yimin haɗi ba faɗamin naji"
"Ahah ba haka bane,kawai dai nima kuɗin hannun nawa ne ya......"
"Kaga banason jin wannan muryartaka mai kamada ta ƴan hamsin,haɗomin shayin kasamu taska injini ya rage maka wani abun,in kuma kasake magana zan baje rumfar nan yanzunnan,kafi kowa sanin banason ƙorafi tamm"
"To shikenan ogah goje barina gama sheƙawa idi tukunna"
"Wanene kuma idi?"
Goje ya faɗa yana duban mazan dasuke zaune a wajen. Wani tsamurarre a gefe Iliyah ya nunawa goje. Suna haɗa ido yayi saurin kawar da kai tareda cewa.
"Ahh bakomai Iliyah haɗa masa zan jira ai"
Yafaɗa muryarsa tana rawa. Ganin har bayan yayi maganar goje bai daina kallonsa ba.
"Kai ɗan garinnan ne kuwa,bansan ka anan yankin ba,ka sanni?"
Goje ya tambayeshi yana ƙare masa kallo kaman yaga ɗan ƙwaro.
"Eh .......hhhh to rani nazo,wannan shine karona na farko,wata na guda kenan a garin"
"Ohh toh...in kanada dabbobi ko wani abu muhimmi karka barshi a waje har zuwa dare,in ba haka ba yazama na bayin Allah,sannan in faɗa ya kaure a lungunku kaji ƙarar wuƙa kada ka fito, ina tausayinka shiyasa na faɗa maka"
Ɗaga kai yayi alamar yaji.
Suna cikin maganar ne Iliyah ya miƙowa goje ruwan shayin tareda yankan biredi.
Karba yayi maƙwat saida yayi rabin kofin,kafin yanki rabin biredin ya tauna.
Kafin kaceme yatashi dashi,wata gyatsa yayi kana ya miƙe daga kan bencin.
"Sai gobe kuma"
Dukka a tare suka masa a sauƙa lafiya mutanen wajen.
Cikin gida ya nufah yana haɗa hanya.
Wata ajiyar zuciya suka sake a tare,kaman wanda aka basu horon ɗauke numfashi idan ya tafi su sake.
"Kai Iliyah wanann ɗin waye shi,shima a anguwar nan yake"
Idi yafaɗa yana zare ido,har sannan hankalinsa bai koma daidai ba da ganin gojen.
Dariyah wani saurayi yayi a gefe kafin yace.
"Goje kenan kake ji,watansa guda baya cikin garin,jiya dai muka ganshi ya dawo,bakada labarin sunyi caca ne shida baban su ubaidu,ya cinye shi yace yabashi kudinsa shikuma bashida ko sisi. Dayaga yana shirin yankashi ya fanshi kansa da ƴarsa,yanzu haka muna nan mun zuba ido wai wani satin za'a ɗaura aure"
"Kai mtsww yarinyar nan kuwa ga kyau ga hankali,wai a rasa dawa za'a haɗata sai goje,ai an cuceta wlh. Kai mutuminnan fah naji ƙishin ƙishin ma wai asiri ma idan akayi masa baya kamashi,gashi da wani ɗan banzan ƙarfi,sarkin garinnan ma shayin horashi yake,shiyasa idan yaci kayanka yanda kasan yaci kayan uwarsa haka yakeyi"
"To kai bakada labarin abinda yayi yai batan zana bashi ba alamunsa,naji fah wai haddashi a waɗanda suka 'balle masana'antar shinkafa ta garinnan,ƴan sanda sunzo kama su suka kashe guda biyu. Amma suma sun kama barayin guda uku. An kamashi aka kulleshi,bamu san mai yayiwa shigaban fursunan ba da kansa yasako shi......hmmm wannan mutumin ai ya wuce yanda kuke tsammani"
"Kai ku bar wannan zancen haka,tunda munanan dashi ai zaiga komai mah,ya batun ni honarable neh,kuna ga zaici siyasar nan kuwa,naji ance yaraba mashina a hamsin a garinnan"
"Rabu damu da wannan barawon,ko tsafi yake da tsohuwar zaba bazan dangwala masa ƙuri'ah ta ba,haka suke barayin banza,suna zaune a office suna satar kuɗin mutane da biro,shuru bakajin ɗuriyarsu sai siyasa tazo tukunna........
Barina bar teburin mai shayinnan nayi gaba......
___**___
Gidan matsakaicine kuma na daidai ƙarfi,ginin ƙasane anyi masa ya'be da sumunti,amma wani wajen duk ya bubbule saboda daɗewa,kuma ba wani kula ake dashi sosai ba.
Kofah biyune a gidan,inda iyayen goje suke,saidai babansa ya rasu sai inna mairo kawai ita kaɗaice a ƙofar. Sai kuma ƙofar malam Audu ƙanin babansa da matarsa gaji da ƴaƴansu,yana aikine a gidan wani alhaji,daga bashi ɗaki a gidan gaji ta tattara da ƴaƴan ta suka bishi,suna can yau kusan wata shida. Ƙofarsu shuru,anan goje ya ɗaure saniyarsa.
Saikuma ƙofar goje,shima ɗaki ɗayane na kasa da banɗaki a gefe,kullum ƙofar ɗakin a garkame take da ƙwado,kaman wani abin arziƙine a ciki ba kayan dauɗa ba.
Sanda gaji tana nan kullum sai sunyi rigima idan ya daki ƴaƴanta in suka shiga ƙofar,inta fara masifah sai yace zai doketa tukunna tayi shuru,shiyasa tafiyin masifar idan baya nan,dan a gabansa kam ko mijinnata ma albarka.
Kullum cikin ƙorafi take wai inna mairo tazo itada ɗanta sun takura musu. Shiyasa da malam audu yasamu aiki itama tabishi,dan itama inna mairon da a birni suke itada mijinta,yana aikin masinja a kotu,yin ritayarsa ne yasaka su dawowa mahaifarsu,shekararsu biyar kenan da dawowa.
Amma goje ya fitini garin kaman dama anan ya tashi.
A zaune take tasaka kayan yin igiyarta tanan tukawa,gidan tsitt kaman bakowa,tun abin yana damunta har ta saba yanzu.
Bayyi sallama ba dan dama bayi yake ba saidai ta ɗaga ido idan taji motsinsa.
Jijjiga kai tayi tareda yimasa magana,ganin ya yaɗau buta yana jijjiga wa,da alama ba ruwa a ciki.
"Yau kuma daga ina"
"Daga jeji a can na kwana"
"Ohhh gari ya hargitse da abinda ka jawo na auren ƴar gidan uwaisu,sunzo nan jiya akan batun,Nayimusu kwatancen gidan da kawunka yake,amma sunce abin baya wani buƙatar manya. Nayi ta zuba idon shigowarka amma banganka ba sai yanzu,wai dan Allah yaushe zaka daina........"
"Ina zuwa inna barina rage marata tukunna,nasha shayi yanzu a wajen Iliyah"
"Yau ɗin ma,kabiyashi kuɗinsa ne,do Allah ka tausayawa mutuminnan da shan shayinsa karka karya masa jari"
"Kai daɗina dake inna kowa yazo yamiki ƙorafi akaina saiki yarda wai,Allah zan fara karya ƙafar duk mai shigo gidannan yana kawo zancena,yanzu dai barina zaga bayan gida,banyi sallannan da ake da safe bama fah"
"Ehhh bakayi sallahr asuba ba,har goma tayi,goje yanzu goje kanaso kuwa........"
"Kai kai kai inna wai abin magana baya miki yawane,yanzu da kika rikeni da yanzu nayi alwala,kinga kenan laifinki ne idan banyi da wuri ba koh"
Sakin baki tayi tareda tsayawa da murɗa igiyar tana kallonsa har ya shige cikin banɗakin,rabonta da ganinsa tun jiya da safe data saka masa koko yasha ya fice,wai yanzu kuma yazo yana cemata laifinta ne da bayyi sallah da wuri ba,hmmm babu mamaki ma sauran sallolin babu wacce yayi a ciki,dan hakan ba ƙaramin aikinsa bane.
"Allah ya kyauta"
Tafaɗa tana cigaba da tukarta.
Bayan ya fito daga banɗakin bai tashi zuge zee ɗin wandon a ko ina ba saida yazo gaban inna mairon.
"To wata sabuwa,shi wandonne duk ka baro banɗakin baka jugeshi ba sai a gabana?"
"Mtsww bazaki gani ganeba wandonne ya matseni daƙyar nage zugeshi"
"Sai akace kuma dole sai kasaka shi koh,zauna muyi maganar nan,dan tana nan a ƙahon zuciyata da ita na kwana. Inaso kayi aure goje ina so naga wanann rana,amma ban taba tunanin irin wanan auren zakayi ba,wanda ko a tarihi ban daba jinsa,yanzu kaida shi babban kobon kunyiwa yarinyar nan adalci kenan iyee,ace kuna wai caca ku saka rayuwarta a ciki?"
"Inna mai nayine anan wajen,ina lafina a cikin wannan lamarin,ko saboda kullum ni laifi nake kai. Gayennan bani nace yayi caca dani ba bashi da ko sisi,shikansa yasan bana ɗaukar asara,kuɗi nace yabani bashida shi yabani ƴar sa. Yanzu ni bakiga ma cuta tah yayi ba,nifah saniya tah sailuba tah na saka a cacar nan,daya cinyeta fah shikenan zuwa zayyi ya siyarta,shiƙuwa ƴar sa da mutanen wajen suka roƙeni na karba wazan kaiwa yasiye ta,dole fah saidai nasaka ta a gidannan nayita kiwon da babu riba,amfanin ɗayane zata dunga yimiki aiki kinga saiki huta dama bakida lafiyar ƙafah. To banda wannan ta ina zan ƙaru da ƴarsa faɗamin shi"
"Yanzu ƴar adam ƴar mutane kake haɗawa da wata can dabba,nidai dan Allah in an kawo yarinyar nan karka cutar da itah kaji?"
"Dan ta wannan ne bani zaki faɗawa ba,ba a kaina zata zauna ba,in ta kiyaye abinda aka ce mata to ta tsira"
"To naji daɗin hakan,yarinyar nan tausayi take bani sosai. Ya batun inda zaku zauna toh,ko kai a gyaramuku sashen Kawunnaka ku tare a can,tunda shi baya nan"
"Nida wa zamu tare ɗin,dan Allah ki bar wannan zancen,ba ga nan ɗaki a gefenki ba ta zauna mana,in zancen Waccan dattijon kike kwanannan zaki gansu sun dawo,waye zai zauna da wannan matar itada tambadaɗɗun ƴaƴannata"
Inna mairo taji haushin abinda yace,to amma yazatayi ,tasan a kaff rayuwarsa babu wanda baya maidawa magana in ka ɗauketa,ciki kuwa harda sarkin garin.
"Kabar wannan zancen dama nasan shi kakeson yi,ɗakinnaka dai zaka gyara ku zauna a can,wanne irin aurene kai kana can ita tana nan,taya zaku fahimci juna a haka."
"Fahimtar juna hhhhhhh wai to kawai tazo gidan ta zauna mana toh,dole sai anyi mata aure dani tukunna ......afff banyi sallar ba ashe,barina je na gurguzata kafin ta anjiman tazo"
Tashi yayi da sauri ya nufi ƙofar tasa,inna mairo ta share masa harabar wajen kuwa. Makulli yasaka ya buɗe ɗakin,bayan ya shiga ya maida ƙofar kaman munafuki.
___***___
Kaya take naɗewa na wankinsu da tayi a injin wanki tana waƙar ado gwanja,kana ganinta kasan duniya tana gara masa.
"Sakwara daɗi luwai mun samu guri luwai,kai wlh rayuwar masu kuɗi da daɗi sosai. Ba ruwanka da surfe,ba ruwanka da hura wutar murhu,gas ne kana ɗorawa ka gama,ga wanki ma hajiya tabarka ka saka a inji,ga cin daɗi ga albashi. Kai kuɗi yayi ni gaji"
Lace na a jikinta mai tsada doguwar riga wanda hajiya matar mai gidan tabata kunce,tsabar samun guri ƴaƴanta su Atika har kunna kallo suke a babban falo.
Ita tanayi mata wanke wanke da abinci,shikuma Malam audu yana gadi da kuma ban ruwa ga fulawoyi.
Karaff Atika ta bugo ƙofar ta shigo da gudu cikin ɗakinnasu da aka basu,wanda yake a boys quarter na gidan.
"Gaji gaji nashiga uku shikenan asirina ya tonu tawa ta ƙare gaji"
Riƙota gaji tayi tana tambayar ta lafiya take wannan hakin kaman ta kashe wani.
"Kee lafiya atika mai yasameki haka,ki nutsu kiyimin bayani mana mai ya faru ne"
"Gaji ki tattara kayanki mubar gidanann,baba ma ki faɗamasa kar ya dawo gidannan mu tafi gida gaji,mu koma gida kawai"
"Ke dallah kimin bayanin mai yafaru ne wai,mai kikayiwa hajiyanne,naga ɗazu ta fita daga gidan ma bata nan"
"Eh ta tafi amma komai ta manta saita dawo,shine.....shine.... Tasameni nida alhaji akan gadonta toh. Toh saita yanki jiki tafaɗi,kuma dama tanada hawan jini.......wlh gaji inaga ta mutu,idan ta mutu wannan sojan ɗan uwannata bazai ƙyalemu ba sam,kizo mukoma gida wlh kafin su kashemu"
Sakin hannun Atika gaji tayi ta faɗa akan gado yaraff mai kunnenta yake jiyo mata haka.
"Atika mai kikace wai...hajiyah ta kamaki da mijinta a kan gadonta,idan ma iskanci zakiyi kiyi mana,amma taya daƙiƙancinki zaisa ki bari ta kamaku,ni ai mai farinciki ce idan har yaga yana sonki zai aureki,amma kafin komai ya tabbata shikenan kin zawo mana asarar wannan arziƙi da muka fara lasa. Taya kike ganin zasu barmu mu fita daga gidannan iyee batareda sun lahanta muba"
"Gaji bama wannnan ba,ƙanwarta wannan fatin itama ta ganmu,kuma shi sojan yana waje shiya dawo dasu ɗaukar wani abu a mota"
"Meeee kikkka ceeee shikkenan tafaru ta ƙare,wlh bazan faɗawa malam ba,dolene shima ya dawo ya karbi nasa luguden,ban isa shansa nikaɗai ba aradu. Ke kuma bari a gama yimana na nan kema mu tsira na baki naki...........
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
Ture atika gaji tayi daga bakin ƙofar ɗakin tana leƙawa,cikin ƙanƙanin lokaci ta haɗa gumi shirkif,banda zagin ƴar tata babu abinda take na aika aikar data jawo musu.
A kan idonta sojan ya fito da hajiya a hannunsa,fati tana binsu tana kuka,shikuma mai gidan ya biyosu cikeda kunya da sanyin jiki.
Har sunzo fita daga gidan wasu sojoji guda biyu suka iso bakin ƙofar gidan,magana suke da ƙanin hajiyan na wani lokaci kafin suka fita daga gidan a mota.
Shima alhajin mota ya ɗauka yabisu a baya.
Kenan gadinsu zayyi kada su fita a gidan komai.
Duk abinda yafaru akan idon gaji itada atika,a tunaninsu idan suka bar gidan suma zasu fice,saidai da alama ba haka bane,dan sojojin a bakin ƙofar gidan suka tsaya suna jajjagawa.
Suna cikin haka har yamma tayi liƙis hankalinsu ya gagara kwanciyah,ba halinda matar gidanne ya damesu ba illah su halin dazasu shiga.
"Hmmm mlm audu har yanzu bai dawo ba,kaddai yasan mai yafaru ya gudu ya barmu a ciki,tukunna ma mai yasa zasu hanamu fita toh daga gidan"
Kallon uwar tata atika tayi tareda cewa.
"Yanzu haka fatinnan ce tafaɗawa sojojinnan karsu barmu mu fita,dan daman tun a ɗakin ɗazu tace saita ɗaiɗaita rayuwata nida iyayena,dama ta tsaneni"
"Laaahaulah wala ƙuwwata shik........"
Bata gama salatin ba aka banko ƙofah,Fati ce firiri da ita,gyalene a jikinta hannunta ɗauke da key ɗin mota tana jijjigashi,cikeda tsiwa takalli gaji tareda cewa.
"Kar kiyi salati yanzu,ki bari saikinga kina hango wuta kafin sannnan zaki fara salati.
Don ku fito dasu daga ɗakin zuwa filin gidan"
Tana gama faɗin hakan tafita daga ɗakin,wasu murtuƙa murtuƙan mutane guda biyu suka fito da gaji itada atika zuwa filin gidan.
"Dan Allah kayi a hankali karka karya min allon kafaɗa,kaga ƙashin na tsufah ne"
Gaji ta faɗa tana sallalami.
Zubasu akayi a filin wajen da sanyi la'asar.
"Don kuyi musu horo wanda zai jirgita kamanninsu nan da zuwa gobe kada su runtsa idonsu,matsiyata macuta kawai,wato duk abinda anty Abida tayi muku da haka zaku saka mata,kin tura ƴar ki tana cin amanarta,idan kuka kasheta saiku aureshi ku mallakeshi,ku a dole kunga gida. Yau kuwa zaku yi danasanin shigowa garinnan ma ba gidannan ba"
Tana gama maganar kaman jira suke suka hau su gaji da duka ta ko ina babu tsayawa. Tun suna ganin farar wuta har ja tafara haska musu a idonsu.
Ƙarar buga get ne hasasu tsayawa da dukan domin suga wanene,fati ce ta taka fiƙi fiƙi zuwa bakin get ɗin.
Da Mlm Audu suka haɗa ido,hannunsa riƙe dana ɗansa na mijin ƙarami,sauran mata guda uku kuma ƙannen atika suna biye dashi a baya,kayan makaranta ne a jikinsu wacce hajiyan ta sakasu wata biyu dasuka wuce.
Killer smile fati tasake masa tareda cewa.
"Ahh mlm audu ka dawone to sannunka da zuwa shigomana ciki"
Abin yayi masa bambarakwai,danshi dai yasan wannan yarinyar ba kulashi take ba,baidai ce komai ba yayi ta maza yashiga gidan.
Dama wai suna ne yana gadi,tun safe fice sai ya wuni bai dawo ba,yanacan wajen sharholiyarsa,banda gadin ma menene wane aiki zai iya,ko noma ƙaramar gona kasa nomawa yake a shekara.
Da gaji yafara haɗa ido tayi gurfano kaman mai karbar gafara,hancinta da bakinta sunyi dama dama da yawu da jini da majina.
Zaro ido yayi yana shirin fita waje da gudu wani soja ya kamoshi ramm ta rigarsa ta baya.
"Malam ina kuma zakaje,maimakon ka tsaya ka cecemu wato guda kake shirin yi koh,saikazo duk mu haɗu muyi karbi azabar tare,tunda kaima yar kace ba iya ni kaɗai ba"
Bayan gaji ta gama bayanin da dashshshiyar muryarta,fati ce ta ɗora ta bashi labarin abinda atikan tayi.
"Yanzu kaima saika jona su,shima ku haɗashi don"
Aikuwa buɗar bakinsa yace.
"Yallabai wannan labarin da madam ta bayar banida masaniya akan sa,saina wuni bana gidanann bansan mai ake kitswa,dan Allah ku barni na tafi da sauran ƴaƴan"
"Baaba ya zakace haka,wlh kasan abinda yake tsakanina da Alhaji,naga kasha kamamu cikin dare,idan kafara magana sai ya baka dubu goma kayi shuru,daga baya kamma dayace maka aure na zayyi na zama matar gidannan har murna kayi,kake cemin nayi ƙoƙari da dabara na mallakeshi a tafin hannuna,wai har na samu na fitar da anty Abida a gidannan"
Kowa a wajen zaro ido yayi da bayanin atikan,ciki kuwa harda gaji,ita nata baƙincikin ɗaya yanda ake bashi kuɗi duk dare batada masaniyah.
Fati itada sojijinta basu suka bar su gaji ba sai dare,hakan ma suka gamasu da karnukan su suyita binsu da gudu har gari ya waye,kafin asuba duk sun suma babu inda yake aiki a jikinsu.
__***__
[Sumaimah a mahangar gani]
Yau da wuri na tashi,ba kaman jiyaba da bacci ya ɗaukeni har rana ta fito na makara.
Kai tsaye bayan na gyara ɗakinnamu kamar kullum ƙofar su ammin na nufah.
Koko take zubawa yaran da suka kewaye ta a kofi.
Gaisheta nayi kafin na koma gefe na zauna,saida ta gama dasu tukunna,kafin ta zubamin nawa,jiya girkinta ne da kuma yau,gobe da jibi nasan na inna rammah ne,akwai rowar abinci kenan. Yanzu su biyune a ƙofar Aina'u amaryar baban tayi yaji bata nan,wannan kamma inaga auren tacan tacan,dan ita irin matannane masu shegen son abin hannun miji,idan akwai to da zama,amma idan babu saita ɗebi jaraba tai tayi babu gairah babu dalili. Shikuwa baba samunsa ɗaya idan yayo caca ta gara masa,inkuwa ba haka ba saidai kowa yasan ta kansa,dan kuɗin sana'ar tasa ma ta Aune Aunen kayan abinci dayake a kasuwa kullum su yayah Musbahu ne masu fama da cikaton uwar kuɗin ma ballantana kuma riba.
Hannun nasa na karbi kokon da ammi ta miƙomin,bayan na gama tunanin na yi faɗi ba'a tambayeki ba.
Bayan mun gama gyara wajen nayi kafin na hau kiciniyar ɗora abincin Siyarwa,yau kasuwar garimu ce,dan haka da wuri ake yi kuma yafi na kullum yawa.
Banason wannan ranar ta zagayo,saboda nafi daɗewa a wajen tallen,ga tarin marasa ɗa'a a wajen,saidai kuma ta wani wajen nafi sonta,dan nima inayin wani abun nawa natafi dashi,inna samu riba na saka a asusu.Kuma itama ammi tana sallamata idan na dawo.
Bayan abincin ya kammalu shiryawa nayi nazo ɗauka zuwa kasuwar,shinkafa da miya ce da kuma waje,sai kabeji.
Nida Asiyah muka tafi,dan tunda aurena za'ayi dole itama tafara zuwa dan ta gane kan siyar da abincin.
Kodaɗɗun kayana ne a jikina normal na tsakar gida atampa,sai barin hijabin dana saka,wanda yafara mutuwa ta sama saboda tsufah. Ba wai kayane aka wareni ba'ayimin ba,dama gidaje dayawa masu irin ƙarfinmu daga shekara sai shekara suke ganin ɗinki,hakan ma atampar roba ce. Sauran yara kowa uwarsa na ƙoƙarin ganin tasake masa,wanda kuma ƴan mata ne sun fara hira samarinsu suyi musu. To ni kuwa ciki wannene nakeda shi ɗaya,shiyasa a gidannamu nafi kowa ƙarancin suturar sakawa,hana rantsuwa nema Yah Musbahu yayimin ankon ƴan matan gidan da akayi wata shida dasuka wuce,shine na samu nake ado dashi ranar juma'a.
Kasancewar kasuwar da ɗan tazara tsakaninta da gidanmu,shiyasa saida muka dan taka kafin muka isa.
Wajen rumfata ta kullum na ajiye kayan,itama Asiyah na sauƙe mata nata,yarinyar ba wata babba bace a shekaru,amma nan idan anjima in tafara magana da masu siyan abinci samari,sai ka ɗauka wata hamshaƙiyar budurwa ce,abin yana bani mamaki yanda muhallinnamu gaba ɗaya ya koma haka.
Jejjera komai nayi a muhallinsa na fara zubawa wanda suka zo siyah,wanda dama costomominmmu ne na kullum,sai kuma waɗanda ba'a rasawa.
Hankalina ya tafi wajen zuba abincin,buƙatata na sallami wadanda suka rufemin kai,ohh abin babu daɗi idan aka rufeka kana zuba abincin,wai a hakanma Asiyah na taimakona da zuba
Showing 6001 words to 9000 words out of 60324 words
"Ahah ba haka bane,kawai dai nima kuɗin hannun nawa ne ya......"
"Kaga banason jin wannan muryartaka mai kamada ta ƴan hamsin,haɗomin shayin kasamu taska injini ya rage maka wani abun,in kuma kasake magana zan baje rumfar nan yanzunnan,kafi kowa sanin banason ƙorafi tamm"
"To shikenan ogah goje barina gama sheƙawa idi tukunna"
"Wanene kuma idi?"
Goje ya faɗa yana duban mazan dasuke zaune a wajen. Wani tsamurarre a gefe Iliyah ya nunawa goje. Suna haɗa ido yayi saurin kawar da kai tareda cewa.
"Ahh bakomai Iliyah haɗa masa zan jira ai"
Yafaɗa muryarsa tana rawa. Ganin har bayan yayi maganar goje bai daina kallonsa ba.
"Kai ɗan garinnan ne kuwa,bansan ka anan yankin ba,ka sanni?"
Goje ya tambayeshi yana ƙare masa kallo kaman yaga ɗan ƙwaro.
"Eh .......hhhh to rani nazo,wannan shine karona na farko,wata na guda kenan a garin"
"Ohh toh...in kanada dabbobi ko wani abu muhimmi karka barshi a waje har zuwa dare,in ba haka ba yazama na bayin Allah,sannan in faɗa ya kaure a lungunku kaji ƙarar wuƙa kada ka fito, ina tausayinka shiyasa na faɗa maka"
Ɗaga kai yayi alamar yaji.
Suna cikin maganar ne Iliyah ya miƙowa goje ruwan shayin tareda yankan biredi.
Karba yayi maƙwat saida yayi rabin kofin,kafin yanki rabin biredin ya tauna.
Kafin kaceme yatashi dashi,wata gyatsa yayi kana ya miƙe daga kan bencin.
"Sai gobe kuma"
Dukka a tare suka masa a sauƙa lafiya mutanen wajen.
Cikin gida ya nufah yana haɗa hanya.
Wata ajiyar zuciya suka sake a tare,kaman wanda aka basu horon ɗauke numfashi idan ya tafi su sake.
"Kai Iliyah wanann ɗin waye shi,shima a anguwar nan yake"
Idi yafaɗa yana zare ido,har sannan hankalinsa bai koma daidai ba da ganin gojen.
Dariyah wani saurayi yayi a gefe kafin yace.
"Goje kenan kake ji,watansa guda baya cikin garin,jiya dai muka ganshi ya dawo,bakada labarin sunyi caca ne shida baban su ubaidu,ya cinye shi yace yabashi kudinsa shikuma bashida ko sisi. Dayaga yana shirin yankashi ya fanshi kansa da ƴarsa,yanzu haka muna nan mun zuba ido wai wani satin za'a ɗaura aure"
"Kai mtsww yarinyar nan kuwa ga kyau ga hankali,wai a rasa dawa za'a haɗata sai goje,ai an cuceta wlh. Kai mutuminnan fah naji ƙishin ƙishin ma wai asiri ma idan akayi masa baya kamashi,gashi da wani ɗan banzan ƙarfi,sarkin garinnan ma shayin horashi yake,shiyasa idan yaci kayanka yanda kasan yaci kayan uwarsa haka yakeyi"
"To kai bakada labarin abinda yayi yai batan zana bashi ba alamunsa,naji fah wai haddashi a waɗanda suka 'balle masana'antar shinkafa ta garinnan,ƴan sanda sunzo kama su suka kashe guda biyu. Amma suma sun kama barayin guda uku. An kamashi aka kulleshi,bamu san mai yayiwa shigaban fursunan ba da kansa yasako shi......hmmm wannan mutumin ai ya wuce yanda kuke tsammani"
"Kai ku bar wannan zancen haka,tunda munanan dashi ai zaiga komai mah,ya batun ni honarable neh,kuna ga zaici siyasar nan kuwa,naji ance yaraba mashina a hamsin a garinnan"
"Rabu damu da wannan barawon,ko tsafi yake da tsohuwar zaba bazan dangwala masa ƙuri'ah ta ba,haka suke barayin banza,suna zaune a office suna satar kuɗin mutane da biro,shuru bakajin ɗuriyarsu sai siyasa tazo tukunna........
Barina bar teburin mai shayinnan nayi gaba......
___**___
Gidan matsakaicine kuma na daidai ƙarfi,ginin ƙasane anyi masa ya'be da sumunti,amma wani wajen duk ya bubbule saboda daɗewa,kuma ba wani kula ake dashi sosai ba.
Kofah biyune a gidan,inda iyayen goje suke,saidai babansa ya rasu sai inna mairo kawai ita kaɗaice a ƙofar. Sai kuma ƙofar malam Audu ƙanin babansa da matarsa gaji da ƴaƴansu,yana aikine a gidan wani alhaji,daga bashi ɗaki a gidan gaji ta tattara da ƴaƴan ta suka bishi,suna can yau kusan wata shida. Ƙofarsu shuru,anan goje ya ɗaure saniyarsa.
Saikuma ƙofar goje,shima ɗaki ɗayane na kasa da banɗaki a gefe,kullum ƙofar ɗakin a garkame take da ƙwado,kaman wani abin arziƙine a ciki ba kayan dauɗa ba.
Sanda gaji tana nan kullum sai sunyi rigima idan ya daki ƴaƴanta in suka shiga ƙofar,inta fara masifah sai yace zai doketa tukunna tayi shuru,shiyasa tafiyin masifar idan baya nan,dan a gabansa kam ko mijinnata ma albarka.
Kullum cikin ƙorafi take wai inna mairo tazo itada ɗanta sun takura musu. Shiyasa da malam audu yasamu aiki itama tabishi,dan itama inna mairon da a birni suke itada mijinta,yana aikin masinja a kotu,yin ritayarsa ne yasaka su dawowa mahaifarsu,shekararsu biyar kenan da dawowa.
Amma goje ya fitini garin kaman dama anan ya tashi.
A zaune take tasaka kayan yin igiyarta tanan tukawa,gidan tsitt kaman bakowa,tun abin yana damunta har ta saba yanzu.
Bayyi sallama ba dan dama bayi yake ba saidai ta ɗaga ido idan taji motsinsa.
Jijjiga kai tayi tareda yimasa magana,ganin ya yaɗau buta yana jijjiga wa,da alama ba ruwa a ciki.
"Yau kuma daga ina"
"Daga jeji a can na kwana"
"Ohhh gari ya hargitse da abinda ka jawo na auren ƴar gidan uwaisu,sunzo nan jiya akan batun,Nayimusu kwatancen gidan da kawunka yake,amma sunce abin baya wani buƙatar manya. Nayi ta zuba idon shigowarka amma banganka ba sai yanzu,wai dan Allah yaushe zaka daina........"
"Ina zuwa inna barina rage marata tukunna,nasha shayi yanzu a wajen Iliyah"
"Yau ɗin ma,kabiyashi kuɗinsa ne,do Allah ka tausayawa mutuminnan da shan shayinsa karka karya masa jari"
"Kai daɗina dake inna kowa yazo yamiki ƙorafi akaina saiki yarda wai,Allah zan fara karya ƙafar duk mai shigo gidannan yana kawo zancena,yanzu dai barina zaga bayan gida,banyi sallannan da ake da safe bama fah"
"Ehhh bakayi sallahr asuba ba,har goma tayi,goje yanzu goje kanaso kuwa........"
"Kai kai kai inna wai abin magana baya miki yawane,yanzu da kika rikeni da yanzu nayi alwala,kinga kenan laifinki ne idan banyi da wuri ba koh"
Sakin baki tayi tareda tsayawa da murɗa igiyar tana kallonsa har ya shige cikin banɗakin,rabonta da ganinsa tun jiya da safe data saka masa koko yasha ya fice,wai yanzu kuma yazo yana cemata laifinta ne da bayyi sallah da wuri ba,hmmm babu mamaki ma sauran sallolin babu wacce yayi a ciki,dan hakan ba ƙaramin aikinsa bane.
"Allah ya kyauta"
Tafaɗa tana cigaba da tukarta.
Bayan ya fito daga banɗakin bai tashi zuge zee ɗin wandon a ko ina ba saida yazo gaban inna mairon.
"To wata sabuwa,shi wandonne duk ka baro banɗakin baka jugeshi ba sai a gabana?"
"Mtsww bazaki gani ganeba wandonne ya matseni daƙyar nage zugeshi"
"Sai akace kuma dole sai kasaka shi koh,zauna muyi maganar nan,dan tana nan a ƙahon zuciyata da ita na kwana. Inaso kayi aure goje ina so naga wanann rana,amma ban taba tunanin irin wanan auren zakayi ba,wanda ko a tarihi ban daba jinsa,yanzu kaida shi babban kobon kunyiwa yarinyar nan adalci kenan iyee,ace kuna wai caca ku saka rayuwarta a ciki?"
"Inna mai nayine anan wajen,ina lafina a cikin wannan lamarin,ko saboda kullum ni laifi nake kai. Gayennan bani nace yayi caca dani ba bashi da ko sisi,shikansa yasan bana ɗaukar asara,kuɗi nace yabani bashida shi yabani ƴar sa. Yanzu ni bakiga ma cuta tah yayi ba,nifah saniya tah sailuba tah na saka a cacar nan,daya cinyeta fah shikenan zuwa zayyi ya siyarta,shiƙuwa ƴar sa da mutanen wajen suka roƙeni na karba wazan kaiwa yasiye ta,dole fah saidai nasaka ta a gidannan nayita kiwon da babu riba,amfanin ɗayane zata dunga yimiki aiki kinga saiki huta dama bakida lafiyar ƙafah. To banda wannan ta ina zan ƙaru da ƴarsa faɗamin shi"
"Yanzu ƴar adam ƴar mutane kake haɗawa da wata can dabba,nidai dan Allah in an kawo yarinyar nan karka cutar da itah kaji?"
"Dan ta wannan ne bani zaki faɗawa ba,ba a kaina zata zauna ba,in ta kiyaye abinda aka ce mata to ta tsira"
"To naji daɗin hakan,yarinyar nan tausayi take bani sosai. Ya batun inda zaku zauna toh,ko kai a gyaramuku sashen Kawunnaka ku tare a can,tunda shi baya nan"
"Nida wa zamu tare ɗin,dan Allah ki bar wannan zancen,ba ga nan ɗaki a gefenki ba ta zauna mana,in zancen Waccan dattijon kike kwanannan zaki gansu sun dawo,waye zai zauna da wannan matar itada tambadaɗɗun ƴaƴannata"
Inna mairo taji haushin abinda yace,to amma yazatayi ,tasan a kaff rayuwarsa babu wanda baya maidawa magana in ka ɗauketa,ciki kuwa harda sarkin garin.
"Kabar wannan zancen dama nasan shi kakeson yi,ɗakinnaka dai zaka gyara ku zauna a can,wanne irin aurene kai kana can ita tana nan,taya zaku fahimci juna a haka."
"Fahimtar juna hhhhhhh wai to kawai tazo gidan ta zauna mana toh,dole sai anyi mata aure dani tukunna ......afff banyi sallar ba ashe,barina je na gurguzata kafin ta anjiman tazo"
Tashi yayi da sauri ya nufi ƙofar tasa,inna mairo ta share masa harabar wajen kuwa. Makulli yasaka ya buɗe ɗakin,bayan ya shiga ya maida ƙofar kaman munafuki.
___***___
Kaya take naɗewa na wankinsu da tayi a injin wanki tana waƙar ado gwanja,kana ganinta kasan duniya tana gara masa.
"Sakwara daɗi luwai mun samu guri luwai,kai wlh rayuwar masu kuɗi da daɗi sosai. Ba ruwanka da surfe,ba ruwanka da hura wutar murhu,gas ne kana ɗorawa ka gama,ga wanki ma hajiya tabarka ka saka a inji,ga cin daɗi ga albashi. Kai kuɗi yayi ni gaji"
Lace na a jikinta mai tsada doguwar riga wanda hajiya matar mai gidan tabata kunce,tsabar samun guri ƴaƴanta su Atika har kunna kallo suke a babban falo.
Ita tanayi mata wanke wanke da abinci,shikuma Malam audu yana gadi da kuma ban ruwa ga fulawoyi.
Karaff Atika ta bugo ƙofar ta shigo da gudu cikin ɗakinnasu da aka basu,wanda yake a boys quarter na gidan.
"Gaji gaji nashiga uku shikenan asirina ya tonu tawa ta ƙare gaji"
Riƙota gaji tayi tana tambayar ta lafiya take wannan hakin kaman ta kashe wani.
"Kee lafiya atika mai yasameki haka,ki nutsu kiyimin bayani mana mai ya faru ne"
"Gaji ki tattara kayanki mubar gidanann,baba ma ki faɗamasa kar ya dawo gidannan mu tafi gida gaji,mu koma gida kawai"
"Ke dallah kimin bayanin mai yafaru ne wai,mai kikayiwa hajiyanne,naga ɗazu ta fita daga gidan ma bata nan"
"Eh ta tafi amma komai ta manta saita dawo,shine.....shine.... Tasameni nida alhaji akan gadonta toh. Toh saita yanki jiki tafaɗi,kuma dama tanada hawan jini.......wlh gaji inaga ta mutu,idan ta mutu wannan sojan ɗan uwannata bazai ƙyalemu ba sam,kizo mukoma gida wlh kafin su kashemu"
Sakin hannun Atika gaji tayi ta faɗa akan gado yaraff mai kunnenta yake jiyo mata haka.
"Atika mai kikace wai...hajiyah ta kamaki da mijinta a kan gadonta,idan ma iskanci zakiyi kiyi mana,amma taya daƙiƙancinki zaisa ki bari ta kamaku,ni ai mai farinciki ce idan har yaga yana sonki zai aureki,amma kafin komai ya tabbata shikenan kin zawo mana asarar wannan arziƙi da muka fara lasa. Taya kike ganin zasu barmu mu fita daga gidannan iyee batareda sun lahanta muba"
"Gaji bama wannnan ba,ƙanwarta wannan fatin itama ta ganmu,kuma shi sojan yana waje shiya dawo dasu ɗaukar wani abu a mota"
"Meeee kikkka ceeee shikkenan tafaru ta ƙare,wlh bazan faɗawa malam ba,dolene shima ya dawo ya karbi nasa luguden,ban isa shansa nikaɗai ba aradu. Ke kuma bari a gama yimana na nan kema mu tsira na baki naki...........
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[05]
Ture atika gaji tayi daga bakin ƙofar ɗakin tana leƙawa,cikin ƙanƙanin lokaci ta haɗa gumi shirkif,banda zagin ƴar tata babu abinda take na aika aikar data jawo musu.
A kan idonta sojan ya fito da hajiya a hannunsa,fati tana binsu tana kuka,shikuma mai gidan ya biyosu cikeda kunya da sanyin jiki.
Har sunzo fita daga gidan wasu sojoji guda biyu suka iso bakin ƙofar gidan,magana suke da ƙanin hajiyan na wani lokaci kafin suka fita daga gidan a mota.
Shima alhajin mota ya ɗauka yabisu a baya.
Kenan gadinsu zayyi kada su fita a gidan komai.
Duk abinda yafaru akan idon gaji itada atika,a tunaninsu idan suka bar gidan suma zasu fice,saidai da alama ba haka bane,dan sojojin a bakin ƙofar gidan suka tsaya suna jajjagawa.
Suna cikin haka har yamma tayi liƙis hankalinsu ya gagara kwanciyah,ba halinda matar gidanne ya damesu ba illah su halin dazasu shiga.
"Hmmm mlm audu har yanzu bai dawo ba,kaddai yasan mai yafaru ya gudu ya barmu a ciki,tukunna ma mai yasa zasu hanamu fita toh daga gidan"
Kallon uwar tata atika tayi tareda cewa.
"Yanzu haka fatinnan ce tafaɗawa sojojinnan karsu barmu mu fita,dan daman tun a ɗakin ɗazu tace saita ɗaiɗaita rayuwata nida iyayena,dama ta tsaneni"
"Laaahaulah wala ƙuwwata shik........"
Bata gama salatin ba aka banko ƙofah,Fati ce firiri da ita,gyalene a jikinta hannunta ɗauke da key ɗin mota tana jijjigashi,cikeda tsiwa takalli gaji tareda cewa.
"Kar kiyi salati yanzu,ki bari saikinga kina hango wuta kafin sannnan zaki fara salati.
Don ku fito dasu daga ɗakin zuwa filin gidan"
Tana gama faɗin hakan tafita daga ɗakin,wasu murtuƙa murtuƙan mutane guda biyu suka fito da gaji itada atika zuwa filin gidan.
"Dan Allah kayi a hankali karka karya min allon kafaɗa,kaga ƙashin na tsufah ne"
Gaji ta faɗa tana sallalami.
Zubasu akayi a filin wajen da sanyi la'asar.
"Don kuyi musu horo wanda zai jirgita kamanninsu nan da zuwa gobe kada su runtsa idonsu,matsiyata macuta kawai,wato duk abinda anty Abida tayi muku da haka zaku saka mata,kin tura ƴar ki tana cin amanarta,idan kuka kasheta saiku aureshi ku mallakeshi,ku a dole kunga gida. Yau kuwa zaku yi danasanin shigowa garinnan ma ba gidannan ba"
Tana gama maganar kaman jira suke suka hau su gaji da duka ta ko ina babu tsayawa. Tun suna ganin farar wuta har ja tafara haska musu a idonsu.
Ƙarar buga get ne hasasu tsayawa da dukan domin suga wanene,fati ce ta taka fiƙi fiƙi zuwa bakin get ɗin.
Da Mlm Audu suka haɗa ido,hannunsa riƙe dana ɗansa na mijin ƙarami,sauran mata guda uku kuma ƙannen atika suna biye dashi a baya,kayan makaranta ne a jikinsu wacce hajiyan ta sakasu wata biyu dasuka wuce.
Killer smile fati tasake masa tareda cewa.
"Ahh mlm audu ka dawone to sannunka da zuwa shigomana ciki"
Abin yayi masa bambarakwai,danshi dai yasan wannan yarinyar ba kulashi take ba,baidai ce komai ba yayi ta maza yashiga gidan.
Dama wai suna ne yana gadi,tun safe fice sai ya wuni bai dawo ba,yanacan wajen sharholiyarsa,banda gadin ma menene wane aiki zai iya,ko noma ƙaramar gona kasa nomawa yake a shekara.
Da gaji yafara haɗa ido tayi gurfano kaman mai karbar gafara,hancinta da bakinta sunyi dama dama da yawu da jini da majina.
Zaro ido yayi yana shirin fita waje da gudu wani soja ya kamoshi ramm ta rigarsa ta baya.
"Malam ina kuma zakaje,maimakon ka tsaya ka cecemu wato guda kake shirin yi koh,saikazo duk mu haɗu muyi karbi azabar tare,tunda kaima yar kace ba iya ni kaɗai ba"
Bayan gaji ta gama bayanin da dashshshiyar muryarta,fati ce ta ɗora ta bashi labarin abinda atikan tayi.
"Yanzu kaima saika jona su,shima ku haɗashi don"
Aikuwa buɗar bakinsa yace.
"Yallabai wannan labarin da madam ta bayar banida masaniya akan sa,saina wuni bana gidanann bansan mai ake kitswa,dan Allah ku barni na tafi da sauran ƴaƴan"
"Baaba ya zakace haka,wlh kasan abinda yake tsakanina da Alhaji,naga kasha kamamu cikin dare,idan kafara magana sai ya baka dubu goma kayi shuru,daga baya kamma dayace maka aure na zayyi na zama matar gidannan har murna kayi,kake cemin nayi ƙoƙari da dabara na mallakeshi a tafin hannuna,wai har na samu na fitar da anty Abida a gidannan"
Kowa a wajen zaro ido yayi da bayanin atikan,ciki kuwa harda gaji,ita nata baƙincikin ɗaya yanda ake bashi kuɗi duk dare batada masaniyah.
Fati itada sojijinta basu suka bar su gaji ba sai dare,hakan ma suka gamasu da karnukan su suyita binsu da gudu har gari ya waye,kafin asuba duk sun suma babu inda yake aiki a jikinsu.
__***__
[Sumaimah a mahangar gani]
Yau da wuri na tashi,ba kaman jiyaba da bacci ya ɗaukeni har rana ta fito na makara.
Kai tsaye bayan na gyara ɗakinnamu kamar kullum ƙofar su ammin na nufah.
Koko take zubawa yaran da suka kewaye ta a kofi.
Gaisheta nayi kafin na koma gefe na zauna,saida ta gama dasu tukunna,kafin ta zubamin nawa,jiya girkinta ne da kuma yau,gobe da jibi nasan na inna rammah ne,akwai rowar abinci kenan. Yanzu su biyune a ƙofar Aina'u amaryar baban tayi yaji bata nan,wannan kamma inaga auren tacan tacan,dan ita irin matannane masu shegen son abin hannun miji,idan akwai to da zama,amma idan babu saita ɗebi jaraba tai tayi babu gairah babu dalili. Shikuwa baba samunsa ɗaya idan yayo caca ta gara masa,inkuwa ba haka ba saidai kowa yasan ta kansa,dan kuɗin sana'ar tasa ma ta Aune Aunen kayan abinci dayake a kasuwa kullum su yayah Musbahu ne masu fama da cikaton uwar kuɗin ma ballantana kuma riba.
Hannun nasa na karbi kokon da ammi ta miƙomin,bayan na gama tunanin na yi faɗi ba'a tambayeki ba.
Bayan mun gama gyara wajen nayi kafin na hau kiciniyar ɗora abincin Siyarwa,yau kasuwar garimu ce,dan haka da wuri ake yi kuma yafi na kullum yawa.
Banason wannan ranar ta zagayo,saboda nafi daɗewa a wajen tallen,ga tarin marasa ɗa'a a wajen,saidai kuma ta wani wajen nafi sonta,dan nima inayin wani abun nawa natafi dashi,inna samu riba na saka a asusu.Kuma itama ammi tana sallamata idan na dawo.
Bayan abincin ya kammalu shiryawa nayi nazo ɗauka zuwa kasuwar,shinkafa da miya ce da kuma waje,sai kabeji.
Nida Asiyah muka tafi,dan tunda aurena za'ayi dole itama tafara zuwa dan ta gane kan siyar da abincin.
Kodaɗɗun kayana ne a jikina normal na tsakar gida atampa,sai barin hijabin dana saka,wanda yafara mutuwa ta sama saboda tsufah. Ba wai kayane aka wareni ba'ayimin ba,dama gidaje dayawa masu irin ƙarfinmu daga shekara sai shekara suke ganin ɗinki,hakan ma atampar roba ce. Sauran yara kowa uwarsa na ƙoƙarin ganin tasake masa,wanda kuma ƴan mata ne sun fara hira samarinsu suyi musu. To ni kuwa ciki wannene nakeda shi ɗaya,shiyasa a gidannamu nafi kowa ƙarancin suturar sakawa,hana rantsuwa nema Yah Musbahu yayimin ankon ƴan matan gidan da akayi wata shida dasuka wuce,shine na samu nake ado dashi ranar juma'a.
Kasancewar kasuwar da ɗan tazara tsakaninta da gidanmu,shiyasa saida muka dan taka kafin muka isa.
Wajen rumfata ta kullum na ajiye kayan,itama Asiyah na sauƙe mata nata,yarinyar ba wata babba bace a shekaru,amma nan idan anjima in tafara magana da masu siyan abinci samari,sai ka ɗauka wata hamshaƙiyar budurwa ce,abin yana bani mamaki yanda muhallinnamu gaba ɗaya ya koma haka.
Jejjera komai nayi a muhallinsa na fara zubawa wanda suka zo siyah,wanda dama costomominmmu ne na kullum,sai kuma waɗanda ba'a rasawa.
Hankalina ya tafi wajen zuba abincin,buƙatata na sallami wadanda suka rufemin kai,ohh abin babu daɗi idan aka rufeka kana zuba abincin,wai a hakanma Asiyah na taimakona da zuba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3 Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21