ba, sosai nake kuka, na dade kuma ina kukan, bansan minti ko awan da dauka ba ina kuka.
"DanMakaho" naji an fada
Da sauri na dago kai don ganin me min kiran nan wanda tabbas ya sanni tunda ya kirani da sunan da yan Unguwa kadai ke ce min.
Na sanshi, ina ganinshi a Unguwa, Dan shaye-shayene, ya sha rokona kudin da zai ci abinci duk da na san karya ne shaye-shaye zaiyi dadu ban taba hanashi ba, da shi da yan bencin Eskaley na sha raba musu naira dubu dubu.
Da kyar na ambaci sunashi "Haruna, me kakeyi a nan?" Haruna ya danyi daria yace ai ni nan bana sati 2 k'warara banzo nan ba, kai ne dai zan tambaya me kake anan. Ban iya ce mishi komai ba na duk'ar da kaina.
Gaskia DanMakaho Babanku ya kwafsa, ji yanda ake ganin mutuncinshi amma wa shine zai yi wannan kwafsin? Harda dukan Hajia Mancy gaban kowa, Kai ya mugun kwafsawa.
Kamar jira nake na fashe da wani sabon kukan, be lallasheni ba, bai hanani ba, bai kuma tafi ya barni ba".
Sai da na tsagaita kuka na kafin na dago kai na ga hannunshi a mik'e alamun wani abu yake so na karba daga hannun.
World kenan, ka sha shi, wallahi ka sha shi damuwar da kake ciki zai bace bat, ka dan ta6a world ba ka da wata matsala.
Kallo daya na ma kullin garin na kauda kai. Zama yayi kusa dani
Kagane ko ka sha taimaka min, ka sha fiddo ni cikin damuwa da yanayi, in ka bani kudi, kaga abunda nake siya nan, dagaske in na sha shi wallahi bana da wata sauran damuwa, wallahi World duniya ne, duk yanda kake cikin damuwa, bakinciki, kuncin rayuwa, da ka zuk'a so daya damuwar zata kwaranye, zuk'a ta biyu kuma zakaji kanka a kan gajimare, ka gwada zuk'a daya, da kanka zaka nemi k'ari, in kuma ka zuk'a damuwarka bata gushe ba kayi kan duk abunda kake so".
Runtse Ido na nayi, na yarda gajeran tunani gareni, shaidan ya buga min ganga, a cikin Cell dinnan na zubdar da duk wani tarbiyan da Mancy ta min shekara 25, Wallahi Beebs da na bude World na fara zuk'a ta hanci, sai da na zukeshi tass, Haruna ya so ya kwace amma na hanashi, burina damuwa na ta kau".
Ido na a runtse na ji ni a wani irin yanayin da ban taba shiga ba, wani yanayi mai wuyar fasali, wani yanayin da ban taba saninshi ba. Wanda suka dade a harkar da wuya su ja World fiye da biyar, ni ko na ja shi ya fi so 20, mamaki na Haruna keyi yanda ya ga nayi bagas a k'asa ido na a runtse in rausaya da kaina hagu in rausaya da shi dama.
Haruna na tsoron kar na haukace, don in yayi yawa yana sawa a zare, sunana ya fara kira
DanMakaho
DanMakaho shiru ba amsa ido na runste
A kira na uku ne na bude ido tare da sakin wani irin murmushi.
Cikin jin dadi haruna yayi wani juyi, tare da jinjina hanayenshi guda biyu alamun ya sara min gami da cewa;
MAANNNKAAAASSSSS.......
Yes Guys your one and Only Nene is here
Who's happy?
Vote and comment line by line please
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Sha Daya1⃣1⃣
(MANKAS II)
(Note: wannan Events din ya faru ne Bayan dawowan Nene daga London lokacin da Nasiban Rafeeq ta Haihu. Fahimt?)
A kan idonta a ka wuce dashi cikin motar yan sanda, ranta a bace, sai dai ya ta iya? Fuuu ta shige bayan motar da aka kawota, ko magana bata iya mishi ba ta wuce Gidan Lema.
"Banda Sakarai shanyayye, wa ke tura yaronshi police station?" Haka tayi ta fadi har ta shiga cikin Gidan Lema, Mami ta mata sannu da zuwa, Nene tace "ke yau ni naga k'awar Saude".
Sai da Mami ta dafe k'irji tace "a ina Nene?".
"Wannan Kishiyar Maryaman"
"Nene dagaske an Saki Hajia Maryam?"
"Ke ina baki kina k'in karba, Makira ce Matar nan, wai ke in gaya miki Yaro na samu bakin gate ya bani labarin duk abunda aka ma Maryama, ke fa da naje samu nayi sun ma Takwaran Zaidu Bawan Allah Rubdugu, aiko na shigar mai, na tsokale wa Uban Ido, ita kuma na lallasata".
Mami tace "yanzu Nene fitanki har kinyi Dambe?" Nene tace "aa fa ni fa ba dambe nayi ba, bugun tsiya na mata, ke dallah ina kaiki.
Ke shaida ce irin So din da Alhaji Zaki yake ma Matarshi Maryama da Yaranshi, kina zuwa Gidan Kema, kinga kyakyawar Alak'a tsakaninsu, ke kawai sai rana daya, ya auri tsohuwar Matarshi, ya zabure ya ma Matarshi duka gaban 'yan anguwa, ya cika mata saki 3 ya sa aka kwashe mata kaya, ya zo ya tsani yaranshi, ya shigo da Agola su biyu, ya fifita su fiye da yaran cikinshi, me zakice? Me kike ganin ya faru?"
Mami ta danyi jim kafin tace "ta na iya yiwuwa Chanji ne kawai, ko dokin sabon auren da yayi ne".
Hannu Nene ta sa a kai dauke da takaici tace "ke wai bakiji me nace ba, don yana dokin aure sainya juya ma Yaran cikinsa ba? Ya kike magana ne kamar ba ki san aikin asiri ba, ke da Saude ta rafka muku asiri ke da Mijinki aka rabaku tsawon shekaru?.
Mami tace "kawai banson zargin Asirin ne, tunda bamu da hujjah".
Nene tace "wai ya kike magana? In ba asiri ba meye? Hujja ya wuce wanda na karanto maki, ke wai don uwar yaron nan da ni zai sa a kulle a pirisin?".
Mami ta zaro Ido, tace ya akayi? "Aa wai mun bugar mishi Mata, ya kira YanSanda wai su tafi dani da Zaidu Bawan Allah, nace mishi ya kira min Habibu, da yaga uwar bari, sai cewa yayi a barni amma a tafi da Dan, yanzu dan na chan kulle, ki latso min Mijinki".
Sai ko gasu shigo tare da Uncle Zaid.
Nene ko ta tarbesu "Oyoyo Sannu da zuwanku" Uncle Zaid ya murmusa yace "Nenemu ni da Seebi".
Jawo hannunshi tayi ta zaunar dashi tace "wai Zaidu Bawan Allah, ina kawata Hajia Maryama da ke Tudun Matawalle wanda ka taba kaini Gidanta?" Cikin fahimtarta yace "Matar Speaker Ali Zaki?".
Tafi tayi cikin jin dadi tace "itafa"
Uncle Zaid da neman k'arin bayani yace "me ya sameta?".
Nene tace "to asiri kishiyarta ta ma Mijinta ya saketa saki 3 bayan ya lakada mata na jaki, ya kuma juya ma yaran Baya, kai wai jiya suka kori su Raliya masu abincin da na kai ma Maryama, aiko Raliya tazo ta gaya min duk abunda ke faruwa, ni ko na wanke kafa na sa Sabitu ya kaini Gidan.
Kai wai daga isa na naga sun saka takwaranka Zaidu a tsakiya suba ta jibgarshi, ni ko naci dammarata nayi kansu".
Kai wai sai ga 'yan Sanda sunzo wai tafiya da mu, wai zasu samu bayan Karta, wai mun bigi Matarshi, niko nace wallahi bai isa ba, sai dai a tafi da danshi ba dai ni ba, kuma nace a latso min Habibu ai ba su kadai bane Manya".
Daddyn Rafeeq ya jinjina kai yace "Gaskia da Ali Zaki yayi Babban kuskusre da yayi gigin Kulleki" Nene ta yi darian jin dadi tace "yo shiyasa na bashi tsoro wallahi, shegen ya tsorata, ai gaba da gabanta".
Uncle Zaid ya girgiza kai yace "wai Nenenmu ni da Seebi yanzu dambe kikayi? wai ba ma na hanaki Shiga abunda bai shafeki ba?".
"Yo ai naga Zaidu Bawan Allah ko meye nama Hajia Maryama ban fadi ba, matar da ta soni kamar Uwarta, ke Aisha da muke Makka wani ciwo da nayi, wallahi ita ke hidima dani, duk nisan Samanmu sai ta sauki ta siya min abinci da magani, ta rirrikeni in zan fadi, ni ko gani da raki da fada, yanda kika san diyata haka nake watseta , duk tsarabar da na maku ita ke zabar maku kuma so dayawa ita ke biyan kudin, karamcin Maryama mara misaltuwa ne, to yanzu don na taimaka ma yaranta sai ace nayi shiga sharo ba shanu?".
Duk suka jinjina kai, tace "Alhaji Habibu DonAllah kayi man taimako, kaje polis station ka sa a firdo Takwaran Zaidu Bawan Allah, kuje kuyi belinshi, wallahi dan gata ne, be saba irin rayuwar nan ba".
Daddyn Feeq yace "InshaAllah Nene, bari inyi waya inji yana a wani Police Station ne".
Ba jimawa yace "yana Police Station din Tudun Matawalle, barin je inji". Nene tayi wuf tace "muje". Gardama da ita bata lokacine, fits sukayi su Uku, Nene da Alhaji Habibu da kuma Zaid BawanAllah.
Ko da suka isa Police Station din tuni DPO ya fito ya tarbesu, ba bata Lokaci Alhaji Habib ya buk'aci a saki dan Gidan Alhaji Ali Zaki da aka kawo dazun". Jim DPO yayi kafin yace "anya kuwa Alhaji? Alhaji Zaki yace mu rik'eshi kar mu sake mu ba kowa Bail dinshi, kayi hakuri Sir yaron kangararre ne, Mahaifinshi ke da rights akan shi kuma yace a hukuntashi".
Nan Nene ta fara surfa musu ruwan Bala'i wanda Su Haruna da ke bayan Karta sun ji banda Zaid da ya dade a duniyar da World ta kaishi. Da k'yar Uncle Zaid ya firda Nene daga police station din don da har ta fara maganar dukan DPO.
Daga Station basu wuce ko ina ba sai Gidan Alhaji Zaki, iso aka musu har parlo, tare da hamshak'iyar suka fito, suna ganin Nene Shafaatu ta sha mur, riko hannunta Alhaji Zaki yayi suka karasa cikinParlon, hannu ya ba Zaid da Daddyn Feeq sukayi Musabaha".
Alhaji Habibu yace "Alhaji Ali, Nene ta zo mana da wata magana wai ka sanya an kulle Zaid, munje muyi bailing dinshi sunje ba bail, Alhaji komai yayi zafi maganinshi Allah, kayi hakuri ka firdoshi".
Kallon Hajia Shafa yayi ta banka mishi harara, lokaci daya ya fara bala'i "Haba Alhaji Lema, wai ni ina ruwanku dani da iyalina? Shin Zaid din ba yaro na bane? Ina ruwanku ko yanka shi zanyi? DonAllah ina ganin Girmanka, ka tsaya a nan, ba zan dauki shiga sharo ba shanu ba".
Nene ta katseshi ta hanyar cewa "Kai dallah sakarai rufa ma wa mutane baki, ka na zaune sai juya ka ake kamar Masa, kai Asirin ma sai fa sakarai take ma tasiri, shiyasa da ta kamaka tayi maka mugun kamu, to wallahi ka natsu kayi wa kanka kanka fada".
Ta matsa kusa da Shafa'atu ta sake mata wani zazzafan Rankwashi wanda ya sanyata ihu, a tare Alhaji Zaki da Zaid Lema suka tashi, Zaid yayi kan Nene, Zaid ya janyeta yana "Haba Nene".
"Ni Zaidu wallahi ban san harka da Stupid, nidai a Sako min Amanar da Allah ya bani".
Shafa'atu wanda rankwashin ya shigeta ta fara kuka "wallahi Alhajina sai ka sakeni, ba zan iya ba, ace har Gidana wata tsohuwa zata dinga bina tana duka na? Kamar yar yarinya? Ni wallahi ba zan iya ba".
Hankalin Ali Zaki ya tashi da sauri yace "Alhaji Habib Lema, ba gaya ma ina mugun jin kunyarka, ku fitar min daga Gida, ku fita daga harkan Gidana, wallahi in Mamarka ta sake taba Matata wallahi ba zamu kwashe da kyau ba".
Aiko ya tunsura Nene tace "Allah ya tsine maka in har ka bari muka kwashe da kyau, Shege, mara hankali".
Zaid ya ja hannunta tayi ta fizgewa, da k'yar ya iya fitar da Nene daga Parlon, ga Nene da karfi.
"Alhaji Habib Lema, ka ja mata kunne, ta fita daga harkan Gidana, ko kuma hukuma ta shiga tsakaninmu, ai mata Iyaka da Gidana".
Daddyn Feeq be iya magana ba sai dai fitan da yayi a zucciye.
A Mota yace "Don Girman Allah Nene ki fita daga harkan Gidan Zaki, Nene ta ya zan iya dauka in wani ya miki rashin kunya, Nene ki sa mishi ido, duk daren dadewa gaskia zata bayyana, Dan shi ne, chan cikin ranshi akwai sonshi a cikin shi, donAllah kar ki sake zuwa Gidan".
Zaid ma ya shiga lallashinta da tausassun lafazi, yana cewa ta bisu da addua, Allah ne zai kare ma Maryama Yaranta.
Takaici ya hana Nene cewa komai sai Girgiza k'afar da takeyi tana tunanin yanda zata shigo Gidan Alhaji Zaki karfe ukun dare ta ci ubansu daga shi har Matar.
***
Kwana na 2 a Cell, banda wata damuwa, saboda me? Saboda World, sosai yake batar min da duk wata damuwata. Baba bai zo ba, bai kuma ce a sakeni ba, so ba ranar fita daga wannan wurin.
A kwana na ukun ne Ina zaune kawai naga wani kurtu ya lek'o yace "kai Dan Gidan Zaki fito" mamaki ya cikani, to Baba ya hakura kenan, ya sa an firdoni, tashi nayi na fita sai ganin Dogarawa fiye da uku tsaye da dorinarsu.
Dogarawan nan suka tisa k'eyata bayan sun sanar dani cewa mai Martaba Sarkin Katsina ke nema na. Motar Emirates muka Shiga Har Fadar Sarki dake K'ofar Soro, wani dogaribya fara shiga bayan Mintuna Goma sai gashi ya dawo yace mu shiga.
Ina Shiga Fadar gabana ya fadi, ganin Dalo durk'use gaban Fada, daga gefe kuma Baba ne da Aunty Shafa, sai Hudu da Annah, sai wata da ke Durk'ushe tana ta bayani ta bawa Fada baya".
Muryarta kawai ya ankarar dani ko wacece.
"Nene ce".
Kwakwalwata ta fahimci cewa Nene ce dai ta kawo Baba k'ara.
****
Tun bayan dawowar su Nene daga Gidan Zaki ta rasa sukuni, bata da wani madafa ga shi Zaidu kamar yayi kuka wurin rokonta a kan kar ta sake zuwa Gidan Alhaji Zaki. Bata san ya zatayi ba har kwana 2 suka shide bata da wani dabara, duk tayi sukuku, bari ta kira Seebinta ko zataji sanyi.
Zuwa yanzu Nene ta iya kiran Mutanen London a waya da taimakon hotunan su wanda Zaidu Bawan Allah ya sa a jikin ko wani Contact, Hoton Seebi ta lalubo cikin contacts din ta danna kira don tana da kudi fiye da Dubu 10 cikin wayar duk don kiran Mutanen London wanda Zaidu BawanAllah ne ke sawa".
"Hellooo Neh-Neh" taji muryarshi
Da sauri tace "Dunkum. Kai na kira?" Ta na mai dauke wayan daga kunnenta tana sake duba screen din don ganin wa ta kira kuma dai hoton Nasibar ne.
Mur ta sha kamar yana gabanta tace "kai dallah ba mai wayar wayarta". Dan daria yayi yace "Neh-Neh kinyi missing dina ne? Baki nemeni kwana biyu ba".
Yau bata da lokacinshi cewa tayi "kai Arr, ina Nasibar?" Dan daria ya sakeyi yace "Sunje wani Birthday Party ita da Yarona".
Tsaki Nene tayi tace "Wani yace ba yaronka bane? Rasa kunya beran kitchen, kace ta kirani in ta dawo".
"Wai ya Neh-Neh yau sai gwasuleni akeyi? Wai ba mun shirya ba? Ai mun bar fada ko? Ko yau kin tuna kanki a Airport ne wurin masu Red din Kunne" ya karashe yana daria.
"Wallahi Dunkum ubanka zanci"
Guntun tsaki yayi yace "kinga Matsalarki ko Zagi? Wai ba Uncle Zaidu ya hanaki Zagi ba? Barin kirashi in gaya mai".
Da sauri ta katseshi "kai dallah tsaya kaji, ka tuna Hajia Maryama Mamarsu Takwaran Zaidu BawanAllah da Dalo?".
Rafeeq yace "Eh na tuna kawarki da kike bamu labarinta, me miki Wanki a Makka".
Cike da jin dadi tace "Good, good Dunkum, to wallahi Mijinta ya mata Saki Uku, ya mata dukkan tsiya gaban Mutane" nan ta shiga bashi labari kamar a gabanta akayi, har zuwa zuwanta na farko da dukan da ta ma shafa, da kulle Danmakaho da akayi da zuwan su karban bailing dinshi".
Ran Rafeeq ya baci, wai yaushe mutane zasu bar zama Victim din Matar Uba? Karon shi da Saude ya tuno, abubuwan da tayi da yanda ta shiga tsakaninshi da Mahaifiyarshi ya tuno, guntun tsaki yayi yace
"Neh-neh Wai are Women Selfish?".
Nene tace "Uwar me? Hausa zakai man dallah".
Tsaki yayi yace "Neh-neh tunda Baban bai dubi Girman Daddy ba ya ci muku mutunci, ai yana da magabata, in ya fi karfin Magabata ai bai fi karfin Hukuma ba, in ko yafi karfinsu bai isa ya fi Karfin Baban Kowa na Katsina ba".
Nene tace "Sarkin Katsina".
Rafeeq yace "Shine Magana kawai, Neh-neh ba tare Kukaje Makka da Amaryar Sarki ba?".
Nene cikin Jin dadi tace "ehmana dakin mu daya da matar sarki da Maryama".
Rafeeq yace "ki samu ganinta ta miki hanya kawai".
Allah Dunkum? Yace "wallahi kuwa"
Tace "Zaidu Bawan Allah ya rokeni kan na fita daga harkarsu wallahi".
Rafeeq yace "Nene sharesu wallahi, ki taimaka musu, ni na san sharrin Matar Uba, DonAllah kar ki karaya".
Cikin Samun Karfin Guiwa tace "tankiyu Dunkum, i lobiyu, i miss you Dunkum".
Yace "Yeah Right i miss you too My Amazing Granny".
Ji yayi tace "Uwarka ka zaga"
Tsaki yayi yace "kina da damuwa wallahi, ke fa kika fara turancin, kuma in an miki sai ya zama laifi?"
"Oho dai kace ma Matarka in ta ga dama ta kirani" dif ta kashe wayar.
Ta yanke Hukunci, Washegari karfe 8 na safe tafita, bata gaya ma kowa ba balle a hanata, ko driver bata bi ta kanshi ba ta samu A daidaita Sahu ta hau sai Gidan Sarki, Part din Gimbiya, aka ma Nene iso, bayan wasu mintuna Gimbiya ta fito, aiko ta rungumo Nene, suka gaisa cike da mutunta Juna.
Nene tace "mai Martaba na nan? Shi nazo gani? Ko yana da bak'i?" Gimbiya tace "ko da bak'i ai zai ga Nenenmu ina fatan Lafiya?"
Nene tace "k'aran Sakaran Mijin Maryama na kawo".
Gimbiya tace "wani abun ya sakeyi? Ko sati biyu baayi ba da Maryama ta zo nan maganar rik'on yaya wai don ya saketa sai dai su bita".
Nene tace "kinji Gilu ko? Ashe kun ma san da maganar, to shekaran jiya wacchan naje Gidan, naga matar da kanenta da uban sun mishi taron dangi sai bugunsh suke wai bayan nan kuma ya kulleshi a Police station, ke cin kashi kala kala ake musu a gidan nan, nace aiko suna da Gata, shine na garzayo don Ganin Mai Martaba". Gimbiya ta mik'e tace barinje in mai bayani.
Bayan Sarki ya saurari Nene ya aika a Kira Mishi Alhaji Ali Zaki da Iyalanshi Gabaki daya, sannan ya tura Police Station a sako Zaid.
Wannan Kenan
*****
"Aa Allah ya kara ma Imani, Matata suka tarar mawa, Nene kuwa harni ta tsokale wa ido" Nene tayi karaf tace "ba gaskia bane, kaine dai kuka taran mashi, ni ina ni ina dambe? Ina neman shekara Saba'in da dori? Ta ya tsohuwa kamata zata iya Dambe da kai da wanchan matashin da kuma Matarka? DonAllah Mai Martaba
Showing 39001 words to 42000 words out of 132816 words
"DanMakaho" naji an fada
Da sauri na dago kai don ganin me min kiran nan wanda tabbas ya sanni tunda ya kirani da sunan da yan Unguwa kadai ke ce min.
Na sanshi, ina ganinshi a Unguwa, Dan shaye-shayene, ya sha rokona kudin da zai ci abinci duk da na san karya ne shaye-shaye zaiyi dadu ban taba hanashi ba, da shi da yan bencin Eskaley na sha raba musu naira dubu dubu.
Da kyar na ambaci sunashi "Haruna, me kakeyi a nan?" Haruna ya danyi daria yace ai ni nan bana sati 2 k'warara banzo nan ba, kai ne dai zan tambaya me kake anan. Ban iya ce mishi komai ba na duk'ar da kaina.
Gaskia DanMakaho Babanku ya kwafsa, ji yanda ake ganin mutuncinshi amma wa shine zai yi wannan kwafsin? Harda dukan Hajia Mancy gaban kowa, Kai ya mugun kwafsawa.
Kamar jira nake na fashe da wani sabon kukan, be lallasheni ba, bai hanani ba, bai kuma tafi ya barni ba".
Sai da na tsagaita kuka na kafin na dago kai na ga hannunshi a mik'e alamun wani abu yake so na karba daga hannun.
World kenan, ka sha shi, wallahi ka sha shi damuwar da kake ciki zai bace bat, ka dan ta6a world ba ka da wata matsala.
Kallo daya na ma kullin garin na kauda kai. Zama yayi kusa dani
Kagane ko ka sha taimaka min, ka sha fiddo ni cikin damuwa da yanayi, in ka bani kudi, kaga abunda nake siya nan, dagaske in na sha shi wallahi bana da wata sauran damuwa, wallahi World duniya ne, duk yanda kake cikin damuwa, bakinciki, kuncin rayuwa, da ka zuk'a so daya damuwar zata kwaranye, zuk'a ta biyu kuma zakaji kanka a kan gajimare, ka gwada zuk'a daya, da kanka zaka nemi k'ari, in kuma ka zuk'a damuwarka bata gushe ba kayi kan duk abunda kake so".
Runtse Ido na nayi, na yarda gajeran tunani gareni, shaidan ya buga min ganga, a cikin Cell dinnan na zubdar da duk wani tarbiyan da Mancy ta min shekara 25, Wallahi Beebs da na bude World na fara zuk'a ta hanci, sai da na zukeshi tass, Haruna ya so ya kwace amma na hanashi, burina damuwa na ta kau".
Ido na a runtse na ji ni a wani irin yanayin da ban taba shiga ba, wani yanayi mai wuyar fasali, wani yanayin da ban taba saninshi ba. Wanda suka dade a harkar da wuya su ja World fiye da biyar, ni ko na ja shi ya fi so 20, mamaki na Haruna keyi yanda ya ga nayi bagas a k'asa ido na a runtse in rausaya da kaina hagu in rausaya da shi dama.
Haruna na tsoron kar na haukace, don in yayi yawa yana sawa a zare, sunana ya fara kira
DanMakaho
DanMakaho shiru ba amsa ido na runste
A kira na uku ne na bude ido tare da sakin wani irin murmushi.
Cikin jin dadi haruna yayi wani juyi, tare da jinjina hanayenshi guda biyu alamun ya sara min gami da cewa;
MAANNNKAAAASSSSS.......
Yes Guys your one and Only Nene is here
Who's happy?
Vote and comment line by line please
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Sha Daya1⃣1⃣
(MANKAS II)
(Note: wannan Events din ya faru ne Bayan dawowan Nene daga London lokacin da Nasiban Rafeeq ta Haihu. Fahimt?)
A kan idonta a ka wuce dashi cikin motar yan sanda, ranta a bace, sai dai ya ta iya? Fuuu ta shige bayan motar da aka kawota, ko magana bata iya mishi ba ta wuce Gidan Lema.
"Banda Sakarai shanyayye, wa ke tura yaronshi police station?" Haka tayi ta fadi har ta shiga cikin Gidan Lema, Mami ta mata sannu da zuwa, Nene tace "ke yau ni naga k'awar Saude".
Sai da Mami ta dafe k'irji tace "a ina Nene?".
"Wannan Kishiyar Maryaman"
"Nene dagaske an Saki Hajia Maryam?"
"Ke ina baki kina k'in karba, Makira ce Matar nan, wai ke in gaya miki Yaro na samu bakin gate ya bani labarin duk abunda aka ma Maryama, ke fa da naje samu nayi sun ma Takwaran Zaidu Bawan Allah Rubdugu, aiko na shigar mai, na tsokale wa Uban Ido, ita kuma na lallasata".
Mami tace "yanzu Nene fitanki har kinyi Dambe?" Nene tace "aa fa ni fa ba dambe nayi ba, bugun tsiya na mata, ke dallah ina kaiki.
Ke shaida ce irin So din da Alhaji Zaki yake ma Matarshi Maryama da Yaranshi, kina zuwa Gidan Kema, kinga kyakyawar Alak'a tsakaninsu, ke kawai sai rana daya, ya auri tsohuwar Matarshi, ya zabure ya ma Matarshi duka gaban 'yan anguwa, ya cika mata saki 3 ya sa aka kwashe mata kaya, ya zo ya tsani yaranshi, ya shigo da Agola su biyu, ya fifita su fiye da yaran cikinshi, me zakice? Me kike ganin ya faru?"
Mami ta danyi jim kafin tace "ta na iya yiwuwa Chanji ne kawai, ko dokin sabon auren da yayi ne".
Hannu Nene ta sa a kai dauke da takaici tace "ke wai bakiji me nace ba, don yana dokin aure sainya juya ma Yaran cikinsa ba? Ya kike magana ne kamar ba ki san aikin asiri ba, ke da Saude ta rafka muku asiri ke da Mijinki aka rabaku tsawon shekaru?.
Mami tace "kawai banson zargin Asirin ne, tunda bamu da hujjah".
Nene tace "wai ya kike magana? In ba asiri ba meye? Hujja ya wuce wanda na karanto maki, ke wai don uwar yaron nan da ni zai sa a kulle a pirisin?".
Mami ta zaro Ido, tace ya akayi? "Aa wai mun bugar mishi Mata, ya kira YanSanda wai su tafi dani da Zaidu Bawan Allah, nace mishi ya kira min Habibu, da yaga uwar bari, sai cewa yayi a barni amma a tafi da Dan, yanzu dan na chan kulle, ki latso min Mijinki".
Sai ko gasu shigo tare da Uncle Zaid.
Nene ko ta tarbesu "Oyoyo Sannu da zuwanku" Uncle Zaid ya murmusa yace "Nenemu ni da Seebi".
Jawo hannunshi tayi ta zaunar dashi tace "wai Zaidu Bawan Allah, ina kawata Hajia Maryama da ke Tudun Matawalle wanda ka taba kaini Gidanta?" Cikin fahimtarta yace "Matar Speaker Ali Zaki?".
Tafi tayi cikin jin dadi tace "itafa"
Uncle Zaid da neman k'arin bayani yace "me ya sameta?".
Nene tace "to asiri kishiyarta ta ma Mijinta ya saketa saki 3 bayan ya lakada mata na jaki, ya kuma juya ma yaran Baya, kai wai jiya suka kori su Raliya masu abincin da na kai ma Maryama, aiko Raliya tazo ta gaya min duk abunda ke faruwa, ni ko na wanke kafa na sa Sabitu ya kaini Gidan.
Kai wai daga isa na naga sun saka takwaranka Zaidu a tsakiya suba ta jibgarshi, ni ko naci dammarata nayi kansu".
Kai wai sai ga 'yan Sanda sunzo wai tafiya da mu, wai zasu samu bayan Karta, wai mun bigi Matarshi, niko nace wallahi bai isa ba, sai dai a tafi da danshi ba dai ni ba, kuma nace a latso min Habibu ai ba su kadai bane Manya".
Daddyn Rafeeq ya jinjina kai yace "Gaskia da Ali Zaki yayi Babban kuskusre da yayi gigin Kulleki" Nene ta yi darian jin dadi tace "yo shiyasa na bashi tsoro wallahi, shegen ya tsorata, ai gaba da gabanta".
Uncle Zaid ya girgiza kai yace "wai Nenenmu ni da Seebi yanzu dambe kikayi? wai ba ma na hanaki Shiga abunda bai shafeki ba?".
Gimtsa baki tayi tace "yi hakuri Mamman".
Mami tayi daria tace "yau Zaidu Bawan Allahn zaa watse?".
"Yo ai naga Zaidu Bawan Allah ko meye nama Hajia Maryama ban fadi ba, matar da ta soni kamar Uwarta, ke Aisha da muke Makka wani ciwo da nayi, wallahi ita ke hidima dani, duk nisan Samanmu sai ta sauki ta siya min abinci da magani, ta rirrikeni in zan fadi, ni ko gani da raki da fada, yanda kika san diyata haka nake watseta , duk tsarabar da na maku ita ke zabar maku kuma so dayawa ita ke biyan kudin, karamcin Maryama mara misaltuwa ne, to yanzu don na taimaka ma yaranta sai ace nayi shiga sharo ba shanu?".
Duk suka jinjina kai, tace "Alhaji Habibu DonAllah kayi man taimako, kaje polis station ka sa a firdo Takwaran Zaidu Bawan Allah, kuje kuyi belinshi, wallahi dan gata ne, be saba irin rayuwar nan ba".
Daddyn Feeq yace "InshaAllah Nene, bari inyi waya inji yana a wani Police Station ne".
Ba jimawa yace "yana Police Station din Tudun Matawalle, barin je inji". Nene tayi wuf tace "muje". Gardama da ita bata lokacine, fits sukayi su Uku, Nene da Alhaji Habibu da kuma Zaid BawanAllah.
Ko da suka isa Police Station din tuni DPO ya fito ya tarbesu, ba bata Lokaci Alhaji Habib ya buk'aci a saki dan Gidan Alhaji Ali Zaki da aka kawo dazun". Jim DPO yayi kafin yace "anya kuwa Alhaji? Alhaji Zaki yace mu rik'eshi kar mu sake mu ba kowa Bail dinshi, kayi hakuri Sir yaron kangararre ne, Mahaifinshi ke da rights akan shi kuma yace a hukuntashi".
Nan Nene ta fara surfa musu ruwan Bala'i wanda Su Haruna da ke bayan Karta sun ji banda Zaid da ya dade a duniyar da World ta kaishi. Da k'yar Uncle Zaid ya firda Nene daga police station din don da har ta fara maganar dukan DPO.
Daga Station basu wuce ko ina ba sai Gidan Alhaji Zaki, iso aka musu har parlo, tare da hamshak'iyar suka fito, suna ganin Nene Shafaatu ta sha mur, riko hannunta Alhaji Zaki yayi suka karasa cikinParlon, hannu ya ba Zaid da Daddyn Feeq sukayi Musabaha".
Alhaji Habibu yace "Alhaji Ali, Nene ta zo mana da wata magana wai ka sanya an kulle Zaid, munje muyi bailing dinshi sunje ba bail, Alhaji komai yayi zafi maganinshi Allah, kayi hakuri ka firdoshi".
Kallon Hajia Shafa yayi ta banka mishi harara, lokaci daya ya fara bala'i "Haba Alhaji Lema, wai ni ina ruwanku dani da iyalina? Shin Zaid din ba yaro na bane? Ina ruwanku ko yanka shi zanyi? DonAllah ina ganin Girmanka, ka tsaya a nan, ba zan dauki shiga sharo ba shanu ba".
Nene ta katseshi ta hanyar cewa "Kai dallah sakarai rufa ma wa mutane baki, ka na zaune sai juya ka ake kamar Masa, kai Asirin ma sai fa sakarai take ma tasiri, shiyasa da ta kamaka tayi maka mugun kamu, to wallahi ka natsu kayi wa kanka kanka fada".
Ta matsa kusa da Shafa'atu ta sake mata wani zazzafan Rankwashi wanda ya sanyata ihu, a tare Alhaji Zaki da Zaid Lema suka tashi, Zaid yayi kan Nene, Zaid ya janyeta yana "Haba Nene".
"Ni Zaidu wallahi ban san harka da Stupid, nidai a Sako min Amanar da Allah ya bani".
Shafa'atu wanda rankwashin ya shigeta ta fara kuka "wallahi Alhajina sai ka sakeni, ba zan iya ba, ace har Gidana wata tsohuwa zata dinga bina tana duka na? Kamar yar yarinya? Ni wallahi ba zan iya ba".
Hankalin Ali Zaki ya tashi da sauri yace "Alhaji Habib Lema, ba gaya ma ina mugun jin kunyarka, ku fitar min daga Gida, ku fita daga harkan Gidana, wallahi in Mamarka ta sake taba Matata wallahi ba zamu kwashe da kyau ba".
Aiko ya tunsura Nene tace "Allah ya tsine maka in har ka bari muka kwashe da kyau, Shege, mara hankali".
Zaid ya ja hannunta tayi ta fizgewa, da k'yar ya iya fitar da Nene daga Parlon, ga Nene da karfi.
"Alhaji Habib Lema, ka ja mata kunne, ta fita daga harkan Gidana, ko kuma hukuma ta shiga tsakaninmu, ai mata Iyaka da Gidana".
Daddyn Feeq be iya magana ba sai dai fitan da yayi a zucciye.
A Mota yace "Don Girman Allah Nene ki fita daga harkan Gidan Zaki, Nene ta ya zan iya dauka in wani ya miki rashin kunya, Nene ki sa mishi ido, duk daren dadewa gaskia zata bayyana, Dan shi ne, chan cikin ranshi akwai sonshi a cikin shi, donAllah kar ki sake zuwa Gidan".
Zaid ma ya shiga lallashinta da tausassun lafazi, yana cewa ta bisu da addua, Allah ne zai kare ma Maryama Yaranta.
Takaici ya hana Nene cewa komai sai Girgiza k'afar da takeyi tana tunanin yanda zata shigo Gidan Alhaji Zaki karfe ukun dare ta ci ubansu daga shi har Matar.
***
Kwana na 2 a Cell, banda wata damuwa, saboda me? Saboda World, sosai yake batar min da duk wata damuwata. Baba bai zo ba, bai kuma ce a sakeni ba, so ba ranar fita daga wannan wurin.
A kwana na ukun ne Ina zaune kawai naga wani kurtu ya lek'o yace "kai Dan Gidan Zaki fito" mamaki ya cikani, to Baba ya hakura kenan, ya sa an firdoni, tashi nayi na fita sai ganin Dogarawa fiye da uku tsaye da dorinarsu.
Dogarawan nan suka tisa k'eyata bayan sun sanar dani cewa mai Martaba Sarkin Katsina ke nema na. Motar Emirates muka Shiga Har Fadar Sarki dake K'ofar Soro, wani dogaribya fara shiga bayan Mintuna Goma sai gashi ya dawo yace mu shiga.
Ina Shiga Fadar gabana ya fadi, ganin Dalo durk'use gaban Fada, daga gefe kuma Baba ne da Aunty Shafa, sai Hudu da Annah, sai wata da ke Durk'ushe tana ta bayani ta bawa Fada baya".
Muryarta kawai ya ankarar dani ko wacece.
"Nene ce".
Kwakwalwata ta fahimci cewa Nene ce dai ta kawo Baba k'ara.
****
Tun bayan dawowar su Nene daga Gidan Zaki ta rasa sukuni, bata da wani madafa ga shi Zaidu kamar yayi kuka wurin rokonta a kan kar ta sake zuwa Gidan Alhaji Zaki. Bata san ya zatayi ba har kwana 2 suka shide bata da wani dabara, duk tayi sukuku, bari ta kira Seebinta ko zataji sanyi.
Zuwa yanzu Nene ta iya kiran Mutanen London a waya da taimakon hotunan su wanda Zaidu Bawan Allah ya sa a jikin ko wani Contact, Hoton Seebi ta lalubo cikin contacts din ta danna kira don tana da kudi fiye da Dubu 10 cikin wayar duk don kiran Mutanen London wanda Zaidu BawanAllah ne ke sawa".
"Hellooo Neh-Neh" taji muryarshi
Da sauri tace "Dunkum. Kai na kira?" Ta na mai dauke wayan daga kunnenta tana sake duba screen din don ganin wa ta kira kuma dai hoton Nasibar ne.
Mur ta sha kamar yana gabanta tace "kai dallah ba mai wayar wayarta". Dan daria yayi yace "Neh-Neh kinyi missing dina ne? Baki nemeni kwana biyu ba".
Yau bata da lokacinshi cewa tayi "kai Arr, ina Nasibar?" Dan daria ya sakeyi yace "Sunje wani Birthday Party ita da Yarona".
Tsaki Nene tayi tace "Wani yace ba yaronka bane? Rasa kunya beran kitchen, kace ta kirani in ta dawo".
"Wai ya Neh-Neh yau sai gwasuleni akeyi? Wai ba mun shirya ba? Ai mun bar fada ko? Ko yau kin tuna kanki a Airport ne wurin masu Red din Kunne" ya karashe yana daria.
"Wallahi Dunkum ubanka zanci"
Guntun tsaki yayi yace "kinga Matsalarki ko Zagi? Wai ba Uncle Zaidu ya hanaki Zagi ba? Barin kirashi in gaya mai".
Da sauri ta katseshi "kai dallah tsaya kaji, ka tuna Hajia Maryama Mamarsu Takwaran Zaidu BawanAllah da Dalo?".
Rafeeq yace "Eh na tuna kawarki da kike bamu labarinta, me miki Wanki a Makka".
Cike da jin dadi tace "Good, good Dunkum, to wallahi Mijinta ya mata Saki Uku, ya mata dukkan tsiya gaban Mutane" nan ta shiga bashi labari kamar a gabanta akayi, har zuwa zuwanta na farko da dukan da ta ma shafa, da kulle Danmakaho da akayi da zuwan su karban bailing dinshi".
Ran Rafeeq ya baci, wai yaushe mutane zasu bar zama Victim din Matar Uba? Karon shi da Saude ya tuno, abubuwan da tayi da yanda ta shiga tsakaninshi da Mahaifiyarshi ya tuno, guntun tsaki yayi yace
"Neh-neh Wai are Women Selfish?".
Nene tace "Uwar me? Hausa zakai man dallah".
Tsaki yayi yace "Neh-neh tunda Baban bai dubi Girman Daddy ba ya ci muku mutunci, ai yana da magabata, in ya fi karfin Magabata ai bai fi karfin Hukuma ba, in ko yafi karfinsu bai isa ya fi Karfin Baban Kowa na Katsina ba".
Nene tace "Sarkin Katsina".
Rafeeq yace "Shine Magana kawai, Neh-neh ba tare Kukaje Makka da Amaryar Sarki ba?".
Nene cikin Jin dadi tace "ehmana dakin mu daya da matar sarki da Maryama".
Rafeeq yace "ki samu ganinta ta miki hanya kawai".
Allah Dunkum? Yace "wallahi kuwa"
Tace "Zaidu Bawan Allah ya rokeni kan na fita daga harkarsu wallahi".
Rafeeq yace "Nene sharesu wallahi, ki taimaka musu, ni na san sharrin Matar Uba, DonAllah kar ki karaya".
Cikin Samun Karfin Guiwa tace "tankiyu Dunkum, i lobiyu, i miss you Dunkum".
Yace "Yeah Right i miss you too My Amazing Granny".
Ji yayi tace "Uwarka ka zaga"
Tsaki yayi yace "kina da damuwa wallahi, ke fa kika fara turancin, kuma in an miki sai ya zama laifi?"
"Oho dai kace ma Matarka in ta ga dama ta kirani" dif ta kashe wayar.
Ta yanke Hukunci, Washegari karfe 8 na safe tafita, bata gaya ma kowa ba balle a hanata, ko driver bata bi ta kanshi ba ta samu A daidaita Sahu ta hau sai Gidan Sarki, Part din Gimbiya, aka ma Nene iso, bayan wasu mintuna Gimbiya ta fito, aiko ta rungumo Nene, suka gaisa cike da mutunta Juna.
Nene tace "mai Martaba na nan? Shi nazo gani? Ko yana da bak'i?" Gimbiya tace "ko da bak'i ai zai ga Nenenmu ina fatan Lafiya?"
Nene tace "k'aran Sakaran Mijin Maryama na kawo".
Gimbiya tace "wani abun ya sakeyi? Ko sati biyu baayi ba da Maryama ta zo nan maganar rik'on yaya wai don ya saketa sai dai su bita".
Nene tace "kinji Gilu ko? Ashe kun ma san da maganar, to shekaran jiya wacchan naje Gidan, naga matar da kanenta da uban sun mishi taron dangi sai bugunsh suke wai bayan nan kuma ya kulleshi a Police station, ke cin kashi kala kala ake musu a gidan nan, nace aiko suna da Gata, shine na garzayo don Ganin Mai Martaba". Gimbiya ta mik'e tace barinje in mai bayani.
Bayan Sarki ya saurari Nene ya aika a Kira Mishi Alhaji Ali Zaki da Iyalanshi Gabaki daya, sannan ya tura Police Station a sako Zaid.
Wannan Kenan
*****
"Aa Allah ya kara ma Imani, Matata suka tarar mawa, Nene kuwa harni ta tsokale wa ido" Nene tayi karaf tace "ba gaskia bane, kaine dai kuka taran mashi, ni ina ni ina dambe? Ina neman shekara Saba'in da dori? Ta ya tsohuwa kamata zata iya Dambe da kai da wanchan matashin da kuma Matarka? DonAllah Mai Martaba
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14 Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45