su farida sunce wai a wajen mairo kika kwana,ince dai ba wani abin cutarwa yayi miki ba koh"
Ta faɗa tana ƙara matsowa kusa dani tareda rage murya. Lallai wannan matar akwai gulma,ji yanda ta lanƙwashe murya kaman rantse duniya zakace tausayina take ji,kaman ba itace suke husuma da ƴar ta akan kuɗi ba..
Ƴar dariya nayi ta wayance wa kafin nace.
"Ahhah babu komai inna gaji,ba abinda yayimin,kawai dai zan zauna a wajen inna ne na ɗan wani lokaci kafinna koma sashen mijinnawa,ni barina tafi idan babu wani abin"
Miƙewa nayi xan bar ƙofar muryar Atika ta tsayar dani.
"Lahh gaji kin manta wanke wanken can fah,cikina jiya ciwo yake ban kwanta da wuri ba,shiyasa na makara da safe banyi wanke wanken ba,ga kuma talle da zan fita,gaji ko zata taimakamin dashi dan Allah"
Kaman zatayi kuka take maganar harda sakin wani munafukin nishi,shuru nayi naji abinda gajin zatace.
"Ohh ehh hakane kam bazayyi wu harki gama wanke wanke ki fitamin da awarar nan ba. Sumaimah in bazakiyi komai ba ko zakiyi wanke wanke can kai,yi haƙuri nasaka amarya aiki"
Banyi mamaki ba,dan dama nasaka a raina hakan zata faru,saurin haɗiye takaici na nayi tareda ajiye murmushi akan fuskata na kallesu..
"Ahh ba komai ai bari nayi wanke wanken toh"
"Yawwa to bari zan kawo miki omon yin wanke wanken."
Inna wacce tafara tuka igiyarta sai gani tayi nafara jijjiƙa kayan wanke wanke,mamaki abin yabata tasaki baki..
"Ahh keda nace ki barshi akwai meyi"
"Ahah vakomai inna,wai atikan ce cikinta yana ciwo batayi bacci da wuri ba saita makara,gakuma zata fita talle"
"Atikance ta faɗa miki haka,zancen banza kenan,yarinyar da har nayi bacci na tashi fitsari na ganta ta shigo gidan,itace za'ace batada lafiyah,kawai dai suda sun iya rainawa mutane hankali kai.. Kin ajiye kwanukannan barinaje na samu gajin,wannan ai rashin daidai ne,daga kawo ki gida jiya har an baki aiki yau"
"Waye ke nema na gani nan nakawo mata soso da omo,harda za'ace wani ban kyautaba na bata wanke wanke,menene rashin kyautawar tawa a ciki iyee,dan kawai maiyin aikin batada lafiya nace tayi na rana ɗaya shine abin magana,bata wanke wanken a gidansu ne? Naga kowa a garinnan yasani itakeyin aikin gidnasu kaff,ba wani gata ne da itaba ballantana a ce bata tab'a yi ba.
Ni nace me a gidannan,kullum sai nayi tuwo na ciyarda wata,ko a bani cefane ko ba'a baniba sai nayi tuwo,akwai wanda yake taimakata da ƙwandala a gidannan ne?
Da nace tayi na kwana ɗaya,to yanzu na fasa,wanke wanke da shara kullum ita zata dungayi a gidannan,indai har wasu suna so na dungayin abinci dasu"
Tana gama faɗin hakan ta zefamin soda da soson wanke wanken.
Wayyyo Allah nah yanzu da soda zan dungayi,ni wanke wanken bai dameni ba kaman sodar,jikina kwata kwata baya sonta ko kaɗan,nan da nan hanni na sai ɗaɗe ya tsatstsage..
Wani tarin abune yazo ya tarimin a maƙoshi,wato inna kula inaga ƙalubalena na gidan ba goje bane kenan gaji ce.
A hankali nake yi ina duba hannuna ko yayi wani abun har na gama tsaff,Alhamdulillah bai tsage ba amma yayi za sosai,to yau kenan nasan nan da wani ɗan lokacin zai fatattakema.
Bayan nagama barandar inna Mairo na koma na zauna,ido na tsurawa yanda take tukawa nayi,abin abin sha'awa,inaso naga mutum yana sana'a.
Da farko taso bani haƙuri akan abinda yafaru,nice naƙi na ɗauko wani zancen,zamane da allah kaɗai yasan ƙarshensa,idan yazamo kullum sai ta bani haƙuri to abin bazai tafi daidai ba..
Hira muke jefi jefi,tana bani labarai na zamansu a garin da baban goje yayi aiki,wani nayi dariya wani na jijjiga kai.
Ƙarar buɗe ƙofar goje nayi,hakanne yasa na juya da sauri wajen,wash ashe yana nan,harga Allah ni manta ma dashi..
Nufo idan muke yayi kamar kullum da riga da wando a jikinsa ƙanana masu duhu,Allah ne kaɗai yasan yaushe suka ga ruwa..
"Innna ykk"
Yafaɗa yana zama a bakin barandar.
"Kalau mana nake,kaman yanda ka sanni,ina ka shiga kwana biyu,sai kuma ka koro matarka jiya da daddare koh"
Runtse ido nayi ƙirjina yana lugude,inda inna tana ganin zuciyata da batayi wannann maganar ba,na samu bai kula dani ba a wajen,yanzu ta saka ya juyo da idonsa inda nake.
Wani kallo yayi min kaman yaga dutse kafin yace.
"Kwana biyu naje wani wuzilinne shiyasa kika jini shuru,batun wannan kuma dama fah tun farko na faɗamiki,zuwa tayi tai abinda yasaka tazo,ke na kawowa ita,in bakyaso ta tashi ta tafi ubanta yabani kuɗina. Amma batun ta zauna a sashe na ban yadda da wannan ba sam."
"Hmmm kaidai kace haka,zata zauna a wajena na ɗan wani lokaci,idan kun shirya saita koma ɗakinta"
"Ɗakinta kuma,akan idonki fah mukaxo nida yarana muka gina ɗakinnan,yanzu rana tsaka lokaci guda kin bata shi?"
Ganin yafarajin haushin abinda inna ke cewa ne yasaka ni yimata alama da ido,kaman kuwa ta gani saida sanja zancen. Amma kuma tasake kwafsawa.
"Sabo dayi gawa da gatsine,saida ranar Allah tayi kafin ka fito,ita matar taka inka fita karyawa saika kawo mata nata,tunda kasan a ƙarƙashinka yanzu take koh"
"Wajen Iliyah zanje nasan ya ajiyemin,daga can zan wuce saina juyo kuma"
Huhhh na sauƙe ajiyar zuciya,ganin bai ɗaga zancen da innan tayi masa ba,da alama bayason duk wani zance daya shafeni ne inaga.hmmm niyafimin ai,gaba takaini gobarar titi a jos.

          __***__

"Audu ya dai wajen aikin,naji ance wai ka dawo kenan bazaka komaba"
Uwaisu ya tambayi Audu baffan goje.
"Inakuwa komawa,waccar yarinyar ta rabani da samun arziƙina,tabarni da zaman majalisa da shan lofe"
"Yarinya kuma wacce kenan?"
"Ƴar wajena mana Atika,matar gidance takamata da mijinta,shine fah suka yi mana korar kare gabaɗayah"
"Hhhhhh hoɗan kace tayi gado kenan,ka manta yanda kake lokacin da muna matasa,yayanka yayi ta fama dakai,yanzu ma nasan ba sanja sani tayi ba saidai ya ragu kawai,kai anyi yawan duniya fah"
"Jiya ba yau ba ba,ai wannan yarinya uwaisu inaga da damani ta shanye,dan ita bayan halina hadda na uwarta tahaɗa ma,nida zan samu na bada itah a cacar ma wani ya ɗauka wlh inaso"
"Ahh ba saika jarraba ba,inda mai rabo ai sai ya ɗauka,amma kana ganin zata yarda kayi biyan caca da itah,tunda kace gaji ta iyoo to ba fah kasan sai ankai ruwa rana"
"Ehh to kuma kace wani abun,amma dai uwaisu tundaga wannan lamarin ka daina caca koh?"
"Ina kuwa ina nan inayi,yau ma inada wata caca da wani ɗan fulani,naji ance bai iya ba so yake ya gwada,wayo zanyi masa muyi,idan nayi nasara saina tambayeshi yabani ƴar sa,kasan su fulani da kyau,yanda na rabu da tawa ƴar nima saina auro wata a sanadin caca Audu"
"Kai car uba,amma uwaisu kai maƙurane,kana da dabara sosai,kuma kaman wannan sanadin cacar na aure abune mai daɗi da sauƙi,kana cinye mutum saiya baka ƴar sa,babu ruwanka dayimata wata wahala,tunda anriga anyi yarjejeni ya. Muje nima zanga yanda zata kaya,baza'a barni a baya ba sam"
Tashi sukayi da hnazarinsu zuwa sansanin da suke cacar.
Kamar kullum a cike yake da mutane kowa na sha'anin gabansa..
Bayan sun isa wajen da goje uwaisu ya haɗa ido,saidai yau ba caca yake ba,a gefe yake da a zaune yana duniyar tunani. Bayan sun haɗa ido kowa kawar da nasa yayi kaman baiga ɗayaba,saikace ba surukai bane.
Manga ne a zaune shida dan fulanin suna ta surutu da hausarsa wacce bata fita.
Suma zama sukayi a wajen aka fara dasu.
"Ɗan fulani so kake kafara caca?"
"Ehh fah,naga abun tana kawo Cede sosai,wani daya ci jiya kawai sai ya ɗebe dukka,nima inason na ɗebe dukka yau"
Kallon kallo sukayi a tsakaninsu su uku,kafin uwaisu yafara magana..
"To shikenan karka damu,idan kayi nasara zaka ɗebe dukka,amma kafinnan mai zaka saka wanda in an cinye ka aka bayar?"
"Uhm zan caka komai amma banda sanuwa,bama bada sanuwa a wannan wasan"
"Ehh to naji,ni zan saka gonata,idan kayi nasara ka ɗauka takace"
"Dagaske kake,gona noma babba zaka bani inna yi nacara?"
"Ehh amma kai mai zaka saka,kana da ƴaƴa mata ne?"
"Eh inada ƴaƴa mana,huɗu mata sai maza biyu,sauran basa nan suna gurin innarsu,tare muke kaɗai da Deejah,itace kuma babba"
"Uhm to zaka saka Deejah idan nayi nasara ka bani aurenta?"
"Na baka Deejah kabani gona inna ci,kaikuma ka ɗauki deeja inka ci,amma Deejah ƙarama ce,aurenta sai shekarar gaba. Bazatayi aure yanzu ba,amma zanbaka ita wajenka. Saidai Deejah tanada......."
"Kaga tunda ka amince a fara kawai,koda tanada wani masoyin babu shi yanxu sai ni"
"Ba masoyi gareta ba tanada......"
"Bar wannan zancen kayi shi daga baya,yanzu dai a fara"
Mutane kowa hankalinsa wajensu ya koma lokacin da suka fara,ana haka har cinye ɗan fulani a caca,kowa a gun dama yasan uwaisu wayo yayiwa ɗan fulani dan ya auri ɗiyarsa,ko kunya bayaji yarinya ƙarama gashi tsofai tsofai,tausayin ɗan fulani ne ya kamasu ganin cutar da uwaisu yayi masa,saidai kuma babu yanda zasuyi tunda yayarda.
"Yanzu ka cinye Deejah,a wajenka zata zauna kenan?"
Dariyah uwaisu yasaka tareda shafa gemunsa cikin shauƙi,ehh yanzu nine mijin Deejah,zan riƙeta a wajena a nan da shekara ɗaya takai aure"
"Ohh kada ma kayi alƙawarin auren Deejah,nidai tunda na baka ita kanada ikon kayi duk abinda zakayi da itah........uwaishu ya ɗauki Deejah,jauro ya rabuda Deejah,yau zanyi barci na more babu Deejah.....heeho jauro yaji daɗi yau ya rabu da Deejah"
Kokararsa yaja a ƙasa yayi ihu kana ya sheqe da dariyah.
Da mamaki kowa a wajen yake kallon jauro,wanda yake murna da farinciki kaman anyi masa albishir da kujerar makkah.
"Kai jauro ƴar ka cefah zaka rabuda itah,amma kuma kake wannan murnar?"
Manga ya tambayeshi cikeda mamaki.
"Ahah Deejah ɗiya ta ce amma nasan Altine wayo tayimin tabani Deejah ta gudu,ni nasan ba jini na ba Deejah,don batayi kama da mutane ba wanga ɗiya,Hoɗan hanci kaman 'bauna fah take,kullum jeji take wuni saboda fitinarta,gata da aljanu masu saka wutar nan,mun take musu gidansu da shanu suka shiga jikin Deejah,sannan uwarta tana duba ƙasa suma suka sake shiga jikin Deejah,kai Deejah dai ba mutum ba kawai,kows ya gudu ya barni da Deejah fah. Nima yanzu na rabu da Deejah shikenan,uwashu ni zani gida na shaida mata,gobe zan kawo maka Deejah,dama kuwa tanason zaman birni. Yanzu saina ajiye jakar kuɗina a ko ina tunda babu Deejah. Hoɗan caca ta rabani da Deejah nikam naji daɗi"
Ɗora sandarsa yayi a kafaɗa ya tafi yana faɗa. Wani suman tsaye mutanen wajen sukayi,banda shi uban gayyar dayake jin abin kaman a mafarki.
Bayan wajen yayi tsitt na wani lokaci dariya sukaji an kwashe da itah a bayansu,suna juyawa suka ga ashe gojene.
"Ohh dama wannan baban Deejah da take yawo cikin dare a daji,muma kenan zamu huta masu zaman daji da gamuwa da itah,babu dama karenmu yakama zomo saita tumurmusheshi ta ɗauke. Tunda zata dawo cikin gari da zama mayi farauta cikin kwanciyar hankali"
Yana gama maganar ya tashi shima yabar wajen yana dariya,tunda kuwa goje yayi dariyah to abin mai muni ne sosai......





Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*


Mallakar SADI-SAKHNA


PROFICIENT WRITER ASSOCIATION



*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[11]


[Sumaimah a mahangar gani]

Kwanci tashi hausawa kecewa a sarar mai rai,yau satina a guda kenan a gidan aurennawa.
Abubuwa da dama sun faru,wanda duk yawancinsu na rashin daɗi ne. Mutanen gidan kaman dama jira suke nazo,kowa ya daina komai a gidan na aikace aikace,inka ɗauke awara kawai da gaji takeyin kayarta. Itama wani lokacin nice ke haɗa wutar,ko dolene ma in mutum yaga abinda nake ya tausayamin kuma yaji haushina,nima haushin kannawa nakeji,to amma ya zanyi. Yanda gaji ta faɗa hakane ita ke ciyar da gidan kusan,nima ta wani wajen inaganin ƙoƙarinta akan hakan.
Dan haka dolene nayimata aikace aikace,duk da kuwa sunyimin yawa,ranar dana gwada cewa bazanyi ba zage zage tafara da gori,wanda duk akan inna mairo ya ƙare. Nikuma tausayin dattijuwar nake sosai,shiyasa nakeyin komai da jikina zai ɗauka indai gaji zata ƙyalemu.
A bangaren goje kuwa bazance lafiya ba,har yanzu babu abinda dai ya haɗani dashi,tunda ba zaman gidan ma yake sosai ba,in ya shigo ma iya karnukansa ne a gabansa. Abinda nake masifar tsoro kenan,hakanne yasaka inna tace ya fita dasu waje.

Yanzu nagane da wuri nake gama ayyukana na samu waje na zauna,muyi ta hira da inna,kwana biyun farko dana ta'ba soda hannuna ya tsage danayiwa gaji magana cewa tayi ita taga damar siyah. Inna data kulada hakanne ta bani kuɗi na siyi sabulu.
Ɗakin inna nufah ina ta tuna tunane wanda suka zama aikina na kodayaushe,tun ina saka ran mafarkin samun rayuwa mai sauƙi yanzu na cire wannnan a raina,haka ƙaddara take kuma a haka zan ƙare inaga.
Turuss nayi a bakin ƙofar,inna nasamu tana shishshirya kayanta a wani bakko,wani razana nayi kaman ɗan da uwarsa zata tafi ta barshi.
"Inna ina zakije?"
Nafaɗa a sanyaye.
Itama diriricewa tayi,kaman da alama batasan zan shigo ɗakin ba.
"Uhm ɗiyar nan wlh garinmu zanje,ɗan ƙanina ne yayi aure sannan kuma anyi mana rasuwa wancan satin,da tun wancan satin naso tafiya,to kinga bazan tafi na barki ke kaɗai daga zuwa ba,shiyasa nace barina dakata saikinyi ko satine tukunna"
Haɗiye hawayena nayi,banason tafiyar tata,amma kuma wacece ni dazanyi sanadiyyar hanata zuwa taga danginta. Cikin dauriyah na gyara muryata na tambayeta.
"Inna inkin tafi yaushe zaki dawo?"
"Uhm zanyi kaman sati biyu tunda ina tunanin na barki,amma da wata biyu nake ko ɗaya"
Datace sati biyu har zan roƙeta ta rage,saikuma naji ashe dannice ma shiyasa zatayi sati biyun.
"To shikenan inna Allah ya dawo dake lafiyah,amma kunyi sallama da gojene,nasan yau ba lallai yadawo ba sai dare"
"Ehh nasani ai shiyasa mukayi maganar dashi jiyah"
Gyalenta tasaka na biyota zuwa waje,ƙofar gaji tashiga wadda kaman kullum take fama da yaranta,Atika bata nan tafita talle.
"To gaji nizan je gida,sati biyu zanyi na dawo,don Allah gaji ki kulada itah,ki daina yimata wannan abin dan Allah yabaki dama,kar watarana goje ya tareki bazakuyi da daɗi ba......."
"Haba mairo yakamata ki kama girmanki fah,fisabillillahi mai nayiwa yarinyar nan,dan kawai nace ta tayani aikace aikace,in batayimin ba akwai yanda zan amfaneta ne,kawai saidai in ta ciyar da itah. Dazakice goje yagani shima nasan babu abinda zaice,tunda kowa yasani dama dan haka ya yarda tazo gidan,saboda da dunga aiki ta fanshi kuɗin da ubanta yakasa biya a caca"
Jan ƙafafuna nayi na bar ƙofar,kunnuwana bazasu iya jure jin waɗannan kalamai ba masu matuƙar ɗumi,duk da cewar nasan gaskiya take faɗa ba ƙarya ba.
A bakin fita ƙofar gida na tsaya ina jiran inna harta fito,murmushi na ƙaƙalo nayi mata lokacin da muka haɗa ido,don banason tafara bani wannan haƙurin,itama tasan hakan shiyasa bata ɗagomin zancen ba.
"To Sumaimah ni zan tafi saikuma Allah yasa na dawo,ki duba ban kaɗen katifata akwai ɗari biyar ki dunga siyan koko da safe"
Kukane ya kufcemin lokacin data fice daga cikin gidan ta tafi.
Shikenan saini kaɗai a gidan,in kasheni ne ma zasuyi daga goje har gajin babu mai ƙwata ta a wajensu.
Da gudu na nufi ɗakinnamu nida itah na faɗa akan katifa,kuka nake ta rubza har saida nayi na ƙoshi kaina yayi ciwo kafin nai shuru.
A haka bacci ya ɗaukeni bansani ba.
Ƙiran sallahr azahar ne da wani masallaci gefe damu suka ƙwallah ya tasheni,hamma nayi ta yunwa kafin na saƙƙo daga kan gadon innan.
Har na idar da sallah cikina yana ƙara na neman abincin,ganin abin baxai kainiba yasa na zari takalmina na nufi ƙofar gaji.
Rabon abinci take a kwanuka ƙanana,kowa sai an zuba masa nasa.
Muna haɗa ido da itah ta watsamin harara tareda cewa.
"Mayyah kawai,ni banga amfanin zuwanki gidannan ba sam,shi wanda ya ajiyeki ko oho"
Naji haushin abin amma ya zanyi,mutumin daya ke nema ina zayyi iyayi.
Cakuɗaɗɗiyar jallof ɗin ta yafata a kwano a turomin gabana.
"Gashinan wlh kaɗan zan baki,tunda ko ɗora girki bakiyi ba yau,wannan na wanke wanke da sharar da kikayi ne"
Ɗauka nayi bance komai ba na fita daga ƙofar,a raina ji nayi gwanda ma gidanmu,ko ba komai ranar girkin ammi mutum zaici abinci ya ƙoshi,amma kuma gwanda ban babu jarabar su inna rammah saina gaji,sannan kuma babu zuwa talle kullum.
Ɗakin innan na koma na zauna,kallon abincin nake kaman za'a bawa ɗan yaye.
Nasaka hannu kenan a ciki na jiyo muryar Shareefah a kofar gidan,sallama take tayi amma bata shigoba,da alama tsoro take kar goje yana gidan.
Fitowa nayi da sauri na tareda ina murna,bayan sati guda wani ya tuna dani ya nemi inda nake.
Ɗakin innan muka shiga da ita,sai ɗari ɗari take idonta akan ƙofar goje,nasan shi take dubawa ko zata gani,amma saina sake tambayarta.
"Wakike nema ne Shareefah kike ta juyawa?"
"Kutt harma tambayata zakiyi,wannan mijinnaki mana,ke kina gida bakiji abinda yayi limamin gari ba koh"
Zaro ido nayi tareda jijjiga kai,bansan mai yafaru ba dagaske,taya zan sani ina zaune a cikin gida.
"Bansani ba mai yafaru,mai yayiwa liman ɗin"
"Bawai liman ɗin yayi wa ba,ɗan gidan liman fah ya ɗauke,har yanzu bai dawo dashi ba wai sai yayi sati a wajensa,anyi magiyar amma shuru,kinsan in suka kai mutum wannan madakatar tasu kuwa saita Allah"
"Mai.....mai ɗan liman ɗin yayi masa"?
"Bai faɗi mai yayi masa ba,kawai cewa ake wai dan liman ya zagesu ne a mubarin huɗuba"
Hannayena karkarwa suka farayi,dan kawai anyi maganar ka a mumbari saika saci ɗan liman?.
A tabarmar ɗakinna zauna dana tuna ashe a tsaye muke shigowarmu ɗakin. Itama zama tayi tana cigaba da bani labarin wane hali garin yake ciki.
Dungurar kwanon abincin nayi da ƙafata,sai sannan na tuna ashe fah abinci nake. Kwanon na kawo tsakiyar mu,cikeda kunya nayiwa Shareefah tayin abincinnawa.
Itama ta kulada hakan,dan kallon tausayi tafara yimin,kafin ta jijjiga kai alamar bazata ciba.
"Uhm Sumaimah abin ya ɗauremin kai,ya naga kayanki kuma a nan ɗakin?"
"Anan nake kwana ai,mai kike gani"?
"Abubuwa dayawa,Sumaimah nasan mijinki abin tsoro ne kowa yasan haka,amma anan kam naga rashin wayonki da rashin dabararki wacce da nasanki da itah. Shin idan baki tunkareshi ba kin gyarashi taya zakiyi rayuwa mai kyau,wlh Sumaimah mutane irin goje idan suka gyaru matansu suna morewa,kuma ko wannan abin dayake a gari zai bari,kowa fah ke yake tsammani kiyi tasiri a rayuwar goje,saboda gani ake silar shiryuwarsa ce a aurenki,amma kuma ki gudu ki dawo ɗakin innarsa da zama? Ko.........."
"Kiyi haƙuri kiyi shuru haka Shareefah,nikuwa nasan cewar akwai haƙƙinsa akaina,amma karki manta bafah nice na gujeshi dan raɗin kaina ba,yacemin idan ban fitaba zai hukuntani,idan kuma nasake dawowa saidai wata bani ba. To kece zakijene iyee faɗamin"
Sakin ajiyar zuciyah Shareefah tayi kafin tace.
"Ehh to kuma hakane,amma mai zai hana ki fara wasu dabaru dazasu janyo hankalinsa gareki a sannu"
"Kaman me kike gani zanyi,ni tsoronsa nakeji Shareefah,saidao tunda nazo gidannan bai tabayimin komai ba na mugunta,sai gaji ce dai......"
"Uhmm na gaji mai sauƙi ne idan har kika fahimtar dashi yagane muhimmancinki,shizai yimiki maganin gaji,koda da wahala amma ki gwadah kinji,komai
Showing 18001 words to 21000 words out of 60324 words