faruwa dashi ne yau ?” tayiwa kanta tambayar tana mai jin wani irin tashin hankali mai tsanani yana shigarta “bayansa ta cigaba da kallo har sanda ya qarasa shigewa office dinsa ya zauna jikinta a sanyaye ta dawo ta zauna inda sauran abokan aikinta ke cike da tsannain murna.”yusura ta matso kusa daita ta dafa kafadarta tana cewa “lafiya maryma meke faruwa mr ata ya bawa kowa kyautar mota amman ya hanaki ?”I don’t know yusura ban san meke faruwa ba bansan dalilinsa ba but is like sir his not in good mood today ki natsu sosai maryama kiyi tunani baki yi masa laifin komai ba dan bazai yuwu ace ya bawa kowa kyautar mota ya hanaki ba ?”tai shiru kawai tana tunanin mutumin da suka wuni dashi jiya kuma lafiya lafiya suka rabu dashi babu wata matsala kawai dai tafi tunanin miskilancinsa ne ya motsa. numfashi ta sauke da qarfi tana cewa” yusura kije kiyi abinda ke gabanki ni ban damu da kyautar motar da ya baku ba dan ko bai bani ba inada niyyar zan siya lokaci kawai nake jira ta qarasa maganar tana hura hanci tare da runtse idanunta tana mai jin zafin abinda yayi mata.”



Yana zaune rike da file yana dubawa maryama ta shigo office dinsa batare data tsaya neman izininsa ba ta tsaya a gabansa tare da goya hannunwanta duka abaya yayinda kwayar idanunta ke kansa muryarta a sanyaye tace “sir !”ya d’ago tsumammun idanunshi ya zuba mata sai data ji wani irin mummunar fad’uwar gaba sannan taji wani abu ya caki zuciyarta sai dai tayi qoqarin danne abinda taji a zuciya da sansar jikinta ta motsa lip’s dinta ahankali ta soma magana a natse “thank you for yesterday sir .”daman shine dalilin zuwana d’azu office dinka ba wani bane kawai ina son na gode maka ne bisa qoqarinka akaina domin ka dawo min da farincikina” shiru yayi kawai yana kallon kyakkyawar fuskarta da qaramin bakinta da burinsa a yanzu ya jisa cikin bakinsa yana sarrafasa tana gama fad’ar haka ta juya a natse ta nufi kofar fita batare datai masa maganar keyn motarta ba .”


ya ajiye file din hannunsa yana ya cigaba da kallon bayanta yaji kamar ana zarar ranshi ne a zaune da yake ,idanunshi na kanta har ta shiga office dinsu ta samu waje ta zauna ta soma aikinta batare da wata damuwa ba ,can bayan wasu mintuna duk abokan aikinta suka fita zuwa break ,office din ya saura ita kad’ai, ta mike a natse taje inda aka tanada masu ruwan zafi ta tara cup ta tsiyaya ruwan zafi ta had’a shayi ta soma sha ahankali tana lumshe idanunta ahankali mr ata ya tashi daga mazauninsa ya fito har zai karya kwana sai ya hango bayanta tsaye shiru bata ko motsi dan haka ya shiga office dinsu har lokacin tana tsaye hannunta rike da cup qamshin daddaden turarensa ne yasa ta juyo da sauri aiko taji tayi karo da mutu tsaye a gabanta da sauri ta d’ago shi din ta gani tsaye yana dubanta da tsumammun idanunshi gashi har ruwan tea ya d’an ta’ba masa gaban rigarsa a rikice ta soma cewa so..” sorry sir ban..”bansan kana tahowa ba.”


ya tsura mata ido kawai yana kallon yadda duk ta rikice tana faman furta masa “sorry sir “what happened maryama ?” ya sorry yaki qarewa haka ?”.maryama why are you so distracted ?” Sorry sir am ..” bai tsaya jin mai zata sake cewa ba ya fita ya koma office dinsa ya d’auki kwalin tissue ya ajiye akan table ya zari kwaya d’aya ya soma goge jikinsa.” oh Allah meke shirin faruwa dani ne yau ?” ta ajiye cup din hannunta da karfi akan table ta biyosa alokacin daya zauna yana goge saman takalmin qafarsa dan ruwan tea ya sauka akansu muryarta a sanyaye tace “kayi hakuri dan Allah ba da gangan nayi ba “is okay “.
ya fad’a yana lumshe ido .”Jin haka yasa ta juya tana mai jin sanyi aranta dan tafi son taji muryarsa da yanayinsa haka bata son ganinsa cikin fushi ko miskilanci domin hakan yana rikitata sosai if kar yayi wani tunani kamar yadda sultana tayi ai data bashi flowers din data siyo danshi ko hakan zai qara sanyaya zuciyarsa amman tasan halinsa bahagon mutun ne kuma gara ma da sultana tai mata gargadi dan shima haka zai fassara ta ,ta shigo office dinsu da niyyar ciro flower din da niyyar ta yar a shara sai dai taga wayam babu jakarta a inda ta ajiye babu alamunta ta sake dubawa taga babu, ina jakata yake kuma anan fa na ajiye jakata ?”ta fad’a tana duddubawa tana sake tambayar kanta, nan take ta rikice tana sake dubawa alokcin mr ata ya fito ya nufi qasa .”



tayi shiru kawai tana tunani inda jakarta ya shiga kafin ahankali ta jiyo sautin muryar sultana abayanta “kalli nan maryama !”maryama ta juyo da sauri tana kallonta, sultana ta nuna mata kan makeken table din mr ata jakarta dake makale da takada mai ruwan kasa data makala flower ta gani ajiye akai ,har ana iya hango flowers din dake ciki da sauri ta zaro ido waje tana cewa “mai yasa zaki min haka sultana ?”ai gode min ya kamata kiyi domin na saukaka miki “na sakaki ?me yasa zaki min haka “?no no !! yanzu me kike tunani idan mr ata ya gani ?”ta fad’a cikin tsannain tashin hankali gani nayi kina so kina jin tsoro har qarin taimako nayi miki ta yadda zaki samu shiga a wajensa ba dai bazakiji gargadin da na miki ba ai..”kafin sultana ta sake cewa wani abu da sauri maryama ta ra’ba ta gefenta ta nufi office din mr ata inda sultana ta tsaya tana kallon bayanta tana murmushin mugunta. “


cak maryama taja ta tsaya daga tafiyar saurin da take sakamakon jiyo qamshinsa datai ta d’an juyo ahankali shi din ne yana taku cikin yanyanayi na jin kai ,fuskar nan tashi a had’e ta gefenta ya ra’ba ya wuce yana satar kallonta hannu ta kai saman goshinta ta dafe tana kallonsa ta rasa meke mata dadi can tayi wani tunani dan haka ta matsa gaban kofar tace “sir may I coming ?”ya kalleta a natse daga inda yake yace “are you okay ?kayi hakuri ina distoping dinka over daman na manta jakar aikina ne ko zan iya shigowa na d’auka?” da hannunsa ya bata umarni ta shiga ahankali tamkar kazar da kwai ya fashewa aciki ta kai hannunta ta d’auki jakarta ganin idan ta tsaya tura flower din sosai cikin jakarta zai iya fahimtar wani abu tayi tunanin boye jakar abayanta alokacin da ya juyo da saurin idanunshi suka sauka akanta .”kallo daya yayi mata ya fahimci alamun rashin gaskiya atattare daita .”


Muryarsa a kasalance yace “me kike boyewa ? muryarta cike da in..ina tace “amm ..”umm no babu komai “show m your hands zaro idanunta tayi tana cewa “babu komai sir jakata ce”.uhm nasan jakarki ce but let me see .”gabad’aya maryama ta rikice tayi fuska kalar tausayi ta ciro jakar ta rike a hannunta tana nuna masa a tunaninta ganin jakar kawai zai yi ya barta ta wuce kawai sai taga ya kawo hannunsa zai kar’bi jakar.”ta sakar masa jikinta na rawa ,ya tsurawa jakar ido da takardar dake jikin jakar makale yana kallo yana jin wani irin zirrrr a gabdaya ilahirin sansar jikinsa yayinda qararrawar soyayya ta buga a zukansu .ahankali maryama tasa gefen mayafinta tana rufe fuskarta cike da jin tsananin kunya gabdaya a matukar tsorace take da irin kallon da yake mata yana wa flowers din hannunsa, ta sake kai hannunta daya ta rufe fuskarta saboda tsannain kunyar data kamata kallonta yayi yana cewa”. menene wannna .”?
”amm umm daman dan naga irin taimakon da ka min shine na siya d’an wannna abun dan na ba..”


“Meke damunki ?” menen ma’anar wannnan kuma “?sir kawai dai nayi amafani dashi ne dan nayi maka go….” maryama !”ya kira sunanta cikin wani irin salo yana dawowa gabana ya tsya yana tsura mata idanunshi kafin ahankali yace “kin fara sona ne ?”da sauri ta girgiza masa kanta jikinta na d’aukar rawa” ai ni yanzu babu wani maganr soyayya araina aikina da kulawa da rayuwar dan’uwana ne kawai agabana amman babu wata soyayya araina ina jin ma haka zan qarar da rayuwata babu soyayya bare au” shiiiii ya daura yatsana hannunsa akan lip’s dinta yana cigaba da kallonta “ki natsu da kyau maryama ki saurari zuciyarki kin kamu da son mr ata .”no no sir akan wani dalili zakace haka ?”me zai sa zuciyata ta min haka ?”bazan ta’ba yarda zuciyata tayi min haka ba, idan kuma dan flower din nan ne kayi wannan tunanin dan Allah ka daina zan iya maka rantsuwa da alqurani babu digon sonka araina ga wacce ke maseefar sonka can “.ta qarashe mgnr tana nuna masa kofar wajen office dinsa .”



numfashi ya sauke da qarfin yana jin wani irin zafi aransa bai san sanda yayi wulli da jakarta da flowers din ba yana jan tsaki ,tabi gurin da jakarta da flowers dinta ya sauka da kallo ranta yayi mugun baci akan abinda yayi ,nan take idanunta ya ciko da ruwan hawaye tana kallonsa yaja baya ya zauna akan kujera ya d’aura hannunsa daya akan table yana mai jin wani irin rad’ad’i a qirjinsa numfashi ma da kyar yake saukewa kafin ahankali ya nuna mata hanyar waje da hannunsa “get out !” ya fad’a a matukar tsawace babu mutsu ta nufi kofar fita har ta bude kofar sai dai ta kasa fita ta juyo tana kallonsa a tsanake bayan kamr minti biyar ta d’auke idanunta akanshi ta fita tana sauke numfashi sama sama .”



Wani murmushin farinciki ya bayyana akan fuskar sultana ashe ba abinda take tunanin bane acikin zuciyarsa taji dadin wannan wulakanci da sake yiwa maryama da banzar flower ta .zama maryama tayi tana tunanin abinda yasa reactions dinsa ya canza daga tace ba son shi take ba ?”wasu maganganunsa na jiya akan yaya sadam ne suka shiga dawo mata daki daki wani irin yrrrr taji a gabad’aya ilahirin jikinta alokacin data tuno yadda yasa hannunwansa duka  ya zagaye kugunta dashi jiya ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma mata magana cikin wata irin   kasalalaliyar murya mai  cike da tausayawa "maryama duniya cike take da jarabawa kala kala amman idan kayi imani da Allah ,Allah yana tare da kai ,ki manta komai da duk abinda ya faru a tsakaninki da mutumin nan  zaki iya samun madadinsa koma wanda ya fishi arayuwarki ki sani da kice kika mutu da yanzu  yana tare da wata ko nadiya sun cigaba da rayuwarsu daga inda suka tsaya"ki  mantashi arayuwarki hakan shi zai bawa wani damar mallakarki ko baki damar mallakar wani ."wani irin numfashi ta sauke da qarfi tana cewa “na fara tunanin kamar mr ata sona yake idan ba haka ba mai zai sa daga nace dan me yasa zan so shi zai ji haushi ?kai kai maryama ba haka bane bazai ji dadi ba yana son yasan ko kin fara son shi ne sakamakon flower da yaji kince shi kika kawowa to me yasa yaji haushi“?



Yayinda mr ata ranshi ya cigaba da ‘baci juyi kawai yake yi akan kujera yana jin ciwo a cikin zuciyarsa ,ya mike ya bude fridge ya dauki roban ruwa mai sanyi ya dawo mazauninsa ya zauna sannan ya bude ya kai baki nan idanunshi ya sauka akan flowers da jakarta shiru yayi kawai yana kallon flower yana tunanin maganarta me yasa zuciyata zata min haka ?”bazan ta’ba yarda zuciyata tai min haka ba idan kuma dan flowers din nan ne kayi tunanin haka, ka daina zan iya maka rantsuwa da alqurani babu digon sonka araina ga wacce ke matsefar sonka can.”numfashi ya sauke da ajiyar zuciya atare sannan ya fara shan ruwa ,bai sauke ba sai daya shanye tass sannan yayi wurgi da gorar ya sake miikewa tsaye dan ya rasa meke masa dadi.”ahankali ya qaraso ya tsaya gaban jakarta yana kallo kafin ahankali ya duka flower da tace dan shi ta siya ya d’auka yana kallo sai kuma yaji kashi hamsin na damuwarsa ta kau ahankali ya dinga jin zuciyarsa na karkafa masa gwiwar ta fara son shi kuma nan kusa ko bai furta mata ba zata iya nuna masa ,ina ma son shi ta fara da bai san adadin dadin da zai ji ba yau ,ahankali ya bude yar saman suit dinsa ya tura flower yana jin wani irin maseefafen soyayyarta na shigarsa sai dai fuskar nan a had’e take ya d’ago kanshi yana kallonta ta cikin glas




Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.


Page 37




Sadam ne zaune a babban parlour’n hotel din da suka kama dake  lejico wanda ke cikin ikoyi hotel shiru yayi cikin tsananin damuwa sanye yake da jallabiya brown colour mai gajeren hannu,a natse ya kai kwayar idanunshi zuwa ga had’ad’den agogon dake manne a bangon parlour’n.” karfe shida na yamma daidai yanzu ta buga, ahankali ya d’auke kwayar idanunshi cike da damuwa ya maida zuwa bakin kofar shigowa parlour’n zuciyarsa na wani irin bugawa da qarfin gaske numfashi ya sauke sannan ya kai hannusa ya shafa sumar kanshi yana sake duba agogo,” a lissafinsa zuwa yanzu nadiya na can ATA company ,gabadaya ya rasa dalilin da yasa yaji ya kasa samun natsuwa ko dan yana jin kamar akwai wata a qasa ne ?”ya rab kasa ba wani shiri bane aka shirya wa nadiya yayi maganar a fili yana d’auke kanshi zuwa kan ‘dan qaramin stood din dake gabansa wanda ke d’auke da tiren kayan marmari .”jiki a sanyaye ya d’auki Koren apple ya kai bakinsa ya gutsura kad’an tare da cigaba da kallon tauraron d’an adam din daya kunna "knocking din kofar parlour da yaji ana yi shi yasa ya d’auki remut da sauri ya rage sautin qarar TV sannan ya yunkura ya mike  yaje ya bud’e kofar .”



“nadiya ya gani tsaye rungume da hannuwanta duka a qirji tana dubansa,da wani irin sauri ya riko hunnunta ya sanyata ajikinsa ya rungumeta tsam tsam yana sauke numfashi da ajiyar zuciya atare . bayan kamar second goma ya janyeta zuwa gefensa domin ya samu damar maida kofar ya rufe.”cike da tsananin son juna suka tsurawa junansu ido suna kallon juna kafin ahankali suka tsakarwa juna murmushi,sadam na cewa “banyi expecting zaki dawo lafiya ba , na d’auka shiri ne aka shirya miki dan a gano wani abu akanmu “nadiya ta sauke numfashi kana tace “sosai kuwa my heart shiri ne kamar yadda kayi expecting sai dai na nuna masu kwarewa domin kuwa na d’aurasu a wani bagire da bazasu ta’ba fahimtar Komai akanmu ba ,domin kuwa na shirya masu bayanan qarya kuma sun yarda da hakan kuma sun amince dani .”tana gama fad’ar haka suka samu waje suka zauna cike da kulawa sadam ya turawa nadiya tiran kayan marmari nan na gabansa sannan ya nufi fridge ya kawo mata maltina da ruwa mai sanyi" tare da tsura mata idanunshi .”



“Uhm fad’a min wani irin bayanan qarya kika fad’a masu ?”nan take nadiya ta shiga zayyano masa qaryar data fad’a masu tun daga farko har qarshe sannan ta qara da cewa ko kasan cewar maryama baqaramin tashin hankali ta shiga ba sakamakon jin cewar ni da kai masoya ne ?”ta fad’a tana wata irin dariya mai sauti ,”na tabbatar mata kai din nawa ne alokacin baya, amman kuma data lura alokacin da nake mata bayanin soyayyarmu,data fahimci har a yanzu ma kai din nawa ne amman dake wannan yarinyar mahauka ciya ce sai kuka take mai tattare da jimamin rashinka .”my heart sosai fa yarinyar nan ta kamu da sonka anya kuwa my heart wani abu bai shiga tsakaninku ba ?”domin kuwa a irin kallon da nayi mata da tawa fahimtar ta d’an dani dadin ka ne yasa ta damu da rashinka ?”fad’a min menene gaskiyar magana ka kusanceta ko .”?ta qarasa maganar fuskarta tana nuna alamun damuwa da kishi.”



Yaya sadam yayi shiru kawai yana kallonta da sauraronta cike da Jin haushin maganar haka ma zuciyarsa sam taji babu dadi kiran maryama da mahaukaciya datai .” karta ga ya guji kowa akanta ta nemi ta dinga ci masa fuska duk fa lalacewa maryama tashi ce kuma jininsa ce kuma har zuwa yanzu tana nan amatsayin matarsa “kin sha furta min wannan kalmar atsakanina da maryama ko mun d’an d’ani dadin juna ne yasa na kasa furta kalmar saki agareta,wannan kalmar baya damuna kamar kalmar haukan da kike danganta maryama dashi ,”karki manta dangan takata da maryama ,ni daita dagin juna ne da suke da tsananin shakuwa amman ina son daga yau wannan kalmar ta zamo qaro na qarshe da zai sake fitowa daga bakinki shiru tayi tana kallonsa da bayanannen mamaki “yes karki sake dangatata dashi banason dan zamu iya samun gagarumin matsala dake.” ya qarasa maganar yana had’e fuska “numfashi ta sauke sannan tace “okay shikenan naji kayi hakuri “.ta fada tare da kamo hannunsa cikin nata a natse bai ce daita qala ba ta cigaba da magana “kayi magana mana kayi shiru kana kallon wani gefe dabam huci ya furzar yana Kai hannunsa goshinsa “na fa baka hakuri duk da ni nasan
Showing 126001 words to 129000 words out of 176292 words