,tayi zane taga baiyi ba ta dunkule ta yar da takardar ta sake bud’e wani shima haka ta d’aura pencil a bakinta lokacin sultana ta shigo ta wuceta ta shiga office din mr ata "haba yaya me yasa zaka min hk bayan kasan  saboda kai na zabi aiki akar kashinka"me zanyi ai yayanki ne shima kuje can ku qarata dan ni ban d’aukeki a matsayin mai aiki ba saboda you're totally nonsense ,duk maganganun da suke maryama tana iya jiyowa sai dai ko d’ago kanta batayi ba .”


waya ya d’aga yayi maganr second goma sannan ya ajiye ya tashi yana tafiya ahankali ya fito har yayi taku biyu kafarsa taci karo da daya daga cikin takardun da marayama ta yar  anatse ya kai idanunshi kafin daga baya ya dan ja wondonsa kad’an ya duka tare da dauka ya mike had’e bud’ewa a hankali yana dubawa taga tsayuwarsa amman ko kallonsa batayi ba, ta cigaba da abinda take dan tunaninta ba’a wurinsa yake ba tunanin yadda zata masa abinda yake bukata ta kama gabanta take ."



Ya cigaba da kallo mace ta fara zanawa sanye da kayan weeding ajikinta a hankali ta d’ago tana kallonsa tsaye ya d’aura hannusa d’aya akan kujera ,d’ayan kuma yana rike da takardan ahanakali ta mike tsaye a daidai lokacin ya kalleta cikin sa’a idanunsu ya tsarke ckin juna saurin dauke idanunta tai ta maida Kan aikinta tana tunanin tare da sa pencil abakinta shi kuwa tundaya daura idanunshi akanta bai dauke ba sai daya kai minti talatin "sir sir!! ammm "Nace kice wani abu ne ?shiru tayi kawai tana kallonsa ya maida idanushi kan zanen da take yanzu wani yanayi suka tsinci kansu “set! ta kasa zama Kmr yadda ya bukata  ya mika mata hannu alamun ta bashi pencil din hannunta ,babu mutsu ta goge kan pencil din saboda ta sakashi cikin bakinta ta mika masa ya kar’ba ya d’aura akan zenen da take ."


"Me kike qoqarin zanawa anan ?”Abinda ka bukata ne sir “ta bashi amsa anatse cike da kwarewa ya shiga gyara mata yana mata bayanin yadda zatai sun d’auki lokaci yana mata bayani sultan yazo ya wuce kasancewar koina a wurin glass ne duk yadda zaka wuce zaka ga mutun kawai idanunshi ya sauka akansu ya tsaya yana qare masu kallo batare da sun sani ba amamn yaso ace yasan me suke tautaunawa akai sai dai babu damar hakan dan hk ya wuce ya kama gabansa ."


Mr ATA yayi mata gyara sosai kinga yadda zakiyi amman kin tsaya salo da son nuna iyawa alhalin duk nonsense kike zanawa.” yana gama fad’ar haka ya ajiye pencil din hannunsa duk da ya zageta amman fuskarta cike take da farinciki ,tace "kai gaskiya yayi kyau sosai ,ya kad’a kai ai kinga yadda ake yi amman kin damu mutane kin iya zane yanzu kin fahimci ba iya kwarewarki yasa aka nemoki kiyi aiki anan ba ?”ta gyad’a masa kai alamun “”eh!har ya juya ta kirasa "sir! ya juyo yana kallonta a tsanake yana jin wani iri akanta abinda yake ji akanta na dabam ne ,abu ne da bai ta'ba jinsa akan kowace mace ba. abun ne mai tsaya wa arai .”


“Ko zan iya cewa wani abu ? karki ce komai dan bana son jin komai ki zauan ki cigaba da aiki kawai kai ta gyd’a masa shi kuma yasa kai ya wuce ."ta sake zama ta cigaba da aiki bayan kamar second goma ya shigo hannunsa rike da cup biyu d’auke da coffee ya ajiye mata cup d’aya mai d’auke da sunan kamfaninsu sannna ya kalli aikinta ta kallesa “sir dan allah ka bari na tafi gida lokaci ya soma ja hankalin iyayena zai tashi “babu inda zaki sai kin gama min aikina ya sake juyawa rike da nashi cup din yana kur’ba ahankali .”


Sosai tayi concentrate akan aikinta ta sake zaro wata takarda ta cigaba a natse ya fito daga office dinsa zai fita idanunshi ya sauka akanta diret inda take ya nufa ya tsaya yana kallonta yana tsaye sectary dinsa ta qaraso ta tsaya tana cewa” sir ina bukatar ka saka hannunka anan ya cire hannunsa d’aya cikin aljihunsa ya amshi biron hannunta ya saka hannu yana saka hannu amman hankalinsa da idanunshi yana kan maryama ita kanta sectary tana lura dashi tana mamakin yadda ya damu da yarinyar da yadda yake yawon kallonta byn duk ba haka yakewa sauran yammatan dake aiki akarkashin ba ."


Bayan ya gama ta wuce shi kuma ya qarasa kusa da maryama yayi daf daita sosai ,hannunsa d’aya cikin ajihun wondonsa yana duban aikin da take ,jin tsayuwar mutun yasa ta d’ago idanunsu suka tsarke cikin juna suka dinga kallon juna har basa son ko kifta idanunsu da kyar ya iya d’auke idanunshi ya kalli zanen da take "har yanzu kina Kan aikin nan ?"eh ina kai sir kokari nake na qarasa na wuce na tafi gida “yayi shiru yana tunani dan baya son ta wuce abu biyu ne aransa yana son hukuntata ta hanyar ‘bata mata lokaci haka kuma baya son tayi nisa dashi dan yana son akoda yaushe tana kusa dashi yana matukar son ya bayyana mata sirrin dake ranshi amman ya fuskanci yarinyar tana da matukar zafin kai da tsautsauran raayi tare da rainin hankali ,ba lallai lokaci daya ya samu had’in kanta ba ."


Ya kalli zanen sannan ya d’auki pencil yana sake mata bayanin yadda zatai daga can bayansu kuwa sultana ce tsaye tana dubansu ashe bata wuce gida ba idan fa tayi sakaci wannan yarinyar zata yi galaba akan ya Adam zata iya mallake zuciyarsa dan taga gbdy ya maida hankalinsa kanta abinda bata ‘bata gani ba kenan sauraran wata yarinya ko kula da ayyukan ma'aikatan dake kula da kamfanin yayinda a bayan sultana sultan ne ya tsaya yana sauke numfashi "kiyi hattara wannan yarinyar ta kware sosai akan aikinta irinsu ATA yake bukata dan tasan aikinta ni nayi danasani da ban d’auketa ba idan kikayi sake zakiyi loosing opportunities dinki na zuwanki wannan kamfanin domin ki siye zuciyarsa ,ya kamata kiyi duk abinda zakiyi wannan yarinyar ta bar kamfaninan .”


ranta a matukar ‘bace ta juyo tana kallonsa “ kai me yasa bakawa mutun fatan alkhairi sai na tsiya addua ya kamata ka min saboda kasan yadda nake son ya Adam arayuwata bai kamata ka fad'a min hk ba ,ba wai bai kamata ba kawai Kiyi abinda ya dace ba sha shanci ba yana gama fad’ar hk ya juya ya koma office dinsa itama ta juya ."


Mr ATA ya ajiye pecil din hannunsa sannan ya juya ya wuce har yayi taku biyu tace"sir ko zan iya wucewa gida yanzu saboda lokaci ya tafi sosai tayi mgnr tana duba agogon hannunta ya kalleta a natse yace " bake ba barin wurin nan sai kin qarasa aikin nan domin ina bukatarsa karfe bakwai daidai zaa zo akar’ba yana gama fadar haka ya juya ta koma ta zauna hankalinta a matukar tashe tare da saka pencil acikin bakinta can dai taga bata da wani mafutar da ya wuce ta cigaba da aikinta  fitsari ta soma ji sosai  marayama ta mike tsaye sakamakon marata dake kokarin kulewa ta nufi bayi tana shiga sultana ta qaraso taga yanayin zanenta yayi kyau sosai zane ne da zai d’auki hankali mutun hakan yasa haushi ya kamata lallai sultan yayi gsky idan batayi hattara ba wannna yarinyar zata gama da zuciyar ya Adam dan haka ta d’auki cup din coffe din da mr ATA ya ajiyewa maryama ta  juye gbdy akan zanen ta bar wajen da sauri ta koma gefe ta tsaya tana jiran taga me zai faru ."


maryama na dawowa ta iske tashin hankali nan take ta gigice ta dinga kallon zanen tana kuka ta d’auki d’aya daga ciki takardan wani ma har ya fara yagewa tana kallo "waye yayi min hk ?garin yaya haka ta kasance ?cikin haka mr ATA ya shigo sakamakon jin sautin kukanta idanunshi ya sauka akan zanen "what !?ya furta da karfi me ye haka zan gani Ke fa nake jira dan by this time ya kamata ace ina gida "?nima haka na gani na shiga toilet nayi fitsari na dawo na gansu haka "you're very stupid” ya fad'a a zafafe yana duba zanen sultana dake gefe babu abinda take sai murmushin jin dadi tayi Kmr bata gansu ba "amman dai ke anyi dakikiyar yarinya wani irin iskanci ne hk ?garin yaya ma haka ta faru ?”


“Wallahi sir ban san yaakayi ba ni me yasa ma ka kawo coffe tunda ai bance maka zan sha ba ."?ta fad’a cikin muryar kuka ."Okay  dan na kawo miki coffe shine ya zama laifi ?“yes dan bana shan coffe bashi da kyau kai ma ka daina sha yana da illa shiyasa ni bana sha "okay zaki gane baki da wayo dan babu inda zaki yau sai kingama min aikina” ya fad'a tsawace tare da juyawa. tabi shi da kallo hawaye na zubo mata bata jin zata iya dan bata san ta inda zata fara ba dan haka ta tattara takurduta ta zuba acikin jakarta ta nufi office dinsa tayi knowking ya bata izini ta shiga yana zaune sectary dinsa na gefensa itama ta gaji sosai amman babu yadda zatai yi tunda mai gidanta bai wuce ba bata da damar wucewa "karki soma kawo min wani uzuri ko bani hakuri ."ya fad’a amatukar fusace .”



"No sir babu daya daga ciki da zanyi nazo na fad’a maka ina son zan wuce gida ya juyo ya kalleta a kaikaice “ na fad'a miki babu inda zaki har sai kingama aikin da na baki a matukar fusace ta soma magan “sir karka manta ni macece ka duba lokaci yanzu ka gani ta kalli agogon hannunta ,gsky ni dare yayi ban saba kai wa dare a waje ba ,yanzu ma nasan hnakalin iyayena na can a tashe ni dai gsky zan wuce ko babu izininka “tana gama fadar hk ta juya da sauri sectary ta shiga kiran sunanta maryama !maryama!! amman ina ko juyowa batayi ba ta cigaba da tafiya.”shiru yayi yana tunani gbdy kwakwa luwarsa ta toshe ya rasa me yake son yayi, shima babu shiri ya mike yayi waje da sauri  sectary some ta daga hannunta sama tana cewa "thank you maryama ta fad'a tana tattara kayansa ta fito da sauri ta biyo bayansa .”

Babu yawa ayi hakuri dashi 😭🙏🙏

Mmn sudai[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 13


Jikin budurwar na kyarma tace “wani abokin aikina ne wallahi”ta fad’a a rikice tana maida hankalinta ga wayar “kana jina?” okay gani nan zuwa yanzu “daga haka ta kashe wayar gbdy, maryama tayi shiru tare da zuba mata shayayyun idanunta tana kallonta qirjinta na dokowa da qarfi “tabbas wannna muryar da taji yanzu daga cikin wayarta tasanta kuma ba muryar kowa bace face muryar ya sadam dinta ,jikinta a matukar sanyaye ta mika mata cup din ruwa data kawo mata tana cewa”wanan murya kamar ta sadam ?”da sauri budurwar tace “no! d’an dai kina cikin alhinin rashinsa ne kikaji kamar irin nashi ne amman sam sam bashi bane wannna ,tayi maganar a rud’e zufa na karyo mata .”


“kad’an tasha ruwan ta mika mata cup din tana cewa “na gode sosai da kulawarki sai dai ina ganin zan wuce yanzu dan duk na duba banga document din da nake bukata ba “.ta qarasa maganr cike da damuwa akan fuskarta kamar da gaske “shikenan mun rasa komai na project dinmu amman allah yasa ya zame mana alkairi “Ameen! maryama ta amsa mata da haka .”tana jin wani iri a gabad’aya ilahirin jikinta yayinda kallo d’aya zakawa budurwar nan kasan bata cikin natsuwarta ba kamar sanda ta shigo ba, a yanzu a kallon da maryama take mata tamkar mai laifi ce tsaye a gabanta ji tayi kamar kar ta bari ta wuce har sai umma ta dawo sun hadu da juna ,gyaran murya budurwar nan tayi kana tace “maryama ni zan wuce duk da naso na tsaya mu had’u da umma amman wannan kiran da kika ga na amsa na gaugauwa ne ana bukatar gani na yanzu wani aiki ne ya taso amman in sha allahu zan dawo cikin satin nan muga juna da umma .”



Naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke tace “Kamar kin shiga zuciyata tunanin da nake kenan ku had’u da umma amman shikenan sai kin dawo muna zuba ido murmushi ya bayyana akan fuskar budurwa sannan ta soma qoqarin fitowa daga d’aki a tare suka fito .”har bakin part din umma ta rakata inda ta hango baba gali tsaye tare da aunty salma cike da tsinkewar zuciya maryama tai sallama da budurwar ta juyo ta koma bangaren umma kai tsaye dakin ta koma ta maida komai inda yake sannna ta dawo parlour’ madadin ta cigaba da karatunta sai kawai ta kira layin yusura taji yadda ko ta samu damar mikawa madam some zanenta kira d’aya ta d’auka.”


Bangaren baba gali kuwa hankalinsa kacokan ya maida kan aunty salma dake tsaye gefensa yana dubanta”maryama kamar yau bataje aiki ba “uhm ta furta tana dariyar mugunta “ai muddin ina raye kuma malamaina na aiki an dakatar daita kenan dan yadda nida ya’yana bamuji dadin rayuwa ba to wallahi itama bazataji ba muddin ina raye .” baba gali ya gyad’a kai kawai yana gyara tsayuwarsa inda aunty salma ta cigaba da magana “ka duba kaga alamarin yaron nan yusuf gabad’aya ya daina neman inda muke dan ma aikin malam yana tasiri har yanzu ajikinsa ai da dawo zai wajen wannan Shegiyar yarinyar“ai kuwa da ya cucemu kina kallo fa kullum sai na kiran layin mahaifinsa amman magana d’aya ce muyi hakuri .” wannan alamari ya fara damuna matuka dan dai burina auren ya tabbata “kar wannan ya dameka kai dai kayi shiru kawai abunka ka zuba masu ido har zuwa sanda zata fashe “.


“Allah ta wajena akwai shirin da kikeyi kenan akasa ?sosai kuwa shirin kuma babban shiri ne ai na rantse da Allah muddin ya’yana basu fara barin gidan nan zuwa gidan miji ba babu inda maryama zata sai dai bayan raina .”murmushi jin dadi ta subewa baba gali itama aunty salma murmushi take tana kallon fuskar mijinta dake kwance da annuri sosa keya ya hau yi yace “an gaishe da salama uwar gidan gali amman mai zai hana kisa ayi aikin da wannan matar zata damka mana takardun gidan biredin da ma duk wani abu daya zamo mallakin sadam ne .itama murmushi tayi tace “sha kuruminka mijina me kake ci nã baka na zuba ai duk sai sun dawo tafin hannunmu sai yadda mukayi dasu kai dai ka zuba ido kawai zaka sha kallo “an gama ranki shi dade ahaka ya juya ya nufi hanyar fita waje ita kuma ta shige ciki tana zagin maryama da umma .”



Da misalin karfe goma na daren ranar Mr ata yana zaune a tsakiyar gadonsa system ne agabansa yana duba sakonin mutane sai dai duk wani motsi da bugun da zuciyarsa takeyi makale take da tunanin maryama kusan ma yace tunaninta ya hanashi sukuni baya jin zai iya jurar rashinta yau kawai da bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba yana jinsa cikin matsi da takura shiru yayi yana cigaba da aikinsa yayinda ahankali maganganunta suke zuwa masa daki daki babu abinda brain dinsa bai kawo masa ba ,wani yayi tsaki wani yayi murmushi yayinda itama .”bangaren maryama itama ta kasa runtsawa tunani muryar da taji d’azu take .”
muryar sai kuwa take mata acikin kunnuwanta dan koda tasanarwa umma zuwan budurwar itama cikin yanayi na tashin hankali ta hauta da fad’a tace ita sam sam bata san wata mai sunan anifa ba mai yasa zata amince daita dan haka karta sake irin wannan ganganci “.


maryama ta qara da sheida mata muryar data ji nan kuma jikin umma yayi sanyi tace “ haba maryama wai mai yasa bazaki manta komai ba dan dai kin saka kulafucinsa aranki ne yasa kike jin kamar yana raye banda abunki mutumin da’aka binne agabanki “amman kuma umma ai babu abinda Allah bazai iya ba “to shikenan tunda kince haka Allah yasa yana raye amman yana raye me yasa bazai dawo garemu ba ?”ta qarasa maganar tana fesar da wani numfashi mai zafi kana ta samu waje ta zauna ta zabga tagumi tare da lumshe idanunta .”maryama tayi wani juyi tana sake lulawa duniyar tunani .”



“idan tayi tunanin rayuwarta da irin kalubalin data fuskanta arayuwarta sai ta dawo tunanin mr ata duk dai ta dan samu natsuwa kadan dan yusura ta sheida mata bai je office yau ba “ko dai taje aiki gobe ne ko zai share bazai ce mata komai ba ?Aa maryama karki je aikin nan gobe?tayiwa kanta gargadi “ karkiyi kuskure zuwa domin kuwa ba qaramin aikinsa bane ya tozartaki kamar yadda saba tozarta duk wanda yaso, ahankali ta sauke numfashi tana kallon inda kayan aikinta yake .”nan ta soma tunanin ko zatayi wani abu koda na awa biyu ne idan ma baza taje aiki gobe ba ta kaiwa yusra da safe kamar yadda
Showing 42001 words to 45000 words out of 176292 words