"So fa kikace sis" So kuwa sis Arman ya jima da fara sonki fahimta ce kawai bakiyiba amma Arman ba k'aramun so yake maki ba ko ince kuke yiwa junanku.







"kamo hannunta Aira ta yi ta ce " sis kina nufin yaya Arman sona yake"kwarai kuwa Ke wace irice Aira da baki gane so ,baki ganin kishinki b'arob'aro a idanunshi Abunda ya faru dazu ma Kad'ai ya isa ya k'ara tabbatar maki da irin son da Arman yake maki Bayan nan ma alamomin soyayyarki da yake gwada maki a fili suke ba a boye ba Aira ko k'aramun yaro zai iya fahimtar soyayyar dake tsakaninku ni a zato na kinjima da ganewa kiyi tunani ki gani".







Ajiyar zuciya Aira ta sauke tare da lulawa duniyar tunani tun daga rayuwarsu ta baya har zuwa yanzu ,me yasa a cikin gidan ita kadai yake sakewa,me yasa ita kadai yake farantawa,ita kadai ya damu da ita,ita kadai yake kishinta ita kadai da dama Tabbas sai yanzu ta gane Yaya Arman sonta yake sosai gabanta ya fad'i kallon Amma tayi tace "To sis ni kuma ina sonshi? Ta k'arasa fad'a cikin sigar shagwaba Dariya Amma tayi sosai ta ce .







" ke sis wlh baki rabo da abun Dariya ni zaki tambaya ai zuciyarki zaki tambaya"Turo baki tayi ta ce "To fad'amun menene alamomin so?Alamomin so suna da yawa Aira Amma zanfada maki Kad'an daga cikinsu saiki duba kiga idan kina daga cikinsu " Shak'uwa tayi yawa tana daga cikin Alamun so,damuwa da halin da dayan ku yake ciki "Damuwa da rashinshi a kusa dake koda kuwa na y'an dak'ik'a ne,kishi,shine babbar alamar Zurmiya a cikin soyayya,kyautatawa,ko da yaushe idan kika kalleshi kiji farinciki ya mamaye zuciyarki koda kuwa a waya Ne,jin bazaki iya rabuwa dashi ba duk rintsi duk wuya " ga sunan da yawa Aira kiyi tunani.





Shiru tayi tare da Zurmiyawa duniyar tunani Tabbas inko hakane so ta jima da afkawa kogin soyayyar yaya Arman soyayyarma ba ta wasaba cike da damuwa ta ce "Tabbas sis najima da Fara son yaya Arman koma Ince da soyayyarshi na ginu tun bansan kaina ba nakejin Duka abubuwan nan da kika lissafo game dashi ina tsananin sonshi son ma bana wasa ba a da haukana na d'auka duk wannan din shakuwa ce saida kika lissafo nagane Abunda ake nufi da so da Chan shirmen banza na kawai nake sannan ta kamo hannun ta tace.









" Sis ya zanyi help me please ina sonshi sosai ya zanyi kin tabbata shima yana sona"Cike da tausayin y'ar uwar tata ta ce "Karki damu sis son da yake maki ya linka son da kike mashi Wanda na gani a idanuna kedai kawai ki bari har zuwa lokacin da zai furta miki" Hakika indai kika samu Yaya Arman sis kingama samun wani jin dad'i a duniya Dan nasan zaiyi wuya a samu Wanda zai kula dake ya nuna maki tsantsar k'auna da soyayya Bayan yaya Arman Dan Arman mutum ne da kowace mace ta sameshi ta more ,Abu d'aya kawai nake Tsoro kuma nake jiye muku Iyayenmu na tabbata Abba Da Daddy bazasu tab'a yarda Kuyi Aure ba inba wani ikon na ubangiji ba shine Babban abunda yake tsoratani"Hawaye sosai Aira take ta ce "Ina sonshi sis Bazan yarda a rabamu dashi ba Abba bazai iya rabamu ba Inajin da sonshi aka halicceni a yanzu bana jin tsoro ko shakkun komai da zan tunkara indai akan a rabamu da yaya Arman ne na gwammace Ranar na mutu".









ta fad'a tana fashewa da kuka " Sosai Amma ta tausayawa y'ar uwar tata Rungumeta tayi ta ce "Insha Allahu sis babu mai rabaku sai mutuwa nan tayi ta Lallashinta ranar daki daya suka kwana Wanda Aira baccci kauracewa idanunta yayi sakat tunanin Arman ya hanata bacci da kalaman y'ar uwarta Tabbas tasan indai hakane so to baiyi mata kamun wasa ba yayi mata kamun da ita kanta bazata iya control d'in zuciyarta ba sai Bayan asuba bacci ya d'auketa hakan yasa washegari tayi ranar bacci sai 12 ta tashi.





©©©©©©©©©©©©©



B'angaren Arman Shima hakan ta kasance Dan Sosai yakejin son Aira a ranshi Wanda shi kanshi bazai iya kwatanta shi da komai ba Sosai yakejin Haushi idan ya tuno ganinta da yayi da wani a tsaye tunani yake akan ya fito ya furtawa Aira abunda ke ranshi koko ?zata amince dani ko akasin haka? Ta na sona kamar yanda nake sonta ko har yanzu Kallon yaya takemun?Daren ranar bacci kauracewa Idanunshi yayi Yasan son Da yakewa Aira daga Allah ne Dan koda bai shiga zuciyar zukatan masoya ba yaji yanda sukejiba ya tabbata son da yake yiwa Airanshi babu wani mahaluk'in masoyin da zai iya yiwa masoyiyarshi kalarshi ba.





Washegari jiki ba kwari ya tashi koda mumy ta tambayeshi lafiyanshi qlau kawai yace mata nan take fad'a mashi Daddynshi jirginsu ya taso tun d'azu sun kusa isowa sai sannan ya d'anji sanyi sanyi a ranshi Dan sosai yakeson ganin Daddy Mummy tace yaje ya shirya nan da 30 minutes zai k'arasa.





Arman da kanshi shida Mummy suka taryo Daddy daga Airport Hannun Daddy rik'e da na Arman Dan ko Wanda bai saniba yasan irin tsananin son da Daddy ke yiwa Arman kasancewarshi shi d'aya tilon d'anshi a duniya.





Bayan Daddy ya huta yaci abinci Mummy sai Nan nan take da mijin nata Kallon Arman yayi ya ce "Son ya London d'in Fatan ka dawo lafiya" Lfyqlau Daddy "Masha Allah yaushe kuma zaka koma wajen Aikin naka" ran Monday sukace Daddy nama zata zasu d'an bani Hutu tunda kaga su suka turani London d'in nadawo na zata sunbani ko hutun 2weeks ne amma jiya sun kirani suke ceman Monday suke Son na koma"Dafa kanshi Dady yayi ya ce "Toh nan kusa kenan Kaga yau muna Friday to Allah ya kaimu Monday din Ai nasan d'ana jarumine Shiyasa basason suyi missing d'in aikishi ".







Murmushi Arman yayi Dan sosai yakejin dad'in yanda Daddy kullum ke kod'ashi shi d'anshi jarumine jajirtaccene tun yana yaro haka yake cemashi shi jarumine Ranar Yini sukayi suna Hira da Daddy Dan ko gidan Inna bai lek'a ba Yau cikin hirar ne yake cewa "Daddy Inna na ta nemanka" murmushi yayi ya ce "Insha Allahu gobe idan na huta zanje na gaisheta.







Washegari Daddy da Arman su kaje ya gaishe da Inna shida Security d'inshi Wanda koda yaushe suna biye dashi Arman bai samu ganin Aira ba dan Inna tace mai suna makaranta kasancewar da safe sukaje daga Chan suka wuce asibitoci Dan duba marassa lafiya sannan yayi musu alheri sosai wannan na Daga cikin abunda yasa mutanen jahar suke tsananin sonshi da son mulkinshi danshi mutum ne mai kirki da kuma tausayi ga Gaskiya da rukon amana.





Ran Sunday da dare Arman ya je gidan Inna Dan bankwana da Airanshi koda ya fad'a mata zai koma wajen Aiki kuka ta sanya mashi ita batason yake nesa da ita dak'yal ya lallab'ata yace zasu dinga Video call kullum kuma suna waya duk saiyaji bayason ma Tafiyar Dan dai ya zama dole Amma shi Zama da Airan shi ya fiye da mashi komai.





Tunda Arman ya tafi kullum cikin waya suke da video call kamar ma suna tare Aira suncigaba da Jarabawarsu ta neco ita da Amma sosai suka maida hankalinsu ga karatunsu har yanzu babu Wanda yasan da wayar Aira a cikin gidan Bayan Amma koda yaushe son Arman Kara ninkuwa yake a cikin Zuciyarta.







Ranar da Arman ya cika sati Biyu da tafiya Ranar Su Aira suka gama neco d'insu sai farinciki suke suda class mate d'insu ana tashan hotuna a wayar Aira nan Duk wasu suka amshi numbobinta ranar ji suke kamar karsu rabu daga karshe suka sha kuka musamman Aira ita da frnds d'inta Khady bestynta sosai suka shaku koda yaushe a school tare suke yawo nan sukayiwa juna Alk'awarin ziyartar juna akai akai Sai wajejen 6 suka gama hotuna da bankwana suka fito Bakin gate domin tafiya gida Suna fitowa Wata wulfefiyar Mota Fara me masifar kyau Aira ta gani parke .







Ganin mai fitowar ne ya sanyata wara idanu sosai yayi cikin sky blue din shadda ta tasha Aiki hular kanshi hadaddiya wadda a k'alla zata kai 100k Rungume yake da hannayenshi da suke sanye da Wrist din zinare kara wara idanu tayi Dan tabbatarwa da shi d'inne koko Gizau ne shiko kafeta yayi da idanu murmushi kawai yake sakar mata sosai tayi mashi kyau cikin unifoam dinta Light blue Hijab da Dark blue din wando y'ar k'aramar hijab dinta tare da rafar rigarta da ta sauko har gwuiya anyi mata hular hijab d'in da yadin wandon jelar rigarma haka ji yake Kamar ya je ya rungumota Aira ganin da gaske shi d'inne de gabanta ai batasan lokacin da ta saki Hannun Khady ba ta ruga a guje tayi wajenshi tare da Rungumeshi tama mance ta tsiraran mutanen class d'insu dake wajen Cike da murna da farincikin ganinshi ta ce My yaya........✍🏿



*Share fisabilillah*


*_Miss Hajo ce*_🤙🏿
[5/30, 23:01] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏
Hot love story♥️🔐

```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*

📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚

بسم الله الر حمن الر حين

*BOOK ONE*📔
🅿️...............13&14

Cikin zazzak'ar muryarshi Mai cike da kassala a hankali ya ce "My Cutie baki girma har yanzu ko kin manta gaban mutane muke kike rungumeni " ya fada kamar bashi yayi maganar ba murmushi tayi tare da sakinshi ta ce "Sorry yaya murnar ganin kace ta sa na ma manta da mutane a gurin" Aike gimbiyace bakya laifi my cutie "Uhm My yaya ammafa Gaskiya kayi surprise Dina da yawa bantab'a tunanin zaka zoba" Ranar graduation d'in Cutie na guda ace banzoba ai Abu baiyi dad'iba yanzu dai ki shigo mu tafi gida ma ida maganar a hanya ko"to my yaya bari naje nakira Amma Tana barin wajen ya zagaya ya shiga mota.




Aira na komawa khady tayi mata Dariya tace “ummm kwt har anfara love kenan kice mu fara shiri kece bikin farko a mate “harara ta galla mata tace “sa’idinawa kawai yaya nane to sannan tace muntafi sai mun had’e online “tukwana sukayi hug din juna suka rabu Amma na baya Aira na gaba haka suka tafi a hanya sai satar kallonta yake harsuka isa ba mai cewa uffan sunzo daidai bakin gate din inna sukaga fitowar motar Abba ta gate d’in gidansu cikin faduwar gaba Aira tayi k’asa da kanta dan kar Abba yaganta abunda bata saniba tuni yaganta saida taga wucewarsu tukwana ta dago tana sauke ajiyar zuciya Shidai Arman girgiza kai kawai nan ya gyara parking a waje Amma ta fita tare da cewa thnks Aira zata bude motar taji kulle juyowa tayi ta kalleshi saita sakar mai murmushi shima ya mayar mata tare da cewa.



“Ina kika saka wayarki jiya nayi ta kira a kashe”uhm yaya wlh wayarce kasan boyeta nake bana yawo da ita ko tsakar gida dan kar wani yagani shiyasa tana locker d’ita tun jiya sai da zamu sch nadaukota dan muyi hotuna “.


“Ajiyar zuciya ya sauke ya ce “nazata ba lafiya shiyasa na taho saida nazo nan nake tambayar haidar a bangaren inna yacemun kuna sch yau kuke last paper “wayyo yaya wai saboda baka sameni ba a waya kawai ka taho i’m sorry “ta fad’a ta na langabar da kai”Shitttt Kin manta bakya laifi komai kikayi daidaine my cutie “sannan ya dauko wata karamar waya daga cikin kwali tana gani ya daga ya saka wani sabon sim card tukwana ya bude ta yace “amshi wannan karamace saikidinga yawo da ita yanda duk sanda na kira zan sameki “murmushin jin dadi tayi tace Thnks my yaya”banson godiyarnan fa daman kinsan yau kuke graduation shine baki sanar daniba “uhm yaya na manta shiyasa “Allah bada sa a Ya fitar da sakamako me kyau kawai yace sannan yace “zan wuce dear baki bukatar komai”Eh yaya bana bukatar komai ganinka ma ya wayadas Bazaka shiga ku gaisa da inna ba “dazu mungaisa ai zanje na hutane kafin gobe na wuce “kamar zatai kuka tace “yaya gobe kuma yayi kusa ai”Zandawo soon yanzun akwai aikin da na baro shiyasa I am sorry gobe idan ba jirgin Safe zanhau ba zanbiyo muyi bankwana idan kuma na samu na safe na wuce kawai “hawaye ne suka fara zubar mata tace “shikenan yaya Allah ya kiyaye ya tsaremun kai “handkerchief ya d’auko ya fara share mata hawayen ya ce “Idan nazo kinamun kuka idan zan koma zandaina yawan zuwa dan bakisan yanda nakejin kukanki a cikin zuciyata ba “cikin sauri ta had’iye kukanta da take shirin cashews’




“sorry yaya bazan sakeba banson kana nesa dani ne shiyasa idan ka tafi yaushe zaka dawo “shima ji yake kamar yayi kukan yace “nafi kowa bukatarki a kusa dani dan bayanda zanyine next week insha Allah zanshigo na kwana biyu “to my yaya Allah ya maidoka lafiya “ki kulamun da kanki kinji my cutie “murmushi tayi tace “kaima ka kulamun da kanka sun dan taba hira kadan tukwana yayi mata bankwana ya wuce ji suke kamar karsu rabu da juna.




Aira koda ta shiga gida bata iske kowaba sai Ummy da Haidar da amma da suka dawo tare “Ya Ummy ina y’an gidan naga ba kowa bangaren inna ma bata nan”ta fad’a tana Waige waige “Suntafi kai Mamy asibiti “wara idanu tayi tace “Asibiti kuma me ya sameta “Haihuwa zatai “langabar dakai tai tace “wayyo Allah sauketa lafiya ranar bangarensu ta kwana sai addua take Allah sauke mamy lafiya dakyal bacci b’arawo yayi awon gaba da ita.


************

Arman kai tsaye guest house dinshi ya wuce dan yasan ya biya ta gida Mummy saisunji dalilin da yazo to yace musu saboda Aira ko me hakan yasa ya wuce chan bayan yayi wanka t-shirt kawai ya sanya da gajeran wando fresh milk kad’ai yasha tukwana yabi lafiyar gado dan akwai gajiya sosai tattare dashi yau jinshi yake cikin farinciki saboda ya hadu da Airanshi lumshe ido yayi a hankali ya ce “I love her so much Cox she’s beautiful “tunowa lokacin da yaganta cikin unifoam yake kyakkyawar fuskarta kawai yake ta hangowa da yanda take sakar mai murmushinta mai narkar da zuciya tuno lokacin da ta rungumeshi yayi ji yayi tsikar jikinshi ta tashi kamar wanda aka tsunkula haka ya zabura rumtse idonshi yayi sosai kafin ya bude su mikewa yayi ya dauko wani hotonta sosai tayi kyau cikin Wata black laffaya daga gani hoton bai jima ba kafe hoton yayi da idanu bako kiftawa kafin ya fara shafa hoton yana murmushi shi kad’ai yace “I love you my Aira ina sonki sosai Airata ki soni please ko kadan ne yafada yana marairaicewa (🤣nikam nace Arman karfa ka haukace)rungume hoton yayi a haka baccci me dad’i ya daukeshi cike da mafarkin Airanshi.

*********
Washegari Su Aira su na bacci Ummy ta tashesu cikin murna tace ku tashi yanzu mama ta kira Mamy ta haihu “Aira kamar an tsikareta haka ta tashi tace “da gaske Ya Ummy me ta Haifa”nima ban tambaya ba yanzu dai Mama ta kira tace da asuba ta haihu mu gyara gidan tare da Laure(yar aikin su)ba jimawa zasu dawo.


Cikin murna Aira ta tashi da dinga murna nan suka gyara gidan wajejen 12 su Mamy suka dawo gida inna dauke da jaririn mamy ko duk tayi lakwas Aira sai murna take ganin k’anin nata shima fari me kyau dan duka d’iyan Mamy su ukkun fararene Haidar ne ma baiyo hasken mamy sosai ba nan yan barka da yan uwa suka fara shigowa.


Aira ko bayan flowers ta koma domin kiran Arman taji ya tafi ko zaizo dan taga har anyi la’asr tana sand’o ta ciro k’aramar wayar da ya bata daman ta hardace number dannawa kawai tayi saitaga yamayi mata save da My yaya murmushi tayi tanajin karason Arman na ratsa kowani sassa na jikinta saida kiran ya katse kafin ta kara kira taji kiranshi ya shigo murmushi jin dadi tayi tare da kissing d’in wayar tace I love you my yaya tukwana tayi picking..........✍🏿


Manage ba yawa 😊

Share saboda Allah 👏


_*Miss Hajo ce_*🤙🏿
[5/30, 23:01] Hajo: 🍏 *NI DA YAYA ARMAN* 🍏
Hot love story♥️🔐

```MALLAKAR```
*Hajara L Sadeq*

📚 *JARUMAI WRITER’S ASSOCIATION * 📚

بسم الله الر حمن الر حين

*BOOK ONE*📔
🅿️...............15&16

Daga dayan bangaren Arman ya ce "Hello Cutie ykk " lfyqlau yaya harka tafi ko"ta fad'a cikin sigar shagwaba "Yanzu haka ina Abuja my cutie jirgin 9 nabi shiyasa bansamu nazo nayi maki bankwana ba".





"Ayya to Sannu ya gajiyar hanya "Alhmdllh ya fad'a yace Yadai Naji kamar kina cikin farinciki my cutie Shakomun " Dariya tayi jin ya ce Wai shak'omun ta ce "Yaya Mamy ta haihu fa ".







Daga bangarenshi kamar tana ganinshi ya zaro ido ya ce "da gaske cutie Ah dole muyi farinciki me muka samu" Namiji ni nama zaci mace zata Haifa na samu y'ar uwa kawai sai ta haifi namiji"ta fada tana turo baki .







Dariya yayi har tana jiyowashi cikin waya sosai k'uruciyarta ke burgeshi komai ya fito daga bakinta fad'a kawai take cikin shagwaba ta ce " Dariya ma kakemun ko"Sorry my Beauty Kece kikaban Dariya kince ke mace kikeso ko?"Eh yaya ni mace nakeso " To yanzu shikenan tunda Mai faruwa ta faru saimuyi addu'ar idan Kikayi Aure Haihuwarki ta farko ki haifo mana mace mai kama da ke ko?wara idanu tayi kamar yana gabanta kunya duk tabi ta lullubeta ga yanda yayi maganar ya d'an kulle mata kai "Ki haifo mana?sai muyi addua?Aranta take maimaitawa me yake nufi ?







tsinkayar muryarshi tayi da cewa " Yadai cutie kikayi shiru"Uhm "kawai tace duk kunyarshi ma takeji" Shiko bangarenshi da gangan yayi mata har yanzu yana so ya furta mata Kalmar so amma ya kasa hakan yasa ya yanke shawarar nuna mata k'arara yanda zata gane ko baice yana sonta ba ta d'auko hanya.







Jin tayi shiru ya sanyashi sauya maganar da cewa"Ki d'auko mun hoton kanan namu ki turoman"Ajiyar zuciya ta sauke jin ya sauya maganar ta ce "To yaya Anjima zand'aukarma" Hango Ummy tayi na nufo wajen cikin Sauri ta ce "Yaya sai anjima Ga ya ummy nan ta maza ta katse wayar ta boye bayanta.





" Ummy ko tab'e baki tayi Dan ta ganta sarai ta ce "Kidaibi A Sannu rawar kan nan taki karta kaiki ta baroki Manya
Showing 9001 words to 12000 words out of 33558 words