don Amaka ko taraiya da masu salla Bata son nayi bare Kuma addinin su ya burgeni ai idan akwai abinda yafi kisa to sai Amaka tayi min shi Amma sai nayi maza na cewa nafisat Babu matsala

Hikimar da nayi itace hearphon nake sakawa a kunne na in saurari Kira ata yadda nake so babu Wanda yasan me nakeji

Abin mamakin da na kula dashi Ni da kaina shine yawan mafarkai da nakeyi Wai gani Ina kallon mutane suna salla wani lokacin ma Zan ganni a cikin sahun salla anayi tare Dani Kuma Wai wani gari ne da ba Legos ba don mafi yawan mutanen da muke sallar tare dasu farare ne tas masu dogon gashi Matan su Sanya da hijabi da Nikabi mazan kuwa sanye da fararen doguwar Riga sun Kuma yafa wani farin mayafi ko ja ko Baki kowa dai da kalar dake kanshi
Idan na farka sai inji Ina begen wannan wuri da na ganni in Kuma ji muradin inyi salla amma Kuma Ina tsoron Amaka ta ganni Dole nayi shiru

Kwana biyu Ina sauraren karatun Nan Ran Nan sai tsautsayi ya samu waya ta ta lalace gashi Kuma muna cikin strike wato yajin aiki bare fauziyya ta sake tura min karatun Alkur ani Dole na wuce kasuwa na siyo CD masu yawa na kawo mota na zube idan fita ta Kama Ni na saurara idan kuwa babu kowa a gidan sai na dawo mota na kunna na saurara

Tsautsayi Wai in ya wuni baya kwana Ranar Nan Yaya na Sony ya dawo gida babu kowa ya iskeni na kure volume cikin Kira a ta malamin da har na hardace sunan shi wato sudais na kasa kunnuwa Ina saurare har ban San lokacin da Sony ya shigo ba sai da Naga inuwar mutum akaina na farga dashi a tsaye ya zubo min idanu Yana Huci tamkar zai hadiye mu Ni da motar tawa inda Kuma na San kashina ya bushe don gashi can ma ya kwarmatawa Amaka da Maazi Nkem kafin Nan ma nasan shima ba kyale Ni zaiyi ba sai naji a jikina............











Labarin GARWASHI na kudine ga duk me bukatar Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669




Kar ku Bari ayi Babu ku don labarin GARWASHI daban yake da sauran






Gidan iko shine sunan ke cewa saduwar ALHERIπŸ’ƒπŸΏ
πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€





πŸ’πŸ’πŸ’ GARWASHIπŸ’πŸ’πŸ’
Page
29//30
Hadiza Bara'u Gidan iko





Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne


Sadaukarwa ga haj Lubabatu Ali Mai chanji marubuciyar Amaryar zamani akan Rashin mahaifin ta Alh Ali Mai chanji marnar gangare Allah yayi mishi Rahama yasa kwanciyar shi hutawa tare da namu iyayen duka dama dukkan musulmin duniya


Fatan ALHERI ga mahaifiyata haj Rabi atu Abubakar magaji Yar Adua Allah ya Kara nisan kwana Mai Albarka


Kayatar wa gareku masoyan littafin GARWASHI hakika kun cancanci yabawa Gidan iko na godiya Allah ya Kara daukaka


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


...........Da sauri na Danna stop na kashe Gaba na na balli balli ganin mazuran da Sony ke min
Kafin ma na fito daga motar sai ji nayi ya shakoni ya finciko daga motar Yana kwada min wani Mari da faskeken hannun shi me kama da faranti

"Wato dama abinda Amaka ke Fadi akan ki gaskiya ne har kin Soma kawo Mana su cikin gida?
Ganin da gaske Yake zai jibge Ni ya barni da ciwon jiki don bashi da kirki wurin duka shiyasa ma Amaka ke bashi go ahead din ya jibgeni in nayi laifi akasin Emmanuel Wanda baya da zafi akan komai kuma ko laifi nayi akace ya jibge Ni afuwa ma shi Yake nema min akasin wannan marar kirkin Sony don Haka nayi nufin kwacewa in gudu Amma sai na Gane Bai Rike Ni don ya saki ba ya Rike Ni ne don ya Nadi banza don Haka nasoma kicin kicin kwacewa shi Kuma ya Soma kwada min Marika Yana masifa inda nayi RAM da hannun shi na Galla mishi uban cizo Wanda ya tilas ta shi sakina na kuwa auna aguje na fada daki na maido sakata Ina kuka

Inajin shi Yana zuba Ruwan tijara Wai su zamu kunyata duk kokarin su Amaka da Maazi Nkem da suke Rike da addinin mu sau da kafa sai nice shegiyar da Zan nuna musu addinin nasu ba na gaskiya bane? To yau sai ya karya min kafa guda

Inajin shi nayi shiru don nasan sai su Amaka sunfi shi shafawa akan Lamarin Ni kuwa gani da wata irin zuciya wadda duk abinda take so to son shi kawai takeyi . In nace so to Ina nufin so Haka Kuma duk abinda take ki kinshi take da gaske in nace ki to ina nufin ki shiyasa naji Arai na su daiyi su Gama Amma babu Mai canja min Ra ayi na ai wuya Bata kisa sai kwana ya Kare

Sony Yana zaune falo Yana fada madam Amaka da Maazi Nkem suka shigo suka same shi Yana tijara maazi Nkem ya tambaye shi abinda Yake wa fada ya Kuma kwashe abinda ya sameni inaji
Amaka ta daki kirji tana fadin Kai me kake cewa my son? Ya sake maimaita mata abinda ya ji ya Kuma gani sai kawai Amaka ta kwasa aguje ta Soma dukan kyauren dakin tana fadin na bude ko ta karya kyauren ta shigo wato banji maganar da ta fada min ba ta Kar na sake nayi kawance da hausawa shine ma don na Raina ta na shigo mata gida da Yan wake waken masu salla na kunna Mata ? Wato na Raina ta ko? To na fito Naga yadda zatayi Dani

Da dai ta gane ba Zan bude ba sai ta juyo Kan Sony ta Rufe shi da duka tamkar shine yayi Mata laifin Wai don me ya barni Bai yi min laga laga ba? Ya nuna Mata cizon da na Galla mishi Wanda yake digar jini
Shi kuwa Maazi Nkem ya gama mutuwa daga zaune ba Kuma komai yake takaici ba sai don in igwai yaji halin da nake ciki Dole ne su fasa Aure na su Kuma sun kwashi Rayukan su sun Dora Akan Aure na gidan igwai

Duk Ina Jin su nayi bakam don nasan bude dakin daidai Yake da tarbar damusar dake Jin yunwa Amma Kuma ga mamaki na sai naji ana sako makulli za a bude sai Kuma na tuna Ashe fa akwai safaya na makullan don Haka sai nayi maza na fada ban daki na Rufe inda Nan ma ban tsira ba Amaka ta cakumo Ni ta fito Dani sai Huci takeyi inda Kuma na Gane Kashi na ya gama bushewa

Shake Ni Amaka tayi da duka karfin ta tana fadin
"Gara dai na kashe ki da kija min abin kunya ace yata ta koma salla Ni kuwa wace Riba naci ? Saboda kin Raina Ni na hanaki gaisa wa da su shine kike shigo min gida da Yan wake waken su kina kunnawa to fada min addinin da Kika zaba? Fada min nace ! Ta fada da Amon murya

Ni Kuma naji Shaka sosai don na yarda na Amince Amaka kasheni din zatayi don bata shakeni don na Rayu ba A a sai dai don ta Mikani lahira Wai ko zata huta da Bakin cikin da nake Shirin jawo Mata
Maazi Nkem ne ya dakawa Amaka tsawa Yana fadin
"Zaki kashe min yarinya ne ko Yaya? Da sauri Amaka ta sakeni inda Emmanuel ya kamo Ni ya taso Ni Yana min sannu
Maazi Nkem ya Rufe Amaka da masifa Akan kokarin kisan da take Shirin yi

Maazi Nkem ya kamo hannu na ya wuce Dani dakin shi Yana maido kyauren dakin ya Rufe kafin ya fuskance Ni

"Gaya min abinda kike nufi shin Zaki bar addinin mu ne na iyaye da kakanni Koko Yaya? Sanin da nayi mishi shima ba son hausawa da musulunci Yake ba sai na kadaa kaina Alamar A a karatun ne dai yake burgeni sai kawai naji shima Maazi ya Rufe Ni da duka Amma na makale ajikin shi Ina fadin kuskure ne ba Zan sake ba kafin ya saurara min Yana Huci

A Ranar Hana Ni abinci sukayi Kuma sukace idan suka sake ganina da hausa man ko waye to Zan fadawa Yan garin mu

Kasset din CD CD dina kuwa duka Amaka ta kwaso su ta saka guduma ta dandake su Redion cikin motar ma sai da ta saka Sony ya cire ta Wai taga gidan uban da Zan Kuma sauraran karatun

Allah cikin ikon shi aka janye strike muka koma makaranta na samu su fauziyya da sumayya na cewa fauziyya ta tura min karatun Nan ta kuwa tura min masu yawa naci gaba da Jin abuna ta cikin hearphon inda Kuma naci gaba da mafarkai Akan wannan kayataccen wurin muna salla wani lokacin ma har littafi nake ganina na bude Ina karatu inda Kuma wata da mukeyin sallar a tare tace na Daina saka kayan da nake sakawa Allah baya son irin Haka in Rika saka irin nasu wato doguwar Riga in Kuma Rika Rufe jikina don Yana da matukar Daraja in son samu ne ma in Rika Rufe fuska ta Nikabi
Abinda ya bani mamaki bayan na farka daga wannan mafarki shine matar da taba Ni wannan shawarar ba fa da hausa tayi maganar ba ba Kuma da yaren mu na Igbo ba da wani harshe Mai matukar Dadi Kuma maganar sai ya zamo tamkar irin karatun da nake saurara kalar maganar Tata Amma Kuma Wai na fahimci abinda take nufi sai kuma na yanke shawarar siyo kayan Nan da matar Nan ta shawarce Ni Amma Kuma sai zuciya ta tambaye Ni to ta Ina Zan Soma saka kayan Nan? Ba dai Nan gidan da sony da Amaka suke ba? Ashe kuwa da sauran kallo

Ana Haka NE auren Sony ya taso muka SHIGA sabgar bikin shi da Amaryar shi sisiliya wadda ta Jima tana dakon son shi

Na SHIGA kasuwa don na siyowa Amaka Ashoke Wanda zata Rabawa kawayen ta tunda tuni dama aka tanadi less din Ashoke ne babu don Haka na nufi kasuwa cikin mota ta inda tun kafin na Kai na Soma Jin kaina Yana juyawa Alamar dai ciwona zai tashi kenan don gaskiya tunda na Soma sauraren karatun Alkur ani ya Dade Bai tashi ba don Haka a yau sai naji Alamar zai tashi kamar na koma gida na fadawa Amaka ba Zan iya zuwa ba Amma Kuma sai Naga ai na kusa cimma kasuwar kawai na karasa in yaso in na suyo Mata Ashoken in baro motar na hawo ta haya don na tabbatar ba Zan iya tuko ta na nadawo ba in yaso ko Emmanuel ne yazo ya daukar min

Haka kuwa na karasa kasuwar cikin shigar kana nanun Kaya da dogon takalmi high hill sai dogon gashi na da ya Sha gyara sai kyalli yake har ya sauko Kan kafada ta
Na fito daga motar Ina karajin kaina Yana juyawa . Abinda kawai na sani na Kuma Rike shine na San lokacin da na maida kyauren motar na Rufe daga Haka ban Kuma sanin abinda ya faru kaina ba anan aka makenk na Fadi kasa a tsakiyar kasuwa. Kuma wannan lamarin shine mabudin bude kofar kaddarar da ta hado Ni da mahaifin ku Umar faruk har zuwa lokacin da kaddara tayi Aikin ta ta kaddaro kaddarar da faifan kaddarar ya bude har zuwa inda ake a yau a Kuma yanzu.................












Labarin GARWASHI na kudine ga duk me son cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669









Labarin GARWASHI daban yake da sauran Kar ku Bari ayi Babu ku







Sunana Hadiza Bara'u Gidan iko ke cewa saduwar ALHERIπŸ’ƒπŸΏπŸ₯°

πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€





πŸ’πŸ’πŸ’ GARWASHIπŸ’πŸ’πŸ’
Page
31//32
Hadiza Bara'u Gidan iko






Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne



Sadaukarwa ga Ahalin gidan ma aiki da duk masu kaunar shi da gaskiya suka Kuma bisu da kyautatawa


Tukwici ne ga Hadiza ta maman Aliyu da hafsat da Zainab sani maman jinio da Zahra

Fatan ALHERI ga Maryam Bara'u Mero Allah ya gyara min ke

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


.. .......Ina kwance shame shame a tsakiyar kasuwa inda aljanu na suka buge Ni na Kuma Fadi babu Alamar motsi ko numfashi Amma abin mamaki babu Wanda yabi ta kaina bare ya kawo min dauki koda ta mayar Dani inuwa ne Amma kowa sai ya wuce Ni abin shi Amma Kuma ga faruk abin ba Haka Yake ba don Akan idon shi hakan ta faru ya Kuma jira yaga Ni ko wani daga cikin yarena ko zai tallafa min Amma kowa sai dai ya kalleni ya wuce don Haka ya karaso a kaina ya Kuma fahimci matsalar tawa ta bugun iska ce don Haka sai ya Soma tofe Ni da ADDU OI cikin ikon Mai sama kuwa sai naji tamkar ana zuba min Ruwan sanyi Wanda ya farkar Dani daga wannan wahalar. Na bude idona Ina kallon shi inda naji Yana karanto wani karatu Wanda na taba Jin irin shi a Bakin Mai karatun Nan wato sudais. Ga mamaki na Sai naji tamkar ana zare min wani Abu marar Dadi ajikina ana kuma mayar min da wani sasaanyan Abu Mai sanyi har zuciya ta

"Sannu yayi min cikin sanyin murya na amsa da yauwa Ina kallon shi da irin kulawar da ya bani alhalin shi din ba yarena da addinin na Daya dashi ba Akasin su Wanda na fito a yare da addinin na dasu din Basu kula ba sai Wanda Amaka Bata son nayi mu Amala dasu to Ni kuwa saboda Allah ya za ayi na mance da hausawa ko na Daina kulasu alhalin su din suna min karamci tamkar dai a cikin su nake?

Ya dauko min key din mota ta da na watsar a can gefe ga Kuma Yar jakar post dina da kudina suke ciki itama na watsar sai shine ya tattaro min su ya bani Yana fadin Zan iya tuka motar ? Na ce mishi ba Zan iya ba ya Kuma tambaya ta me Zan siya? Na fada mishi na Kuma nuna mishi shagon da Zan SHIGA idan na koma gida Zan turo Yaya na ya daukar min motar. Ya Miko min key dina da jakata na karba Ina mishi godiya da irin taimakon da yayi min yace babu komai Wai yiwa Kaine

Na SHIGA shagon da Zan siyi Ashoken Ashe Wai shine Mai shagon na siya na biyashi inda yayi min sauki ya Kuma fada min gaskiya Akan Wanda na Fara zaba cewa quality din su ba na sosai ba inda ya nuna min Mai kyau na Kuma siya muka Rabu Ina Mai farin cikin haduwa ta da shi da Kuma irin taimakon da ya bani ba tare da ya duba koni wacece ba ya taimake Ni babu kyama babu duba addini

R
Tun daga wannan Rana sai nayi sabo da Umar faruk sabo kuwa Mai yawa har ta Kai duk abinda Zan siya to wurin shi Zan siye shi kuma na lura Yana da sani sosai ta fuskar addini sai na Kara kusantar shi don na Soma fada mishi abinda nakeji Akan addinin su shi Kuma Yana fada min ita Rabauta in Allah ya Rabautar da bawa ko a ki ko aso sai yayi .Kuma a yadda ya fahimci lamarina mahaifa na basa so Kuma su iyaye biyayya ake musu a duk abinda sukayi umarni . Haka yayi ta bani shawarwari Akan nayiwa iyayena biyayya Bai taba fada min na bijire ba sai naji ya Kara burgeni lamarin shi Kuma ya tsaya min Arai na kasa mantawa dashi

Musayar lambar waya da mukayi dashi wani lokacin nakanji kamar na kirashi Amma Kuma sai naji Yana min kwarjini tsoro Kuma ya kamani ince to in na kirashi in ce mishi me?
Duk yadda naso na yakice shi na kasa Domin kuwa sai mafarkin shi nakeyi Wai muna salla a tare dashi a kayataccen wurin Nan
Ban Ankara ba naji zuciya ta taja Ni na afka a soyayyar Umar faruk Wanda na kwana biyu ban je shagon shi ba don Ina tsoron yace baya Sona tunda Ni din ba jinsin sa bane kuma ba yaren shi bane me yuwa ma yafi Amaka tsanar mu Amma Kuma nasan daga gareshi dai ba Zan samu hakan ba sai dai ko ta bangaren iyayen shi don na tabbata yadda Amaka Bata Sona da hausawa Haka shima Umar din Koda shi ya Soni to iyayen shi ba zasu Soni ba kasancewar Ni din ba yaren shi bace tuna hakan da nayi sai ya jefa Ni a cikin Rudani

Ban boyewa kawayena ba na makaranta sai da na fada musu abinda Yake damuna Akan Umar faruk inda sumayya tayi ta min dariya tann fadin
"Kai Justina kin SHIGA hannu gaskiya Amma Kuma lamarin naku da mamaki don yazo ne akarkace don in har naki iyayen sun yarda da Auren musulmi to shi nashi ba zasu yarda ba Amma kiyi ta ADDU A in da ALHERI Allah ya tabbatar ya Kuma kawo hanya Mai sauki ta tabbatuwar lamarin
Ita kuwa nafisat Rabi u cewa tayi da ace dai na musulunta ne abin zaizo da sauki Amma Kuma Yaya nake ganin iyaye na zasu karbi musulunci na?

Sai Kuma na hango Ranar da za ace wa Amaka gani na musulunta bana ko shakka bindigar Maazi Nkem zata dauko ta harbeni don ita da kanta take fadin zata kasheni ne in dai nace Zan biyewa hausawa bare Kuma ace na SHIGA musuluncin da ta gama tsana a Duniya. Ban boyewa nafisat yadda Amaka ke tsanar musulmi ba ita Kuma tace gaskiya Akwai matsala. Na SHIGA damuwa ba kadan ba inda duk suka Gane na Gama kamuwa da soyayyar Umar faruk inda Kuma waya ta tayi Kara na duba sai nayi Arba da sunan Umar faruk
Showing 21001 words to 24000 words out of 30837 words