kafin na ɗauke idona. Ta inda tashi ba tanan take fitaba harta gama wanda ya isheta tafitah.
Wani hawayennne naji yana shirin zibomin na takaici,kai.......shima bai isa ba,yayi ta jiƙemin fuska Kenan,ya isheshi haka yayi rabonsa.
Kwanon abincin na ɗauko na cinye,dama ban taba ƙoshi dashi ba,cikina har ya saba da wannan.
Alwala na ɗauro nayi sallah,daga nan kuma sai bacci,dan shikam babu laifi ina samunsa a gidan,bakaman gidanmu ba.
Ban daɗe da kwanciya ba kukan saniyar goje ya tasheni,da sauri na fito daga ɗakin na nufi kewayennata,kar itama a sace ta kamar kuɗina,goje yazo yace nina sayar ta,inada a ranar kwanana ya ƙare a duniyah.
Bayan mutum naga yana jujjuyata,gabana ne yayi rass,ban saduda ba dai nayi ta maza na leƙa.
Da Tunga muka haɗa ido,aikuwa sai na sauƙar da ajiyar zuciyah himmm.
Shima daya fuskar tawa saida yayi murmushi.
"Ohh kinace barawo ne,in banda abinki wanene a cikin garinnna sai saci sanuyar goje?"
"Uhm to duk da hakan dai"
"Dama nazo gyara wajennata ne,wataƙila gobene zai dawo,duk da yace ki kulada ida amma nasan ba lallai ki iya gyara wajen ba."
"Hakane kam nagode sosai tun......uhm wai menene ainihin sunanka ne?"
Danni banason waɗannan sunayen haukar dasuke sakawa kansu..
Jimm yayi kaman mai tunani,can kuma sai yace.
"Sunana Al'amin"
"Suna mai ma'ana amma ka boyeshi,nagode al'amin barina tafi to tunda naga kaine"
Ohh a zuciyata ji nake kaman nace masa su gaji sun ɗauke kuɗin daya bani,amma nasan hakan ba abune mai yiyuwa ba,bazan iyah faɗaba sam.
Haka na bar wajen na nufi ɗakin inna.
Tun ana gobe goje zai dawo har an kwana huɗu babu shi babu alamarsa,inna ma dazata dawo tun jiya bata dawoba.
Ko bazasu dawo bane guduwa sukayi suka barni,ni bata goje nake bama,in yanaso kar ya dawo tacan tacan huta roro,amma inna ji nake kaman mahaifiyata ce ta tafi tabarni.
Jiya bacci dan barawone shiyasa yasamu damar ɗaukata,tunani sunyimin yawa barkatai,ga kuma ciwon ta hannyena sukeyi na yin amfani da soda.
Da ita ake amfani a komai na gidan,har wanka ma saita aiko su kursiyyah waisu kawomin,saboda tsabar munafurci da mugunta.
Duk matakan danake bi wajen bata taba hannuna sosai ba dole saida tayimin illah a ƙarshe,kwana biyar ne kacal dana fara amfani da ita,amma sai kace an saka hannyena a wuta matar ta tashi haka suka koma.
Shi kansa abincin ma bata bani wanda zai isheni yanzu,banda karkarwa babu abinda jikina yakeyi wani lokacin.
Gunwa zanjene ma da matsalata,gidanmu zanje wanda sunsan dama da hakan suka kawoni dan su rabu dani,kokuma ƙawar tawa da banida aiki sai ɗora mata wahala. Gaskiya hakan da kunyah,zanyi haƙuri na zauna,idan har ajalina kenan Allah yasa na cika da imani.
Warware hannyen nayi da tsumman danake sakawa indai zan taba ruwa,ko kuma abu wanda zamemin illah.
Hanyar wajen saniyar sa na nufah domin zuba mata abinci,da inajin haushin sakamata abinci,amma yanzu itama tausayinta nakeji,wai a yanda nake ɗinna ita kuma dani ta dogara na zuba mata abinci,nida ko bani nawa ya isheni ba'ayi.
Kwanonnata na ɗauke zan ɗebo mata dusa,saidai me.....da kayan goje na haɗa ido a cikin kewayen saniyar,duk ta takasu sunyi duƙu-duƙu kaman basu taba ganin ruwa ba.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Shine dai kaɗai abinda bakina yakeda ƙarfin amsabatawa.
Ɗiban kayan nayi na taho dasu zuwa ƙofarmu. Sakasu nayi a gaba inda kallonsu,harda singlet ɗinsa da komai ma na kayansa aka zuba a wajen,sai zarnin fitsarin saniyah sukeyi.
Yanzu shin taya zan fara wanke kayannan,kayana ma bana wankewa bazan iya ba,hannaye na bazasu iya gurzawa su fita ba,inaga kuma waɗannan harda su jeans,na iyah wankewa.
Sakasu nayi a cikin ruwa na zuba sodar akai na ajiyesu,idna suka jiƙa saina wanke.
Tun da rana har dare,idan naje wankewar ina fara mitstsikawa in ciwo ya ratsani saina ajiye na tafi,naga ta kaina nikam a gidannan,taya zan rayu da haka?.
Da daddare haka nayi yarfe hannu har bacci ya ɗauke,yanzu yakai ko tafasu a sallah banayi,inaga idan naje asibiti yankesu zasuyi suce sun rube,inaji ina gani za'a maidani kuturwa???? Gaskiya gobe dole nasan abinyi.....
Washagari da safe na tashi zan yunƙura kenan naji zuutt a marata..wata sabuwa kenan inji ƴan caca.
Wayyo shima ciwonnan wannan watan kam da yayimin uzuri mana,kenan wasa wasa na kusa wata a gidannan.
Yunƙurawa nayi na tashi zaune ina cije baki,saboda riƙewar da marata tayi gamm.
Banɗaki na lojana naje,daga nan na dawo ɗaki na kwanta,shigowar kursiyyah nagani da ajiyemin ɗumame. Yauda masifa kenan,na faɗa a raina.
Cinye tuwonnan zanyi bazan barshi ba,idan kuma ta gano naci tuwonta banyi wanke wanke ba bansan yazamu ƙare ba.
Duk da ciwon danake ji haka na daure na sauƙa ƙasan ɗakin,buɗe kwanon nayi mukayi ido da ido da karin tuwon guda ɗaya. Dama kullum ɗaya take sakamin kaman rai..
Miyar babu daɗi haka na suɗeshi,jinsa nake kaman nama saboda yunwa.
Amai nafaraji yana tahomin,dan dama ko a gida haka nakeyin al'ada da wuyah,kowanne wata saina sha wahala a ranar farko.
Komawa nayi kan gadon inna,nayi rigingine ina kallon sama,saboda amai ɗin ya koma. Idan na bari tuwonnan ya su'buce daga cikina bansan lokacin dazan samu wani abincin ba a yau.
[Goje a mahangar gani]
Kwana goma kenan tunda muka tafi wajen aikin,fasa banki mukaje yi a gwagwalada,to bayan munyi da alama ƴan sanda da sojoji sun sani da wuri,hakanne yasa aikin ya baci,aka kashe wasu daga cikinmu,wasu kuma aka kamasu. Mudai bamufi mu huɗu ba muka tsira a cikin mutum sha biyar .
Jeji muka furma da guda har sannan kuwa bamu jefar da kuɗin da muka ɗebo ba yana wajenmu.
A jejin muka buya tsawon wannan lokacin,saboda neman da jami'an tsaro suke mana.
Munsha baƙar wuyah muka dawo sansanin ƙungiyar.
Masu jiran ƙofar ne suka buɗe mana muka shiga,bayan sun gama bincike mu tukunna.
A gajiye muka wuce inda ogan yake muka jefa masa jakunkunan kuɗin.
Saida ya ƙaremana kallo saikuma ya tuntsire da dariyah yana nuna mu da hannu.
Yayi kaman daƙiƙa biyar yana wannan dariyah kana kuma yayi shuru yana goge hawayen da dariyar ta sakashi.
"Ku kalleku sai kace birirrika,da kyau da kyau,ni banyi zaton ma zaku tsira ba wlh,danaga baku dawo ba inace na kasheku ne"
Numfashina sama sama yakeyi saboda baƙinciki,yayinda zuciyata ke rayamin na kasheshi kawai ya daina numfashi. Saidai haka na danni zuciyata nayi masa tambaya.
"Meyasa kake tunanin zamu mutu?"
"Saboda nina ƙira ƴan sanda da sojoji na faɗamusu zakuzo yin fashi a banki. To ya kaji toh,duk lokacin dana ɗebi sabin yara haka nakeyi musu,tahaka nake gwada jarumtar su,shiyasa bamuda mutane dayawa sai jarumai. Ya kaji salo.........."
Tun kafin ya gama maganar nakai masa wani farmaki,fitt na so yanke maƙogaransa,saidai dayake ya san dabarun faɗa yagoce da sauri na sameshi a jijiyoyin wuyan sa na dama.
Ihu yasaka yana dafe wajen,yayinda jini yafara tsartuwa yana wanke rigar jikinsa..
Yaran dazuke wajen da gudu suka ɗaukeshi zuwa wani wajen da bansan inane ba,yayinda nikuma wasu suka rirriƙeni zuwa wani ɗaki mai kama da prison.
Idona a tsaye yake gamm babu alamar tsoro ko kuma nadamar abinda nayi masa,hasalima takaici naji da ban yanke maƙogaronsa ba.
Ina nan a cikin cell ɗin har tsawon kwana uku,waɗanda suka kawoni wajenne suka fito dani.
Kaya suka miƙomin iri ɗayah da wanda ogan yake sakawa,cikin girmamawa suka miƙamin kayan tareda yimin alamun na biyosu.
Wani ɗaki suka nunamin nashiga,akwai gado a ciki da kuma banɗaki,ba laifi yayi kyau kam.
Wanka nayi na wanke wannan ɗauɗar jejin,duk da ma ni ba gwanin tsafta ba,amma naji daɗi sosai.
Kayan da suka bani na saka kana na fito.
Cigaba da sakeyi da binsu har mukazo wajenda aka taramu da farko.
Maimakon ogannmu yanzu wani mutumine sanye a suit akan kujerar.
Bashida suffar ƙarfi amma kuma yana da suffar sanin duniya akan fuskarsa,sannan kuma kana ganinsa kasan kuɗi ya zauna masa.
Murmushi yayi kana ya min alamar na matso,ba musu kuwa cikin nima nuna isata na ƙarisa wajen.
"Goje kake da suna koh? Ka burgeni sosai ka burgeni da jarumtar daka nuna jiyah,wanda hakan yasa na baka matsayinsa,shiyasa ka ganka da waɗannan kayan. Saidai ba tsallen da kayi ya kawoka tabb da rijiyah,idan ka sa ke yin wani to zaka jika a ciki tsundummm,wanda zaka iya yin dubu baka fito ba.
Nine shugaba na ukun da ake cewa zaku haɗu dashi in kuka tsallake aikin farko,a samana akwai shugabanni biyu,ni nabiyun nasani bansan na farkon ba,shigaba na biyune yasan wanene na uku. Dan haka barkanka da zamowa na hannun damana"
Tafi yafara yayinda sauran ƴan kungiyar ma suka fara,lallai wajennan akwai haɗari,jiya na lahanta shugabansu har sun maidani a matsayinsa??.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
*Duk wanda shafinnan yamasa daɗi yayi comment please,finally dai Sumaimah tah............ku karanta ku gani dai........*🤣🤣🤣
________________________________
*Book 1*
Chp[19]
Gyara tsayuwa ta nayi bayan sun gama tafin.
"To nagode shugaba da wannan karramawar,amma batun rijiya ni dama dana so yin tsalle ba nufina zuwa wajen rijiyah ba,kaine ka kaini wajen rijiyar,dan haka yin tsallena na faɗa rijiyar ma duk yana wajenka. Mun tafi akan zamuyi sati ɗaya,gashi munyi sati biyu bamu koma gidaba"
"Karka damu da wannan zaku kowa zai iya tafiya gidansu,aikinnan ya gamu saurna kuma nagaba idan yataso.
Kuɗin da kuka samu nasarar ɗakkowa kungiya bazata karba ba an bakushi ku raba,su ɗau kashi ɗaɗɗaya su baka kashi biyu."
Naji daɗin kuɗin tunda dama abinda yakawoni kenan ,amma nayi mamaki da banjisu a cikin raina sosai ba.
Mota DON3 ɗin yabani kyauta,saidai nace masa banaso,danna kula a ɗan tsorace yake dani karna yi masa tawaye kaman oganmu,amma ni bashine a gabana ba sam,so nake naje naga wacce wainar su Tunga suke toyawa.
Madadin haka wani na ɗauka a mutane wajen ya tuƙoni zuwa garinna mu wanda yake district ɗin gwagwaladanne.
Da daddare na iso,ban wuce gidaba sai kawai na nufi madakatarmu,babu kowa dan haka kai tsaye ɗakina dayake cikin jejin na nufah.
Jakar kuɗin na ajiye kawai nayi kwanciyata,saboda narama baccin wahalar da banyi ba kwana da kwanaki.
Hasken ranar daya hudo ta rufin ɗakinne ya haske ido na,wanda hakan yasakani yin miƙa na tashi na zauna.
Fitowa nayi daga cikin bukkar na nufi kogi,wanda yake a ɗan gangare idan mutum yayi ƴar tafiyah.
Wanka nayi kana nayi alwala,salloli biyu ake bina,isha asuba da kuma azahar wacce akayi yanzu..
Ina cikin yin sallahr Tunga ya shigo bukkar,ganin ina sallah yasa ya tafi.Nasan abinci zaije ya kawomin.
Bayan na gama jakar kuɗin danazo da itah na buɗe buzun dayake tsakiyar ɗakin,kuɗin na zuba a ciki sauran kuma na barsu a jakar.
Jakar kayan aikina ma bazan koma da itah gidaba duk anan zan barsu.
Shigowa yayi yana cikin rarraba kuɗin a kan buzu,kallo ɗaya yayi musu ya kawar idonsa tareda miƙamin kwanon abincin daya riƙo.
"Ogah ga abinci,ka dawo kuma babu magana sai kawai naganka a jeji"
"Kamawa tayine,a gajiye nake shiyasa banshiga garinnan ku ba,ya aikin dana barku dashi ya tafi?"
"Yatafi yanda ake so,kawaidai kuɗinne bai bamuba,ana wannan matsalar sanjin kuɗin"
"Ga wannan ka bi kan kowa da rabonsa,ni barina wuce gida na sanja kaya"
Kuɗin na miƙa masa dami masu yawa,cikin fara'ah da washe baki kuwa ya karba.
"Ogah ta samu kenan,shiyasa fah mukeyinka,inka samu kana yaga mana,ba kaman tsohon kwarkwaroncan ba daka gama dashi"
A ƙaramar jaka na saka sauran kuɗin wanda zanyi amfani dasu na fitoh.
Hanyar gida na nufah,kaman kullum kowa ya ganni sai ya sanja hanya.
Ina shiga ƙofar tawa na ganta kaca kaca,yanda na tafi haka na dawo na sameta babu abinda aka taba.
Buɗe ɗakin nayi na shiga,shi da alamar anyi masa shara kaman sau ɗaya dana tafi,cije baki nayi ina jijjiga kai,lallai ma yarinyar nan ta rainani.
Cire kayan jikina nayi na zubasu gefe.
Gajeren wandona da singlet nake nema,amma banga waɗanda nake son sakawar ba,nan na tuna su na cire lokacin dana tafi.
Fitowa nayi na nufi kewayen saniyata,tana kallona tafara jujjuyawa,gabanta ƙwaraff babu abinci ko kaɗan. Saidai kuma amma babu rama a jikinta,to yaushe kenan take bata abinci,kodai ba ta bata kai?.
Ƙofar innan nashiga a zuciye,mai zan gani kaya nagani a cikin bokiti an jiƙasu. Kuma indai ba gizo idanuna yakeminba kayana nagani a jiƙe a cikin bokiti,wannan kuma wanne wari suke fitarwa haka.
Nasan dai kayana duk dattinsi bazasuyi wannan warin ba.
Dan takaici bansan lokacin dana bankaɗa labulen ɗakin innan ba na shiga.
A kwance take sai sharar bacci take hankalinta kwance,wani cije baki nayi tareda runtse ido,zuciya ta tafarfasa take,yayinda ƙwaƙwalwata ke kwaranyomin wanne nau'in hukuncin dazanyi mata.
Fita nayi daga ɗakin naƙira su durwa wanda na barsu a wajen Tunga,ɗazu da suka ganni a hanya suka biyoni,bokitin data jiƙamin kayannawa na ɗauka na shiga dashi cikin ɗakin shima......hmmm yau waye zai hanani hukuntaki,na daɗe banga wanda ya rainamin hankali kamar ta ba.
[Sumaimah a mahangar gani]
Bayan na gama cinye tuwon inanan kwance naji kursiyyah tashigo ɗakin.
"Sumaimah wai kizo inji gaji kiyi wanke wanke,ko bakisan hadda kwanukan yin awara ba a ciki?"
"Kije kice mata yau baxan iya yin aiki ba banida lafiyah"
"Chabɗi wlh ba wani rashin lafiyah,bakida lafiyar ne zaki cinye kuma tuwon dana kawo miki? Ai wlh saina cewa gaji wai kince bazakiyi ba ne"
Tana gama faɗin hakan ta fita daga ɗakin,runtse ido na nayi lokacin da cikinnawa yayi wani danƙa kaman zai cire taciki.
Tun safe nake juye juye akan gadon,bani na samu bacci ba sai wajen azahar tukunna.
Baccin duk da yana cikeda yunwa amma yana min daɗi sosai. Kaman a sama naji sauƙar ruwa a jikina,wata ajiyar zuciya nasaki tareda tashi na zauna ina rarraba ido.
Warin kashin shanu naji a cikin ruwan haɗe da warin soda. Tofarwa wanda yashiga bakina nake ina tari. Har sannan ban dawo hayyacina naga waya aikatamin hakan ba,amma nasan ba maiyyimin wannan aika aikar sai gaji.
Juyowa nayi,saidai maimakon naga gajin,da fuskar kare muka haɗa ido yana min gurnani,saikuma wasu ƙafafu a tsaye. Binsu nayi da kallo zuwa sama,har idanunnawa suka haɗu dana goje,wanda ƙasumbarsa ta ƙara yawa,ga idonnan kaman na zaki yaga abin farautarsa.
Ihu nakeson yi kozan tashi daga mafarkin danake,amma kuma nasan ba mafarkin bane zahiri ne..
Matsawa nake da baya har nakai jikin gini akan gadon,tunda nasan shine ban ɗaga idona na sake kallonsa ba.
Magana yafarayi da wannan maganar tasa mai diri.
"Yaushe nayi wasan dazaki rainani,shin abinda nasakaki kenan dana tafi,nace miki kada ki karya ɗaya daga cikin ayyukan dana sakaki,amma wani abin takaicin ko guda ɗaya daga cikinsu bakiyi ba,wato duk abinda zanyi nayi koh?"
"Dan Allah kayi haƙuri wlh"
Fizgo hannuna yayi ya jefani a tsakiyar ɗakin,jikina banda karkarwa babu abinda yake,saboda razanar danayi jinina ya tsinke sai zuba yake duk ya bata kan gadon da kuma jikina,nasan yagani amma ko a jikinsa,Allah yasama yasan menene.
"Ki rufemin baki,kada ki kuskura ki ambaci wannan kalmar da na tsani jinta in anyimin laifi wato haƙuri,saboda bana haƙurin"
Since sarƙar jikin karen hannunsa yayi,da alama banni dashi zayyi ya fiffigani,aikuwa hakanne dan sunshe shi yayi yana shirin barin ɗakin.
Wani takaici ne gamida baƙin ciki suka tokare min maƙoshi,take kuwa sukayi nasarar kawarda tsoronsa dayake cikin zuciyata,yazamana haushinsa da kuma mamaki irin na halinsa sunfi gaban tsoron danakeyi masa. Wannan ba mutum bane,taya mutum zai dunga jin tsoron halitta irin wannan ma.
"Dakata kada ka fitah"
Nikaina nayi mamakin umarnin dana bashi,yaushe nasamu wannan jarumtar haka? Tsayawar kuwa yayi bai fitan ba,ba wai danna isa ne yasakashi tsayawar ba,saidan mamaki daya cikashi.
Juyowa yayi tareda ɗaga gira yana kallona,yayinda nima na ɗaga nawa idon nasaka su a nasa,saƙo nake son isarwa da ruhinsa bawai shi ba,saƙon kuma bazai kai inda nakeso ba idan ba idonsa nake kalla ba.
"Badai kasheni kakeson yi ba,idan kasheni zakayi ka kasheni da kanka,basai kasaka halittar da batayiwa Allah komai ba ɗaukar rai,Naga abubuwa da yawa a rayuwata sannan duk da banda galihu a duk ina naje,amma hakan bashi zai saka nakasa tsarewa kaina darajata wanda Allah yabani na ƴa mace. Bana fatan labarin mutuwa ta ya yaɗu cewa karene ya yayyagata a ɗaki har ta mutu,gwanda mutane suce mijinta ne ya yankata,wanda bai san cinta ba,baisan shanta ba,baisan ya ta kwana ko ta tashi ba,dabbarsa ta fita daraja,Dan kawai yayi tafiyar da bata san ya tafi ba,yadawo yaga batayi aikin daya sakata ba,bai tambayi dalili ba kawai sai ya yankata. A wannan tafiyar bai ajiye mata abinci ba ko kuɗin magani,sannan bai bata izinin tafiyah ko ina ba,shin dutse ya ajiye kamai,saniyar sa ya damu da itah akan a bata abinci,amma matar da ajiye ko oho. Duk da hakan tayi iya koƙarinta wajen ganin cika umarnin daya bata,amma ƴan gindasu sunƙi barinta ta cika ɗin,shikuma bai biɗi sanin daliliba hukunci kawai ya iya zartarwa na son kansa."
Kukane ya kufcemin na abubuwan da suka faru a gidan wanda suka dawo cikin kaina.
"Indai wannan rayuwar ce mai kamada ta bautar mutanen farko to wlh ka kasheni goje bana tsoro,duk hukuncin dazaka min na daɗe da sanin kwatankwacinsa,kaya da kake faɗa kuma ƴaƴan gaji ne suka zuba a kewayen saniya,na kasa wankewa ne saboda hannyena ciwo ne dasu......bazan iyaba ka ɗau raina kawai kaman yanda kake iƙirari ko yaushe,ka ɗauka kawai na huta,dama tunda nake mai na tsinta na farinciki a duniyar ne??? Kullum zullumin mai zai faru. In baka kasheni bama yunwar cikina zata kasheni,gaji bazata sake bani abinci ba nasan,saboda bazan iya yimata aikin da innayi take bani ba. Dan haka ni gwanda ka kashenin ma kafin yunwar da kasheni"
Rarrafawa nayi na riƙe ƙafar wandonsa,har raina ni na gaji da wannan zaman rayuwar.
Jikina karkarwa yake na wuyah,dakuma kukan danakeyi,karen dayake gefena sai gurnani yake,amma ba tashi nake ba,na daina ma tsoronsa,mai jiran mutuwa wanne tsoro zaiji ne"
"Tashi .....ki tashi nace"
Abinda yakeson nayin nasan bazan iya ba,amma barina gwada nagani.
Miƙewa nayi daga rarrafen inaso na tsaya akan ƙafata,wani juuuuu jiri yaɗebeni,kafin idona ya rufe sai naji ni a hannun mutum ba tsakar ɗaki ba.
Nauyi idanuwan sukayimin,amma haka na dage na buɗeshi,akan farin cilin idonnawa ya sauƙa,fanka tanayi walwal a samana.
Gefe na kaikaita kaina na kalla,window nagani na glass ga kuma farin fenti,tunani na fara na shin a ina nake ne.
Yunƙurin tashi nayi sai naji hannuna a ɗaure,hannayen na kalla duk an ɗaɗɗauresu da bandeji,da alama magani aka shafamun to waye yayi min.
Allura na gani a ɗayan hannun wata igiya tayi sama ruwa yana shiga jikina,Asibitine wai??
Na tambaya a raina,gyaran murya naji hakanne yasa na kalli mutumin dayake kan kujera a zaune,tun ɗazu yake kallo na ban kulaba.
Ƴar razana nayi ganin ya kafeni da ido.
"Meyasa kika taba abinda kinsan jikinki bayaso?"
"Soda ce"
"Ban tambaye ki menene ba,cewa nace meyasa kike amfani da itah,bayan kinsan jikinki bayaso,Tunga ya faɗamin cewar yabaki dubu biyu,mai kika siya toh?"
"Uhm na
Showing 33001 words to 36000 words out of 60324 words
Wani hawayennne naji yana shirin zibomin na takaici,kai.......shima bai isa ba,yayi ta jiƙemin fuska Kenan,ya isheshi haka yayi rabonsa.
Kwanon abincin na ɗauko na cinye,dama ban taba ƙoshi dashi ba,cikina har ya saba da wannan.
Alwala na ɗauro nayi sallah,daga nan kuma sai bacci,dan shikam babu laifi ina samunsa a gidan,bakaman gidanmu ba.
Ban daɗe da kwanciya ba kukan saniyar goje ya tasheni,da sauri na fito daga ɗakin na nufi kewayennata,kar itama a sace ta kamar kuɗina,goje yazo yace nina sayar ta,inada a ranar kwanana ya ƙare a duniyah.
Bayan mutum naga yana jujjuyata,gabana ne yayi rass,ban saduda ba dai nayi ta maza na leƙa.
Da Tunga muka haɗa ido,aikuwa sai na sauƙar da ajiyar zuciyah himmm.
Shima daya fuskar tawa saida yayi murmushi.
"Ohh kinace barawo ne,in banda abinki wanene a cikin garinnna sai saci sanuyar goje?"
"Uhm to duk da hakan dai"
"Dama nazo gyara wajennata ne,wataƙila gobene zai dawo,duk da yace ki kulada ida amma nasan ba lallai ki iya gyara wajen ba."
"Hakane kam nagode sosai tun......uhm wai menene ainihin sunanka ne?"
Danni banason waɗannan sunayen haukar dasuke sakawa kansu..
Jimm yayi kaman mai tunani,can kuma sai yace.
"Sunana Al'amin"
"Suna mai ma'ana amma ka boyeshi,nagode al'amin barina tafi to tunda naga kaine"
Ohh a zuciyata ji nake kaman nace masa su gaji sun ɗauke kuɗin daya bani,amma nasan hakan ba abune mai yiyuwa ba,bazan iyah faɗaba sam.
Haka na bar wajen na nufi ɗakin inna.
Tun ana gobe goje zai dawo har an kwana huɗu babu shi babu alamarsa,inna ma dazata dawo tun jiya bata dawoba.
Ko bazasu dawo bane guduwa sukayi suka barni,ni bata goje nake bama,in yanaso kar ya dawo tacan tacan huta roro,amma inna ji nake kaman mahaifiyata ce ta tafi tabarni.
Jiya bacci dan barawone shiyasa yasamu damar ɗaukata,tunani sunyimin yawa barkatai,ga kuma ciwon ta hannyena sukeyi na yin amfani da soda.
Da ita ake amfani a komai na gidan,har wanka ma saita aiko su kursiyyah waisu kawomin,saboda tsabar munafurci da mugunta.
Duk matakan danake bi wajen bata taba hannuna sosai ba dole saida tayimin illah a ƙarshe,kwana biyar ne kacal dana fara amfani da ita,amma sai kace an saka hannyena a wuta matar ta tashi haka suka koma.
Shi kansa abincin ma bata bani wanda zai isheni yanzu,banda karkarwa babu abinda jikina yakeyi wani lokacin.
Gunwa zanjene ma da matsalata,gidanmu zanje wanda sunsan dama da hakan suka kawoni dan su rabu dani,kokuma ƙawar tawa da banida aiki sai ɗora mata wahala. Gaskiya hakan da kunyah,zanyi haƙuri na zauna,idan har ajalina kenan Allah yasa na cika da imani.
Warware hannyen nayi da tsumman danake sakawa indai zan taba ruwa,ko kuma abu wanda zamemin illah.
Hanyar wajen saniyar sa na nufah domin zuba mata abinci,da inajin haushin sakamata abinci,amma yanzu itama tausayinta nakeji,wai a yanda nake ɗinna ita kuma dani ta dogara na zuba mata abinci,nida ko bani nawa ya isheni ba'ayi.
Kwanonnata na ɗauke zan ɗebo mata dusa,saidai me.....da kayan goje na haɗa ido a cikin kewayen saniyar,duk ta takasu sunyi duƙu-duƙu kaman basu taba ganin ruwa ba.
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un. Shine dai kaɗai abinda bakina yakeda ƙarfin amsabatawa.
Ɗiban kayan nayi na taho dasu zuwa ƙofarmu. Sakasu nayi a gaba inda kallonsu,harda singlet ɗinsa da komai ma na kayansa aka zuba a wajen,sai zarnin fitsarin saniyah sukeyi.
Yanzu shin taya zan fara wanke kayannan,kayana ma bana wankewa bazan iya ba,hannaye na bazasu iya gurzawa su fita ba,inaga kuma waɗannan harda su jeans,na iyah wankewa.
Sakasu nayi a cikin ruwa na zuba sodar akai na ajiyesu,idna suka jiƙa saina wanke.
Tun da rana har dare,idan naje wankewar ina fara mitstsikawa in ciwo ya ratsani saina ajiye na tafi,naga ta kaina nikam a gidannan,taya zan rayu da haka?.
Da daddare haka nayi yarfe hannu har bacci ya ɗauke,yanzu yakai ko tafasu a sallah banayi,inaga idan naje asibiti yankesu zasuyi suce sun rube,inaji ina gani za'a maidani kuturwa???? Gaskiya gobe dole nasan abinyi.....
Washagari da safe na tashi zan yunƙura kenan naji zuutt a marata..wata sabuwa kenan inji ƴan caca.
Wayyo shima ciwonnan wannan watan kam da yayimin uzuri mana,kenan wasa wasa na kusa wata a gidannan.
Yunƙurawa nayi na tashi zaune ina cije baki,saboda riƙewar da marata tayi gamm.
Banɗaki na lojana naje,daga nan na dawo ɗaki na kwanta,shigowar kursiyyah nagani da ajiyemin ɗumame. Yauda masifa kenan,na faɗa a raina.
Cinye tuwonnan zanyi bazan barshi ba,idan kuma ta gano naci tuwonta banyi wanke wanke ba bansan yazamu ƙare ba.
Duk da ciwon danake ji haka na daure na sauƙa ƙasan ɗakin,buɗe kwanon nayi mukayi ido da ido da karin tuwon guda ɗaya. Dama kullum ɗaya take sakamin kaman rai..
Miyar babu daɗi haka na suɗeshi,jinsa nake kaman nama saboda yunwa.
Amai nafaraji yana tahomin,dan dama ko a gida haka nakeyin al'ada da wuyah,kowanne wata saina sha wahala a ranar farko.
Komawa nayi kan gadon inna,nayi rigingine ina kallon sama,saboda amai ɗin ya koma. Idan na bari tuwonnan ya su'buce daga cikina bansan lokacin dazan samu wani abincin ba a yau.
[Goje a mahangar gani]
Kwana goma kenan tunda muka tafi wajen aikin,fasa banki mukaje yi a gwagwalada,to bayan munyi da alama ƴan sanda da sojoji sun sani da wuri,hakanne yasa aikin ya baci,aka kashe wasu daga cikinmu,wasu kuma aka kamasu. Mudai bamufi mu huɗu ba muka tsira a cikin mutum sha biyar .
Jeji muka furma da guda har sannan kuwa bamu jefar da kuɗin da muka ɗebo ba yana wajenmu.
A jejin muka buya tsawon wannan lokacin,saboda neman da jami'an tsaro suke mana.
Munsha baƙar wuyah muka dawo sansanin ƙungiyar.
Masu jiran ƙofar ne suka buɗe mana muka shiga,bayan sun gama bincike mu tukunna.
A gajiye muka wuce inda ogan yake muka jefa masa jakunkunan kuɗin.
Saida ya ƙaremana kallo saikuma ya tuntsire da dariyah yana nuna mu da hannu.
Yayi kaman daƙiƙa biyar yana wannan dariyah kana kuma yayi shuru yana goge hawayen da dariyar ta sakashi.
"Ku kalleku sai kace birirrika,da kyau da kyau,ni banyi zaton ma zaku tsira ba wlh,danaga baku dawo ba inace na kasheku ne"
Numfashina sama sama yakeyi saboda baƙinciki,yayinda zuciyata ke rayamin na kasheshi kawai ya daina numfashi. Saidai haka na danni zuciyata nayi masa tambaya.
"Meyasa kake tunanin zamu mutu?"
"Saboda nina ƙira ƴan sanda da sojoji na faɗamusu zakuzo yin fashi a banki. To ya kaji toh,duk lokacin dana ɗebi sabin yara haka nakeyi musu,tahaka nake gwada jarumtar su,shiyasa bamuda mutane dayawa sai jarumai. Ya kaji salo.........."
Tun kafin ya gama maganar nakai masa wani farmaki,fitt na so yanke maƙogaransa,saidai dayake ya san dabarun faɗa yagoce da sauri na sameshi a jijiyoyin wuyan sa na dama.
Ihu yasaka yana dafe wajen,yayinda jini yafara tsartuwa yana wanke rigar jikinsa..
Yaran dazuke wajen da gudu suka ɗaukeshi zuwa wani wajen da bansan inane ba,yayinda nikuma wasu suka rirriƙeni zuwa wani ɗaki mai kama da prison.
Idona a tsaye yake gamm babu alamar tsoro ko kuma nadamar abinda nayi masa,hasalima takaici naji da ban yanke maƙogaronsa ba.
Ina nan a cikin cell ɗin har tsawon kwana uku,waɗanda suka kawoni wajenne suka fito dani.
Kaya suka miƙomin iri ɗayah da wanda ogan yake sakawa,cikin girmamawa suka miƙamin kayan tareda yimin alamun na biyosu.
Wani ɗaki suka nunamin nashiga,akwai gado a ciki da kuma banɗaki,ba laifi yayi kyau kam.
Wanka nayi na wanke wannan ɗauɗar jejin,duk da ma ni ba gwanin tsafta ba,amma naji daɗi sosai.
Kayan da suka bani na saka kana na fito.
Cigaba da sakeyi da binsu har mukazo wajenda aka taramu da farko.
Maimakon ogannmu yanzu wani mutumine sanye a suit akan kujerar.
Bashida suffar ƙarfi amma kuma yana da suffar sanin duniya akan fuskarsa,sannan kuma kana ganinsa kasan kuɗi ya zauna masa.
Murmushi yayi kana ya min alamar na matso,ba musu kuwa cikin nima nuna isata na ƙarisa wajen.
"Goje kake da suna koh? Ka burgeni sosai ka burgeni da jarumtar daka nuna jiyah,wanda hakan yasa na baka matsayinsa,shiyasa ka ganka da waɗannan kayan. Saidai ba tsallen da kayi ya kawoka tabb da rijiyah,idan ka sa ke yin wani to zaka jika a ciki tsundummm,wanda zaka iya yin dubu baka fito ba.
Nine shugaba na ukun da ake cewa zaku haɗu dashi in kuka tsallake aikin farko,a samana akwai shugabanni biyu,ni nabiyun nasani bansan na farkon ba,shigaba na biyune yasan wanene na uku. Dan haka barkanka da zamowa na hannun damana"
Tafi yafara yayinda sauran ƴan kungiyar ma suka fara,lallai wajennan akwai haɗari,jiya na lahanta shugabansu har sun maidani a matsayinsa??.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Shaida kuma ta nan
09035784150
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
*Duk wanda shafinnan yamasa daɗi yayi comment please,finally dai Sumaimah tah............ku karanta ku gani dai........*🤣🤣🤣
________________________________
*Book 1*
Chp[19]
Gyara tsayuwa ta nayi bayan sun gama tafin.
"To nagode shugaba da wannan karramawar,amma batun rijiya ni dama dana so yin tsalle ba nufina zuwa wajen rijiyah ba,kaine ka kaini wajen rijiyar,dan haka yin tsallena na faɗa rijiyar ma duk yana wajenka. Mun tafi akan zamuyi sati ɗaya,gashi munyi sati biyu bamu koma gidaba"
"Karka damu da wannan zaku kowa zai iya tafiya gidansu,aikinnan ya gamu saurna kuma nagaba idan yataso.
Kuɗin da kuka samu nasarar ɗakkowa kungiya bazata karba ba an bakushi ku raba,su ɗau kashi ɗaɗɗaya su baka kashi biyu."
Naji daɗin kuɗin tunda dama abinda yakawoni kenan ,amma nayi mamaki da banjisu a cikin raina sosai ba.
Mota DON3 ɗin yabani kyauta,saidai nace masa banaso,danna kula a ɗan tsorace yake dani karna yi masa tawaye kaman oganmu,amma ni bashine a gabana ba sam,so nake naje naga wacce wainar su Tunga suke toyawa.
Madadin haka wani na ɗauka a mutane wajen ya tuƙoni zuwa garinna mu wanda yake district ɗin gwagwaladanne.
Da daddare na iso,ban wuce gidaba sai kawai na nufi madakatarmu,babu kowa dan haka kai tsaye ɗakina dayake cikin jejin na nufah.
Jakar kuɗin na ajiye kawai nayi kwanciyata,saboda narama baccin wahalar da banyi ba kwana da kwanaki.
Hasken ranar daya hudo ta rufin ɗakinne ya haske ido na,wanda hakan yasakani yin miƙa na tashi na zauna.
Fitowa nayi daga cikin bukkar na nufi kogi,wanda yake a ɗan gangare idan mutum yayi ƴar tafiyah.
Wanka nayi kana nayi alwala,salloli biyu ake bina,isha asuba da kuma azahar wacce akayi yanzu..
Ina cikin yin sallahr Tunga ya shigo bukkar,ganin ina sallah yasa ya tafi.Nasan abinci zaije ya kawomin.
Bayan na gama jakar kuɗin danazo da itah na buɗe buzun dayake tsakiyar ɗakin,kuɗin na zuba a ciki sauran kuma na barsu a jakar.
Jakar kayan aikina ma bazan koma da itah gidaba duk anan zan barsu.
Shigowa yayi yana cikin rarraba kuɗin a kan buzu,kallo ɗaya yayi musu ya kawar idonsa tareda miƙamin kwanon abincin daya riƙo.
"Ogah ga abinci,ka dawo kuma babu magana sai kawai naganka a jeji"
"Kamawa tayine,a gajiye nake shiyasa banshiga garinnan ku ba,ya aikin dana barku dashi ya tafi?"
"Yatafi yanda ake so,kawaidai kuɗinne bai bamuba,ana wannan matsalar sanjin kuɗin"
"Ga wannan ka bi kan kowa da rabonsa,ni barina wuce gida na sanja kaya"
Kuɗin na miƙa masa dami masu yawa,cikin fara'ah da washe baki kuwa ya karba.
"Ogah ta samu kenan,shiyasa fah mukeyinka,inka samu kana yaga mana,ba kaman tsohon kwarkwaroncan ba daka gama dashi"
A ƙaramar jaka na saka sauran kuɗin wanda zanyi amfani dasu na fitoh.
Hanyar gida na nufah,kaman kullum kowa ya ganni sai ya sanja hanya.
Ina shiga ƙofar tawa na ganta kaca kaca,yanda na tafi haka na dawo na sameta babu abinda aka taba.
Buɗe ɗakin nayi na shiga,shi da alamar anyi masa shara kaman sau ɗaya dana tafi,cije baki nayi ina jijjiga kai,lallai ma yarinyar nan ta rainani.
Cire kayan jikina nayi na zubasu gefe.
Gajeren wandona da singlet nake nema,amma banga waɗanda nake son sakawar ba,nan na tuna su na cire lokacin dana tafi.
Fitowa nayi na nufi kewayen saniyata,tana kallona tafara jujjuyawa,gabanta ƙwaraff babu abinci ko kaɗan. Saidai kuma amma babu rama a jikinta,to yaushe kenan take bata abinci,kodai ba ta bata kai?.
Ƙofar innan nashiga a zuciye,mai zan gani kaya nagani a cikin bokiti an jiƙasu. Kuma indai ba gizo idanuna yakeminba kayana nagani a jiƙe a cikin bokiti,wannan kuma wanne wari suke fitarwa haka.
Nasan dai kayana duk dattinsi bazasuyi wannan warin ba.
Dan takaici bansan lokacin dana bankaɗa labulen ɗakin innan ba na shiga.
A kwance take sai sharar bacci take hankalinta kwance,wani cije baki nayi tareda runtse ido,zuciya ta tafarfasa take,yayinda ƙwaƙwalwata ke kwaranyomin wanne nau'in hukuncin dazanyi mata.
Fita nayi daga ɗakin naƙira su durwa wanda na barsu a wajen Tunga,ɗazu da suka ganni a hanya suka biyoni,bokitin data jiƙamin kayannawa na ɗauka na shiga dashi cikin ɗakin shima......hmmm yau waye zai hanani hukuntaki,na daɗe banga wanda ya rainamin hankali kamar ta ba.
[Sumaimah a mahangar gani]
Bayan na gama cinye tuwon inanan kwance naji kursiyyah tashigo ɗakin.
"Sumaimah wai kizo inji gaji kiyi wanke wanke,ko bakisan hadda kwanukan yin awara ba a ciki?"
"Kije kice mata yau baxan iya yin aiki ba banida lafiyah"
"Chabɗi wlh ba wani rashin lafiyah,bakida lafiyar ne zaki cinye kuma tuwon dana kawo miki? Ai wlh saina cewa gaji wai kince bazakiyi ba ne"
Tana gama faɗin hakan ta fita daga ɗakin,runtse ido na nayi lokacin da cikinnawa yayi wani danƙa kaman zai cire taciki.
Tun safe nake juye juye akan gadon,bani na samu bacci ba sai wajen azahar tukunna.
Baccin duk da yana cikeda yunwa amma yana min daɗi sosai. Kaman a sama naji sauƙar ruwa a jikina,wata ajiyar zuciya nasaki tareda tashi na zauna ina rarraba ido.
Warin kashin shanu naji a cikin ruwan haɗe da warin soda. Tofarwa wanda yashiga bakina nake ina tari. Har sannan ban dawo hayyacina naga waya aikatamin hakan ba,amma nasan ba maiyyimin wannan aika aikar sai gaji.
Juyowa nayi,saidai maimakon naga gajin,da fuskar kare muka haɗa ido yana min gurnani,saikuma wasu ƙafafu a tsaye. Binsu nayi da kallo zuwa sama,har idanunnawa suka haɗu dana goje,wanda ƙasumbarsa ta ƙara yawa,ga idonnan kaman na zaki yaga abin farautarsa.
Ihu nakeson yi kozan tashi daga mafarkin danake,amma kuma nasan ba mafarkin bane zahiri ne..
Matsawa nake da baya har nakai jikin gini akan gadon,tunda nasan shine ban ɗaga idona na sake kallonsa ba.
Magana yafarayi da wannan maganar tasa mai diri.
"Yaushe nayi wasan dazaki rainani,shin abinda nasakaki kenan dana tafi,nace miki kada ki karya ɗaya daga cikin ayyukan dana sakaki,amma wani abin takaicin ko guda ɗaya daga cikinsu bakiyi ba,wato duk abinda zanyi nayi koh?"
"Dan Allah kayi haƙuri wlh"
Fizgo hannuna yayi ya jefani a tsakiyar ɗakin,jikina banda karkarwa babu abinda yake,saboda razanar danayi jinina ya tsinke sai zuba yake duk ya bata kan gadon da kuma jikina,nasan yagani amma ko a jikinsa,Allah yasama yasan menene.
"Ki rufemin baki,kada ki kuskura ki ambaci wannan kalmar da na tsani jinta in anyimin laifi wato haƙuri,saboda bana haƙurin"
Since sarƙar jikin karen hannunsa yayi,da alama banni dashi zayyi ya fiffigani,aikuwa hakanne dan sunshe shi yayi yana shirin barin ɗakin.
Wani takaici ne gamida baƙin ciki suka tokare min maƙoshi,take kuwa sukayi nasarar kawarda tsoronsa dayake cikin zuciyata,yazamana haushinsa da kuma mamaki irin na halinsa sunfi gaban tsoron danakeyi masa. Wannan ba mutum bane,taya mutum zai dunga jin tsoron halitta irin wannan ma.
"Dakata kada ka fitah"
Nikaina nayi mamakin umarnin dana bashi,yaushe nasamu wannan jarumtar haka? Tsayawar kuwa yayi bai fitan ba,ba wai danna isa ne yasakashi tsayawar ba,saidan mamaki daya cikashi.
Juyowa yayi tareda ɗaga gira yana kallona,yayinda nima na ɗaga nawa idon nasaka su a nasa,saƙo nake son isarwa da ruhinsa bawai shi ba,saƙon kuma bazai kai inda nakeso ba idan ba idonsa nake kalla ba.
"Badai kasheni kakeson yi ba,idan kasheni zakayi ka kasheni da kanka,basai kasaka halittar da batayiwa Allah komai ba ɗaukar rai,Naga abubuwa da yawa a rayuwata sannan duk da banda galihu a duk ina naje,amma hakan bashi zai saka nakasa tsarewa kaina darajata wanda Allah yabani na ƴa mace. Bana fatan labarin mutuwa ta ya yaɗu cewa karene ya yayyagata a ɗaki har ta mutu,gwanda mutane suce mijinta ne ya yankata,wanda bai san cinta ba,baisan shanta ba,baisan ya ta kwana ko ta tashi ba,dabbarsa ta fita daraja,Dan kawai yayi tafiyar da bata san ya tafi ba,yadawo yaga batayi aikin daya sakata ba,bai tambayi dalili ba kawai sai ya yankata. A wannan tafiyar bai ajiye mata abinci ba ko kuɗin magani,sannan bai bata izinin tafiyah ko ina ba,shin dutse ya ajiye kamai,saniyar sa ya damu da itah akan a bata abinci,amma matar da ajiye ko oho. Duk da hakan tayi iya koƙarinta wajen ganin cika umarnin daya bata,amma ƴan gindasu sunƙi barinta ta cika ɗin,shikuma bai biɗi sanin daliliba hukunci kawai ya iya zartarwa na son kansa."
Kukane ya kufcemin na abubuwan da suka faru a gidan wanda suka dawo cikin kaina.
"Indai wannan rayuwar ce mai kamada ta bautar mutanen farko to wlh ka kasheni goje bana tsoro,duk hukuncin dazaka min na daɗe da sanin kwatankwacinsa,kaya da kake faɗa kuma ƴaƴan gaji ne suka zuba a kewayen saniya,na kasa wankewa ne saboda hannyena ciwo ne dasu......bazan iyaba ka ɗau raina kawai kaman yanda kake iƙirari ko yaushe,ka ɗauka kawai na huta,dama tunda nake mai na tsinta na farinciki a duniyar ne??? Kullum zullumin mai zai faru. In baka kasheni bama yunwar cikina zata kasheni,gaji bazata sake bani abinci ba nasan,saboda bazan iya yimata aikin da innayi take bani ba. Dan haka ni gwanda ka kashenin ma kafin yunwar da kasheni"
Rarrafawa nayi na riƙe ƙafar wandonsa,har raina ni na gaji da wannan zaman rayuwar.
Jikina karkarwa yake na wuyah,dakuma kukan danakeyi,karen dayake gefena sai gurnani yake,amma ba tashi nake ba,na daina ma tsoronsa,mai jiran mutuwa wanne tsoro zaiji ne"
"Tashi .....ki tashi nace"
Abinda yakeson nayin nasan bazan iya ba,amma barina gwada nagani.
Miƙewa nayi daga rarrafen inaso na tsaya akan ƙafata,wani juuuuu jiri yaɗebeni,kafin idona ya rufe sai naji ni a hannun mutum ba tsakar ɗaki ba.
Nauyi idanuwan sukayimin,amma haka na dage na buɗeshi,akan farin cilin idonnawa ya sauƙa,fanka tanayi walwal a samana.
Gefe na kaikaita kaina na kalla,window nagani na glass ga kuma farin fenti,tunani na fara na shin a ina nake ne.
Yunƙurin tashi nayi sai naji hannuna a ɗaure,hannayen na kalla duk an ɗaɗɗauresu da bandeji,da alama magani aka shafamun to waye yayi min.
Allura na gani a ɗayan hannun wata igiya tayi sama ruwa yana shiga jikina,Asibitine wai??
Na tambaya a raina,gyaran murya naji hakanne yasa na kalli mutumin dayake kan kujera a zaune,tun ɗazu yake kallo na ban kulaba.
Ƴar razana nayi ganin ya kafeni da ido.
"Meyasa kika taba abinda kinsan jikinki bayaso?"
"Soda ce"
"Ban tambaye ki menene ba,cewa nace meyasa kike amfani da itah,bayan kinsan jikinki bayaso,Tunga ya faɗamin cewar yabaki dubu biyu,mai kika siya toh?"
"Uhm na
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12 Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21