"Wallahi dubu daya tace, ashe dama kai ka dauka, in kace kana so ai DanMakaho dubu daya ba komai bace, zan baka, amma meyasa zaka daukar man kudi?".
Daddy yace "Zaka sake kudin nan ko sai ranka ya baci?" sai da Daddy ya sake maimaitawa kafin ya sakar, ran Daddy a bace yace "Shege Barawon Banza, kaji haushi" halbi Zaid yayi da Bokitin Wanki, ya shige daki rai a dagule.
***
Zaune suke gaba ki daya , Fira sukeyi har Yara suna dariya, daga bisani sukaji an fara iface iface, sosai su ke jin abunda ke faruwa daga kan tabarmar da suke zaune,
Labiba ta mik'e da sauri ta k'arasa jikin Bangon Gidan, nan taji komai,
Girgiza ka ta farai kamar k'adangaruwa, "Wallahi ba sata yayi ba, Aunty Aseeyah wallahi dubu daya ta ce, kudina ne, ni na bashi, Aunty DanMakaho ba Barawo bane, Ya Illahi".
°°°°°°°
Kindly Vote and Comment Line by Line
#1love
#DM
#anatare
#™SonSo
#FWA
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DANMAKAHO 😉
4⃣
Rikota tayi da hannu biyu, "Labiba, ki yi min magana". Naunayar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta bata labarin abun da ya faru dazun.
Aunty Aseeyah tace "Labiba, akwai abubuwa da yawa dake faruwa gidan Alhaji Ali Zaki, tun kafin zuwanmu Unguwar nan, ba zaki gane ba, amma akwai 6oyayyen alamari tsakanin duk wani rai da ke cikin gidan, wanda ba hurumin mu bane, ba mu da wata alak'a dasu da ta wuce makwafataka".
Labiba ga kalli Matar Yayanta " Aunty, Hakkin Makwaftaka fa? wannan babban hak'k'i ne, ya kamata a yi wani abu a kai, so biyu ina jin Makirar Matar nan na hada makircinta, ba zata tsaya a nan ba, ba za kuma ta bari ba, ya kamata Aunty a tari Alhaji Zakin".
"Hmm, Labiba, fadan da ya fi k'arfinka sai ka maida shi wasa, ba abunda za mu iya yi. Hajia Shafa, ta zarce tunaninki, bana son matsala da Hajia Shafa, yanda ba abunda ya taba hada mu, bana son komai ya hadamu, amma tabbas Dan Makaho da k'anwarshi na buk'atar Addu'a, shi kawai zamu taya su".
Hannu ta sa ta ja dankwalinta baya, murya k'asa k'asa tace " Sakarai! Kamar ba namiji ba, ba ya iya kare kanshi? Meyasa be iya k'aryatasu in sun mishi sharri? Mts"
Aunty Aseeyah tace "Magana kike?" girgiza kai tayi tare da mik'ewa ta shige daki
5/5/2013
1:30pm
Tunda garin Allah ya waye zuciyarta ke mata kitse-kitse, DANMAKAHO k'wak'walwarta ke kwada ma kira, baza ta iya shaidashi a hanya ba don ba saninshi tayi ba, dalili take so ya sa ta ga DanMakaho, kamar shekaran jiya, da tunaninshi ta tashi, ta damu da lamarinshi, abu kamar a film ko a littafan hausa, so take ta shiga rayuwarshi, so take taji damuwanshi, abun da kamar wuya, amma sosai take so ta hadu dashi, haduwarsu ta farko in brief ne, ko ganin fuskarshi ba ta samu tayi ba, gashi yau ba ta zuwa Makaranta balle ta sa ran ganinshi a Waje, haka kurum ta tsiri zuwa Gidansu Aisha.
Yara na Tahfiz, Parlo ta iske Yayanta da Matarshi, a gefen Kujera ta zauna tana musu murmushi "Yaya, ina neman izinin zuwa Gidansu Aisha Usman, Mamarsu ke son ganina, har cewa tayi in ban zo ba, ita zata zo".
Dan dariya sukayi kafin Yayan yace "Kinsan Gidan ne?" Girgiza kai tayi alamun aa kafin tace "kwatance ta min" yace "to bari naci Abinci na saukeki" tace "to shikenan nagode".
*
Da kwatance suka gano Gidansu Aisha, dari biyu ya bata yace " ki hau Adaidaita sahu, kuma kar ki kai Maghrib"
Godia ta mishi, Aisha ta gaisheshi sannan suka shiga Gida.
Ina za'a saka Labiba don murna, tunda ta tako cikin gidansu Aisha ta ke cin karo da Soyyayar mutanen gidan, har Mai aikinsu ta san Labeeba, da kaunar da ke tsakaninsu.
Ya Illahi, haka suke sonta? Barin ma Mamar Aisha da take ji kamar ta goyata, kayan mak'ulashe a ka cika gabanta, daga bisani a ka kawo mata Abinci mai rai da lafia, ita dai Labiba daria take tayi, tana cikin cin Samosa Aisha ta k'atseta da cewa "Zo muje ki gaida Daddy".
Kunya ya kama Labiba, "DonAllah ki bari sai anjima" Aisha bata saurareta ba, sai jan hannunta tayi don ta mik'e tsaye tare da janta ta na gaba Labiba na bin ta a baya.
Har k'asa ta durkusa ta gaida Daddy, Daddy ya amsa cikin kulawa ya dauko dubu biyu ya bata, bata iya amsa ba sai dai Aisha ta amsar mata sukayi Godia suka koma dakinsu Aishan. Sai da Laasar yayi suka yi Alwala don yin Sallah.
Labiba na adduointa ta ji kamar ihu daga waje, sai da ta kasa kunnuwanta sai taji ashe Ihun murna ne da alamun bak'i sukayi, tashi tayi ta ninke Darduma, ta zauna gami da tsiyayo kunun Aya a Cup. Aisha ce ta shigo fuskarta dauke da murna. "Besty kinsan me? Cousins dinmu ne sukazo daga Abuja wallahi dadi kamar ya kasheni".
Labiba tace "Inye, fatan sunzo Lafiya" "Lafiya lau wallahi, taso muje ku gaisa" hararar wasa ta jefeta dashi, ta dan muskuta tace "tafiya zanyi ni, banason marace yayia ina waje, kuma dai zaun daura Sanwar dare" Aisha ta san ta mata tunda tun bayan Azahar tazo, don tace zata tafi yanzu ba wani abu ne. Mikewa tayi tace to "barin sanar da Mama".
Labeeba tace "ke dai jira mu tafi tare, katon gyalenta Khashka me kauri ta yafa, Aisha kuma ta janyo wata yar gyale bayan ta mata packaging su Samosa da Springrolls tace a kai ma su Ameera.
Ba ta Parlor inda ta barsu, ba dai har sun tashi ba? Da sauri ta ja hannun Labeeba sukayi tsakar Gida, inda ta gansu tsaitsaye, kallo ta bisu dashi kafin tace "Yaya Hafeez ba dai kun fito ba". "wallahi kuwa A'i, gwara muje mu gaida Hajia Kaka kafin ta kira Abba tace Munfi Awa 8 a katsina bamuje mun gaisheta ba".
Dariya sukayi gabaki daya, Mama tace za kuci Gidanku, Sirrikar tawa kuke ma iyashege?" daria suka sakeyi. Mama tace "Af! Labeeba ba dai kin fito ba" ta dan k'araso garesu cikin takunta tace "Wallahi Mama gwara na tafi, Marece yayi" Mama tace "eh Gaskia ne".
Dukkansu Maza Ukun idanuwansu suka zuba ma Labeeba, idanuwa taji a kanta, ta dan dago ta kallesu su ukun a lokaci daya tace "Ina wuninku? Kunzo lafiya?" amsawa sukayi a tare suna kallonta sosai, Aisha tace "Besty, wadannan sune yanuwana rabin Jikina, kika tsaga tsokata Jininsu kawai zaki gani".
Dariya Labeeba keyi wanda ke k'ara ma fuskarta kyau, ta cigaba da sauraron Aisha, "ga Yaya AbdulHafiz ga Yaya Abdulmajeed kuma ga Yaya Jawad, yau yau dinnan suka zo daga Abuja don Sada zumunci" wani murmushin ta sakeyi, tace "Barkanku da zuwa Katsina ta dikko Ya Abdulhafiz Ya Abdulmajeed da Yaya Abdul-" ta dan yi shiru tana son tuno sunan gudan, wanda suka kurawa junansu ido shi da ita, murmshi ya mata ya girgiza kai yayi yace "ba Yaya Abdul bane, Yaya Jawad ne" kamar bitar karatu ta maimaita "Yaya Jawad".
Aisha ta katsesu tace "Brothers, ga Besty ta, Labiba Ahmad" a tare sukace "Labiba" Mama ta dan murmusa tace "cikinku wa zan ba Diyata?" ta fada tana dafa Labibar da tayi saurin sadda kai k'asa".
Yaya Abdulmajeed yayi karaf yace "Ni zaki ba Antisco, Yaya Hafiz na da Mata, dama nine online, kinga sai in hada da Aminiyarta na aure, kinga no kishi".
Aisha ta harareshi, tace "sai me don na hada Miji da Besty ai ba wani abu bane, ba dai kai bane Mijin"
Dariya Ya Majeed yayi yace "to ni nace ke na ke nufi ne? Nidai Antisco ina so" Mama ta yi Daria, ta maida dubanta ga wanda take ma Labiba kwadayi tace "Jawad fa?" murmushi kawai yayi da ya sake kallon Labiba.
Ya Hafiz yace "nifa bangane ina da Mata ba, don ina da Mata sai aka ce ba zan iya sake ta biyu ba?".
Antisco tayi daria tace "to zan raba gardama, kuzo ayi tseren gudu, wanda ya riga zuwa bakin Gate, shi zan ba damar daidaitawa da Diyata Labiba".
Kafin ta rufe baki tuni Jawad ya ruga a guje ya isa bakin gate daria suka sa baki dayansu, Abdulmajeed yace "Cheating! Ni fa Mancy ban shirya ba, gaskia a sake" Mama tace "Wani ya hanaka shiri da wuri? Ni Jawad na ba dama" Ya Majeed ya cubune fuska yace "dama Antisco na lura kin fi san Jawad" Daria suka sa baki daya.
Labiba tayi saurin katsetsu da cewa "barin tafi, yamma na k'arayi" Mama tace "ki tsaya su Jawad su sauke ki sai Aisha ta raka ki" Labiba tace "Baban Amira Zaiyi fada, bari dai in samu Keke Napep" duk sai ta burgesu duka.
Mama tace "Gaskia ne, to besty mungode, mungode Allah saka da Alheri, ki gaida Aunty Aseeyar da yaranta" Labiba tayi murmushi jin sunan da Mama ta kirata dashi wai 'Besty' tace "sai anjimanku" tayi Gaba Aisha ta bita a baya.
"Nidai Antisco wallahi tayi min ina so" Jawad ke fadin maganar nan, Antisco tace "dagaske Jawad?" "wallahi Antisco" Mama tace "maza je ka karbo numberta, gwara ta baka da hanunta" da dan gudugudu ya bi bayansu, har sun fita bakin gate, k'arasawa yayi gunsu yana dan haki, Aisha tace "Ya Jawad ya akayi ne kake gudu?" wani kallo me wuyar fassaruwa yabi Labiba dashi tare da cewa, "Zuciyata na biyo, zuciyata, ta tafi dashi" tafi Aisha tasa, ita kuma Labiba ta rufe fuskarta da hannu biyu.
Dan gefe Aisha ta tsaya don basu wuri su dan tautana.
Kallonta yake cikin ido, duk jarumta irin tata sai da ta kasa jure kallon, sadda kanta tayi k'asa, cike da shauk'i Jawad yace "Labee" da sauri ta dago ta kalleshi, jin sunan da ya kirata dashi, murmushi mai nuna jin dadi ta mishi.
"Ba zan tsayar da ke ba, Yamma nayi, ki bani numbernki DonAllah" "ka karba gurin Aisha" girgiza kai yayi da sauri yace "Haram, ke zaki bani da hannunki, in kuma hanani zakiyi shikenan" yayi fuskan tausayi kamar mai shirin kuka.
Dan daria tayi me k'ayatarwa tace "be maka kyau ba" ya dan kallota yace "mene?" tace "shagwabar mana" dan bubbuga k'afa ya fara yi kamar dan yaro, da sauri tace "Ya hakuri Baby kar ka tara min jama'a kawo wayar na sa ma".
"Baby,Wow, sunan da aka bani yayi dadi" da sauri ta girgiza kanta da hannuwanta bibbiyu kamar mai yin bye bye tace "ni fa ba wannan Babyn nake nufi ba, naga kana abun yara ne shiyasa na kiraka da Baby". Kafadunshi ya daga " Oho, nidai zan dauka a matsayin Dayan, yanzu dai gashi ki samin number" karba tayi ta sa Numberta.
Tsaida mata Keke Napep sukayi, Jawad ya bude mata k'ofa yace "kin k'i yarda na kaiki Gida ko?" murmushi tayi tace "Bye Ya Jawad" lumshe ido yayi ya bude "Good bye Labee" Aisha ta bude baki ganin yanda Bestynta da danuwanta suka shagala da aika wa junansu sak'onni, "Hello! An manta dani ko? To ina wurin besty?" Kunya ya sa Labeeba rufe fuska tana daria, ta umarta mai Keke Napep da su wuce.
***
5:45pm
Tuk'i Yaya Hafiz keyi cike da nutsuwa, sun fito daga Unguwar Alk'ali Gidan Kakarsu, zasu tafi su aje Sak'o kafin su wuce Masauki don Gobe zasu wuce Abuja.
Yaya Hafiz yace "Yauwa Majeed, kira Yaron Mancy mu biya mu kai mai sak'on nan don ni gaskia nagaji ni da fita sai gobe".
AbdulMajid ya ciro wayarshi daga Aljihu ya latso numbern da Mancy ta bashi, har wayar ta katse ba a dauka ba, sake dialing yayi nan ma ba answer.
"Ba ya dauka fa" cewar Majeed, Hafiz yace "Kira Mancy ka gaya mata" dialing Numbern Mancy din yayi ringing na biyu ta dauka.
"Assalam Majeed" ta fada cike da Murna, "Hello Mancy ina wuni, dama mun ta kiranshi dan mu bashi sak'on be dauka ba" "Oh Allah, sorry na wahalar daku, ko ku barshi" Majeed yace "haba Mancy, har muzo gari kuma mu juyo da sak'o? Ba wani abu bari na sake kira InshaAllah zamu sameshi".
"Nagode sosai, bari nima in kira k'anwarshi in ba ya nan sai ta amsa" nan suka katse wayar.
Tudun Matawallen suka nufa kamar yanda Mancy ta gaya musu.
Majeed be fasa trying numbern shi ba, Jawad har ya k'ulu, shi fa be son bacin lokaci, tsaki ya sake yi, shi ba Fan din Mancy bane, be kuma k'inta, kawai dai bata cikin 'yan kayanshi kamar yanda yayyunshi biyu ke yinta.
Sun fi minti 10 a cikin Tudun Matawalle basu san inda zasu ba, sake kiran Mancy Majeed yayi tace "kuyi hakuri, wallahi wayar k'anwar tashi kashe take, na kuma ta kiranshi be dauka ba wallahi, kuyi tafiarku kawai Majeed".
"To Mancy ya sunan Maigidan sai muyi sallama mu bada a ajiye musu" dan jim tayi na wasu sakwanni kafin tace "kawai Majeed ku dawo ba wani abu" ba ya so ya matsa sai cewa yayi "to Mancy, amma banji dadi ba" ya kashe wayar ya ce masu "tace a bari kawai, amma banji dadi ba wallahi".
A k'ufule Jawad yace " to ya zamuyi, nan zamu lallace? Ya Hafiz mu tafi please" ta Mirror Hafiz ya kalli k'aninshi da harara yace "Jawad!!!" kawar da kai yayi, Hafiz yace "Majeed sake kira" Majeed yace "for the 14th time, Allah ka sa ya dauka".
Bencin Eskaley
World DanMakaho ya zuk'a, sarauta ta sa mai, k'afa daya kan daya ya daura, yana kallon kowa a dage, me tsautsayi kawai zai shiga harkanshi yau, yanda yake jin kanshi tsaf zai kakarya mutum.
Master da su Haruna ke buga Whot, suna yi suna busar sigari, yau ma basu da arzikin siyan World,sunyi ma Eskaley Magiya amma fir ya k'i basu".
"Wai Mankas ba wayarka ke k'ara ba tun dazun, kusan so 10?" Haruna yace "yo ina zai iya dauka, World fa ya ta6a" Master yace "yo in baka dauka ka kashe shegia mana, ni nan ta cikan kunne"
Tsaki Eskaley ya buga ya mik'e ya nufa Mankas hannu ya sa a Aljihun gaba inda Wayar ke k'ara, dauka yayi kafin ya amsa da "Hello?".
"Eh Hello, Zaid?" daga bangaren Eskaley yace "Eh to ba Zaid din bane" daga dayan bangaren a ka ce "DonAllah gamu a Tudun Matawalle, sak'o aka bamu daga Abuja mu kawo ma Zaid, don Allah ina zamu sameshi?" Eskaley yace "kuna ta ina?" "mun dan shiga cikin Anguwar" "Ayya, ku dawo farkon Anguwar, akwai wani kiosk nan Yellow".
Eskaley ya kalli su Master yace "Daga Abuja aka aiko wasu gun Mankas, gashi Mankas na birnin Sin ya zaayi?" Master yace "to ya fa? Uban kowa ya san Mankas na eh ya ne".
Horn sukaji na wani mota bak'a k'irar 507, duk suka tashi don yau kakarsu ta yanke sak'a.
Wayar Mankas ta sake ringingin Eskaleh ya dauka " Hello? Kaine a bakar Mota? Eh nan ne, barin zo" Eskaley yayi gaba, su Master na binshi a baya.
Ta Window suke kallon masu tunakaro su, "'Yan Shaye-Shaye ne" cewar Jawad "Mai ya hada yaron Mancy da Shaye-Shaye?" inji Hafiz, ba su da wannan amsar illa fitowa da sukayi gabaki dayansu.
Musabaha sukayi da dukkansu harda Jawad da ya mik'a musu hannu a kyamace, su ko 'yan bencin Eskaley kamar su musu Sujjada don biyayya, Hafiz ya kallesu daya bayan daya, ya lura duk ba na kirki cikinsu, duk warin Sigari suke, daurewa dai yayi magana yace "Ina Zaid?" Master da Haruna suka kalli juna suna tunanin waye Zaid? Shaf sun manta da wani Zaid".
Kafin Master yace "au Mankas? Gashi chan baya, in sak'o ne ku kawo a bashi" Majeed yace "Aa, hannu da hannu zamu bashi" Haruna yace "Ai Mankas ya hau network, ba zai gane bayanin da zaku mishi ba, mune Aminnanshi".
" DanUwarku Mahaukaci ne ni da ba zan gane bayani ba?" gabaki dayansu suka juya, Mankas ne ke tunkaro su, tuni Master da Haruna suka matsa mai ya k'araso yana k'are musu kallo duk a dage, ya tsaya kan Jawad mai kallonshi a k'yamace, Mankas ya wurga mishi mugun kallo shima kafin ya kalli su Master yace Duk ku ware?".
Hafiz ya mik'a mishi hannu, k'in amsa yayi, ran Jawad ya mugun baci, Majeed yace "Zaid, Mancy ce ta bamu sak'o mu baka".
Runtse ido yayi da k'arfi ya bude, tuni ya dawo hayyacinsa, Hafiz ya nufa da sauri ya dan durkusa " DonAllaj kayi hak'uri babban Yaya kuyi hakuri, wallahi akasi aka samu" daga yanda yake magana sun san a buge yake, yana dai k'okari ya dawo hayyacinsa ne.
Hafiz ya girgiza kai yace "Zaid, Mancy Mutuniyar kirki ce, donAllah ka bar Shaye-Shaye" da sauri Zaid yace "Wallahi na bari, ba zan k'ara dama yau na fara" sun san ba gaskia ya fada ba amma dai suka share" Majeed ya bude Booth ya dauko Ghana MustGo dan k'arami ya mik'a mishi.
Karba yayi, yace "nagode, Allah tsareku, ko uban wa ya tabaku ku gayan naci uwar mutum, duk garin Katsina, ko da kuwa Sarkin Katsina ne".
Takaici ya sa Jawad saurin fadawa Mota, Majeed ya girgiza kai yana mai fatan shiriya, shiko Hafiz da yake Ustazu ne sai da ya sake masu Mankas da abokanshi nasiha kan su bar Shaye-Shaye.
Nan suka fara mishi rantsuwar kaffara kan sun daina ba za su sake ba. Master har yana k'arawa da cewa dama don rashin abun yi ne ya sa suke Shaye-Shaye. Hafiz kudi ya ciro kusan 10k ya basu.
Master yayi wuf ya amshe tare da zuba Godia kamar zasu goyasu. Addua suka dinga zuba musu har Hafiz ya shige Mota ya ja suna mishi byebye.
Mankas be tsaya bin ta kudin da aka basu ba ya dauki ghanar nan ya danna a guje yayi Gida kamar wani zararre.
Su ko su Master yau take Sallah, World suka siya kowa qulli biyar biyar.
Washegari
5/05/2013
Tashi sukayi yau ba ruwa a Gidan, Drums dinsu empty, dama da k'yar suka samu Ruwan Alwala da Asuba, ko ruwan da zasu dafa suyi kalaci basu dashi.
"Oh ni Labiba ya zamuyi? Gashi Baban Amira bacci yake yi balle yaje nemo mai ruwa, bansan tadashi wallahi" Labiba tace "to Aunty Aseeyah ko in fita inga in zan samu mai Ruwan?" dan shiru tayi tace "Oh, ko zaki dan lek'a Gidan Alhaji Zaki ki samo mana a Kettle? Naga su borehole garesu".
Ba tare da wani tunani ba tace "eh wallahi
Showing 6001 words to 9000 words out of 132816 words
Daddy yace "Zaka sake kudin nan ko sai ranka ya baci?" sai da Daddy ya sake maimaitawa kafin ya sakar, ran Daddy a bace yace "Shege Barawon Banza, kaji haushi" halbi Zaid yayi da Bokitin Wanki, ya shige daki rai a dagule.
***
Zaune suke gaba ki daya , Fira sukeyi har Yara suna dariya, daga bisani sukaji an fara iface iface, sosai su ke jin abunda ke faruwa daga kan tabarmar da suke zaune,
Labiba ta mik'e da sauri ta k'arasa jikin Bangon Gidan, nan taji komai,
Girgiza ka ta farai kamar k'adangaruwa, "Wallahi ba sata yayi ba, Aunty Aseeyah wallahi dubu daya ta ce, kudina ne, ni na bashi, Aunty DanMakaho ba Barawo bane, Ya Illahi".
°°°°°°°
Kindly Vote and Comment Line by Line
#1love
#DM
#anatare
#™SonSo
#FWA
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DANMAKAHO 😉
4⃣
Rikota tayi da hannu biyu, "Labiba, ki yi min magana". Naunayar ajiyar zuciya ta sauke kafin ta bata labarin abun da ya faru dazun.
Aunty Aseeyah tace "Labiba, akwai abubuwa da yawa dake faruwa gidan Alhaji Ali Zaki, tun kafin zuwanmu Unguwar nan, ba zaki gane ba, amma akwai 6oyayyen alamari tsakanin duk wani rai da ke cikin gidan, wanda ba hurumin mu bane, ba mu da wata alak'a dasu da ta wuce makwafataka".
Labiba ga kalli Matar Yayanta " Aunty, Hakkin Makwaftaka fa? wannan babban hak'k'i ne, ya kamata a yi wani abu a kai, so biyu ina jin Makirar Matar nan na hada makircinta, ba zata tsaya a nan ba, ba za kuma ta bari ba, ya kamata Aunty a tari Alhaji Zakin".
"Hmm, Labiba, fadan da ya fi k'arfinka sai ka maida shi wasa, ba abunda za mu iya yi. Hajia Shafa, ta zarce tunaninki, bana son matsala da Hajia Shafa, yanda ba abunda ya taba hada mu, bana son komai ya hadamu, amma tabbas Dan Makaho da k'anwarshi na buk'atar Addu'a, shi kawai zamu taya su".
Hannu ta sa ta ja dankwalinta baya, murya k'asa k'asa tace " Sakarai! Kamar ba namiji ba, ba ya iya kare kanshi? Meyasa be iya k'aryatasu in sun mishi sharri? Mts"
Aunty Aseeyah tace "Magana kike?" girgiza kai tayi tare da mik'ewa ta shige daki
5/5/2013
1:30pm
Tunda garin Allah ya waye zuciyarta ke mata kitse-kitse, DANMAKAHO k'wak'walwarta ke kwada ma kira, baza ta iya shaidashi a hanya ba don ba saninshi tayi ba, dalili take so ya sa ta ga DanMakaho, kamar shekaran jiya, da tunaninshi ta tashi, ta damu da lamarinshi, abu kamar a film ko a littafan hausa, so take ta shiga rayuwarshi, so take taji damuwanshi, abun da kamar wuya, amma sosai take so ta hadu dashi, haduwarsu ta farko in brief ne, ko ganin fuskarshi ba ta samu tayi ba, gashi yau ba ta zuwa Makaranta balle ta sa ran ganinshi a Waje, haka kurum ta tsiri zuwa Gidansu Aisha.
Yara na Tahfiz, Parlo ta iske Yayanta da Matarshi, a gefen Kujera ta zauna tana musu murmushi "Yaya, ina neman izinin zuwa Gidansu Aisha Usman, Mamarsu ke son ganina, har cewa tayi in ban zo ba, ita zata zo".
Dan dariya sukayi kafin Yayan yace "Kinsan Gidan ne?" Girgiza kai tayi alamun aa kafin tace "kwatance ta min" yace "to bari naci Abinci na saukeki" tace "to shikenan nagode".
*
Da kwatance suka gano Gidansu Aisha, dari biyu ya bata yace " ki hau Adaidaita sahu, kuma kar ki kai Maghrib"
Godia ta mishi, Aisha ta gaisheshi sannan suka shiga Gida.
Ina za'a saka Labiba don murna, tunda ta tako cikin gidansu Aisha ta ke cin karo da Soyyayar mutanen gidan, har Mai aikinsu ta san Labeeba, da kaunar da ke tsakaninsu.
Ya Illahi, haka suke sonta? Barin ma Mamar Aisha da take ji kamar ta goyata, kayan mak'ulashe a ka cika gabanta, daga bisani a ka kawo mata Abinci mai rai da lafia, ita dai Labiba daria take tayi, tana cikin cin Samosa Aisha ta k'atseta da cewa "Zo muje ki gaida Daddy".
Kunya ya kama Labiba, "DonAllah ki bari sai anjima" Aisha bata saurareta ba, sai jan hannunta tayi don ta mik'e tsaye tare da janta ta na gaba Labiba na bin ta a baya.
Har k'asa ta durkusa ta gaida Daddy, Daddy ya amsa cikin kulawa ya dauko dubu biyu ya bata, bata iya amsa ba sai dai Aisha ta amsar mata sukayi Godia suka koma dakinsu Aishan. Sai da Laasar yayi suka yi Alwala don yin Sallah.
Labiba na adduointa ta ji kamar ihu daga waje, sai da ta kasa kunnuwanta sai taji ashe Ihun murna ne da alamun bak'i sukayi, tashi tayi ta ninke Darduma, ta zauna gami da tsiyayo kunun Aya a Cup. Aisha ce ta shigo fuskarta dauke da murna. "Besty kinsan me? Cousins dinmu ne sukazo daga Abuja wallahi dadi kamar ya kasheni".
Labiba tace "Inye, fatan sunzo Lafiya" "Lafiya lau wallahi, taso muje ku gaisa" hararar wasa ta jefeta dashi, ta dan muskuta tace "tafiya zanyi ni, banason marace yayia ina waje, kuma dai zaun daura Sanwar dare" Aisha ta san ta mata tunda tun bayan Azahar tazo, don tace zata tafi yanzu ba wani abu ne. Mikewa tayi tace to "barin sanar da Mama".
Labeeba tace "ke dai jira mu tafi tare, katon gyalenta Khashka me kauri ta yafa, Aisha kuma ta janyo wata yar gyale bayan ta mata packaging su Samosa da Springrolls tace a kai ma su Ameera.
Ba ta Parlor inda ta barsu, ba dai har sun tashi ba? Da sauri ta ja hannun Labeeba sukayi tsakar Gida, inda ta gansu tsaitsaye, kallo ta bisu dashi kafin tace "Yaya Hafeez ba dai kun fito ba". "wallahi kuwa A'i, gwara muje mu gaida Hajia Kaka kafin ta kira Abba tace Munfi Awa 8 a katsina bamuje mun gaisheta ba".
Dariya sukayi gabaki daya, Mama tace za kuci Gidanku, Sirrikar tawa kuke ma iyashege?" daria suka sakeyi. Mama tace "Af! Labeeba ba dai kin fito ba" ta dan k'araso garesu cikin takunta tace "Wallahi Mama gwara na tafi, Marece yayi" Mama tace "eh Gaskia ne".
Dukkansu Maza Ukun idanuwansu suka zuba ma Labeeba, idanuwa taji a kanta, ta dan dago ta kallesu su ukun a lokaci daya tace "Ina wuninku? Kunzo lafiya?" amsawa sukayi a tare suna kallonta sosai, Aisha tace "Besty, wadannan sune yanuwana rabin Jikina, kika tsaga tsokata Jininsu kawai zaki gani".
Dariya Labeeba keyi wanda ke k'ara ma fuskarta kyau, ta cigaba da sauraron Aisha, "ga Yaya AbdulHafiz ga Yaya Abdulmajeed kuma ga Yaya Jawad, yau yau dinnan suka zo daga Abuja don Sada zumunci" wani murmushin ta sakeyi, tace "Barkanku da zuwa Katsina ta dikko Ya Abdulhafiz Ya Abdulmajeed da Yaya Abdul-" ta dan yi shiru tana son tuno sunan gudan, wanda suka kurawa junansu ido shi da ita, murmshi ya mata ya girgiza kai yayi yace "ba Yaya Abdul bane, Yaya Jawad ne" kamar bitar karatu ta maimaita "Yaya Jawad".
Aisha ta katsesu tace "Brothers, ga Besty ta, Labiba Ahmad" a tare sukace "Labiba" Mama ta dan murmusa tace "cikinku wa zan ba Diyata?" ta fada tana dafa Labibar da tayi saurin sadda kai k'asa".
Yaya Abdulmajeed yayi karaf yace "Ni zaki ba Antisco, Yaya Hafiz na da Mata, dama nine online, kinga sai in hada da Aminiyarta na aure, kinga no kishi".
Aisha ta harareshi, tace "sai me don na hada Miji da Besty ai ba wani abu bane, ba dai kai bane Mijin"
Dariya Ya Majeed yayi yace "to ni nace ke na ke nufi ne? Nidai Antisco ina so" Mama ta yi Daria, ta maida dubanta ga wanda take ma Labiba kwadayi tace "Jawad fa?" murmushi kawai yayi da ya sake kallon Labiba.
Ya Hafiz yace "nifa bangane ina da Mata ba, don ina da Mata sai aka ce ba zan iya sake ta biyu ba?".
Antisco tayi daria tace "to zan raba gardama, kuzo ayi tseren gudu, wanda ya riga zuwa bakin Gate, shi zan ba damar daidaitawa da Diyata Labiba".
Kafin ta rufe baki tuni Jawad ya ruga a guje ya isa bakin gate daria suka sa baki dayansu, Abdulmajeed yace "Cheating! Ni fa Mancy ban shirya ba, gaskia a sake" Mama tace "Wani ya hanaka shiri da wuri? Ni Jawad na ba dama" Ya Majeed ya cubune fuska yace "dama Antisco na lura kin fi san Jawad" Daria suka sa baki daya.
Labiba tayi saurin katsetsu da cewa "barin tafi, yamma na k'arayi" Mama tace "ki tsaya su Jawad su sauke ki sai Aisha ta raka ki" Labiba tace "Baban Amira Zaiyi fada, bari dai in samu Keke Napep" duk sai ta burgesu duka.
Mama tace "Gaskia ne, to besty mungode, mungode Allah saka da Alheri, ki gaida Aunty Aseeyar da yaranta" Labiba tayi murmushi jin sunan da Mama ta kirata dashi wai 'Besty' tace "sai anjimanku" tayi Gaba Aisha ta bita a baya.
"Nidai Antisco wallahi tayi min ina so" Jawad ke fadin maganar nan, Antisco tace "dagaske Jawad?" "wallahi Antisco" Mama tace "maza je ka karbo numberta, gwara ta baka da hanunta" da dan gudugudu ya bi bayansu, har sun fita bakin gate, k'arasawa yayi gunsu yana dan haki, Aisha tace "Ya Jawad ya akayi ne kake gudu?" wani kallo me wuyar fassaruwa yabi Labiba dashi tare da cewa, "Zuciyata na biyo, zuciyata, ta tafi dashi" tafi Aisha tasa, ita kuma Labiba ta rufe fuskarta da hannu biyu.
Dan gefe Aisha ta tsaya don basu wuri su dan tautana.
Kallonta yake cikin ido, duk jarumta irin tata sai da ta kasa jure kallon, sadda kanta tayi k'asa, cike da shauk'i Jawad yace "Labee" da sauri ta dago ta kalleshi, jin sunan da ya kirata dashi, murmushi mai nuna jin dadi ta mishi.
"Ba zan tsayar da ke ba, Yamma nayi, ki bani numbernki DonAllah" "ka karba gurin Aisha" girgiza kai yayi da sauri yace "Haram, ke zaki bani da hannunki, in kuma hanani zakiyi shikenan" yayi fuskan tausayi kamar mai shirin kuka.
Dan daria tayi me k'ayatarwa tace "be maka kyau ba" ya dan kallota yace "mene?" tace "shagwabar mana" dan bubbuga k'afa ya fara yi kamar dan yaro, da sauri tace "Ya hakuri Baby kar ka tara min jama'a kawo wayar na sa ma".
"Baby,Wow, sunan da aka bani yayi dadi" da sauri ta girgiza kanta da hannuwanta bibbiyu kamar mai yin bye bye tace "ni fa ba wannan Babyn nake nufi ba, naga kana abun yara ne shiyasa na kiraka da Baby". Kafadunshi ya daga " Oho, nidai zan dauka a matsayin Dayan, yanzu dai gashi ki samin number" karba tayi ta sa Numberta.
Tsaida mata Keke Napep sukayi, Jawad ya bude mata k'ofa yace "kin k'i yarda na kaiki Gida ko?" murmushi tayi tace "Bye Ya Jawad" lumshe ido yayi ya bude "Good bye Labee" Aisha ta bude baki ganin yanda Bestynta da danuwanta suka shagala da aika wa junansu sak'onni, "Hello! An manta dani ko? To ina wurin besty?" Kunya ya sa Labeeba rufe fuska tana daria, ta umarta mai Keke Napep da su wuce.
***
5:45pm
Tuk'i Yaya Hafiz keyi cike da nutsuwa, sun fito daga Unguwar Alk'ali Gidan Kakarsu, zasu tafi su aje Sak'o kafin su wuce Masauki don Gobe zasu wuce Abuja.
Yaya Hafiz yace "Yauwa Majeed, kira Yaron Mancy mu biya mu kai mai sak'on nan don ni gaskia nagaji ni da fita sai gobe".
AbdulMajid ya ciro wayarshi daga Aljihu ya latso numbern da Mancy ta bashi, har wayar ta katse ba a dauka ba, sake dialing yayi nan ma ba answer.
"Ba ya dauka fa" cewar Majeed, Hafiz yace "Kira Mancy ka gaya mata" dialing Numbern Mancy din yayi ringing na biyu ta dauka.
"Assalam Majeed" ta fada cike da Murna, "Hello Mancy ina wuni, dama mun ta kiranshi dan mu bashi sak'on be dauka ba" "Oh Allah, sorry na wahalar daku, ko ku barshi" Majeed yace "haba Mancy, har muzo gari kuma mu juyo da sak'o? Ba wani abu bari na sake kira InshaAllah zamu sameshi".
"Nagode sosai, bari nima in kira k'anwarshi in ba ya nan sai ta amsa" nan suka katse wayar.
Tudun Matawallen suka nufa kamar yanda Mancy ta gaya musu.
Majeed be fasa trying numbern shi ba, Jawad har ya k'ulu, shi fa be son bacin lokaci, tsaki ya sake yi, shi ba Fan din Mancy bane, be kuma k'inta, kawai dai bata cikin 'yan kayanshi kamar yanda yayyunshi biyu ke yinta.
Sun fi minti 10 a cikin Tudun Matawalle basu san inda zasu ba, sake kiran Mancy Majeed yayi tace "kuyi hakuri, wallahi wayar k'anwar tashi kashe take, na kuma ta kiranshi be dauka ba wallahi, kuyi tafiarku kawai Majeed".
"To Mancy ya sunan Maigidan sai muyi sallama mu bada a ajiye musu" dan jim tayi na wasu sakwanni kafin tace "kawai Majeed ku dawo ba wani abu" ba ya so ya matsa sai cewa yayi "to Mancy, amma banji dadi ba" ya kashe wayar ya ce masu "tace a bari kawai, amma banji dadi ba wallahi".
A k'ufule Jawad yace " to ya zamuyi, nan zamu lallace? Ya Hafiz mu tafi please" ta Mirror Hafiz ya kalli k'aninshi da harara yace "Jawad!!!" kawar da kai yayi, Hafiz yace "Majeed sake kira" Majeed yace "for the 14th time, Allah ka sa ya dauka".
Bencin Eskaley
World DanMakaho ya zuk'a, sarauta ta sa mai, k'afa daya kan daya ya daura, yana kallon kowa a dage, me tsautsayi kawai zai shiga harkanshi yau, yanda yake jin kanshi tsaf zai kakarya mutum.
Master da su Haruna ke buga Whot, suna yi suna busar sigari, yau ma basu da arzikin siyan World,sunyi ma Eskaley Magiya amma fir ya k'i basu".
"Wai Mankas ba wayarka ke k'ara ba tun dazun, kusan so 10?" Haruna yace "yo ina zai iya dauka, World fa ya ta6a" Master yace "yo in baka dauka ka kashe shegia mana, ni nan ta cikan kunne"
Tsaki Eskaley ya buga ya mik'e ya nufa Mankas hannu ya sa a Aljihun gaba inda Wayar ke k'ara, dauka yayi kafin ya amsa da "Hello?".
"Eh Hello, Zaid?" daga bangaren Eskaley yace "Eh to ba Zaid din bane" daga dayan bangaren a ka ce "DonAllah gamu a Tudun Matawalle, sak'o aka bamu daga Abuja mu kawo ma Zaid, don Allah ina zamu sameshi?" Eskaley yace "kuna ta ina?" "mun dan shiga cikin Anguwar" "Ayya, ku dawo farkon Anguwar, akwai wani kiosk nan Yellow".
Eskaley ya kalli su Master yace "Daga Abuja aka aiko wasu gun Mankas, gashi Mankas na birnin Sin ya zaayi?" Master yace "to ya fa? Uban kowa ya san Mankas na eh ya ne".
Horn sukaji na wani mota bak'a k'irar 507, duk suka tashi don yau kakarsu ta yanke sak'a.
Wayar Mankas ta sake ringingin Eskaleh ya dauka " Hello? Kaine a bakar Mota? Eh nan ne, barin zo" Eskaley yayi gaba, su Master na binshi a baya.
Ta Window suke kallon masu tunakaro su, "'Yan Shaye-Shaye ne" cewar Jawad "Mai ya hada yaron Mancy da Shaye-Shaye?" inji Hafiz, ba su da wannan amsar illa fitowa da sukayi gabaki dayansu.
Musabaha sukayi da dukkansu harda Jawad da ya mik'a musu hannu a kyamace, su ko 'yan bencin Eskaley kamar su musu Sujjada don biyayya, Hafiz ya kallesu daya bayan daya, ya lura duk ba na kirki cikinsu, duk warin Sigari suke, daurewa dai yayi magana yace "Ina Zaid?" Master da Haruna suka kalli juna suna tunanin waye Zaid? Shaf sun manta da wani Zaid".
Kafin Master yace "au Mankas? Gashi chan baya, in sak'o ne ku kawo a bashi" Majeed yace "Aa, hannu da hannu zamu bashi" Haruna yace "Ai Mankas ya hau network, ba zai gane bayanin da zaku mishi ba, mune Aminnanshi".
" DanUwarku Mahaukaci ne ni da ba zan gane bayani ba?" gabaki dayansu suka juya, Mankas ne ke tunkaro su, tuni Master da Haruna suka matsa mai ya k'araso yana k'are musu kallo duk a dage, ya tsaya kan Jawad mai kallonshi a k'yamace, Mankas ya wurga mishi mugun kallo shima kafin ya kalli su Master yace Duk ku ware?".
Hafiz ya mik'a mishi hannu, k'in amsa yayi, ran Jawad ya mugun baci, Majeed yace "Zaid, Mancy ce ta bamu sak'o mu baka".
Runtse ido yayi da k'arfi ya bude, tuni ya dawo hayyacinsa, Hafiz ya nufa da sauri ya dan durkusa " DonAllaj kayi hak'uri babban Yaya kuyi hakuri, wallahi akasi aka samu" daga yanda yake magana sun san a buge yake, yana dai k'okari ya dawo hayyacinsa ne.
Hafiz ya girgiza kai yace "Zaid, Mancy Mutuniyar kirki ce, donAllah ka bar Shaye-Shaye" da sauri Zaid yace "Wallahi na bari, ba zan k'ara dama yau na fara" sun san ba gaskia ya fada ba amma dai suka share" Majeed ya bude Booth ya dauko Ghana MustGo dan k'arami ya mik'a mishi.
Karba yayi, yace "nagode, Allah tsareku, ko uban wa ya tabaku ku gayan naci uwar mutum, duk garin Katsina, ko da kuwa Sarkin Katsina ne".
Takaici ya sa Jawad saurin fadawa Mota, Majeed ya girgiza kai yana mai fatan shiriya, shiko Hafiz da yake Ustazu ne sai da ya sake masu Mankas da abokanshi nasiha kan su bar Shaye-Shaye.
Nan suka fara mishi rantsuwar kaffara kan sun daina ba za su sake ba. Master har yana k'arawa da cewa dama don rashin abun yi ne ya sa suke Shaye-Shaye. Hafiz kudi ya ciro kusan 10k ya basu.
Master yayi wuf ya amshe tare da zuba Godia kamar zasu goyasu. Addua suka dinga zuba musu har Hafiz ya shige Mota ya ja suna mishi byebye.
Mankas be tsaya bin ta kudin da aka basu ba ya dauki ghanar nan ya danna a guje yayi Gida kamar wani zararre.
Su ko su Master yau take Sallah, World suka siya kowa qulli biyar biyar.
Washegari
5/05/2013
Tashi sukayi yau ba ruwa a Gidan, Drums dinsu empty, dama da k'yar suka samu Ruwan Alwala da Asuba, ko ruwan da zasu dafa suyi kalaci basu dashi.
"Oh ni Labiba ya zamuyi? Gashi Baban Amira bacci yake yi balle yaje nemo mai ruwa, bansan tadashi wallahi" Labiba tace "to Aunty Aseeyah ko in fita inga in zan samu mai Ruwan?" dan shiru tayi tace "Oh, ko zaki dan lek'a Gidan Alhaji Zaki ki samo mana a Kettle? Naga su borehole garesu".
Ba tare da wani tunani ba tace "eh wallahi
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3 Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45