takaice zan iya shan kwalin cigari biyar a rana shisa 'yan bencin Eskaley suke ce min MANKAS.
Hello Bibilicious fans, afuwan, komai ya daidaita nagode da adduoinku da fatan alherinku gareni.
#Ilove
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Tara (ABUNDA YA FARU)
Labiba na ta girgiza kai tace "donAllah ka gaya min mai ya maidaka haka?".
Dan kallonta yayi lafij yace "are you not listening? Ba ki fahimci duk abunda na fada miki ba yanzu? Isnt it obvious? Matar Uba ta maidani haka, ke ko komai sai an gaya miki kafin ki fahimta?".
Sausauta murya Labiba tayi tace "naji, ina son sanin Meyasa ka fara shaye-shaye? Wacce rana ka fara shan Sigari? Meye dalilinka na shan Sigari?"
Kallonta kawai DanMakaho yayi, mai take so ya sanar da ita baya ga abunda ya gaya mata yanzu? Ya lura ta na da naci sosai, tsaki yayi ya yayi hanyar k'ofa yace;
"Nagaya miki yunwa nakeji, ina da buk'atar cin abinci".
Gunguni tayi tace "da kana jin yunwa da ba ka banka ma cikinka wuta da sassafe ba".
Waigowa yayi yace "me kikace?"
Baki ta zumburo tace "fa banyi magana ba".
Kai ya girgiza sosai yace "kina wasa dani Labiba, zan miki hankali"
Ya sa kai ya fice, da sauri ta mik'e tsaye ta figi jakkarta ta bi bayanshi.
"Tsaya, ya zaka barni a nan?" Be juyo ba yace "dama ni na kawo ki?" "To wai ta ina zan fita?" Bai fasa tafiyar ba yace "ta inda kika shigo".
"Seriously?" Bai amsata ba yayi gaba abunshi, ba ta da zabin da ya wuce ta tsallaka fasassun bulo ta ketara zuwa Gidansu.
**__**_**_**_**_**_**_
Wannan Sakin da Alhaji Ali ya mata, ya girgiza duk wani gabban jikinta, ta san dole ya dau hukunci, ta san shirun da ya mata yana neman hukuncin da ya dace da ita, amma Saki? Saki har uku? Ba ta tunanin ta canchanci Saki Uku, ita da ta soshi tsakaninta da Allah, tun bai kai haka ba, ta zauna dashi da dadi ba dadi, ta shanye bakincikin da danginshi suka ta k'unsa mata, wai ita ya saka saboda danshi? yanzu ya zata yi? Ita fa ba ta so ta yarda, don tunanin na barazanar fasa mata kwanyar kai.
Yunk'uri tayi daga inda take durk'ushe a tsakiyar unguwa ta nufa Gidan da niyar shiga, sai dai kash akwai masu tsaron Gidan, suka sa mata fullstop daga bakin gate, tayi magiyar ta yi haukan amma a banza, wani ma daga cikin securities din ya shaida mata in ta sake zuwa zai ya daureta.
Kuka Shafa'atu keyi sosai, kallo daya zakayi mata ka san tana cikin tashin hankali, da ta ga ba sarki sai Allah, sai ta ja kafarta ta nufa Unguwarsu Aminiyarta Er Rabi.
Hankali tashe ta isa Gidan, jikin kawarta ta fada ta fashe da kuka mai ban tausayi, hankalin Er Rabi ya tashi, ta shiga lallashinta da kyar ta samu ta bata labarin duk abunda ya faru.
Kirji Er Rabi ta dafe, Saki uku? Yau an shiga uku, a kan wani dalili zai sakeki? Shi be san tsautsayi ba? Hmm Shafa'atu, wallahi banga laifin kowa ba sai laifinki, tun yaushe nake binki kan ki barar da cikin Maryama? Tun yaushe nake ce miki a batar da Zaid, saboda ni wallahi na san yaron nan shi zaiyi Sillar barin gidan ashe Hassashe na ya tabbata, yau mun shiga uku, sai da Alh Ali ya fara mahaukacin Azziki zai sakeki?"
Kuka Shafa ta fashe dashi tace " nidai ki taimaka min in koma, magiya ta fara yi mata, Er Rabi ta lura kawarta na son zarewa, dawowa kusa da ita tayi, ta tariyota jikinta tana lallashinta tace "kinsan dai a yanzu ba aure tsakaninki da Ali, sai kin sake wani auren".
"Wallahi ina da wanda zai aureni ya sakoni a yau dinnan" Er Rabi tace "dakata Hajia, ina ke ina aure yau? Ko kin manta shari'ah ne? Akwai Idda a kanki, bayan nan ma dai ina so na farko ki kwantar da hankalinki, na biyu kuma ki yarda dani ki bar min komai".
Share hawayenta tayi tace "eh na bar miki komai, na yarda dake".
Washegari Er Rabi ta fita tun kan gari ya waye, Shafa'atu ba ta tashi ta ganta ba, kasa hakuri tayi tayi wanka ta fita zuwa Gidan Alhaji Ali, kamar jiya masu gadi suka ci mata mutunci, suka hanata shiga, wuri ta samu ta rakube a inda marok'a ke zama don jiran fitowan Alhaji Ali duk safiyya, ta san ya kusa fita Office, bayan 1hr sai ga Motocinshi sun fara fitowa, da sauri ta mik'e tsaye ta nufe Motar da take da tabbaci yana ciki don ya tsaya yana sallamar marok'a, yana hangota ya ciro kudadden da be san yawansu ba ya ba wani Yaronshi yace ka raba ma kowa, ya kallo driver yace mu tafi, kafin ta karaso tuni driver yayi gaba, sauri sauri gudu gudu ta bi bayan motar, daga bisani ta tsaida kekenapep tace ya kaita Office din Speaker, tana isa kuwa ta iske karnuka irin police dogs dinnan, securities suka sake mata su bisa umurnin Ogansu, a guje ta bar gurin da kyar ta tsira ta koma Gidan Er Rabi tana haki Rai a bace.
Daidai da dawowan ErRabi, rik'ota tayi ganin tana neman kifewa "Hajia Shafa'atu meya faru? Lafiya?" Tana haki tace "Karnuka Ali ya sa aka sakar min, da kyar na tsere".
Ran Er Rabi bace tace "yanzu wurin shi kikaje Shafa'atu? Gashi ya wulakantaki a banza".
Sai da nace ki bar min komai" ita dai Shafa'atu bata bar kuka da kumbure kumbure ba.
Er Rabi tace "saurareni da kyau, daga gurin mallamina nake, na kai mishi kukanki, amma yace na kaiki, don ya kalli kwayar idanunki ya karanto miki matsalolinki, kinsan shi baa mai katsalandan, shiyasa banje dake tun wuri ba, in ba shi yace azo da mutum ba, ba a mishi jaye-jaye, aikinshi kamar yankan wuka, kuma ba kya fadin damuwarki da ya kalleki ya san damuwarki ta mecece"
Shafa'atu da ta natsu tana sauraronta tace "Er Rabi, kina da tabbacin zai magance min masalata, shi da bai santa ba ta ina zai maganceta?"
Shafa'atu tace "La Ilah, ya kike magana? Wai baki yarda dani bane?".
Hawayenta ta share mata ta kwantar mata da hankali, sai da ta ga hankalinta ya dawo gareta kafin ta fara magana,
"Banda haufi kan Mallam, sai dai in ban kai mai kuka na ba, da naje yake magance minshi"
"Yace inje dake" wuf Shafa'atu tayi tace "to wai jiran me mukeyi ne? Danallah mu tafi"
Er Rabi ta mike, suka fita gabaki daya basu tsaya ko ina ba sai tashar da zai kaisu kauyen Marmara.
Babban Gidane don Gidan kadai ne gini bulo, maigadi bai tsaya musu iso ba don Er Rabi yar Gida ce.
Mallam na zaune a wani parlorn da yaji kayan alatu, rik'e yake da wani zungureriyar chasbaha a hannayennshi biyu.
Daga wani tuntun Er Rabi ta zauna, ganin haka yasa Shafa'atu zama kusa da k'afar ErRabi. Er Rabi tace "Mallam kaga nadawo ko? Mutuniyar ce ba ta da sany shiyasa muka taho yau ba gobe ba".
Mallam da tun da suka shigo yake bin Shafa'atu da wani kallo, cikin rashin sabo da irin kallon da ya ke mata ta gaisheshi, ya amsata da faraarsa.
Ya fara magana ba tare da ya daina jan Chazbaharsaba
"A gurguje Sunanki Shafa'atu, kin auri mai girma Speaker Alh Ali Zaki tun baida komai, kin so shi tsakani da Allah, ba ki taba haihuwa ba, kin shanye bakin cikin dangin Miji, kin zauna da kishiyarki lafiya ba wai don kina sonta ba, sai don Mijinku, ta haihu, son duniya Alhaji Ali ya daura ma dan nan, kika zo kika fara kishi da dan, kika nakasa mishi ido, Alhaji Ali ya miki Saki uku, yanzu kina sonshi, kina so ki dawo gidanki, kina so wannan karon in kin dawo ki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
Da mamaki yanda ya karanto mata labarin Rayuwarta take gyada kai "hakane wallahi, ka taimakeni, da na sake aure zan kashe auren in koma ya aureni, bana so na samu matsala, bana so wani ya bani matsala wurin komawa Gidana, bana son kowa ya sake daga kai ya kalleni a wulakance".
Mallam yace "kije ki gama Idda ki dawo" ba gardama ta tashi tayi gaba Er Rabi kuwa ta tsaya suka danyi magana da Mallam kafin ta fita.
Bayan ta gama Iddah
Er Rabi ta jadadda mata kan Rashin yi ma Mallam Gardama, da kuma bin duk wani abunda yace tayi, ka nan suka koma Gidan Mallam.
"Shafa'atu aikina ba kamar na saura bane, bana aikin Ammaja, ina da kudi, bana karyar aiki, bana aikin da zai warware bayan shekaru dubu, ko mai zai faru aikina nike warwareshi da hannuna, ki gaya min, zaki iya bin sharrudda na?"
Da sauri ta gyada kai, don ita ta matsu ta koma Gidan aurenta, a yan watanni hudu, ji take kamar an rura mata wutan son Alh Ali tace "Mallam na shirya, zanyi duk abunda kace"
"Aikina ba a hadashi da na kowa, ni na fara sa hannuna cikin Alamarinki, ni na bude aikin ki, in kika koma gun wani ya miki aiki daga yanzu, aikin da na riga na sanya hannu, to zaki biya da ranki, mutuwa zakiyi".
Baki na rawa tace "Ni wallahi ban san kowa ba"
Yace "kamar yanda na gaya miki a zuwanki na wanchan karon, in har na karanceki daidai, a yanzu kina so ki koma gidanki, kina so wannan karon in kin komaki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
"Eh haka ne, haka nake so"
A takaice yace "to hakan ba zai faru a yanzu ba".
Gwalalo ido tayi hankalinta tashe yace "na duba sosai, ba wani abun kirki da na hango, ba Alheri, ko kin koma ba zaki tarar da komai ba sai bakinciki da kunci, kyara, hantara da tsangwama, ke babu ma hanyar komawarki a yanzu don ba karamar tsana dangin suka miki ba, kuma akwai kariya sosai a Jikin Alhaji Ali da Iyalenshi, so a yanzu ba zai yiwu ba, shawara, ko kiyi hakuri har sai lokacin da zan dubo daidai, ko kuma shi Alhaji Alin ki hakura da shi baki daya".
Fashewa tayi da kuka tace "Bangane ba, wallahi ba zan iya hakuri da shi ba, zan jira har sai lokacin da ka gano Alheri, ko nan da shekara 50 ne".
Dariya mallam yayi yace "be ma kai shekara50 ba, shekara sha biyar(15) ne ba yawa".
Fargaba, tsoro suka dura a kirjinta a yayinda ta hango iyakar gaskiarshi, cikin rudu take cewa "bangane shekara 15 ba, Mallam donAllah bar wasa muyi maganar da ya kamata".
Dariya yayi yace "Kina ganin kamar wasa nake, kije ki gwada auren Alhaji Ali, ai ba ma zaiyiwu bane, in kina son burin ki ya cika, ki daure ki cika shekaru 15 dinnan zaki ga ribar hakuri, har ki dafa dutse ki sha romonta".
"Mallam wai wani irin Shekaru 15? In na mutu kafin nan fa? In shi ya mutu fa? Kai in akayi K'iyama kafin shekarun su zagayo fa?"
"Ke ki bar wannan tunanin bana so ki hango komai sai nasara, ki kallo nasara har kin sameshi, a lokacin Arziki ninkin ba ninkin, kuma sai yadda kikace, kuma a duk inda kike, in dai shekarun suka cika, sai ya nemoki, ko da kina kasar sin".
Shiru tayi tana wasu tunani, ta waiga ta kalli ErRabi wacce take daga mata kai alamun amincewa, basirarta ta dode, zuciyarta ta bushe, hangen dogon buri take, take zuciyarta ta dinga hasko mata abubuwan jin dadi da ke jiranta nan da shekara Sha biyar.
"Na fahimta Mallam, shekara wata rana kwana ce, kamar gobe ne, Allah ya kaimu".
Mallam ya murmusa "to akwai wasu maganin da zan dinga rubuta miki a, ke da kanki zaki dinga wanke shi"
Ido ta gwalalo, tsoro ya rufeta.
"Kwantar da hankalinki, ni zan aureki, kinga kawai da nagana aiki a kanki, da na sakeki, kawai sai ki aure tsohon mijinki".
Da yake zuciyarta ta dakushe, ba ta da mafadi, ta amince da bukatar Mallam, Mallam ya aureta, ya cigaba da aiki a kanta a cewarshi, sakinta yayi bayan Sati 1.
Abun mamaki wai don auren da sukayi na kwanan 7. Shafaatu ta samu ciki, murna Shafaatu tayi harda kuka, gani take aikin Mallam ya fara ci, bata son Mallam ko kadan, amma inta tuna nan da shekaru sha hudu da rabi zata auri masoyinta na asali sai ta ji dadi.
Ba yanda Mallam beyi kan ta zubda cikinta ba ta ki, son cikinta take sosai, kuma ita da ba ta taba ko da bari ba akan me zata zubar da cikinta, aiko ta na son abunta".
Mallam yace "shi ko ba ruwanshi"
tace "ta yarda".
Yace "Kiyi tafiyarki, ki cigaba da rayuwarki kamar kowa, 18/10/2008 Alhaji Ali zai zo wurinki a duk inda kike,ki rubuta ki ajiye, ki fara irga kwana daga yau".
Da Murna ta bar Gidan Mallam ta koma Gidan Er Rabi, ta hade kayanta da yan kudadden da take dasu ta koma Gidansu da ke Jos.
Uwarta ta shiga tashin hankali da ta gaya mata sakinta a kayi, amma ta kwantar da hankalinta ganin hankalin diyarta a kwnace yake. Zaune suke da dadi ba dadi, lokacin haihuwarta ta yayi ta haifi diya Mace suka sa mata suna Amina suna ce ata Annah.
Bata damu ta gaya ma mallam ba don ya riga da yace ba ruwanshi da diyar, don shi mallam bai san iya adadin yaranshi ba.
Haka Shafa'atu tayi rayuwar Jos da dadi ba dadi,duk da son Ali Zaki beta bacewa ba.
Shafa'atu na da Labarin Gidan Alhaji Zaki kaf dinshi, duk abunda suke ciki Er Rabi na gaya mata.
Tare take da Mahaifiyarta, da diyarta da k'aninta Hudu da ba zai wuce tsaran Zaid ba, ko ya girmeshi ba da yawa bane.
A shekararsu ta 5 ne Mamarta ta fara wani irin ciwo, sosai rashin Lafiyarta ya kwantar da ita a babban Asibitin Jos, bincike ya nuna Hantarta ce ta kumbura, kuma tana buk'arta a mata open surgery.
Hankalin Shafa'atu ya tashi, ta rasa inda zata neman kudi, gashi ba kudin nan, damar duk buga buga ce.
Duk inda zata aron kudi sai ace babu. Ta kira Er Rabi a waya tace ta ara mata dubu dari3, Er Rabi tace "wallahi bata dashi babu" hankalinta ya tashi, ErRabin ce hope dinta, yanzu ya zatayi? Katsina zuciyarta ke kira mata, kawai taje gurin Alhaji Ali.
Ba doguwar Shawara washegari ta shirya Annah, suka bi Motar haya zuwa Garin Katsina, shi kuma Hudu zai zauna wurin Mama kafin su dawo.
Suna isa duk a gajiye, Annah ta fita hayyacinta, ga yunwa ga gajiyar Mota, direct ta nufa Offishinshi duk da Marece yayi.
Wurin Secretary dinshi ta buk'aci ganinshi, Secretary tace "ba ki da appointment, kuma 4 ya wuce, baya ganin visitors, kuma he is about to leave, ki bari sai gobe" magiya ta fara yi mata, Annah ta fara kuka.
"Meke faruwa a nan?" Muryarshi ta doki kunnuwanta, da sauri ta waiga inda yake tsaye, ya fito daga office ga wasu mutane masu bakin suit da bakin Gilashi suna gefenshi.
Idonshi ya sauka kanta, nan da nan fuskarshi ta hade, kafin ta yi magana yace a kausashe "me kikeyi a nan? Bana ce kar ki kara fitowa gaban idona ba? Bance miki bana son sake ganinki ba? Bance miki na tsani ko da kalonki ba? At this instant, bace min daga gani kafin na sa a Wulak'antaki".
Dama tuni take zube gabanshi, kuka take tana girgiza kai "Alhajina, ka taimakeni, Mama na chan kwance bata da lafia"
Bai saurareta ba yayi umurni da a fitar da ita.
A wulakance a ka fitar da ita, tana kuka ta karasa Gidan Er Rabi, ErRabi ta basu Abinci, ta tausheta da cewa nan da shekara 10 zata dawo Gidanshi sai ta fanshi bakincikin da ya kunsamata na shekaru, a haka ta dinga lallabata.
"DonAllah muje ki rakani wurin Mallam, kila zai taimaka min, ga Annah ma, be ma san ya take ba, kuma diyarshi ce"
Er Rabi tayi saurin katseta, "aa Shafa'atu ba haka kukayi ba, sai da yace zai baki magani ki zubar da cikin Annah kikace aa, kikace ya bar miki cikinki, harda kuka, yace kar ki taba zuwa gabanshi da diyrki, kar ki taba ambatonshi a matsayin uban diyarki, kikace kin amince, yanzu kuma kice muje gurinshi? Karki manta yace ya gama aikinshi kanki rana kawai zaki jira, yace duk randa kika zo mishi da maganar diyarki zai kwance komai da ya kulla kinga kinyi jiran banza, Shekara 5 ta tafi a banza, komai ya tashi a banza, ke dai kiyi hakuri yanzu, gobe ki koma Jos a fara ma Mama maganin hausa zaa dace".
Kuka Shafa'atu kawai take, Washegari da Asuba tayi Sakkon komawa garin Jos ranta 6ace, ta na dawowa da kwana daya Mamarta tace ga Garinku nan, ta girgiza da mutuwar Mahaifiyarta ta sha kuka son ranta tana tausayin kanta da na kaninta Hudu, basu da kowa, basu da komai.
Rayuwa ya mata zafi, dole ta rayu kafin Burinta ya cika, dole ta zama karfin Annah da Hudu, dole duk su rayu, mikewa tayi tsaye ta fara Abincin Saidawa kamar yanda sukeyi a da, kasancewar ta iya Girki, kuma akwai Tsafta ya sa take samun Customers. Kuddirinta na nan, ranta chunkushe, Ganinta Ali zaki ne yayi sanadiyar mutuwar Mahaifiyarta, da ya taimaka mata, da amma Uwar ta aiki da ta warke, Ta k'agara Shekaru 10 su cika ta fanshe Bakincikinta.
Bayan Shekara Goma
18/10/2008
Yau take Sallah a gurin Hajiya Shafa'atu, kwalliya ta ci ta sa tsaddaden leshin da Allah kadai ya san inda aka samu kudin dinkawa, harta lalle sai da aka K'unsa mata, yanda ka san Sabuwar Amarya.
Da karfe 1 na rana Annah ta shigo dakinsu, tace "wai ni Mummy ina Baban nawa? Har yanzu bai iso ba?"
Shafa'atu ta fara girgiza kafarta, ita fa a ganinta ko garin yau be idasa wayewa ba zata ga Alinta, gashi har an fara kiraye kirayen Sallah.
Ba ta so ta sa shakku a Aikin Mallam, Shekaru 15 tayi tana jiran Ranar nan, ga ranar tazo, gashi ranan ya mata kama da sauran ranakun da suka shude, ba wani abu special game da ranar yau, ko dai tayi wauta da sakaci da ta yarda da maganganun Mallam? Ko Annah bata amsa ba ta ciro wayarta ta latso Er Rabi, Er Rabi na dauka
Showing 27001 words to 30000 words out of 132816 words
Hello Bibilicious fans, afuwan, komai ya daidaita nagode da adduoinku da fatan alherinku gareni.
#Ilove
#DM
#SonSoFWA
#anatare
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: Babi na Tara (ABUNDA YA FARU)
Labiba na ta girgiza kai tace "donAllah ka gaya min mai ya maidaka haka?".
Dan kallonta yayi lafij yace "are you not listening? Ba ki fahimci duk abunda na fada miki ba yanzu? Isnt it obvious? Matar Uba ta maidani haka, ke ko komai sai an gaya miki kafin ki fahimta?".
Sausauta murya Labiba tayi tace "naji, ina son sanin Meyasa ka fara shaye-shaye? Wacce rana ka fara shan Sigari? Meye dalilinka na shan Sigari?"
Kallonta kawai DanMakaho yayi, mai take so ya sanar da ita baya ga abunda ya gaya mata yanzu? Ya lura ta na da naci sosai, tsaki yayi ya yayi hanyar k'ofa yace;
"Nagaya miki yunwa nakeji, ina da buk'atar cin abinci".
Gunguni tayi tace "da kana jin yunwa da ba ka banka ma cikinka wuta da sassafe ba".
Waigowa yayi yace "me kikace?"
Baki ta zumburo tace "fa banyi magana ba".
Kai ya girgiza sosai yace "kina wasa dani Labiba, zan miki hankali"
Ya sa kai ya fice, da sauri ta mik'e tsaye ta figi jakkarta ta bi bayanshi.
"Tsaya, ya zaka barni a nan?" Be juyo ba yace "dama ni na kawo ki?" "To wai ta ina zan fita?" Bai fasa tafiyar ba yace "ta inda kika shigo".
"Seriously?" Bai amsata ba yayi gaba abunshi, ba ta da zabin da ya wuce ta tsallaka fasassun bulo ta ketara zuwa Gidansu.
**__**_**_**_**_**_**_
Wannan Sakin da Alhaji Ali ya mata, ya girgiza duk wani gabban jikinta, ta san dole ya dau hukunci, ta san shirun da ya mata yana neman hukuncin da ya dace da ita, amma Saki? Saki har uku? Ba ta tunanin ta canchanci Saki Uku, ita da ta soshi tsakaninta da Allah, tun bai kai haka ba, ta zauna dashi da dadi ba dadi, ta shanye bakincikin da danginshi suka ta k'unsa mata, wai ita ya saka saboda danshi? yanzu ya zata yi? Ita fa ba ta so ta yarda, don tunanin na barazanar fasa mata kwanyar kai.
Yunk'uri tayi daga inda take durk'ushe a tsakiyar unguwa ta nufa Gidan da niyar shiga, sai dai kash akwai masu tsaron Gidan, suka sa mata fullstop daga bakin gate, tayi magiyar ta yi haukan amma a banza, wani ma daga cikin securities din ya shaida mata in ta sake zuwa zai ya daureta.
Kuka Shafa'atu keyi sosai, kallo daya zakayi mata ka san tana cikin tashin hankali, da ta ga ba sarki sai Allah, sai ta ja kafarta ta nufa Unguwarsu Aminiyarta Er Rabi.
Hankali tashe ta isa Gidan, jikin kawarta ta fada ta fashe da kuka mai ban tausayi, hankalin Er Rabi ya tashi, ta shiga lallashinta da kyar ta samu ta bata labarin duk abunda ya faru.
Kirji Er Rabi ta dafe, Saki uku? Yau an shiga uku, a kan wani dalili zai sakeki? Shi be san tsautsayi ba? Hmm Shafa'atu, wallahi banga laifin kowa ba sai laifinki, tun yaushe nake binki kan ki barar da cikin Maryama? Tun yaushe nake ce miki a batar da Zaid, saboda ni wallahi na san yaron nan shi zaiyi Sillar barin gidan ashe Hassashe na ya tabbata, yau mun shiga uku, sai da Alh Ali ya fara mahaukacin Azziki zai sakeki?"
Kuka Shafa ta fashe dashi tace " nidai ki taimaka min in koma, magiya ta fara yi mata, Er Rabi ta lura kawarta na son zarewa, dawowa kusa da ita tayi, ta tariyota jikinta tana lallashinta tace "kinsan dai a yanzu ba aure tsakaninki da Ali, sai kin sake wani auren".
"Wallahi ina da wanda zai aureni ya sakoni a yau dinnan" Er Rabi tace "dakata Hajia, ina ke ina aure yau? Ko kin manta shari'ah ne? Akwai Idda a kanki, bayan nan ma dai ina so na farko ki kwantar da hankalinki, na biyu kuma ki yarda dani ki bar min komai".
Share hawayenta tayi tace "eh na bar miki komai, na yarda dake".
Washegari Er Rabi ta fita tun kan gari ya waye, Shafa'atu ba ta tashi ta ganta ba, kasa hakuri tayi tayi wanka ta fita zuwa Gidan Alhaji Ali, kamar jiya masu gadi suka ci mata mutunci, suka hanata shiga, wuri ta samu ta rakube a inda marok'a ke zama don jiran fitowan Alhaji Ali duk safiyya, ta san ya kusa fita Office, bayan 1hr sai ga Motocinshi sun fara fitowa, da sauri ta mik'e tsaye ta nufe Motar da take da tabbaci yana ciki don ya tsaya yana sallamar marok'a, yana hangota ya ciro kudadden da be san yawansu ba ya ba wani Yaronshi yace ka raba ma kowa, ya kallo driver yace mu tafi, kafin ta karaso tuni driver yayi gaba, sauri sauri gudu gudu ta bi bayan motar, daga bisani ta tsaida kekenapep tace ya kaita Office din Speaker, tana isa kuwa ta iske karnuka irin police dogs dinnan, securities suka sake mata su bisa umurnin Ogansu, a guje ta bar gurin da kyar ta tsira ta koma Gidan Er Rabi tana haki Rai a bace.
Daidai da dawowan ErRabi, rik'ota tayi ganin tana neman kifewa "Hajia Shafa'atu meya faru? Lafiya?" Tana haki tace "Karnuka Ali ya sa aka sakar min, da kyar na tsere".
Ran Er Rabi bace tace "yanzu wurin shi kikaje Shafa'atu? Gashi ya wulakantaki a banza".
Sai da nace ki bar min komai" ita dai Shafa'atu bata bar kuka da kumbure kumbure ba.
Er Rabi tace "saurareni da kyau, daga gurin mallamina nake, na kai mishi kukanki, amma yace na kaiki, don ya kalli kwayar idanunki ya karanto miki matsalolinki, kinsan shi baa mai katsalandan, shiyasa banje dake tun wuri ba, in ba shi yace azo da mutum ba, ba a mishi jaye-jaye, aikinshi kamar yankan wuka, kuma ba kya fadin damuwarki da ya kalleki ya san damuwarki ta mecece"
Shafa'atu da ta natsu tana sauraronta tace "Er Rabi, kina da tabbacin zai magance min masalata, shi da bai santa ba ta ina zai maganceta?"
Shafa'atu tace "La Ilah, ya kike magana? Wai baki yarda dani bane?".
Hawayenta ta share mata ta kwantar mata da hankali, sai da ta ga hankalinta ya dawo gareta kafin ta fara magana,
"Banda haufi kan Mallam, sai dai in ban kai mai kuka na ba, da naje yake magance minshi"
"Yace inje dake" wuf Shafa'atu tayi tace "to wai jiran me mukeyi ne? Danallah mu tafi"
Er Rabi ta mike, suka fita gabaki daya basu tsaya ko ina ba sai tashar da zai kaisu kauyen Marmara.
Babban Gidane don Gidan kadai ne gini bulo, maigadi bai tsaya musu iso ba don Er Rabi yar Gida ce.
Mallam na zaune a wani parlorn da yaji kayan alatu, rik'e yake da wani zungureriyar chasbaha a hannayennshi biyu.
Daga wani tuntun Er Rabi ta zauna, ganin haka yasa Shafa'atu zama kusa da k'afar ErRabi. Er Rabi tace "Mallam kaga nadawo ko? Mutuniyar ce ba ta da sany shiyasa muka taho yau ba gobe ba".
Mallam da tun da suka shigo yake bin Shafa'atu da wani kallo, cikin rashin sabo da irin kallon da ya ke mata ta gaisheshi, ya amsata da faraarsa.
Ya fara magana ba tare da ya daina jan Chazbaharsaba
"A gurguje Sunanki Shafa'atu, kin auri mai girma Speaker Alh Ali Zaki tun baida komai, kin so shi tsakani da Allah, ba ki taba haihuwa ba, kin shanye bakin cikin dangin Miji, kin zauna da kishiyarki lafiya ba wai don kina sonta ba, sai don Mijinku, ta haihu, son duniya Alhaji Ali ya daura ma dan nan, kika zo kika fara kishi da dan, kika nakasa mishi ido, Alhaji Ali ya miki Saki uku, yanzu kina sonshi, kina so ki dawo gidanki, kina so wannan karon in kin dawo ki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
Da mamaki yanda ya karanto mata labarin Rayuwarta take gyada kai "hakane wallahi, ka taimakeni, da na sake aure zan kashe auren in koma ya aureni, bana so na samu matsala, bana so wani ya bani matsala wurin komawa Gidana, bana son kowa ya sake daga kai ya kalleni a wulakance".
Mallam yace "kije ki gama Idda ki dawo" ba gardama ta tashi tayi gaba Er Rabi kuwa ta tsaya suka danyi magana da Mallam kafin ta fita.
Bayan ta gama Iddah
Er Rabi ta jadadda mata kan Rashin yi ma Mallam Gardama, da kuma bin duk wani abunda yace tayi, ka nan suka koma Gidan Mallam.
"Shafa'atu aikina ba kamar na saura bane, bana aikin Ammaja, ina da kudi, bana karyar aiki, bana aikin da zai warware bayan shekaru dubu, ko mai zai faru aikina nike warwareshi da hannuna, ki gaya min, zaki iya bin sharrudda na?"
Da sauri ta gyada kai, don ita ta matsu ta koma Gidan aurenta, a yan watanni hudu, ji take kamar an rura mata wutan son Alh Ali tace "Mallam na shirya, zanyi duk abunda kace"
"Aikina ba a hadashi da na kowa, ni na fara sa hannuna cikin Alamarinki, ni na bude aikin ki, in kika koma gun wani ya miki aiki daga yanzu, aikin da na riga na sanya hannu, to zaki biya da ranki, mutuwa zakiyi".
Baki na rawa tace "Ni wallahi ban san kowa ba"
Yace "kamar yanda na gaya miki a zuwanki na wanchan karon, in har na karanceki daidai, a yanzu kina so ki koma gidanki, kina so wannan karon in kin komaki mallake komai,ki juya komai kuma kar wanda ya kalleki ya ce miki don me, ko ba haka ba?".
"Eh haka ne, haka nake so"
A takaice yace "to hakan ba zai faru a yanzu ba".
Gwalalo ido tayi hankalinta tashe yace "na duba sosai, ba wani abun kirki da na hango, ba Alheri, ko kin koma ba zaki tarar da komai ba sai bakinciki da kunci, kyara, hantara da tsangwama, ke babu ma hanyar komawarki a yanzu don ba karamar tsana dangin suka miki ba, kuma akwai kariya sosai a Jikin Alhaji Ali da Iyalenshi, so a yanzu ba zai yiwu ba, shawara, ko kiyi hakuri har sai lokacin da zan dubo daidai, ko kuma shi Alhaji Alin ki hakura da shi baki daya".
Fashewa tayi da kuka tace "Bangane ba, wallahi ba zan iya hakuri da shi ba, zan jira har sai lokacin da ka gano Alheri, ko nan da shekara 50 ne".
Dariya mallam yayi yace "be ma kai shekara50 ba, shekara sha biyar(15) ne ba yawa".
Fargaba, tsoro suka dura a kirjinta a yayinda ta hango iyakar gaskiarshi, cikin rudu take cewa "bangane shekara 15 ba, Mallam donAllah bar wasa muyi maganar da ya kamata".
Dariya yayi yace "Kina ganin kamar wasa nake, kije ki gwada auren Alhaji Ali, ai ba ma zaiyiwu bane, in kina son burin ki ya cika, ki daure ki cika shekaru 15 dinnan zaki ga ribar hakuri, har ki dafa dutse ki sha romonta".
"Mallam wai wani irin Shekaru 15? In na mutu kafin nan fa? In shi ya mutu fa? Kai in akayi K'iyama kafin shekarun su zagayo fa?"
"Ke ki bar wannan tunanin bana so ki hango komai sai nasara, ki kallo nasara har kin sameshi, a lokacin Arziki ninkin ba ninkin, kuma sai yadda kikace, kuma a duk inda kike, in dai shekarun suka cika, sai ya nemoki, ko da kina kasar sin".
Shiru tayi tana wasu tunani, ta waiga ta kalli ErRabi wacce take daga mata kai alamun amincewa, basirarta ta dode, zuciyarta ta bushe, hangen dogon buri take, take zuciyarta ta dinga hasko mata abubuwan jin dadi da ke jiranta nan da shekara Sha biyar.
"Na fahimta Mallam, shekara wata rana kwana ce, kamar gobe ne, Allah ya kaimu".
Mallam ya murmusa "to akwai wasu maganin da zan dinga rubuta miki a, ke da kanki zaki dinga wanke shi"
Ido ta gwalalo, tsoro ya rufeta.
"Kwantar da hankalinki, ni zan aureki, kinga kawai da nagana aiki a kanki, da na sakeki, kawai sai ki aure tsohon mijinki".
Da yake zuciyarta ta dakushe, ba ta da mafadi, ta amince da bukatar Mallam, Mallam ya aureta, ya cigaba da aiki a kanta a cewarshi, sakinta yayi bayan Sati 1.
Abun mamaki wai don auren da sukayi na kwanan 7. Shafaatu ta samu ciki, murna Shafaatu tayi harda kuka, gani take aikin Mallam ya fara ci, bata son Mallam ko kadan, amma inta tuna nan da shekaru sha hudu da rabi zata auri masoyinta na asali sai ta ji dadi.
Ba yanda Mallam beyi kan ta zubda cikinta ba ta ki, son cikinta take sosai, kuma ita da ba ta taba ko da bari ba akan me zata zubar da cikinta, aiko ta na son abunta".
Mallam yace "shi ko ba ruwanshi"
tace "ta yarda".
Yace "Kiyi tafiyarki, ki cigaba da rayuwarki kamar kowa, 18/10/2008 Alhaji Ali zai zo wurinki a duk inda kike,ki rubuta ki ajiye, ki fara irga kwana daga yau".
Da Murna ta bar Gidan Mallam ta koma Gidan Er Rabi, ta hade kayanta da yan kudadden da take dasu ta koma Gidansu da ke Jos.
Uwarta ta shiga tashin hankali da ta gaya mata sakinta a kayi, amma ta kwantar da hankalinta ganin hankalin diyarta a kwnace yake. Zaune suke da dadi ba dadi, lokacin haihuwarta ta yayi ta haifi diya Mace suka sa mata suna Amina suna ce ata Annah.
Bata damu ta gaya ma mallam ba don ya riga da yace ba ruwanshi da diyar, don shi mallam bai san iya adadin yaranshi ba.
Haka Shafa'atu tayi rayuwar Jos da dadi ba dadi,duk da son Ali Zaki beta bacewa ba.
Shafa'atu na da Labarin Gidan Alhaji Zaki kaf dinshi, duk abunda suke ciki Er Rabi na gaya mata.
Tare take da Mahaifiyarta, da diyarta da k'aninta Hudu da ba zai wuce tsaran Zaid ba, ko ya girmeshi ba da yawa bane.
A shekararsu ta 5 ne Mamarta ta fara wani irin ciwo, sosai rashin Lafiyarta ya kwantar da ita a babban Asibitin Jos, bincike ya nuna Hantarta ce ta kumbura, kuma tana buk'arta a mata open surgery.
Hankalin Shafa'atu ya tashi, ta rasa inda zata neman kudi, gashi ba kudin nan, damar duk buga buga ce.
Duk inda zata aron kudi sai ace babu. Ta kira Er Rabi a waya tace ta ara mata dubu dari3, Er Rabi tace "wallahi bata dashi babu" hankalinta ya tashi, ErRabin ce hope dinta, yanzu ya zatayi? Katsina zuciyarta ke kira mata, kawai taje gurin Alhaji Ali.
Ba doguwar Shawara washegari ta shirya Annah, suka bi Motar haya zuwa Garin Katsina, shi kuma Hudu zai zauna wurin Mama kafin su dawo.
Suna isa duk a gajiye, Annah ta fita hayyacinta, ga yunwa ga gajiyar Mota, direct ta nufa Offishinshi duk da Marece yayi.
Wurin Secretary dinshi ta buk'aci ganinshi, Secretary tace "ba ki da appointment, kuma 4 ya wuce, baya ganin visitors, kuma he is about to leave, ki bari sai gobe" magiya ta fara yi mata, Annah ta fara kuka.
"Meke faruwa a nan?" Muryarshi ta doki kunnuwanta, da sauri ta waiga inda yake tsaye, ya fito daga office ga wasu mutane masu bakin suit da bakin Gilashi suna gefenshi.
Idonshi ya sauka kanta, nan da nan fuskarshi ta hade, kafin ta yi magana yace a kausashe "me kikeyi a nan? Bana ce kar ki kara fitowa gaban idona ba? Bance miki bana son sake ganinki ba? Bance miki na tsani ko da kalonki ba? At this instant, bace min daga gani kafin na sa a Wulak'antaki".
Dama tuni take zube gabanshi, kuka take tana girgiza kai "Alhajina, ka taimakeni, Mama na chan kwance bata da lafia"
Bai saurareta ba yayi umurni da a fitar da ita.
A wulakance a ka fitar da ita, tana kuka ta karasa Gidan Er Rabi, ErRabi ta basu Abinci, ta tausheta da cewa nan da shekara 10 zata dawo Gidanshi sai ta fanshi bakincikin da ya kunsamata na shekaru, a haka ta dinga lallabata.
"DonAllah muje ki rakani wurin Mallam, kila zai taimaka min, ga Annah ma, be ma san ya take ba, kuma diyarshi ce"
Er Rabi tayi saurin katseta, "aa Shafa'atu ba haka kukayi ba, sai da yace zai baki magani ki zubar da cikin Annah kikace aa, kikace ya bar miki cikinki, harda kuka, yace kar ki taba zuwa gabanshi da diyrki, kar ki taba ambatonshi a matsayin uban diyarki, kikace kin amince, yanzu kuma kice muje gurinshi? Karki manta yace ya gama aikinshi kanki rana kawai zaki jira, yace duk randa kika zo mishi da maganar diyarki zai kwance komai da ya kulla kinga kinyi jiran banza, Shekara 5 ta tafi a banza, komai ya tashi a banza, ke dai kiyi hakuri yanzu, gobe ki koma Jos a fara ma Mama maganin hausa zaa dace".
Kuka Shafa'atu kawai take, Washegari da Asuba tayi Sakkon komawa garin Jos ranta 6ace, ta na dawowa da kwana daya Mamarta tace ga Garinku nan, ta girgiza da mutuwar Mahaifiyarta ta sha kuka son ranta tana tausayin kanta da na kaninta Hudu, basu da kowa, basu da komai.
Rayuwa ya mata zafi, dole ta rayu kafin Burinta ya cika, dole ta zama karfin Annah da Hudu, dole duk su rayu, mikewa tayi tsaye ta fara Abincin Saidawa kamar yanda sukeyi a da, kasancewar ta iya Girki, kuma akwai Tsafta ya sa take samun Customers. Kuddirinta na nan, ranta chunkushe, Ganinta Ali zaki ne yayi sanadiyar mutuwar Mahaifiyarta, da ya taimaka mata, da amma Uwar ta aiki da ta warke, Ta k'agara Shekaru 10 su cika ta fanshe Bakincikinta.
Bayan Shekara Goma
18/10/2008
Yau take Sallah a gurin Hajiya Shafa'atu, kwalliya ta ci ta sa tsaddaden leshin da Allah kadai ya san inda aka samu kudin dinkawa, harta lalle sai da aka K'unsa mata, yanda ka san Sabuwar Amarya.
Da karfe 1 na rana Annah ta shigo dakinsu, tace "wai ni Mummy ina Baban nawa? Har yanzu bai iso ba?"
Shafa'atu ta fara girgiza kafarta, ita fa a ganinta ko garin yau be idasa wayewa ba zata ga Alinta, gashi har an fara kiraye kirayen Sallah.
Ba ta so ta sa shakku a Aikin Mallam, Shekaru 15 tayi tana jiran Ranar nan, ga ranar tazo, gashi ranan ya mata kama da sauran ranakun da suka shude, ba wani abu special game da ranar yau, ko dai tayi wauta da sakaci da ta yarda da maganganun Mallam? Ko Annah bata amsa ba ta ciro wayarta ta latso Er Rabi, Er Rabi na dauka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10 Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45