nan gefe da gari"
"Dama akwai kaji kuka gasa mana zomo jiyah,hadda cemin babu komai cikin garinnan banda waɗancan karashiyoyin?"
Cikin bacin rai yayi maganar yana hararar taska,wanda yake mazari yana sunne kai. Al'adarsu ce dama a babbaka wuta a gasa kajin mutane da kuma awaiansu idan sunyi dare a waje basu koma gida ba,duk garin kowa yasan yaran goje da cinye dabbobin mutane,gashi babu wanda ya isa cewa kanzil,kaima da ana ci babbaka zasuyi su cinye. Yaran su samari masu tasowa duk ya maidasu yaransa sai abinda yace,wani abun takaicin kakai ƙara wajen sarki babu abinda za'ayi,dan in dukane ko ɗauri yanda kasan ka ɗaure itace haka zaka gani,shikansa sarkin ƴaƴansa uku duk yaransa ne,sai abinda yace shi zasuyi bana ubannasu ba,idan aka masa horo haka zai hanasu zuwa gida har tsawon wata guda,matansa haka zasu ɗaga masa hankali dole sai ya janye abinda yace.
A zaune yake akan wata kujera a tsakar dajin ta fatun awakin mutane,da ba shine shugaban dawar ba,wani mutum ne mungu baƙiƙƙirin dayazo daga sudan. Gabaɗaya duk ya takuramusu komai shi sai kansa,goje ko shekara biyar baiyyi da zuwa garin ba shida iyayensa.
Tunda farko dama bai ɗauki rainin hankalin Damazau ba,shugabansu a lokacin.
Kullum cikin sa'insa suke,har goje yayi nasarar yanke maƙogaransa wata rana yazama shine sarkin dawar,shekara biyu baya. Abubuwa da dama sun faru lokacin,kowa a garin banda kama sunan goje babu abinda yake,matsi da takuri ya ƙara yawaita a cikin garin,yayinda su kuma yaransa suka fara fantama sunayin yanda suka ga dama,saboda yanda goje yabasu lasisin yin yanda ransu yake so a duk sanda sukaga dama.
Tura cinyar kazar yayi a bakinsa ya zuge tsokar kafin ya wullar da ƙashin.
"Shege dama yanada kazi bula bula haka muke cin zomaye,indai bayyi ƙara ba ku dunga ɗebo mana uku a kowacce rana,in yayi magana kuce yazo yasameni,ƴan kare da jajayen kunne sai suyita tara dabbobi yawun mutum yana cinƙewa in yagani,su basuci ba basu bawa mutum ba."
"Angama ogah goje,ai saima ka gansu da rai,manya manya fah,naji ance wai kawun Ragarus neh"
Yafaɗa yana kallon wani saurayin bafulatani a gefensa riƙe da kwari da baka a hannunsa.
"Ragarus kace dukiyarku ce muke shirin hawa kai,kaji nace bakwa ci koh,to yazanyi hakan kuke saika saka sorry fah"
"Ogah kenan ai bai daɗe da dawowa ba ne,dani kaina saina fi haka,dan a bayan kwanaki kam dole zan more"
"Sheege ɗan kawu,to tsugunna ka dangwali arziƙi"
"Ai ogah wani dangwalar arziƙin ma sai matar ogah tazo gida,zamuyi shagali"
Dariya suka saka da shewa,amma lokaci ɗaya goje ya turbune fuska yana muzurai,wani kallon tsare rai yayiwa taska,har hakan yakasa sakashi haɗiye naman daya saka a baki.
"Taskaaah ka iya bakinka fah in kana son kwana da fatar bakinka,yaushe raini yafara shiga tsakani da har kake haɗani da mace, harda wani zakuyi shagali......hmmm ai naji haushi ɗazu,wai me yasaka ma ban cirewa wannan tsohon ƴan maraina bane,kamanni yayi caca dani bashi ko sisi,kuma har yana saka ran cinye saniyata wai,kutt Sailuba fah yakeson cinyewa wai a caca,kuma ma harda fansar saniyata da wata gajarabil ɗin ƴar sa,kai ya jawo mata ma aradu,zataci ƙaniyar tane muddin da taka gonata"
"Ayi haƙuri ogah bazai sake faruwa ba"
Taska yafaɗa yana sunkuyar dakai.
Jefah naman dayake hannunsa yayi kan ganyen dayake gabansa,tashi yayi daga kan kujerar tasa yana gyara zaman wandon jikinsa. Ta saman wutar ya tsallaka maimakon yabi ta gefe.
Bai waiwayo ya kallesu ba har ya ƙule cikin jejin.
Dukkan sauran yaran kowa taska ya kalla yana jiye masa.
"Kai taska wlh jagos ne,kalli fah yanda ka kunnashi,kasan fah yau ya juƙi hayaƙi dayawa a sama yake over. Da alama tunda ya nufi gidansa na cikin jeji to saita Allah kenan,ranar fah dana fishi gurnani naji yanayi a cikin ɗakin,anya kuwa ogah goje mutum ne kuwa?"
Dukkansu mai bayanin suka zuba ido,saboda jin abinda yafaɗa.
Ɗaya daga cikinsu ne wanda tun ɗazu bayyi magana ba yana gefe,wato Tunga,kuma shine na hannun daman goje,yafi sanin sirrinsa fiyeda su.
"Kai Ragarus kafiye fah surutu,da alama so kake yasaka shuru na har abada,kuma inna sakejin kana bibiyar sawunsa na abinda yake saina faɗa masa tamm. Mazaje mugama mu tafi gida,ogah nasan bazai dawo ba sai gobe,kunsan kuma munada ƴar tsamar da zamu buga da ƴan solo gobe,tunda sun ƙalubalance mu."
Dukkansu shuru sukayi da zancen,amma daga yanda Tunga yayi magana to akwai ƙamshin gaskiya a maganar Ragarus kenan.
___***___
Tafiya yake kansa tsaye zuwa cikin dajin,duk da dare da kuma rashin haske,da kuma hanyar duk ciyawa da itatuwa,amma haka yake jefah ƙafafunsa ko jikinsa,kana gani kasan yasan hanyar da yarda ƙafafunsa su kaishi.
Yaɗanyi tafiya mai nisa kafin yafara haɗa hanya yana dafe kai,wani numfashi yafara saki daga cikin ƙirjinsa wanda yake bada sauti mai diri.
A haka yana tafiyar da ƙyar cikin jarumta har ya isa gaban wata bukka ita kaɗai a cikin dokar ɗajin. Buɗe ƙyauren yayi ya faɗa cikinta,ɗakin vaƙiƙƙirin yake anyi masa yabe da baƙin fenti, na shuni,wani buzu ne a tsakar cikin bukkar shima baƙi,bayan haka babu komai a cikin ɗakin.
Faɗawa yayi kan buzun yana riƙe kai,tareda fitar da wani ƙaraji kaman na karshiyah.
Ya daɗe a wannan yanayin yana birgima kafin ya fara fitar da wani numfashi mai nauyi.
Buɗe idanuwansa yayi wanda sukayi tamkar garwashi saboda jan da sukayi.
Ɗakin ya zubawa idanuwan kaman mai nazari,can kuma sai ya tashi ya zauna. Buzun ya ɗaga ya ɗauki tabar wiwi ya kunna mata wuta,zuƙar hauka yakeyi mata tana shiga cikin kansa na tsawon lokaci.
Kaman an tsikareshi yasake jefar da itah yana riƙe kai,da alama dai wata ƙarace yakeji wanda kunnuwansa basason hakan sam.
Sakin kunnen yayi ya faɗi a wajen tamkar matacce,ko numfashi bayayi na kirki...........
Ku nima na shiga ruɗani,mai yasameshi haka,suwaye suka fara yarda da maganar Ragarus🤣🤣🤣.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
Dare yayi sosai,bakajin komai sai ƙarar jemagu da kuma karnuka,wasu na gidanne na yayunmu,wasu kuma na maƙwantane. Banason haushin karnuka ko kaɗan,to amma kuma yazanyi da saurayin kakata,shikansa wanda ake shirin ɗaura ƙaddarata da tasa yafi kowa yawan karnuka a yankinnamu.
Tashi nayi na zauna ina kallon ɗakinnamu,ba wani girma ne dashi ba,amma yaran dasuke ɗakin Allah yayi yawa dasu,basuda wani takamaimai yawansu,saboda wani lokacin suna raguwa,yayinda wani lokacin kuma yawansu ke haura misali,kaman dai yau.
Dan duk matar gidan da mijinta yake ɗakinta nan take koro ƴar ta ta kwana,su kwana suna birgima suna fitsari,a barni da gyaran ɗakin kullum kaman ibada.
Duk cikin ɗakin nice babba,nayi rayuwa a ɗakin da ƴan matan gidan,a hankali aka fara aurensu har suka ƙare kaff sauran ni kaɗai,saikuma bazawarai wanda suka dawo daga gidan nasu auren amma su basa yarda su shigo wannan kurkukun kwana.
Ba ƙarar haushin karen ko kuma gwartin yaranne ya hanani bacci ba,bace abinda ya faru,tun ɗazu nayi nayi na runtsa amma na gagara,ko nayi niyyar baccin babu abinda nake gani sai fuskar goje mai kama da dodo,inaga kaff gidannamu babu wanda yakaini tsoronsa,bansani ba ashe dashi zan ƙare rayuwata.
Ahh anya kuwa nabari a kaini wajennasa wani satin? Zuciyata wacce take suya tayimin wanann tambayar.
Abu biyu sukazo cikin kaina,shinna gudu kokuma na na kashe kaina?. Dukkansu ba abune mai kyau ba,amma idan na bari aka kaini in shi ya kasheni shikenan na rataya a kansa koh?
Tashi nayi daga kan katifar bayan na ɗauke cinyoyin yaran da suke kaina,tsakar gidan na fito ina kallon taurari da kuma farin wata,sukam sunji daɗinsu sai haske sukeyi,ko yaushe zanga haske nima a rayuwata oho.
Hankalina yana wajen kallon saman saikuma najiyo kaman alamar matsin mutum a kewayen dabbobi na gidan.
Gaba nane naji ya buga,mai mutum kuma yake a tuken dabbobi da tsawon darennan.
Da kaman vazan ƙarisa ba karnaje aljanine nayi gamo,saikuma to zuciya da zon gulma,na dayyi ta maza na nufi kewayen.
A hankali nake tafiya ina sanɗa har na iso daidai wajen ta baya,tsugunnawa nayi na kara kaina tareda nutsuwa,domin naji mai ake cewa.
Muryar Inna rammah kuma matar baba ta biyu? Itada inna atika, matar kawu Ɗahe. Mai kuma suke a kewayen dabbobi da daddare,naga dai in wajen dabbobi ma sukaje sukam babu nasu aciki,awakin ammi ne a wajen sai kuma ragunan mazan gidan da suke kiwo.
Wata zuciyar ce tabani kaddai satar dabbobi zasuyi,ko kuma suyi musu illah,,dan hakan ba wani babbane daga cikin aikinsu ba,daga su har ƴayansu ba mutuncine ko tausayine dasu ba,nikaɗai sai Allah muka san baƙar izayar dana sha a hannunsu,damma wai a hakan basamin wani abun saboda a wajen ammi baba ya damƙani lokacin daya kawo ni gidannan ina ƴar ƙarama,kuma suna shakkarta itada kayanta.
Kaina na ɗaga kaɗan ina leƙawa domin naga wacce akuyah zasu ɗauka,saidai ga mamakina ba akuya suke ɗauka ba,rami sukayi a wajen suna binne wani abu da bansan menene ba.
Can kuma sainaji inna rammah tafara magana.
"Ke wai fah hakanma munyi da gaske,da tuni ƴayan mu suna nan zaune itakuma tayi aure,da ai bamu yarda da zancen Ƴar boka ba,datace mana muddin wannan ƴa tana gidannan to ƴayan mu bazasu auru ba. Naji fah kaman cewa yake ɗazu wai inna gonarsa zai siyar ya kaiwa goje kuɗin,yafasa bashi itah,kiji kayan baƙin asirin da uwartata tayi mata na farin jini ya yaye tahana ƴaƴanmu masu tasowa aure"
"Iyi kuma fah,bare ma ni mai yara ƙanana ai dole na tashi tsaye ki gafah shekarar da muka mata maganinnan shikenan sai ƴayanmu suka fara auruwa kaman ana musu ruwan mazaje daga sama,da kuwa ita kaɗai suke gani da gashi a gidannan,kallon maza sukeyiwa yayanmu"
"Hmm yanzu dai mungama da wanann,muddin yayi aiki to Baban su Hajjo bazai sake yin wani maganar fasa aurenta ga goje ba,suje can in ma babbakata zayyi ya babbaka ta. Itama Deeja(ammi) munafuka saikace bada ita aka haɗa vaki ba lokacin yimata magani na farko,saboda taga duk samarin ƴaƴan ta ita suke so,yanzun kuma dan taga dukkan manyan ƴaƴanta sun ƙare shine tace wai yanzu ba ruwanta"
"Wlh ƙarya take kedai bari asiyanta ta taso yanda take ji da yarinyar nan,tun yaushe ta tashi tsaye idan taga bazata auru ba, to yanzu idan Baban su hajjo yaƙi aurarta ga goje ya zamuyi kenan?"
"Wlh indai wanann kam ya karye toh haukata ta zanyi,yarinya jarabbabiyah ga kyau kaman mayyah irinna uwarta,keda bamu kauda uwar ba ai da yanzu bazamu samu kansa ba,yanda yake son ta kaman zai mutu.....maza ai munafukaine"
"Ko itama mu aikata wajen uwartata ba,duk da bansan Zinarunba amma in haka take kaman ƴarata kam dole zai jauce akan ta,haka suke da ƙira kaman su sukayi kansu"
"Zakuwa mu sanja mata kamanni,ke nifah na tsani ƴar nan,menene bamu gani ba a wajen baban hajjo akan ta,indai wannan karon bata bar gidannan ba to kuwa zamuyi babban shiri,in ma Deejah ce yanzu takeson kareta to da ita zamu haɗa..........."
Bangama jin mummunan labarin da suke ba na sulale a wajen,saboda yanda ƙafafuna suke rawa bazan iya gama ji ba sam.
Hawayene kawai yake zirara a idona,yayinda dukkan wani abu dayake amfani a cikina ya dauƙi yajin aiki na wasu daƙiƙu.
Tun inajin hayaniyarsu da shewarsu har na daina ji da alama sun bar wajen,na daɗe ina zargin mutanen gidannan namu basu san Allah ba,amma yau kam na tabbatar.
Gari yafara haske asuba ta gabato,kafin na bar wajen na nufi ɗakinmu,ikon Allah ne kaɗai ya kaini ɗakin.
Dana kwanta ma ba bacci nayi ba,zuru nayi har assalatu tayi.
Ɗankwalin danake yin sallah dashi na ɗauka na fita daga ɗakin zuwa inda nake sallah,a canne ƙofar wani baban yayanmu wanda yagina ƙofarsa amma bayyi aureba,a wajen nakeyin sallah,saboda ɗakinmu kam nasan bazzayi sallah ba.
Bayan na idar da sallahr na daɗe ina roƙon Allah kaman yanda na saba,yau kam banyi karatun Ƙur'ani dayawa ba,saboda yanda bacci ke fizgata,ban samu damar komawa ɗakiba anan bacci yayi gaba dani.
Zafin rana ne yafara cin ƙafafuna,hakanne yasa na tashi na zauna,safiya tayi ashe har rana tafito bansani ba.
Ajiyar zuciya nayi dan ma yau banice dayin wanke wanke ba,shara kawai zanyi sai ɗora abincin siyarwar ammi. Dan haka cikin nutsuwa na tashi na ninke abin sallahr tawa zan bar ƙofar.
Motsin mutum naji hakanne yasa na ɗaga idona.
Da yaya Musbahu na haɗa ido yana tsaye yana kallona.
Rusunawa nayi na gaisheshi,yanada mutunci shikam sosai,dan ko hayaniyar gidan bata wani dameshi ba,shine babban ɗan ammi,yayi diploma yana koyarwa a makarantar secondry ta garin.
"Sumaimah lafiya kikazo nan kina bacci,na dawo daga sallah naga kinyi bacci anan"
"Ahh bakomai kawai baccinne ya ɗan daukeni"
"Ohh toh,kiyi haƙurifah da abinda baba yayi miki kinji,in kika jure komai zai wuce kinji,yau ma nayi masa maganar a masallaci, amma sai ya hauni da faɗa,kuma jiya da mukayi masa magana yace zai bashi kuɗin yafasa aura miki shi,amma kuma yau da asuba ya dage sai ya aura miki shi,abin yabani mamaki"
Idon ne ya cicciko lokacin danaji abinda yaya Musbahu yace,maganar dasu inna rammah sukayi jiyace ta faɗo min araina,wato su yayah Musbahu ne suka tausheshi akan aurar dani ga wancan dodon,har ya yarda su kuma waɗannan matan suka sake juyar da kansa.
Saurin share hawayen idona nayi tareda jijjiga masa kai.
"Babu komai yah Musbahu in hakan shine ƙaddarata banida zabi illah na rungumeta,dama dolene bawa yayarda da ƙaddara mai kyau ko kuma akacin haka.
Har nazo fita daga ƙofar tasa yasake yimin magana.
"Kije ammi tana ta nemanki kinji,ga wannan kuma ki boye ki dunga siyan koko,an bani albashina jiyah"
Yafaɗa yana miƙomin naira ɗari biyar.
Wani kukane ya tahomin lokacin dana saka hannu na karba,wannan karon ban tare shi ba nayita kunza kayana,tun yana rarrashi na har yabari yabar ƙofar.
Allah ne kaɗai yasan yanda nake ƙaunarsa a cikin yan uwannanwa,da kuma yanda yake birgeni,shikam ya fita zakkah a gidannan.
Harna isa ƙofar ammi ina kwarara masa ruwan Addu'a ta samun nasara a raina,Allah ya haɗashi da mace tagari ba irin matan gidannan ba,dan daga kan iyayen har surukan kaman an cuɗasu an rabasu haka suke.
A baranda na sameta tana tsince shinkafar daza'a dafa in anjima,wajen kaca kaca da miyar tuwo da kuma kunu,ina yara suka zuzzubar lokacin da suka karya.
Gaisheta nayi kafin na leƙa ɗakin inna rammah mah. Tanata masifah da yaranta suna rashin ji.
Fuskarta dauke da murmushi da amsamin,kaman ba itace ta gama faɗin kalaman da mutumin dayasan zai mutu bai kamata ya furta ba.
Tuwo nah na ɗauka naci nakai kwanon wajen wanke wanke.
Bishirah da asiyah ne suke wanke wanken,ƴar rammah da kuma ammi.
Harara ta Bishirah tayi dana ajiye kwanon cikeda tsiwa.
"Wai mutum bazai ci abinci da wuri ba dan mulki,sai an kusa gama wanke wanke ya kawo kwano"
Kunnenta na riƙe ta bangaren danake,dan abin yayimim ciwo,yarinyar da in auren shekara sha biyu zanyi saina kusa haifarta take faɗamin wannan maganar.
"Ke wato kin iya rashin kunya koh,yaushene ma kuke wanke wanken,naga saikuyi sati bakuyi ba nina ke,dan an fara baku shine har kun fara tsiya koh?"
Maganar inna rammah najiyo daga bakin ɗakinta lokacin da Bishirah ta kwanɗa ihu kaman ina zare mata rai.
"Sake mata kunne to ƴar gadon marasa mutunci,baƙin cikin menene haka da har zaki cire mata kunne,so kike ki nakasata tayi zaman gida kaman ke?"
Sakin kunnennan ta nayi,yayinda maganganunta kemin zafi a rai,kallon baki isheni ba nayi mata kafin na ɗau tsintsiya na fita share harabar ƙofar tamu,duk abinta dai nasan bazata dakeni ba,da dai ta dakeni komai ma tayimin,amma yanzu na wuce duka,saidai tayi min muguntar boye ta asiri.
Abinda yafarune ma ya faɗomin a rai,hakanne yasa na nufi kewayen dabbobin kaman da niyyar cewa shara zanyi.
Akan wajen da sukayi binne binnen idona ya sauƙa,tabbas kam ba mafarki nake ba..
Jan lilon ƙafafuna nayi zuwa wajen,tsugunnawa nayi idon kyam akan abinda ƙarfi da yaji yakeson rabani da gidanmu.
Harna saka hannun zan tone wajen saikuma na tuna maganganunsu,wataƙila inna tone asirinnan ya karye baba yagane kuskuren da yayi a caca,har ya nemi kin auramin goje,to amma su inna rammah fah,zasu barni na cigaba da zama harna samu miji daidai dani nayi aure. Tabbas ba karamin aikinsu bane su aikata abinda sukayi iƙirarin faɗa.
Inkuma yanda suka fada dagskene na tarewa ƴaƴansu farin jininsu wanda nasan bokane yafadamusu dan ya ci kudinsu,toh zan tursasa ammi sake cutar dani muddin akan ƴar tane Asiyah.
Wanda hakan zai zama abune da bazanso ya kasance ba.
Maida kasar dana fara tonewa nayi na binne wajen cikin sanyin jiki,na zabi barin gidan kawai,koma mai zaimin yayimin Allah ne ke riƙeda rai na ai,wuya kuwa bata kisa sai kwana yaƙare.
Tashi nayi na barbaje ƙasar tareda fara share wajen,banyi niyya ba amma inna ƙiyi kar suyi tunanin naga abinda sukayi jiyan.
Wannan wace irin rayuwa ce,ace wai aisiri akayi maka amma ka ƙwammaci ka barshi ya hau kanka......ke duniyah.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
_Wannan shafin Sadaukarwa ga *Real gudaliyah* chief admin da ƙungiyar zafafah,nagode sosai sosai. Dama sauran masu nuna soyayya ga littafina ina godiya sosai._
________________________________
*Book 1*
Chp[04]
Saida ya daidaita hasken a cikin idonsa kafin ya buɗe idon dukka. A kwance yake a inda ya suma jiya,wato cikin bukkar,yunƙurawa yayi babu salati bare godiya ga Allah.
Kakkaɗe jikinsa yayi daga ƙurar dayayi kafin ya fito daga cikin bukkar yayi wata miƙa.
Ido ya haɗa da karnuka guda uku,murtuƙa murtuƙa a kwance a filin wajen,suna kallon ya fito suka nufi inda yake.
Feɗuwa yayi dukka suka amsa masa kaman sunji mai yace.
Hanyar dazata kaishi cikin gari ya nufah kansa tsaye yana tafe suna take masa baya,yanda yake baƙi fuskarnan duk gashi haka suma suke.
Duk hanyar dayabi yara matsawa suke harda samari.
A wajen mai shayin unguwarsu ya zauna akan benci,su kuma karnukan suka tsaya a bayansa kaman wasu fadawa.
"Kai iliyah yiyomin haɗin shayinnan da kake min,kaga na juyeshi a cikina nan"
Dama murya a shaqe,ta kuma haɗu da tashi a bacci,banda hamami babu abinda yake,amma hakan ko kaɗan bai dameshi ba,haka wanda yake gefensa ma ko mai zayyi bai isa yace ya dame shin ba.
Ido suka haɗa da Iliyah wanda yake ta aikin juyah shayi daga wannan kofin zuwa wannan.
"Amma goje na wata biyar fah ya taru akan ka ko ƙwandala baka rage ba"
"To dolene saina rage koda banni da kuɗi iyee,kai akan shayin zaka dunga tsayarmin,idan bazaka
Showing 3001 words to 6000 words out of 60324 words
"Dama akwai kaji kuka gasa mana zomo jiyah,hadda cemin babu komai cikin garinnan banda waɗancan karashiyoyin?"
Cikin bacin rai yayi maganar yana hararar taska,wanda yake mazari yana sunne kai. Al'adarsu ce dama a babbaka wuta a gasa kajin mutane da kuma awaiansu idan sunyi dare a waje basu koma gida ba,duk garin kowa yasan yaran goje da cinye dabbobin mutane,gashi babu wanda ya isa cewa kanzil,kaima da ana ci babbaka zasuyi su cinye. Yaran su samari masu tasowa duk ya maidasu yaransa sai abinda yace,wani abun takaicin kakai ƙara wajen sarki babu abinda za'ayi,dan in dukane ko ɗauri yanda kasan ka ɗaure itace haka zaka gani,shikansa sarkin ƴaƴansa uku duk yaransa ne,sai abinda yace shi zasuyi bana ubannasu ba,idan aka masa horo haka zai hanasu zuwa gida har tsawon wata guda,matansa haka zasu ɗaga masa hankali dole sai ya janye abinda yace.
A zaune yake akan wata kujera a tsakar dajin ta fatun awakin mutane,da ba shine shugaban dawar ba,wani mutum ne mungu baƙiƙƙirin dayazo daga sudan. Gabaɗaya duk ya takuramusu komai shi sai kansa,goje ko shekara biyar baiyyi da zuwa garin ba shida iyayensa.
Tunda farko dama bai ɗauki rainin hankalin Damazau ba,shugabansu a lokacin.
Kullum cikin sa'insa suke,har goje yayi nasarar yanke maƙogaransa wata rana yazama shine sarkin dawar,shekara biyu baya. Abubuwa da dama sun faru lokacin,kowa a garin banda kama sunan goje babu abinda yake,matsi da takuri ya ƙara yawaita a cikin garin,yayinda su kuma yaransa suka fara fantama sunayin yanda suka ga dama,saboda yanda goje yabasu lasisin yin yanda ransu yake so a duk sanda sukaga dama.
Tura cinyar kazar yayi a bakinsa ya zuge tsokar kafin ya wullar da ƙashin.
"Shege dama yanada kazi bula bula haka muke cin zomaye,indai bayyi ƙara ba ku dunga ɗebo mana uku a kowacce rana,in yayi magana kuce yazo yasameni,ƴan kare da jajayen kunne sai suyita tara dabbobi yawun mutum yana cinƙewa in yagani,su basuci ba basu bawa mutum ba."
"Angama ogah goje,ai saima ka gansu da rai,manya manya fah,naji ance wai kawun Ragarus neh"
Yafaɗa yana kallon wani saurayin bafulatani a gefensa riƙe da kwari da baka a hannunsa.
"Ragarus kace dukiyarku ce muke shirin hawa kai,kaji nace bakwa ci koh,to yazanyi hakan kuke saika saka sorry fah"
"Ogah kenan ai bai daɗe da dawowa ba ne,dani kaina saina fi haka,dan a bayan kwanaki kam dole zan more"
"Sheege ɗan kawu,to tsugunna ka dangwali arziƙi"
"Ai ogah wani dangwalar arziƙin ma sai matar ogah tazo gida,zamuyi shagali"
Dariya suka saka da shewa,amma lokaci ɗaya goje ya turbune fuska yana muzurai,wani kallon tsare rai yayiwa taska,har hakan yakasa sakashi haɗiye naman daya saka a baki.
"Taskaaah ka iya bakinka fah in kana son kwana da fatar bakinka,yaushe raini yafara shiga tsakani da har kake haɗani da mace, harda wani zakuyi shagali......hmmm ai naji haushi ɗazu,wai me yasaka ma ban cirewa wannan tsohon ƴan maraina bane,kamanni yayi caca dani bashi ko sisi,kuma har yana saka ran cinye saniyata wai,kutt Sailuba fah yakeson cinyewa wai a caca,kuma ma harda fansar saniyata da wata gajarabil ɗin ƴar sa,kai ya jawo mata ma aradu,zataci ƙaniyar tane muddin da taka gonata"
"Ayi haƙuri ogah bazai sake faruwa ba"
Taska yafaɗa yana sunkuyar dakai.
Jefah naman dayake hannunsa yayi kan ganyen dayake gabansa,tashi yayi daga kan kujerar tasa yana gyara zaman wandon jikinsa. Ta saman wutar ya tsallaka maimakon yabi ta gefe.
Bai waiwayo ya kallesu ba har ya ƙule cikin jejin.
Dukkan sauran yaran kowa taska ya kalla yana jiye masa.
"Kai taska wlh jagos ne,kalli fah yanda ka kunnashi,kasan fah yau ya juƙi hayaƙi dayawa a sama yake over. Da alama tunda ya nufi gidansa na cikin jeji to saita Allah kenan,ranar fah dana fishi gurnani naji yanayi a cikin ɗakin,anya kuwa ogah goje mutum ne kuwa?"
Dukkansu mai bayanin suka zuba ido,saboda jin abinda yafaɗa.
Ɗaya daga cikinsu ne wanda tun ɗazu bayyi magana ba yana gefe,wato Tunga,kuma shine na hannun daman goje,yafi sanin sirrinsa fiyeda su.
"Kai Ragarus kafiye fah surutu,da alama so kake yasaka shuru na har abada,kuma inna sakejin kana bibiyar sawunsa na abinda yake saina faɗa masa tamm. Mazaje mugama mu tafi gida,ogah nasan bazai dawo ba sai gobe,kunsan kuma munada ƴar tsamar da zamu buga da ƴan solo gobe,tunda sun ƙalubalance mu."
Dukkansu shuru sukayi da zancen,amma daga yanda Tunga yayi magana to akwai ƙamshin gaskiya a maganar Ragarus kenan.
___***___
Tafiya yake kansa tsaye zuwa cikin dajin,duk da dare da kuma rashin haske,da kuma hanyar duk ciyawa da itatuwa,amma haka yake jefah ƙafafunsa ko jikinsa,kana gani kasan yasan hanyar da yarda ƙafafunsa su kaishi.
Yaɗanyi tafiya mai nisa kafin yafara haɗa hanya yana dafe kai,wani numfashi yafara saki daga cikin ƙirjinsa wanda yake bada sauti mai diri.
A haka yana tafiyar da ƙyar cikin jarumta har ya isa gaban wata bukka ita kaɗai a cikin dokar ɗajin. Buɗe ƙyauren yayi ya faɗa cikinta,ɗakin vaƙiƙƙirin yake anyi masa yabe da baƙin fenti, na shuni,wani buzu ne a tsakar cikin bukkar shima baƙi,bayan haka babu komai a cikin ɗakin.
Faɗawa yayi kan buzun yana riƙe kai,tareda fitar da wani ƙaraji kaman na karshiyah.
Ya daɗe a wannan yanayin yana birgima kafin ya fara fitar da wani numfashi mai nauyi.
Buɗe idanuwansa yayi wanda sukayi tamkar garwashi saboda jan da sukayi.
Ɗakin ya zubawa idanuwan kaman mai nazari,can kuma sai ya tashi ya zauna. Buzun ya ɗaga ya ɗauki tabar wiwi ya kunna mata wuta,zuƙar hauka yakeyi mata tana shiga cikin kansa na tsawon lokaci.
Kaman an tsikareshi yasake jefar da itah yana riƙe kai,da alama dai wata ƙarace yakeji wanda kunnuwansa basason hakan sam.
Sakin kunnen yayi ya faɗi a wajen tamkar matacce,ko numfashi bayayi na kirki...........
Ku nima na shiga ruɗani,mai yasameshi haka,suwaye suka fara yarda da maganar Ragarus🤣🤣🤣.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[03]
[Sumaimah a mahangar gani]
Dare yayi sosai,bakajin komai sai ƙarar jemagu da kuma karnuka,wasu na gidanne na yayunmu,wasu kuma na maƙwantane. Banason haushin karnuka ko kaɗan,to amma kuma yazanyi da saurayin kakata,shikansa wanda ake shirin ɗaura ƙaddarata da tasa yafi kowa yawan karnuka a yankinnamu.
Tashi nayi na zauna ina kallon ɗakinnamu,ba wani girma ne dashi ba,amma yaran dasuke ɗakin Allah yayi yawa dasu,basuda wani takamaimai yawansu,saboda wani lokacin suna raguwa,yayinda wani lokacin kuma yawansu ke haura misali,kaman dai yau.
Dan duk matar gidan da mijinta yake ɗakinta nan take koro ƴar ta ta kwana,su kwana suna birgima suna fitsari,a barni da gyaran ɗakin kullum kaman ibada.
Duk cikin ɗakin nice babba,nayi rayuwa a ɗakin da ƴan matan gidan,a hankali aka fara aurensu har suka ƙare kaff sauran ni kaɗai,saikuma bazawarai wanda suka dawo daga gidan nasu auren amma su basa yarda su shigo wannan kurkukun kwana.
Ba ƙarar haushin karen ko kuma gwartin yaranne ya hanani bacci ba,bace abinda ya faru,tun ɗazu nayi nayi na runtsa amma na gagara,ko nayi niyyar baccin babu abinda nake gani sai fuskar goje mai kama da dodo,inaga kaff gidannamu babu wanda yakaini tsoronsa,bansani ba ashe dashi zan ƙare rayuwata.
Ahh anya kuwa nabari a kaini wajennasa wani satin? Zuciyata wacce take suya tayimin wanann tambayar.
Abu biyu sukazo cikin kaina,shinna gudu kokuma na na kashe kaina?. Dukkansu ba abune mai kyau ba,amma idan na bari aka kaini in shi ya kasheni shikenan na rataya a kansa koh?
Tashi nayi daga kan katifar bayan na ɗauke cinyoyin yaran da suke kaina,tsakar gidan na fito ina kallon taurari da kuma farin wata,sukam sunji daɗinsu sai haske sukeyi,ko yaushe zanga haske nima a rayuwata oho.
Hankalina yana wajen kallon saman saikuma najiyo kaman alamar matsin mutum a kewayen dabbobi na gidan.
Gaba nane naji ya buga,mai mutum kuma yake a tuken dabbobi da tsawon darennan.
Da kaman vazan ƙarisa ba karnaje aljanine nayi gamo,saikuma to zuciya da zon gulma,na dayyi ta maza na nufi kewayen.
A hankali nake tafiya ina sanɗa har na iso daidai wajen ta baya,tsugunnawa nayi na kara kaina tareda nutsuwa,domin naji mai ake cewa.
Muryar Inna rammah kuma matar baba ta biyu? Itada inna atika, matar kawu Ɗahe. Mai kuma suke a kewayen dabbobi da daddare,naga dai in wajen dabbobi ma sukaje sukam babu nasu aciki,awakin ammi ne a wajen sai kuma ragunan mazan gidan da suke kiwo.
Wata zuciyar ce tabani kaddai satar dabbobi zasuyi,ko kuma suyi musu illah,,dan hakan ba wani babbane daga cikin aikinsu ba,daga su har ƴayansu ba mutuncine ko tausayine dasu ba,nikaɗai sai Allah muka san baƙar izayar dana sha a hannunsu,damma wai a hakan basamin wani abun saboda a wajen ammi baba ya damƙani lokacin daya kawo ni gidannan ina ƴar ƙarama,kuma suna shakkarta itada kayanta.
Kaina na ɗaga kaɗan ina leƙawa domin naga wacce akuyah zasu ɗauka,saidai ga mamakina ba akuya suke ɗauka ba,rami sukayi a wajen suna binne wani abu da bansan menene ba.
Can kuma sainaji inna rammah tafara magana.
"Ke wai fah hakanma munyi da gaske,da tuni ƴayan mu suna nan zaune itakuma tayi aure,da ai bamu yarda da zancen Ƴar boka ba,datace mana muddin wannan ƴa tana gidannan to ƴayan mu bazasu auru ba. Naji fah kaman cewa yake ɗazu wai inna gonarsa zai siyar ya kaiwa goje kuɗin,yafasa bashi itah,kiji kayan baƙin asirin da uwartata tayi mata na farin jini ya yaye tahana ƴaƴanmu masu tasowa aure"
"Iyi kuma fah,bare ma ni mai yara ƙanana ai dole na tashi tsaye ki gafah shekarar da muka mata maganinnan shikenan sai ƴayanmu suka fara auruwa kaman ana musu ruwan mazaje daga sama,da kuwa ita kaɗai suke gani da gashi a gidannan,kallon maza sukeyiwa yayanmu"
"Hmm yanzu dai mungama da wanann,muddin yayi aiki to Baban su Hajjo bazai sake yin wani maganar fasa aurenta ga goje ba,suje can in ma babbakata zayyi ya babbaka ta. Itama Deeja(ammi) munafuka saikace bada ita aka haɗa vaki ba lokacin yimata magani na farko,saboda taga duk samarin ƴaƴan ta ita suke so,yanzun kuma dan taga dukkan manyan ƴaƴanta sun ƙare shine tace wai yanzu ba ruwanta"
"Wlh ƙarya take kedai bari asiyanta ta taso yanda take ji da yarinyar nan,tun yaushe ta tashi tsaye idan taga bazata auru ba, to yanzu idan Baban su hajjo yaƙi aurarta ga goje ya zamuyi kenan?"
"Wlh indai wanann kam ya karye toh haukata ta zanyi,yarinya jarabbabiyah ga kyau kaman mayyah irinna uwarta,keda bamu kauda uwar ba ai da yanzu bazamu samu kansa ba,yanda yake son ta kaman zai mutu.....maza ai munafukaine"
"Ko itama mu aikata wajen uwartata ba,duk da bansan Zinarunba amma in haka take kaman ƴarata kam dole zai jauce akan ta,haka suke da ƙira kaman su sukayi kansu"
"Zakuwa mu sanja mata kamanni,ke nifah na tsani ƴar nan,menene bamu gani ba a wajen baban hajjo akan ta,indai wannan karon bata bar gidannan ba to kuwa zamuyi babban shiri,in ma Deejah ce yanzu takeson kareta to da ita zamu haɗa..........."
Bangama jin mummunan labarin da suke ba na sulale a wajen,saboda yanda ƙafafuna suke rawa bazan iya gama ji ba sam.
Hawayene kawai yake zirara a idona,yayinda dukkan wani abu dayake amfani a cikina ya dauƙi yajin aiki na wasu daƙiƙu.
Tun inajin hayaniyarsu da shewarsu har na daina ji da alama sun bar wajen,na daɗe ina zargin mutanen gidannan namu basu san Allah ba,amma yau kam na tabbatar.
Gari yafara haske asuba ta gabato,kafin na bar wajen na nufi ɗakinmu,ikon Allah ne kaɗai ya kaini ɗakin.
Dana kwanta ma ba bacci nayi ba,zuru nayi har assalatu tayi.
Ɗankwalin danake yin sallah dashi na ɗauka na fita daga ɗakin zuwa inda nake sallah,a canne ƙofar wani baban yayanmu wanda yagina ƙofarsa amma bayyi aureba,a wajen nakeyin sallah,saboda ɗakinmu kam nasan bazzayi sallah ba.
Bayan na idar da sallahr na daɗe ina roƙon Allah kaman yanda na saba,yau kam banyi karatun Ƙur'ani dayawa ba,saboda yanda bacci ke fizgata,ban samu damar komawa ɗakiba anan bacci yayi gaba dani.
Zafin rana ne yafara cin ƙafafuna,hakanne yasa na tashi na zauna,safiya tayi ashe har rana tafito bansani ba.
Ajiyar zuciya nayi dan ma yau banice dayin wanke wanke ba,shara kawai zanyi sai ɗora abincin siyarwar ammi. Dan haka cikin nutsuwa na tashi na ninke abin sallahr tawa zan bar ƙofar.
Motsin mutum naji hakanne yasa na ɗaga idona.
Da yaya Musbahu na haɗa ido yana tsaye yana kallona.
Rusunawa nayi na gaisheshi,yanada mutunci shikam sosai,dan ko hayaniyar gidan bata wani dameshi ba,shine babban ɗan ammi,yayi diploma yana koyarwa a makarantar secondry ta garin.
"Sumaimah lafiya kikazo nan kina bacci,na dawo daga sallah naga kinyi bacci anan"
"Ahh bakomai kawai baccinne ya ɗan daukeni"
"Ohh toh,kiyi haƙurifah da abinda baba yayi miki kinji,in kika jure komai zai wuce kinji,yau ma nayi masa maganar a masallaci, amma sai ya hauni da faɗa,kuma jiya da mukayi masa magana yace zai bashi kuɗin yafasa aura miki shi,amma kuma yau da asuba ya dage sai ya aura miki shi,abin yabani mamaki"
Idon ne ya cicciko lokacin danaji abinda yaya Musbahu yace,maganar dasu inna rammah sukayi jiyace ta faɗo min araina,wato su yayah Musbahu ne suka tausheshi akan aurar dani ga wancan dodon,har ya yarda su kuma waɗannan matan suka sake juyar da kansa.
Saurin share hawayen idona nayi tareda jijjiga masa kai.
"Babu komai yah Musbahu in hakan shine ƙaddarata banida zabi illah na rungumeta,dama dolene bawa yayarda da ƙaddara mai kyau ko kuma akacin haka.
Har nazo fita daga ƙofar tasa yasake yimin magana.
"Kije ammi tana ta nemanki kinji,ga wannan kuma ki boye ki dunga siyan koko,an bani albashina jiyah"
Yafaɗa yana miƙomin naira ɗari biyar.
Wani kukane ya tahomin lokacin dana saka hannu na karba,wannan karon ban tare shi ba nayita kunza kayana,tun yana rarrashi na har yabari yabar ƙofar.
Allah ne kaɗai yasan yanda nake ƙaunarsa a cikin yan uwannanwa,da kuma yanda yake birgeni,shikam ya fita zakkah a gidannan.
Harna isa ƙofar ammi ina kwarara masa ruwan Addu'a ta samun nasara a raina,Allah ya haɗashi da mace tagari ba irin matan gidannan ba,dan daga kan iyayen har surukan kaman an cuɗasu an rabasu haka suke.
A baranda na sameta tana tsince shinkafar daza'a dafa in anjima,wajen kaca kaca da miyar tuwo da kuma kunu,ina yara suka zuzzubar lokacin da suka karya.
Gaisheta nayi kafin na leƙa ɗakin inna rammah mah. Tanata masifah da yaranta suna rashin ji.
Fuskarta dauke da murmushi da amsamin,kaman ba itace ta gama faɗin kalaman da mutumin dayasan zai mutu bai kamata ya furta ba.
Tuwo nah na ɗauka naci nakai kwanon wajen wanke wanke.
Bishirah da asiyah ne suke wanke wanken,ƴar rammah da kuma ammi.
Harara ta Bishirah tayi dana ajiye kwanon cikeda tsiwa.
"Wai mutum bazai ci abinci da wuri ba dan mulki,sai an kusa gama wanke wanke ya kawo kwano"
Kunnenta na riƙe ta bangaren danake,dan abin yayimim ciwo,yarinyar da in auren shekara sha biyu zanyi saina kusa haifarta take faɗamin wannan maganar.
"Ke wato kin iya rashin kunya koh,yaushene ma kuke wanke wanken,naga saikuyi sati bakuyi ba nina ke,dan an fara baku shine har kun fara tsiya koh?"
Maganar inna rammah najiyo daga bakin ɗakinta lokacin da Bishirah ta kwanɗa ihu kaman ina zare mata rai.
"Sake mata kunne to ƴar gadon marasa mutunci,baƙin cikin menene haka da har zaki cire mata kunne,so kike ki nakasata tayi zaman gida kaman ke?"
Sakin kunnennan ta nayi,yayinda maganganunta kemin zafi a rai,kallon baki isheni ba nayi mata kafin na ɗau tsintsiya na fita share harabar ƙofar tamu,duk abinta dai nasan bazata dakeni ba,da dai ta dakeni komai ma tayimin,amma yanzu na wuce duka,saidai tayi min muguntar boye ta asiri.
Abinda yafarune ma ya faɗomin a rai,hakanne yasa na nufi kewayen dabbobin kaman da niyyar cewa shara zanyi.
Akan wajen da sukayi binne binnen idona ya sauƙa,tabbas kam ba mafarki nake ba..
Jan lilon ƙafafuna nayi zuwa wajen,tsugunnawa nayi idon kyam akan abinda ƙarfi da yaji yakeson rabani da gidanmu.
Harna saka hannun zan tone wajen saikuma na tuna maganganunsu,wataƙila inna tone asirinnan ya karye baba yagane kuskuren da yayi a caca,har ya nemi kin auramin goje,to amma su inna rammah fah,zasu barni na cigaba da zama harna samu miji daidai dani nayi aure. Tabbas ba karamin aikinsu bane su aikata abinda sukayi iƙirarin faɗa.
Inkuma yanda suka fada dagskene na tarewa ƴaƴansu farin jininsu wanda nasan bokane yafadamusu dan ya ci kudinsu,toh zan tursasa ammi sake cutar dani muddin akan ƴar tane Asiyah.
Wanda hakan zai zama abune da bazanso ya kasance ba.
Maida kasar dana fara tonewa nayi na binne wajen cikin sanyin jiki,na zabi barin gidan kawai,koma mai zaimin yayimin Allah ne ke riƙeda rai na ai,wuya kuwa bata kisa sai kwana yaƙare.
Tashi nayi na barbaje ƙasar tareda fara share wajen,banyi niyya ba amma inna ƙiyi kar suyi tunanin naga abinda sukayi jiyan.
Wannan wace irin rayuwa ce,ace wai aisiri akayi maka amma ka ƙwammaci ka barshi ya hau kanka......ke duniyah.
Littafi na ɗaya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na ɗaya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.
3131951977
Auwal Sadiya
First bank
Ko katin mtn ta nan
09035784150
VTU ta nan
2347068390570
Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------
Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please*SANADIN CACA*
Mallakar SADI-SAKHNA
PROFICIENT WRITER ASSOCIATION
*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
_Wannan shafin Sadaukarwa ga *Real gudaliyah* chief admin da ƙungiyar zafafah,nagode sosai sosai. Dama sauran masu nuna soyayya ga littafina ina godiya sosai._
________________________________
*Book 1*
Chp[04]
Saida ya daidaita hasken a cikin idonsa kafin ya buɗe idon dukka. A kwance yake a inda ya suma jiya,wato cikin bukkar,yunƙurawa yayi babu salati bare godiya ga Allah.
Kakkaɗe jikinsa yayi daga ƙurar dayayi kafin ya fito daga cikin bukkar yayi wata miƙa.
Ido ya haɗa da karnuka guda uku,murtuƙa murtuƙa a kwance a filin wajen,suna kallon ya fito suka nufi inda yake.
Feɗuwa yayi dukka suka amsa masa kaman sunji mai yace.
Hanyar dazata kaishi cikin gari ya nufah kansa tsaye yana tafe suna take masa baya,yanda yake baƙi fuskarnan duk gashi haka suma suke.
Duk hanyar dayabi yara matsawa suke harda samari.
A wajen mai shayin unguwarsu ya zauna akan benci,su kuma karnukan suka tsaya a bayansa kaman wasu fadawa.
"Kai iliyah yiyomin haɗin shayinnan da kake min,kaga na juyeshi a cikina nan"
Dama murya a shaqe,ta kuma haɗu da tashi a bacci,banda hamami babu abinda yake,amma hakan ko kaɗan bai dameshi ba,haka wanda yake gefensa ma ko mai zayyi bai isa yace ya dame shin ba.
Ido suka haɗa da Iliyah wanda yake ta aikin juyah shayi daga wannan kofin zuwa wannan.
"Amma goje na wata biyar fah ya taru akan ka ko ƙwandala baka rage ba"
"To dolene saina rage koda banni da kuɗi iyee,kai akan shayin zaka dunga tsayarmin,idan bazaka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2 Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21