yaso saina tambaye shi naje gidan su Shareefah,nasan zan samu abinda zanci a gidan.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
Har na fita daga gidan rai na bai daina zafi,lallai wannan yarinyar wuyanta yayi kauri. Lokacin danaji maganar nan baƙaramin baci raina yayi ba,kaman ni....nine zatace nayi mata ciki,kai barima na koma nasake tattaka ta dan ubanta.
Juyawa nayi gidan,har nafara shiga na hango gaji ta jefar da Sumaimah a ƙasa,wato akan ta zata huce saboda na daki ƴar ta ko.
Maganganu gajin tafara faɗawa Sumaimah,wacce kana ganin fuskarta kasan abinda take faɗamata ba ƙaramin zafi suke mata ba. Kai mata mata.....shiyasa fah ni banason shirgi dasu,wato rashin shiga harkarta da banayi shima abin magana ne da har za'ayi mata gori dashi.
Niyyar ƙarisawa nayi,ganin gaji tana shirin ɗauke Atika daga inda nace ta tsugunna,dama nasan hakan zata faru,tsoratar da Sumaimah zatayi ta ɗauketa daga wajen,musamman data ganta wawiyah ce batada wayo.
Siririyar maganar ta naji,cikin sanyi take amayarwa gaji duk maganar data fesa mata,dama ta iyah magana haka,nida nayi zaton ma kurmiyace. Tun bata kai haka ba muna yawan cin karo da ita a hanya in zata makaranta,sai ta juyah da gudu kaman taga aljani,tun abin yana bani mamaki har na daina.
Amma yanzu ta dawomin da mamakina,ina ganinta wawiyah ashe tanada wayo,ehh tunda gaji tasaka wannan magana da alama takaita bango ne.
Fitowa nayi daga gidan na tafi inda su Tunga suke hukunta Sageer,har na isa wajen da tunanin faɗan matan a raina.
Lokacin dana isa wajen sun mammaujeshi sun ɗaure shi,a zaune suke suna taɗin siyasa,na wani chairman paty dayake so muyi masa aiki.
Ina isa wajen sukayi shuru tareda bani gaisuwa,amsawa nayi kana na samu waje na zauna.
"Ogah goje gashi nan mun ɗan tabashi kaman yanda ka nema. Iya shegen ma ya iya kawai,ashe ƙaramin ɗan iskane,daga dukan farko fah ya rojaye kaman wata ƙanƙara"
Ragarus ne yafaɗa yana cigaba da jujjuyah sandar hannunsa.
"Hmm ku sunceshi ku kaishi ƙofar gidansu,duk ya isheni bana ma son ganinsa,ku tabbatar kun bar masa jan gargaɗi a rubuce na saka hannuna"
Dama duk masu bin matannan suna lalatasu yanda kasan ƴan daudu haka suke,sai shegen surutun tsiya da ƙarya,matan ma sun fisu ƙwari. Ko mai ma matan suke gani a jikinsu oho.
Jawabin da chairman party yafaɗa suka maiyarmin,akan yanaso muyi masa aiki,saidai suyi masa badai ni ba,dan inada wani aiki da zamu fita da ƙungiyar DC,Jiyah suka turomin takardar inda zan samesu da daddare,za'a tattauna yanda plan ɗin zai tafi,nasan bazai wuce sati ɗaya ba samu fita aikin.Bazan faɗawa sauran abinda yake faruwa,iyah Tunga ne kawai yasan zancen. Yau ma nake shirin naɗashi shugaba mai riƙon ƙwaryah kafin na dawo,bazayyi yu dan bana nan na hanasu yin aiki ba,musamman kuma dana san zasu samu kuɗi sosai idan sunyi ɗin.
"Bakomai za'ayi masa aiki,duk da bananan a lokacin,amma zan yimasa gargaɗi kaman ina nan. Zanyi tafiyah maybe wani satin,zan iyah kaiwa satin ban dawo ba,dan haka Tunga zai zagorance ku idan bana nan.
Basuji daɗin abinda nace ba,sannan nasan dole zasuso sanin ina zanje,amma koda zasu sani ba yanzu ba tukunna.
Jeji na nufah Ina riƙe kai,wannan ciwon kan narasa daga ina yake zuwa,duk sanda nafara jinsa saina dunga jin kaman ba nanne yakamata na kasance,kaman inada wani wajen bayan nan,kaman akwai wata rayuwar bayannan danake da itah. To amma a ina take,yaushe zan bar wannan masifaffen ciwon dayake juyar da rayuwata,haka nake kwana na tashi,amma tunda nake bantaba jin nutsuwa ba,kullum acikin duhu nake,lokaci lokaci ko a bacci ina hango wani haske ɗan ƙarami a can nesa,sai nayi gudu nayi gudu inaso na kamoshi sai ya bace ya ƙyaleni ni kaɗai.
Ƙarisowa wajen bukkar tawa tacikin jejin nayi,da sanina nayi mata fenti baƙi,saboda a baƙin wajen kawai nake iyah bacci ,hakan ma nafison cikin jeji,shiɗimma ba cikin salama ba,sai an kai ruwa rana,kowa ka tambayeshi yasan ba ƙalau nake ba,akwai abinda yake cin rayuwata da kaɗan kaɗan.
Bani na tashi daga baccin wahalar daya ɗaukeni ba sai a kusan la'asar.
Tashi nayi naga abinci Tunga yakawomin,dama hakan yakasance al'adarsa,bansan mai nayi masa ba ya damu da rayuwata,shin mai nakeyi daya kamata a damu dani?.
Banci da yawa ba na ajiyeshi nabar bukkar. Kai tsaye gida na nufah,nasan waccar sheɗaniyar yarinyar ba lallai ne ta tashi ba tana wajen.
Duk hanyar danabi yara guduwa suke,wasu nayi ƴar dariya wasu kuma na jijjiga kai,amma dai hakan yana min daɗi,naga ana tsorona,koba komai zan jini tamkar sarki.
Pa kwance na ganta luff a inda nace ta tsugunnan,inuwa har da kusa iso inda take.
"Keee...."
Firgitt tayi tatashi zaune,jikinta sai rawa yake na azabar data sha,kaman wacce tayi wanka da rairayi,ƙasa take kallo,amma kana iya gano bushasshen hawayen daya haɗu da ƙasa a fuskarta.
"Tashi ki tafi,gobe ma ki sake sakoni cikin sabgarki"
Yunƙurin tashi tayi,mangar mangar tanufi ƙofar su,wato sai gida an doki kare aka,da sanda yaje satar kajin gidan basu sani ba kuwa.
Takardar da aka aikomin nake karantawa,abinnan yana bani mamaki,yaushe inna ta sakani a makaranta ne,kwata kwata bana tuna shigata makaranta,amma kuma ina karanta abinda aka rubuta da hausa da kuma turanci,ko yaren turanci akayi sainaji inajin mai akace,har naji inason na maida amsa kuma da yaren.
Ƙarar motsin tafiyar mutum naji,hakanne yasa ajiye takardar ina jira naga wanene zai shigo.
Sallamar Sumaimah naji a bakin ƙofar,saida tazo bakin ƙofar naga kayan dana bata wanki ne a hannunta.
A bakin ƙofar ta tsaya,ita bata shigo ba ita kuma bata koma ba,ganin abin har yafara bani haushi yasa nace.
"Idan bazaki shigo ki ajiye ba toki koma dasu"
Da sauri kaman jira take ta tsallako cikin ɗakin,a gaban akwatina ta tsugunna,dayake can take kallo sai hakan yabani damar kallon bayanta. Atamfah ce a jikinta sabuwa,tunda nake ban taba kallonta da sabon kaya ba sai yanzu..
Zuge akwatin tayi ta jera kayan a cikin tass kafin ta mayar ta rufe. Kallon ɗakin nake sai a sannan ma na kulada gyaran da tayiwa ɗakinsa,harda yanar gizon da take jikin ɗakin duk ta cireta,nayi ƙarya idan nace bayyi kyau ba.
Tashi tayi zata fita saikuma ta tsayah,kallonta nayi anan nagane abu takeso tace,ganin yanda bakinta yake motsi.
"Menene"
Na tambayeta saboda na hutasar da itah,nasan in dai a hakanne saimu wuni batace komai ba,so nake kuma ta tafi tabani waje akwai abinda zanyi.
"Uhmm ......uhmm dama inaso nake gidan su Shareefah ne ƙawata,babu nisa kafin magriba zan dawo"
Shuru nayi ina nazarin maganar tata,shin dama na taba cewa karta fitane,intanaso da koma gidansu ma mana,yau ubanta yabani kuɗina yace ƴar sa ta dawo gida ba riƙeta zanyi ba,wani salon munafurci ne hakan ko mai?.
"Shin dama tunda kikazo gidannan kinji nace kada ki fitane?"
Saurin jijjiga kanta tayi tana wasa da ƙasan rigarta,sai tayi kamar an tare bera a buhun daddawa.
"Ahah ba haka bane,Allah ya hani mata da fita daga gidan mazajensu batareda izinin mazajen ba,idan kuma mace ta aikata hakan to mala'iku zasuyi ta tsine mata har taje ta dawo,shiyasa idan mace tanason gujewa hakan to ta tambayi izinin mijinta a duk lokacin dazata fita waje"
"Tohh wata sabuwa,da ba'a garinan kike ba sai nace a ina kikaji,jeki idan zaki wata anguwar ma kada ki sake zuwa kimin wannan iyayin"
"Toh nagode"
Bata jira na bata sake cewa komai ba ta fita da sauri daga ɗakin.
••∆∆∆••
Tunda ƴan gidan sukaga Deejah ta ƙona ɗakin rammah kowa yake masifar tsoronta,komai tayi babu wanda yake cewa uffan a wunin ranar..
Da dare yayi ɗakin yara ammi ta nuna mata,kaman bazata shiga ba kuma sai ta nufi ɗakin,shigarta keda wuyah sukaga yaran ɗakin kowa yana fitowa da gudu,da suna ihu wasu kuma suna matsar ƙwallah.
Matan gidan duk wadda da yaranta a ɗakin fitowa suka yi,jin ihun yara yaƙi ci yaƙi cinyewa.
Asiyah ce tayi ƙarfin halin faɗin abinda ya faru,tunda ita da ɗab girmanta,dan zasuyi shekaru ɗaya da Deejah.
"Muna kwance kawai ji mukayi ta fara dukanmu,wai duk mu fita daga ɗakin mu koma na iyayenmu,ba kowa yaƙi ajiyeta a ɗakinsa ba,itama bazata kwana da kowa ba,kuwa wai duk wanda yasake shiga ɗakin saita vabbakeshi da ransa..
Shuru sukayi suna sauraran Asiyah,yayinda kowa yakama hannun ɗansa yana rarrashinsa,kowa ta abinda yake faɗa ya shige ƙofarsa.
Washagari da safe kamar kullum hayaniya ta kaure ko ina,itadai rammah ranar a gidnasu ta kwana,saboda anyi ta bata baki ta zauna tace sai uwaisu ya rufa mata ɗaki kafin ta dawo,yanzu dole zaije ko ina fallan kwano yake ya nemo yazo ya rufamata ɗakin..
Fitowa tayi tana mitstsika ido,jikinta duƙu duƙu yanda ta kwanta haka ta tashi.
Ƙofar su ammin tashigo ana zuzzubawa yara koko zasu tafi makaranta.
Tana zuwa batayiwa kowa magana ba ta ɗauki ɗan botikin kokon ta kafa a bakinta,ƙwatt ƙwatt saida taga bayansa ta ajiye tana gyara baki.
Yaran da suke zaune a gaban ammi suna jira a saka musu,ganin abinda ya faru suka fara kuka wasu harda burburwa. Sakin baki ammi tayi ludayin garwayawar a hannunta tana kallonta.
"Innar ubaidu wai baki gama saka sukarin bane,ki miƙomin nasamu nasha na tafi gonar can yaukam na dubo,zamu mai taki"
"Uhmm koko kam ai ya ƙare"
"Ke wannan wanne zancen shashanci ne,idan kunyi abincin siyarwa ku hanani yau kam ai nina saya da kuɗi na koh"
"Ehh nima danace maka ya ƙare ai bani na shanye da ƴaƴana ba koh? Ƴar ka ce ta shanye"
"Wacce ƴar tawa wai,ya faɗa yana banƙada labulen ɗakin"
Da Deejah suka haɗa ido tana suɗe bokitin kunun,dariya tayi masa irin ta aljanu,da haƙoranta kamar tsitstsige.
"Na shanye baba,na shanyen kunu,aradu ga zaki kamar an saka zuma,wanda wanccan babannawa yake bani babu suga haka,ashe bayyi ƙaryaba daya ce a cikin gari daɗi kukeji,ko kazar gidannan dana ci jiya tafi zomayen jeji daɗi ,ai nikam naji daɗi na tunda na dawo nan da zama"
Wani irin rammm gaban uwaisu ya buga,shida yake cewa yau zai maidata wajen ubanta yabashi haƙuri,shine zatace wai bazata koma ba anan zata zauna,in shi ina zama da aljana gida ɗaya,kokon da za'a rabawa yaran gidan harda shi,ta kafa kai ta kwankwaɗeshi,da wanne tukunn zaiji? Ga gyaran ɗakin ramma ma zaizo yayi.
Jefarda bokitin tayi can gefe,barass kuwa ya rabe biyu,dama yaji jiki sosai.
Hanyar waje ta nufah tana goge hannunta a jikin kayannata,jinin kazar jiyama yana jikin kayan.Wato haka takeyi shiyasa inta zo kusan mutum warin dauɗa ya dameshi.
Tana fita daga ƙofar Ammi ta kaɗe zaninta ta tashi,kallon uwaisu tayi tareda cewa.
"Inka fita ka siyomin bakitin roba a waje,a gaban idon ka ta fasamin nawa"
Tunzurowa yayi jin abinda tace.
"Mai kike nufi kenan,komai tayi nizan biya,saboda nine nayi ko?"
"In bakaine kayi bama ai ta dalilinka tazo gidan tayi,tunanin ka kenan ni zan dunga ɗaukar asara,saboda nice nayi cacar aka kawomin ita?"
Buuu ya kaɗe rigarsa yayi hanyar waje,da Rabi yaci karo a hanyar mashiga matar ƙaninsa umaru.
Kuka take ta girmanta,hannunta ɗauke da matacin ƙosan ta. Saida tayi kukan ta matse kafin tafara magana cikin masifah.
"Wlh bazan yardaba,uban me akemin a gidan dazanyi haƙuri,ba'a ɗaukemin sabulu ba,magani kokuma ishashshen abinci,nazo na samo kuɗin jarin da taimakon ƴan uwana ina sana'a,kuma azo a nakasa ni wlh sai an biyani,in ba haka ba wlh ɗan sanda zan ƙira"
Tsayawa uwaisu yayi yana kallonta tana masifah tana kuka,ta inda take shiga batanan take fita ba,buɗe baki yayi zai tambayeta yaji wata matar tana faɗamasa abinda ya faru.
"Waccar ƴar taka da tazo jiyace tana suyar ƙosai tashigo ƙofar,batayi wata-wata ba ta dira akan suyar ƙosanta,wanda ta tara a cikin matacin duk ta cinyeshi,a garin ɗiban ƙosan kuma ta zubar mata da man suyar wanda yake kan wutah"
Runtse ido uwaisu yayi yana maimaito jawabin,iyah jiya kawai aka kawota amma tayi asarar da baisan adadinta ba,wannan wace irin masifah ce,tunda yake ko ƴaƴan sa basu taba yimasa abinda tayi ba. Shin ta inama zai fara,gashi tafita waje,yasan a can ma dole sai tayi wani abun. Cikin sanyin jiki ya fita wajen,jikinsa ya haɗa gumi shirkif,duk da sanyin safiyar da ake.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
Ina komawa ɗakin inna tsalle na farayi da murna,banyi zaton zai barni na fita hakan cikin sauƙi ba.
Sai yanzu ne zan yi fita ta daɗi,ba wancan ɗiban ruwan ba,shikenan idan naje sai magriba nadawo.
Hijabi na saka wanda inna mairo tayimin a auren,babu laifi mai kyau nekam a daidai kuɗinsa.
Takalmin shima na ɗakko,dan tunda aka kawoni gidan ban ta'ba sakashi ba sai yau.
Bayan na shirya ƙofar gaji na shiga yi mata sallama,hmmmm zata kulani ne ma,tana fama da jinyar ƴar ta.
Nazo shiga ƙofar tsayawa nayi jin abinda suke cewa.
"Ai duk laifinkine gaji,tun yausshe kike cewa zaki yi maganinsa har yanzu abu yaƙiyi,kai ba abin ka ɗakko masa ƴan daba ba shine shugabansu,mutanen garinma tsoron hukuntashi sukeyi,sannan asiri tun yaushe kike cewa zakiyi har yanzu bakiyi ba"
Atika ce take faɗa tana kuka saboda gaji tana dunduma mata jikinta take faɗa.
"Dallah yimin shuru,ke bakiga abinda kikayi ba koh,kinje kinyi ciki a wajen zubarwa kince nasa ne,dama ai dole zance ya koma kunnensa,kuma sanin kankine ba shuru zayyi ba da wannan lamarin.....waccar yarinyar cema dole zata shiga hannuna na kamata gamm,har wuyanta yayi ƙwari tana gasamin magana son ranta? Lallai batasan wacece niba da alama"
Jijjiga kai nayi jin maganganunnasu ba wasu sabi bane,dama na saba dajin irinsu tun a gidanmu.
Ƙarisawa nayi cikin ƙofarta ta bakina ɗauke da sallama,sun ɗan razana saboda tsarguwar kona ji mai suke cewa,nikuwa ban basu ƙofar dazasu san cewar na jisun ba sam.
"Uhm gaji nizan tafi gidan ƙawata saida magriba zan dawo"
Wata harara ta maka min,daganan bata sake cewa komai ba tacigaba da kulada ƴar tata,nima kuma daman ban tsammaci amsar ba,na faɗa mata ne saboda haƙƙinta ne a matsayinta na wacce muke zaune gida ɗayah.
Tafiyah nake cikin nutsuwa hankali kwance har na isa gidan su Shareefah,kasancewar ranar asabar ce nasan daman tanan bata tafi makarantar islamiyyah ba.
Da tsalle ta tarbeni tana murna muka zauna,sai dariyah take tarasa abincewa,da alama zuwannawa yayi mata bazata.
"Shareefah ya mutanen gidan?"
"Uhm gida kalau yanzu nnan ummah kuwa ta tafi gidan suna"
Bayan mungama gaisawar shuru nayi,idan nace banajin yunwa wlh nayi ƙarya,jikina karkarwa yake kaman an jonamin lantarki,kunya nake ji na roƙeta abinci,amma haka na daure na tambaya.
"Uhm.....Shareefah yunwa nakeji kunada abinci dan Allah"
Zaro ido tayi tana tafe kirji,da alama ta kulada yanda jikina yake karkarwa ne.
"Nashiga uku Sumaimah ji yanda jikinki yaje karkarwa,bankula ba saida kikayi magana nagani. Abinci babu yawa yara sun cinye,amma barina kawo miki sauran kici,inyaso saina yimiki wani abun ko ɗan wake ne"
Tana gama faɗin hakan ta tashi da sauri ta kawomin,tuwon shinkafa ne da miyar taushe.
Malmala biyu ce,saboda yunwar danake ji nan da nan na cinyeshi,kai abinci rahama nan da nan naji jina da ganina sun dawo waral.
Tashi nayi ina tayata muna jefah ɗan waken dayake da yawa tayi harda na gidan,zance muke wanda yawanci rabinsa na islamiyyarmu ne,yanda take bani labarin ƙawayenmu zasuyi aure,wata ƙwallah ce ta zubomin nayi saurin gogewa,uhmm su zasu auri wanda suke so suma suna sonsu.
Shareefah ta kulada yanda yanayina ya sanja,ta buɗe baki zatayi magana kenan Hamisu yashigo ƙanin Shareefan.
"Anty Shareefah gacan ƴan sanda zasu tafi da baban Anty Sumaimah caji office"
"Me ubana kuma? Toh mekuma yayi za'a kaishi caji office"
Shareefah ce ta kalli hamisun cikeda damuwa,musamman ganin yanda yanayin ƙawar tata ya sanja.
"Hamisu mai yafaru,anya kuwa kaji daidai?"
"Wlh shi naji ana cewa,wai wannan ƴar da aka bashi a caca ce take jawo,ta zubarwa matar gidan man suyar ƙosai ta cinye ƙosan kuma,sannan ta ƙone ɗakin inna rammah. Amma abinda yasa aka kamashi yanzun wai wani yaro ta bulawa kai da dutsi,yanzu haka an tafi asibiti dashi kaman bazayyi rai ba,shine da batakai ɗauri ba aka kama Babanku sai yayi biyan kuɗin magani"
Duk maganar dayake ban fahimce shi,wacce ƴa aka bashi a sanadin caca kuma,bayan ni daya bayar wata kuma aka kawo masa? Shareefah na kallah wacce iyah ita kaɗaice nasan zata bani amsar wannan tambayar,dan daga ganin yanayinta ya nuna tasan kwanan zancen.
"Wacce ƴa yake magana akai ne Shareefah?"
Shuru tayi da bazata bani amsa ba,can kuma saita kwashe abinda ya faru ta faɗamin,yanda baba yayiwa ɗan fulani wayo dan ya auri ƴarsa,ƙarshe kuma rishe ya juye dashi......wai ni meyasa irin wannan abubuwan suke faruwa da garinmu ne,kodan muna lungu shiyasa abubuwan ashsha sukayi yawa kai. Cikin garin Kwalin ma haka suke fama da irin waɗannan abubuwan?.
Jijjiga ni Shareefah tayi,tana zaton koh suman tsaye nayi,habadai wannan abun yasakani suman tsaye? Ai naga wanda ya fishi ma.
Ɗaɗɗaya nake jefah ɗan waken a bakina,ɗazu yabani sha'awa sosai,amma yanzu ya fita akaina sam,saboda abinda yafaru.
Tundaga lokacin kuma zancen namu yakoma na Deejah,sabuwar ƙanwar tawa,wani abun nayi dariyah wani na jijjiga kai,ance dai mugunta babu kyau,amma wlh banji tausayinsu ba sam,suma ji yanda naji inda daɗi.
Idan an kwana biyu zanje gidan nima na ganta,yanda ake bani labarin kam batada maraba da aljana.
Ganin duhu yafara yasa na tashi zan tafi,har sannan umman Shareefah bata dawo ba.
"Toh Shareefah barina tafi gida nikam duhu ya fara"
"To shikenan Sumaimah kici gaba da haƙuri komai zai zai zama tarihi,karkiyimata wanke wanken gobe,kiyi zaman ki,zan aiko miki da abin karyawa Inshaallah,to wai shi meyasa bazai dunga baki abinci bane,ba zamansa kike bane?"
"Bamu kai kan wannan ba tukunna,amma kuma a yanda na kula kaman yanada sauƙin kai"
"Eh toh hakane,kaman yanda kika ce zan dunga kawo miki abincin har sai lokacin da taga gurbinki kuka daidai ta,shima kuma dan Allah Sumaimah ki dunga gwada dabararki irin ta mata akansa,idan kinga kuma abin bazai gyaruba sai a san nayi"
Kallonta nake da tana maganar,shin ana samun ƙawa irinta kuwa yanzu,nikam duk da banyi sa'ar mijiba amma ƙawa kam mashaallah kawai zance.
Rungumeta nayi ƙyam ina mayar da kukan dayake idona,saboda godiyar danake son yimata ma bazai isa ba.
Bayan munyi sallama hanyar gidannawa na kama,ɗazu Shareefah tace ko zanje caji office nace mata bazani ba. A tambayar danayi iyah gidnasu kawai na tambaya,koda na tambaya ma nai zanje na iyo,nace masa me? A matsayina dai na ƴar sa
Showing 27001 words to 30000 words out of 60324 words
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Shaida kuma ta nan
09035784150
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[15]
[Goje a mahangar gani]
Har na fita daga gidan rai na bai daina zafi,lallai wannan yarinyar wuyanta yayi kauri. Lokacin danaji maganar nan baƙaramin baci raina yayi ba,kaman ni....nine zatace nayi mata ciki,kai barima na koma nasake tattaka ta dan ubanta.
Juyawa nayi gidan,har nafara shiga na hango gaji ta jefar da Sumaimah a ƙasa,wato akan ta zata huce saboda na daki ƴar ta ko.
Maganganu gajin tafara faɗawa Sumaimah,wacce kana ganin fuskarta kasan abinda take faɗamata ba ƙaramin zafi suke mata ba. Kai mata mata.....shiyasa fah ni banason shirgi dasu,wato rashin shiga harkarta da banayi shima abin magana ne da har za'ayi mata gori dashi.
Niyyar ƙarisawa nayi,ganin gaji tana shirin ɗauke Atika daga inda nace ta tsugunna,dama nasan hakan zata faru,tsoratar da Sumaimah zatayi ta ɗauketa daga wajen,musamman data ganta wawiyah ce batada wayo.
Siririyar maganar ta naji,cikin sanyi take amayarwa gaji duk maganar data fesa mata,dama ta iyah magana haka,nida nayi zaton ma kurmiyace. Tun bata kai haka ba muna yawan cin karo da ita a hanya in zata makaranta,sai ta juyah da gudu kaman taga aljani,tun abin yana bani mamaki har na daina.
Amma yanzu ta dawomin da mamakina,ina ganinta wawiyah ashe tanada wayo,ehh tunda gaji tasaka wannan magana da alama takaita bango ne.
Fitowa nayi daga gidan na tafi inda su Tunga suke hukunta Sageer,har na isa wajen da tunanin faɗan matan a raina.
Lokacin dana isa wajen sun mammaujeshi sun ɗaure shi,a zaune suke suna taɗin siyasa,na wani chairman paty dayake so muyi masa aiki.
Ina isa wajen sukayi shuru tareda bani gaisuwa,amsawa nayi kana na samu waje na zauna.
"Ogah goje gashi nan mun ɗan tabashi kaman yanda ka nema. Iya shegen ma ya iya kawai,ashe ƙaramin ɗan iskane,daga dukan farko fah ya rojaye kaman wata ƙanƙara"
Ragarus ne yafaɗa yana cigaba da jujjuyah sandar hannunsa.
"Hmm ku sunceshi ku kaishi ƙofar gidansu,duk ya isheni bana ma son ganinsa,ku tabbatar kun bar masa jan gargaɗi a rubuce na saka hannuna"
Dama duk masu bin matannan suna lalatasu yanda kasan ƴan daudu haka suke,sai shegen surutun tsiya da ƙarya,matan ma sun fisu ƙwari. Ko mai ma matan suke gani a jikinsu oho.
Jawabin da chairman party yafaɗa suka maiyarmin,akan yanaso muyi masa aiki,saidai suyi masa badai ni ba,dan inada wani aiki da zamu fita da ƙungiyar DC,Jiyah suka turomin takardar inda zan samesu da daddare,za'a tattauna yanda plan ɗin zai tafi,nasan bazai wuce sati ɗaya ba samu fita aikin.Bazan faɗawa sauran abinda yake faruwa,iyah Tunga ne kawai yasan zancen. Yau ma nake shirin naɗashi shugaba mai riƙon ƙwaryah kafin na dawo,bazayyi yu dan bana nan na hanasu yin aiki ba,musamman kuma dana san zasu samu kuɗi sosai idan sunyi ɗin.
"Bakomai za'ayi masa aiki,duk da bananan a lokacin,amma zan yimasa gargaɗi kaman ina nan. Zanyi tafiyah maybe wani satin,zan iyah kaiwa satin ban dawo ba,dan haka Tunga zai zagorance ku idan bana nan.
Basuji daɗin abinda nace ba,sannan nasan dole zasuso sanin ina zanje,amma koda zasu sani ba yanzu ba tukunna.
Jeji na nufah Ina riƙe kai,wannan ciwon kan narasa daga ina yake zuwa,duk sanda nafara jinsa saina dunga jin kaman ba nanne yakamata na kasance,kaman inada wani wajen bayan nan,kaman akwai wata rayuwar bayannan danake da itah. To amma a ina take,yaushe zan bar wannan masifaffen ciwon dayake juyar da rayuwata,haka nake kwana na tashi,amma tunda nake bantaba jin nutsuwa ba,kullum acikin duhu nake,lokaci lokaci ko a bacci ina hango wani haske ɗan ƙarami a can nesa,sai nayi gudu nayi gudu inaso na kamoshi sai ya bace ya ƙyaleni ni kaɗai.
Ƙarisowa wajen bukkar tawa tacikin jejin nayi,da sanina nayi mata fenti baƙi,saboda a baƙin wajen kawai nake iyah bacci ,hakan ma nafison cikin jeji,shiɗimma ba cikin salama ba,sai an kai ruwa rana,kowa ka tambayeshi yasan ba ƙalau nake ba,akwai abinda yake cin rayuwata da kaɗan kaɗan.
Bani na tashi daga baccin wahalar daya ɗaukeni ba sai a kusan la'asar.
Tashi nayi naga abinci Tunga yakawomin,dama hakan yakasance al'adarsa,bansan mai nayi masa ba ya damu da rayuwata,shin mai nakeyi daya kamata a damu dani?.
Banci da yawa ba na ajiyeshi nabar bukkar. Kai tsaye gida na nufah,nasan waccar sheɗaniyar yarinyar ba lallai ne ta tashi ba tana wajen.
Duk hanyar danabi yara guduwa suke,wasu nayi ƴar dariya wasu kuma na jijjiga kai,amma dai hakan yana min daɗi,naga ana tsorona,koba komai zan jini tamkar sarki.
Pa kwance na ganta luff a inda nace ta tsugunnan,inuwa har da kusa iso inda take.
"Keee...."
Firgitt tayi tatashi zaune,jikinta sai rawa yake na azabar data sha,kaman wacce tayi wanka da rairayi,ƙasa take kallo,amma kana iya gano bushasshen hawayen daya haɗu da ƙasa a fuskarta.
"Tashi ki tafi,gobe ma ki sake sakoni cikin sabgarki"
Yunƙurin tashi tayi,mangar mangar tanufi ƙofar su,wato sai gida an doki kare aka,da sanda yaje satar kajin gidan basu sani ba kuwa.
Takardar da aka aikomin nake karantawa,abinnan yana bani mamaki,yaushe inna ta sakani a makaranta ne,kwata kwata bana tuna shigata makaranta,amma kuma ina karanta abinda aka rubuta da hausa da kuma turanci,ko yaren turanci akayi sainaji inajin mai akace,har naji inason na maida amsa kuma da yaren.
Ƙarar motsin tafiyar mutum naji,hakanne yasa ajiye takardar ina jira naga wanene zai shigo.
Sallamar Sumaimah naji a bakin ƙofar,saida tazo bakin ƙofar naga kayan dana bata wanki ne a hannunta.
A bakin ƙofar ta tsaya,ita bata shigo ba ita kuma bata koma ba,ganin abin har yafara bani haushi yasa nace.
"Idan bazaki shigo ki ajiye ba toki koma dasu"
Da sauri kaman jira take ta tsallako cikin ɗakin,a gaban akwatina ta tsugunna,dayake can take kallo sai hakan yabani damar kallon bayanta. Atamfah ce a jikinta sabuwa,tunda nake ban taba kallonta da sabon kaya ba sai yanzu..
Zuge akwatin tayi ta jera kayan a cikin tass kafin ta mayar ta rufe. Kallon ɗakin nake sai a sannan ma na kulada gyaran da tayiwa ɗakinsa,harda yanar gizon da take jikin ɗakin duk ta cireta,nayi ƙarya idan nace bayyi kyau ba.
Tashi tayi zata fita saikuma ta tsayah,kallonta nayi anan nagane abu takeso tace,ganin yanda bakinta yake motsi.
"Menene"
Na tambayeta saboda na hutasar da itah,nasan in dai a hakanne saimu wuni batace komai ba,so nake kuma ta tafi tabani waje akwai abinda zanyi.
"Uhmm ......uhmm dama inaso nake gidan su Shareefah ne ƙawata,babu nisa kafin magriba zan dawo"
Shuru nayi ina nazarin maganar tata,shin dama na taba cewa karta fitane,intanaso da koma gidansu ma mana,yau ubanta yabani kuɗina yace ƴar sa ta dawo gida ba riƙeta zanyi ba,wani salon munafurci ne hakan ko mai?.
"Shin dama tunda kikazo gidannan kinji nace kada ki fitane?"
Saurin jijjiga kanta tayi tana wasa da ƙasan rigarta,sai tayi kamar an tare bera a buhun daddawa.
"Ahah ba haka bane,Allah ya hani mata da fita daga gidan mazajensu batareda izinin mazajen ba,idan kuma mace ta aikata hakan to mala'iku zasuyi ta tsine mata har taje ta dawo,shiyasa idan mace tanason gujewa hakan to ta tambayi izinin mijinta a duk lokacin dazata fita waje"
"Tohh wata sabuwa,da ba'a garinan kike ba sai nace a ina kikaji,jeki idan zaki wata anguwar ma kada ki sake zuwa kimin wannan iyayin"
"Toh nagode"
Bata jira na bata sake cewa komai ba ta fita da sauri daga ɗakin.
••∆∆∆••
Tunda ƴan gidan sukaga Deejah ta ƙona ɗakin rammah kowa yake masifar tsoronta,komai tayi babu wanda yake cewa uffan a wunin ranar..
Da dare yayi ɗakin yara ammi ta nuna mata,kaman bazata shiga ba kuma sai ta nufi ɗakin,shigarta keda wuyah sukaga yaran ɗakin kowa yana fitowa da gudu,da suna ihu wasu kuma suna matsar ƙwallah.
Matan gidan duk wadda da yaranta a ɗakin fitowa suka yi,jin ihun yara yaƙi ci yaƙi cinyewa.
Asiyah ce tayi ƙarfin halin faɗin abinda ya faru,tunda ita da ɗab girmanta,dan zasuyi shekaru ɗaya da Deejah.
"Muna kwance kawai ji mukayi ta fara dukanmu,wai duk mu fita daga ɗakin mu koma na iyayenmu,ba kowa yaƙi ajiyeta a ɗakinsa ba,itama bazata kwana da kowa ba,kuwa wai duk wanda yasake shiga ɗakin saita vabbakeshi da ransa..
Shuru sukayi suna sauraran Asiyah,yayinda kowa yakama hannun ɗansa yana rarrashinsa,kowa ta abinda yake faɗa ya shige ƙofarsa.
Washagari da safe kamar kullum hayaniya ta kaure ko ina,itadai rammah ranar a gidnasu ta kwana,saboda anyi ta bata baki ta zauna tace sai uwaisu ya rufa mata ɗaki kafin ta dawo,yanzu dole zaije ko ina fallan kwano yake ya nemo yazo ya rufamata ɗakin..
Fitowa tayi tana mitstsika ido,jikinta duƙu duƙu yanda ta kwanta haka ta tashi.
Ƙofar su ammin tashigo ana zuzzubawa yara koko zasu tafi makaranta.
Tana zuwa batayiwa kowa magana ba ta ɗauki ɗan botikin kokon ta kafa a bakinta,ƙwatt ƙwatt saida taga bayansa ta ajiye tana gyara baki.
Yaran da suke zaune a gaban ammi suna jira a saka musu,ganin abinda ya faru suka fara kuka wasu harda burburwa. Sakin baki ammi tayi ludayin garwayawar a hannunta tana kallonta.
"Innar ubaidu wai baki gama saka sukarin bane,ki miƙomin nasamu nasha na tafi gonar can yaukam na dubo,zamu mai taki"
"Uhmm koko kam ai ya ƙare"
"Ke wannan wanne zancen shashanci ne,idan kunyi abincin siyarwa ku hanani yau kam ai nina saya da kuɗi na koh"
"Ehh nima danace maka ya ƙare ai bani na shanye da ƴaƴana ba koh? Ƴar ka ce ta shanye"
"Wacce ƴar tawa wai,ya faɗa yana banƙada labulen ɗakin"
Da Deejah suka haɗa ido tana suɗe bokitin kunun,dariya tayi masa irin ta aljanu,da haƙoranta kamar tsitstsige.
"Na shanye baba,na shanyen kunu,aradu ga zaki kamar an saka zuma,wanda wanccan babannawa yake bani babu suga haka,ashe bayyi ƙaryaba daya ce a cikin gari daɗi kukeji,ko kazar gidannan dana ci jiya tafi zomayen jeji daɗi ,ai nikam naji daɗi na tunda na dawo nan da zama"
Wani irin rammm gaban uwaisu ya buga,shida yake cewa yau zai maidata wajen ubanta yabashi haƙuri,shine zatace wai bazata koma ba anan zata zauna,in shi ina zama da aljana gida ɗaya,kokon da za'a rabawa yaran gidan harda shi,ta kafa kai ta kwankwaɗeshi,da wanne tukunn zaiji? Ga gyaran ɗakin ramma ma zaizo yayi.
Jefarda bokitin tayi can gefe,barass kuwa ya rabe biyu,dama yaji jiki sosai.
Hanyar waje ta nufah tana goge hannunta a jikin kayannata,jinin kazar jiyama yana jikin kayan.Wato haka takeyi shiyasa inta zo kusan mutum warin dauɗa ya dameshi.
Tana fita daga ƙofar Ammi ta kaɗe zaninta ta tashi,kallon uwaisu tayi tareda cewa.
"Inka fita ka siyomin bakitin roba a waje,a gaban idon ka ta fasamin nawa"
Tunzurowa yayi jin abinda tace.
"Mai kike nufi kenan,komai tayi nizan biya,saboda nine nayi ko?"
"In bakaine kayi bama ai ta dalilinka tazo gidan tayi,tunanin ka kenan ni zan dunga ɗaukar asara,saboda nice nayi cacar aka kawomin ita?"
Buuu ya kaɗe rigarsa yayi hanyar waje,da Rabi yaci karo a hanyar mashiga matar ƙaninsa umaru.
Kuka take ta girmanta,hannunta ɗauke da matacin ƙosan ta. Saida tayi kukan ta matse kafin tafara magana cikin masifah.
"Wlh bazan yardaba,uban me akemin a gidan dazanyi haƙuri,ba'a ɗaukemin sabulu ba,magani kokuma ishashshen abinci,nazo na samo kuɗin jarin da taimakon ƴan uwana ina sana'a,kuma azo a nakasa ni wlh sai an biyani,in ba haka ba wlh ɗan sanda zan ƙira"
Tsayawa uwaisu yayi yana kallonta tana masifah tana kuka,ta inda take shiga batanan take fita ba,buɗe baki yayi zai tambayeta yaji wata matar tana faɗamasa abinda ya faru.
"Waccar ƴar taka da tazo jiyace tana suyar ƙosai tashigo ƙofar,batayi wata-wata ba ta dira akan suyar ƙosanta,wanda ta tara a cikin matacin duk ta cinyeshi,a garin ɗiban ƙosan kuma ta zubar mata da man suyar wanda yake kan wutah"
Runtse ido uwaisu yayi yana maimaito jawabin,iyah jiya kawai aka kawota amma tayi asarar da baisan adadinta ba,wannan wace irin masifah ce,tunda yake ko ƴaƴan sa basu taba yimasa abinda tayi ba. Shin ta inama zai fara,gashi tafita waje,yasan a can ma dole sai tayi wani abun. Cikin sanyin jiki ya fita wajen,jikinsa ya haɗa gumi shirkif,duk da sanyin safiyar da ake.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Shaida kuma ta nan
09035784150
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[16]
[Sumaimah a mahangar gani]
Ina komawa ɗakin inna tsalle na farayi da murna,banyi zaton zai barni na fita hakan cikin sauƙi ba.
Sai yanzu ne zan yi fita ta daɗi,ba wancan ɗiban ruwan ba,shikenan idan naje sai magriba nadawo.
Hijabi na saka wanda inna mairo tayimin a auren,babu laifi mai kyau nekam a daidai kuɗinsa.
Takalmin shima na ɗakko,dan tunda aka kawoni gidan ban ta'ba sakashi ba sai yau.
Bayan na shirya ƙofar gaji na shiga yi mata sallama,hmmmm zata kulani ne ma,tana fama da jinyar ƴar ta.
Nazo shiga ƙofar tsayawa nayi jin abinda suke cewa.
"Ai duk laifinkine gaji,tun yausshe kike cewa zaki yi maganinsa har yanzu abu yaƙiyi,kai ba abin ka ɗakko masa ƴan daba ba shine shugabansu,mutanen garinma tsoron hukuntashi sukeyi,sannan asiri tun yaushe kike cewa zakiyi har yanzu bakiyi ba"
Atika ce take faɗa tana kuka saboda gaji tana dunduma mata jikinta take faɗa.
"Dallah yimin shuru,ke bakiga abinda kikayi ba koh,kinje kinyi ciki a wajen zubarwa kince nasa ne,dama ai dole zance ya koma kunnensa,kuma sanin kankine ba shuru zayyi ba da wannan lamarin.....waccar yarinyar cema dole zata shiga hannuna na kamata gamm,har wuyanta yayi ƙwari tana gasamin magana son ranta? Lallai batasan wacece niba da alama"
Jijjiga kai nayi jin maganganunnasu ba wasu sabi bane,dama na saba dajin irinsu tun a gidanmu.
Ƙarisawa nayi cikin ƙofarta ta bakina ɗauke da sallama,sun ɗan razana saboda tsarguwar kona ji mai suke cewa,nikuwa ban basu ƙofar dazasu san cewar na jisun ba sam.
"Uhm gaji nizan tafi gidan ƙawata saida magriba zan dawo"
Wata harara ta maka min,daganan bata sake cewa komai ba tacigaba da kulada ƴar tata,nima kuma daman ban tsammaci amsar ba,na faɗa mata ne saboda haƙƙinta ne a matsayinta na wacce muke zaune gida ɗayah.
Tafiyah nake cikin nutsuwa hankali kwance har na isa gidan su Shareefah,kasancewar ranar asabar ce nasan daman tanan bata tafi makarantar islamiyyah ba.
Da tsalle ta tarbeni tana murna muka zauna,sai dariyah take tarasa abincewa,da alama zuwannawa yayi mata bazata.
"Shareefah ya mutanen gidan?"
"Uhm gida kalau yanzu nnan ummah kuwa ta tafi gidan suna"
Bayan mungama gaisawar shuru nayi,idan nace banajin yunwa wlh nayi ƙarya,jikina karkarwa yake kaman an jonamin lantarki,kunya nake ji na roƙeta abinci,amma haka na daure na tambaya.
"Uhm.....Shareefah yunwa nakeji kunada abinci dan Allah"
Zaro ido tayi tana tafe kirji,da alama ta kulada yanda jikina yake karkarwa ne.
"Nashiga uku Sumaimah ji yanda jikinki yaje karkarwa,bankula ba saida kikayi magana nagani. Abinci babu yawa yara sun cinye,amma barina kawo miki sauran kici,inyaso saina yimiki wani abun ko ɗan wake ne"
Tana gama faɗin hakan ta tashi da sauri ta kawomin,tuwon shinkafa ne da miyar taushe.
Malmala biyu ce,saboda yunwar danake ji nan da nan na cinyeshi,kai abinci rahama nan da nan naji jina da ganina sun dawo waral.
Tashi nayi ina tayata muna jefah ɗan waken dayake da yawa tayi harda na gidan,zance muke wanda yawanci rabinsa na islamiyyarmu ne,yanda take bani labarin ƙawayenmu zasuyi aure,wata ƙwallah ce ta zubomin nayi saurin gogewa,uhmm su zasu auri wanda suke so suma suna sonsu.
Shareefah ta kulada yanda yanayina ya sanja,ta buɗe baki zatayi magana kenan Hamisu yashigo ƙanin Shareefan.
"Anty Shareefah gacan ƴan sanda zasu tafi da baban Anty Sumaimah caji office"
"Me ubana kuma? Toh mekuma yayi za'a kaishi caji office"
Shareefah ce ta kalli hamisun cikeda damuwa,musamman ganin yanda yanayin ƙawar tata ya sanja.
"Hamisu mai yafaru,anya kuwa kaji daidai?"
"Wlh shi naji ana cewa,wai wannan ƴar da aka bashi a caca ce take jawo,ta zubarwa matar gidan man suyar ƙosai ta cinye ƙosan kuma,sannan ta ƙone ɗakin inna rammah. Amma abinda yasa aka kamashi yanzun wai wani yaro ta bulawa kai da dutsi,yanzu haka an tafi asibiti dashi kaman bazayyi rai ba,shine da batakai ɗauri ba aka kama Babanku sai yayi biyan kuɗin magani"
Duk maganar dayake ban fahimce shi,wacce ƴa aka bashi a sanadin caca kuma,bayan ni daya bayar wata kuma aka kawo masa? Shareefah na kallah wacce iyah ita kaɗaice nasan zata bani amsar wannan tambayar,dan daga ganin yanayinta ya nuna tasan kwanan zancen.
"Wacce ƴa yake magana akai ne Shareefah?"
Shuru tayi da bazata bani amsa ba,can kuma saita kwashe abinda ya faru ta faɗamin,yanda baba yayiwa ɗan fulani wayo dan ya auri ƴarsa,ƙarshe kuma rishe ya juye dashi......wai ni meyasa irin wannan abubuwan suke faruwa da garinmu ne,kodan muna lungu shiyasa abubuwan ashsha sukayi yawa kai. Cikin garin Kwalin ma haka suke fama da irin waɗannan abubuwan?.
Jijjiga ni Shareefah tayi,tana zaton koh suman tsaye nayi,habadai wannan abun yasakani suman tsaye? Ai naga wanda ya fishi ma.
Ɗaɗɗaya nake jefah ɗan waken a bakina,ɗazu yabani sha'awa sosai,amma yanzu ya fita akaina sam,saboda abinda yafaru.
Tundaga lokacin kuma zancen namu yakoma na Deejah,sabuwar ƙanwar tawa,wani abun nayi dariyah wani na jijjiga kai,ance dai mugunta babu kyau,amma wlh banji tausayinsu ba sam,suma ji yanda naji inda daɗi.
Idan an kwana biyu zanje gidan nima na ganta,yanda ake bani labarin kam batada maraba da aljana.
Ganin duhu yafara yasa na tashi zan tafi,har sannan umman Shareefah bata dawo ba.
"Toh Shareefah barina tafi gida nikam duhu ya fara"
"To shikenan Sumaimah kici gaba da haƙuri komai zai zai zama tarihi,karkiyimata wanke wanken gobe,kiyi zaman ki,zan aiko miki da abin karyawa Inshaallah,to wai shi meyasa bazai dunga baki abinci bane,ba zamansa kike bane?"
"Bamu kai kan wannan ba tukunna,amma kuma a yanda na kula kaman yanada sauƙin kai"
"Eh toh hakane,kaman yanda kika ce zan dunga kawo miki abincin har sai lokacin da taga gurbinki kuka daidai ta,shima kuma dan Allah Sumaimah ki dunga gwada dabararki irin ta mata akansa,idan kinga kuma abin bazai gyaruba sai a san nayi"
Kallonta nake da tana maganar,shin ana samun ƙawa irinta kuwa yanzu,nikam duk da banyi sa'ar mijiba amma ƙawa kam mashaallah kawai zance.
Rungumeta nayi ƙyam ina mayar da kukan dayake idona,saboda godiyar danake son yimata ma bazai isa ba.
Bayan munyi sallama hanyar gidannawa na kama,ɗazu Shareefah tace ko zanje caji office nace mata bazani ba. A tambayar danayi iyah gidnasu kawai na tambaya,koda na tambaya ma nai zanje na iyo,nace masa me? A matsayina dai na ƴar sa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10 Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21