ke macece,kinada baiwa a matsayinki na ƴa mace. Duk kwarjinin na miji da wuyar sha'ani kisa a ranki zaki iya dashi,in kikayi hakan sai kiga komai ya tafi a tsari mai ma'ana"
Ƙirjina ne ya buga kana wasu hawaye masu ɗumi suka zubomin,tabbas idan da yana matsayin ɗan daba a wajena to fah yanzu a matsayin mijina yake. Wannan wasu tarin gaskiya ne masu zafi da kuma matuƙar ɗaci Shareefah ta tunamin,wanda kuma komai zanyi hakan suke bazasu canja ba.
A sanyaye na gama shiryawar Ƙanwar babammu Baaba Ladi ta kamo hannuna muka fito..
Dan dama ita ke kai duk wata yarinya da akayi aurenta ɗakinta..
Bayan mun fita su indo ne suka biyo bayanmu muka fito daga ɗakin
Da ammi naci a karo a bakin ɗakin tana kallona.
Wani kukane naji ya ƙwacemin da bansan ta ina ya faro ba,idan nace babu shaƙuwa tsakanina da ammin to nayi babbar karya,dan tun vanni da wayo na tashi na ganta,da daɗi da babu daɗi dai haka ta riƙeni.
Cikin raunanniyar murya nace.
"Ammi .........."
Ban iya cewa komai ba dan babu kalmar dazata sake fitowa bayan wannan ɗin.
"Babu komai Sumaimah,ki daure aure dama shi yaƙin matane,kowacce mace da haka ta girma,balle ke naki da kuma tsoro,dan haka saikin haɗa da haƙuri kinji...bazan samu damar rakaki ɗakin ba dan haka kuje Allah ya ƙare yabada zaman lafiyah....saikuma a yayyafi juna na abinda ya faru"
Ɗaga mata kai nayi kawai,dan narasa ma mai zance.
Hanyar waje muka nufah,baba kam tunda ya karbi sadaki na babu wanda ya sakashi a idonsa,dan haka ba zancen yin sallama dashi,in yana nan ma mai zaice min,shiba wa'azi sai min ba ko nasiha,dan in kura zatayi maganin zawo tafara daga kanta tukunna.
A ƙafa muke tafiya shuru babu wanda yake cewa komai har muka isa anguwar su gojen.
Ohh ni Sumaimatu ina ganin rayuwa,aure a yanzu ko maƙwantanku ne sai anje da mota an zagayo dakai. Amma ni ganida ƴan rakiyar da sayyadarmu mukazo. Kodayake ana ta kai waya ke ta kaya na samu ma na tsira da raina da lafiyata.
Baaba ladi ce a gaba,itakuma tayi sallama da muka shiga gidan.
Muryar wata matace daga wata ƙofa ta amsa,kanajin hayaniyarta tun daga bakin ƙofar gidan da yara. Da alama itace matar ƙanin babannasa,wai dagajin muryar ya kuwa jarababbiyace,danni tsabar zama da masifaffu tun daga muryaru nake ganesu.
Iya amsa sallamar bai isheta ba saida tafito daga ƙofar tana riƙeda kunkumi a gabanmu.ohh dama ba ramammiya bace yanda nake hasashenta,tanada ƴar ƙiba. Magana tafara cikeda isa da gadara.
"Ohh amarya ce ta iso sannu zuwa,gashi ango kuwa tun jiya babu shi babu labarinsa. Sunana gaji matar kawunsa nima nan uwarsa ce da........"
"Dan Allah gaji ya isa haka,yanzu suka shigo maimakon ki tarbesu kibasu wajen zama kuma kin tsaya kina surutun da bashida amfani"
Yanzu wata dattijuwa ce tayi magana,wacce na tabbatar itace kenan innar goje kuma surukata. Ita kam tanada kirki da kamala a ido sabanin matar data ƙira da kanta Gaji. Indai haka innarsa take to albasa batayi halin ruwa ba. Koba komai naji daɗi da innarsa ba masifaffiya bace..
Bin innar gojen mukayi zuwa ƙofarta bayan mun wuce gaji a tsaye tana mita.
Ruwa ta kawomana tareda yimana sannu dazuwa.
Gaisuwar mutunci sukayi da Baaba ladi,alamu ya nuna dama sunsan juna kenan..
Bamu daɗe da zama ba baaba ladi tace zasu tafi,yanda kuka san na jawo ta na zaunar da ita haka naji.
Wasu hawaye ne suka fara zubomin ganin da gaske fah tafiya zasuyi su barni.
"Toh Mairo ga nan amana mun kawo miki na ƴar mu,don Allah a dunga duba zamannasu,mu zamu tafi Allah ya kare tsautsayi"
"Ahh har zaku tafi daga zuwa,kuma bakuga ƙofar inda zata zauna ɗin ba"
Zaro ido nayi wacce ƙofar zan zauna,dama ba anan zan zauna ba a wajenta ɗakin danake hangowa?
Innalillahi kaddai can wani gun za'a kaini wajensa,inda zaiji daɗin kasheni hankali kwance koh"
"Ahah mukam zamu tafi,inyaso saiki rakata da kanki mairo"
"Lahh ya kusa dawowa ma da kun tsaya kun gaisa koh"
Dukkansu zarowa ido sukayi hardani wacce zan zauna dashi ɗin.
"Ahah mairo nikam tafiya zanyi,bansani ba ko su ƙawayennna ta zasu tayata zama kafin yazo"
"Ahah"
Suka bada amsa a tare suna zare ido.
Yau na shigesu ni ɗiyad zinaru,haka zanyi rayuwa dashi ???
Ina gani babu kunya dukkansu suka shuri takalmansu zuwa gidansu a kwanciyar hankali,nikuma inna mairo ta nufi ranaki ɗakin gogan.
Sai wasu kalamai take min da banajin abinda take faɗa.
Ƙofar a kewaye take da ginin bulo,ɗaki ɗayane sai banɗakinsa a gefe . Buɗe ɗakin tayi muka shiga..
Babbar katifa ce a ƙasa sai akwatin kayansa,a dungun ɗakinɗakin akwai fankar ƙasa da kuma wani tsohon rediyo.. Kana ganin ɗakin kasan da bahaka yake ba,gyara yasha na wucin gadi.
Dan ga nan inda aka rurrufe shirgi a gefe.
A kan katifar tayimin nuni dana zauna.. Magana take cikin sanyin murya,amma kaman mutum mutumi haka nake kallonta bana cewa uhmm bare uhmuhm. Kaba ɗaya raina ya fita daga gangar jikina yaje wani gu ya buyah..
Bayan ta fita na daɗe a zauna hakan ban motsa ba,dan ji nake kaman in kan zare.
Can bayan wani lokaci nafara jin alamar sautin sawun mutum yana tahowa,zan iya rantsuwa bana Inna bane,in kuwa banata bane to na waye.
"Na mutuwarki ne"
Wata murya wacce nasan ta ruhina ce ya raɗamin a cikin kunne nah.




Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION


*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[09]



Runtse idona nayi,bana ma son naga mai zai kasance.
Buɗe ƙyauren ɗakin yayi ya shigo,da farko bai kulada ni ba sai daya waiwayo tukunna muka haɗa ido.
Kallon mamaki yake bina dashi,nasan bazai wuce nazari yake ba akan mai yakawoni cikin ɗakinnasa..
"Keeee"
Ya faɗa cikin shaƙyƙyƙyiyar murya,wacce take ɗauke da gajiya da kuma takaici.
Shuru nayi ban amsa ba,dan banida wannan ƙarfin halin.
"Wai ba magana nake miki ba,ko ke kurmiya ce bakya magana?"
"Uh.....uhm... Iyee na'am"
"Me ya kawoki cikin ɗakina,duk filin dayake cikin gidannan ki rasa inda zakiyi burki sai cikin ɗakina,mai kike nufi wai anan zaki zauna"
"Ahah dama inna....."
"Mtsww tashi ki fita ki bani waje,idan kuma kika sake na ƙara ganin ƙafafunki a kusada sansani na......saina karya dukkan ƙasusuwan jikinki na babbakeki na ciyar da su durwa"
Me wai ni irin wannnan kashedin haka..
Miƙewa nayi daga kan katifar ƙafafuna suna rawa,haka na jasu zuwa bakin ƙofar,ina jin idanuwansa akan ƙeyata kaman zasu bula su shige,ban waiwaya ba harna fita daga cikin ɗakin.
Tafiya nake kaman ina kan glass har na isa bakin ɗakin inna Mairo. Ƙwanƙwasa mata nake a hankali harna fara da ƙarfi ganin bata buɗe ba.
Cikin muryar bacci tabude kofar tana kallona,nima kallonnata nake har sannan hankalina bai gama kwanciya ba.
"Sumaimah lafiya kuma na ganki anan,gojen bai dawo bane koh......"
"Yadawo koroni yayi,yace idan na sake zuwa kusada ɗakinsa sai ya kasheni"
"Me kisa kuma wacce iri?"
"Dan Allah inna karki sake cewa ba koma,idan kika maidani zai kasheni nikam....."
"Kinga kwantar da hankalinki,shigo nan mu kwanta,idan gari ya waye saina ɗauko miki kayanki a ƙofarsa,sanda komai ya daidai ta in yaso saiki koma"
Jinta kawai nake lokacin dana afka cikin ɗakinnata,dan dama abinda nakeso kenan nakuwa samu,zama da ita daram ba ruwana da wani ɗakin goje,haka kawai ana miji miji ya kasheka a banza..
Gado biyu ne a ɗakinnata,mai rumfa da kuma ƙarami na ƙarfe,shima akwai katifa akai saidai ƙarama,tsayawa nayi inna kallon ɗakin na jiyo muryar innan.
"Ga nan gado saiki kwanta,da su Atika ne suka kwana a kai,to yanzu sun koma wajen uwarsu tunda suka dawo. Sai ki dunga kwanciya anan kafin komai ya daidai..
Ɗaga mata kai kawai nayi banyi magana ba,ina jin haƙarƙarina akan katifa na saki ajiyar zuciyah,koba komai iya yau kam ai na tsira.

[Goje a Mahangar Gani]

Dawowa ta kenan garin cikin darennan,kwana guda da yini bana nan ina can sansanin ƙungiya BC  sun gayyaceni na zama ɗaya daga cikin ƙungiyarsu. Tun wancan satin suka turomin takardar gayyata,sannan basu yarda naje da kowa ba idan zanje wajensu,saboda tsaro.
Fitinanniyar ƙungiya ce data addabi manyan ƙasa dama cibiyar binccike,saboda ƙungiyar tayi ƙaurin suna wajen fashin manyan bankuna da kuma gidajen ƙusosin ƙasa..
Kowa yasan labarinta da kuma irin aika aikarta,saidai babu wsnda yasan sunzo sun buya a wannan ƙungurumin daji.
Abune mai wahala su ɗauki wani yazama ɗaya daga cikinsu,saidai idan sun bincika sunga ehh ya cancanta.
Kamanni da labarin salona ya isa garesu,banida wani sha'awar shiga ƙungiyar,amma kuma ban sani Meyasa wani abu na cikin kaina yake kwaɗaita min shiga ɗin,koba komai baifi ƙara kwarewa ba,kuma dama irin wannan farmaki mai aji nakeson naga inayi..
A bakin jejin su na tsaya jiya,daidai inda suka kwatantamin,saida nayi kaman sa'a guda a wajen kafin naga wasu majaze da baƙaƙen kaya sun nufo inda nake..
Wani baƙin ƙyalle suka yafamin a kaina,kana suka riƙe hannu na muna tafiya.
Cikin duhuwa muke shiga har muka zo daidai wani bakin wani kogon ɗutsi mai masifar girma.
Wasu dakaru ne a wajen a tsaye da manyan manyan bindigogi a hannunsu..
Shigewa mukayi cikin kogon mai lunguna da saƙo kala kala.
Wani sansani muka zo mai matsakaicin fili da mutanen da zasu kai shida a wajen,dukkansu baƙaƙen kaya ne a jikinsu,saidai akwai guda ɗaya wanda shi nasa kayan ja ne.
"Barka da zuwa wannan ƙungiya Goje,mun samu labaranka da yanda ka kawar da yaronmu na garinku,da farko munso yin maganinka,sai kuma mukaga hakan dakayi ma daidai ne,dan kafishi jarumta da kuma kwarjini.
Munyi farinciki daka karbi gayyatar mu kakuma yarda cewar zaka........"
"Dakata a takardar ba'a nuna karbi aikinku ba,kawai takardar amsa gayyata ce,ko banyi daidai ba"
Nafaɗa ina kallon cikin idonsa,dan haka kawai naji banji tsoronsa ba,duk kuwa da yanda suffarsa ta zama abar tsoron..
Tsuke fuska yayi,lokaci ɗaya kuma yasake ta tareda yin shu'umin murmushi.
"Ehh kuma hakane ka faɗi gaskiya,rashin tsoronka ya burgeni. Kaman yanda kake gani nan shine sansanin BC,kuma basai nayi bayani ba kasan menene aikinmu tuntuni. Nine mai faɗa a ji na huɗu,akwai sauran mutane uku a sama na. Shugaba da kuma mataimakansa. Babu wanda yasan wanene shugaban wannan ƙungiyar,shugaba na biyu kuma ni  kaɗaine na sanshi sai Shugaba na uku zamu haɗaka dashi idan ka amince da zama ɗayan Mutane biyu da suke kulada reshe biyu na wannan ƙungiyar,Idan ka amince da wannan aiki nan gaba zamu iya baka damar riƙe sansaninka na garinku. Wanda kana da wannan damar idan ka nuna mana waye kai,saika haɗu da shugaba na uku. Abinda kuma shine muhimmi bamu yadda wani yasan da wannan maganar ba"
"Harshe zaku yankemin in wani yasani? Da kunsan inada wannan inaga bazamu zo nan daku ba. Ni zan tafi in kun gama faɗin abinda kuke ganin yakamata na sani"
"Uhm ba matsala zaka iyah tafiyah,kanada damar yin tunani har nan da kwana uku,zuwa sannan zakaga ɗan aikenmu izuwa gareka"
Daga haka nayi sallama dasu muka fito daga wajen nida wanda suka rakoni.
Ajiyeni kenan da sukayi yanzu a ƙofar gida suka tafi. Garin yayi tsitt bakajin komai sai ihun mutanennamu wato karnuka,da alama dare yayi kenan.

Cikin gidan ma shuru yayi kaman babu kowa a ciki,duk wannan hayaniya ta gaji da ƴaƴan ta yanzu shuru kaman basa nan.
Ƙofata na nufah kaina tsaye,mamaki abin ya bani dana ga ƙofar ɗakina a buɗe,ban kawo komai ba dan nayi tunanin ko inna ce tayi min shara,saboda dama takanyi min idan na ɗau lokaci. Aikuwa indai hakane nasan saita zubarmin wasu abubuwan,na tsani a tabamin shirgina..
Toh ikon Allah,dana shiga warin wannan tsinken da take sakamin naji( turaren tsinke).
Takalmin kafata na cire na wurgashi wajen danake ajiyesu,gobe sai nayi gyara kenan,don duk ta ɗebi shirigina ta rufesu a gefe..
Waiwayo wa nayi wajen shimfiɗi na zan kwanta,da mutum nayi arba a zaune akan katifar,nidai nasan babu wanda muke irin wannan wasan dashi,da har zaizo kan katifata ya zauna,ba kuma barawo bane,inda shine bazai zauna shuru kaman ya mutu ba.
Lura danayi kaman macece tunda harda lullubi akan ta yasa na tunada wancan auren. Kutt amma wannan cin fuskar yayi wa,nace su kawota ta dunga aiki basai an ɗaura mata aure ba,masu kwainanen gari sunce ba haka ba,yanzun kuma na yarda da hakan bai ishesu ba sai an kawo ta cikin ɗakina.
Cikeda hassala nayi mata magana,danaji taƙi amzawa nayi zaton rai ni ne,sai kuma naga jikinta yafara rawa,wato tsorone yasakata kasa magana,hmmm mata dai,shiyasa fah a rayuwata na tsani sabgar dazata haɗani dasu,sunada wuyar sha'ani sosai..
Bayan tafita daga ɗakin ajiyar zuciya nasake,gajiyar dana ɗebo ce ta dawo cikin kaina,ga kuma nauyi da kaina yake..
Ohh no bai kamata naji wannan muryar ba yau.. Na faɗa cikin gajiyawa ina dafe kaina wanda nake jin jijiyoyin sa suna rirriƙewa.
Jujjyawa kan nake ina duban ɗakin,yanzu taya zan fara neman abinda zan busa a ɗakin,nasan babu makawa inna ta zubar da waɗanda na ajiye.
Faɗawa kan gadon nayi ina kallon silin ɗin dana haɗa da jarida da kuma lilo.
Dummm komai naji ya ɗaukemin,vanda juyawa babu abinda duniyar tawa takeyi,a haka na kasance har bacci ya ɗaukeni.

[Sumaimah a mahangar gani]

Hannu naji yana bubbagani,can kuma sai naji murya ƙasa ƙasa tana min magana..
Saida baccin ya dan bar idona kafin na naji ashe inna ce take tashina.
"Ƴar nan tashi kiyi sallah anyi assalatu,ko bakyayine"
Tasake maimaitawa a sanyaye.
Juyi nayi kafin na tashi zaune,ohh ban taba tunanin kwana na nafarko a gidan zanyi bacci hadda juyi ba kamar haka.
Kallonta nayi da farin hijabi a jikinta,hannunta riƙeda carbi tana kan sallaya.
Na lura da hakanne saboda hasken ɗan Club da ake haɗawa ya haska ɗakin..haka kawai naji ta burgeni,indai bawai mantawa nayi ba,tunda nake babu wanda ya taba tashina sallahr asuba a gidan mu.
Saƙƙowa nayi daga kan gadon wanda yanxu yazama nawa.
Inda buta take ajiye na nufa na ɗauka domin zuwa banɗaki.
Bayan na idar da sallah gaisheta nayi ta amsa cikin sakin fuska,har zuwa lokacin lazimi takeyi,nima danaga haka ban koma baccin ba saina fara nawa.
Muryar ta can sama sama naji tanamin magana,firgit na kalleta,kenan bacci na cigaba dayi a zaune.
"Sumaimah ki koma ki kwanta mana,ke ba kaman mu ba da baccin mu yanzu yayi ƙaranci,bare kuma kunsha hidimar biki,ki koma kiyi baccin ki kinji"
Ɗaga mata kai nayi,dan dama hakan nakeso.
Muryar inna naji tana magana da wasu yara,hakanne yasa na buɗe idona,lokacin rana ta fito tangargar.
Fitowa nayi daga ɗakin na zauna a tabarmar da take zaune..
"Kin tashi kenan,ga abin karyawa toh.."
"Ɗumamen tuwo ne sai kuma wani ɗan kwano da awara a cikin kaman guda bakwai,sai kuma kofin kokoh"
"Hmm kiyi haƙuri fah ƴar nan,amarya da aka sani da cin kaji a ranar farko kega abinda kika samu,wlh banda kuɗine,awarar ma a wajen gaji na karbo nace ta bawa baƙuwa"
Allah sarki tausayinta ne yakamani,hmm batasan a hakan kayan daɗi tabani ba akan abinda nake ci a gidan.
"Lahh inna karki damu,shimfiɗar fuska ma da kika bani tafimin komai da kike tunani,fatana Allah bamu ikon zama cikin aminci"
"Ameen ƴar nan,gaskiya ko kusa baki dace da wancan huhun ba,kawai dai ƙaddara ce da idan tazo baza'a tsallake ba. Sannan dan Allah kiyi haƙuri da son kaina,dan lokacin da naji wannan batun nayi niyyar na hanashi,amma kuma sai nayi tunanin wataƙila sanadin shiryuwarsa ne aurennaki. Yanzu dana ganki ma na ƙara tabbatar da hakan,dan inaga sai an zage garinnan kafin a samu mace irinki,kiyi haƙuri kiyi haƙuri kinji"
"Inna kidaina bani haƙuri,nima lokacin da Naji labarin kwana nayi ina Addu'a akan Allah kar ya hadani dashi,amma dana ga an ɗaura aurena dashi jiya sai nayi tunanin inaga shine mafi alkhairin dana daɗe ina roƙon Allah yabani,dan haka ki daina wannan bada haƙurin ba laifinki bane,fatana Allah yabani ikon jure duk abinda zaije yazo."
"Ameen kiyi ta haƙuri da sannu zakiga mafita"
Zancen duk ya isheni,tunda gani nazo gidan to kuma banason tuna wai dama ban xo ba,dan haka nayi ƙokarin kawar da zancen..
"Uhm inna wanne aikin za'ayi ne a gidan?"
"Ehh toh banice yanzu da tuwo ba gaji ce take saita bani,wanke wanke kuma atika ce take,idan bata nan kuma ninayi in su farida suna nan su jijjiƙa"
"Toh bari naje na gaishe ta ma,sainaji wanne aiki zan kama mata"
"Ahah kijidai ku gaisa,amma batun aiki ko zakiyi ma ai sai kinyi kaman sati ko sati biyu,dan haka kada ki damu kanki atika ai tana nan zata zo tayi wanke wanken"
To nacewa inna tareda kallon inda uban tulin wanke wanken yake,wasu manyan tukwane na abincin siyarwa da kuma su kansu kwanikan abincin siyarwar sun cika wajen famm,ƙudaje sai bin miyar data bushe suke,kaman dai na gidanmu haka yake..

Sallama nayi a bakin ƙofar,babu wanda ya amsa,sai hayani ya suke,inaga ma basuji shigowa ta ba.
Ban dai yi ƙasa a gwiwa ba na ƙarisa wajen da suke zaunen.
Gaji ce suke ta musu itada wata matashiyar budurwa,wacce ta juya bayan ta can.
"Haba gaji,idan baki yarda dani ba wazai yarda da nine,nace miki ban ɗau kuɗinki ba,yakikeso nayi ne wai?"
"Atika nafasan halinki,kwanannan na kula bakida kuɗi,koya nayi wasafai dana wa ɗebewa zakiyi,ya za'ayi ace har dubu biyu ta b'ata a cikin cinikin"
"To shikenan ai gani ki cazeni mana,kokuma ka jaka ta nan"
"Ohh shasha zaki mayarni ma,na caje........"
"Salamu alaikum"
Nasake sallama dan su san ina wajen..
A tare suka juyo inda na ɗora idona akan Budurwar..
"Atika??"
"Na faɗa cikeda mamaki"
Wani kallon juya ido tayimin tareda cewa cikin muryar duniyanci..
"To ya ranki,kinyi mamakin gani nane komai?"





Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION


*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[10]


Atika....dama ƴar gidannan ce? Nayiwa kaina wannan tambayar,har sannan ban gaskata hakan ba.
Tun tana yarinya dama na santa,fitinanniya ce ga faɗa ga kuma kwaɗayi na abin hannun maza..
Ko zuwa na na ƙarshe ma a wajen talle saida ta nemi muyi,nice na shareta kaman bata wajen,gashi idan taga wani yana ciniki ita batayi zaka ga jaraba da msganganu,dan ma ita bata kwantai,dama ƙirarinta kenan,idan tayi ma mutanenta zasu saye ta..
Tabb dole kam tayi,yanzu nagane dalili ba'a ƙasa ta ɗiba ba.
Ko hanya banason mu haɗu da itah,ba kunya takeji ba saita tara maka mutane,ashe zamuzo mu haɗa gida ɗaya da ita ma,tabbb ɗi jan.
Dauke kaina nayi daga kanta na kalli gajin.
"Uhm Inna gaji ina kwana,an tashi lafiya?"
Wani rausaya tayi tareda gyara ƙunzugun zaninta,nasan bazai wuce nace mata inna ba yasa ta wannan shan ƙamshin.
Amsawa tayi a fizge tareda cewa..
"Amarya bakya laifi ko kina kashe ɗan masu gida,ya kwanan amarci keda angonnaki,naji
Showing 15001 words to 18000 words out of 60324 words