.ya ce to ummi, xanba
umman ki kudin mota ko? ummi ta ce,to na
gode.ta miqe ta fita ta bar mahaifanta cikin farin
ciki jin dadin natsuwarta, suna godiya ga Allah
mai shirya bayinsa.lkcn da ta shirya dan xuwa
kabuga.sai umma tace ki kwana dan bana san ta
fiyan yamma,kabuga da nisa.tace to sannan ta
dauki kayanta kala guda, sannan ta fito.har xata
wuce sai ta shiga gidan alhj qarami,sahura na
ganinta ta hade rai,daman daqar take amsa
gaisuwan ummi tunda ta dawo.ummi ta gaisheta
a ciki ta amsa,sam ummi bata damu ba,tace
umma ina fati?ta yatsine baki tace tana gidan
abba,tace to inta xo ki ce mata naje kabuga sai
gobe xan dawo.umman bashir tayi tsaki,tare da
cewa ni yar aiken ki ne?ita dai ta wuce.tun
dawowan ummi suke shiri da fati kamar me,ko
yaushe suna tare suna fira.ummi tana mata
labarin mkrtn su.ita kuma fati tana bata lbrn
saurayin da tayi fahad,da irin son da take
masa.ummi tace tab,ni ko xanyi saurayi nafi san
irin ya abba...... . fati ta dubeta da al'ajabi kina
nufin ya abba kike so?ummi ta xabura tana fadin
tir, ko a mafarki Allah ya kyauta.ina nufin mai irin
hirarsa da tsafta.fati ta qyalqyale da dariya tare
da cewa ai na xaci shi kike cewa,inko ya ji kici
duka ummi ta ce,ai ni ba ma da shi nake ba
tab,shi da yayi auran so?kusan ko yaushe
yanayin hiran tasu kenan.ummi tana tafe
wadansu samari suka yi ta binta, sun shawo
kanta ta tsaya da kyar,kuma har ta masu
kwatancen gidansu. kwanaki uku bayan haka tana
ki shingide kan kujeran dakin umma,misalin
takwas saura ma dare.krtn wani littafi take yi na
hausa da fati ta ara mata,sam ita bata taba krnt
irin littafin ba,amma fati ta ce mata ta karanta da
dadi sunan littafin NAGA TA KAINA na
(sodangi).kasance wan wannan ne karo na farko
da ta taba krnt lbrn soyayya,sai abin ya
birgeta.amma nata ganin gwarxon sojan nan xai fi
dacewa a ce abba ne, jefi jefi takan kalli abba da
ke xaune kan kujera kusa da umma suna wani
xance da bata jiyo su. 'Amma tasan ko me suke
tattaunawa mai mahimmanci ne a gare
su.sallamar wani yaro ne ya katse su,umma da
abba suka amsa mishi a lkc gudu.yace wai ana
kiran ummi a waje inji wadansu.da sauri abba ya
kalla yaron,sam ba xai ce me yasa xance yaran
ya fadar masa da gaba ba.sai ya lumshe ido
sannan ya kalli ummi wadda kunya ta rufe
kasancewar yau ce rana ta farko da aka soma yin
sallama da ita.umma wadda kullum fatanta ummi
ta samu miji,sai tayi murmushi,sannanta ce da
yaron kace tana xuwa.abba ya dube ta da sauri,
umma kin san ko su waye?ta ce, a'a.yace ya
kamata a san ko su wanene dan kin san bata da
kan gado,kowa ma sai ta jajibo kuma ma duk
nawa ummin take da har xata soma tsayawa da
samari?umma tace,to abba ai gara ta kama
dahir, tana qare sakan dire ba sai ayi mata aure
ba?yace gaskiya umma gara ta dan taba krt,dan
yanxu xamani ne na krt.umma tace,tayi acan a
dakinta.ta dubi ummi tasgi kije.ummi ta miqe ta
fita.abba ya miqe shi ma,umma bari dai in gani
ma su kamun kai ne? umma tace to.., . Sun
gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu
tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani
bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka
amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?
suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi
karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida
abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye
ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi
haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san
ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a
masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt
kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma
muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke
kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka
shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a
tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita
kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt
da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame
su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da
gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to
yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi
shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,
tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya
kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai
tace, ina ganin xai fi mu haqura
Showing 3001 words to 6000 words out of 41322 words
hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce
Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba
ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan,
unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan.
Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya
kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira
a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn
Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau
dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin
yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun
zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar
masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke
giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan
mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba
shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama
zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma
ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da
akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan
karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan
aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike
da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa
samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe
wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d
wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko
ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna
shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna
shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna
da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai
gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr
kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma
kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya
wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko
me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za
ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake
ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam
in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu
bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn
Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta
sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na
tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin
motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora
tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda
ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta
mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su
xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi
dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi
ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa
aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su
aka shaida musu cewa mai wannan layin sun
samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm
aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun
rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma
xagawa bandaki tana kuka tana face
majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina
suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in
qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne
sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan
kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta
cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma
shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar
tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe
ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban
sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa
me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na
tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka
hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan
shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san
ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana
kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu
a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta
tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka
nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira
su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta
xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa
hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka
da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa
asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka
shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba
dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba
karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe
su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin
alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a
ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa
stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan
suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma
da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu
ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah
gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma
tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi
da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin
wayar,sai dai bata san inda ta saka sim din ba
sai wanda ta tsinto ne a ciki.ummi dai tayi shiru
ta miqa ma umma waya. kusan qarfe goma sha
daya wayar abba da umma ta taho da ita ta
soma qara,umma ta dauka.alhj ne ya ce ina
wayarki ina ta kira ana cemin a kashe?una tace,
a ku6e take gata ma a hannuna.yace to inata
kira.tace qila faduwan da tayi daxu ne ta samu
matsala.yace to dama zance ne ki dafa masa
ruwan xafi a xuba a flask dan uwan matansa xai
kawo mu yanxun a mota xai amsa ya kai.ta ce to
alhj wayn xai kwana gunsa?yace bashir na nan
kuma matarsa anyi anyi ta qi tafiya shi yasa na
haqura xan dawo dan ba na xauna gun su ba ko?
umma tace amma yaya jikin nashi?ya ce da sauqi
yanxu ma yana son shan tea ne.tace to xan hada
harda wayar tasa inya so ma dunga kiran shi
kafin gari ya waye.ya ce yauwa ki
bada.Alhamdulillah abba jiki ba matsala. Don hk a
ka sallamo shi zuwa gd.kai tsaye gdn su umma a
ka wuce d shi. A salin dakinsa a ka gyara a cikin
kwana nan 3 ya yi ras sannan ya koma shago.
Bishira kuwa lkcn mahaifinta ya ce maza ta koma
dakinta,tunda ga abn d ya samu mijinta.Sun
dawo hr da tafkeken injin Janareto wai yaron ba
ya son duhu. Sannan ga kayan kallo d
saraunsu.TabbasAbba ya ji dadin dawowar
iyalanshi,dn dama yana cike d bukatarsu. Ranar
yini suka yi gyaran gd ita da 'yan uwanta,sai byn
magrib sannan ya shigo d tsarabobi.madara
tatacciya da kaji. Ya dauki dansa cikin jin dadi
yana kallonta cike da so da kauna,Nayi missing
din ku da yawa.URFIN CIKI book 2 part 3
ZURFIN CIKI book 2 part 3
Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:08
Ai bama shiri. shi ne fa ya kawo ni mkrntr kwana
dn kawai baya son ganina. Suka yi ta mamaki.
Can jimawa ya dawo, sun fito rakiyar 'yan
uwansu Safiyya da na Khadija, suka ganshi tsaye
yana danne- dannen waya. Ya taho ya gaida
iyayensu duka,sannan suka koma gefe d ummi,
ya ce Ni ma zan tafi. Ta ce, Ya Abba ko fa
gaisawa ba mu yi ba. Ta karkatar da kai,Cikin
raunin murya tamkar mai shawagaba,ta ci ga ba
da cewa Ya Abba su Umma ba wanda ya ce a
gaishe ni? Sai hawaye suka soma zuba.
Hankicinshi da ke hannunta tasa tana sharar
kwalla.Abba yana da matukar tausayin mace. Don
haka duk da tsanar da ya yi wa Ummi sai da ya
tausaya mata.Ya tausasa Murya. Sun ce in
gaishe ki sosai, za ki ga gyada mai gishiri,
Tsohuwa ta ce a ba ki.Umma ta miki miya, ta
kuma daka miki yaji. Ta ce Na gode, Alhj me
yasai min?ya ce kayan tea ne da lemun kwali. Ta
ce Na gode. Tana ci gaba da share hawaye. Ya
mike Zan tafi. yasa hannu cikin aljihu ya ciro kudi
ya mika mata, ta ce A'a ya Abba ka bar kudinka.
Ya ce Ba ni ne na baki ba,Alhj Karami ne ya ce in
ba ki. Ta sa hannu 2 ta amsa tare d godiya.Sun
raka shi kusa da Gate ita da su khadija,sai kuka
Ummi ke yi. Bayan sun dawo dakinsu ne ta zauna
tana duba kayan da ya lissafo mata,duk ta gani.
Sai kuma saitin sabulun wanka da manshi da
turaransa da hodarsa duk na (Aloe vera.) Shi
kuma bai fada mata ko daga wa ba,ko ba komai
ta dai yi murna sobada tana da 'yan kuraje a
fuska,tasan kuma za su mutu. Sai kuma audagar
mata,tayi dan murmushi. . Tunda Umma taji
sallamar Abba ya shigo dakin ta bar komai tazo
ta zauna tana son jin lbrn Ummi. Abba ya fahimci
Haka,dn haka sai ya boye mata cewa, Ummi na
kuka hr yanzun. Ya nuna mata ai Ummi ta
kwantar da Hankalinta,km tayi hnkl dn ya bincika
ya ji ana ta yabonta. Umma taji dadi Sosai,Sai da
ya fara zuwa gurin Ummu,sannan ya je gida.Ya
samu Bishira tana zaune tana aikin nata,wato
Kallo. Tun da ta dawo daga wankan gida tazo da
janareto da kayan kallo,shi kenan ta sanu abn
yi.Kullum tana gabn (TV)da ta shi da safe in ta
kokarta shi ne ta dafa ruwan tea ko wanka ba za
ta yi wa dan ba,sai lkcn d man injin ya kare. Ya
nufi gurin injin ya kashe,dif din da ta ji komai ya
tsaya shi ne yasa ta zabura ta mike tana fadin
Ba dai har man nan ya kare ba? Ta fito da niyar
dubawa.Abba ta gani tsaye gabn injin yana bn
tsakar gidan da kallo cikin takaici. Ta ce Baban
Walid kashe min injin kayi??Ya ce Eh na kashe dn
Allah dubi gidanki?kalli wanke-wanke kuda na bi
dubi tulin wankin kayan Fitsarin yaronki. Dubi
kicin dinki,kuma ko da bn shiga dakinki da
wannan falon da ki ke kallo ba.na tabbata da
wanda ki ka dauke ko tsinkw a cikin sa.Kila ma
ba ki yi Sallah ba. Ta ce Dan karashe ne fa ya
rage min in gama kallon in zo in yi aikin.Haushi
ya sake kana shi,Sai kurum ya shige daki.
Tsakuwar da ya dora kafa a kai tasa tsigar
jikinshi tashi,sam ya tsani ya shiga daki ya dora
kafa kan datti. Ya dawo yasa takalmanshi ya
shiga da su,Walid yana kwance tun kayan da ya
bar shi da su da safe sune a jikinshi yana ta
bacci cikin fitsarin da ya shafka wanda ba wata
leda da zata hana katifar ta jike. Ko wankan safe
ma ba a mishi ba kenan.A fili ya ce,",Inna lillahi
wa'inna ilaihinr raji'un. ya juya ya nufi shagi. Ita
kam sai ta kunna injinta ta karasa kallonta,
sannanta tashi ta dora girki.sai lkcn ta ma Walid
wanka. Ta dan dauraye kwanukan da za su ci
abnci,wai ta gaji sauran wanke-wanken sai gobe.
Fati ta shigo,Bishira ta ce Yauwa Fatima naji
dadin zuwanki.shuga dakina ki gyara min gado,ki
dan yo min shara. Fati ta ce To. Ta shiga ita ma
duk shegiyar darin ce gurin kuiyar aikin,dn haka
ta dan birbira ta fito ta ce ta gama. Bishira ta ce
Yauwa dan dauraye min kaya can na Walid. Nan
ma tasan sama ta shanya. Bishira ta ce Yauwa
ta ga abnci nan kici.sai ki dauki na Ummarku ki
kai mata. Har Fati ta kai waje,Bishira ta kwala
mata kira. ta ce,Zo ki tafi da wannan galan din
na man fetir kije shagon Babn Walid kice ya taho
mana da shi,dn man ya kare. Koda Fati ta same
shi da galan ta fada mishi sako ya ce Ba zan siya
ba,Maida mata galan din. Ta tafi,Shi kuma ya ci
gaba da mita a zcyrshi. Yana fadin Na daina
sayan man tunda ba za a bari sai dare a kunnan
ba.Gidan Ummanshi yaje,ba ta nan ma taje
barkar Haihuwa. Ko dakin Tsohuwa bai shiga
ba,ya zauna nan falonta.Ya za kula ya zuba
abncinshi ya ci.sannan ya dan huta sai ya fita
zuwa gidan su Ahmad. Cam ya samu wasu daga
cikin abokanshi suka shiga hira. Ranar dai Abba
bai je gida ba sai misalin sha daya ko daya shiga
bai nemi matar gidan ba,ya dibi ruwa ya yi wanka
sannan ya shiga dakin. Ya lalibo makunnan wuta
ya kunna,dn Nefa sun kawo wuta. Tana kwance
irn banzan kwanciyarta da ta iya,dakin sai tashin
wani irin wari yake kamar na ruma,kamar na
fitsari ko na datti.Ya kalli ko'ina kullin kaya ne na
wanki ne,na gaga ne ciki da guri.Ranshi ya
baci,Ya kuma dubanta ga wata kiba da ta tafka.
Tun da ta haihu ta zama rusheshiya,gashi bata
son kama jikinta.Tsaki yaja,sannan ya dauki fiko
ya fita. kan doguwar kujera ya jefa filo,ya kwanta
a gajiye.Amma me?sai ya ji dora gadon bayansa
acikin lema.Da sauri ya mike ya kunna wuta.Duk
fitsarin yaron ne a kan kujerun dakin,dn haka sai
ya nufi dakin da takw aje tarkace ya kunna
wuta,shi ma dai duk shirgi. . Ya share Ya
shimfida ta barma ya kwanta,a ranar ya dauri
aniyar maida dakin ya zama nashi din-din-dn.
Don haka washegari yasa a ka zo a kayi masa
fenti,ya siyo kati fa ya yar da zanin gado,dk wani
abu nashi sai da ya kwashe su. Kafin wata guda
ya maida dakinshi cikakken daki,ya zuba dk wani
abu da yake bukata. kafin ya fita kullum sai ya
gyara dakinsa fes. ita kuma sam bata zuwa
dakin,sai dai in yana da lalura yaje can ya sauke
ya dawo. kazantarta kam ta kai in da ta kai,tunda
hr kayan kashi tana zube su a cikin daki. Ya gaji
yaje ya samu Anty ya fada mata,hr gidan Anty
tazo ta zazzageta,ta tasata suka gyara gidan,
amma ko a jikinta.Washegari ta ci gaba da in da
ta tsaya. Sam babu wanda zai ganta ya ce
haihuwarta daya. ¤¤¤¤¤¤ ¤¤¤¤¤¤ UMMI yau
ba wanda ya kaita murna,domin yau dai an basu
hutu..Sai dai tunaninta zata ko iya kai kanta
gida? Sunyi ban kwana bata da kudin mota, dan
duk tayi taba su safiya kudin gurinta, amma ta ce
yau ko da qafa ne xata gida.sun fito wajan mkrt
wata maryam tana cema,ki tsaya mota xato da
xata kaimu cikin kn.ummi tace baxan jira ba.sai
ga abba kamar daga sama,tsoro ya kamata karya
ce ta xauna gidan abokin sa da yace.hanka linta
ya tashi cikin in ina ta gaida shi ya amsa.ya
shiga mkrtn jim kadan ya dawo.hakan ta sha
alwashin yau ko da shiya saita je gida.shi kam
ma ya manta yai mata wannan maganan ma.ya
sabi akwatinta suka je suka shiga mota. abba
mamakin natsuwan ummi yake yi, ko da yake
baxai ce ta natsu ba, qila lafawa tayi.tundaga
soro ta saki jakanta da bokin tayi ciki da
gudu,cikin kuka tana kiran ummanta.umma ta
share do min tsohuwa tana cikin gida,kada tace
tayi rashin kara,sai tsohuwa ne ta tashi da sauri
tana fadin oyoyo takwara.suka qungume juna
tace to menene kuma na kuka?umma ta fito nan
fa ummi taje ta rungume ta.sai umma ta doje
tace bubi shirme,sakar ni ni.tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin, . Tsohuwa tace haba
suwaiba yarinya tana dokin ganinki amma ki
gwasale ta? abba ya ce daman nasan ba
natsuwan da yarinyan nan tayi,har ina
yabonta.dubi yanda ta xubarda kayan a soro.to
xaki debo su.tsohuwa tace bari ni in debo mata
tunda kai baka da tausayi.laile umma taga
canji,do min ummi dai tunda ta dawo ko qofar
gida bata fita ba,sai ko in an aike ta.sannan
yanxu ba gudu da tsalle tsalle bare tsokana.ga
aiki har girki ita kema umma komai.alhj yana
shan shayi da safe,ummi ta yi sallama ta shiga.
can gefen su umma ta xauna,sannan ta gaida alhj
ta gaida umma wanda ta saka alhj agaba tana
masa fira.wannan qa'idan umma ne bata barin
mijinta shi kadai,in har yana gida.alhj yace
suwaiba kinga ummina ko?laile abba yayi namijin
qoqari. yarinya ta natsu.umma tace Allah ya
amsa addu'an mu ka duba tsayuwan daran da
muka dunga yi bayan tafiyan ta kan cewa Allah
ya kintsa mana ita.alhj yace hakane,ummi dai na
jinsu tana murmushi.can tace alhj anjima xanje
gidan inna saratu in gaishe ta. qanwan sahura ce
da ke aure a kabuga.ya ce to ummi, xanba
umman ki kudin mota ko? ummi ta ce,to na
gode.ta miqe ta fita ta bar mahaifanta cikin farin
ciki jin dadin natsuwarta, suna godiya ga Allah
mai shirya bayinsa.lkcn da ta shirya dan xuwa
kabuga.sai umma tace ki kwana dan bana san ta
fiyan yamma,kabuga da nisa.tace to sannan ta
dauki kayanta kala guda, sannan ta fito.har xata
wuce sai ta shiga gidan alhj qarami,sahura na
ganinta ta hade rai,daman daqar take amsa
gaisuwan ummi tunda ta dawo.ummi ta gaisheta
a ciki ta amsa,sam ummi bata damu ba,tace
umma ina fati?ta yatsine baki tace tana gidan
abba,tace to inta xo ki ce mata naje kabuga sai
gobe xan dawo.umman bashir tayi tsaki,tare da
cewa ni yar aiken ki ne?ita dai ta wuce.tun
dawowan ummi suke shiri da fati kamar me,ko
yaushe suna tare suna fira.ummi tana mata
labarin mkrtn su.ita kuma fati tana bata lbrn
saurayin da tayi fahad,da irin son da take
masa.ummi tace tab,ni ko xanyi saurayi nafi san
irin ya abba...... . fati ta dubeta da al'ajabi kina
nufin ya abba kike so?ummi ta xabura tana fadin
tir, ko a mafarki Allah ya kyauta.ina nufin mai irin
hirarsa da tsafta.fati ta qyalqyale da dariya tare
da cewa ai na xaci shi kike cewa,inko ya ji kici
duka ummi ta ce,ai ni ba ma da shi nake ba
tab,shi da yayi auran so?kusan ko yaushe
yanayin hiran tasu kenan.ummi tana tafe
wadansu samari suka yi ta binta, sun shawo
kanta ta tsaya da kyar,kuma har ta masu
kwatancen gidansu. kwanaki uku bayan haka tana
ki shingide kan kujeran dakin umma,misalin
takwas saura ma dare.krtn wani littafi take yi na
hausa da fati ta ara mata,sam ita bata taba krnt
irin littafin ba,amma fati ta ce mata ta karanta da
dadi sunan littafin NAGA TA KAINA na
(sodangi).kasance wan wannan ne karo na farko
da ta taba krnt lbrn soyayya,sai abin ya
birgeta.amma nata ganin gwarxon sojan nan xai fi
dacewa a ce abba ne, jefi jefi takan kalli abba da
ke xaune kan kujera kusa da umma suna wani
xance da bata jiyo su. 'Amma tasan ko me suke
tattaunawa mai mahimmanci ne a gare
su.sallamar wani yaro ne ya katse su,umma da
abba suka amsa mishi a lkc gudu.yace wai ana
kiran ummi a waje inji wadansu.da sauri abba ya
kalla yaron,sam ba xai ce me yasa xance yaran
ya fadar masa da gaba ba.sai ya lumshe ido
sannan ya kalli ummi wadda kunya ta rufe
kasancewar yau ce rana ta farko da aka soma yin
sallama da ita.umma wadda kullum fatanta ummi
ta samu miji,sai tayi murmushi,sannanta ce da
yaron kace tana xuwa.abba ya dube ta da sauri,
umma kin san ko su waye?ta ce, a'a.yace ya
kamata a san ko su wanene dan kin san bata da
kan gado,kowa ma sai ta jajibo kuma ma duk
nawa ummin take da har xata soma tsayawa da
samari?umma tace,to abba ai gara ta kama
dahir, tana qare sakan dire ba sai ayi mata aure
ba?yace gaskiya umma gara ta dan taba krt,dan
yanxu xamani ne na krt.umma tace,tayi acan a
dakinta.ta dubi ummi tasgi kije.ummi ta miqe ta
fita.abba ya miqe shi ma,umma bari dai in gani
ma su kamun kai ne? umma tace to.., . Sun
gama gaisawa kenan sai ga abba ya fito.ganinsu
tsaye da ummi sai ya tsinci kanshi cikin wani
bacin rai.ya isa gun ya musu sallama, suka
amsa, sannan suka gaisa.yace daga ina kuke?
suka dube shi dayan ya ce lfy dai ko? ummi tayi
karaf ta ce yayana ne.anan suka sake gaida
abba.bai amsa ba, sai ma cewa yayi na tambeye
ku kai ma kana tambayana,wai lfy? suka ce,kayi
haquri,nan suka gabatar da sunansu.mai san
ummi shine nazir, abokinsa kuma sagir. sun 3a
masa cewa dukkansu daga kabuga suke.yace krt
kuke ko kasuwanci? sagir yace,eh krt muke,amma
muna taba kasuwanci a shagon mahaifinsa da ke
kwari.abba ya dan yi jim,sannan yace to kai ka
shirya aure ne?nazir yace eh to, nasan dai kafin a
tashi yi mata aure na shirya.abba ya ce, to ita
kam krt xata yi, kuma c ma buqatan ta hada krt
da soyayya. ya dubi ummi da fatan xaki sallame
su.ya juya gida.sagir ya ce, wannan wanki ne da
gaske? ummi tace qwarai kuwa. nazir ya ce to
yanxu ya kenan? kin ji abin da ya ce.ummi yayi
shiru tana tunani, ita fa basu kwanta mata rai,
tun randa ta hadu dasu,sam basu iya saka kaya
kalar yadda ya abba ke sawa ba.dan haka sai
tace, ina ganin xai fi mu haqura
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2 Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14