ina fatan Allah ya rage masa nauyin ruwan daya jawowa kansa,har ya jawowa wasu ma.
Lokacin dana isa gidan wasu masallatan ma ana ƙiran sallah. Kaman kullum gaji tana ta fama da yaranta,nidai bance mata na dawo na wuce ƙofarmu.
Alwalar magriba nayi na shiga ɗaki,riƙeta zanyi ba lallai na fito ba sai gobe. Ta wani lokacin gwara gidannan,koba komai mutum zai samu nutsuwa da daddare.
Bayan nayi isha fitowa nayi zan shiga banɗaki,goje nagani da wasu baƙaƙen kaya ya fito daga cikin ɗakinsa,wata hula yasaka a kansa itama baƙa irin kayan jikinnasa,yana rataye da wata baƙar jaka.
Bai kulada ni ba saboda yanda na ɗauke numfashina har ya wuce,ban taba ganinsa da irin waɗannan kayan ba,inda banga yanayin jikinsa ba da kuma kayan,bazance shine ba.
Ina kuma zaije da darennan sanye da waɗannan kayan,rai na dai bai kwanta da lamarinba na shige banɗakina.


__***__

[Goje a Mahangar gani]


Daidai misalin ƙarfe 8:00pm na dare na shirya cikin kayan da suka aikomin,wanda shine unform da kowa zai saka na fita aiki.
Bayan nagama saka kayan ɗaya jakar na ɗakko,bindiga ce a ciki sabuwa dal babba mai babban aiki,sai kuma wasu ƙannan bomb guda biyar,sai kuma hula mai tare poison gas guda biyu da kuma wuƙaƙe ƙanana wanda ake sakawa a jiki saboda kota kwana.
Jinjina kai nayi ina mamakin ƙaurin suna irin na wannan ƙungiyar,dole manyan sojojin ƙasa da jami'an tsaro su bazama neman ganin sun wargaza ya kam. Makamansu ko wasu sojojin basu da su. Anya kuwa babu hannun wani babban ƙasa a cigaban ƙungiyar nan. Oho koma menene su suka sani,ni ina ruwana.
Daukar jakar nayi na lanƙaya a bayana,yayinda nake duba agogon hannuna naga lokaci shima duk yana daka cikin abubuwan da suka aikomin dashi.
Bayan na fita daga gidan hanyar bakin gari na nufah,inda jan jira motar dazata ɗaukeni.
Banyi minti talatin ba kuwa sai gata tazo,baƙace dal mai numfashi,kota chairman ɗin garinmu bata kaita ba.
Buɗe gidan baya nayi na shiga,drivern yaja muka nausa wata hanyar da tayi jejin.
Wannan karon basu rufemin idi ba har muka isa sansani wancan lokacin.
Shiga mukayi cikin wajen,wannan karon ba hanyar da mukabi wancan lokacin muka bi ba,watace daban.
Mutumin daya tabeni a karon farko yauma dashi nayi arba,saidai yanzu suit ne a jikinsa yana hakimce a wata jar kujera,wajen ya ƙawatu kam sosai,babu yanda za'a yi mutum yasan akwai wannan daular anan wajen haka.
Mutanen wajen na kalla mun kusa mu goma sha huɗu dukkanmu sanye da kaya iri ɗaya.
"Uhm uhm to abokan aiki barkanku da isowa,sabin zuwa kuma muna yi muku barka da shigowa. Dukkanku sabine tunda baku taba haɗuwa da ogah na uku ba,saidai wasu a cikinku ba wannan ne aikinsu na farko ba,wasu kuma yanzu zasu fara.
Mun taraku ne saboda akwai aikin dazamu fita yau,saidai inaga bazayyi ba,dan har yanzu jirgin da muke jira ya kawomana kayan aiki da kuma bayanan yanda abin zai kasance bai iso ba.Ɗaya yaranmu dasuke dajin Kaduna su sunfita aiki,ku kuma sai munga taku alamar."
Zancen banza kenan,dama kawai taramu sukayi su ganmu,shiyasa fah na tsani zama a ƙasan wani.
Tashi nayi na tsaye zan fita daga wajen batareda nace wani abunba.
"Kai goje ina kuma zakaje,inkana shugaba a sansaninka kayi abinda kaga dama,har ka ture wani daga kujerarsa ka hau,to anan karkayi wannan tunanin sam,in mutum a cikinku yana cin ƙasa to nan ta shuri ce"
Juyowa nayi na kalleshi,ohh tsoro yake karna yi wani abun na karbi kujerar sa komai? Har yavani dariya ma.
"Hmm haba ogah da gimanka kafara wannan maganar tun yanzu? Gida dai zantafi,tunda abinda nazo dominsa bazai faru ba"
Sauƙe ajiya yayi ganin ba abinda yake tunanin bane,wanne wawa ne zaizo waje lokaci guda yakai farmaki,ai sai yaga kamun ludayin kowa tukunna.
"Ba tafiya kowa zayyi ba,munada wajen motsa jiki da horo,a can zaku zauna har zuwa lokacin dazaku fita aiki"
Toh hakan bai wani batamin rai ba,dama ina buƙatar hakan,sannan nariga na sallami yarana ma kafin nazo ɗin.
Har mun tashi zamu bar wajen wani ya shigo wajen da sauri.
Gaban wanda ake ƙira da ogah na huɗun ya nufah,ƙusƙus sukayi magana,daga nan sai ya fitah.
"Toh da alama ma basai munyi jiran ba,mission ɗinku a yau sai fara,an kawo kayan aiki da bayanan"
Yana faɗan hakan ya fitah,kayan aiki kuma,bayan waɗanda suka bamu hadda wasu zasu sake bayarwa..
Muna dai nan zaune suka fara shigowa da wasu jakakkanuna daban.

Wasu motocine dogaye masu tafiyah irin cikin sirinnan a jeji,su zamu shiga zuwa garin gwagwalada. Daga nan kuma a sanar damu wa zamu ƙwamushe.
A yanda naji ana faɗa wai zamu kai sati biyu kafin mu koma gida,na fadawa Tunga sati guda kuma zanyi,nasan zasuyi ta jiran dawowa ta,gashi babu dama in ana cikin aiki mutum ya yi waya gida.


Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*


Mallakar SADI-SAKHNA


PROFICIENT WRITER ASSOCIATION



*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[17]


"Kufitar dani a wajennan nagaya muku,akan me banci sisin kowa ba kuce zanyi kwannan cell"
Jijjiga ƙarfen ɗakin uwaisu yake yana ihu maganganu,tunda rana yake wannan abin har dare yayi,ɗazu kamma abinnasa yafi yawa dayaga lallai a nan wajen zai kwana.
Ƴaƴan sa basu tabayin abinda zai kawoshi nan wajen ba duk iya shegensu,sai gashi wata can daba jininsa ba tasaka shi shiga wannan ɗakin.
Wari da zarni duk sun isheshi,tun yana toshe hanci har ya daina yafara zage zage. Abincin da aka turo masa a kwano tunda rana ko kallonsa bayyi ba,dan rainin hankali yana cikin wannan abinma zasu kawo masa abinci. Cigaba yayi da maganganunsa,ganin har yanzu babu wanda ya kulashi a cikinsu,sai kace ma basu san yanayi ba.
"Nace muku ku buɗeni na tafi gida,meyasa zaku rufeni anan wajen banyi laifin komai ba,wacce tayi hakan ai yakamata ku kamo bani ba"
"Dama da bamu ganta bane ai muka kamaka,ƴar ka tayi ayyuka laifi a gari ta gudu,a ƙa'idar kame kuma dama idan ba'aga ƴa ba ana iya kama uba ko uwa,in ba'aga miji ba ana iya kama mata. Dan haka bazamu sakeka ba sai ka an biya beli kokuma mun kama ƴar ka tukunna,domin laifukan da tayi da yawa.ta karya jari,ta ƙone ɗaki,ta nakasa yaro,sannan kuma ta kaji da dama"
"Wai inji uban waye yace muku ƴata ce ne? In banda munafurci kowa a garinnan yasan kan yawan ƴaƴana,yasan babu wannan abar a cikinsu,haka kawai ga can ubanta a jeji baza'a kamashi ba saini,da girma na da komai,dan rashin adalci"
"Kaga dan Allah kayi mana shuru,wanne girma gareka,duk garinnan babu wanda baisan irin abinda kake aikatawa ba,naga a irin waɗannan laifinnaka ka tura ƴarka auren goje saboda ka hallaka rayuwar ta. Duk da haka baka saduda ba kake ƙoƙarin cutar ɗan fulani ka aure ƴar sa. Dayake Allah ba azzalumin bawa bane sai ya nuna maka ƙarshenka,indai baka daina abinda kake ba ai bakaga komai bama. Kuma kayi shuru ka cika mana kunne,su wanda suka jigaka a cacar su zo su karbeka mana"
Shuru uwaisu yayi tareda samun waje ya zauna,duk abinda Ƴan sandan suka fadamasa babu ƙarya ko ɗaya a ciki. Taya zaiga laifinsu gaskiya suke faɗa,ƙanana dasu suna cimasa mutunci. Inda yakama girmansa kaman sauran sa'anninsa na anguwa duk haka bazata kasance ba.
Tunowa yayi lokacin da aka kai wani dattijo a unguwarsu gidan kurkuku da ɗansa yayi sata,a ranar muganen anguwa aka haɗu harda ɗansa Musbahu aka fito dashi. Amma shi dayake babu wanda yake daraja shi dashi da babu duk ɗaya,ko mutum ɗaya bai gani ba yazo wajensa. Duk mai yajawo masa banda budurwar zuciyarsa.?
Cikin sanyin jiki ya koma ya zauna a ƙasan cell ɗin,abincin da aka kawo masa ya buɗe,jallof ce cakwaɗaɗɗiyah,baka bambamceta da farar shinkafah inba kaga abin taruhu a jikiba.
Haka yasaka hannunsa ya yasa yakai bakinsa,saida ya runtse ido kafin ya hadɗiye,saboda yanda take faɗa da maƙogaransa kan bazata shiga ciki ba.


[Sumaimah a mahangar gani]


Da safe ina zaune naji muryar hamisu ƙanin Shareefah,tashi nayi na fito daga ɗakin na karbi kwanon hannunsa.
Godiya nace yayiwa ummansu da Shareefah kafin koma daki na rufe ƙofah.
Ƙosai ne a ciki mai zafi sannan aka soyah,da murnata na zauna na cinye tass nasha ruwa.
Gado na koma na sake kwanciyah ban fita ba kaman koyaushe,dan dama haka na kimtsa zanyi ɗin.
Can wajen kaman shaɗayan rana naji ana ƙira sunana,muryar namiji ce amman ba goje bane.
Saurin tashi nayi zaune na mutstsike idanuwana na fito.
Da tunga muka haɗa ido yana can ɗan gefe da baranda a tsaye.
Muna haɗa ido murmushi yayimin kana ya kauda idonsa.
"Ina kwana matar ogah"
Uhm wai matar ogah manya,na faɗa a raina,a fili kuwa ɗan murmushi nima nayi tareda cewa.
"Lafiyah kalau Tunga ya zirga zirga"
Amsa wa yayi a taƙaice kafin yafaramin bayanin abinda ya kawoshi.
"Uhm gashi wannan ki riƙe a wajenki,nasan ba lallai yabaki wani abun ba dazai tafi"
Mamaki yabani ganin ya miƙomin dubu biyu.
"wannan kuɗin fa na menene"
"Ko zaki siya wani abun idan buƙatar hakan ta taso,yace bayan ya tafi na kula da duk al'amuransa,baice da harda iyalansa ba amma kuma ninaga kema yakamata a baki wani abin a kuɗin da muka samo,koba komai bazaki rasa abin siya ba"
"Kulada al'amura,tafiyah yayi ne?"
Na tambaya cikeda mamaki.
Shima saida ya zaro ido jin irin tambayar danayi masa,yo ba dole yayi mamaki ba,yaji mata batasan mijinta yayi tafiyah ba.
"Ohh bakisan cewar yayi tafiyah,wani aikine ya taso wanda ya samu bada daɗewa ba,shine suka nemeshi jiyah akan zai fara aikin,yacemin dai na kula masa da komai sati guda zayyi ya dawo. Laah kuma hakane ba lallai ki sani ba,dan yace na faɗamiki kada komai da kike na aikinki ya sauyah,kiyi shi tamkar yana nan"
Ɗaga kai nayi a zahiri,yayinda ta baɗini kuma zuciyata tayi baƙiƙƙirin,wato zayyi tafiyah amma bai faɗamin ba,saima aikowa dayayi akan nacigaba dayimasa gyare gyare,tunda yake baisan cina ko shana ba saidai nayi masa aiki koh? Idan dan yana ganin ya sameni ne ta sanadin caca ai Ko dabbarsa ma ta sanadin wasan kalankuwa ya samota,amma yana kulada ita sosai,sai nice wato zai maida goruba koh?.
Ɗagawa Tunga kai kawai nayi,dan bansan mai zance masa bama. Allah ya dawo dashi lafiyah,shine abinda nasamu cewa bayan Tunga ya tafi. In kulada shi yaso ya bani haƙuri,ganin banason hakanne yasa ya tafi.
Ina nan tsaye a wajen naga gaji ta fito daga ƙofarta,wajenda kayan wanke wankenta suke,ƙuda yabisu yabisu har sun bushe saboda daɗewa a wajen.
Tsayawa tayi a gaban kayan tana kallonsu, kursiyyahce ta kawo kwanon dataci awara zata ajiye a wajen.
"Ke kursiyyah kije ki ƙiramin kawule ya debomin ruwa kuyi wanke wanke"
"Wai nikam gaji wlh bazanyi ba,haka kawai naga tun safe aka ce Atika tayi tace bazatayi ba,saini za'a saka"
Ƙofar tashige tana wani wantsala kamar tarwaɗa. Nidai ina nan tsaye ina kallonsu.
Da rana ma hamisu ne yasake kawomin abinci,amma sannan kam nace masa kada ya sake kawowa.
Dan kafin ya kawomin kursiyyah ta kawomin shinkafa da wake mai da yaji,wai gashi inji gaji nacigaba da aikina na safe.
Murmushi nayi ganin kwana ɗaya kawai harta daddara ta dawo hanyah. Ban musa ba na karba,danni ma daman hakan nakeso,banason kawomin abincin da ake daga gidan su Shareefan.
Ɗaukar daya nayi daga cikin abincin naci,ɗayan kuma na ajiye na yamma.
Washagari da safe ɗumame kaɗan ta gaji tabani,duk yadda naso abin ya tafi yanda zamuyi zaman lafiyah nasan hakan bazai faru ba sam,dan haka tunda nice mai son mu daidaita dole ni zanyi haƙuri da itah,kaman yanda naga inna tana yi da itan,gobe inna zata yi sati guda da tafiyh,sauranta sati ɗaya ta dawo kenan.
Kuɗin da Tunga ya kawomin na ɗako dubu ɗaya a ciki.Soda ta kawomin nayi wanke wanken,sabulun danakeyi dashi ma dama yaƙare wanda inna tasiyamin,nayiwa goje wanki dashi.
Hijabina na saka wanda nake sallah na fito waje ko zanga wani a cikin yaran unguwa ya sayomin sabulu da omo.
Na ɗan daɗe a tsaye kafin na samu wani almajiri da robarsa a hannu yana wurgawa sama.
"Dan mallam dan Allah zo na aikeka mana"
Na fada ina ƙirnsa da hannuna,tahowa yayi da hanzarinsa,kayan jikinsa na kalla,duk sun yayyage sunyi daƙan daƙan dasu,yana dosoni sai zarnine yake tashi. Wai rayuwa kenan,wato idan kaga rayuwar wani dole ka godewa Allah.
"Iyah ta gani"
"Yawwa dan Allah omo zaka siyomin da sabulu a wancan shagon"
"Tah"
Karba yayi ina kallonsa ya nufi shagon,kasancewar ba nisa ina hangoshi har yaje ya dawo.
Hamsin na dauka a kuɗin na bashi,ya karba yana godiyah ya tafi,nikuma na shigo gida.
Ƙofar gaji na shiga siyan awara,tunda nasamo sanji.
Sallama nayi ta amsa ciki ciki,bata huce ba kenan.
"Gaji a bani awara ta ɗari"
Nafaɗa ina miƙamata gudan ɗari biyar ɗin da aka bani a canji,tsayawa tayi tana kallon kuɗin naɗan lokaci kafin ta karba.
"Tohh amarya an fara samun kuɗine a wajen miji?"
"Amarya bazata samu kuɗi ba dole sai in miji ne yabata?"
"To ba cass bare ass,kana kuma babu jiyarar ƴan uwa,ai dole mu tambaya"
"Akwai wasu marasa cass da ass ɗinma a gidan dasuke siyan kayan masu cass da ass ai"
Hmm tace kawai kafin ta ƙirgamin awarar,dan tagano da Atika nake ƴar ta,shigar kaya a gidannan wanene ya kaita,kuma ba sana'ar fari bare ta baƙi,kuɗin jikinta sunfi na jarin awarar ma.
Canjina ta miƙomin na ɗari huɗu da kuma awarar tawa.
Karba nayi bansake cewa komai ba na bar ƙofar,zama nayi na cinye tass nasha ruwa kafin na fito yin wanke wanken.
Ga ɗiban ruwa ma yana jirana na randa ta data goje,da kuma saniyar can,dan dai kar a ɗaure dabba a hanata abincine tausayi ma bazai barka ba,da wlh bazan sake bata komai ba sai ranar dazai dawo,hmmm ga gyaran ɗakinsa ma,shima bazanyi ba sai ana gobe zai dawo inyaso.
Wani satinne ina? Kafin sannan ma idan nayi sa'a inna tadawo lokacin.

__**__

"Toh sabon salo lallai yarinyar nan in banyi da gaske ba tsoronta zan faraji a gidannan..a ina tasamu kuɗi haka hadda sanja ɗari biyar,naga siyayya tayi na sabulu da omo ma a leda"
Buɗar bakin kursiyyah wacce take zaune a gefe sai cewa tayi.
"Ai inna Tunga ne wannan abokin yahya goje ya kawo mata kuɗin,dan ina banɗaki naji yana cewa wai,gashi ta rike kafin gojen yadawo. Tafiya yayi kuma zayyi sati bai dawo ba"
"Ke ƴar nan,kenan baya garin? Haba biri yayi kama da mutum,shiyasa ban ganshi ya shigo gidan ba har zuwa yanzu,wato kuɗi aka kawo mata ta dunga kashewa kafin ya dawo koh. Kuma ta rasa mai zatayi sai siyan omo da sabulu?"
"Wanke wanke zatayi mana dashi"
"Naga na aika ki kaimata sodar wanke wanken,wanne iyayine sai tayi da omo,kaman wata ƴar gayu,kowa ma ai da sodar yakeyi"
"Ohh gaji baki sani ba,ranar naji tana faɗawa inna wai intayi da soda hannunta tsatstsagewa yakeyi"
Barin ƙirga awarar gaji tayi tana kallon kursiyyah,wacce tagama shirin fita tallen safen.
"Oho dama hakane,ya akayi bansan zancen ba kuwa,ni inacan ina tunanin banza,ga hanya mai sauƙi wajen kamata da hannuna,sai nayi mata abinda da ƙafarta zatazo har wajena ta tsugunna,badai ni take mayarwa magana ba"
Gaji ta ƙarisa maganar tana murmushin mugunta.

Oohp anan zan tsaya fah sorry baikai sauran ba da shafi huɗu,wlh na gaji ne shiyasa🙏🏼 muhaɗu gobe kawai.





Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*


Mallakar SADI-SAKHNA


PROFICIENT WRITER ASSOCIATION



*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[18]






Nafito kenan daga ɗaki naga ɗan gaji kursiyyah tana wanki da sabuluna,mamaki abin yabani sosai.
Da sauri na ƙarisa wajen nace.
"Kursiyyah me kike da sabuluna,bakuda shi ne saikin ɗau nawa?"
"Bamudashi ya ƙare,shine gaji tace na ari naki taga kin sayo rannan"
Jimmm nayi ina jinta cikeda takaici,wannan wacce irin rayuwa ce,ace mutum bashida katabus na rayuwarsa,kallon sabulun nayi a hannunta ya kusa ƙarewa saura ƙiriss,gashi gobene cikar sati guda da goje zai dawo,inna ma a satin gaba nake saka ran ganinta.
Miƙa mata hannu nayi ta bani sabulun,bance komai ba na nufi ɗaki,kuɗin dana ajiye dubu ɗaya a wanda Tunga yabani na tafi zan ɗauka,dan omon danake wanke wanke dashi shima ya ƙare,saina siyo dukka.
Kwanon na jawo a cikin carbet ɗin inna inda kuɗin yake,amma mee.....ina buɗewa dubu ɗaya tace ɗaukeni a hankali.
Wata razana nayi ina jijjiga kai,ahah ahah haka bazai faru ba samm,meyasa toh meyasa hakan zata faru?
Waye ya ɗaukemin kuɗi,sannan a wanne dalili?
Hawayene suke zubomin ina kallon kwanon,amma sam na gagara taresu ballantana na hanasu fitowa. Saida nayi mai isata kafin nayi shuru,nasan babu wanda ya haɗa abinnan sai gaji,wato ita dai duk hanyar dazaya wulaƙantani in bata bi ba batajin daɗi koh?.
Tunani natafi meyasa toh ta aiko ƴar ta ta ɗaukemin sabulu,sannan kuma suka sace min kuɗin,kaddai gaji ta gane banason wanke wanke ko wanki da soda kai?? Inkuwa hakane wannan kam shine dalili.
Tunowa nayi da kayan goje da ban wanke ba akan sai yau tukunna,ga kuma gyaran ƙofarsa shi ba na tashi sam.
Guntun sabulun na ɗauka nafita waje,wankin kayan zanyi kafin lokaci ya ƙure.
Basuda yawa kayan dan haka sabulun ya isheni na wanke su tass,ina gamawa ƙofarsa naje na gyara itama kafin na dawo ɗaki na kwanta.
Sauran wanke wanke shikuma ya zanyi dashi,shine hanyar abincina kaɗai,dan haka dole nayi,kuma ko a shari'ah tafita tunda tabani abinda suma dashi suke wanke wanken. Shareefah ce tafaɗomin a raina,amma nayi saurin kawarda tunanin ta,ahah bazayyiwu dan naga tana taimakamin shikenan daga matsala ta tasomin saina tunkareta ba,rayuwata ce gidan aure na ne,dan haka dolene na maganceshi da kaina basai wani ya taya ni ba.
Ina nan kwance ina duniyar tunanin kirsiyyah tashigo da kwanon abincina,dayake na kula bashine target ɗinta ba hanani abincin,koban je ba tana kawomin.
Ajiyewa tayi a tsakar ɗaki,harta tashi zata tafi nace.
"Ke kursiyyah a cikinku waye ya shigo ɗakinnan ya ɗauki dubu a cikin kwano?"
Dafe ƙirji tayi tareda zaro ido,daga nan kuma saita zunduma ihu ta fita da gudu tana kuka kaman na zare mata rai.
Da kallo na bita bakina a sake,anya waɗannan yaran mutanene,yara ƙanana daku amma duk kuna fanɗare,tashi nayi na zauna,dan nasan gaji tana zuwa. Aikuwa hasashena bai tafi a banza ba,in gama zama najiyo sababinta tana tahowa.
"Dan tsabar munafurci da samun wajen zama,har kin samu bakinda zaki ƙira ƴaƴana barayi,uban me kika taba kamasu sun ci miki tunda kike?"
Har ɗakin tashigo ta riƙe kunkumi tana tayi,nidai kallonta nayi sau ɗaya
Showing 30001 words to 33000 words out of 60324 words