sauri ta bude ta ga Zaid ne.
"Akwai Sauro, zan kwana a nan in har baki fada min wani abu mai dadi ba".
Tashi tayi da sauri ta lek’a ta window ta ganshi a takure, A fili tace “ina abunda ya dameni? Ka kwana nan mtss, kalaman yaudaranka ba zasu yi tasiri a kaina ba”. Hayewa tayi Gado tayi adduar Bacci kafin baccin yayi awon gaba da ita.
Sauron Katsina marasa kunya a gaban idonka ma sai su cijeka balle bayan idonka, haka Saurayen Tudun Matawalle sukayi dinner da DanMakaho, tun yana sosawa, yana kashesu da hannu, yana tsaki gashi bai da abun rufa, taurin kai da ya sa ma ranshi, shi ya hanashi shiga daki ko da ya dauko abun rufa ne, haka dan MAKAHO ya kwana a waje wanda bacci rabi a bude ya yishi, sai gaba da Asuba bacci mai nauyi yayi awon gaba dashi.
Alarm dinta ya tadata, bude dakin tayi ta fito, idonta tsaye yayi chan sashen, wani murmushin takaici tayi tare da mamaki, wai dagaske kwanan yayi a nan? Sai taji zafi kuma, bata ji dadi ba, kamar ta karasa gunshi ta k’yaleshi ta shiga Toilet ta wanko bakinta tare da dauro Alwala, ta shiga kitchen ta dauko babban tukunya ta cikashi taf da ruwa sannan ta janyo risho (stove) ta kunna ta daura tukunyan kafin ta fito daga kitchen din sai da ta sake kallonshi kafinta shige daki k’irjinta na mata nauyi.
Rakaatanil Fajr tayi kafin tayi Asuba tayi zikrorinta na safe kafin ta tashi don tada yara ta musu Wanka yau Monday.
Ta fito rik’e da hannun Ameera, yana nan bai motsa ba.
Itama ta rasa abunyi, yau ko Asuba be yi ba, yana nan yana baccin asara a waje. Baban Amira ne ya turo k’ofar Gidan hannu shi dauke da Bak’in Leda wanda shakka babu Breadi ne da madara da lipton da milo na sachet, wanda duk rannan da zasu sha tea baya dawowa daga Sallahr Asuba sai gari ya waye ya tsaya siyansu.
Ganinshi ya sa Labiba dawowa daga tunaninta kar yace DanMakahon take kallo, tace “Yaya Ina Kwana” ya amsa da “Lafiya lau Aunty Labs” Amira tace “Baba ina kwana” yace “Lafia Amirori wanka zaayi ko?” Tace “uhm” Labiba tayi saurin shigewa Kewaye da Amira ta dauki bokiti ta shiga kitchen ta diba ruwan zafi ta k’ara a na tukunyan ta sirka kafin ta shiga yi ma Amira Wanka.
Kamar dai kullum in yana Gida, Baban Amira ya dauko tsintsiya don Share tsakar Gidan, Aunty Aseey na Kitchen tana hada Tea a dogon Jug, Labiba ta shiga da Amira ta fito da Sabit dan mishi wanka taji muryan Yayanta yana “SubhanAllah, DanMakaho ne chan?”.
Da sauri ta kallesu taga Yayan na k’okarin k’etara Gidan Alh Zaki.
Ta naji Aunty Aseey na cewa “yanzun haka shaye shaye yayi ta kai mai karo shiyasa yayi Mankas a waje”.
Labiba tayi saurin dafe kai.
Mallam Muhammad ya fara bubbuga shi tare da cewa “DanMakaho, tashi gari ya waye fa” firgigit ya tashi a dan tsorace tare da murzan idonshi na hagu.
“Dan Makaho ba dai anan ka kwana ba? Ji cizon sauro ko ina a jikinka”.
Zaid ya bi jikinshi da kallo, ya ga cizon sauro runtuma runtuma.
“Kayi Sallahr Asuba kuwa?” Ya ji Mallam Muhammad na tambayanshi
“Aa” ya girgiza kai.
“Haba DanMakaho, ka san k’arfe nawa yanzu? Bakwai ta yi fa, me ya ja maka rashin Sallah har gari ya waye”.
Idonshi na hagu ya sake murzawa kafin yace “barin shiga ciki”.
Labiba ya kalla wacce tayi saurin kauda idonta kafin ya juya ya shige dakinshi.
Mallam Muhammadu cike da tausayawa ya girgiza kai ya cigaba da sharanshi.
Aunty Aseey ta shige kitchen don cigaba da hada kalaci.
Ita kuma Labiba ta shige daki don shirya Sabit.
Ko da ya shiga Daki, toilet ya wuce direct yayi wanka kafin ya doro Alwala, yazo yayi Sallah rakaa biyu kafin ya zauna a kan kujera yana tunanin Labiba.
Ta tsaneshi har haka?
Har yace mata zai kwana a waje ta ki furta mishi kalma mai dadi?
Dagaske ta bar son shi?
To ko daman ba son shi din takeyi ba tausayinshi take?
“Ba tausayinka nake ba, sonka nake, sosai nake son ka”
Kalamanta ne suka dawo mishi kamar a lokacin take ambaton su a lokacin da yake tambayarta in tausayinshi take.
To ko dai ta sadak’as ne? Son da yake mata ba zai saka ta dole ba, ba zai tilasta mata wurin dawo da son shi a zuciyarta ba, tunani fiye da dubu a kanshi ya rasa abun yi.
Tunda ta shiga daki, take tunani, hankalinta baya wurin shafa man da take yi a jikin Sabit.
“A waje ya kwana?”
Don me zai kwana a waje? Baida hankali ne? Yanzu in malaria ta kamashi fa? Akan me zai kwana waje? Akan me? Ya burgeta ya kuntata ma kanshi a kan me? Oh Allah, ya zatayi? Dagaske ya fara sonta?”.
Muryar Amira taji inda ta ke cemata “Aunty Labs, kina lafta ma Sabit mai a jiki” da sauri hankalinta ya dawo jikin Sabit da aka kusa kwashe rabin roban Vaseline a jikinshi”
“Ya Rabb” kawai ta iya cewa.
A B U J A
Suna Zaune gabaki daya kan Dining Table suna breakfast Umma ke cema Babansu “Abba wai kasan Jawad Zance yaje Katsina ranar Asabar?”.
Jawad ya ma Umma wani kallon “haba Umma ya zakiyi irin maganar nan a gabana”.
Dariya tayi ta maida hankalinta gurin Abbansu
Abba ko yace “Lallai Autan Umma an girma, har ana zuwa Zance wani gari?”.
Murmushi Mancy tayi tace “ai Ya isa Aure, sai a mishi”.
Abdulmajeed yace “to wai kana nufin Overtaking dina zakayi ne?”
Mancy tace “ai gwara yayi tunda kai ka tsaya wasa”.
Abdulmajeed yayi dariya yace “kai Mancy”.
Abba yace “to ya sukace gidansu Yarinyan?”.
Jawad yace “Abba haka yayanta yace in tura manya na aje neman izinin chan Edo State”.
Abba ya aje kofin Shayinshi yace “Edo state kuma?”.
Da sauri Umma tace “Aiki ya kai babansu chan shine suke zama har yayi retire, yarinyar ma chan aka haifeta, amma yan arewa ne”.
Abba yace “kuma kana sonta?” Ba tare da ya kalleshi ba Jawad yace “Eh Abba”.
“Ya sunan Babanta?”
“Alhaji Ahmad Dakata”.
“Cikin garin Edo?”
Jawad yayi jim yace “bansani ba Abba, sai na tambayeta”.
Abba yace “Aa ba maganarta bane, kace ta hadaka da Yayanta, sai ka hadasu da Yayanku suyi magana, yayanku should report to me, ko ya kira Baba Usman dinku suyi magana”.
A ladabce yace “To Abba”
Mimi da ke wasa da dankali a baki tace “Abba nima ka min Aure”.
Dariya suka saka baki daya.
Yasmin ta fito sanye da doguwar riga mai kama da ‘yar kanti ta wuce dakin Zaid, daidai da fitowar Labiba rik’e da jakka da alamu Makaranta zata, Labiba tayi saurin dauke kai ta shiga dakin Aunty Asee don mata sallama, murmushi Yasmin tayi ta shige dakin Zaid.
Zaune ta ganshi cikin yanayi.
Da sauri ta karasa gunshi tana tambayarshi “Lafiya Zaid?”
Hanayenshi ya nuna mata ta bi hannun da kallo.
“Wani abu kamar cizon sauro”
Murmushin takaici yayi yace “ba kama bane, cizon sauron ne”.
Yasmin na bin duk ilahirin jikinshi da kallo tace “to me ya faru? Ji fa yanda suka cijeka har fuska, garin yaya? Bakayi fleeting bane? Ko maganin sauron nan da kake kunawa ya k’are ne? Ji fa kamar ka kwana a kwata, chabda har saman goshi”.
“Beebs ce, Labiba ce”.
“Meya sameta Zaid?”
Kamar zaiyi kuka ya kwashe komai ya gaya mata.
Yasmin ranta ya baci tace “saboda bata gaya maka magana mai dadi ba ka kwana a waje? Ji ciwon sauro a jikinka sunfi dari, ji yanda suka ma ja da fata, sun sha jininka, Zaid Malaria ta kamaka already, kuma kasan da wani abu yayi triggering ciwonka it will only worsen, Zaid what were you thinking? You had to prove that to her? Oh Allah, ba zan ga laifinka ba don So ne, So banzan abu ne, it makes us do stupid things, nikam tashi muje Asibiti, mu fara treating Malaria tun kafin ta mana mummunan Kamu”.
Ganin yanda ta tashi hankinta ne ya sa shi nadamar gaya mata dabara ta fado mai yace “Na sha Anti Malaria fa” tace “wanne?”yace “ACT” ina kwalin?” Yace “baki yarda dani bane?”.
Kafin tace wani abu ta hango Labiba ta window zata fita Gida.
Da sauri tace “Ina Zuwa”
Yace “Ina Zakije?”
Ta fara yafiya tace “ka jirani yanzu zan dawo”.
Da sauri ta koma cikin Gida ta dauko Wayarta da Key ta fita.
Sauri sauri gudu gudu ta karasa inda motarta take cewa “kai bude min gate”
Yau zaayi ta ta k’are ni da Labiba, makarantar zan kaita.
Bude gate akayi ta kunna motar ta fita da saurinta.
Labiba kuwa tafiya takeyi da sauri don bata so ta makara, yau 9 zatayi lectures gashi 8:30 ta yi, kafin taje School 9 tayi k’ila ta wuce, a zuciyarta take fatan akwai bus da taje zata tashi kar kuma ayi tsaye tsaye direct ta samu har batagarawa.
Bata kai ga isa shagon Eskaley ba Motar Yasmin ya sha gabanta.
Da mamaki ta kalleta.
Yasmin ta zage Window tace “Shigo”
Labiba tace “Makaranta Zanje fa”.
Yasmin tace “Hassan Usman Polytechnic Department of Animal Health and Production Technology, chan nayi nima”.
Labiba tayi jim, kaafin ta zagaya ta bude gaba ta zauna.
Wani irin sansanyan k’amshi taji ya bugi hancinta, k’amshin motar ya hade da k’amshin jikinta, zata iya bambance na motar da kuma na jikinta, don zata rantse ta ji kamshinta daga inda take dazu a gida da suka hadu, lallai kam wannan ‘yar kamshi ce, da Ita da Zuciyarta kawai suke wannan firar.
Yasmin ta gyara kan sitiyari ta fita daga Unguwan tana juya sitiyari cike da k’warewa.
Labiba ta fara shawara da zuciyarta chan ta yanke shawaran gaisheta tace “Ina kwana Aunty”.
Yasmin ta maida hankalinta ga Titi ba tare da ta kalleta ba tace “Lafiya lau”.
Ba wanda ya sake magana.
Yasmin shatata gudu takeyi cikin minti da bai wuce 10 ba tana gaban K’ofar Batagarawa, mai makon ta shiga School din sai tayi parking gaban Gate din.
Labiba ta kalleta da dan murmushi a fuskanta tace “Nagode” ta sa hannu zata bude k’ofar ta fita taji Yasmin ta danna Lock kofar ta datse ta ki buduwa.
Labiba ta kalleta da mamaki tana jiran bayani.
Yasmin fuska ba annuri tace “karfe nawa kike da lectures?”
Labiba tace “karfe 9”
Yasmin ta kai idonta ga agogon motarta tace “muna da sauran Minti 11, i will make it fast, Labiba, kin san cewa Zaid waje ya kwana Jiya?”.
Labiba ta dan kau da kai kafin tace “ni ban sani ba”.
Yasmin tace “Oh baki sani ba? To bari na gaya miki, Zaid waje ya kwana, a daren jiya ya furta miki Kalaman da na dade inaso na ji daga bakinshi, a daren jiya ya tona asirin zuciyanshi da na dau shekaru ina son ji daga bakinshi, a daren jiya ya furta miki abunda bai taba furta min ba, ya buk’aci ki ce mishi ko da ‘thank you’ ne amma kin faskara, ya rok’i ki gaya mishi magana mai dadi amma sai kika jefe kalamanshi da kalmar Yaudara”.
“Zaid bai cire rai ba, ya miki barazanar kwana waje in baki mishi magana mai dadi ba amma ko a jikinki, to ashe ba barazana bace ba, Kwanan yayi a waje, mosquitoes kuwa suka samu Abincin Dinner suka far mai, jikinshi yau ba ma tsaka tsinke duk cizon sauro ne wanda ina da tabbaci malaria ya kamashi lokaci kadan zai kwanta ciwo, ke ce sanadi kuma, kuma Wallahi wani abu ya samu Zaid, ba zan yafe miki ba”.
Labiba tace “kema son shi kike ai, to meyasa kike son ganin kin hadamu?”.
Yasmin tayi murmushi mai ciwo tace “ba ruwanki, na gaya miki kar kiyi Kishi dani, ni ba damuwanki bace, as long as kina zuciyarshi, to sai nayi yanda nayi ya sameki”.
“Zaid na Sonki sosai, yana matuk’ar kaunarki, in har kikayi amfani da son da yake miki wurin wahalar da zuciyarshi, baki yi wa SO adalci ba, ba ki chanchanci ki furta kalmar SO ba”.
Labiba ta turo baki tace “nifa ba sona yakeyi ba, haka kawai yake cewa yana sona, kema kin yarda dashi, haushi fa kawai yakeji don yana ganina da wasu”.
Cike da takaici Yasmin tayi tsaki, ji take kamar ta rufe labiba da duka.
Wayarta ta ciro ta danyi latse latse kafin ta daga wayar sama.
Labiba ta ji muryan Yasmin na fitowa daga jikin wayar da alama recording ne tayi playing inda taji muryan Zaid na cewa;
“Ki tambayeni Yas, tambayeni".
Taji muryan Yasmin din na cewa “Ina son sani, kana son Labiba ko ba ka sonta?".
"INA SONTA".
Labiba ta fara kaita bango a kausashe yace “ki bi a hankali Labiba, shawara nake baki yanzu, kuma dai lallabaki nakeyi, ina da halin maida Zaid nawa nikadai, amma ba zanyi ba saboda yana Sonki, bana so inyi Son kai, i dont want to be selfish, in har kika bari na sa Selfishness a cikin lamarin nan, Labiba in har ki ka bari na zabi kaina akan kowa, wallahi Zaid ba zai sake kallonki ba, Zaid ba zai sake bi ta kanki ba, ko iskar da ya deboki Zaid ba zai sake kallo ba, Zaid zai zama nawa, nikadai in har kika kaini bango Labiba, Fitar min a mota”.
A sukwane ta bude k’ofar ta fita, yanayin Yasmin ya bata tsoro, da sauri ta fara tafiya tana yi tana waigen Yasmin, Yasmin ta bude wuta ta yi wani irin reverse ta hau kan Titi, Labiba tsoro ya kamata, ganin yanda ta bude wuta a fili tace “Allah ya tsare” wani irin So Yasmin take ma Zaid da har zata sadaukar da kai haka ta nema mishi abunda yake so? Lallai in itace wallahi saidai ya mutu, in be sonta ba zata taba hadashi da wacce yake so ba.
Shiru tayi kafin Zuciyarta ya tambayeta tambayar da take son amsarta “Amma dagaske Zaid din na Sonta? Muryarshi ta tuna Radam ta wayar Yasmin inda yace “INA SONTA” zata rantse gaskia ya fada, ba zai ma wacce ta tambayeshi karya ba, ta aminta da kalamanshi, zuciyarta tayi naam dashi”.
Ta dafe saitin Zuciyar tace “Ina Sonka Zaid, Wallahi ina Sonka”.
#1love
#DM
%anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR 2⃣5⃣
(SON SO ❤💖)
Tana shiga aji ta zauna, Besty bata kai ga zuwa ba, wayarta ta cire a jakka ta latso numbern Aishar, ringing biyu ta dauka "Hello Besty kina ina ne?" Daga bangaren Aishar tace "muna first gate gani nan karasowa.
Ta window Labiba ta hango Mallam na nufowa Ajinsu, daidai da rurin wayarta, ta duba ta ga Jay ne, ga kuma Mallam nan zuwa, ta san in bata dauka yanzu ba, ba zai damu da tana Lectures ba zai ta kwala mata kira, dauka tayi tare da sa kai kan desk.
"Hello Jay, Goodmorning".
Jawad daga bangarenshi yace "GoodMorning Baby, ya kike? Bacci kike halan?".
Labiba tace "Jay, yau Monday ka manta ne? Gani nan cikin Aji, ga ma Lecturer dinnan ya shigo, zan kiraka in na fito"
"Okay okay donAllah yi min sending Numbern Yaya Muhammadu, yanzu donAllah, kafin a fara lectures din".
Labiba bata son jan magana, ga Lecturer ya shigo ajin, ya fara cewa a shirya ya sa tace "Okay" tare da datse kiran.
Labiba ta tura ma Jawad numbern Baban Amira daidai da shigowar Aisha ta shigo class din da sauri ta ma kanta mazauni kusa da labs tare da tsunkulinta, gira Labiba ta daga mata tare da maida hankalinta gurin Lecturer da ke bayani.
A B U J A
Jawad kamar zazzabi tuni ya ma Office din yayanshi diran mikiya.
Bayan Secretary ya mishi Iso Jawad ya shiga farfajian offishin yayanshi suka gaisa.
Yaya Abdulhafiz yace "yadai autan Umma?"
Jawad yace "Yaya dazun ne Abba yace na baka numbern Yayan Labiba ka kirashi shine na amso numbernshi".
Yayan ya murmusa yace "Jawad, Abbanka ya kirani, ya min bayani".
Cike da jin dadi Jawad yace "Yauwa Yaya, ga numbern kirashi donAllah".
Yayan yace "tun yanzu Jawadb? Kamar jira ake"
Yace "Eh wallahi Jira akeyi, nidai call him now".
Yayar ya yi dialling Numbern Baban Amira Ringing daya aka dauka, Jawad ya ma yayanshi nuni da ya saka handsfree haka kuwa yaya Abdulhafiz yayi.
"Hello Assalam Alaikum"
Daga chan bangaren Mallam Muhammadu ya amsa da "Waalaikum Salam"
"Sunana Abdulhafiz Abu Shamsu, nine Babban wa a guri Jawad mai neman k'anwarka Labiba".
Baban Amira yace "to to, muna lafia?"
Suka sake sabon gaisuwa.
Yaya Abdulhafiz yace "Mahaifina ya Umurceni da na tuntubeka da Maganan Jawad".
Baban Amira yace "MashaAllah, kamar yanda na gaya ma Jawad, nace mai Inda gaske yake da Aure yazo, ya turo Manyanshi ga Manyanta, sai su nema mishi izinin zuwa zance kafin ayi na neman Aure".
Yaya Abdulhafiz yace "dama haka ya kamata, to yaushe zamu iya zuwa?"
"Ko yaushe kuka Shirya".
Yaya Abdulhafiz yace "shikenan zan tuntubi magabatarmu da maganan, kaima ka tuntubi naku, tunda ga waya sai mu ji yanda zaayi, amma for now muna son sanin Asalinku, Abbanmu ke tambaya".
Baban Amira yace "Mahaifanmu na cikin Garin Edo,a unguwar Uromi, Bari zan maka Text"
Yaya Abdulhafiz yace to shikenan mungode kwarai dagaske, ba, mu yan Anguwan Alk'ali ne, da ka tambayi Gidan Shamsu Abdulrahman Alo, zaa gwada maka gidan kakaninmu, sunan Mahaifin Alhaji Abu Shamsu, nima haka zan maka text gudun mantuwa".
Baban Amira yace "Ba laifi mungode kwarai".
Yaya Abdulhafiz yace "Sai kun jimu".
Sukayi Sallama.
Jawad baki uwa gonar audugu don burinshi na kan cika.
E D O
"Muhammadu kace akwai yaro mai neman Labibata?"
Daga bangaren Baban Amira yace "Eh Abba, suna ma maganar zuwa gunku neman Izini".
Alhaji Ahmad Dakata yace "MashAllahu, ya maganar mu?"
Duk da ya san maganar yace "Wacce Abba?"
Yace "Muhammadu Alkawarin da ka min na cewa da Labiba ta samu Miji zaka cireta daga Makaranta ka maido man Ita Gida na mata aure".
Baban Amira yace "ban manta ba Abba".
Abban yace "yauwa, auren shine rufin asirin duk wata diya mace, wanda tayi Allah ya sa mai Albarka, in Mijinta na da raayin karatu sai ya sakata in baidashi kuwa sai tayi yar sanaa tunda haka sauran yayyinta sukayi, amma Labiban ta amince ko?".
Baban Amira yace "Eh Abba, ita ta bashi numberta ya ba yayanshi ya kirani ai, kuma da yazo Gidana na gaya mata zan turo muku su, kaga ko tanayi tunda ta barshi yazo Gidana".
Baban yace "MashaAllah, wallahi naji dadi sosai, sai kaima ka fara naka binciken yanda suma zasuyi, in babu wata matsala sai a hade da bikin Yaruwarta Samira kafin Azumi".
Baban Amira yace "to InshaAllah Abba, a gaida su Mami da mutanen Gidan".
Sukayi Sallama.
K A T S I N A
Strike Din Likitoci bai dade ba, a hanyar Yasmin ta komawa Gidan Alhaji Zaki ta samu wayar sun dawo Yajin Aiki, ta
Showing 87001 words to 90000 words out of 132816 words
"Akwai Sauro, zan kwana a nan in har baki fada min wani abu mai dadi ba".
Tashi tayi da sauri ta lek’a ta window ta ganshi a takure, A fili tace “ina abunda ya dameni? Ka kwana nan mtss, kalaman yaudaranka ba zasu yi tasiri a kaina ba”. Hayewa tayi Gado tayi adduar Bacci kafin baccin yayi awon gaba da ita.
Sauron Katsina marasa kunya a gaban idonka ma sai su cijeka balle bayan idonka, haka Saurayen Tudun Matawalle sukayi dinner da DanMakaho, tun yana sosawa, yana kashesu da hannu, yana tsaki gashi bai da abun rufa, taurin kai da ya sa ma ranshi, shi ya hanashi shiga daki ko da ya dauko abun rufa ne, haka dan MAKAHO ya kwana a waje wanda bacci rabi a bude ya yishi, sai gaba da Asuba bacci mai nauyi yayi awon gaba dashi.
Alarm dinta ya tadata, bude dakin tayi ta fito, idonta tsaye yayi chan sashen, wani murmushin takaici tayi tare da mamaki, wai dagaske kwanan yayi a nan? Sai taji zafi kuma, bata ji dadi ba, kamar ta karasa gunshi ta k’yaleshi ta shiga Toilet ta wanko bakinta tare da dauro Alwala, ta shiga kitchen ta dauko babban tukunya ta cikashi taf da ruwa sannan ta janyo risho (stove) ta kunna ta daura tukunyan kafin ta fito daga kitchen din sai da ta sake kallonshi kafinta shige daki k’irjinta na mata nauyi.
Rakaatanil Fajr tayi kafin tayi Asuba tayi zikrorinta na safe kafin ta tashi don tada yara ta musu Wanka yau Monday.
Ta fito rik’e da hannun Ameera, yana nan bai motsa ba.
Itama ta rasa abunyi, yau ko Asuba be yi ba, yana nan yana baccin asara a waje. Baban Amira ne ya turo k’ofar Gidan hannu shi dauke da Bak’in Leda wanda shakka babu Breadi ne da madara da lipton da milo na sachet, wanda duk rannan da zasu sha tea baya dawowa daga Sallahr Asuba sai gari ya waye ya tsaya siyansu.
Ganinshi ya sa Labiba dawowa daga tunaninta kar yace DanMakahon take kallo, tace “Yaya Ina Kwana” ya amsa da “Lafiya lau Aunty Labs” Amira tace “Baba ina kwana” yace “Lafia Amirori wanka zaayi ko?” Tace “uhm” Labiba tayi saurin shigewa Kewaye da Amira ta dauki bokiti ta shiga kitchen ta diba ruwan zafi ta k’ara a na tukunyan ta sirka kafin ta shiga yi ma Amira Wanka.
Kamar dai kullum in yana Gida, Baban Amira ya dauko tsintsiya don Share tsakar Gidan, Aunty Aseey na Kitchen tana hada Tea a dogon Jug, Labiba ta shiga da Amira ta fito da Sabit dan mishi wanka taji muryan Yayanta yana “SubhanAllah, DanMakaho ne chan?”.
Da sauri ta kallesu taga Yayan na k’okarin k’etara Gidan Alh Zaki.
Ta naji Aunty Aseey na cewa “yanzun haka shaye shaye yayi ta kai mai karo shiyasa yayi Mankas a waje”.
Labiba tayi saurin dafe kai.
Mallam Muhammad ya fara bubbuga shi tare da cewa “DanMakaho, tashi gari ya waye fa” firgigit ya tashi a dan tsorace tare da murzan idonshi na hagu.
“Dan Makaho ba dai anan ka kwana ba? Ji cizon sauro ko ina a jikinka”.
Zaid ya bi jikinshi da kallo, ya ga cizon sauro runtuma runtuma.
“Kayi Sallahr Asuba kuwa?” Ya ji Mallam Muhammad na tambayanshi
“Aa” ya girgiza kai.
“Haba DanMakaho, ka san k’arfe nawa yanzu? Bakwai ta yi fa, me ya ja maka rashin Sallah har gari ya waye”.
Idonshi na hagu ya sake murzawa kafin yace “barin shiga ciki”.
Labiba ya kalla wacce tayi saurin kauda idonta kafin ya juya ya shige dakinshi.
Mallam Muhammadu cike da tausayawa ya girgiza kai ya cigaba da sharanshi.
Aunty Aseey ta shige kitchen don cigaba da hada kalaci.
Ita kuma Labiba ta shige daki don shirya Sabit.
Ko da ya shiga Daki, toilet ya wuce direct yayi wanka kafin ya doro Alwala, yazo yayi Sallah rakaa biyu kafin ya zauna a kan kujera yana tunanin Labiba.
Ta tsaneshi har haka?
Har yace mata zai kwana a waje ta ki furta mishi kalma mai dadi?
Dagaske ta bar son shi?
To ko daman ba son shi din takeyi ba tausayinshi take?
“Ba tausayinka nake ba, sonka nake, sosai nake son ka”
Kalamanta ne suka dawo mishi kamar a lokacin take ambaton su a lokacin da yake tambayarta in tausayinshi take.
To ko dai ta sadak’as ne? Son da yake mata ba zai saka ta dole ba, ba zai tilasta mata wurin dawo da son shi a zuciyarta ba, tunani fiye da dubu a kanshi ya rasa abun yi.
Tunda ta shiga daki, take tunani, hankalinta baya wurin shafa man da take yi a jikin Sabit.
“A waje ya kwana?”
Don me zai kwana a waje? Baida hankali ne? Yanzu in malaria ta kamashi fa? Akan me zai kwana waje? Akan me? Ya burgeta ya kuntata ma kanshi a kan me? Oh Allah, ya zatayi? Dagaske ya fara sonta?”.
Muryar Amira taji inda ta ke cemata “Aunty Labs, kina lafta ma Sabit mai a jiki” da sauri hankalinta ya dawo jikin Sabit da aka kusa kwashe rabin roban Vaseline a jikinshi”
“Ya Rabb” kawai ta iya cewa.
A B U J A
Suna Zaune gabaki daya kan Dining Table suna breakfast Umma ke cema Babansu “Abba wai kasan Jawad Zance yaje Katsina ranar Asabar?”.
Jawad ya ma Umma wani kallon “haba Umma ya zakiyi irin maganar nan a gabana”.
Dariya tayi ta maida hankalinta gurin Abbansu
Abba ko yace “Lallai Autan Umma an girma, har ana zuwa Zance wani gari?”.
Murmushi Mancy tayi tace “ai Ya isa Aure, sai a mishi”.
Abdulmajeed yace “to wai kana nufin Overtaking dina zakayi ne?”
Mancy tace “ai gwara yayi tunda kai ka tsaya wasa”.
Abdulmajeed yayi dariya yace “kai Mancy”.
Abba yace “to ya sukace gidansu Yarinyan?”.
Jawad yace “Abba haka yayanta yace in tura manya na aje neman izinin chan Edo State”.
Abba ya aje kofin Shayinshi yace “Edo state kuma?”.
Da sauri Umma tace “Aiki ya kai babansu chan shine suke zama har yayi retire, yarinyar ma chan aka haifeta, amma yan arewa ne”.
Abba yace “kuma kana sonta?” Ba tare da ya kalleshi ba Jawad yace “Eh Abba”.
“Ya sunan Babanta?”
“Alhaji Ahmad Dakata”.
“Cikin garin Edo?”
Jawad yayi jim yace “bansani ba Abba, sai na tambayeta”.
Abba yace “Aa ba maganarta bane, kace ta hadaka da Yayanta, sai ka hadasu da Yayanku suyi magana, yayanku should report to me, ko ya kira Baba Usman dinku suyi magana”.
A ladabce yace “To Abba”
Mimi da ke wasa da dankali a baki tace “Abba nima ka min Aure”.
Dariya suka saka baki daya.
Yasmin ta fito sanye da doguwar riga mai kama da ‘yar kanti ta wuce dakin Zaid, daidai da fitowar Labiba rik’e da jakka da alamu Makaranta zata, Labiba tayi saurin dauke kai ta shiga dakin Aunty Asee don mata sallama, murmushi Yasmin tayi ta shige dakin Zaid.
Zaune ta ganshi cikin yanayi.
Da sauri ta karasa gunshi tana tambayarshi “Lafiya Zaid?”
Hanayenshi ya nuna mata ta bi hannun da kallo.
“Wani abu kamar cizon sauro”
Murmushin takaici yayi yace “ba kama bane, cizon sauron ne”.
Yasmin na bin duk ilahirin jikinshi da kallo tace “to me ya faru? Ji fa yanda suka cijeka har fuska, garin yaya? Bakayi fleeting bane? Ko maganin sauron nan da kake kunawa ya k’are ne? Ji fa kamar ka kwana a kwata, chabda har saman goshi”.
“Beebs ce, Labiba ce”.
“Meya sameta Zaid?”
Kamar zaiyi kuka ya kwashe komai ya gaya mata.
Yasmin ranta ya baci tace “saboda bata gaya maka magana mai dadi ba ka kwana a waje? Ji ciwon sauro a jikinka sunfi dari, ji yanda suka ma ja da fata, sun sha jininka, Zaid Malaria ta kamaka already, kuma kasan da wani abu yayi triggering ciwonka it will only worsen, Zaid what were you thinking? You had to prove that to her? Oh Allah, ba zan ga laifinka ba don So ne, So banzan abu ne, it makes us do stupid things, nikam tashi muje Asibiti, mu fara treating Malaria tun kafin ta mana mummunan Kamu”.
Ganin yanda ta tashi hankinta ne ya sa shi nadamar gaya mata dabara ta fado mai yace “Na sha Anti Malaria fa” tace “wanne?”yace “ACT” ina kwalin?” Yace “baki yarda dani bane?”.
Kafin tace wani abu ta hango Labiba ta window zata fita Gida.
Da sauri tace “Ina Zuwa”
Yace “Ina Zakije?”
Ta fara yafiya tace “ka jirani yanzu zan dawo”.
Da sauri ta koma cikin Gida ta dauko Wayarta da Key ta fita.
Sauri sauri gudu gudu ta karasa inda motarta take cewa “kai bude min gate”
Yau zaayi ta ta k’are ni da Labiba, makarantar zan kaita.
Bude gate akayi ta kunna motar ta fita da saurinta.
Labiba kuwa tafiya takeyi da sauri don bata so ta makara, yau 9 zatayi lectures gashi 8:30 ta yi, kafin taje School 9 tayi k’ila ta wuce, a zuciyarta take fatan akwai bus da taje zata tashi kar kuma ayi tsaye tsaye direct ta samu har batagarawa.
Bata kai ga isa shagon Eskaley ba Motar Yasmin ya sha gabanta.
Da mamaki ta kalleta.
Yasmin ta zage Window tace “Shigo”
Labiba tace “Makaranta Zanje fa”.
Yasmin tace “Hassan Usman Polytechnic Department of Animal Health and Production Technology, chan nayi nima”.
Labiba tayi jim, kaafin ta zagaya ta bude gaba ta zauna.
Wani irin sansanyan k’amshi taji ya bugi hancinta, k’amshin motar ya hade da k’amshin jikinta, zata iya bambance na motar da kuma na jikinta, don zata rantse ta ji kamshinta daga inda take dazu a gida da suka hadu, lallai kam wannan ‘yar kamshi ce, da Ita da Zuciyarta kawai suke wannan firar.
Yasmin ta gyara kan sitiyari ta fita daga Unguwan tana juya sitiyari cike da k’warewa.
Labiba ta fara shawara da zuciyarta chan ta yanke shawaran gaisheta tace “Ina kwana Aunty”.
Yasmin ta maida hankalinta ga Titi ba tare da ta kalleta ba tace “Lafiya lau”.
Ba wanda ya sake magana.
Yasmin shatata gudu takeyi cikin minti da bai wuce 10 ba tana gaban K’ofar Batagarawa, mai makon ta shiga School din sai tayi parking gaban Gate din.
Labiba ta kalleta da dan murmushi a fuskanta tace “Nagode” ta sa hannu zata bude k’ofar ta fita taji Yasmin ta danna Lock kofar ta datse ta ki buduwa.
Labiba ta kalleta da mamaki tana jiran bayani.
Yasmin fuska ba annuri tace “karfe nawa kike da lectures?”
Labiba tace “karfe 9”
Yasmin ta kai idonta ga agogon motarta tace “muna da sauran Minti 11, i will make it fast, Labiba, kin san cewa Zaid waje ya kwana Jiya?”.
Labiba ta dan kau da kai kafin tace “ni ban sani ba”.
Yasmin tace “Oh baki sani ba? To bari na gaya miki, Zaid waje ya kwana, a daren jiya ya furta miki Kalaman da na dade inaso na ji daga bakinshi, a daren jiya ya tona asirin zuciyanshi da na dau shekaru ina son ji daga bakinshi, a daren jiya ya furta miki abunda bai taba furta min ba, ya buk’aci ki ce mishi ko da ‘thank you’ ne amma kin faskara, ya rok’i ki gaya mishi magana mai dadi amma sai kika jefe kalamanshi da kalmar Yaudara”.
“Zaid bai cire rai ba, ya miki barazanar kwana waje in baki mishi magana mai dadi ba amma ko a jikinki, to ashe ba barazana bace ba, Kwanan yayi a waje, mosquitoes kuwa suka samu Abincin Dinner suka far mai, jikinshi yau ba ma tsaka tsinke duk cizon sauro ne wanda ina da tabbaci malaria ya kamashi lokaci kadan zai kwanta ciwo, ke ce sanadi kuma, kuma Wallahi wani abu ya samu Zaid, ba zan yafe miki ba”.
Labiba tace “kema son shi kike ai, to meyasa kike son ganin kin hadamu?”.
Yasmin tayi murmushi mai ciwo tace “ba ruwanki, na gaya miki kar kiyi Kishi dani, ni ba damuwanki bace, as long as kina zuciyarshi, to sai nayi yanda nayi ya sameki”.
“Zaid na Sonki sosai, yana matuk’ar kaunarki, in har kikayi amfani da son da yake miki wurin wahalar da zuciyarshi, baki yi wa SO adalci ba, ba ki chanchanci ki furta kalmar SO ba”.
Labiba ta turo baki tace “nifa ba sona yakeyi ba, haka kawai yake cewa yana sona, kema kin yarda dashi, haushi fa kawai yakeji don yana ganina da wasu”.
Cike da takaici Yasmin tayi tsaki, ji take kamar ta rufe labiba da duka.
Wayarta ta ciro ta danyi latse latse kafin ta daga wayar sama.
Labiba ta ji muryan Yasmin na fitowa daga jikin wayar da alama recording ne tayi playing inda taji muryan Zaid na cewa;
“Ki tambayeni Yas, tambayeni".
Taji muryan Yasmin din na cewa “Ina son sani, kana son Labiba ko ba ka sonta?".
"INA SONTA".
Labiba ta fara kaita bango a kausashe yace “ki bi a hankali Labiba, shawara nake baki yanzu, kuma dai lallabaki nakeyi, ina da halin maida Zaid nawa nikadai, amma ba zanyi ba saboda yana Sonki, bana so inyi Son kai, i dont want to be selfish, in har kika bari na sa Selfishness a cikin lamarin nan, Labiba in har ki ka bari na zabi kaina akan kowa, wallahi Zaid ba zai sake kallonki ba, Zaid ba zai sake bi ta kanki ba, ko iskar da ya deboki Zaid ba zai sake kallo ba, Zaid zai zama nawa, nikadai in har kika kaini bango Labiba, Fitar min a mota”.
A sukwane ta bude k’ofar ta fita, yanayin Yasmin ya bata tsoro, da sauri ta fara tafiya tana yi tana waigen Yasmin, Yasmin ta bude wuta ta yi wani irin reverse ta hau kan Titi, Labiba tsoro ya kamata, ganin yanda ta bude wuta a fili tace “Allah ya tsare” wani irin So Yasmin take ma Zaid da har zata sadaukar da kai haka ta nema mishi abunda yake so? Lallai in itace wallahi saidai ya mutu, in be sonta ba zata taba hadashi da wacce yake so ba.
Shiru tayi kafin Zuciyarta ya tambayeta tambayar da take son amsarta “Amma dagaske Zaid din na Sonta? Muryarshi ta tuna Radam ta wayar Yasmin inda yace “INA SONTA” zata rantse gaskia ya fada, ba zai ma wacce ta tambayeshi karya ba, ta aminta da kalamanshi, zuciyarta tayi naam dashi”.
Ta dafe saitin Zuciyar tace “Ina Sonka Zaid, Wallahi ina Sonka”.
#1love
#DM
%anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
BABI NA ASHIRIN DA BIYAR 2⃣5⃣
(SON SO ❤💖)
Tana shiga aji ta zauna, Besty bata kai ga zuwa ba, wayarta ta cire a jakka ta latso numbern Aishar, ringing biyu ta dauka "Hello Besty kina ina ne?" Daga bangaren Aishar tace "muna first gate gani nan karasowa.
Ta window Labiba ta hango Mallam na nufowa Ajinsu, daidai da rurin wayarta, ta duba ta ga Jay ne, ga kuma Mallam nan zuwa, ta san in bata dauka yanzu ba, ba zai damu da tana Lectures ba zai ta kwala mata kira, dauka tayi tare da sa kai kan desk.
"Hello Jay, Goodmorning".
Jawad daga bangarenshi yace "GoodMorning Baby, ya kike? Bacci kike halan?".
Labiba tace "Jay, yau Monday ka manta ne? Gani nan cikin Aji, ga ma Lecturer dinnan ya shigo, zan kiraka in na fito"
"Okay okay donAllah yi min sending Numbern Yaya Muhammadu, yanzu donAllah, kafin a fara lectures din".
Labiba bata son jan magana, ga Lecturer ya shigo ajin, ya fara cewa a shirya ya sa tace "Okay" tare da datse kiran.
Labiba ta tura ma Jawad numbern Baban Amira daidai da shigowar Aisha ta shigo class din da sauri ta ma kanta mazauni kusa da labs tare da tsunkulinta, gira Labiba ta daga mata tare da maida hankalinta gurin Lecturer da ke bayani.
A B U J A
Jawad kamar zazzabi tuni ya ma Office din yayanshi diran mikiya.
Bayan Secretary ya mishi Iso Jawad ya shiga farfajian offishin yayanshi suka gaisa.
Yaya Abdulhafiz yace "yadai autan Umma?"
Jawad yace "Yaya dazun ne Abba yace na baka numbern Yayan Labiba ka kirashi shine na amso numbernshi".
Yayan ya murmusa yace "Jawad, Abbanka ya kirani, ya min bayani".
Cike da jin dadi Jawad yace "Yauwa Yaya, ga numbern kirashi donAllah".
Yayan yace "tun yanzu Jawadb? Kamar jira ake"
Yace "Eh wallahi Jira akeyi, nidai call him now".
Yayar ya yi dialling Numbern Baban Amira Ringing daya aka dauka, Jawad ya ma yayanshi nuni da ya saka handsfree haka kuwa yaya Abdulhafiz yayi.
"Hello Assalam Alaikum"
Daga chan bangaren Mallam Muhammadu ya amsa da "Waalaikum Salam"
"Sunana Abdulhafiz Abu Shamsu, nine Babban wa a guri Jawad mai neman k'anwarka Labiba".
Baban Amira yace "to to, muna lafia?"
Suka sake sabon gaisuwa.
Yaya Abdulhafiz yace "Mahaifina ya Umurceni da na tuntubeka da Maganan Jawad".
Baban Amira yace "MashaAllah, kamar yanda na gaya ma Jawad, nace mai Inda gaske yake da Aure yazo, ya turo Manyanshi ga Manyanta, sai su nema mishi izinin zuwa zance kafin ayi na neman Aure".
Yaya Abdulhafiz yace "dama haka ya kamata, to yaushe zamu iya zuwa?"
"Ko yaushe kuka Shirya".
Yaya Abdulhafiz yace "shikenan zan tuntubi magabatarmu da maganan, kaima ka tuntubi naku, tunda ga waya sai mu ji yanda zaayi, amma for now muna son sanin Asalinku, Abbanmu ke tambaya".
Baban Amira yace "Mahaifanmu na cikin Garin Edo,a unguwar Uromi, Bari zan maka Text"
Yaya Abdulhafiz yace to shikenan mungode kwarai dagaske, ba, mu yan Anguwan Alk'ali ne, da ka tambayi Gidan Shamsu Abdulrahman Alo, zaa gwada maka gidan kakaninmu, sunan Mahaifin Alhaji Abu Shamsu, nima haka zan maka text gudun mantuwa".
Baban Amira yace "Ba laifi mungode kwarai".
Yaya Abdulhafiz yace "Sai kun jimu".
Sukayi Sallama.
Jawad baki uwa gonar audugu don burinshi na kan cika.
E D O
"Muhammadu kace akwai yaro mai neman Labibata?"
Daga bangaren Baban Amira yace "Eh Abba, suna ma maganar zuwa gunku neman Izini".
Alhaji Ahmad Dakata yace "MashAllahu, ya maganar mu?"
Duk da ya san maganar yace "Wacce Abba?"
Yace "Muhammadu Alkawarin da ka min na cewa da Labiba ta samu Miji zaka cireta daga Makaranta ka maido man Ita Gida na mata aure".
Baban Amira yace "ban manta ba Abba".
Abban yace "yauwa, auren shine rufin asirin duk wata diya mace, wanda tayi Allah ya sa mai Albarka, in Mijinta na da raayin karatu sai ya sakata in baidashi kuwa sai tayi yar sanaa tunda haka sauran yayyinta sukayi, amma Labiban ta amince ko?".
Baban Amira yace "Eh Abba, ita ta bashi numberta ya ba yayanshi ya kirani ai, kuma da yazo Gidana na gaya mata zan turo muku su, kaga ko tanayi tunda ta barshi yazo Gidana".
Baban yace "MashaAllah, wallahi naji dadi sosai, sai kaima ka fara naka binciken yanda suma zasuyi, in babu wata matsala sai a hade da bikin Yaruwarta Samira kafin Azumi".
Baban Amira yace "to InshaAllah Abba, a gaida su Mami da mutanen Gidan".
Sukayi Sallama.
K A T S I N A
Strike Din Likitoci bai dade ba, a hanyar Yasmin ta komawa Gidan Alhaji Zaki ta samu wayar sun dawo Yajin Aiki, ta
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30 Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45