so ko baya so,dn haka na
hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan
mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in
hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan.
Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice
jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8
ZURFIN CIKI book 2 part 8
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18
Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya
manta sam da batun motar da yazo da ita a
kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya
shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na
tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m
5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi
saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi
kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai
juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce,
Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina
da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata
tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin
ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi
nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole
ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da
hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan
neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana
kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta
suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya.
Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe
ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko
Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk
mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin
zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci
ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya
kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan
da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan
gidan,Musamman Umma wadda ta same ta
kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a
kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira
Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran
Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi
ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya
ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu
a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita
Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy.
Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a
dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati
Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi?
Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan
Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga
bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi
ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji
ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun
gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi
ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi.
ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari
in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da
mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta
ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin?
Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa
Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana
cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna
wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma
ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce
To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce,
Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance
ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake
yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya
daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce,
Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude
ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai
6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon
Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi
kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to
tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita
asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka
iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku
asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a
kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da
Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can
kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar
yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma
Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan
mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba
suka dauko shi. Bishira taso zuwa amma suka ce
ba wuri ta bar shi kawai. Asibitin kudi ne kuma
likita guda ne ya duba su. Ummi dai hawan jini
ne don ita a ka fara dubawa. Gado likitan ya
bata,sannan Abba ya shiga shima likitan ya ce
jininsa ya hau,amma ba kamar nata ba. Nan ya
roki likitan cewa kada ya fada ma iyayensu abnda
ke damunsa,ya rubuta mishi magunguna kawai.
Likitan ya ce Ba komai. Amma me ya ke
damunku kai da sister dinka ciwonku iri daya
kuma ya kama ku a lkc daya? Abba ya ce Ba
komai lalura ce kawai a ka kaddara ta same su
lkc daya.Da Abba ya fito sai ya ce ma su Alhj
Zazza6i ne. sai dai shi kanshi ya ji mmkn
ciwonsu iri daya. Yana jingine da bango a dakin
da a ka ba Ummi gado,yayin da Bashir ya tsaya a
gabn gadon Umma tana zaune a kan kujera. Alhj
krm d Bbba suka shigo tare da Likitan ya kalli
Abba Yarona kana bukatar bacci ga. Abba ya ce
To yanzun zan tafi gida. Ya iso kan Ummi wadda
a ka daura ma ruwa,ya ce ku barta ta huta bata
bukatar hayaniya,don haka ku rage daga cikin
dakin. Alhji ya ce, To mun gode. Suka tafi suka
bar Umma. A mota Alhj ya ce da Abba,ka fada a
wurin ainkan? ya ce, Eh abokin aikina ya kira ni
kuma na fada masa. Alhj ya ce,To shi
kenan,yanzun sai muje can gidanmu zaka fi
hutawa... .Yanayin aikinku ne ba ka samun bacci
ko? eh kurum Abba ya ce,amma shi yasan
tunanin Ummi ne ya ke hana shi bacci da
matsalolin da yake hangowa. Yinin ranar yasha
bacci,sai kusan 4 ya tashi ya yi Sallah,ya ji dadin
jikinshi. Bishira tana gidan Umman Bashir wai ita
da tazo jinyar miji,tana bata lbrn wai Abba bai
fada mata ba shi da lfy ba,ya kira Alhj yazo yana
ta min surutai wai mijina ya fita ban sani
ba,meye- meye? Umman Bashir ta ce, Da Allah
kyale su,don wani sabon iskanci ma wai Bashi ne
ke son Ummi. Bishira ta mike zumbur tare da
cewa, Bashir fa ki ka ce Umma? Hu'um,lallai da
wani abu. Bashi da ya tsani Ummi shi ne zai ce
yana sonta? Umma ta ce, Sannu 'yar albarja,ashe
kin fahimta,? Tabbas nasan ke za ki fahimta,to in
gaya miki Bashir ko yau da safe fa sai da muka yi
ta dashi. Dubi yadda Bashir ke min biyayya amma
yau ina fada yana fada. wai hr da ce min shi bai
ga wani mugun halin Suwaiba da nike fada
ba,tana min alkairi amma ni kullum ina binta da
sharri. Kai dai jin wannan zancan ka san ba yin
Bashir ba ne,don haka na ce masa ba komai
nasan ba yin ka ba ne. Bishira ta ce,Tabdi,Umma
sai kin tashi tsaye. Ta ce ke dai bari ai ina cikin
wani hali shi kanshi miji naki sai na nema masa
taimako. Don wannan ciwon nashi ban yarda shi
ba, kuma lkcn daya. Fati ta shigo gidan da
sallama,ta shiga dakinsu ta canza kaya. Umma
ta ce,sai ina? ta ce Ya Abba ne ya ce in zo in
canza kaya zamu je asibiti wurin Ummi. Bishira
ta mike ya farka ne? Ta ce Eh hr ya yi wanka da
sallah Umma ta ce Bari in same shi bai gama jin
sauki ba zai tafi wurin wata can kema banza
mara kishi kin taho jiki Na 6ari,Fati ta ce,Umma
don Allah ki daina irin wannan abubuwan,wlh
Umman su Ummi bata yin haka Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka ga . Bishira ta fita
tana fadin Ai Ummi yanzun ita ce uwar Fati, don
bata jin mgnr kowa sai ta Ummi,tunda ta dawo
mkrnt. Sun samu Tsohuwa ma hr ta shiga
mota,shi kuma Abba yana jingine a jikin Motar
yana sanye da shadda (Sky blue) Rigar 'yar 3
Quarter kanshi da hula. Bishira ta ce,Babn Walid
hr ka tashi? ya dube ta,sannan ya kai idanunshi
kan fati Shiga muje. Bishira taja baya Ina ba in
da za ni. Ya kalleta ke Kuma ke da wa? Wa ya
fada miki da ke nake? yaja tsaki. Ta iso Ummar
tasu Abba ka hakura mana da wannan tafiyar. Ta
ce Naji sauki Umma. Tsohuwa ta ce, Mai sunan
Malam ka shiga don Allah mu tafi. cikin sauri ya
fada mota suka wuce. Yana yi wa Umman nuni
da Hannu wai yana zuwa. Tsohuwa ta
ce,Kinibibin banza ne da wannan matar taka mai
sunan Malam kana bukata kara aure,me a ke da
kazamar mace? Abba ya ce, Tsohuwa sha
kuruminki zan sake aure,ke ce ma za ki bani, Ta
ce, Ni a wa zan shiga maka gaba a baka ku taru
kai da matarka ku halakata?Duk da Abba yana
jin jikinshi gim, sai da ya dar dara,sannan ya ce,
Sai ka ce ma su yankan kai? Tsohuwa kuma da
za ki ce na cika zcy yanzun ba ga mata nan ina
da ita ba tana kawo miki karan ina dukanta ne?
Tsohuwa ta ce Tabdi,ni yaushe ma wannan
guzumar matar taka zata zo guna da sunan kawo
min kara? Ban da ma haka ni bani shi da mara
kunya. Ya ce, sai Ummi ko? koda yake ita ai
takwararki ce shi yasa lkcn da tayi tata rashin
kunya ta zama 'yar lelanki. Tsohuwa ta ce ai
wannan ba kuciya ba ce? Yanzun ko kai ba ka fi
ta hankali ba.Abba da fati suka sa dry. suna isa
dakin suka samu Umma suna waya da Alhj,Ummi
kowa hr lkcn bacci take yi. Abba ya jingina da
bango yayin da Tsohuwa da Fati suka je suka
tsaya a gabn gadon. Sunyi Sallama da Alhj shi
ma ya kira ne ya ji ko Ummi ta farka. Ta ce
masa ba ta farka ba,kuma Likitan ya ce an fi son
tayi baccin. Nan suka gaisa tare da tambayar mai
jiki,Abba kallon Ummi yake,yau daya duk ta fyade
kmr ta yi sati,sonta da tsananin kaunarta ne
suka sake mamaye ko'ina na jikinshi. Ya kalli
Umma wadda ke tambayar nashi jikin, ya ce da
sauki. Sannan ya kalli Ummi tare da cewa Umma
wai dame Ummi ta fara? Umma ta ce kamar ya
ya? Ya ce mmkn ciwon Ummi nake,wai hawan
jini?Dama can bata da lfy ne? Tsohuwa ta amshe
da cewa, ko kai ai kasa mata hawan jini,irin
tsanar da ka mata Mai sunan Malam ai ta isa.
Abba ya ce Don Allah Tsohuwa ki daina mgnr
nan. Ya dubi Umma yana me kara maimaita
tambayarshi. Ta ce ko kusa ai kasan Ummi bata
cika laulayi ba ma,lalura ce dai yanzun bata ga
babba ba ta ga yaro,amma mafari daga yi mata
zancen aure shi kenan take ta kuka. Abba ya ce
to don Allah Umma ku barta da zancen nan,ina
krtn take so tayi kayanta,don gudun hawan jinin
nan kada yakw tashi akai-akai. Tsohuwa ta ce
Don kawai kada jinita ya hau sai a zura mata ido
kada tayi aure?ai ko lallai sai dai kada jininta ya
sauka. in ya hau,aure ya haifeta dole tayi shi,in a
kasarmu ce ta Zamfara wane ita. . Abba ya ce
Muje in kai ki gidan Tsohuwa. Ta ce ban tafiya,
sai naga dama Umma da fati suna ta musu dry.
Nan dai Abba ya fita yaje wurin likitan ya amshi
takardn maganin,dn da farko bai rubuta ba
magaungunan ba. Kwanan Ummi 3 a asibiti a ka
sallem ta. Abba ya kwashe su zuwa gida.
Saurayinta Sahabi zuwanshi 2, kuma sun je da
mahaifiyarshi. sai lkcn ne ma ta mishi kallon
tsaff,sam ita ba sonshi take yi ba,sai dai gara shi
da Bashir. Kuma ta lura Bashir din da gaske yake
yi. Domin kullum zai zo safe da yamma,haka nan
yakan dan tsaya hr yafi Abba wanda ke zuwa sau
daya hr tana cewa ina ma yadda Bashir ke nuna
tausayinshi a gare ta Abba ne. An shuri sati 2 da
sallamo ta kuma ta warke sarai,sai dai fa hr
yanzun Alhj yana nan kan bakanshi,ganin Bashir
na son takura mata sai ta daina fita. Abba ya
kira Basshir shagonshi wani yammaci,ya sake
fada masa ya rabu da Ummi sai dai yau da
lallashi yazo masa,. Ya ce Bashir ka ga
mahaifiyarmu bata sonka da ummi,dn haka ka
hkr ka nemi wata,na maka alwashin kashe ko
nawa ne dn yin hakan zai faranta ran Umma.
Bashir ya yi 'yar dry,sannan ya mike tsaye Ya
Abba kenan! kana tsammanin ni wawa ne?nasan
ba don Umma ka ke fafutukar in bar Ummi ba
kana yi ne don kana sonta. Gaban Abba ya
fadi,cikin saurin baki Abba ya ce,In ji wa ya fada
maka? Allah ya kiyaye. kai ka san Ummi kanwa
na dauke ta. Bashir ya kakki cikin idon
Abba,sannan ya ce,"Haba Malam,fadan da ka ke
da kalaman da ka ke furtawa suna nuna kishinka
ne karara. Dubi cikin idanunka,kishinUmmi ka ke
yi. don haka sai ka hkr ka bar min ita,domin ka
san ba wanda zai fi girgiza Umma tsakanina da
kai irin ka. Ya nuna Abba da yatsa, Za tafi bakin
ciki ka zama mijin Ummi fiye da ni. Abba ya daga
hannu ya falla mishi mari Bashir ya dafe wurin
sannan ya kalli sau 'yan shagon wadanda marin
ya janyo hankalinsu. Don farko ba su san abn da
a ke tattaunawa ba.Bashir ya ce, ka mare ni?
Abba ya ce, Zan kara maka,ko za ka rama ne?
Bashir ya ce, Ba zan rama ba,amma zan fada ma
su Alhj yau dinnan ina son Ummi. ya fita fuu.
Abba ya zauna ya rike kai yana huci. shi kam
Bashir ya kudurci niyyar fada wa iyayensu yau
dinnan. Abba ya kira wayar Umma ta daga suka
gaisa lkcn karfe 6 na yamma ya ce, Ummi fa? ta
ce Gata can kwance. Ya ce Ba dai jikin ba? ta ce
A" aikin karance-karancenta take. Ya ce, Ba ni ita
Umma. Umma ta kwala ma Ummi kira,ta mika
mata wayar tare da cewa "Yanyanki ne ke son
magana da ke. Yau ce rana ta farko da suka yi
waya a matsayin shi na Abba,ita kuma Ummi, in
an debe lkcn da suka yi waya a matsayin shi na
Abba ita kuma Suhailat. Tayi sallama cikin sanyi
murya can kasan makoshinta ya amsa tare da
runtse ido sakamakon tsigar jikinshi da ta tashi.
Ya ce "Ummi ta ce Na'am yaya. Ya ce "Kina son
Bashir? ta raunana murya. Yaya am sorry to say
bana son shin gsky. Ya ce To yau kam zai sanar
da su Alhj cewa yana sonki,in kina san kida
wanda ki ke so to ki gabatar da shi kafin shi ya
rigaki. Takaici ya kama ta, kamar ta ce, Ni kai na
ke so.......ya ce kina jina? ta ce,To Ya ce, kin san
in su Alhj suka ji ba ki da mafita,Ummi ta ce To
ni fa bani da wanda nake so shi ne ban san
yadda zan yi ba. Ya ce, shi kenan matsalarki ce.,
ya kashe wayar. Ummi tayi shiru tana tunanin
mafita,ko dai ta hkr ne ta aure Bashir din? kai a'a
to kuma gashi wanda take so ya ce matsalarta
ce. Can dai ta yanke yadda zata yi,don haka ta
kosa Alhj ya dawo. Tun kafin suje wurin cin abnci
ta same su a dakinshi su da Umma,ya yii wanka
yana kokarin fita sallar magriba. Ta ce Alhj dama
wanda ya ke zuwa gurina ne ya ce in fada muku
iyayenshi za su zo. Dadi ya kashe Alhj ya ce To
to dan nan unguwar ne? ta ce Eh ya ce To
madallah dama wannan yaron na sabon titi din
nan Suwaiba wanda kwanaki nake fada miki
nasan ubansa a kasuwarmu ya ke? Ta ce Naji
wanda ya soma zuwa wurin Ummi? ya ce Shifa,
Uban danai masa zancen naga dansa wurin 'yata
sai cewa ya yi auran gida za su yi masa,ko ni na
so hadin nan sai dai Allah bai so ba. Ya kalli
Ummi Yaushe za su zo? ta ce Ya dai ce in
tambaya ne. Alhj ya ce To Allah ya kawo su. Da
dare Sahabi yazo ta ce Sahabi an ce in maka
mgn ka turo ya ce Alhamdulillah, dama ina son in
miki mgn sai ina tsoron kada ki ce ya yi wuri don
haka gabe zan turo. Bashir yazo ya zauna gabn
Alhj suna cin abnci ya gaishe su. Suka amsa ya
yi shiru yana tunanin ta ina zai fara? Alhj Babba
ya ce ya ya Bashir akwai wata matsala ne?Ya ce
Am dama ina son in ce ni dai ina son Ummi ne.
Ummi kuma?Alhj karami?Ya ce Eh Alhj Babba ya
ce Ta amma ya aka yi kayi nauyin baki hr a ka
ba wani dama? Bashir ya ce Alhj Wanene? Alhj
karami ya ce Sai ka san shi? koda ba a tambaya
ba, ba zan ba da goyon baya a baka Ummii ba,
tashi ka bamu wuri. Abba ya ce, Bashir je ka ci
gaba da addu'a Allah yasa Ummi ta zam
rabinka,zan so haka dn na jima ina son zumuncin
nan. Iyayen Sahabi sun zo kuma an basu hr ma
an tsaida ranar daya fa ta Fati. Tun daga ranar
Ummi kullum cikin kuka take wanda iyayenta
suka kasa gane nufinta. Bashir bai daina cin
alwashin sai ya auri Ummi ba, dn haka kullum
cikin aiken kiranta yake. Ban da haka ma ya
maida hnkl kan sana'arshi tunda ubansa ya mishi
gorin wa zai ba shi mata ya ki tsayawa sana'a
nashi ganin in ya rike sana'a r za a ba shi. Abba
kuwa ya ji ya yi ma gidan wai don ya goge Ummi
a ranshi. Anya "ZURFIN CIKIN nan zai kai su? .
Sai mu hadu a littafi na Uku don jin yadda za a
kare. ZURFIN CIKI book 3 part 1
ZURFIN CIKI book 3 part 1
Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:21
Na Halima Abdullahi K/Mashi 1... Abba ya fito
cikin suit bakake, yayi kyau matuka hatta
takalminshi sawu ciki baki ne, tamkar wani black
America. Igiyar wuyan ta zauna tsam, sai kamshi
yake. Dakin Bishira ya nufa ya daga labule, ta
dago ta kalle shi yayi matukar birgeta. Tana
alfahari da shi matsayin mijinta, ya ce "Kin
shirya?" ta ce,, "Zuwa ina?' Ya ce, "A'a, jiya fa na
sanar da ke ki shirya da wuri zamu je asibiti ki
gaida Ummi". Ta watso mishi wani kallo uku
saura kwata, tare da cewa "Ko garin nan ba a
sanyi ba zan fita gaida wata can Ummi ba bare
da sanyin nan." Ya ce, "Dalili ta mike tsaye "Ciwo
bai kai mutuwa
Showing 15001 words to 18000 words out of 41322 words