“Saboda me to zaki bada hakuri tunda kinsan bakiyi laifi ba?”ya fad’a a fusace yana qoqarin zare hannunsa cikin nata tayi saurin rikewa tana shagwabe masa “yanzu akan maryama zaka canza min “.ba akanta bane akan kalmar hauka ne banason kina kiranta da kalmar hauka domin ke kanki kinsan babu alamar haka a attare daita “naji kayi hakuri bazan sake ba shiru yayi mata yaki cewa komai “haba mana my heart ka saki ranka mana wallahi idan kana nuna min haka sai naji kamar kana sonta ne “ta qarasa mgnr tana kwanto masa ajiki numfashi ya sauke tare da cewa “shikenan naji naji !! ta dan dago daga jiknsa tana kallonsa “to kayi min murmushi .”
murmushin takaici yayi itama dai murmushin tayi kana ta cigaba da magana “ga dukkanin alamu company ata sun nuna zan samu aiki da company dan nasan tunda suka d’aukeni dole zaa sake nemana still dai shiru sadam yayi sannan yayi kicin kicin da fuskarsa “my heart!”ta kirasa bai amsa mata ba amma hakan bai sa ta damu ba ta cigaba da maganarta “da zarar na samu aiki kudi zasu samu kenan ,da zarar mun samu kudi zamu bar wannan wajen ko ba haka ba ?”shiru dai yayi mata .”
ta numfasa tare da gyara zamanta “what’s our next plan my heart ?”stil dai shiru yayi dan shi baya jin zai wani barta tayi aiki da wannan kamafanin “my heart kamin magana mana ?”tai maganar tana kai hannunta sansar jikinsa “ba batun samun kudi bane damuwatq dan banason Kiyi aiki a wannan kamfanin ,domin ina son muyi nisa da nan ne mu qara gaba muje inda babu wanda zai ganmu ko wanda ya sanmu far away from everyone “.and far away from maryama ba ..”ta fad’a tana tsarke yatsun hannunsu tare da rungumesa ajikinta” amman kuma duk wannan abun daka lissafa suna bukatar kudi “karki damu zamu samu kudi qasar ma zamu bari gbdy dan haka kar na sake jin batun zakiyi aiki da wannan kamfanin matsawar kina son ki cigaba da ganina a tare dake ko kuma yuwar aurenmu dan kina sake tada maganar aiki da wannan kamfani wallahi na fasa aurenki .”sake rungumeshi tayi tsam ajikinta tana shakar qamshin jikinsa.”shikenan naji duk abinda kace shi zanyi.”
*****
Qarfe takwas da wasu ‘yan mintuna motar mr ata ta qaraso titin capitor sakamakon hoodop din da suka iske akan hanyarsu ahankali suka shigo unguwarsu maryama ,direba ya samu waje a gefen titi yayi parking ya fito daga cikin motar ya rufe murfin mota yayi gaba kad’an abunsa inda mr ata ya maida kwayar idanunshi kan maryama still yana rike da yatsunta hannunta muryarsa a kasalance ya kira sunanta “maryama .”!
bata amsa ba sai dai ta waigo inda yake zaune tana kallonsa tana kallon yadda yake ciza lips dinsa ,gefe guda kuma tana jin sauyi a sansar jikinta sakamakon hannunta dake cikin nashi sosai ya sanya kwayar idanunshi cikin nata duk da babu wani wadataccen haske acikin motar amman tana jin kwayar idanunshi ajikinta ta Lumshe idanunta hasken wayarsa ya kunna ya haska fuskarta ya tsurawa fusakr ido yaga yadda idanunta suka kumbura sukai wani irin girma fuskarta tayi jajir .”cikin wani irin yanayi yake kureta da kallonshi kafin yaja ajiyar zuciya ya sauke sosai ya kwantar da muryarsa“ya kike jin zuciyarki yanzu ?”kina jin damuwa har yanzu ?yayi mata tambayar ajere sai data had’iye wani abu daya tsaya mata a makoshi kana ta soma magana a natse “ban ta’ba tunani cewar cikin lokacin kankani irin wannan zai sa naji damuwata ta wattanni sun gushe ba ,ta qarasa magana muryarta da alamun son yin kuka “wallahi naji relief sosai amman hakan bazai sa na iya mantawa da d’anuwana ba “ta qarasa maganar tana runtse idanunta “maryama wannan duk mai sauki ne akan ki cigaba da rainon soyayyar matace acikin zuciyarki ,sannan rage damuwar zai sa ki cigaba da rayuwarki cikin salama kamar kowa ,forget your past and leave your present “ko kin fahimci abinda nake nufi.”
“naji zanyi duk abinda kace kuma naji dadin gudumuwar daka bani dan ka taimakeni kuma naji dadi sosai “maryama kin yarda sosai da wannan mutumin kuma ina ji a zuciyata har yanzu akwai wani space da kika bashi acikin zuciyarki “wannan haka ne ban ta’ba jin na yarda da wani halitta kamar yaya sadam ba amman ta yaya kasan har yanzu sadam yana da sauran space acikin zucyta?”shiru yayi kawai yana kallonta yana jin wani iri acikin ranshi “sir !”mai yasa kayi shiru kana kallona ?still dai shiru ya cigaba dayi yana cigaba da kallonta zuciyarsa cike da zallar kishi “sir me kake tunani ?bai ce mata komai ba illa ya runtse idanushi “amman nace sir yaakayi kasan cewar idan nayi kuka irin na yau zanji relief ?”ya sake damke yatsunta da karfi tare da sake runtse idanunshi gam “sir ko kai ma ka ta’ba tsintar kanka cikin irin yanayin dana tsinci kaina ne ?”shiru yayi kawai yana tunanin irin rayuwar wahalar da yayi akanta wacce bazai ta’ba mantawa ba “bazai iya kirga sau adadi nawa ya sha giya akan zafin rashinta ba sigari kam ma baa maganarta bare kuma zubar hawayensa “.
“sir !sir !! ta sake kira sunansa ahankali har sau biyu ajere sakamakon ganin moond dinsa ya canza “sir me kake tunani ne ko maganata ta ’bata maka rai ne ?”no !”ya fad’a atakaice bata bata min rai ba amman abinda nake baqata dake ki goge wannan soyayyar dake binne a zuciyarki domin bawa wata soyayyar dama shiga rayuwarki yana gama fad’ar haka yace muje ko “.ta kasa fita daga cikin motar ta tsura masa idanunta tana tunanin abinda ya bata masa rai ganin ta kasa tuno wace kalma ce tai sanadiyyar canza masa mood dinsa taga gara kawai ta bashi hakuri sosai tayi kasa da muryarta “kayi hakuri .”!
“ba hakurinki nake bukata ba ki goge wannan banzar soyayyar shine abinda nafi buqata “naji zanyi qoqarin yin abinda ka buqata duk da hakan ba abu ne mai sauki agareni ba bayan halaccin ya sadam agareni umma ma abar dubawa ce taso ni ada baya can kuma har a yanzu tana qauna ,ta bani dukkanin wani gata da kulawa tun ina qarama har zuwa girmana ,bata son damuwata yanzu haka tana can zaman jirana bata bacci matsawar bata ga shigowata ba tana girmamani kuma tana tsananin sona zatai iya yin komai akaina “the most special thing in this world to me is my special mumy wato umma wannan yana daga cikin dalilin da yasa cire ya sadam araina zai yi matukar wahala agareni dan umma bazata iya ciresa a rayuwarta ba amman zanyi qoqarin ragewa da fatan bazaka damu da jin haka ba ?”ta qarasa maganar tana kallon yatsun hannunsu dake tsake cikin juna.”
Numfashi ya sauke yana cewa “is okay na fahimceki” na gode sosai Allah ya biya maka bukatunka na alkhairi a kasan zuciyarsa ya amsa da” ameen!”tana qoqarin fitowa daga cikin motar kira ya shigo wayarta ahankali ta koma ta zauna tare da ciro wayarta sunan umma ta gani yana yawo akan screen din wayar da sauri taja koren maddani tana qoqarin kai wayar kunnenta ya rike tsintsitar hannunta tare da saka wayar a hands free “maryama kina ne ?”kiyi maza ki qaraso gida yau alkubus nayi mana nasan zakiji dadi sosai”kyakkywan murmushi ne ya bayyana akan fuskar maryama sannan tace “sosai kuwa umma nah gani nan yanzu zan shigo ,to shikenan kiyi sauri kinsan idan yayi sanyi bashi da dadin ci” umma ta fad’a cike da kulawa “yanzu nan zaki ganni ummata sai kin shigo umma ta fad’a tana katse kiran inda maryama ta kalli mr ata fuskarta da bayyananne murmushi “tabbas ya yarda matar na tsananin sonta wanda hakan yasa yaji zuciyarsa ta dan bata wani matsugune acikinta har bakin get din gidansu ya rakota sai daya ga shigarta sannan ya juya ya wuce gida .”
Ahankali ya shigo parlour mami ya ajiye yar saman suit dinsa akan hannun kujera idanunshi na kan mami dake tsaye ta d’ago ta kallesa a natse kafin ahankali ta qaraso zuwa inda yake ta tsaya tana tambayarsa”lafiyarka meke faruwa na ganka haka ?”shiru yayi kawai yana hura hanci tasan halinsa a duk sanda yayi haka baya bukatar acigaba da damunsa akan abu “ ka qarasa d’akin ka kayi wanka kazo kaci abinci kanshi kawai ya gyada sannan ahankali ya zagayeta ya haye sama bayan wasu mintuna mami taji shiru bai sauko ba ta nufi dakinsa a zaune ta iskeshi shiru cikin yanayi na tsananin tunani ta zauna kusa dashi “wai meke damunka ne “?ta tamabyesa cike da kulawa “babu abinda ke damuna sweetheart ko kina tunanin akwai abinda zan iya boyewa kyakkywar mahaifiyata ?”harara shi tayi tana cewa ”akwai mana sau nawa ina tambayarka abu kace min babu komai alhalin kuma ni nasan da komai din .”shiru yayi batare da yace uffan ba “nifa nasan halin d’ana,nasan yanayinsa kuma nasan yanayin damuwarsa kawai dai ka fad’a min “ya kamo yatsun hannunta cikin nashi yana cewa “babu komai sweetheart just believe me, I can’t believe you adamcy amman dai me kake son kaci muna da rice and stew da farfesun kan rago muna da tuwon semoveter da miyar danyar kubewa da cat fish, muna da light soup daakayi mix dinsa da kan rago da kayan ciki da busashen kifi muna da ..” sweetheart alkubus zanci .”
“ alkubus zaka ci bayan shekaru masu yawa rabon daka ci “?“yes shi zanci sweetheart ya fad’a yana lunshe mata tsumammun idanunshi shiru tayi kawai tana kallonsa ,kin bude idanunshi yayi saboda gabadaya jinsa yake acikin wani iri yanayin kamar ya yi kuka ko ya samu salama a zuciyarsa da Kyar ya bude idanunshi sakamakon jin shirun mami “kiyi hakuri sweetheart nasan bazan samu ba “babu wannan ranar da d’ana zai ce ga abinda zai ci ni kuma na kasa masa tayi maganar kamar zatai kuka “na dade ina expecting haka kullum burina naji kace zakaci abinci da mahaifinka yafi so shiyasa naji maganar wani iri”bari naje nayi maka just ka bani lokaci kad’an yanzu zanje nayi maka alkubus “ ta mike ta fita da sauri tana goge gutun hawayen daya cika gefen idanunta.”
“Kai umma qamshi allubus din ya cika koina agidan nan ,da gaske maryma?allah kuwa barin ma qamshin miyar maza maza kije kiyi fresh up kizo kici tun kafin yayi sanyi “okay umma ta fad’a tare da nufar hanyar dakinta da sauri .” bangaren mr ata zaune suke shi da mami akan gado tana bashi alkubus abaki “sweetheart !”bata amsa ba ta tsaya tana kallonsa me kike tunani haka ?”ina tunanin wasu abubuwa da suka gabata ne sannna kuma ina kallon kyakkywan d’ana .”sweetheart ki daina dogon tunani haka kinji kin rasa abba amman kuma kina damu biyar ina son ganinki cikin farinciki’ “uhm ta furta a kasan ranta sannan ta soma mgn “kana son ganina cikin farinciki amman zuciyarka ta kasa amsar zabina kuma farin cikina ?”tayi maganar cike da rauni ina tsananin jin tausayin maryam” yanzu haka nata rayuwar zai kare cikin rashin jin dadin rayuwa?mai yasa adam?ni abinda nake so kuma yafi komai mahimanci arayuwata shine ka yarda ka kuma amince da cewar cikin jikinta naka ne kuma zaka so shi kamar yadda naka uban ya soka ya kuma nuna maka gata ,ina son naga murmu shi akan fuskar maryam I just want to see the smile on her face .”shiru yayi yana kallonta kafin ahankali ya motsa lips dinsa “sweetheart kin kasa fahimtar zuciyar adamcy dinki abinda bazai ta’ba yuwa bane is not possible na amince …”
Cak zuciyar mami ta tsaya ta daina bugawa yadda ya kamata tare da zuba masa idanunta” ki rabu da damuwar yarinyar nan kawai ta girbi abinda ta shuka dan Allah sweetheart ki bar min maganarta ,ki barni a yadda na tsaida zuciyata shiru ne ya biyo baya kafin ahankali ta cigaba da motsa labbanta “batun wacan yarinyar fa ?”yayi shiru kawai yana dubanta fuskarsa da alamun tambaya “wacan yarinyar data shigo rayuwarka nake nufi ko ..”ko itama bazaka ce wani abu akanta ba ka kawo min ita ni zan fad’a mata cewar kana sonta kuma nasan zata fahimceni ina son naga ka zama cikakken mutun adamcy duk da kai baka bin umarnina ni zan maka komai amatsayina na uwa zan baka farinciki daka qasa bani saboda tsnanin son da nake maka ta qarasa maganar kamar zatai kuka “tunda naji zuciyata tana son ganin yarinyar tabbas rayuwar adamcy nace .”shiru yayi kawai tare da zuba mata idanunshi yana shafa fuskashi da tafin hannunsa yana tunain maganganun maryama wanda har lokacin zuciyarta tana ga wani ,gabansa ne ya dinga bugawa da qarfi “sweetheart karki damu maryama zatazo ta ganki “
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
39
Ahankali ATA yake kallonta cike da tsananin shaukin qaunarta yayinda cike da yanayi na tsananin damuwa yaga ta janyo gefen mayafinta tana goge hawayen dake fita daga cikin kwarnin idanunta ganin hawaye take zubarwa hakan ya sake kunno wutar damuwarsa”oh my goodness god !”yanzu menene abun kuka kuma ?” ya furta a fili yana mai runtse tsumammun idanunshi tare da Jin wani irin tausayinta na ratsa tsantsar jikinsa “why zanji tausayinta bayan ni ne abun tausayi? ya furta yana jan tsaki sannan ya Kai hannunsa ya dafe saman goshinsa yana murzawa yana jin wani irin zafi da ciwo yayinda zuciyarsa ta dinga tuttukin bakinciki”why maryama!”? “mai yasa baza ki fahimci irin zunzu runtun qaunar da nake miki ba?”kusan minti shabiyar yana tsaye zuciyarsa na jin rad’adin azabar rashin son data furta masa yanzu, kafin ahankali ya bud’e idanunshi ya tsura mata daga inda yake har lokacin tana zaune tana janyo numfashi da kyar.”yayi shiru tare da tura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa yana taku acikin office din ,wani tunani yayi dan haka nan take ya soma taku ahankali ya qaraso zuwa bakin kofar office dinsu ya tsaya tare da rike kugunsa yayinda kwayar idanunshi ke yawo a sansar jikinta ”
“qamshin turarensa daya kawowa hancinta ziyara ne yasa ta sauke wani naunauyen ajiyar zuciya ,sai dai ta qara sunkuyar da kanta qasa tana kallonsa tsaye a bakin kofar shigowa shi bai shigo ciki ba shi bai juya ya wuce ba, wanda hakan yayi sanadiyyar da gaban ta ya dinga dokawa da qarfi gefe guda kuma ta dinga jin wani sabon tashin hankali from know where yana shigarta.” ahankali take hango tahowarsa zuwa inda take zaune gabanta ne ya cigaba da lugud’en bugu tana zaune har ya iso inda take ya tsaya kyam yana kallonta tamkar ranar ya fara ganinta .”
d’ago kanta tayi tana mai mikewa tsaye da sauri tare da goge hawayen idanunta ,bai ce mata uffan ba illa tsumammun idanunshi daya zuba mata tamkar zai cinyeta wanda yasa nan take numfashinta ya dinga sauka da sauri sauri ta tsarke yatsun hannunta cikin juna tana sake jin mummunar fad’uwar gaba mai tsanani, bata san dalili ba amman kwata kwata bata son ganin yanayinsa haka domin yanayi ne dake matukar d’aga mata hankali da tsorata zuciya da gangar jikinta.”
tsurawa juna ido sukai na second goma kafin ahankali ata ya janye kwayar idanunshi akanta yana mai shafa sumar kanshi ,wani abu yaji yana tsarga masa tun daga tsakiyar kanshi har zuwa yatsun qafafun sa,ganin har loakcin kuka take wanda shi aganinsa shi ya kamaci yayi mata kuka saka makon mahaukacin soyayyarta dake huda duk wani sansar na jikinsa .”cikin wani irin sauri zuciyarsa yake bugawa kamar zata fito daga cikin qirjinsa nan take tausayin kanshi ya kama shi bai san sanda ya buga mata wani razanannen tsawa tare da furta “enough maryama !” nan take kukan da take ya tsaya cak sai shesheka “bana son jin sautin sheshekar kukan !”nan take shima ta had’iye jikinta na wani irin rawa, yanayinsa ya qara mata jin tsorasa “. matsota yayi sosai sukai mugun daf da juna da sauri ta d’auke numfa shi ,da zai qara taku guda tak to lallai zasu had’e cikin juna “maryama !”ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya mai matuqar ratsa zuciya “kasa amsawa tayi ila ta kame jikinta waje d’aya tana mai sake sunkuyar da kanta had’e da tattaro jarumta ta sanyawa jikinta“I don’t want to see your tears .”da sauri ta d’ago kanta ,a natse ta zuba masa shayayyun idanunta still akwai ruwan hawaye acikinsu “ki goge hawayen nan ki kuma saki fuskarki .” ido cikin ido take kallonta ko kifta idanunta batayi,shima bangaresna kallonta yake yana faman busa mata hucin numfashinsa.”
Ta dinga jin kamar ta barshi ta kama gabanta amman kuma Tana tsananin jin tsoron abinda zai biyo baya dan a kallon da take masa zai iya aikata komai “smile !” ta jiyo fitowar sautin daga bakinsa.a d’an rikice take kallonsa batare da tayi abinda ya bukata ba “nace kiyi dariya”! Dan banason ganin wannan yanayin akan fuskarki “gaba daya maryama ta rud’e ta gigice tana kallonsa da sabon mamaki akan fuskarta “nace kiyi dariya !”wannan karon a fusace yayi maganar batasan sanda ta soma murmushin yake ba wanda ya bayyana d’an murmushin a saman lebbansa yayinda idanunshi ke kanta .”
Ganin irin kallon da yake mata yasa ta janye jikinta tana cigaba da murmushin data saka masa sunah “gashi karka kasheni a natse tabi gefensa ta wuce tana taku a natse ,ya tsura ma bayanta ido yana kallonta tana taku ahankali ,wani naunauyen ajiyar zuciya ya sauke kai tsaye office dinsa ta nufa ta duka ta d’auki jakarta ta fito ta nufi hanyar fita, tafiya kad’an tayi ya
Showing 129001 words to 132000 words out of 176292 words
“Saboda me to zaki bada hakuri tunda kinsan bakiyi laifi ba?”ya fad’a a fusace yana qoqarin zare hannunsa cikin nata tayi saurin rikewa tana shagwabe masa “yanzu akan maryama zaka canza min “.ba akanta bane akan kalmar hauka ne banason kina kiranta da kalmar hauka domin ke kanki kinsan babu alamar haka a attare daita “naji kayi hakuri bazan sake ba shiru yayi mata yaki cewa komai “haba mana my heart ka saki ranka mana wallahi idan kana nuna min haka sai naji kamar kana sonta ne “ta qarasa mgnr tana kwanto masa ajiki numfashi ya sauke tare da cewa “shikenan naji naji !! ta dan dago daga jiknsa tana kallonsa “to kayi min murmushi .”
murmushin takaici yayi itama dai murmushin tayi kana ta cigaba da magana “ga dukkanin alamu company ata sun nuna zan samu aiki da company dan nasan tunda suka d’aukeni dole zaa sake nemana still dai shiru sadam yayi sannan yayi kicin kicin da fuskarsa “my heart!”ta kirasa bai amsa mata ba amma hakan bai sa ta damu ba ta cigaba da maganarta “da zarar na samu aiki kudi zasu samu kenan ,da zarar mun samu kudi zamu bar wannan wajen ko ba haka ba ?”shiru dai yayi mata .”
ta numfasa tare da gyara zamanta “what’s our next plan my heart ?”stil dai shiru yayi dan shi baya jin zai wani barta tayi aiki da wannan kamafanin “my heart kamin magana mana ?”tai maganar tana kai hannunta sansar jikinsa “ba batun samun kudi bane damuwatq dan banason Kiyi aiki a wannan kamfanin ,domin ina son muyi nisa da nan ne mu qara gaba muje inda babu wanda zai ganmu ko wanda ya sanmu far away from everyone “.and far away from maryama ba ..”ta fad’a tana tsarke yatsun hannunsu tare da rungumesa ajikinta” amman kuma duk wannan abun daka lissafa suna bukatar kudi “karki damu zamu samu kudi qasar ma zamu bari gbdy dan haka kar na sake jin batun zakiyi aiki da wannan kamfanin matsawar kina son ki cigaba da ganina a tare dake ko kuma yuwar aurenmu dan kina sake tada maganar aiki da wannan kamfani wallahi na fasa aurenki .”sake rungumeshi tayi tsam ajikinta tana shakar qamshin jikinsa.”shikenan naji duk abinda kace shi zanyi.”
*****
Qarfe takwas da wasu ‘yan mintuna motar mr ata ta qaraso titin capitor sakamakon hoodop din da suka iske akan hanyarsu ahankali suka shigo unguwarsu maryama ,direba ya samu waje a gefen titi yayi parking ya fito daga cikin motar ya rufe murfin mota yayi gaba kad’an abunsa inda mr ata ya maida kwayar idanunshi kan maryama still yana rike da yatsunta hannunta muryarsa a kasalance ya kira sunanta “maryama .”!
bata amsa ba sai dai ta waigo inda yake zaune tana kallonsa tana kallon yadda yake ciza lips dinsa ,gefe guda kuma tana jin sauyi a sansar jikinta sakamakon hannunta dake cikin nashi sosai ya sanya kwayar idanunshi cikin nata duk da babu wani wadataccen haske acikin motar amman tana jin kwayar idanunshi ajikinta ta Lumshe idanunta hasken wayarsa ya kunna ya haska fuskarta ya tsurawa fusakr ido yaga yadda idanunta suka kumbura sukai wani irin girma fuskarta tayi jajir .”cikin wani irin yanayi yake kureta da kallonshi kafin yaja ajiyar zuciya ya sauke sosai ya kwantar da muryarsa“ya kike jin zuciyarki yanzu ?”kina jin damuwa har yanzu ?yayi mata tambayar ajere sai data had’iye wani abu daya tsaya mata a makoshi kana ta soma magana a natse “ban ta’ba tunani cewar cikin lokacin kankani irin wannan zai sa naji damuwata ta wattanni sun gushe ba ,ta qarasa magana muryarta da alamun son yin kuka “wallahi naji relief sosai amman hakan bazai sa na iya mantawa da d’anuwana ba “ta qarasa maganar tana runtse idanunta “maryama wannan duk mai sauki ne akan ki cigaba da rainon soyayyar matace acikin zuciyarki ,sannan rage damuwar zai sa ki cigaba da rayuwarki cikin salama kamar kowa ,forget your past and leave your present “ko kin fahimci abinda nake nufi.”
“naji zanyi duk abinda kace kuma naji dadin gudumuwar daka bani dan ka taimakeni kuma naji dadi sosai “maryama kin yarda sosai da wannan mutumin kuma ina ji a zuciyata har yanzu akwai wani space da kika bashi acikin zuciyarki “wannan haka ne ban ta’ba jin na yarda da wani halitta kamar yaya sadam ba amman ta yaya kasan har yanzu sadam yana da sauran space acikin zucyta?”shiru yayi kawai yana kallonta yana jin wani iri acikin ranshi “sir !”mai yasa kayi shiru kana kallona ?still dai shiru ya cigaba dayi yana cigaba da kallonta zuciyarsa cike da zallar kishi “sir me kake tunani ?bai ce mata komai ba illa ya runtse idanushi “amman nace sir yaakayi kasan cewar idan nayi kuka irin na yau zanji relief ?”ya sake damke yatsunta da karfi tare da sake runtse idanunshi gam “sir ko kai ma ka ta’ba tsintar kanka cikin irin yanayin dana tsinci kaina ne ?”shiru yayi kawai yana tunanin irin rayuwar wahalar da yayi akanta wacce bazai ta’ba mantawa ba “bazai iya kirga sau adadi nawa ya sha giya akan zafin rashinta ba sigari kam ma baa maganarta bare kuma zubar hawayensa “.
“sir !sir !! ta sake kira sunansa ahankali har sau biyu ajere sakamakon ganin moond dinsa ya canza “sir me kake tunani ne ko maganata ta ’bata maka rai ne ?”no !”ya fad’a atakaice bata bata min rai ba amman abinda nake baqata dake ki goge wannan soyayyar dake binne a zuciyarki domin bawa wata soyayyar dama shiga rayuwarki yana gama fad’ar haka yace muje ko “.ta kasa fita daga cikin motar ta tsura masa idanunta tana tunanin abinda ya bata masa rai ganin ta kasa tuno wace kalma ce tai sanadiyyar canza masa mood dinsa taga gara kawai ta bashi hakuri sosai tayi kasa da muryarta “kayi hakuri .”!
“ba hakurinki nake bukata ba ki goge wannan banzar soyayyar shine abinda nafi buqata “naji zanyi qoqarin yin abinda ka buqata duk da hakan ba abu ne mai sauki agareni ba bayan halaccin ya sadam agareni umma ma abar dubawa ce taso ni ada baya can kuma har a yanzu tana qauna ,ta bani dukkanin wani gata da kulawa tun ina qarama har zuwa girmana ,bata son damuwata yanzu haka tana can zaman jirana bata bacci matsawar bata ga shigowata ba tana girmamani kuma tana tsananin sona zatai iya yin komai akaina “the most special thing in this world to me is my special mumy wato umma wannan yana daga cikin dalilin da yasa cire ya sadam araina zai yi matukar wahala agareni dan umma bazata iya ciresa a rayuwarta ba amman zanyi qoqarin ragewa da fatan bazaka damu da jin haka ba ?”ta qarasa maganar tana kallon yatsun hannunsu dake tsake cikin juna.”
Numfashi ya sauke yana cewa “is okay na fahimceki” na gode sosai Allah ya biya maka bukatunka na alkhairi a kasan zuciyarsa ya amsa da” ameen!”tana qoqarin fitowa daga cikin motar kira ya shigo wayarta ahankali ta koma ta zauna tare da ciro wayarta sunan umma ta gani yana yawo akan screen din wayar da sauri taja koren maddani tana qoqarin kai wayar kunnenta ya rike tsintsitar hannunta tare da saka wayar a hands free “maryama kina ne ?”kiyi maza ki qaraso gida yau alkubus nayi mana nasan zakiji dadi sosai”kyakkywan murmushi ne ya bayyana akan fuskar maryama sannan tace “sosai kuwa umma nah gani nan yanzu zan shigo ,to shikenan kiyi sauri kinsan idan yayi sanyi bashi da dadin ci” umma ta fad’a cike da kulawa “yanzu nan zaki ganni ummata sai kin shigo umma ta fad’a tana katse kiran inda maryama ta kalli mr ata fuskarta da bayyananne murmushi “tabbas ya yarda matar na tsananin sonta wanda hakan yasa yaji zuciyarsa ta dan bata wani matsugune acikinta har bakin get din gidansu ya rakota sai daya ga shigarta sannan ya juya ya wuce gida .”
Ahankali ya shigo parlour mami ya ajiye yar saman suit dinsa akan hannun kujera idanunshi na kan mami dake tsaye ta d’ago ta kallesa a natse kafin ahankali ta qaraso zuwa inda yake ta tsaya tana tambayarsa”lafiyarka meke faruwa na ganka haka ?”shiru yayi kawai yana hura hanci tasan halinsa a duk sanda yayi haka baya bukatar acigaba da damunsa akan abu “ ka qarasa d’akin ka kayi wanka kazo kaci abinci kanshi kawai ya gyada sannan ahankali ya zagayeta ya haye sama bayan wasu mintuna mami taji shiru bai sauko ba ta nufi dakinsa a zaune ta iskeshi shiru cikin yanayi na tsananin tunani ta zauna kusa dashi “wai meke damunka ne “?ta tamabyesa cike da kulawa “babu abinda ke damuna sweetheart ko kina tunanin akwai abinda zan iya boyewa kyakkywar mahaifiyata ?”harara shi tayi tana cewa ”akwai mana sau nawa ina tambayarka abu kace min babu komai alhalin kuma ni nasan da komai din .”shiru yayi batare da yace uffan ba “nifa nasan halin d’ana,nasan yanayinsa kuma nasan yanayin damuwarsa kawai dai ka fad’a min “ya kamo yatsun hannunta cikin nashi yana cewa “babu komai sweetheart just believe me, I can’t believe you adamcy amman dai me kake son kaci muna da rice and stew da farfesun kan rago muna da tuwon semoveter da miyar danyar kubewa da cat fish, muna da light soup daakayi mix dinsa da kan rago da kayan ciki da busashen kifi muna da ..” sweetheart alkubus zanci .”
“ alkubus zaka ci bayan shekaru masu yawa rabon daka ci “?“yes shi zanci sweetheart ya fad’a yana lunshe mata tsumammun idanunshi shiru tayi kawai tana kallonsa ,kin bude idanunshi yayi saboda gabadaya jinsa yake acikin wani iri yanayin kamar ya yi kuka ko ya samu salama a zuciyarsa da Kyar ya bude idanunshi sakamakon jin shirun mami “kiyi hakuri sweetheart nasan bazan samu ba “babu wannan ranar da d’ana zai ce ga abinda zai ci ni kuma na kasa masa tayi maganar kamar zatai kuka “na dade ina expecting haka kullum burina naji kace zakaci abinci da mahaifinka yafi so shiyasa naji maganar wani iri”bari naje nayi maka just ka bani lokaci kad’an yanzu zanje nayi maka alkubus “ ta mike ta fita da sauri tana goge gutun hawayen daya cika gefen idanunta.”
“Kai umma qamshi allubus din ya cika koina agidan nan ,da gaske maryma?allah kuwa barin ma qamshin miyar maza maza kije kiyi fresh up kizo kici tun kafin yayi sanyi “okay umma ta fad’a tare da nufar hanyar dakinta da sauri .” bangaren mr ata zaune suke shi da mami akan gado tana bashi alkubus abaki “sweetheart !”bata amsa ba ta tsaya tana kallonsa me kike tunani haka ?”ina tunanin wasu abubuwa da suka gabata ne sannna kuma ina kallon kyakkywan d’ana .”sweetheart ki daina dogon tunani haka kinji kin rasa abba amman kuma kina damu biyar ina son ganinki cikin farinciki’ “uhm ta furta a kasan ranta sannan ta soma mgn “kana son ganina cikin farinciki amman zuciyarka ta kasa amsar zabina kuma farin cikina ?”tayi maganar cike da rauni ina tsananin jin tausayin maryam” yanzu haka nata rayuwar zai kare cikin rashin jin dadin rayuwa?mai yasa adam?ni abinda nake so kuma yafi komai mahimanci arayuwata shine ka yarda ka kuma amince da cewar cikin jikinta naka ne kuma zaka so shi kamar yadda naka uban ya soka ya kuma nuna maka gata ,ina son naga murmu shi akan fuskar maryam I just want to see the smile on her face .”shiru yayi yana kallonta kafin ahankali ya motsa lips dinsa “sweetheart kin kasa fahimtar zuciyar adamcy dinki abinda bazai ta’ba yuwa bane is not possible na amince …”
Cak zuciyar mami ta tsaya ta daina bugawa yadda ya kamata tare da zuba masa idanunta” ki rabu da damuwar yarinyar nan kawai ta girbi abinda ta shuka dan Allah sweetheart ki bar min maganarta ,ki barni a yadda na tsaida zuciyata shiru ne ya biyo baya kafin ahankali ta cigaba da motsa labbanta “batun wacan yarinyar fa ?”yayi shiru kawai yana dubanta fuskarsa da alamun tambaya “wacan yarinyar data shigo rayuwarka nake nufi ko ..”ko itama bazaka ce wani abu akanta ba ka kawo min ita ni zan fad’a mata cewar kana sonta kuma nasan zata fahimceni ina son naga ka zama cikakken mutun adamcy duk da kai baka bin umarnina ni zan maka komai amatsayina na uwa zan baka farinciki daka qasa bani saboda tsnanin son da nake maka ta qarasa maganar kamar zatai kuka “tunda naji zuciyata tana son ganin yarinyar tabbas rayuwar adamcy nace .”shiru yayi kawai tare da zuba mata idanunshi yana shafa fuskashi da tafin hannunsa yana tunain maganganun maryama wanda har lokacin zuciyarta tana ga wani ,gabansa ne ya dinga bugawa da qarfi “sweetheart karki damu maryama zatazo ta ganki “
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
39
Ahankali ATA yake kallonta cike da tsananin shaukin qaunarta yayinda cike da yanayi na tsananin damuwa yaga ta janyo gefen mayafinta tana goge hawayen dake fita daga cikin kwarnin idanunta ganin hawaye take zubarwa hakan ya sake kunno wutar damuwarsa”oh my goodness god !”yanzu menene abun kuka kuma ?” ya furta a fili yana mai runtse tsumammun idanunshi tare da Jin wani irin tausayinta na ratsa tsantsar jikinsa “why zanji tausayinta bayan ni ne abun tausayi? ya furta yana jan tsaki sannan ya Kai hannunsa ya dafe saman goshinsa yana murzawa yana jin wani irin zafi da ciwo yayinda zuciyarsa ta dinga tuttukin bakinciki”why maryama!”? “mai yasa baza ki fahimci irin zunzu runtun qaunar da nake miki ba?”kusan minti shabiyar yana tsaye zuciyarsa na jin rad’adin azabar rashin son data furta masa yanzu, kafin ahankali ya bud’e idanunshi ya tsura mata daga inda yake har lokacin tana zaune tana janyo numfashi da kyar.”yayi shiru tare da tura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa yana taku acikin office din ,wani tunani yayi dan haka nan take ya soma taku ahankali ya qaraso zuwa bakin kofar office dinsu ya tsaya tare da rike kugunsa yayinda kwayar idanunshi ke yawo a sansar jikinta ”
“qamshin turarensa daya kawowa hancinta ziyara ne yasa ta sauke wani naunauyen ajiyar zuciya ,sai dai ta qara sunkuyar da kanta qasa tana kallonsa tsaye a bakin kofar shigowa shi bai shigo ciki ba shi bai juya ya wuce ba, wanda hakan yayi sanadiyyar da gaban ta ya dinga dokawa da qarfi gefe guda kuma ta dinga jin wani sabon tashin hankali from know where yana shigarta.” ahankali take hango tahowarsa zuwa inda take zaune gabanta ne ya cigaba da lugud’en bugu tana zaune har ya iso inda take ya tsaya kyam yana kallonta tamkar ranar ya fara ganinta .”
d’ago kanta tayi tana mai mikewa tsaye da sauri tare da goge hawayen idanunta ,bai ce mata uffan ba illa tsumammun idanunshi daya zuba mata tamkar zai cinyeta wanda yasa nan take numfashinta ya dinga sauka da sauri sauri ta tsarke yatsun hannunta cikin juna tana sake jin mummunar fad’uwar gaba mai tsanani, bata san dalili ba amman kwata kwata bata son ganin yanayinsa haka domin yanayi ne dake matukar d’aga mata hankali da tsorata zuciya da gangar jikinta.”
tsurawa juna ido sukai na second goma kafin ahankali ata ya janye kwayar idanunshi akanta yana mai shafa sumar kanshi ,wani abu yaji yana tsarga masa tun daga tsakiyar kanshi har zuwa yatsun qafafun sa,ganin har loakcin kuka take wanda shi aganinsa shi ya kamaci yayi mata kuka saka makon mahaukacin soyayyarta dake huda duk wani sansar na jikinsa .”cikin wani irin sauri zuciyarsa yake bugawa kamar zata fito daga cikin qirjinsa nan take tausayin kanshi ya kama shi bai san sanda ya buga mata wani razanannen tsawa tare da furta “enough maryama !” nan take kukan da take ya tsaya cak sai shesheka “bana son jin sautin sheshekar kukan !”nan take shima ta had’iye jikinta na wani irin rawa, yanayinsa ya qara mata jin tsorasa “. matsota yayi sosai sukai mugun daf da juna da sauri ta d’auke numfa shi ,da zai qara taku guda tak to lallai zasu had’e cikin juna “maryama !”ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya mai matuqar ratsa zuciya “kasa amsawa tayi ila ta kame jikinta waje d’aya tana mai sake sunkuyar da kanta had’e da tattaro jarumta ta sanyawa jikinta“I don’t want to see your tears .”da sauri ta d’ago kanta ,a natse ta zuba masa shayayyun idanunta still akwai ruwan hawaye acikinsu “ki goge hawayen nan ki kuma saki fuskarki .” ido cikin ido take kallonta ko kifta idanunta batayi,shima bangaresna kallonta yake yana faman busa mata hucin numfashinsa.”
Ta dinga jin kamar ta barshi ta kama gabanta amman kuma Tana tsananin jin tsoron abinda zai biyo baya dan a kallon da take masa zai iya aikata komai “smile !” ta jiyo fitowar sautin daga bakinsa.a d’an rikice take kallonsa batare da tayi abinda ya bukata ba “nace kiyi dariya”! Dan banason ganin wannan yanayin akan fuskarki “gaba daya maryama ta rud’e ta gigice tana kallonsa da sabon mamaki akan fuskarta “nace kiyi dariya !”wannan karon a fusace yayi maganar batasan sanda ta soma murmushin yake ba wanda ya bayyana d’an murmushin a saman lebbansa yayinda idanunshi ke kanta .”
Ganin irin kallon da yake mata yasa ta janye jikinta tana cigaba da murmushin data saka masa sunah “gashi karka kasheni a natse tabi gefensa ta wuce tana taku a natse ,ya tsura ma bayanta ido yana kallonta tana taku ahankali ,wani naunauyen ajiyar zuciya ya sauke kai tsaye office dinsa ta nufa ta duka ta d’auki jakarta ta fito ta nufi hanyar fita, tafiya kad’an tayi ya
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44 Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59