shi ya kamani musamman da na tuno inda Yake karatu wato Egypt sai Naga lallai Dole zafin Nigeria ma yasa shi Baki


"Yaya ne Zahra me kike so? Halan cakulat din Zaki kwashe min? Nayi murmushi Wanda ya taho da hawayen tausayin shi matukar yaga dayan mu cikin damuwa to yafi mu SHIGA damuwa don Haka nace

"Dama Yaya Abdullahi wani tunani nayi me zai Hana a siyar da wannan sabuwar Jeep din ta Daddy sai inga kamar ta Isa ta fansar Mana gidan mu hannun su kawu gide Koko Yaya kake gani?.....


"Kin ko yi tunani Mai kyau Zahra ya akayi ma bamuyi wannan tunanin Ni da Ammi ba? Muje ma yanzu in fada mata shawarar ki don itace ma mafita

Ammi da taji abinda Yaya Abdullahi ya sanar da ita sai tace
"Shiyasa ba a Raina tunanin yaro kowa da irin balagar da Ubangiji yayi mishi wani azancin magana wani Kuma ta hangen nesa kunyi tunani Bari nayiwa mama magana sai ayiwa abban su Nana magana ya samo Mana me siye

Haka kuwa akayi motar Bata dauki lokaci ba aka siyar da ita kasancewar sabuwa ce ajiki Kuma sabuwar yayi sai gashi kudin ta sun iso kudi masu auki kuwa inda Yaya Abdullahi yace duka ma asiyar dasu ko wani kasuwancin sai ayi da kudin su.

Haka kuwa akayi sai dai su din basuyi Darajar ta farko ba Domin kuwa Basu kaita Daraja ba inda Kuma har yanzu ba a samu Wanda zai karbi motar Ammi ba inda abban su Nana yace Yana tsoron mutane ne saboda ba bu Allah a ransu shi Kuma Yana tsoron ya kawo Wanda zai zalunci bayin Allah Amma yace Ammi ta Kara hakuri in Sha Allah za a samo Wanda zai karba


Kwanakin da su kawu gide suka diba na kwana talatin ya na cika kuwa sai gasu wannan karon daga shi sai kawu madu suka Zo

"Yaya kun tattare kayan ku dai ko Abdullahi? Fadar kawu madu
Yaya Abdullahi yace Eh kawu Amma akwai wani hanzari ba gudu ba Ina son ku Kira dillali yayiwa gidan Nan kudi muji idan zamu iya biya sai mu biya.....

Kawu gide yace ai shi din aikin shi kenan yiwa Kaya kudi don duk dabbobin garin su shike musu kudi wannan gidan ma zai iya mishi kudi....

Yaya Abdullahi yayi murmushi Yana fadin kawu ai dillalin dabbobi daban da na gidaje.......

"Au me kake nufi kenan? Kana nufin ba Zan iya mishi kudi ba kenan? Yanzu in ubanka ne Zaka karyata shi irin Haka? Da sauri Yaya Abdullahi ya bashi hakuri Yana fadin ba Haka bane

Ya Sha mur Yana micincina idanu ya dubi gidan Yana fadin Banda an kashe gidan da kazanta ai har million Tara zai iya kaiwa inda Abdullahi ya sauke ajiyar zuciya Yana godewa Allah da yasa hadamar tasu ba Mai yawa bace Amma Kuma da ya nemi su rage sai suka ce in yayi musu a million Tara din su biya in kuwa Bai musu ba to su nema gaba don yanzu zasu Rufe gidan.......


"Yayi kawu mun gode muje banki a Ciro kudin
Haka suka tafi da kawu gide aka Ciro kudin aka damka wa kawu madu inda Yaya Abdullahi yace su bashi takardun gidan da suka amsa.

Kawu madu ya Kara gyara Rikon da yayiwa kudin Yana fadin
"Ai Kai da uwar ka Baku da wayo tunda kukayi nufin yaudarar mu dama sai da nace akwai kudin marigayi a cikin banki abinda ta kawo Dan debowa kawai tayi ta boye sauran to wadan Nan kudin idan dai har ummaru zai dawo Duniya to zasu dawo gareku idan har son gidan Nan kukeyi sai kun Kuma kawo wata million taran kafin ku zauna acikin wannan gidan su Kuma wadan Nan kudin mun Rage ne daga cikin kason gadon mu don Haka idan Kuna da muradi kwa iya fiddo wasu kudin shima kafin Nan da Rana irin ta yau sati guda Daya Tak muka Baku idan da kudi ku zauni gida idan Kuma babu to na Rantse maka da kabarin uwa ta kayan ku ma waje Zan auna muku su kaji na Gaya maka

Ya dubi kawu gide Yana fadin
"Muje gide. Da Haka suka fice Rungume da tarin kudin har million Tara

Ammi ta sauke tagumin ta da doguwar ajiyar zuciya babu Mai motsin kirki bare magana inda Kuma yaya Abdullahi yace karar su zai Kai Amma Ammi tace Kar ya Fara ya dai Ida kwaso sauran kudin ya basu inda Ni Kuma nace Mata da dai mu Kuma Basu kudin suyi tafiyar su dasu gara mu siyi wani gidan tunda ta Hana ayi karar su don wannan damar da suka samu ce tasa suke tsula iskancin su

Sai dai duk da saka cigiyar da akayi na gidan da zamu siya da akayi kafin cikar wa adin da su kawu gide suka bamu yazo shiru ba a samu ba har zuwa Ranar da su kawu suka dawo don Jin inda aka kwana don Basu ma jira jin wani bayani ba inda kawu madu ya Soma fito da kayan mu Yana watso su kwar gida duk wani Abu da ya tarbi gabanshi surowa kawai Yake Yana watso su waje

Ammi tacewa Yaya Abdullahi ya kwaso sauran kudin dake bankin ya bawa su kawu madu shi Kuma yace Yana tsoron ya dauko sauran kudin ya Basu suyi Mana yadda sukayi a farko Amma ganin sai watsi suke Mana da Kaya yasa yaje ya fito da kudin Amma yace sai sun bashi takardun gidan kafin ya Mika musu kudin.....

Kawu gide ya Miko mishi takardun a cikin jakar da suke tun farko kafin Yaya Abdullahi ya Mika musu kudin suka fashe da Dariya a lokaci Daya kafin kawu madu yace

"Ai tunda kukace yaudara ce aikin ku mu da kune in Baku fiddo Mana hakkin mu ta Arziki ba ai zaku fito dashi ta tsiya
Wai Kai Dan Boko ba zaka bada kudi ba sai an baka takardu to ga takardu Nan Amma fa na bogi ne na asalin suna hannun mu idan kazo zaka iya biyan wata million taran na maido maka su don Haka ku fito zamu datse gidan mu...............










Labarin GARWASHI na kudine ga duk me son Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669



Kar ku Bari ayi Babu ko don littafin GARWASHI daban yake da sauran




Sunana Hadiza Bara'u Gidan




Ke cewa saduwar ALHERIπŸ’ƒπŸΏ
πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€




πŸ’πŸ’πŸ’ GARWASHIπŸ’πŸ’πŸ’
Page
13//14
Hadiza Bara'u Gidan iko




Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne


Sadaukarwa ga iyayena guda biyu Uwa da Uba Allah kayi musu Rahama ka yafe musu kayi musu dukkan wata Alfarma da kakewa muminan bayinka


Ba zan taba mantawa da wadan Nan mutanen ba
Anty Jamila Yusha u
Anty Rahane sani Dan Kani
Anty Amina brn kebbi
Antyn Yola Allah ya Kara sutura

Sai haj Saliha Abubakar Abdullahi Zaria Allah ya Kara lafiya

🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


............Yaya Abdullahi ne yaga da gaske suke Shirin izo keyar mu waje su Rufe gidan gashi Kuma babu inda zamu Kai kayan da sukayi Mana watsi dasu kofar gida bare inda zamu saka hakarkarin mu mu kwanta

Ya zube Agaban kawu gide yana Rokon shi Alfarma.....

"Kawu kaifa uban mu ne don Allah Kar ku tozarta mu bamu da inda zamu koma kuji tausayin mu sau biyu fa Kuna karbe Mana kudi don Allah Kar ku Rufe Mana gida.....

"Ai tunda kukace ku Yan iska ne Kai da Uwar ka ai kun gamu manyan Yan iska tunda babu Arziki a cikin lamarin ku babu yadda bamuyi da ita ta fiddo Mana hakkin mu ba Taki Kuma Kai da muke ganin namu ne ka goyawa kafurar Uwar ka baya ko gidan ubanwa kuka samo wadan Nan kudin Haka in ba satar su Uwar ka tayi ba? To ko zaku shekara kuna kawo wasu kudin da sunan fansar wannan gidan to muma zamu shekara karbe muku kudi tunda abin naku yazo da Raini da yaudara wannan gidan dai ko kwai kuka NASA cikin shi sai kun barshi in ma Ruhin ku ke ciki sai dai ku marawa ubanku baya

Ya Soma hado Kan get din Yana kokarin Rufewa Dole muka ido kwaso kayan mu Yaya Abdullahi Kuma ya karbi key din motar Ammi dake parking space ya fito da ita muna kallo ya bugawa kofar manyan kwaduna sukayi gaba suka barmu muna tattare kayan mu da sukayi watsi dasu.
Dole gidan mama muka shigar da kayan mu acikin shagon gidan muma Nan mukayi mazauni don can cikin gidan dakin mama ne da na Mai gidan ta sai na Ya'yan su don Haka abban Nana yace idan zamu iya Zama a cikin shagon to mu koma kafin ya cigita Mana gida

Na dubi shagon Wanda kofar shi take cikin soron Kuma akwai wadda ke fita waje inda beraye ke gadar su son Ransu yau anan Allah yayi ikon shi Akan mu da komawa Rayuwa lallai bawa Bai Gama sauyawa ba sai Ranar da ya komawa Ubangiji

Muka koma Rayuwar cikin shago mu duka muka gwamutsu a wuri Daya har da Yaya Abdullahi Wanda yaso ya bar Mana Nan ya koma kwana waje duk da kasancewar yanayin damuna da ake ciki Amma Ammi tace Bata San zancen ba tunda wurin Yana da girma Dole suke wuri Daya shi da sulaiman Ni Kuma Ni da Ammi

Mama tayi ta fada da taji dalilin wannan wulakancin da su kawu sukayi Mana na karbe Mana kudi har sau biyu Kuma sukayi mana watsi da kayan mu......

"Haba Amina wannan ai Ragon azanci kikayi da Kika Bari aka sake Basu wasi kudin mutumin da Bai iya son dan uwan shi ba yaushe kike tunanin zai tausayawa Ahalin sa? Kuma ai maganar Abdullahi ai itace gaskiya da kin bari yayi karar su ai shi alkalin ba irin su Yake ba yanzu irin haka ke da Dadi saboda Allah? In ma da gaske suna da hakkin ai ba zasu karbe muku kudi har sau biyu ba ai in mutum ya Gane kana shakkar shi to shi Kuma lokacin ne zai bude kofofin tozarta ka me akeyi da muguyen dangi irin wadan Nan? Ammi sai hakuri take Bata tana kuka don gani takeyi ta batawa mama Rai don da gaske mama ta fusata ba kadan Amma Dole mama tayi hakuri tace

"Naji babu Dadi ne Amina da ace a gabana hakan ta faru wallahi ba Zan kyale su ba don zanyi wankan tsarki ne in siyi fadan Nan in yaso Ni dasu mu gurfana gaban kuliya manta sabo haba me akeyi da dangi irin wadan Nan ai gara a Raba gari kowa ya tsaya matsayin shi tunda Wanda ya hada ya Raba ko shi din ma ai ba dadin su yaji ba Amina kema kinfi kowa sanin hakan

Rayuwar mu ta koma a gidan mama inda Yaya Abdullahi ke bude shagon shi na tsohon gidan mu muna samun na hidimar yau da kullum duk da kayan shagon sunyi kasa kwarai mun cinye sai Dan abinda ba za a Rasa ba

Akace zari dai Daya Bata barin Dame domin ko sannu ahankali kayan shago suka Kare kaf mun cinye su tas har ta Kai abinda za a Kai baka sai Mama ta tallafa Mana inda duk muka fita a kamannin mu na asali muka koma wasu Yan Allah ya Baku mu samu😭

Hakika mama ta taka Rawar gani Akan mu da Rayuwar mu domin ko tsayin zaman mu a gidan ta tayi Mana hidima da dawainiya ita da mijin ta Wanda shima ba karfi ne dashi ba . Idan ammi na kuka tana godewa mama akan karamcin da take Mata sai Mama tace ai Nima kinyi min karamci Amina shi kuwa Dan halak baya manta halacci Ni meye bakiyi min ba lokacin da muka SHIGA namu halin kwatankwacin irin wannan? Sai na Gane akwai hikima cikin wata Karin magana da malam bahaushe yayi da yace ka yada ALHERI ka tsince shi a gaba domin ko ban mance ba lokacin da Ammi keyin girki ta aikawa mama sau uku a Rana lokacin da Abban Nana yayi tafiya neman kudi komai ammi bawa mama takeyi ko ta nema ko Bata nema ba hatta da omo da Sabulu aika Mata takeyi sai gashi yau da ace ammi irin Rayuwar Nan tayi irin ta kaza me ci ta goge Baki ko muguwar makotaka tayi Ashe da bamu San inda zamu jefa Kan mu ba

Muna cikin wannan halin tsaka Mai wuyar ne Kuma aka samu gidan haya Amma a can kofar marusa sai dai kudin da zamu Fara biya ma babu su sai mamace ta biya Mana muka kwaso muka dawo kofar marusa muka baro makotan kirki irin mama muka dawo wata unguwa me cike da kwatoci da gidajen laka Mai Rufin kwano ko silin Babu kasa Kuma babu tiles Sai daben sumunti. Daki biyu ne a gidan inda mukayi masauki a Daya Ni da Ammi da sulaiman muka barwa Yaya Abdullahi Daya sai dai Kuma inda take a kasa take dabo shine babu abinda zamu juya na Sana a Wanda Dole sai da shi ko da Rayuwa zata tafi yadda ake so saboda bukatun yau da kullum Dole muka Rungume hannuwa inda Kuma mama da Abban Nana sukayi Mana karamcin nasu suka biyo mu da shinkafa da garin masara da garin Dan wake Ni da kaina naji araina da ace abban Nana ne danginmu akasin su kawu gide da zumunci Bai zamo zumuncin zamani ba Kuma da ba a zagi Yan uwa da dangi ba Haka muka Mike da kaddarar da Ubangiji ya zano zata same mu . Gidan da muke ciki na wata masifaffiyar tsohuwa ne marar hakuri kamar zawo wadda Allah yayiwa Arzikin gidaje da shaguna Wanda ta bayar ake haya ake biyan ta kudin hayar Wanda Kuma ya kuskure Bai biya ba zai jita tamkar yaji a ido ko Kuma in yanayin damuna ne baka biya ba tasa a kware maka kwanon Rufin dolen ka ka biya ko ka Kara gaba
Kuma baka Fara SHIGA muhallin ta sai ka biyata kudin da kukayi na wata ukune ko shekara

Na dawo Daya makaranta inda na shigo sabuwar unguwar mu inda nake wuce mutane suna min Rakiya da ido na Kuma San Rashin sani NE ya kawo hakan ko da Yake nasan a yadda nake ko da Rayuwa tayi Mana sauyi me yawa na Rashin abubuwa masu yawa Amma Kuma hakan Bai sa na Rasa abubuwa uku ba wato kwarjini da tsabta da Kuma kyawu ba wannan Kam Koda na Rasa komai ban Rasa su ba don Haka sai na wuce Abu na bana kulawa Kuma dama Ni din ba me son wasa ko shirme bace bare sharholiyar Yan mata masu irin shekaru na komai nawa cikin nutsuwa da kame Kai ko cikin kawaye ban Faye SHIGA ba kawaye na ma biyu NE a makaranta Suma ba nice na SHIGA jikin su ba sune suka shigo Wai Ina burgesu sai muke kadaran kadahan don ban saki jiki dasu sosai ba

Na shigo gida na iske ammi a tsakar gida tana girki tsakar Rana don babu kichen a gidan sai tsakar gida take girki inda na iske ammi na sakun Dan wake abinda na tsana a Rayuwa ta don duk Ranar da Kai Dan wake a cikina Koda kwara daya ne sai nayi ta zagawa bandaki cikina baya son sa Amma sanin da nayi ammi ta San bana son shi yanzu ne da na furta zata ce zata sama min wani abun Dole na maye kiyayyar Dan waken da soyayya bayan nayi Mata sannu da gida da Kuma aiki

"Yauwa Zahra ta kiyi hakuri kici Dan waken Nan sai ki Sha Yar kanwa gata Nan ba zai Bata Miki ciki ba naso na sama Miki ko garin kwaki ne Amma abin ya gagara.....

Zuciya ta naji ta karye saboda tausayin ammi na dubeta sai zufa take a tsakiyar Rana inda wahala ta sauko Mata da wani irin tsufa tamkar ba itace Yar gayun Nan da Daddy ke kambamawa a fagen kyau.

Haka muka ci Dan waken Nan Amma Kuma kamar hadin Baki mu duka ukun muka kware da Rudewar ciki muna ta zagaya bandaki Ni da Yaya Abdullahi da sulaiman ammi ta Rude ta fito ta siyo Mana magani flajin kafin muka samu afuwa

Zaman Shirun da Rashin abinyi yasa Yaya Abdullahi yanemi shawarar ammi Akan ta barshi ya dauki motar ta ya Soma sufurin ko don kudin hayar da ke kusanto mu Dole ammi ta yarda Yaya Abdullahi ya Soma sufuri zuwa Kano ko funtua duk inda dai ya samu fasinja a Haka muka samu Rufin Asiri Mai yawa Ashe wannan Jan motar na Yaya Abdullahi shima wata kaddarar ce ke Shirin sauka Akan mu kaddarar da zata girgiza mu fiye da kaddarorin da suka Riske mu a Baya.............













Labarin GARWASHI na kudine ga duk me son Jin cikakken labarin zai biya 300 ne kacal Akan wannan account din 1780003378 Eco Bank ko Kuma katin MTN Akan wannan layin 08035191669




Wannan labarin na GARWASHI daban yake da sauran Kar ku Bari ayi Babu ku






Gidan iko ke cewa saduwar ALHERIπŸ’ƒπŸΏ
πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€πŸ–€




πŸ’πŸ’πŸ’ GARWASHIπŸ’πŸ’πŸ’
Page
15//16
Hadiza Bara'u Gidan iko




Hakkin mallakar ma na gidan iko ne Kuma abin kiyayewa ne


Sadaukarwa ga Yan kungiyar kainuwa writes associated Gaba Daya kaf Ranka takaf ban cire ko guda ba Allah ya Kara daukaka

Sadaukarwa ta biyu ga dukkan musulmin da Ubangiji ya jarabta da kuncin Rayuwa Allah ka fidda bayin ka daga kunci da talauci ka maye da gurbin Arziki


Ban manta masoya ba har Abada kuwa ba Zan manta Babu abinda yafi a furta maka ana kaunar ka musamman Irina da ban Kai ba ban Kuma iya ba


🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹


........... Wannan wahalar da Yaya Abdullahi ya samu kanshi a Rana tsaka ta Jan mota da sufuri tayi matukar tafiyar da kumarin jikin sa

Ya Kara dafewar fata ya Kuma Kara Rama Akan wadda ya samu
Showing 9001 words to 12000 words out of 30837 words