Duk da ina cikin tashin hankali sai da na murmusa da jin zanttutukan Nene. Bayan Sarki ya ji bayanan Nene da kuma na Baba da na Shafa'atu, aka min tambayoyi aka ma Dalo tambayoyi Sarki ya yanke hukunci.
"Alhaji Ali Zaki, wannan ya zama karo na karshe da zamuyi zama kanka da yaranka, na saurari komai, na fahimci komai, ba ruwan Matarka da Yaranka, ba ruwanta da su, ke shafaatu ba ruwanki da duk abunda zai ma yaranshi, ba ruwanki da hanashi, ba ruwanki da sa shi, na miki iyaka da su, yauwa ba kuma da k'ayyade musu abincin cinsu, gidan ubansu ne, yana iya sakin ki, amma bai iya sakinsu, kina jina?".
Shiru tayi bata amsa ba, bata ankara ba sai jin Dorina tayi a bayanta, wani irin bank'arewa tayi tare da sakin ihu, haka wannan dogarin ya sake shada mata a baya yace "kinji ko ba kiji ba?" Da sauri tace "naji wallahi, wallahi naji".
Hankalin Alhaji Ali ya tashi amma ba abunda zai iyayi da ya wuce sanya ido, Sarki ya ja ma Baba kunne sosai, kafin ya tambaye in akwai mai magana.
Nace ina da magana "Masters nakeyi, saura kwanakin da ba su wuce 3 na fara jarabawa, Baba yayi freezing accounts dina, ya kwace duk wani abun da ya bani, ya hanani komawa don kammala karatuna".
Sarki yace "Alhaji Zaki hakane?" Baba ya fara in ina yace "Wallahi Mai martaba, ba kudi ne, amma inshaAllah da komai ya daidaita zan maidashi".
Sarki yace "to madallah, duk da zaiyi wuya ace kai baka da halin maidashi karatu ba damuwa bane wannan, indai be rasa ci da sha ba to komai mai sauki ne, wannan tsakaninku ne, ku tashi ku tafi, ku kuma in akwai wani abu kuna iya zuwa Fada ku sanar dani, akwai mai magana?".
Baba yace "eh ni, mai Martaba, donAllah ace ma wanchan Tsohuwar kar ta sake zuwa man gida, tayi nesa da iyalina donAllah, ayi mata iyaka da Gidana". Nene ta murmusa tace "indai Gidanka ne ba zan kara zuwa ba".
Murmushin da takeyi ne ya fadar ma Baba da Aunty Saude Gaba, ba su yarda ba, wannan tsohuwa akwai bariki".
Sarki yace "to Madallah"
A haka ya sallame mu, ko ba komai Nene ta kwatar mana yanci ta siya mana mutunci, ta nuna mana muna da sauran gata.
Nene ta rik'e hannuna da na Dalo ta ja mu waje tace "ku je Gida, da kunga abunda bai muku ba ku kirani, ka kula da kanwarka" sosai hankalinmu ya kwanta.Nene ta tsaida abun hawa tayi tafiyarta Gida abunta.
Mu kuma da Motar Emirate a ka maidamu Gida, ba wanda yace ma kowa komai sai ni da Dalo da ke fira jefi jefi.
A ranar Baba yaje Gidan Alhaji Lema don kara ja mishi kunne kan Uwarshi, lokacin sun fito daga Masallaci shi da Abbii(baban Nasiba) a nan ne ma ya san Mamarshi na wani Case, shi kuma Alhaji Lema a nan ne ya san cewa Nene taje Gidan Sarki, hakuri Abbi ya ba Baba. Nan suka shiga tattaunawa tsakaninsu.
Abbi yace "wallahi ko me zaa ma Nene ba zata fita daga harkansu ba, oh Allah Nene ita bata damuwa taje ta siya fada da kudinta".
Alhaji Habib yace "kawai Zaidu gobe ya wuce da ita Kaduna kawai, ta dan kwana biyu chan".
Da kissa da kissina zasu bar Gidan ba tare da sun sake waiwayan gidan sarki ba, ki kulla makirci da duk wani sharrin da zaki iya musu, fadan ba naki bane, ya zama na Uba da yaranshi, ke kawai ki zama 'yar kallo. Hudubar yar rabi kenan da tazo Gidanta, haka kawai zatayi dole tayi taka tsantsan bata son duk abunda zai sake hadata da gidan Sarki don ta ji Dorunar nan, ta san me zatayi. Da kansu zasu bar Gidan baki alekum.
SAI DAI ME?
Rayuwa ta cigaba mana, ba dadi, ba mu taba waya da Mancy ba tunda ta bar katsina, tunda na dawo ni ke shiga kitchen in dafa Abincina, ban yarda na ci abincinsu ba, wani community school Baba ya maido Dalo wai be da kudin biyan makarantar da take a da, amma kin san me? Chan ya maida Annah, ga hudu da ke fantamawa cikin Motocin Gida ni ko nawa kallo.
In naji Bakinciki kamar ya kasheni, na kanje dakin Haruna na shak'a World, a hankali na dinga taba Sigari har ya zame min jiki, a rana sai in sha kara fiye da biyar, komai ya cigana da wakana Babanmu na fiffita Bare kanmu, kashi ya fimu daraja, banda Abinci da wurin kwana ba komai na Babanmu a wurinmu, ke sai yazo ma na daina damuwa da komai, na daina shakkun Baba, na fetsare, na koma abota da su haruna na zama wani dan jagaliya, na koma Taraiyya da yan Bencin Eskaley. World din na batar min da duk wata damuwa, sai likafa ta cigaba sai in zuqi World na bi da kwalin Sigari guda, to fa Sigar Zuk'i daya nake mishi ya kare na cillar na kunna wata, shiyasa suke ce min Mankasssss...
Ke kwatsam wata rana ina daki Dalo ta shigo dakina Hankalinta tashe, tana kuka wai ance mata ina shaye-shaye, ni abokinsu Eskaley ne. Hankalina ya tashi bana so ta taba ganin wannan side din nawa, nima kukan na sa nace mata "wallahi zan bari, ba zan karaba". Da kyar na samu tayi shiru na lallasheta. Rakata nayi har dakinta a cikin Gida, tausayinta ke kamani, duk ta fige ta lallace ta kuma yi duhun bak'i".
Nazo wucewa daidai dakina na da na ji muryar Hudu na cewa "eh na saka mai a karkashin katifar shi" sai na ji Aunty Shafa tace "Yauwa kawai ai shi ya dauke su" sai kuma suka sa darian shewa.
Kafadu na na daga, ba su dameni ba, na wuce dakina da ke baya, na dauko ragowar World na zuk'e, na zauna ina recieving current din da World ke bani a lokaci daya ina busar sigari, ina jina a gajimare naji an banko kofar Daki.
Baba, da Anty Shafa ne, a dage na kallesu na watsar na cigaba da bankan Abuna".
Cike da hargowa Baba yace "Kai DanMakaho, ina Sarka da yan kunnen Zinarin Matata da ka shiga ka sace a dakinta?" Duk da Maganar ta buga zuciyana ban dago na kallesu ba na cigaba da busar Sigarina".
Aunty Shafa ta fara kukan munahinci tace "wallahi da idona naga ya fito dashi daga dakina, na mishi magana kan ya bani abuna ya min zagi ta uwa ta uba, shime nace ni ba zanyi komai ba balle ace ban kyauta ba, bari kai ka dawo tunda kai ka haifeshi sai ya baka".
Wani murmushin bakinciki nayi wanda ya sa na zuk'e ragowar Sigarin, ido na ya kada yayi jazir, amma dai tak bance musu ba.
Cin kwalar rigata Baba yayi "Danubanka yana ina? Hudu duba min dakin nan".
Don rainin Wayau Hudu ya daga Katifata kawai sai ga sarka da yan kunne? Kutumar.
Wai sai suka shiga rafka Salati.
"Wallahi kai ba dana bane ba, ni ban haifi Barawo ba, Maryama ta dade tana haintata, cikin shege tayi ta lakafa min Da, ashe Barawo ne, Allah ya isa tsakanina da Maryama, ta sa na raini Barawo, shege dan shegia, Allah ya isa na, Allah ya tsine ma Maryama".
Da sauri na kwace kaina nayi hanyar Fita.
Muryar Makirar naji tana cewa "dama Alhaji baka san DanMakaho Shege bane? Be da Uba, kai a ka dauka sakarai a ka lakafa maka shi, kai kuma ka raineshi tsakaninka da Allah".
Wani kukan Kura nayi na finciko hannun Baba na tillashi waje, kafin su ankara na sa mukulli na kulle Dakin, kafin ta farga da me nake niyyan yi na ciro Charger Laptop dina na dinga laftarta ta da shi, ihu takeyi na sa k'afa na tande kafafuwan ta, shi ko Baba daga waje Hankalinshi a tashe yana ta kokarin budewa, ya rasa yanda zaiyi.
Sai da nagaji da kaina na kyaleta, duk tayi laasar, fuskarta tayi suntum, wannan shine ba a rabu da bukar ba, ita zaman shekara 15 din da tayi ba wai don ta zo dan Miji na dukanta bane, ita bata ma ga wani chanji ba, bata ga ribar shekarun da ta dauka ba, zuwa zatayi ta samu Er Rabi dole a sake sabon Zama.
Ni ko na kyasta Sigarina na hau busawa, bude k'ofa nayi na bi ta inda Baba ke tsaye cike da tashin hankali, ya na ko ganina ya hau la'anta ta.
"Allah ya tsine maka DanMakaho, Allah ya watse maka Karama, Allah ya kwashe maka Albarka, Allah ya laance ka" ya dinga tsina na.
•••••
Kalar kukan da Labiba keyi ne ya sa shi tsaida labarin, murmushi mai cike da tarin takaici da bakinciki yake yace "Kefa kika dameni da na baki labarina, kuma da na fara sai kuka?".
"INA SONKA"
Ta tsaida duk wata na'urar da ke jikinshi daga aiki.
Da kyar ya iya lallubo kalmar "Sha biyu Saura, dare yayi sosai, tashi muje na rakaki Gida".
"DAGASKE, Ina Sonka".
Cikin ido ya kalleta ya hango tsantsar Gaskiarta tsakani da Allah, wannan wace iri ce? Wace kala ce cikin Mata? Ya san ba da dabi'ar 'yan arewa, don babu wata 'yar arewa da zatayi abubuwan da Labiba keyi, ba 'yar arewa mai ajin da zata kalli Namiji gatsau haka ta gaya mishi kalmomi masu tsada, dauke kanshi yayi sakamakon binshi da wani kallo da takeyi.
Ba tare da ya kalleta ba yace "Its Late, ki tashi na rakaki Gida".
Hawayenta ta goge ta mik'e tsaye yayi gaba ta bishi a baya, da hasken Torchlight ya haska Fasassun Blocks ya tsallakesu, ya haska mata itama ta tsallake. Har tsakar Gidansu Labiba ya shiga.
Da taimakon Hasken Farin Wata suke kallon juna cikin Ido.
"So na kikeyi? Ko tausayina kikeyi?" Ya tambayeta kwayar idonshi kan nata.
"In tausayina kike ji, nagode, ki bari, ni bana bukatar tausayin kowa"
"In kuma sona kikeyi, shima ki bari, bana bukatar a So ni".
So biyu ta kyafta idanuwanta kafin ta tsaidasu a kanshi tace Dagaske Sonka Nikeyi.
Bata ganewa ya fada a ranshi, ya juya ya barta a tsaye, tafiyanshi yayi, ya sake tsallaka Fassassun blocks ya shige Gidansu, kan idonta ya bude kofar dakinshi ya shiga ya maida ya rufe.
Zubewa tayi a kan guiwowinta biyu a k'asa a hankali ta furta YA RABB.....
INTERMISSION.
Vote and comment line by line please..
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#staytuned
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
Babi na Sha Uku
(SO❤)
Runtse ido tayi ba tare da ta ga mai yake shirin yi ba, ta tsorata matuk'a da yanayinshi, Idonta a runtse bakinta kawai ke motsi, girgiza kai yayi ya ciro Jallabiyarshi ta Gado ya zura, chan gefen Gado ya zauna yana shafa Mai.
Jikinta rawa kawai yake daga inda yake yaji adduar da takeyi "Allah ka tsareni da tsarewarka, Allah ka kubutar dani, Allah ka yafe mishi na san ba halinshi bane".
Wani murmushi ya subuce mishi mai kama da na takaici, ita ko ganin shirun yayi yawa ya sa ta dan bude ido, ba ta ganshi ba, ware idonta tayi ta duba gefe, abun mamaki zaune ta ganshi yana shafa Mai.
Murmushi tayi tare da gyara zamanta, tace "har raina na san ba zaka min komai ba".
Mur ya sha "Me kika zo yi?" Da murmushi a fuskarta tace "nazo ganinka ne" a tak'aice yace "Fita" tashi tayi ko a jikinta tace "to bari naje, dama ba dadewa zanyi ba, na ganka ai".
Kallon Mamaki ya bita da shi, wai ta yaya take a haka? Wulakanci ya mata fa, amma Dubeta ko a jikinta, tsakaninta da Allah babu abunda ya dameta.
Tashi yayi ya sha gabanta yace "Okay kina ji ba, duk randa kika sake zuwa min daki, sai na tari Yayanki na gaya mishi kullum sai kinzo min daki".
Kamar doll baby, haka ta kyafta idanuwanta tace "ashe kenan kullum zaka tare shi ka gaya mishi, don ni ba zan bar zuwa ganinka ba, sosai nake sonka Yayana".
Cike da takaici yace "Huh!! Wai ke bakya jin nauyin ce ma mutum kina sonshi? Ko haka kuke a Kudu? Ashe haka Matan kudu suke? Kenan a Kudu, Mata ba su da Aji? Mata ke tallan kansu? To ki saurareni da kyau, in wannan haukan da kikeyi ne kike kira da So, ki sani ni ba zan taba son Mace Mara Aji ba, ba zanso ballagaza irinki ba mai tallan kanta, Macen da zan so ko nan gaba zata kasance mai Aji, mai kunya".
Sake kyafta idonta tayi tace "Ka So ni donAllah".
Da takaici yace "Are you not listening? Maganar da na gama miki kenan, ba zan taba sonki ba, don baki da aji, bana son classless person, kina zuwa dakin Namiji, wa ya san ko dama haka kike? Wa ya san iya adadin mutanen da kika kai kanki wurinsu? Ohh, tunda kike nuna rashin tsoro a duk abunda nake yunkurin miki wayasan ko kin saba? Waya san ko ke yar hannu ce? Dallah ki fice min a daki, ki koyo kamun kai, ki zama mai Aji da har ni zan kawo kaina wurinki ba ke ki kawo kanki wurina ba kingane?".
Har ga Allah bata ma jinsa, hankalinta na gun yanayinsa, komai nashi abun burgewa ne, yanayinshi, yanayin maganarsa, yanayin fushinsa, ba abunda ya fi burgeta kamar yanda yake sa hannun damanshi yana murzan idon Hagunshi.
Murmushi cike da fuskarta tace "Har raina nake Sonka".
Takaici kamar ya kasheshi ya sa hannu ya tura mata kafadunta duka biyu yace "Dallah Mallama ki fitan min a daki" ya mata koran wulakanci, ita ko, ko a jikinta tayi murmushi ta wuce gida sadaf sadaf.
WasheGari ta sake fakar Idanun Aunty Asiya ta fada dakinshi, ba ya nan, bata ji dadi ba ko kadan, ta so ganinshi, da tunaninshi ta kwana jiya ta kuma tashi dashi jiya.
Da kallo ta bi dakin a hargitse, katifa ba gyara, duk lungu da sak'on dakin akwai karan sigarin da aka sha, ta bude toilet ta ga shima datti, ba ta son k'azanta.
Hijab dinta ta aje gefe ta hau gyaran dakin. Ta waiga ta waiga bata ga tsintsiyar shara ba, ta fita da sauri ta fada gidansu, kasancewar bango ya rushe ya sa suka daina zaman tsakar gida.
Labiba ta dauko tsintsiya da abun kwashen shara, da ledar Aerial, ta koma dakin, share dakin tayi tas, in har aka auna bolan dakin Mankas sai tayi tiya uku, kuma ba wani datti ke ciki ba illa ragowan sigari da kwali kwali, bak'ar leda ta samu ta juyesu tas ciki.
Toilet ta shiga ta wanke tas, ta bude Wardrobe din, Ghana Must Go ne, hannu ta sa ta bude zip din ta ga atamfa da laces sai shadda da yards na maza.
A ranta tace "ji kayayyakin da ba a dinka ba" a fili kuma ace "toh meyasa be dinkawa?" Wani tunani ya zo mata, ta tuna ya ce mata Babansu ya hanasu karban kayan Mancy, in ma ya gani k'onawa zaiyi, "Allah sarki, ba halin dinka kayan da Mancy ta turo muku, abun tausayi".
Kwashe su tsintsiyar tayi ta koma Gidansu.
BENCIN ESKALEY
Su 3 ke zaune a Bencin sai Eskaley da ke cikin shagonshi. Safiya ce amma ko wannensu na banka ma cikinshi hayak'i, ba su da wata damuwa, sigari kawai suke zuk'a.
Mankas daga gefe yake zuk'ar tabarshi, ganin Mota yayi ta ajiyeta a inda ta saba ajiyeta ya kalli su Tero yace "ga Jarabarban chan tazo". Baki daya suka bi gun da kallo. Mikewa Master yayi yace "wallahi warewa zanyi kafin ta iso"
Ya tashi yana niyyan guduwa yaji ta na cewa "Master gaban Babarka zan bika na lakada maka na jaki".
Chak ya tsaya tare da juyowa yana yak'en dole "Na matsu, Zan dan zagaya ne" mur ta sha tace "zagayawan uwarka, ban sigarin" kallonta ya tsayi yana kallon sigarin da yanzu ya kunnata, zaiyi asarar naira gomarshi da ita kadai ta rage mishi a dunia ya siya sigarin, muryarta yaji "za ka bani ko kuwa?" Tsaki yayi ya mik'a mata karar. Kafa ta sa ta murje shi tas, kafin ta matsa gun Haruna ta kwace nashi ta yar a kwata.
Na karshen Mankas ya zuk'a ya busa hayak'in, cikin fada yace "ka zuk'i uwarka, kuma ita ka busa ma hayak'i a fuska ba ni ba". Murmushi yayi ya tashi tsaye tare da furta sunanta "NeNe".
Iya k'arfinta ta sakar mishi Rank'washi a kai tace "Allah ya shiryeka Zaidu, nidai Wallahi—-" shiru tayi don Master, Haruna da Eskaley suka hada baki wurin k'arasa mata maganar da ta yi niyyanyi na "Zaidu Bawan Allah ba haka yake ba" kallo ta bi su dashi, so milliyan in zata ce haka, to so milliyan zasu karasa mata saboda maganar kenan "Zaidu bawan Allah" ba haka yake ba, kullum indai har ta zo to inshaAllahubsai ta fadi haka.
Mur ta sha tace "Uwarku kuke kwaikwaiya bani ba".
Gum sukayi suka ja bakinsu sukayi shiru, zama tayi kan bencin cike da isa don haka suke kullun.
Eskaley ne ya fara gaidata kafin sauran suka gaisheta har Mankas din, ta amsa tare da kallon Zaid tace "kai dai baka ji ko? Ka cigaba, kar ka fasa wannan bushe-bushen, kai ko kunya bakaji? Bakinka yayi bak'i dubeka donAllah".
Kai Zaid ya shafa yace "InshaAllah Zan bari Nene, ki tayani da addua, kai arr makaryaci, kullum haka kake cewa kuma baka bari, wallahi Zaid ka fita idona, randa zan tona maka Asiri wurin uwarka zaka sha mamakina, ka san dai ban tsoronka ko?".
Da sauri ya rude ya fara rantse ranste "wallahi Nenenmu na bari, ban k'arawa, dagaske bazan k'ara ba". Ko a jikinta don ta san k'arya ba yau ya fara shi ba, ta kuma san ba bari zaiyi ba, amam ba zata fasa mishi addua ba, harara ta galla mishi tace "ka je ka dauko Abincin cikin mota ko kuwa?".
Be tsaya tunanin yaushe tace yaje ya dauko abinci ba sai ma nufar motar da yayi da gudu.
Kallo ta bi Haruna, Master da Eskaley tace "Ce muku ku bar Shaye-shaye bata baki ne ko?".
Eskaley yace "Nenenmu zamu bari"
Kamar ta mareshi tace "dallah rufa min baki, ba kai ne dan iskan da ke saida musu ba".
Eskaley ya ja baki yayi gum.
Tsautsayi yasa Haruna cewa "ai daga yau mun bari, ba zaki taba kama mu da shan wani abu ba".
"ka min shiru ko sai na
Showing 42001 words to 45000 words out of 132816 words
Duk da ina cikin tashin hankali sai da na murmusa da jin zanttutukan Nene. Bayan Sarki ya ji bayanan Nene da kuma na Baba da na Shafa'atu, aka min tambayoyi aka ma Dalo tambayoyi Sarki ya yanke hukunci.
"Alhaji Ali Zaki, wannan ya zama karo na karshe da zamuyi zama kanka da yaranka, na saurari komai, na fahimci komai, ba ruwan Matarka da Yaranka, ba ruwanta da su, ke shafaatu ba ruwanki da duk abunda zai ma yaranshi, ba ruwanki da hanashi, ba ruwanki da sa shi, na miki iyaka da su, yauwa ba kuma da k'ayyade musu abincin cinsu, gidan ubansu ne, yana iya sakin ki, amma bai iya sakinsu, kina jina?".
Shiru tayi bata amsa ba, bata ankara ba sai jin Dorina tayi a bayanta, wani irin bank'arewa tayi tare da sakin ihu, haka wannan dogarin ya sake shada mata a baya yace "kinji ko ba kiji ba?" Da sauri tace "naji wallahi, wallahi naji".
Hankalin Alhaji Ali ya tashi amma ba abunda zai iyayi da ya wuce sanya ido, Sarki ya ja ma Baba kunne sosai, kafin ya tambaye in akwai mai magana.
Nace ina da magana "Masters nakeyi, saura kwanakin da ba su wuce 3 na fara jarabawa, Baba yayi freezing accounts dina, ya kwace duk wani abun da ya bani, ya hanani komawa don kammala karatuna".
Sarki yace "Alhaji Zaki hakane?" Baba ya fara in ina yace "Wallahi Mai martaba, ba kudi ne, amma inshaAllah da komai ya daidaita zan maidashi".
Sarki yace "to madallah, duk da zaiyi wuya ace kai baka da halin maidashi karatu ba damuwa bane wannan, indai be rasa ci da sha ba to komai mai sauki ne, wannan tsakaninku ne, ku tashi ku tafi, ku kuma in akwai wani abu kuna iya zuwa Fada ku sanar dani, akwai mai magana?".
Baba yace "eh ni, mai Martaba, donAllah ace ma wanchan Tsohuwar kar ta sake zuwa man gida, tayi nesa da iyalina donAllah, ayi mata iyaka da Gidana". Nene ta murmusa tace "indai Gidanka ne ba zan kara zuwa ba".
Murmushin da takeyi ne ya fadar ma Baba da Aunty Saude Gaba, ba su yarda ba, wannan tsohuwa akwai bariki".
Sarki yace "to Madallah"
A haka ya sallame mu, ko ba komai Nene ta kwatar mana yanci ta siya mana mutunci, ta nuna mana muna da sauran gata.
Nene ta rik'e hannuna da na Dalo ta ja mu waje tace "ku je Gida, da kunga abunda bai muku ba ku kirani, ka kula da kanwarka" sosai hankalinmu ya kwanta.Nene ta tsaida abun hawa tayi tafiyarta Gida abunta.
Mu kuma da Motar Emirate a ka maidamu Gida, ba wanda yace ma kowa komai sai ni da Dalo da ke fira jefi jefi.
A ranar Baba yaje Gidan Alhaji Lema don kara ja mishi kunne kan Uwarshi, lokacin sun fito daga Masallaci shi da Abbii(baban Nasiba) a nan ne ma ya san Mamarshi na wani Case, shi kuma Alhaji Lema a nan ne ya san cewa Nene taje Gidan Sarki, hakuri Abbi ya ba Baba. Nan suka shiga tattaunawa tsakaninsu.
Abbi yace "wallahi ko me zaa ma Nene ba zata fita daga harkansu ba, oh Allah Nene ita bata damuwa taje ta siya fada da kudinta".
Alhaji Habib yace "kawai Zaidu gobe ya wuce da ita Kaduna kawai, ta dan kwana biyu chan".
Abii yace "anya zata yarda ta bishi?
Alhaji Habib yace "wannan kuma aikin Zaidu bawan Allah ne". Dariya sukayi baki daya.
Da kissa da kissina zasu bar Gidan ba tare da sun sake waiwayan gidan sarki ba, ki kulla makirci da duk wani sharrin da zaki iya musu, fadan ba naki bane, ya zama na Uba da yaranshi, ke kawai ki zama 'yar kallo. Hudubar yar rabi kenan da tazo Gidanta, haka kawai zatayi dole tayi taka tsantsan bata son duk abunda zai sake hadata da gidan Sarki don ta ji Dorunar nan, ta san me zatayi. Da kansu zasu bar Gidan baki alekum.
SAI DAI ME?
Rayuwa ta cigaba mana, ba dadi, ba mu taba waya da Mancy ba tunda ta bar katsina, tunda na dawo ni ke shiga kitchen in dafa Abincina, ban yarda na ci abincinsu ba, wani community school Baba ya maido Dalo wai be da kudin biyan makarantar da take a da, amma kin san me? Chan ya maida Annah, ga hudu da ke fantamawa cikin Motocin Gida ni ko nawa kallo.
In naji Bakinciki kamar ya kasheni, na kanje dakin Haruna na shak'a World, a hankali na dinga taba Sigari har ya zame min jiki, a rana sai in sha kara fiye da biyar, komai ya cigana da wakana Babanmu na fiffita Bare kanmu, kashi ya fimu daraja, banda Abinci da wurin kwana ba komai na Babanmu a wurinmu, ke sai yazo ma na daina damuwa da komai, na daina shakkun Baba, na fetsare, na koma abota da su haruna na zama wani dan jagaliya, na koma Taraiyya da yan Bencin Eskaley. World din na batar min da duk wata damuwa, sai likafa ta cigaba sai in zuqi World na bi da kwalin Sigari guda, to fa Sigar Zuk'i daya nake mishi ya kare na cillar na kunna wata, shiyasa suke ce min Mankasssss...
Ke kwatsam wata rana ina daki Dalo ta shigo dakina Hankalinta tashe, tana kuka wai ance mata ina shaye-shaye, ni abokinsu Eskaley ne. Hankalina ya tashi bana so ta taba ganin wannan side din nawa, nima kukan na sa nace mata "wallahi zan bari, ba zan karaba". Da kyar na samu tayi shiru na lallasheta. Rakata nayi har dakinta a cikin Gida, tausayinta ke kamani, duk ta fige ta lallace ta kuma yi duhun bak'i".
Nazo wucewa daidai dakina na da na ji muryar Hudu na cewa "eh na saka mai a karkashin katifar shi" sai na ji Aunty Shafa tace "Yauwa kawai ai shi ya dauke su" sai kuma suka sa darian shewa.
Kafadu na na daga, ba su dameni ba, na wuce dakina da ke baya, na dauko ragowar World na zuk'e, na zauna ina recieving current din da World ke bani a lokaci daya ina busar sigari, ina jina a gajimare naji an banko kofar Daki.
Baba, da Anty Shafa ne, a dage na kallesu na watsar na cigaba da bankan Abuna".
Cike da hargowa Baba yace "Kai DanMakaho, ina Sarka da yan kunnen Zinarin Matata da ka shiga ka sace a dakinta?" Duk da Maganar ta buga zuciyana ban dago na kallesu ba na cigaba da busar Sigarina".
Aunty Shafa ta fara kukan munahinci tace "wallahi da idona naga ya fito dashi daga dakina, na mishi magana kan ya bani abuna ya min zagi ta uwa ta uba, shime nace ni ba zanyi komai ba balle ace ban kyauta ba, bari kai ka dawo tunda kai ka haifeshi sai ya baka".
Wani murmushin bakinciki nayi wanda ya sa na zuk'e ragowar Sigarin, ido na ya kada yayi jazir, amma dai tak bance musu ba.
Cin kwalar rigata Baba yayi "Danubanka yana ina? Hudu duba min dakin nan".
Don rainin Wayau Hudu ya daga Katifata kawai sai ga sarka da yan kunne? Kutumar.
Wai sai suka shiga rafka Salati.
"Wallahi kai ba dana bane ba, ni ban haifi Barawo ba, Maryama ta dade tana haintata, cikin shege tayi ta lakafa min Da, ashe Barawo ne, Allah ya isa tsakanina da Maryama, ta sa na raini Barawo, shege dan shegia, Allah ya isa na, Allah ya tsine ma Maryama".
Da sauri na kwace kaina nayi hanyar Fita.
Muryar Makirar naji tana cewa "dama Alhaji baka san DanMakaho Shege bane? Be da Uba, kai a ka dauka sakarai a ka lakafa maka shi, kai kuma ka raineshi tsakaninka da Allah".
Wani kukan Kura nayi na finciko hannun Baba na tillashi waje, kafin su ankara na sa mukulli na kulle Dakin, kafin ta farga da me nake niyyan yi na ciro Charger Laptop dina na dinga laftarta ta da shi, ihu takeyi na sa k'afa na tande kafafuwan ta, shi ko Baba daga waje Hankalinshi a tashe yana ta kokarin budewa, ya rasa yanda zaiyi.
Sai da nagaji da kaina na kyaleta, duk tayi laasar, fuskarta tayi suntum, wannan shine ba a rabu da bukar ba, ita zaman shekara 15 din da tayi ba wai don ta zo dan Miji na dukanta bane, ita bata ma ga wani chanji ba, bata ga ribar shekarun da ta dauka ba, zuwa zatayi ta samu Er Rabi dole a sake sabon Zama.
Ni ko na kyasta Sigarina na hau busawa, bude k'ofa nayi na bi ta inda Baba ke tsaye cike da tashin hankali, ya na ko ganina ya hau la'anta ta.
"Allah ya tsine maka DanMakaho, Allah ya watse maka Karama, Allah ya kwashe maka Albarka, Allah ya laance ka" ya dinga tsina na.
•••••
Kalar kukan da Labiba keyi ne ya sa shi tsaida labarin, murmushi mai cike da tarin takaici da bakinciki yake yace "Kefa kika dameni da na baki labarina, kuma da na fara sai kuka?".
"INA SONKA"
Ta tsaida duk wata na'urar da ke jikinshi daga aiki.
Da kyar ya iya lallubo kalmar "Sha biyu Saura, dare yayi sosai, tashi muje na rakaki Gida".
"DAGASKE, Ina Sonka".
Cikin ido ya kalleta ya hango tsantsar Gaskiarta tsakani da Allah, wannan wace iri ce? Wace kala ce cikin Mata? Ya san ba da dabi'ar 'yan arewa, don babu wata 'yar arewa da zatayi abubuwan da Labiba keyi, ba 'yar arewa mai ajin da zata kalli Namiji gatsau haka ta gaya mishi kalmomi masu tsada, dauke kanshi yayi sakamakon binshi da wani kallo da takeyi.
Ba tare da ya kalleta ba yace "Its Late, ki tashi na rakaki Gida".
Hawayenta ta goge ta mik'e tsaye yayi gaba ta bishi a baya, da hasken Torchlight ya haska Fasassun Blocks ya tsallakesu, ya haska mata itama ta tsallake. Har tsakar Gidansu Labiba ya shiga.
Da taimakon Hasken Farin Wata suke kallon juna cikin Ido.
"So na kikeyi? Ko tausayina kikeyi?" Ya tambayeta kwayar idonshi kan nata.
"In tausayina kike ji, nagode, ki bari, ni bana bukatar tausayin kowa"
"In kuma sona kikeyi, shima ki bari, bana bukatar a So ni".
So biyu ta kyafta idanuwanta kafin ta tsaidasu a kanshi tace Dagaske Sonka Nikeyi.
Bata ganewa ya fada a ranshi, ya juya ya barta a tsaye, tafiyanshi yayi, ya sake tsallaka Fassassun blocks ya shige Gidansu, kan idonta ya bude kofar dakinshi ya shiga ya maida ya rufe.
Zubewa tayi a kan guiwowinta biyu a k'asa a hankali ta furta YA RABB.....
INTERMISSION.
Vote and comment line by line please..
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#staytuned
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
Babi na Sha Uku
(SO❤)
Runtse ido tayi ba tare da ta ga mai yake shirin yi ba, ta tsorata matuk'a da yanayinshi, Idonta a runtse bakinta kawai ke motsi, girgiza kai yayi ya ciro Jallabiyarshi ta Gado ya zura, chan gefen Gado ya zauna yana shafa Mai.
Jikinta rawa kawai yake daga inda yake yaji adduar da takeyi "Allah ka tsareni da tsarewarka, Allah ka kubutar dani, Allah ka yafe mishi na san ba halinshi bane".
Wani murmushi ya subuce mishi mai kama da na takaici, ita ko ganin shirun yayi yawa ya sa ta dan bude ido, ba ta ganshi ba, ware idonta tayi ta duba gefe, abun mamaki zaune ta ganshi yana shafa Mai.
Murmushi tayi tare da gyara zamanta, tace "har raina na san ba zaka min komai ba".
Mur ya sha "Me kika zo yi?" Da murmushi a fuskarta tace "nazo ganinka ne" a tak'aice yace "Fita" tashi tayi ko a jikinta tace "to bari naje, dama ba dadewa zanyi ba, na ganka ai".
Kallon Mamaki ya bita da shi, wai ta yaya take a haka? Wulakanci ya mata fa, amma Dubeta ko a jikinta, tsakaninta da Allah babu abunda ya dameta.
Tashi yayi ya sha gabanta yace "Okay kina ji ba, duk randa kika sake zuwa min daki, sai na tari Yayanki na gaya mishi kullum sai kinzo min daki".
Kamar doll baby, haka ta kyafta idanuwanta tace "ashe kenan kullum zaka tare shi ka gaya mishi, don ni ba zan bar zuwa ganinka ba, sosai nake sonka Yayana".
Cike da takaici yace "Huh!! Wai ke bakya jin nauyin ce ma mutum kina sonshi? Ko haka kuke a Kudu? Ashe haka Matan kudu suke? Kenan a Kudu, Mata ba su da Aji? Mata ke tallan kansu? To ki saurareni da kyau, in wannan haukan da kikeyi ne kike kira da So, ki sani ni ba zan taba son Mace Mara Aji ba, ba zanso ballagaza irinki ba mai tallan kanta, Macen da zan so ko nan gaba zata kasance mai Aji, mai kunya".
Sake kyafta idonta tayi tace "Ka So ni donAllah".
Da takaici yace "Are you not listening? Maganar da na gama miki kenan, ba zan taba sonki ba, don baki da aji, bana son classless person, kina zuwa dakin Namiji, wa ya san ko dama haka kike? Wa ya san iya adadin mutanen da kika kai kanki wurinsu? Ohh, tunda kike nuna rashin tsoro a duk abunda nake yunkurin miki wayasan ko kin saba? Waya san ko ke yar hannu ce? Dallah ki fice min a daki, ki koyo kamun kai, ki zama mai Aji da har ni zan kawo kaina wurinki ba ke ki kawo kanki wurina ba kingane?".
Har ga Allah bata ma jinsa, hankalinta na gun yanayinsa, komai nashi abun burgewa ne, yanayinshi, yanayin maganarsa, yanayin fushinsa, ba abunda ya fi burgeta kamar yanda yake sa hannun damanshi yana murzan idon Hagunshi.
Murmushi cike da fuskarta tace "Har raina nake Sonka".
Takaici kamar ya kasheshi ya sa hannu ya tura mata kafadunta duka biyu yace "Dallah Mallama ki fitan min a daki" ya mata koran wulakanci, ita ko, ko a jikinta tayi murmushi ta wuce gida sadaf sadaf.
WasheGari ta sake fakar Idanun Aunty Asiya ta fada dakinshi, ba ya nan, bata ji dadi ba ko kadan, ta so ganinshi, da tunaninshi ta kwana jiya ta kuma tashi dashi jiya.
Da kallo ta bi dakin a hargitse, katifa ba gyara, duk lungu da sak'on dakin akwai karan sigarin da aka sha, ta bude toilet ta ga shima datti, ba ta son k'azanta.
Hijab dinta ta aje gefe ta hau gyaran dakin. Ta waiga ta waiga bata ga tsintsiyar shara ba, ta fita da sauri ta fada gidansu, kasancewar bango ya rushe ya sa suka daina zaman tsakar gida.
Labiba ta dauko tsintsiya da abun kwashen shara, da ledar Aerial, ta koma dakin, share dakin tayi tas, in har aka auna bolan dakin Mankas sai tayi tiya uku, kuma ba wani datti ke ciki ba illa ragowan sigari da kwali kwali, bak'ar leda ta samu ta juyesu tas ciki.
Toilet ta shiga ta wanke tas, ta bude Wardrobe din, Ghana Must Go ne, hannu ta sa ta bude zip din ta ga atamfa da laces sai shadda da yards na maza.
A ranta tace "ji kayayyakin da ba a dinka ba" a fili kuma ace "toh meyasa be dinkawa?" Wani tunani ya zo mata, ta tuna ya ce mata Babansu ya hanasu karban kayan Mancy, in ma ya gani k'onawa zaiyi, "Allah sarki, ba halin dinka kayan da Mancy ta turo muku, abun tausayi".
Kwashe su tsintsiyar tayi ta koma Gidansu.
BENCIN ESKALEY
Su 3 ke zaune a Bencin sai Eskaley da ke cikin shagonshi. Safiya ce amma ko wannensu na banka ma cikinshi hayak'i, ba su da wata damuwa, sigari kawai suke zuk'a.
Mankas daga gefe yake zuk'ar tabarshi, ganin Mota yayi ta ajiyeta a inda ta saba ajiyeta ya kalli su Tero yace "ga Jarabarban chan tazo". Baki daya suka bi gun da kallo. Mikewa Master yayi yace "wallahi warewa zanyi kafin ta iso"
Ya tashi yana niyyan guduwa yaji ta na cewa "Master gaban Babarka zan bika na lakada maka na jaki".
Chak ya tsaya tare da juyowa yana yak'en dole "Na matsu, Zan dan zagaya ne" mur ta sha tace "zagayawan uwarka, ban sigarin" kallonta ya tsayi yana kallon sigarin da yanzu ya kunnata, zaiyi asarar naira gomarshi da ita kadai ta rage mishi a dunia ya siya sigarin, muryarta yaji "za ka bani ko kuwa?" Tsaki yayi ya mik'a mata karar. Kafa ta sa ta murje shi tas, kafin ta matsa gun Haruna ta kwace nashi ta yar a kwata.
Na karshen Mankas ya zuk'a ya busa hayak'in, cikin fada yace "ka zuk'i uwarka, kuma ita ka busa ma hayak'i a fuska ba ni ba". Murmushi yayi ya tashi tsaye tare da furta sunanta "NeNe".
Iya k'arfinta ta sakar mishi Rank'washi a kai tace "Allah ya shiryeka Zaidu, nidai Wallahi—-" shiru tayi don Master, Haruna da Eskaley suka hada baki wurin k'arasa mata maganar da ta yi niyyanyi na "Zaidu Bawan Allah ba haka yake ba" kallo ta bi su dashi, so milliyan in zata ce haka, to so milliyan zasu karasa mata saboda maganar kenan "Zaidu bawan Allah" ba haka yake ba, kullum indai har ta zo to inshaAllahubsai ta fadi haka.
Mur ta sha tace "Uwarku kuke kwaikwaiya bani ba".
Gum sukayi suka ja bakinsu sukayi shiru, zama tayi kan bencin cike da isa don haka suke kullun.
Eskaley ne ya fara gaidata kafin sauran suka gaisheta har Mankas din, ta amsa tare da kallon Zaid tace "kai dai baka ji ko? Ka cigaba, kar ka fasa wannan bushe-bushen, kai ko kunya bakaji? Bakinka yayi bak'i dubeka donAllah".
Kai Zaid ya shafa yace "InshaAllah Zan bari Nene, ki tayani da addua, kai arr makaryaci, kullum haka kake cewa kuma baka bari, wallahi Zaid ka fita idona, randa zan tona maka Asiri wurin uwarka zaka sha mamakina, ka san dai ban tsoronka ko?".
Da sauri ya rude ya fara rantse ranste "wallahi Nenenmu na bari, ban k'arawa, dagaske bazan k'ara ba". Ko a jikinta don ta san k'arya ba yau ya fara shi ba, ta kuma san ba bari zaiyi ba, amam ba zata fasa mishi addua ba, harara ta galla mishi tace "ka je ka dauko Abincin cikin mota ko kuwa?".
Be tsaya tunanin yaushe tace yaje ya dauko abinci ba sai ma nufar motar da yayi da gudu.
Kallo ta bi Haruna, Master da Eskaley tace "Ce muku ku bar Shaye-shaye bata baki ne ko?".
Eskaley yace "Nenenmu zamu bari"
Kamar ta mareshi tace "dallah rufa min baki, ba kai ne dan iskan da ke saida musu ba".
Eskaley ya ja baki yayi gum.
Tsautsayi yasa Haruna cewa "ai daga yau mun bari, ba zaki taba kama mu da shan wani abu ba".
"ka min shiru ko sai na
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15 Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45