dadin yanayinsu, juyowa tayi cikin muryar rada tace “yadai?”.
Shima cikin muryan radan yace “Ba sai kin sake zuwa Gidanmu ba daga yau, ni ne namijin, daga yau ni zan dinga biyoki Gidanku, but we are going to do it Legal, zan zo miki kamar ta yanda duk wani Namiji ke zuwa wurin abar sonshi, i will come through the gates not the walls, lets do it legally ko?”.
Kamar ta maidashi ciki don So tace “Lets do it legally”.
“I love you”
“I love you so much babe shiga ciki”.
Bata juyo ba ta shige daki, shima sai da ya ga ta shige daki ya koma nashi dakin yaga 1am har ta kusa yace “lallai lokaci na gudu in kana tare da masoyi”. Kan katifarshi ya haye yana tunanin Labibarsa.
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉
BABI NA ASHIRIN DA SHIDDA 2⃣6⃣
(BAIKO 💍)
Da yake duk sun sa ma kansu abun, cikin kwanaki biyu su ka binciki Juna, akwai wani Mutum a Benin City, shi Abban Jawad ya tura ma Details kan Alhaji Ahmad Dakata yayi mishi background check kan family dinnan kuma ya samu gamsasshiyar Amsa.
Yace mishi Mutumin babban mutum ne datijo kuma bai da matsala, gidan shi Gidan Mutumci ne.
Haka nan Baban Amira ya binciko Asalin su Jawad a Unguwan Alkali, kasancewar Family dinsu ba boyayye bane, babu wani abun Assha da ya ji game da Family din, ya kira Mahaifinshi ya sanar dashi, baban yace "to Alhamdulilah, kace su turo".
To kafin ma Baban Amira ya kira Yayan Jawad yace mai su turo sai ko ga dan Halak din ya kira ya sanar dashi cewa "Akwai wani Uncle dinsu da yazo Abuja, zai koma ran Friday, to sauk'i suke so ba sai an tado kowa daga Katsina ba a tura su chan Edo neman Izini why not su tafi gobe Alhamis? Ba tare da an wahalar da mutanen katsina ba? Amma fa sai in ba matsala a wurinku be san ko its a short notice ba?".
"Bakomai" Yaya Muhammadu yace, zan gaya musu suyi shirin tarban ku Gobe in Allah ya kaimu, suka rabu a mutunce don yin shirin tafiar su kuma da tarban bakin.
Yaya Abdulhafiz ya gaya ma Abbansu yanda sukayi da Yayan Labiba, shi kuma Abban ya kira k'aninshi ya gaya mishi, k'anen yace bakomsi suna iya tafia gobe su dawo goben Friday sai ya dawo Katsinan.
Abba yace "akwai stress, bari na aiki Abdulmajeed naga ko zamu iya samun tickets to Edo"
A hakan suka rabu.
Yaya Muhammadu ya kira Gida ya musu bayani cewa gobe zasu zo saboda wasu dalilai, Babansu Labiba yace "haba bakomai su zo, ita kuma ka saka ranar kawo min ita Gida, tunda dai ga Miji, a bar karatun haka nan".
Mallam Muhammadu yace "InshaAllah baba, bari dai suzo muga yanda zaayi ba zai gagara ba InshaAllah". A hakan suka rabu.
WASHEGARI EDO STATE
Kamar yanda Abba ya tsara su 5 suka ya tafiar zuwa Edo Benin City, Abba, Daddy Usman, Yaya Abdulhafiz, Yaya Abdulmajeed da shi kanshi Jawad din, a cewar Abba gwara su ga wanda zasu ba diyarsu tun yanzu.
Tafiya ce mai nisa, sun iso Edo after 12, kamar yanda aka umurcesu, Dan Achaba suka tsayar su ka bashi adireshin gidan yayi gaba suka bishi a baya har kofar Gidan Alhaji Ahmad Dakata.
Yana a bakin Gate din Gidanshi tare da Manyan Yaranshi su 4, suka tarbesu cikin mutunci,
Sukayi ma juna Musabaha cike da farinciki kafin Alhaji Dakata ya ja hannun Alhaji Abu Shamsu har cikin Parlo suka zauna.
Bayan 'yan gaishe gaishe, aka ci abinci don sosai Alhaji Dakata ya sa aka musu Abinci har kala 3, sunci sun gyaste.
Alhaji Abu Shamsu ya gabatar da Daddy Usman a matsayin kaninshi kuma waliyi madaurin auren 'yayanshi.
Ya gaya mishi yana da mata biyu da yara 4 Abdulhafiz shine babban danshi sai mai bi mishi Abdulmajeed sai auta a mazamai neman diyarshi kuma Jawad, sai miemee yar shekara 3.
Alhaji Dakata yace "MashaAllahu, Allah ya raya mana zuria, nima dai Matana 2, ko waccen su na da 'yaya takwas, ni mai tarin zuria ne, Babban yaro na shi ne Labiba ke gunshi a Katsina, wannan sunanshi Hamza, sai wannan sunanshi Faruk, ga Aliyu wannan kuma mai sunan babana ne Lawal.
Da faraa suka sake gaisawa.
Daddy Usman Abba yace yayi magana.
"Alhamdulilah kamar yanda ka sani munzo ne don muga tushen Yarinya kuma mu nemi a ba dan wurinmu Izini ya dinga zuwa gunta su fahimci juna".
Alhaji Dakata ya murmusa yace "Mallam Jawad, kai ne ke son Diyata Labiba? Fada min naji daga bakinka".
Jawad ya dago kai ya sauke da sauri irin kwarjinin da mutumin ya mishi.
"Eh nine".
Alhaji dakata yace "ka shirya aure?".
Jawad ya kalli Babanshi kafin yace "eh na shirya".
Alhaji Dakata yace "to MashaAllah, abu yayi kyau, Itama nayi magana da Yayanta yace tana sonka tunda ta barka kazo gida wannan alamace ta yarinya na sonka din, nikuma gaskia a tsarin gidana, ban yarda ayi ta zuwa zancen nan ba, in aka ce yaro na son diyata, in na bincike yaro na binciki halinshi da asalinshi, sai in kirasu a daura aure, bana son bacin lokaci, amma naji dadi yanda ka kwaso min Iyalinka na gani, naji dadi wannan ya nuna halin girma, na amince da ku dari bisa dari, na ba danku Labiba, kuzo duk lokacin da kuka shirya ayi auren".
Alhaji Abu Shamsu ya murmusa yace "Alhamdulilah mun ji dadi sosai da karamci, amma so muke ka gaya mana cewa ga ranar da kake so muzo ayi maganar Aure, diya taka ce, magana ma takace".
Alhaji Dakata yace "wallahi bakomai, ni da kuka nuna kuna son nawa? Ko yaushe kuke so sai ayi, ku dai da kun shirya kuzo".
Alhaji Abu yace "dagaske Alhaji kafada, mu fa a shirye muke, ko yaushe ne, Mu ko yanzu kace a daura ai sai a daura".
Daria sukayi gabaki daya.
Alhaji Dakata yace "to shikenan, faduwa tazo daidai da zama, akwai yaruwar Labiba wato Samira, an saka ranarta, auren nata nan da kwana 45, in babu matsala, ina so in hadesu su biyu na aurars".
Alhaji Abu ya fadada fara'arshi yace "ba wani abu InshaAllah, mu da aka ma gata? hakan ma yayi, ba amfanin raba biki biyu a shekara, gwara kawai a hadesu".
Dadi kamar ya faso zuciyan Jawad jin shi zai yi niyyar aure nan da kasa da wata 2.
Daddy Usman yace "aikam bari in bada kudin neman Aure"
Ya ciro naira dubu dari a Aljihu ya kawo ma Alhaji Dakata har gabanshi.
Ya sa hannu ya karba, yace "naira dubu dari? Ai tayi yawa Alhaji Usman".
Daddy Usman yace "aa bata yi ba, bikin Autan Umma ne fa".
Alhaji dakata yace "aa gaskia tayi yawa, nifa aladar nan wai ta bada kudin neman aure da ina da yanda zani yi dana hanata"
Daddy Usman yace "haha, to tunda dai anayi, shikenan muma munyi".
Alhaji Dakata yace "wallahi sunyi yawa, amma abunda zanyi, na dauki dubu hamsin na neman auren, dubu hamsin na sadakinta".
Alhaju Abu Shamsu yace "shikenan an raba gardama".
Duk sukayi daria suna masu ganin mutuncin juna.
Da zasu tafi aka cika musu booth da Doya da Makani da jarkan Manja, suka rabu suna sambarka da junansu.
Bayan tafiyansu ya kira Mallam Muhammadu ya sanar dashi duk yanda sukayi. Baban Amira yace "hakan yayi Abbanmu, ina kasuwa sai anjima zan koma gida na sanar dasu yanda akayi, MashaAllah abu yayi kyau".
Gidansu ya kachame da Abbansu ya sa bikin Labiba rana daya dana Samira, 'yan uba kam ba su ji dadi ba, balle da labarin yazo muso cewa gidansu mai son auren Labiba mai kudi ke, duk surukan gidan babu mai kudinsu mijin Labiban, a da suna ta jin dadi Samira zatayi aure Labiba batayi ba, yanzu ko ransu ya baci jin ta samu Miji dan Babban gida kuma.
Mamin Labiba kam godia take ma Allah da zai nuna mata bikin Labibarta.
K A T S I N A
A Masallacin Anguwar yayi Sallahr La'asar, Mallam shehu ya tareshi a hanya yana tambayarshi.
"Wai ni Mallam Muhammadu wannan k'anwa taka ya ma sunanta?".
Baban Amira ya murmusa yace "Labiba Sunanta".
Mallam Shehu yace "ita fa, ni ina mamaki, meye hadinta da wannan yaro dan gidan Alhaji Zaki"
Baban Amira bai gane zancen ba yace "wai wa?
Yace "wannan yaro mana DanMakaho"
Da mamaki yace "DanMakaho kuma? Ita fa ko saninshi batayi ba, me ko zai hadssu?".
Mallam Shehu yace "ya zakace ko saninshi batayi ba bayan kullum sai na gansu tare, jiya da tsaye na gansu a shagon Eskaley kuma suka ketaro Anguwa tare, duk wands ya gansu ya san masoya ne, kuma sai da suka tsaya kofar Gidanka sukayi zance kafin ta shige gida".
Mamaki duk ya bayyana a fuskarshi yace "Anya dai? Ba dai Labiba ba".
Mallam Shehu yace "hmm, baka yarda ba ko? Ka dai bincika ka gani, dama nace in gaya ma ne don ka san yanda zakayi ka datse Alakara su tunda dai kowa ya san DanMakaho dan Shaye shayene kafin ta zubar maka da mutunci gwara ka katse ma hanzarinsu gudu".
Baban Amira ya ma rasa abunyi don shifa bai yarda ba, haka ya k'ama hanyar gida jiki a sanyaye.
****
Fitowar ta kenan daga Gida, ta ganshi tsaye ya rungume hannu a kirji kafarsa daya kan bangon gidansu.
Suna hada idanuwa suka murmusa ma Juna, kusan a tare suka ce “Kinyi kyau, kayi kyau”.
Sukayi daria a tare yace “ai ban kai ki ba”.
Tace “ka fini mana”
Yace “ya makaranta? Are you stressed out?”
Tace “i was, amma ganinka ya sa gajiar duk ta tafi”.
Ya dago kai da murmushinshi kafin yace wani abu ya Hango Mallam Muhammad na nufosu.
Ya dan tsorata yace “Shiga Gida Biebbs” da mamaki ta kalleshi tace “meyasa?” Murya k’asa k’asa yace “ga Yayanki nan”.
Ta dan waiga ta ga shi dinne, ko a jikinta don ma murmushi take mishi da ya zo gabansu ya kallesu daya bayan daya.
Labiba tace “Yaya sannu da zuwa”
Baban Amira yace “DanMakaho mai kakeyi a kofar gida na?”.
Zaid ya dan fara in ina yace “bakomai, dama wucewa zanyi”.
Labiba tayi karaf tace “Yaya wurina yazo”
Mallam Muhammadu ya kalleta da mamaki yace “wato maganganun da ake fada game da ke a anguwa”.
“Gaskia ne” Ba tare da ta san me yake nufi ba ta amsa shi.
Mallam Muhammadu yace “Labiba shiga Gida”.
Tace “To Yaya”
Ta kalli Zaid tace “Barin shiga ciki, sai munyi waya”.
Zaid sadda kanshi k’asa kawai yayi, wai ya ta ke haka? Ta ya take iya fadan abunda ke ranta ba tare da ta sakayawa ba? Ai a irin yanayin nan k’arya ya kamata tayi, ansan bata k’arya, amma dai yanda bata ji nauyin yayanta ba ya sa shi jin wani iri.
Yana jira yaji Yayanta yace wani abu amma bai ce ba illa ce mishi sai anjima da yayi.
Ya shiga Gida ya ga Labiba tsaye, kwala ma matarshi kira yayi.
“Asiya, Asiya”.
Sai ko gata ta fito da sauri jin kiran Mijin nata
“Wai dama kinsan Yaron nan DanMakaho na zuwa gurin Labiba?” Ido ta bude tace “wallahi ban sani ba, DanMakaho kuma? Wani irin dan Makaho? Tare ka gansu?”. Ta tambaya tana kallon Labiba.
Labiba tace “Yaya fa bata sani ba”.
Yace “yi min shiru”.
Aunty Aseey tace “dagaske ne? Ke ko me zakiyi dashi?”.
Baban Amira yace “bude kunnenki kiji, kar na sake ganinki da Yaronnan, kuma an sanya ranar aurenki da Jawad, sadakinki dubu hamsin na gun Baba, dazun sukaje neman aure Baba kuma ya amince musu, tunda ya ansa sadakinki”.
Labiba jin abun take kamar Almara tace “Yaya chabda, lallai kam”.
Yace “kin dauka wasa nike?” Kallonshi ta tsaya yi tana karantarshi, iyakar gaskia ta karanto a idanunshi.
“Yaya ta ya akayi bansan shiryshiryen nan ba?”
Yace “kinyi waya da Jawad jiya zuwa yau?”
Tunawa tayi rabon da suyi waya tun ran Tuesday, kuma messages dinshi a whatsapp suna chan tayi hanging.
Tace “Huh, Yaya har kai baka min maganar ba”.
Yace “tunda kika kawo minshi Gida magana ta k’are”.
Ko a jikinta tace “nikam ba a daura ba ai? To ku mayar mai da sadakinshi, nikam DanMakaho nike so, kuma ni shi zan aura”.
Ta shige ciki ta barsu da mamaki, barin ma Baban Amira, Labiba bata taba mishi rashin kunya ba, shekara 26 ya bata, amma yanzu ita take mishi rashin kunya akan Namiji? Namijin ma DanMakaho?.
Zuwa yayi yana kwankwansa mata amma ta ki bude dakin, ran baban Amira ya baci, ya shige daki.
Itama Labiba ranta a jagule ta kira Mamarta ringing daya ta dauka tace “Mami, dagaske an kawo sadakina? Dagaske bikina rana daya dana samira?”.
Mami tace “Eh Labiba, aikam mutanen Kirki”.
Labiba tace “Mami nifa ba zan aureshi ba, so daya yazo nan gidan, kawai suka zagaya suka ma Yaya Muhammadu magana shine ya turasu chan gun Baba”.
Mami tace “Labiba mai kike son cewa? DonAllah nidai ki rufa min Asiri, bakiji me ake ta cewa a cikin Gida ba”.
“Mami su fada abunda suke so, nikam ba zan auri Jawad ba, ina da wanda nake so”.
Mami tace “Labiba kiyi hakuri donAllah, kinsan babanki kaifi daya ne, ya amince musu, ki rufa min asiri”.
Labiba ta lura Maminta ba zata gane ba yanzu tace “Mami zan kiraki, ina zuwa” ta kashe wayarta.
Sukuku ta karashe ranar Alhamis, ba wandata ma magana har yaran yayanta, da daddare ta sha zancenta da Zaid a waya ba tare da ta damu da komai ba, don ba mai mata auren dole so wannan ba matsala bace, ta cigaba da harkan gabanta.
F R I D A Y.
Daddy Usman yazo musu Sallama, Doya da makani damanja Galan Biyu da suka samo jiya a Edo AbdulMajid ya saka mai a booth, yayi breakfast, sukayi dan fira da Yaran Yayanshi kafin yayan ya fito, sannan yayi sallama yace "bari ya tafi".
Gabaki daya Iyalan Alhaji Abu Shamsu suka rakoshi har bakin Mota suka mishi fatan Allah ya sa a isa lafia suna mai mai fatan Alheri.
Daddy Usman ya kama hanyar ta dikko dakin Kara.
***
Tsautsayi ne ya faru da Alhaji Usman a hanyarshi ta komawa Katsina, yana daf da shiga Katsina a Charanci yayi hadari inda Shanu suka gitta mai garin kauce musu ya bige wani Mutumi tare da fadawa wani kwalbatin da ya sa shi buguwa a kai.
Mutanen Anguwa suka kawo dauki, da aka duba sai aka wanda Alhaji Usman din ya bige ya cika don ko shurawa beyi ba.
Da yawa kan idonsu abun ya faru sun san cewa ba laifin Alhaji Usman bane, nan da nan yan garin suka taimaka suka kai Alhaji Usman Asibiti mafi kusa.
Wayarshi wani ya ciri ya cire sim din ya saka a wayarshi don wayar Alhaji Usman din akwai Pattern.
Duba contact list yayi yaga dai ba wani suna Mama ko Baba, sai yaga Contact din My Son.
Da sauri mutumin ya latso numbern.
A B U J A
Abdulmajeed cike da shagwaba yace "Yanzu kai shikenan Abba ka yarda Jawad ya rigani Aure?"
Mancy tace "to tunda baka da niya ba gwara ya yi overtaking dinka ba?".
Abdulmajeed yace "fa Mancy ba laifina bane, ko dazun sai da nace ma Ya Abdulhafiz yama Daddy Usman magana a hada bikin da nawa da na Jawad Abba ya hana, wai ba ya so ya shiga hakkin Daddy, kuma wai karatu takeyi sai ta gama ND1, afterall wallahi cireta ma zanyi daga Poly, Haba Polyn lafia".
Abban ya harareshi yayi saurin sadda kai, Umma tace "gaskia Abbansu da ka bari an hadasu, ai ba shiga Hakkin Aisha diyarka ce kaine waliiyyinta, in ka yanke hukunci kanta ba mai ce maka don me?".
Shiru Abban yayi kafin yace "shikenan, bari Usmanun ya isa zamuyi waya, sai mu ji in zaa iya hadesu".
Abdulmajeed ya gallawa Zaid harara yace "mallam sai ka bar mi gwalo hakan nan, inshaAllah ba zaka rigani aure ba".
Jawad yace "hahah aiko zaka sha madaran mamaki".
Sukayi daria baki daya.
Suna cikin firansu mai dadi ne wayar AbdulMajeed yayi ringing,
Ya kallesu baki daya da murmushi a fuskancshi yace "Daddy Usman ne"
Jawad yace "kace sirikinka ne"
Ya jefeshi da harara.
Mancy tace "kai wani irin Gudu Daddy Usman keyi haka? Har ya isa kenan".
Jin tashin hankali sukayi a muryan Abdulmajeed.
"Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, mai ya sameshi? Yanzu yana ina?".
Kowa na cikin parlorn ya fara tambaya mai ya sami Uncle
Usman.
Kasa magana yayi sai da Abban yace "Kai Abdulmajeed, ka gaya mana mai ya samu Daddyn naku?".
Abdulmajeed kamar yayi kuka yace "Abba hadari Daddy Usman yayi a Charanci, ya bige wani mutjmi har mutumin ya mutu amma shi Daddyn yana Asibiti ba abunda ya sameshi sai dai wai ya bugu a kai".
Tunda ya fara magana suke Salallami da Salati.
Abba cike da kidima ya ciro wayarshi ya kira chan Katsina gidan Iyayenshi ya sanar dasu, da su je Charanchi yanzu yana nan tahowa gobe InshaAllah.
Ya Kalli Iyalanshi da sukayi saye cirko cirko yace musu "ku shirya, gobe inshaAllah zamuje Katsina".
Amsa mishi sukayi duk jikinsu a sanyayye
K A T S I N A
Ai yayewa akayi a Unguwar Alkali harta Hajiarsu Alhajin suka kwasa suka nufa Charanci har su Aishan.
Kafin su je an gano Gidansu Mamacin, suka shiga akayi magana, Allah ya sa Saurayi ne, baida Iyali, Mahaifiyarshi kam taci kuka sosai amma ta yafe Wanda ya bamkeshi yayi kaffara, aka rufo mamacin.
Basu kwana a Charanci ba suka wuto Katsina.
Asibiti zaayi dashi yace shi dai donAllah a kaishi Gidanshi don ya tsorata sosai da abunda ya faru.
Tunda suka dawo Gida ake zuwa yi musu jaje ko wani lungu da sak'o, gidanshi ma bude ya kwana saboda masu shiga da fita, wasu sun kasa hakura safiya tayi su zo, abunku da 'yan dangi.
*
'Yan Abuja tun safe wurin 8 suka fito, Mota biyu sukayi, AbdulMajeed ke jan Abba da Matanshi Umma da Mancy, sai Abdulhafiz ke jan Matarshi Ummita da Jawad da Mimi, a tare suke taafiya ba'a gudu da Abba, shiyasa suke dadewa akan hanya, sai da suka tsaya a Zaria suka ci Abinci a Shagalinku kafin suka sake daukan hanya.
Sun iso Charanci wurin Karfe2, tambaya sukayi gidan da aka banke wani Jiya, har kofar Gidan aka kaisu, suka shiga, sai kallonsu ake tayi aka dai gaigaisa.
Abba yace "ina Mahaifan yaro?"
Aka gwada musu Uwarshi.
Yace "Uba fa?"
Akace ya dade da rasuwa.
Abba ya gabatar da kanshi a matsayin Yayan wanda ya banke mata da, ya roke su gafara, mahaifiyar yaro tace "wallahi Alhaji, lokacin Saminu ne yayi, K'anenka ne sila, amma lokaci yayi ba wata dabara da zai tsaida tafia".
Matar ta burgesu, nan aka musu karamci aka kawo musu ruwa fiya wota (pure water) da damammen fura.
Ba wanda bai sha furan nan ba sai mimi da bata shan fura, suka sha
Showing 93001 words to 96000 words out of 132816 words
Shima cikin muryan radan yace “Ba sai kin sake zuwa Gidanmu ba daga yau, ni ne namijin, daga yau ni zan dinga biyoki Gidanku, but we are going to do it Legal, zan zo miki kamar ta yanda duk wani Namiji ke zuwa wurin abar sonshi, i will come through the gates not the walls, lets do it legally ko?”.
Kamar ta maidashi ciki don So tace “Lets do it legally”.
“I love you”
“I love you so much babe shiga ciki”.
Bata juyo ba ta shige daki, shima sai da ya ga ta shige daki ya koma nashi dakin yaga 1am har ta kusa yace “lallai lokaci na gudu in kana tare da masoyi”. Kan katifarshi ya haye yana tunanin Labibarsa.
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO😉
BABI NA ASHIRIN DA SHIDDA 2⃣6⃣
(BAIKO 💍)
Da yake duk sun sa ma kansu abun, cikin kwanaki biyu su ka binciki Juna, akwai wani Mutum a Benin City, shi Abban Jawad ya tura ma Details kan Alhaji Ahmad Dakata yayi mishi background check kan family dinnan kuma ya samu gamsasshiyar Amsa.
Yace mishi Mutumin babban mutum ne datijo kuma bai da matsala, gidan shi Gidan Mutumci ne.
Haka nan Baban Amira ya binciko Asalin su Jawad a Unguwan Alkali, kasancewar Family dinsu ba boyayye bane, babu wani abun Assha da ya ji game da Family din, ya kira Mahaifinshi ya sanar dashi, baban yace "to Alhamdulilah, kace su turo".
To kafin ma Baban Amira ya kira Yayan Jawad yace mai su turo sai ko ga dan Halak din ya kira ya sanar dashi cewa "Akwai wani Uncle dinsu da yazo Abuja, zai koma ran Friday, to sauk'i suke so ba sai an tado kowa daga Katsina ba a tura su chan Edo neman Izini why not su tafi gobe Alhamis? Ba tare da an wahalar da mutanen katsina ba? Amma fa sai in ba matsala a wurinku be san ko its a short notice ba?".
"Bakomai" Yaya Muhammadu yace, zan gaya musu suyi shirin tarban ku Gobe in Allah ya kaimu, suka rabu a mutunce don yin shirin tafiar su kuma da tarban bakin.
Yaya Abdulhafiz ya gaya ma Abbansu yanda sukayi da Yayan Labiba, shi kuma Abban ya kira k'aninshi ya gaya mishi, k'anen yace bakomsi suna iya tafia gobe su dawo goben Friday sai ya dawo Katsinan.
Abba yace "akwai stress, bari na aiki Abdulmajeed naga ko zamu iya samun tickets to Edo"
A hakan suka rabu.
Yaya Muhammadu ya kira Gida ya musu bayani cewa gobe zasu zo saboda wasu dalilai, Babansu Labiba yace "haba bakomai su zo, ita kuma ka saka ranar kawo min ita Gida, tunda dai ga Miji, a bar karatun haka nan".
Mallam Muhammadu yace "InshaAllah baba, bari dai suzo muga yanda zaayi ba zai gagara ba InshaAllah". A hakan suka rabu.
WASHEGARI EDO STATE
Kamar yanda Abba ya tsara su 5 suka ya tafiar zuwa Edo Benin City, Abba, Daddy Usman, Yaya Abdulhafiz, Yaya Abdulmajeed da shi kanshi Jawad din, a cewar Abba gwara su ga wanda zasu ba diyarsu tun yanzu.
Tafiya ce mai nisa, sun iso Edo after 12, kamar yanda aka umurcesu, Dan Achaba suka tsayar su ka bashi adireshin gidan yayi gaba suka bishi a baya har kofar Gidan Alhaji Ahmad Dakata.
Yana a bakin Gate din Gidanshi tare da Manyan Yaranshi su 4, suka tarbesu cikin mutunci,
Sukayi ma juna Musabaha cike da farinciki kafin Alhaji Dakata ya ja hannun Alhaji Abu Shamsu har cikin Parlo suka zauna.
Bayan 'yan gaishe gaishe, aka ci abinci don sosai Alhaji Dakata ya sa aka musu Abinci har kala 3, sunci sun gyaste.
Alhaji Abu Shamsu ya gabatar da Daddy Usman a matsayin kaninshi kuma waliyi madaurin auren 'yayanshi.
Ya gaya mishi yana da mata biyu da yara 4 Abdulhafiz shine babban danshi sai mai bi mishi Abdulmajeed sai auta a mazamai neman diyarshi kuma Jawad, sai miemee yar shekara 3.
Alhaji Dakata yace "MashaAllahu, Allah ya raya mana zuria, nima dai Matana 2, ko waccen su na da 'yaya takwas, ni mai tarin zuria ne, Babban yaro na shi ne Labiba ke gunshi a Katsina, wannan sunanshi Hamza, sai wannan sunanshi Faruk, ga Aliyu wannan kuma mai sunan babana ne Lawal.
Da faraa suka sake gaisawa.
Daddy Usman Abba yace yayi magana.
"Alhamdulilah kamar yanda ka sani munzo ne don muga tushen Yarinya kuma mu nemi a ba dan wurinmu Izini ya dinga zuwa gunta su fahimci juna".
Alhaji Dakata ya murmusa yace "Mallam Jawad, kai ne ke son Diyata Labiba? Fada min naji daga bakinka".
Jawad ya dago kai ya sauke da sauri irin kwarjinin da mutumin ya mishi.
"Eh nine".
Alhaji dakata yace "ka shirya aure?".
Jawad ya kalli Babanshi kafin yace "eh na shirya".
Alhaji Dakata yace "to MashaAllah, abu yayi kyau, Itama nayi magana da Yayanta yace tana sonka tunda ta barka kazo gida wannan alamace ta yarinya na sonka din, nikuma gaskia a tsarin gidana, ban yarda ayi ta zuwa zancen nan ba, in aka ce yaro na son diyata, in na bincike yaro na binciki halinshi da asalinshi, sai in kirasu a daura aure, bana son bacin lokaci, amma naji dadi yanda ka kwaso min Iyalinka na gani, naji dadi wannan ya nuna halin girma, na amince da ku dari bisa dari, na ba danku Labiba, kuzo duk lokacin da kuka shirya ayi auren".
Alhaji Abu Shamsu ya murmusa yace "Alhamdulilah mun ji dadi sosai da karamci, amma so muke ka gaya mana cewa ga ranar da kake so muzo ayi maganar Aure, diya taka ce, magana ma takace".
Alhaji Dakata yace "wallahi bakomai, ni da kuka nuna kuna son nawa? Ko yaushe kuke so sai ayi, ku dai da kun shirya kuzo".
Alhaji Abu yace "dagaske Alhaji kafada, mu fa a shirye muke, ko yaushe ne, Mu ko yanzu kace a daura ai sai a daura".
Daria sukayi gabaki daya.
Alhaji Dakata yace "to shikenan, faduwa tazo daidai da zama, akwai yaruwar Labiba wato Samira, an saka ranarta, auren nata nan da kwana 45, in babu matsala, ina so in hadesu su biyu na aurars".
Alhaji Abu ya fadada fara'arshi yace "ba wani abu InshaAllah, mu da aka ma gata? hakan ma yayi, ba amfanin raba biki biyu a shekara, gwara kawai a hadesu".
Dadi kamar ya faso zuciyan Jawad jin shi zai yi niyyar aure nan da kasa da wata 2.
Daddy Usman yace "aikam bari in bada kudin neman Aure"
Ya ciro naira dubu dari a Aljihu ya kawo ma Alhaji Dakata har gabanshi.
Ya sa hannu ya karba, yace "naira dubu dari? Ai tayi yawa Alhaji Usman".
Daddy Usman yace "aa bata yi ba, bikin Autan Umma ne fa".
Alhaji dakata yace "aa gaskia tayi yawa, nifa aladar nan wai ta bada kudin neman aure da ina da yanda zani yi dana hanata"
Daddy Usman yace "haha, to tunda dai anayi, shikenan muma munyi".
Alhaji Dakata yace "wallahi sunyi yawa, amma abunda zanyi, na dauki dubu hamsin na neman auren, dubu hamsin na sadakinta".
Alhaju Abu Shamsu yace "shikenan an raba gardama".
Duk sukayi daria suna masu ganin mutuncin juna.
Da zasu tafi aka cika musu booth da Doya da Makani da jarkan Manja, suka rabu suna sambarka da junansu.
Bayan tafiyansu ya kira Mallam Muhammadu ya sanar dashi duk yanda sukayi. Baban Amira yace "hakan yayi Abbanmu, ina kasuwa sai anjima zan koma gida na sanar dasu yanda akayi, MashaAllah abu yayi kyau".
Gidansu ya kachame da Abbansu ya sa bikin Labiba rana daya dana Samira, 'yan uba kam ba su ji dadi ba, balle da labarin yazo muso cewa gidansu mai son auren Labiba mai kudi ke, duk surukan gidan babu mai kudinsu mijin Labiban, a da suna ta jin dadi Samira zatayi aure Labiba batayi ba, yanzu ko ransu ya baci jin ta samu Miji dan Babban gida kuma.
Mamin Labiba kam godia take ma Allah da zai nuna mata bikin Labibarta.
K A T S I N A
A Masallacin Anguwar yayi Sallahr La'asar, Mallam shehu ya tareshi a hanya yana tambayarshi.
"Wai ni Mallam Muhammadu wannan k'anwa taka ya ma sunanta?".
Baban Amira ya murmusa yace "Labiba Sunanta".
Mallam Shehu yace "ita fa, ni ina mamaki, meye hadinta da wannan yaro dan gidan Alhaji Zaki"
Baban Amira bai gane zancen ba yace "wai wa?
Yace "wannan yaro mana DanMakaho"
Da mamaki yace "DanMakaho kuma? Ita fa ko saninshi batayi ba, me ko zai hadssu?".
Mallam Shehu yace "ya zakace ko saninshi batayi ba bayan kullum sai na gansu tare, jiya da tsaye na gansu a shagon Eskaley kuma suka ketaro Anguwa tare, duk wands ya gansu ya san masoya ne, kuma sai da suka tsaya kofar Gidanka sukayi zance kafin ta shige gida".
Mamaki duk ya bayyana a fuskarshi yace "Anya dai? Ba dai Labiba ba".
Mallam Shehu yace "hmm, baka yarda ba ko? Ka dai bincika ka gani, dama nace in gaya ma ne don ka san yanda zakayi ka datse Alakara su tunda dai kowa ya san DanMakaho dan Shaye shayene kafin ta zubar maka da mutunci gwara ka katse ma hanzarinsu gudu".
Baban Amira ya ma rasa abunyi don shifa bai yarda ba, haka ya k'ama hanyar gida jiki a sanyaye.
****
Fitowar ta kenan daga Gida, ta ganshi tsaye ya rungume hannu a kirji kafarsa daya kan bangon gidansu.
Suna hada idanuwa suka murmusa ma Juna, kusan a tare suka ce “Kinyi kyau, kayi kyau”.
Sukayi daria a tare yace “ai ban kai ki ba”.
Tace “ka fini mana”
Yace “ya makaranta? Are you stressed out?”
Tace “i was, amma ganinka ya sa gajiar duk ta tafi”.
Ya dago kai da murmushinshi kafin yace wani abu ya Hango Mallam Muhammad na nufosu.
Ya dan tsorata yace “Shiga Gida Biebbs” da mamaki ta kalleshi tace “meyasa?” Murya k’asa k’asa yace “ga Yayanki nan”.
Ta dan waiga ta ga shi dinne, ko a jikinta don ma murmushi take mishi da ya zo gabansu ya kallesu daya bayan daya.
Labiba tace “Yaya sannu da zuwa”
Baban Amira yace “DanMakaho mai kakeyi a kofar gida na?”.
Zaid ya dan fara in ina yace “bakomai, dama wucewa zanyi”.
Labiba tayi karaf tace “Yaya wurina yazo”
Mallam Muhammadu ya kalleta da mamaki yace “wato maganganun da ake fada game da ke a anguwa”.
“Gaskia ne” Ba tare da ta san me yake nufi ba ta amsa shi.
Mallam Muhammadu yace “Labiba shiga Gida”.
Tace “To Yaya”
Ta kalli Zaid tace “Barin shiga ciki, sai munyi waya”.
Zaid sadda kanshi k’asa kawai yayi, wai ya ta ke haka? Ta ya take iya fadan abunda ke ranta ba tare da ta sakayawa ba? Ai a irin yanayin nan k’arya ya kamata tayi, ansan bata k’arya, amma dai yanda bata ji nauyin yayanta ba ya sa shi jin wani iri.
Yana jira yaji Yayanta yace wani abu amma bai ce ba illa ce mishi sai anjima da yayi.
Ya shiga Gida ya ga Labiba tsaye, kwala ma matarshi kira yayi.
“Asiya, Asiya”.
Sai ko gata ta fito da sauri jin kiran Mijin nata
“Wai dama kinsan Yaron nan DanMakaho na zuwa gurin Labiba?” Ido ta bude tace “wallahi ban sani ba, DanMakaho kuma? Wani irin dan Makaho? Tare ka gansu?”. Ta tambaya tana kallon Labiba.
Labiba tace “Yaya fa bata sani ba”.
Yace “yi min shiru”.
Aunty Aseey tace “dagaske ne? Ke ko me zakiyi dashi?”.
Baban Amira yace “bude kunnenki kiji, kar na sake ganinki da Yaronnan, kuma an sanya ranar aurenki da Jawad, sadakinki dubu hamsin na gun Baba, dazun sukaje neman aure Baba kuma ya amince musu, tunda ya ansa sadakinki”.
Labiba jin abun take kamar Almara tace “Yaya chabda, lallai kam”.
Yace “kin dauka wasa nike?” Kallonshi ta tsaya yi tana karantarshi, iyakar gaskia ta karanto a idanunshi.
“Yaya ta ya akayi bansan shiryshiryen nan ba?”
Yace “kinyi waya da Jawad jiya zuwa yau?”
Tunawa tayi rabon da suyi waya tun ran Tuesday, kuma messages dinshi a whatsapp suna chan tayi hanging.
Tace “Huh, Yaya har kai baka min maganar ba”.
Yace “tunda kika kawo minshi Gida magana ta k’are”.
Ko a jikinta tace “nikam ba a daura ba ai? To ku mayar mai da sadakinshi, nikam DanMakaho nike so, kuma ni shi zan aura”.
Ta shige ciki ta barsu da mamaki, barin ma Baban Amira, Labiba bata taba mishi rashin kunya ba, shekara 26 ya bata, amma yanzu ita take mishi rashin kunya akan Namiji? Namijin ma DanMakaho?.
Zuwa yayi yana kwankwansa mata amma ta ki bude dakin, ran baban Amira ya baci, ya shige daki.
Itama Labiba ranta a jagule ta kira Mamarta ringing daya ta dauka tace “Mami, dagaske an kawo sadakina? Dagaske bikina rana daya dana samira?”.
Mami tace “Eh Labiba, aikam mutanen Kirki”.
Labiba tace “Mami nifa ba zan aureshi ba, so daya yazo nan gidan, kawai suka zagaya suka ma Yaya Muhammadu magana shine ya turasu chan gun Baba”.
Mami tace “Labiba mai kike son cewa? DonAllah nidai ki rufa min Asiri, bakiji me ake ta cewa a cikin Gida ba”.
“Mami su fada abunda suke so, nikam ba zan auri Jawad ba, ina da wanda nake so”.
Mami tace “Labiba kiyi hakuri donAllah, kinsan babanki kaifi daya ne, ya amince musu, ki rufa min asiri”.
Labiba ta lura Maminta ba zata gane ba yanzu tace “Mami zan kiraki, ina zuwa” ta kashe wayarta.
Sukuku ta karashe ranar Alhamis, ba wandata ma magana har yaran yayanta, da daddare ta sha zancenta da Zaid a waya ba tare da ta damu da komai ba, don ba mai mata auren dole so wannan ba matsala bace, ta cigaba da harkan gabanta.
F R I D A Y.
Daddy Usman yazo musu Sallama, Doya da makani damanja Galan Biyu da suka samo jiya a Edo AbdulMajid ya saka mai a booth, yayi breakfast, sukayi dan fira da Yaran Yayanshi kafin yayan ya fito, sannan yayi sallama yace "bari ya tafi".
Gabaki daya Iyalan Alhaji Abu Shamsu suka rakoshi har bakin Mota suka mishi fatan Allah ya sa a isa lafia suna mai mai fatan Alheri.
Daddy Usman ya kama hanyar ta dikko dakin Kara.
***
Tsautsayi ne ya faru da Alhaji Usman a hanyarshi ta komawa Katsina, yana daf da shiga Katsina a Charanci yayi hadari inda Shanu suka gitta mai garin kauce musu ya bige wani Mutumi tare da fadawa wani kwalbatin da ya sa shi buguwa a kai.
Mutanen Anguwa suka kawo dauki, da aka duba sai aka wanda Alhaji Usman din ya bige ya cika don ko shurawa beyi ba.
Da yawa kan idonsu abun ya faru sun san cewa ba laifin Alhaji Usman bane, nan da nan yan garin suka taimaka suka kai Alhaji Usman Asibiti mafi kusa.
Wayarshi wani ya ciri ya cire sim din ya saka a wayarshi don wayar Alhaji Usman din akwai Pattern.
Duba contact list yayi yaga dai ba wani suna Mama ko Baba, sai yaga Contact din My Son.
Da sauri mutumin ya latso numbern.
A B U J A
Abdulmajeed cike da shagwaba yace "Yanzu kai shikenan Abba ka yarda Jawad ya rigani Aure?"
Mancy tace "to tunda baka da niya ba gwara ya yi overtaking dinka ba?".
Abdulmajeed yace "fa Mancy ba laifina bane, ko dazun sai da nace ma Ya Abdulhafiz yama Daddy Usman magana a hada bikin da nawa da na Jawad Abba ya hana, wai ba ya so ya shiga hakkin Daddy, kuma wai karatu takeyi sai ta gama ND1, afterall wallahi cireta ma zanyi daga Poly, Haba Polyn lafia".
Abban ya harareshi yayi saurin sadda kai, Umma tace "gaskia Abbansu da ka bari an hadasu, ai ba shiga Hakkin Aisha diyarka ce kaine waliiyyinta, in ka yanke hukunci kanta ba mai ce maka don me?".
Shiru Abban yayi kafin yace "shikenan, bari Usmanun ya isa zamuyi waya, sai mu ji in zaa iya hadesu".
Abdulmajeed ya gallawa Zaid harara yace "mallam sai ka bar mi gwalo hakan nan, inshaAllah ba zaka rigani aure ba".
Jawad yace "hahah aiko zaka sha madaran mamaki".
Sukayi daria baki daya.
Suna cikin firansu mai dadi ne wayar AbdulMajeed yayi ringing,
Ya kallesu baki daya da murmushi a fuskancshi yace "Daddy Usman ne"
Jawad yace "kace sirikinka ne"
Ya jefeshi da harara.
Mancy tace "kai wani irin Gudu Daddy Usman keyi haka? Har ya isa kenan".
Jin tashin hankali sukayi a muryan Abdulmajeed.
"Inallilahi wa ina ilaihir rajiun, mai ya sameshi? Yanzu yana ina?".
Kowa na cikin parlorn ya fara tambaya mai ya sami Uncle
Usman.
Kasa magana yayi sai da Abban yace "Kai Abdulmajeed, ka gaya mana mai ya samu Daddyn naku?".
Abdulmajeed kamar yayi kuka yace "Abba hadari Daddy Usman yayi a Charanci, ya bige wani mutjmi har mutumin ya mutu amma shi Daddyn yana Asibiti ba abunda ya sameshi sai dai wai ya bugu a kai".
Tunda ya fara magana suke Salallami da Salati.
Abba cike da kidima ya ciro wayarshi ya kira chan Katsina gidan Iyayenshi ya sanar dasu, da su je Charanchi yanzu yana nan tahowa gobe InshaAllah.
Ya Kalli Iyalanshi da sukayi saye cirko cirko yace musu "ku shirya, gobe inshaAllah zamuje Katsina".
Amsa mishi sukayi duk jikinsu a sanyayye
K A T S I N A
Ai yayewa akayi a Unguwar Alkali harta Hajiarsu Alhajin suka kwasa suka nufa Charanci har su Aishan.
Kafin su je an gano Gidansu Mamacin, suka shiga akayi magana, Allah ya sa Saurayi ne, baida Iyali, Mahaifiyarshi kam taci kuka sosai amma ta yafe Wanda ya bamkeshi yayi kaffara, aka rufo mamacin.
Basu kwana a Charanci ba suka wuto Katsina.
Asibiti zaayi dashi yace shi dai donAllah a kaishi Gidanshi don ya tsorata sosai da abunda ya faru.
Tunda suka dawo Gida ake zuwa yi musu jaje ko wani lungu da sak'o, gidanshi ma bude ya kwana saboda masu shiga da fita, wasu sun kasa hakura safiya tayi su zo, abunku da 'yan dangi.
*
'Yan Abuja tun safe wurin 8 suka fito, Mota biyu sukayi, AbdulMajeed ke jan Abba da Matanshi Umma da Mancy, sai Abdulhafiz ke jan Matarshi Ummita da Jawad da Mimi, a tare suke taafiya ba'a gudu da Abba, shiyasa suke dadewa akan hanya, sai da suka tsaya a Zaria suka ci Abinci a Shagalinku kafin suka sake daukan hanya.
Sun iso Charanci wurin Karfe2, tambaya sukayi gidan da aka banke wani Jiya, har kofar Gidan aka kaisu, suka shiga, sai kallonsu ake tayi aka dai gaigaisa.
Abba yace "ina Mahaifan yaro?"
Aka gwada musu Uwarshi.
Yace "Uba fa?"
Akace ya dade da rasuwa.
Abba ya gabatar da kanshi a matsayin Yayan wanda ya banke mata da, ya roke su gafara, mahaifiyar yaro tace "wallahi Alhaji, lokacin Saminu ne yayi, K'anenka ne sila, amma lokaci yayi ba wata dabara da zai tsaida tafia".
Matar ta burgesu, nan aka musu karamci aka kawo musu ruwa fiya wota (pure water) da damammen fura.
Ba wanda bai sha furan nan ba sai mimi da bata shan fura, suka sha
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32 Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45