ce Gidan ango ne shiru, an bisu sun
ce sun fasa. To shi ne na ce me zai hana a daura
da da Bashir? 49... Umma ta ce a daura da Abba.
Ya ce, "Haka ma Aminu ya ce. To ni ban ga
Abban ba ma, amma bari muje Allah yasa hakan
shi ne mafi alkairi". Take a nan a ka daura auren,
Habiba da Idris Alhaji Babba ya kirgo sadaki ya
mika. Alhaji Karami Waliyinta ya amsa, mutane
na ta al'ajabin yanda lamarin ya sauya. Umman
Bashir kuwa Bashir din ne ya shiga gidan hankali
a tashe yana fada mata cewa da Abba a ka
daura. Nan ko ta hau bala'i da zage- zage. Ummi
ko tunda ta jiyo guda na alamta mata an daura
aure, sai ta birkice ta shiga kowa da
numfashinta. Fati da ke kusa da ita tana
lallaminta ita ce ta kwala ihu, ba shiri aka yi
asibiti da Amarya. Fati ta shiga gidansu da kuka,
nan ta taras Ummansu tana bala'i sai lokacin ta
ji da Abba a ka daura. Ta ce da Ummar su to
menen ba shi ke nan ba? Umma ta hau zaginta
tare da cewa, kar ki ga kin yi aure sai in miki
shegen duka, Fati dai ta fice ta bar gidan. Sam
Umma bata ji dar da ciwon Ummi ba, wannan
karon don haka ma bata bi su Asibiti ba, da
kanwarta Saratu a ka tafi. Likitan yayi ta fada
lokacin da yake yi mata allurai, a kuma bata gado
Umma ci gaba tayi da kula da bakinta. Yayin da
zuciyarta take fara kar, ta sani kuma tayi Imani
Allah ba ya tozarta addu'ar bawansa, matsawar
bawan yayi hakuri tare da dogewa. Haka nan in
baka samu biyan bukatarka nan duniya ba lallai
gobe kiyama zaka tarar da abinka. Ta jima tana
rokon Allah yasa 'ya'yan nata biyu su zam miji
da mata su haifa mata jikoki masu albarka. Suma
su Alhaji suna ta sallamar baki sai dai yanzun ba
wanda ya damu ya gani irin Abba. Fatanshi Allah
yasa Abban yayi farin ciki da wannan hukunci da
suka yanke. Salis kuwa burinshi ya zama shi ne
mutum na farko da zai wa Abba wannan albishir
sai dai ya kira layin Abba sama da sau hamsim
bai daga ba. Abinda bai sani ba shi Abba ma gida
ya bar wayar, haka suka gama dauke-daukensu
yayi hira da Jama'a da kuma iyayen Ango da
Amarya don jin ta bakinsu a kan yanda auren ya
juye zuwa na zumunci. Haka nan suka tafi ya
samu abin sawa a Taskar labarai, burinshi yanzu
shi ne ya je ya nemo angon. 28 50.....Abba kam
kofar dan Agundi ya yada zango gidan su Mansir
abokinsu, shi ne kurum cikin abokan Abba da bai
yi aure ba. Yana isa kofar gidan Mansur na
fitowa za shi daurin auren, wani dan layinsu a
Gwammaja suka gaisa. Abba ya ce "Bari in dan
kwanta a dakinka". Mansur cikin mamaki ya ce,
Lafiya? Abba ya ce lafiya lau. Yana kwance dakin
Mansur idanunshi suna kallon agogo, zuciyarshi
tana raya yanzun abar sonshi ta zama matar
Sahabi. Sai dai bai san dalilin da bugawar
agogon karfe sha daya daidai tazo gwame da
bugawar zuciyarshi ba. Zuciyarshi ta fada mishi
cewa wannan alamu ne na an kammala daurin
auren. Wasu hawaye ne suka biyo ta gefen
idanunshi suna sauka a kan filon. Yini zur yana
dakin in lokacin sallah yayi sai ya fito kofar dakin
yayi alwala har duhun Magriba ya gabato. Ya fito
tare da kulle dakin, don Mansur bai dawo ba,
kuma dama ya ce ba zai dawo da wuri ba. Gidan
nashi ba kowa lokacin da ya shiga, kai tsaye
dakinshi ya wuce, ban da idanunshi da suka kai
kan wayarshi ya manta ma yana mallakinta. Ya
kai hannu ya dauka, bai ji mamakin yawan
missed calls din da ya gani ba, kiran Salis ya
sake shigowa. A kasale ya daga, muryar Salis ta
ratsa dodon kunnanshi, fadi yake yana
maimaitawa Ango- Ango. Abba cikin sanyin
murya ya ce "Salis ya haramta a gare ka ka
zolaye ni a halin da nake ciki. Sanin kanka kai
kadai ne kasan yanayin da nake ciki". Salis cikin
zumudi ya ce, "Kana nufin ba ka sani ba?" Abba
ya ce, "Me?" Salis ya ce "To bani goron albishir in
sanar da kai". Abba ya ce, "Don Allah Salis kada
ka min karya". Salis ya ce, "Ina rantsuwa da
wanda ya yi mu Ummi matarka ce, da kai a ka
daura. Ina ka shige lokacin da al'amarin ya canza
salo?" Abba ya mike zumbur. "Ka fa rantse Salis!"
cikin dariya Salis ya ce, "Wai har yanzun ba ka
sani ba? To ka aje min goron albishir dina". Abba
yasa hannunshi a baki ya gatsa, zafin da ya ji ne
ya tabbatar da mishi da ba mafarki yake ba. 51...
Ai sai ya katse wayar ya zube yayi sujjada ya fita
tsakar gida yana furta "Alhamdulillah." Ruwa yaja
ya watsa ma jikinshim sannan ya yi alwala.
Sabuwar shadda ya saka kalar kunkumadi, ya
fesa turare sama da kala hudu. Hula da takalmin
bakake, ya nufi Masallaci, daga can za shi gidan
su Umma don jin karin bayani. Bayan sun idar da
Sallah, mutane suka yi ta masa murna, nan ya
hadu da su Alhaji kawai yau sai ya samu kansa
da kunyar Alhajin. Alhaji ya ce, "Ubana ina ka
shige duk yau?" Ya rasa me zai ce, sai in-ina
"Am...na kwanta ne bana jin dadi". Alhaji yayi
'yar dariya, "Kai dai ka ce kana taya kanwarka
fushi don mun ce ba zamu daga aure ba, to ba
mu daga ba amma Allah cikin ikonsa ya sauya
lamarin". Abba tamkar bai san komai ba, ya ce
"Alhaji me kuma ya faru?" Alhaji Karami ya
karaso gurin su yana cewa, "Kai Abba ina ka
shige ne?" Abba ya dube shi "Nan dan Agundi na
shiga". Alhaji ya ce, "Oho, shi yasa aka yi ta
nemanka. To ka ji kuma yadda lamari ya sauya
ko?" Alhaji Babba ya amsa tare da cewa, "Shi ne
nake massa bayani, wato Abba iyayen yaron nan
Sahabi muka yi ta jiransu su zo gurin daurin
aure, wai ashe su sun fasa. Amma ba su shaida
mana ba har bin su fa nasa aka yi, gashi mun
tara jama'a kawai sai Aminu da Ummanka suka
ce a daura da kai, da ni na ce a daura da Bashir".
Dadi ya lullu6e Abba irin wanda bai ta6a ji ba,
Alhaji ya ci gaba da cewa, kayi hakuri mun kara
maka nauyi ba tare da mun ji ra'ayinka ba". Abba
cikin matukar murna ya ce, "Haba, ai ko ba 'yar
uwata ba ku ka daura min aure da ita zan aminta
bare jinina. Nagode". Sun ji mamakin yanda Abba
yayi murna, duk da sun san biyayya irin tashi ba
zai 'ki ba, tare suka rankaya gidan su Umman, so
kurum yake yaga Ummi. Ba mutane sosai, don
haka har ciki ya kutsa, sai dai suna hada ido da
Umma sai ya ji nauyinta, ta fada da fara'a. "Ina
ka shige Abba?" Yayi dan murmushi, ta ci gaba
"Sai kuma ka ji yanda abu ya kasance?" Ya ce,
"Na ji Umma, Allah yasa haka shi ne alkairi". Ta
ce, "Amin, Insha Allahu". Tamkar ya tambayi ina
Ummin, amma ya kasa. Umma ta ce "A baka
abinci ko?" sai lokacin ya tuna da batun abinci,
amma baya gabanshi, ya ce "Na koshi Umma".
Ta ce, "To ga na 'yan asibiti can in kayi isha'i".
Da sauri ya ce "Wa ke asibiti kuma?" Ta ce,
"Ummi ce, ko 'yan daurin auran ba su watse ba
don ka ji yarintar nan ta hau farin suma don
haushi ko leka su ban yi ba. Tana can it da
Saratu sai Tsohuwa da ta matsa yanzun Alhaji
Karami ya kai ta". Jikin Abba ya yi sanyi, kenan
tsabar rashin sonshi ne ya saka Ummi suma? Ya
ce Umma bani abincin asibitin. Sai da yaje
gidanshi ya dauko dan mukullin motar, a
zuciyarshi yana tambayar kanshi ina kuma
Bishira tayi ne? Zai bude motar kenan muryar
Bashir ta dakar da shi, "Kaci nasarar samun furen
zuciyata, amma ka sani ka kulla abota da rashin
zaman lafiya a novels / ZURFIN CIKI book 3 part 7
ZURFIN CIKI book 3 part 7
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:33
kulla abota da rashin zaman lafiya a gidanka". *
52..A fusace abba ya dubeshi"xansa yan sanda
su rufe min kai inhar zaka cigaba da kiran matata
da furen zuciyarka,rashin zaman lfy kake cewa?
An dade ba'ayi yaki abgdn ba kullum,bashir yace
oho dai ni zanta zuga umma abba yaja tsaki
tareda shigewa motarshi. Bashir yashiga gdnsu
inda su ummanshi dasu bishirabke zaune jugum
jugum tamkar masu zaman makoki,bishira tabi
bashir da kallo lkcn dayace ga ya abba ya can a
waje yashiga mota ya kure wanka,kila ma asibiti
zaije ana fada maku yanaso kuna wani tilasta shi
akayi,bishira cikin dasahhshiyar murya tace aiko
da bala'i don ko bazan yarda ba,umman bashir
tace sha kutuminki bishira,barni dasu zan
maganinsu, bishira tafita fuu,amma saidai. Kafin
ta isa gurin motar tuni ya, Cilla yabar mata
hayaki. Da innna saratu kanwar umma ya soma
cin karo a asibitun suka gaisa,tace ashe kuma
haka abu ya zama? Yace eh"nima dana dawo
dazu nasamu lbrin,tace Allah yasa hakan shine
mafi alkhairi,abba yace ameen inna,ya mai jikin?
Tace dasauki,yace bacci take? Tace a'a ta farka
tun kusan karfe uku,koda fatima ta fada mata
yanda abubuwa zuka zama,tayita yan koke
kokenta,gaban abba yafadi****tabbas ummi ba
son shi take ba inba hka ba meye na kuka? Ya
kalli inna bari in karasa,tace to kaje tshuwa na
ciki,a ranshi yace jaraba road,yasan dai ko yane
sai tshuwa tayi mishi surutu,yana tura kofar
tareda salama suka hada ido da ummi,sun kure
juna da kallo,kowanne nason ya fahimci ya dan
uwansa yadauki abin"tshuwa ta katse su dacewa
to zakin fama sai ynz kaga daman zuwa? Ya
dubeta eh" ai eh ace? To me kikeso ince,tace to
madalla ai na dade da sanin halinka,kuma da ace
iyayenku sunyi shawara dani lallai da baza suyi
wanna hadin ba Domin na tabbata kai zaka
karasa takwara don baka kaunarta, haushi ya
cika abba abba yana kallon tsohuwa yana tuna
amsar data dace da ita, ummi kuwa tsura mishi
ido tayi tana son jin me zaice,yace kamar kin
sani,tace ahaf shiyasa tausan yar nan kebani
tausayi, ta soma matsar ido,yace nima yakamata.
ki tausayamin tnda cusa min ita akayi,ummi
takoma ta kwanta lakwas tareda hakikancewabl
kalaman abba sako ne zuwa gareta,matar cushe
kuma bata daraja,to inaso kasan wani abu
guda,duk randa naji wani abu daidai da
wulakanci, toba kaiba har iyayenka saisun san
naje makura. 52..Dazun nake gaya masu basun
hada kai sun kulla auren nan ba,duk randa suka
kuskura sukazo min da batun warwareshi saina
basu mamaki,abba ya tabe baki tareda kallon
ummi wadda takasa jurewa tashiga rera kuka,ya
isa gaban gadon,"jikin ne ummi? Tayi shuru,kinci
abinci? Nan ma ta share,sai kurum ya nufi wurin
likitan zuciyarshi na kuna bako shakka kukan kin
shi ummi keyi,sun zo da likita ya shiga yimata
fadan kukan da takeyi,a cewar likitan kukan illa
ne ga lafiyarta,tshuwa ta kalli likita dan nan dole
ta koka a dauke ka ahadaka da wanda baya
kaunarka"abba cikin takaici yace subhanallla! Don
Allah tshuwa kibarni inji da abinda ke
gabana,tace ina ruwana da abinda ke
gabanka,likita yayi dariya yace mama yakamata
ki koma gd haka,abba yace bari inkaita
indawo,tace ban binka da can dani kazo? Abba
yace nahuta,likita yayi dariya,da kyar suka lallaba
tshuwa ta tafi da inna saratu,abba yaja kujera ya
zauna gaban gadon,bayan fitan likita Idanu ya
zuba ma ummi,godiya yake ma Allah a zucin shi
daya amsa addu'ar shi yabashi abar sonshi,itako
kai ta dukar a ynz takasa tantance kukan farin
ciki take ko takaicin kalaman ya abbanta? Wani.
Dan zare dake jikin hijabinta take wasa dashi,a
zuciyarta kuma tambayoyi ne da fuska data jefa
masa su,ya katse ta kinci abinci? Ta daga kai
alamun eh" yace to yakamata ki dangana da
kukan haka kisani ni kaina da ina nan bazan bari
su alhji su daura maki aure da wanda bakiso ba.
53..Da sauri ta kalleshi,yace. amma inkin yi hkr
zansame su zamu san yadda zamuyi,ta lumshe
ido a zuciya tace tab! Ai rabamu sai mutuwa,zan
juri duk wani ki dazan gani daga gareka,ya
katsxeta kina zance a zuci fadi abnd kikeson
cewa,tayi tagumi tareda kallonshi,ya abba yakanfi
dacewa sa dan sanda ne ba dan jarida ba,sbd
yanada saurin nazartar mutum,to amma meyasa
yakasa gane tana son shi? Yayi murmushi,zanso
inji abnda kikeb saqawa azuciyarki ko kinn samo
mafita ne? 29. Zancan mafitar nan tana bata
haushi, don haka saita canza zancen da cewa,
tambaya zan maka guda biyu, ya dan yi shiru.
Nazari yake, wace irin tambaya zata masa? Kila
zata tambaye shi ne ko zai amince ya sahale
mata auranshi, ya dubeta amsa daya zan ba ki in
kin yarda, ta ce To dama zance ne ya ka ji
lokacin da labarin sauyawar lamari ya zo gareka?
Ya kura ta da ido, ya tambayi kansa a zuciya, me
yasa take son ji@ yayi dan yake, yi tambayarki ta
gaba, ta tsura mishi ido. Yanzun yaya za ka yi da
maganar Zainab? Ya yi 'yar dariya, wacce amsa
ki ke so a ciki? da sauri ta ce ba ni wannan
amsar. Ya ce, "Kiin manta ni mijin mace hudu ne?
Ta zaro ido kamar ya ya? Ya yi kokarin danne
dariyarsa, sakamakon yanda ya ga ta zarana. Ya
ce, "Ina nufin bayan Zainab har da wata, Ummi ta
hade rai sannan ta zame ta kwanta cike da dana
sanin tambayar. Abba ya yi mamakin kishin
Ummi gare shi, ita da ba sonshi take ba? Ko da
yake an ce mace ko bata son namiji in dai mijinta
ne ta tsani ta ganshi da wata. Duk da haka ya ji
dadin yanda ta nuna kishinta a kanshi, da ya tuna
da Bishira ya ce tab, wata fitinar tana can tana
jirana yau. Sam Ummi bata kara magana ba, shi
kam Abba waya ma yake tayi Inna Saratu ta
dawo, don haka ya mike ya kalli Ummi. Zan tafi
ba tare da ta dago ba ta ce, sai anjima. Ya tafi
yana waiwayonta bayan ya wa Inna Sallama. Kin
shiga gidanshi ya yi sai kusan sha biyu a nufinshi
lokacin Bishira tayi bacci, sannan yaje ya sai
mata wayar da layi don yasan tana son waya.
Kudinshi kenan ma ya kwashe ya sai mata, bai yi
wani motsin kirki ba don kada ta farka, ya bude
dakinshi ya shiga ya fito yana jan ruwan wanka
kenan ta fito daure da zani a kirji. Jikinta ko dan
kwali babu, gaban Abba ya fadi ta ce, "Munafukin
Allah, annamimi dama ashe abinda kuke shiryawa
kenan? To ka sani dole kasa ke ni don ba zan iya
zama da Ummi ba, Allah ya kiyaye in hada miji da
wannan 'yar yarinyar, tunda kai baka ga ai baya
ba". Ya sassauta murya, "Haba Bishira, wannan
abin fa Allah ya kaddaro za a yi haka, matar
murtum kabarinsa. Ta ce, "To wannan ajalinka ce
tunda wancan ya ki shi ne kai a ka cusa maka.
Ya bar jan ruwan ya kama hannunta suka nufi
dakinta, tana ta masifa. Ya ce, kibar maganar
yanzu dare ne duk makota suna ji za su yi, kuma
banga bain da zai sa ki daga hankalinki ba. Kin
san dai ina sonki ko? Ta yi shiru tana kallonshi,
ya ce ina zuwa. Yaje dakinshi wayar ya dauko
mata, ga wayarki. Ta ce, "Eh don ka toshe min
baki k? to bana so, ita wa ya san abinda ka sai
mata? Ya ce, ya ki ke wannan maganar? Ban sai
komai ba ko lefe ma tukunna. Ta mike tare da
jefa mishi kwalin wayar, Ga tsiyarka nan
matsiyaci, dole ka saka min da haka, tuni a ka
gaya min tsiyar talaka na tafe. Haushi ya kama
Abba ya dauki wayarshi ya tafi ya maida yazo ya
dau ruwanshi yayi wanka, yana jiyo kukanta da
duk zage-zagen da take yi. Shi kam katifarshi ya
fada tare da rungume fito yana tunanin ranar da
Ummi zata maye gurbin filon. 30. Har an tada
sallah a Masallaci lokacin da ya farka, ya jima
bai yi irin wannan baccin ba, da hanzari ya fito
ya nufi ban daki don alwala. Abin mamaki Bishira
ce zaune kan kujera a kofar dakinta, matar da sai
ta kai takwas bata farka ba, amma yau bala'in
kishi ya hanata bacci. Ta ce, "Eh na fito a ba ni
takardata na gama zama da kai, ko in da take bai
kalla ba ya ci gaba da abinda ke gabanshi, ya
nufi Masallaci yana jinta tana ina nan ina jira ba
zan zauna ba. Haba, gaskiya naji na tsani
yarinyar ashe mijina zata aura, tsaki ya yi ya
bude gidan ya fice. Har gari ya soma haske yana
cikin masallacin, tunanin zuwa gidan yake, daga
karshe dai ya fita da niyyar zuwa gidan
Ummarshi. Wata zuciyar ta tambaye shi da cewa,
tsoron ta ka ke ji ne? Kar ka zama soko dai a
gidanka. A fili ya furta cewa, tunda na bita ta
lalama ta ki, bari in koma mata ta zafin, ida din
me? Sai ya sauya hanya zuwa gida rai 6ace,
fuska daure ya shiga gidan, tana ta kai-kawo a
tsakar gida. Ta dumfaroshi sai ka ce sabon
kamun hauka, daga ganinshi ta dinfaroshi. "Ka
ban takardata ba ni ba zama da kai, tafiya zan
yi". Ya harareta "Sai da takarda za ki tafi? Lallai
ba ki ji tafiyar ba. To ba zan bada takarda ba,
don ki sani, sai dai in kotu za ki kai can Alkali ya
baki". Ta nufo shi da zummar shako masa kwala,
ya ce Kina ta6a ni sai na zane ki, in yaso ki tafi
da hujja". Ganin yanda Abba ya bude mata wuta
sai taja baya, Ka isa ka zane ni, ai da ka san ka
dake ni, don ko sai ka sha dauri. Ya nufi dakinshi,
wanka ya fito yayi sannan ya yi shirin tafiya aiki,
amma har lokacin tana nan, ga 'yarta ta tashi
daga bacci sai kuka take yi. Ta dauke ta ta goya,
ta shiga dakinta can kuma ta sauke 'yar tasa
kaya ta fito ta dauraye fuska da kafa ta goya 'yar
tasa kaya ta fito taja kofar tana fadin." "Tafiya
zan yi". Ta fito ta same shi yana goge gilashin
motarsa na gaba. Ta ce, Tafiya zan yi sai an
kar6ar min hakkina". Murmushi ya saki, sannan
ya kalleta, ta ina za ki bi in rage miki hanya? Ta
dawo ta duki motar, Ba zan shiga wannan
gwanganin motar ba, kai ne bakon mota. Kafi
kowa sanin daga gidan da na fito, ko motar zuwa
cefanen gidanmu tafi wannan tsarri. Ya ce.
"Gurinki ko? Ni ai bani da wadda ta fita tunda
bata gidan naku nike hawa ba. Sannan kuma
tunda ba za ki zo in rage miki hanya ba shi
kenan sai naga sammaci. Ya shiga motar ya
tasheta yayi gaba, ba tare da ya saurari abinda
take cewa ba. Ta isa gidansu cikin tashin hankali,
Hajiya Zainu ta saurare ta tsaf, sannan ta ce "Kin
dai ga abinda a ke fada miki, kina ganin ba zai
faru ba ke so ya rufe miki ido, to yanzu an zo
gurin. Bishira ta ce, "Ai na gane komai yanzun,
Momy nayi nadama. Ta ce, "To zan tsaya miki
matsalata Babanku, yana nan a gari na kuma san
za su zo iyayen Abba. Amma wannan karon shi
kanshi Babankun zan iya ja da shi, Bishira taji
dadi sosai, don kuwa duk son da ta ke wa Abba
yanzun kishi yasa ya koma 'ki. Gidansu Umma
yaje a gurguje suka gaisa, ya kwashe su da Alhaji
da Alhaji Karami zuwa asibiti, a motar nema ya
ke fada musu cewa Bishira ta tafi gidansu Umma
ta ce a kan me Abba, me ka mata? Ya ce, "Ban
mata komai ba, ya fada musu duk yanda aka yi.
Alhaji Karami ya ce, Sahura ke zugata, itama ai
kwana tayi bala'in. Don haka kada kaje bikonta,
Alhaji Babba ya ce, "Ba za a yi haka ba, da dare
kazo muje, Abba ya
Showing 30001 words to 33000 words out of 41322 words