Dariya Sauban ya tuntsure da ita ya shafa kansa yana fad'in “Aunty jeki sama kisha kallo mana”. ya shige d'akinsa yana cigaba da dariyarsa.
Itama dariyar tayi, a fili tace, “Munaya kin biyamu wlhy, ALLAH ya bamu ikon miki halacci kema fiye da wanda kikai mana”.
Nane, “amin waunti mimi😄”.
)*()*()*()*()*()*()*()*()*()*()*(
To yau dai ga Munaya ga Munubiya a gida, gaban innarsu, ga y'an k'annensu, abin sha'awar harda k'arin y'ay'ansu, ita kanta Innarsu kallo d'aya zai tabbatar maka da farin cikin datake a ciki, badan aureba mixai rabata da y'an y'ay'anta masu tausayinta.
Ranar dai haka muka kusan kwana hira da labaran yaushe gamo, kota yaranma bamayi sai laraba ce da innarmu kemana magana akan mu shayar dasu.
Washe garima mun tashi cikin farin cikin kasancewa da juna, aka dama mana kunun kanwa mai rai da lafiya, yanata k'amshin kayan yaji, ga k'osai mai dad'i a gefe, munacin kayanmu muna hira, Fauziyya ta shigo itama tsaf da ita, jegon ya kar6eta sosai, rungume juna mukayi ni da ita cikin kewa, itama ta zauna muka cigaba da karin kumallon tare, anan take bamu labarin wahalar datasha wajen haihuwa, yanzu hakama ita ba'a mata wankan jegon, saboda jininta yak'i sauka, sosai Muka tausaya mata, da fatan samun lafiya a gareta, nace muma ai munsha wahalar, nabasu labarin nak'udar kwana uku danasha kafin mu taho Nigeria, Munubiya harda hawayenta, dukda itama tasha tata azabar.
Inna dai da Laraba najinsu daga tsohon d'akin su Munayar suna musu dariya, sunsha hirarsu har d'agawar hantsi, saida aka aiko kiran Fauziyya yaronta Na kuka sannan tamik'e ta tafi.
A sannan ne Innaro ta shigo gidan, dama kullum takanzo taga masu jegon, d'akin kowa ta shiga taga sauran, Dan ita Safara'u ma takusa komawa, tunda itace ta fara haihuwa itada Haleematu.
Ni da Munubiya muka gaida Innaro, amsa muna tayi babu yabo babu fallasa, hakkane ya sakani shareta nacigaba da latsa wayar Munubiya da ke hannuna.
Innarmu ta fito daga d'aki d'auke da Abdurraheem daya farka yana kuka.
Innaro ta wani bud'e baki da rik'e ha6a tana kalon innarmu, cikin tafa hannaye tace, “O ni Marwanatu, yanzu nan Ai'sha jikan farinne kike mamuk'a haka tamkar wani autanki?”.
Kallon juna Mukayi ni da Munubiya, sannan muka kalli innaro, ganin Innarmu ta tsaya sororo alamar tad'anji kunya sai Munubiya ta mik'e, inda take taje ta amsa Abdurraheem d'in.
“la'ilahailllahu..”. Innaro tafad'a cikin mik'ewa a zabure alamar mamaki, tace, “A lallai duniya tazo k'arshe, ke kinmafi uwar taku ashe? Dagani babu tambaya nasan Munaya ce wannan, fetsararriya anzo a d'ora daga inda aka tsaya kenan?”.
Murmushi nayi, Na kar6i Abdurraheem da Munubiya ta d'oramin a cinya, saida Na fara shayar dashi sannan Na kalli innaro, nace, “Innaro inhar kin shirya d'orawa daga inda kika tsaya muje zuwa mana, indai bazaki canjaba Munaya ma har abada zabata canjaba, miye laifin Innarmu danta d'akkoshi yana kuka?, rawa kika tarar tana masa ko wata tsiya? Yo nagama kema haka kikaita ma mutane kuka saikinje jiyyar abbanmu India, halan kema kunyar d'an farince.......”.
Bankai k'arshen zancenba innaro ta d'ora hannu bisa ka ta aza mana kuka. Ni da Munubiya muka kuwa kwashe da dariya abinmu, a haka abbanmu ya shigo ya samemu, Innarmu tanata bama innaro hak'uri tak'i saurarenta.
Girgiza kai kawai Abba yayi, Dan akan idonsa komi ya faru, hannu ya d'agama Innarmu alamar ta barta, zata fara magana ya girgiza mata kai. Shiru tayi takoma gefe, innaro saita k'ara k'arfin kukanta wanda harya fara jawo hankalin matan gidanmu, saidai babu damar zuwa kallon kwaf tunda a d'akine.
Hannun innaro Abba ya kama ya zaunar da ita, cikin kwantar da harshe yace, “haba dai inna, yanzu dan ALLAH abinda akayi yarannan Na k'anana yanzuma shi za'a sake azaman dazasuyi Na wata 1 kacal dawasu kwanaki? Haba inna, minene Dan yaro yayi kuka Ai'sha ta d'akkoshi? Inna ina dad'i irin wad'annan abubuwan haka?”.
Share hawaye innaro tayi, tace, “to naji Auwalu, indai nice bazan sake magana akan y'ay'anka da matarka ba....”.
“da yafi”. Nafad'a ina murgud'a baki.
Hararata Abba da Innarmu sukayi, Abba ya rik'e hannun innaro da sauri saboda k'ok'arin tashi da takeyi, “kiyi hak'uri Dan ALLAH inna, niba haka nake nufiba, da ni da abinda Na mallaka ai duk mallakinkine, nafad'a ne dan kawai a zauna lafiya yarannan sugama wanka kowa takoma gidan mijinta cikin salama, tunda kinga dai da yaran d'akinnan ne kawai irin wannan sa6anin ke shiga, yanzufa kika fito d'akin can kina tsokanar yarinyar Haleematu, mizaisa anan kuma hakan bazata kasanceba?”.
“shikenan naji”. Abinda innaro tace kenan kawai ta mik'e ta fice.
Abba ya bita da kallon kawai cike da takaici.
Gaidashi mukayi, ya amsa yana had'iye 6acin ransa, ya tambayemu ya yara?, duk shiru mukayi muka kasa amsashi saboda kunya.
Murmushi yayi, ya kar6i Abdurraheem daya gama shan nono, bayan Innarmu yabi d'akinta d'auke da yaron, dan tunda yamata magana tabar falon ta shige d'akinta.
Zaune ya isketa a bakin gado tayi tagumi tana hawaye.
Ya zauna kusada ita rungume da Abdurraheem, shiru yay yana kallonta, kusan mintuna biyu ya kwantar da yaron a bayansu yamatsa jikinta sosai yana kwantota jikinsa, “kiyi hak'uri Ai'sha, a halin inna babu wanda baki saniba yanzu, tunkan kizama mata a gareni kinsan wannan, to mizaisa hakan yasakaki kuka a yanzu? wani abin nata harda tsufa yanzu, amma kiyi hak'uri dan ALLAH”.
“Ni ba kuka nakeyi saboda abinda inna takeminba, ina kukane saboda rashin jituwar da kullum take k'ara tasiri tsakaninta da yarannan, duk yanda naso hana girmamar irin wad'annan abubuwa n abun ya gagara, bai kamata ace laifina yana shafar jikokinta ba, jinintane fa su, idan ni tace banda asali sukuma ai itace asalinsu ko? wlhy Abbansu banason wad'annan abubuwan, wani lokacin zuciyata takan gaza d'auka”.
“kiyi hak'uri, insha ALLAH komai mai wucewane, yakamata kuma zuwa yanzu kufad'a mana Ku su wanene? Kodan yaranki, dangin mahaifiya sunada matuk'ar tasiri a rayuwar yaro, banason zuwa nan gaba su zargi abinda ba haka yakeba, kodan gudun suma y'ay'ansu su taso suyi musu irin wannan tambayar”.
Murmushin takaici inna tayi, ta d'ago daga jikinsa tana share hawayenta, suduka kallon Abdurraheem daketa motse-motse da k'afafu yana dungurin bayansu sukayi, Abba yay murmushi yana shafa kansa, sannan ya kalli inna yana fad'in “Ai'sha kodan wad'annan yaran, dolene watan watarana sai tarihinsu ya shafi tsokaci dangane da usilin mahaifiya, dukda nawa za'a kawo saifa naki ya taka rawar gani shima”.
Inna tayi murmushi itama tana shafar kumatun Abdurraheem d'in, ta mik'e tsaye tana cewa “karka damu, a bani lokaci, da izinin ALLAH saisun taka tushena da k'afafunsu”.
Abba ya d'auki Abdurraheem ya rungume yana fad'in “ALLAH ya tabbatar”.
Mukan bamusan wainar da ake toyawaba, muna falo yara suna Neman haukatamu da kukansu, dukfa barci suke, amma Meena Na tashi kamar jira suma duk suka tashi masu kawunan kwakwar.😏
Haushi ya isheni nakusa make Amaturrahman datafi kowa daddagewa, saida Munubiya ta rik'e hannuna, “Sweetheart wai baki da hankaline? Uwarmi zaki daka ananne?”.
Cikin tura baki nace, “yo Sweetheart haukatamu zasuyine?”.
Daga inna har Abba dake fitowa baki suka gumtse suna dariya, “A lallai akwai aiki babba a gaban mata ashe?”. Inna tafad'a tana kallon Abba.
Murmushi yayi shima yace, “babba kuwa Ai'sha”. Sai sukayi dariya.
Hakanne yasakamu farga dasu, muka juyo muna kallonsu kowa fuska a tur6une, saboda haushin da yaran suka bamu.
%%%%%%%%%%%%%%%%
Bayan kammala gyara da Sauban yayi, Galadima ya mik'e zuwa cikin d'akin, zama yay ya kunna dukkan Computers d'in d'akin, saida komai ya dai-daita sannan yafara aikinsa cike da kwarewa, har lokacin sallar la'asar yana a d'akin, shiko gajiyar zaman jirginma bata damesa ba, bedroom d'insa ya dawo yay salla sannan ya sauka k'asa, Samha yabama Umarnin abinda yake buk'ata ya dawo yacigaba da aikinsa.
Mintuna kad'an sai gata takawo masa. takan shiga shauk'i idan taga Uncle Sam yana sarrafa Computers d'innan, saitaji tamkar yafi kowa ilimin sarrafa Computer a duniya, amma tasan dole sai ansamu wanda suka fishi, badan karya maketa ba data tsaya taita kallonsa kawai.
Shi baimasan tanayiba, hankalinsa nakan aikinsa gaba d'aya, dukda kansa daya fara ciwo kad'an-kad'an burinsa yakai inda yake hari.
Saida duhun magriba ya gabato sannan yasamu kansa, yanzu ma a d'akin yay sallar magrib, ya zauna karatun Qur'an har time d'in isha'i yayi. Yana idarwa ya d'ora da shafa'i da wutiri, saboda barcin dake damunsa, soyake ya kwanta da wuri, duk abinda yakeyi kafin barci saida yay k'ok'arin kammalashi da k'yar sannan ya kwanta, dukda tunani da kewar yaransa Na neman 6atar da barcin nashi haka yayta yak'i da shi har barcin yaci Galadima akan tunanin.
Samha tazo kawo masa dinner ta iske yanata barci cikin bargo, yama kashe hasken d'akin saina fitilar gefen gadon kawai itakuma haske kad'anne. Ajiye abincin tayi, dukda mawuyacine ya tashi domin cinsa, musamman da saida yamma yamaci d'azun..
(((+)))★(((+)))★(((+)))
Yau kwananmu biyu kenan da dawowa gida, nayi waya dasu Samha duka amma banda uban gayya Galadima, bai nemini ba nima ban nemeshiba, Momma kam kullum sau biyu take kira muyi video call itada Abie, safe da yamma duk takan kirani.
Muna kwance a gado ni da Munubiya, sai kuma mak'e murya takeyi suna waya itada yaa Marwan, koni dake kusa da ita ba komai nakejiba, nayi murmushin takaici ina juya kwanciyata zuwa d'ayan 6arin, danma Na daina jinta gaba d'aya, wata kwalla ta tararmin a ido, ba bak'in cikin kasancewar y'ar uwata a farin cikin nakeba, a', tausayin kainane ya kamani, maybe ita kad'aice zata koma gidan nata mijin banda ni, Na kalli yaranmu da laraba keta musu shirin barci, Aiyaan da Aryaan nata jagwalgwalasu, saurin d'auke k'ananun kwallar dake Neman zubomin nayi.
Ni dai har barci ya d'aukeni bansan lokacin da Munubiya tagama wayarnanba, ban farkaba saida yaran suka farka da kuka, yanzu sabon iskancin da suka tsiro dashi kenan su duka 5 d'in, wato kukan dare, da zarar 2am tayi tamkar an kad'a musu k'ararrarwar tashine, haka zasuyita kuka har sai asubahi ta gabato sukeyin shiru, da zarar asuba tayi saisu hau barci, ko wankan safe za'a musu sai an tashesu, daganan wani sabon barcin suke d'orawa, haka zasu yini barci, sai dare yayi suce basusan zancenba.
ALLAH yau tamkar namusu kuka haka naji, dama ga haushin Ubansu dana kwanta dashi, ficewata nayi daga d'akin nakoma falo Na kwanta, nabar Innarmu da Munubiya da laraba dasu.
🤣ho Munaya kad'anma kenan🤭.
////....//////.....//////....////
A kwanaki biyunnan gaba d'aya Galadima cikin kai kawo yayisu, bashi Company bashi wajejen daduk yake Business, bashi Asibiti wajen Abie, yanason ya killace komai wajen wad'anda zasu iya kula masa da Amana, saboda baisan iya adadin lokacin da zai d'auka a Nigeria ba wannan lokacin, inma zai shigo india bazai dinga wuce kwanaki biyuba zai barta, shima dan yadinga zagayo iyayensa ne.
Har y'ar rama yayi saboda tsabar komawa busy, ga kewar yaransa (niko nace kodai harda uwar yaran🤣🥴).
Momma kawai tasan halin da ake ciki, amma koda wasa basa sanarma Abie komai dangane da hakan, yakanyi dai mamakin komawar Galadima busy a wanan dawowar, dan ko asibiti yaje baya zaman 30minutes yake fitowa. Abie dai ya kasa hak'uri ya tambayi Momma, saita cemasa wani aikine zasuyi a Nigeria gameda Company d'insu, kuma shi aka d'ora akan aikin, shiyyasa yakeson tattara komai wajen mutanansa nanan.
Abie yace, “to ALLAH ya taimaka, yabada nasara fiye da wanda ake tsammani”.
Momma taji dad'in wannan addu'ar, dan haka ta amsa da “Amin” cike da fara'a.
A kwana Na uku Galadima bai samu damar tafiyarba dai, saboda bai kammala uzirorinsa ba, dole ma zai k'ara koda kwana biyune.
Sauban harda rawa dan dad'i, dan shifa bason zaman masarautar nan tasu yakeba🤥.
Yauma a gajiye ya dawo gidan, kallo d'aya zaka masa ka fahimci hakan ko a yanayin tafiyarsane da fuskarsa datai cinkus babu walwala, hannu kawai ya d'agama su Samha dake falo suna gaidashi, harya 6acema ganinsu daga hawan benan idonsu Na kansa, tausayinsa ya kamasu, shidai yana shiga tun a falo yafara zame green jacket d'in dake saman kayansa, ya k'arasa cikin bedroom d'in yana jefa rigar saman sofa da furzar da huci, freight ya bud'e ya d'auki ruwa, batareda kofiba yahau shan kayansa, tas ya shanyeshi ya jefar da robar yana had'iye wanda ke gumtse a bakinsa, sannan ya k'arasa bakin gadon ya zauna ya dafe kansa, tsawon mintuna uku yana a haka shiru, har wayarsa tafara wringing amma bai kulaba, saida aka kira kusan sau uku sanannan yama kalli wayar yana k'aramin tsaki, kamar bazai d'agaba amma saiya d'auki wayar tana gab da tsinkewa, kafin yay picking call d'in ta tsinke. Kiransa yayi dan Nuren ne.
Bugu d'aya Nuren ya d'aga, bayan sun gaisa yake sanar masa yarinyar minister ce batada lafiya, kuma ya lura yarinyar kamar tanada Asthma ma ne.
“Asthma? to miye ya tada ciwon nata? naga dai ba wani Abu dazai iya shafar tashin ciwon nata a gidan?”.
“hakane Brother, wlhy muma bamusan daliliba”.
“Toni yanzu daka kirani mizan muku ina nan?, kufita ku nema mata magani mana”.
“Muftahu ya tafi, dama na gaya maka ne ka Sani kawai”.
“okay. ALLAH yabata lafiya to. Ya maganar Harun?”.
“Sunan sun baza cigiyarsa gidajen redio shida Alhaji Darma, kaga yanda kuwa suka gama rikicewa, da farko sunce yayi Accident shida driver d'insa amma anrasa inda yake shi, to inaga ko driver n ya dawo hayyacinsa ne ya sanar musu shikad'ai yay Accident d'in oho, jiya dai saiga wata sanarwar suna fad'in anyi Garkuwa da shine tunkan accident d'in, amma har yanzu ba'a nemi kud'in fansaba, dan kidnappers d'in basuce komaiba”.
Galadima yay murmushin gefen baki yana susar gashin girarsa a hankali, yad'an cije lips yana fad'in “toko zaku saka kud'ine marayu su sami na abinci da kud'in makaranta”.
Dariya Nuren ya kwashe dashi, yace, “dan ALLAH da gaske kake brother”.
Kwanciya Galadima yayi yana fad'in, “kai d'an air wasa nakeyi”.
Nuren yay kwafa, “wlhy da ace gaske kakeyi Kansan ALLAH saina k'ure dukiyarsa sannan, nakuma rud'asu da cewar ya fad'amin wani sirri, idan basu biyaba zan tona”.
“ALLAH ya shiryeka to”. Galadima yafad'a yana kuma tashi zaune.
“Amin”. Nuren ya amsa.
“Wai anya kuwa zaka shigo yau d'in?”.
“No, maybe ma sai nanda kwana biyu ko uku, bangama hidimomina ba, kudai kuci gaba da kulawa...”.
K'it ya yanke wayar batareda jiran abinda Nuren zai ceba.
Takalminsa ya cire da kayan ya shiga wanka, yad'an jima sannan yafito d'aure da towel ya yafo wani a jikinsa, ya zauna saman sofa yana d'aukar wayarsa, number d'inta ya lalubo, sai kuma ya kasa kira ya kurama number ido kawai, tun randa suka iso hakanne ke faruwa, saiya d'auki wayar kamar zai kira saiya fasa, gashi yanason jin Yaya yaransa da jikin Abdurraheem, ya danna kiran yana cizar lips d'in nasa daya zame masa jiki🙄😏.
_______________
Muna zaune a d'akin mu ni da Ayusher, Feena da sukazo, tirene a tsakkiyarmu munacin d'an wake da Maman yaa Hameed tayi yau dan aikintane, wayata na hannun Feena tana kallon pictures kiran ya shigo, kallona tayi ta kalli wayar ta kwashe da dariya tana mik'omin.
Muduka kallonta mukayi da mamaki, na kar6i wayar ina fad'in, “kekam kokin fara zarewane?”.
Bata bani amsaba, saima dariyarta take cigaba dayi, na kalli wayar nima, a dai-dai nan kiran ya tsinke, sunan mai kiranne ya d'auki hankalina, *_“Rabin raina!”_* na fad'a a saman lips, ni dai banyi saving number kowa hakaba, yanzu na fahimci abinda yabama Feena dariya kenan.
Daga can Galadima yay tsaki, yana jefar da wayar ya mik'e zuwa gaban mirror, saidai kuma zuciyarsa takasa hak'ura, sukda haushin kansa da yakeji na kiranta da yayi, to amma ai dan yaransama yayi, shine zatak'i d'aga masa waya? zuciyarsa tace idan kuma bata kusafa? Kokuma yaran ne suka d'auke mata hankali da kuka.
Iska ya furzo daga bakinsa, dan tuna hakan zata iya yuwuwa kuma, saiya mik'e ya d'auki wayar, lallai yau Munaya takafa tarihi a rayuwarsa, ko Momma idan yay mata kira d'aya bata d'agaba yakan hak'ura saita kirashi, inhar baya mantaba baita6a kiran
Showing 12001 words to 15000 words out of 115198 words
Itama dariyar tayi, a fili tace, “Munaya kin biyamu wlhy, ALLAH ya bamu ikon miki halacci kema fiye da wanda kikai mana”.
Nane, “amin waunti mimi😄”.
)*()*()*()*()*()*()*()*()*()*()*(
To yau dai ga Munaya ga Munubiya a gida, gaban innarsu, ga y'an k'annensu, abin sha'awar harda k'arin y'ay'ansu, ita kanta Innarsu kallo d'aya zai tabbatar maka da farin cikin datake a ciki, badan aureba mixai rabata da y'an y'ay'anta masu tausayinta.
Ranar dai haka muka kusan kwana hira da labaran yaushe gamo, kota yaranma bamayi sai laraba ce da innarmu kemana magana akan mu shayar dasu.
Washe garima mun tashi cikin farin cikin kasancewa da juna, aka dama mana kunun kanwa mai rai da lafiya, yanata k'amshin kayan yaji, ga k'osai mai dad'i a gefe, munacin kayanmu muna hira, Fauziyya ta shigo itama tsaf da ita, jegon ya kar6eta sosai, rungume juna mukayi ni da ita cikin kewa, itama ta zauna muka cigaba da karin kumallon tare, anan take bamu labarin wahalar datasha wajen haihuwa, yanzu hakama ita ba'a mata wankan jegon, saboda jininta yak'i sauka, sosai Muka tausaya mata, da fatan samun lafiya a gareta, nace muma ai munsha wahalar, nabasu labarin nak'udar kwana uku danasha kafin mu taho Nigeria, Munubiya harda hawayenta, dukda itama tasha tata azabar.
Inna dai da Laraba najinsu daga tsohon d'akin su Munayar suna musu dariya, sunsha hirarsu har d'agawar hantsi, saida aka aiko kiran Fauziyya yaronta Na kuka sannan tamik'e ta tafi.
A sannan ne Innaro ta shigo gidan, dama kullum takanzo taga masu jegon, d'akin kowa ta shiga taga sauran, Dan ita Safara'u ma takusa komawa, tunda itace ta fara haihuwa itada Haleematu.
Ni da Munubiya muka gaida Innaro, amsa muna tayi babu yabo babu fallasa, hakkane ya sakani shareta nacigaba da latsa wayar Munubiya da ke hannuna.
Innarmu ta fito daga d'aki d'auke da Abdurraheem daya farka yana kuka.
Innaro ta wani bud'e baki da rik'e ha6a tana kalon innarmu, cikin tafa hannaye tace, “O ni Marwanatu, yanzu nan Ai'sha jikan farinne kike mamuk'a haka tamkar wani autanki?”.
Kallon juna Mukayi ni da Munubiya, sannan muka kalli innaro, ganin Innarmu ta tsaya sororo alamar tad'anji kunya sai Munubiya ta mik'e, inda take taje ta amsa Abdurraheem d'in.
“la'ilahailllahu..”. Innaro tafad'a cikin mik'ewa a zabure alamar mamaki, tace, “A lallai duniya tazo k'arshe, ke kinmafi uwar taku ashe? Dagani babu tambaya nasan Munaya ce wannan, fetsararriya anzo a d'ora daga inda aka tsaya kenan?”.
Murmushi nayi, Na kar6i Abdurraheem da Munubiya ta d'oramin a cinya, saida Na fara shayar dashi sannan Na kalli innaro, nace, “Innaro inhar kin shirya d'orawa daga inda kika tsaya muje zuwa mana, indai bazaki canjaba Munaya ma har abada zabata canjaba, miye laifin Innarmu danta d'akkoshi yana kuka?, rawa kika tarar tana masa ko wata tsiya? Yo nagama kema haka kikaita ma mutane kuka saikinje jiyyar abbanmu India, halan kema kunyar d'an farince.......”.
Bankai k'arshen zancenba innaro ta d'ora hannu bisa ka ta aza mana kuka. Ni da Munubiya muka kuwa kwashe da dariya abinmu, a haka abbanmu ya shigo ya samemu, Innarmu tanata bama innaro hak'uri tak'i saurarenta.
Girgiza kai kawai Abba yayi, Dan akan idonsa komi ya faru, hannu ya d'agama Innarmu alamar ta barta, zata fara magana ya girgiza mata kai. Shiru tayi takoma gefe, innaro saita k'ara k'arfin kukanta wanda harya fara jawo hankalin matan gidanmu, saidai babu damar zuwa kallon kwaf tunda a d'akine.
Hannun innaro Abba ya kama ya zaunar da ita, cikin kwantar da harshe yace, “haba dai inna, yanzu dan ALLAH abinda akayi yarannan Na k'anana yanzuma shi za'a sake azaman dazasuyi Na wata 1 kacal dawasu kwanaki? Haba inna, minene Dan yaro yayi kuka Ai'sha ta d'akkoshi? Inna ina dad'i irin wad'annan abubuwan haka?”.
Share hawaye innaro tayi, tace, “to naji Auwalu, indai nice bazan sake magana akan y'ay'anka da matarka ba....”.
“da yafi”. Nafad'a ina murgud'a baki.
Hararata Abba da Innarmu sukayi, Abba ya rik'e hannun innaro da sauri saboda k'ok'arin tashi da takeyi, “kiyi hak'uri Dan ALLAH inna, niba haka nake nufiba, da ni da abinda Na mallaka ai duk mallakinkine, nafad'a ne dan kawai a zauna lafiya yarannan sugama wanka kowa takoma gidan mijinta cikin salama, tunda kinga dai da yaran d'akinnan ne kawai irin wannan sa6anin ke shiga, yanzufa kika fito d'akin can kina tsokanar yarinyar Haleematu, mizaisa anan kuma hakan bazata kasanceba?”.
“shikenan naji”. Abinda innaro tace kenan kawai ta mik'e ta fice.
Abba ya bita da kallon kawai cike da takaici.
Gaidashi mukayi, ya amsa yana had'iye 6acin ransa, ya tambayemu ya yara?, duk shiru mukayi muka kasa amsashi saboda kunya.
Murmushi yayi, ya kar6i Abdurraheem daya gama shan nono, bayan Innarmu yabi d'akinta d'auke da yaron, dan tunda yamata magana tabar falon ta shige d'akinta.
Zaune ya isketa a bakin gado tayi tagumi tana hawaye.
Ya zauna kusada ita rungume da Abdurraheem, shiru yay yana kallonta, kusan mintuna biyu ya kwantar da yaron a bayansu yamatsa jikinta sosai yana kwantota jikinsa, “kiyi hak'uri Ai'sha, a halin inna babu wanda baki saniba yanzu, tunkan kizama mata a gareni kinsan wannan, to mizaisa hakan yasakaki kuka a yanzu? wani abin nata harda tsufa yanzu, amma kiyi hak'uri dan ALLAH”.
“Ni ba kuka nakeyi saboda abinda inna takeminba, ina kukane saboda rashin jituwar da kullum take k'ara tasiri tsakaninta da yarannan, duk yanda naso hana girmamar irin wad'annan abubuwa n abun ya gagara, bai kamata ace laifina yana shafar jikokinta ba, jinintane fa su, idan ni tace banda asali sukuma ai itace asalinsu ko? wlhy Abbansu banason wad'annan abubuwan, wani lokacin zuciyata takan gaza d'auka”.
“kiyi hak'uri, insha ALLAH komai mai wucewane, yakamata kuma zuwa yanzu kufad'a mana Ku su wanene? Kodan yaranki, dangin mahaifiya sunada matuk'ar tasiri a rayuwar yaro, banason zuwa nan gaba su zargi abinda ba haka yakeba, kodan gudun suma y'ay'ansu su taso suyi musu irin wannan tambayar”.
Murmushin takaici inna tayi, ta d'ago daga jikinsa tana share hawayenta, suduka kallon Abdurraheem daketa motse-motse da k'afafu yana dungurin bayansu sukayi, Abba yay murmushi yana shafa kansa, sannan ya kalli inna yana fad'in “Ai'sha kodan wad'annan yaran, dolene watan watarana sai tarihinsu ya shafi tsokaci dangane da usilin mahaifiya, dukda nawa za'a kawo saifa naki ya taka rawar gani shima”.
Inna tayi murmushi itama tana shafar kumatun Abdurraheem d'in, ta mik'e tsaye tana cewa “karka damu, a bani lokaci, da izinin ALLAH saisun taka tushena da k'afafunsu”.
Abba ya d'auki Abdurraheem ya rungume yana fad'in “ALLAH ya tabbatar”.
Mukan bamusan wainar da ake toyawaba, muna falo yara suna Neman haukatamu da kukansu, dukfa barci suke, amma Meena Na tashi kamar jira suma duk suka tashi masu kawunan kwakwar.😏
Haushi ya isheni nakusa make Amaturrahman datafi kowa daddagewa, saida Munubiya ta rik'e hannuna, “Sweetheart wai baki da hankaline? Uwarmi zaki daka ananne?”.
Cikin tura baki nace, “yo Sweetheart haukatamu zasuyine?”.
Daga inna har Abba dake fitowa baki suka gumtse suna dariya, “A lallai akwai aiki babba a gaban mata ashe?”. Inna tafad'a tana kallon Abba.
Murmushi yayi shima yace, “babba kuwa Ai'sha”. Sai sukayi dariya.
Hakanne yasakamu farga dasu, muka juyo muna kallonsu kowa fuska a tur6une, saboda haushin da yaran suka bamu.
%%%%%%%%%%%%%%%%
Bayan kammala gyara da Sauban yayi, Galadima ya mik'e zuwa cikin d'akin, zama yay ya kunna dukkan Computers d'in d'akin, saida komai ya dai-daita sannan yafara aikinsa cike da kwarewa, har lokacin sallar la'asar yana a d'akin, shiko gajiyar zaman jirginma bata damesa ba, bedroom d'insa ya dawo yay salla sannan ya sauka k'asa, Samha yabama Umarnin abinda yake buk'ata ya dawo yacigaba da aikinsa.
Mintuna kad'an sai gata takawo masa. takan shiga shauk'i idan taga Uncle Sam yana sarrafa Computers d'innan, saitaji tamkar yafi kowa ilimin sarrafa Computer a duniya, amma tasan dole sai ansamu wanda suka fishi, badan karya maketa ba data tsaya taita kallonsa kawai.
Shi baimasan tanayiba, hankalinsa nakan aikinsa gaba d'aya, dukda kansa daya fara ciwo kad'an-kad'an burinsa yakai inda yake hari.
Saida duhun magriba ya gabato sannan yasamu kansa, yanzu ma a d'akin yay sallar magrib, ya zauna karatun Qur'an har time d'in isha'i yayi. Yana idarwa ya d'ora da shafa'i da wutiri, saboda barcin dake damunsa, soyake ya kwanta da wuri, duk abinda yakeyi kafin barci saida yay k'ok'arin kammalashi da k'yar sannan ya kwanta, dukda tunani da kewar yaransa Na neman 6atar da barcin nashi haka yayta yak'i da shi har barcin yaci Galadima akan tunanin.
Samha tazo kawo masa dinner ta iske yanata barci cikin bargo, yama kashe hasken d'akin saina fitilar gefen gadon kawai itakuma haske kad'anne. Ajiye abincin tayi, dukda mawuyacine ya tashi domin cinsa, musamman da saida yamma yamaci d'azun..
(((+)))★(((+)))★(((+)))
Yau kwananmu biyu kenan da dawowa gida, nayi waya dasu Samha duka amma banda uban gayya Galadima, bai nemini ba nima ban nemeshiba, Momma kam kullum sau biyu take kira muyi video call itada Abie, safe da yamma duk takan kirani.
Muna kwance a gado ni da Munubiya, sai kuma mak'e murya takeyi suna waya itada yaa Marwan, koni dake kusa da ita ba komai nakejiba, nayi murmushin takaici ina juya kwanciyata zuwa d'ayan 6arin, danma Na daina jinta gaba d'aya, wata kwalla ta tararmin a ido, ba bak'in cikin kasancewar y'ar uwata a farin cikin nakeba, a', tausayin kainane ya kamani, maybe ita kad'aice zata koma gidan nata mijin banda ni, Na kalli yaranmu da laraba keta musu shirin barci, Aiyaan da Aryaan nata jagwalgwalasu, saurin d'auke k'ananun kwallar dake Neman zubomin nayi.
Ni dai har barci ya d'aukeni bansan lokacin da Munubiya tagama wayarnanba, ban farkaba saida yaran suka farka da kuka, yanzu sabon iskancin da suka tsiro dashi kenan su duka 5 d'in, wato kukan dare, da zarar 2am tayi tamkar an kad'a musu k'ararrarwar tashine, haka zasuyita kuka har sai asubahi ta gabato sukeyin shiru, da zarar asuba tayi saisu hau barci, ko wankan safe za'a musu sai an tashesu, daganan wani sabon barcin suke d'orawa, haka zasu yini barci, sai dare yayi suce basusan zancenba.
ALLAH yau tamkar namusu kuka haka naji, dama ga haushin Ubansu dana kwanta dashi, ficewata nayi daga d'akin nakoma falo Na kwanta, nabar Innarmu da Munubiya da laraba dasu.
🤣ho Munaya kad'anma kenan🤭.
////....//////.....//////....////
A kwanaki biyunnan gaba d'aya Galadima cikin kai kawo yayisu, bashi Company bashi wajejen daduk yake Business, bashi Asibiti wajen Abie, yanason ya killace komai wajen wad'anda zasu iya kula masa da Amana, saboda baisan iya adadin lokacin da zai d'auka a Nigeria ba wannan lokacin, inma zai shigo india bazai dinga wuce kwanaki biyuba zai barta, shima dan yadinga zagayo iyayensa ne.
Har y'ar rama yayi saboda tsabar komawa busy, ga kewar yaransa (niko nace kodai harda uwar yaran🤣🥴).
Momma kawai tasan halin da ake ciki, amma koda wasa basa sanarma Abie komai dangane da hakan, yakanyi dai mamakin komawar Galadima busy a wanan dawowar, dan ko asibiti yaje baya zaman 30minutes yake fitowa. Abie dai ya kasa hak'uri ya tambayi Momma, saita cemasa wani aikine zasuyi a Nigeria gameda Company d'insu, kuma shi aka d'ora akan aikin, shiyyasa yakeson tattara komai wajen mutanansa nanan.
Abie yace, “to ALLAH ya taimaka, yabada nasara fiye da wanda ake tsammani”.
Momma taji dad'in wannan addu'ar, dan haka ta amsa da “Amin” cike da fara'a.
A kwana Na uku Galadima bai samu damar tafiyarba dai, saboda bai kammala uzirorinsa ba, dole ma zai k'ara koda kwana biyune.
Sauban harda rawa dan dad'i, dan shifa bason zaman masarautar nan tasu yakeba🤥.
Yauma a gajiye ya dawo gidan, kallo d'aya zaka masa ka fahimci hakan ko a yanayin tafiyarsane da fuskarsa datai cinkus babu walwala, hannu kawai ya d'agama su Samha dake falo suna gaidashi, harya 6acema ganinsu daga hawan benan idonsu Na kansa, tausayinsa ya kamasu, shidai yana shiga tun a falo yafara zame green jacket d'in dake saman kayansa, ya k'arasa cikin bedroom d'in yana jefa rigar saman sofa da furzar da huci, freight ya bud'e ya d'auki ruwa, batareda kofiba yahau shan kayansa, tas ya shanyeshi ya jefar da robar yana had'iye wanda ke gumtse a bakinsa, sannan ya k'arasa bakin gadon ya zauna ya dafe kansa, tsawon mintuna uku yana a haka shiru, har wayarsa tafara wringing amma bai kulaba, saida aka kira kusan sau uku sanannan yama kalli wayar yana k'aramin tsaki, kamar bazai d'agaba amma saiya d'auki wayar tana gab da tsinkewa, kafin yay picking call d'in ta tsinke. Kiransa yayi dan Nuren ne.
Bugu d'aya Nuren ya d'aga, bayan sun gaisa yake sanar masa yarinyar minister ce batada lafiya, kuma ya lura yarinyar kamar tanada Asthma ma ne.
“Asthma? to miye ya tada ciwon nata? naga dai ba wani Abu dazai iya shafar tashin ciwon nata a gidan?”.
“hakane Brother, wlhy muma bamusan daliliba”.
“Toni yanzu daka kirani mizan muku ina nan?, kufita ku nema mata magani mana”.
“Muftahu ya tafi, dama na gaya maka ne ka Sani kawai”.
“okay. ALLAH yabata lafiya to. Ya maganar Harun?”.
“Sunan sun baza cigiyarsa gidajen redio shida Alhaji Darma, kaga yanda kuwa suka gama rikicewa, da farko sunce yayi Accident shida driver d'insa amma anrasa inda yake shi, to inaga ko driver n ya dawo hayyacinsa ne ya sanar musu shikad'ai yay Accident d'in oho, jiya dai saiga wata sanarwar suna fad'in anyi Garkuwa da shine tunkan accident d'in, amma har yanzu ba'a nemi kud'in fansaba, dan kidnappers d'in basuce komaiba”.
Galadima yay murmushin gefen baki yana susar gashin girarsa a hankali, yad'an cije lips yana fad'in “toko zaku saka kud'ine marayu su sami na abinci da kud'in makaranta”.
Dariya Nuren ya kwashe dashi, yace, “dan ALLAH da gaske kake brother”.
Kwanciya Galadima yayi yana fad'in, “kai d'an air wasa nakeyi”.
Nuren yay kwafa, “wlhy da ace gaske kakeyi Kansan ALLAH saina k'ure dukiyarsa sannan, nakuma rud'asu da cewar ya fad'amin wani sirri, idan basu biyaba zan tona”.
“ALLAH ya shiryeka to”. Galadima yafad'a yana kuma tashi zaune.
“Amin”. Nuren ya amsa.
“Wai anya kuwa zaka shigo yau d'in?”.
“No, maybe ma sai nanda kwana biyu ko uku, bangama hidimomina ba, kudai kuci gaba da kulawa...”.
K'it ya yanke wayar batareda jiran abinda Nuren zai ceba.
Takalminsa ya cire da kayan ya shiga wanka, yad'an jima sannan yafito d'aure da towel ya yafo wani a jikinsa, ya zauna saman sofa yana d'aukar wayarsa, number d'inta ya lalubo, sai kuma ya kasa kira ya kurama number ido kawai, tun randa suka iso hakanne ke faruwa, saiya d'auki wayar kamar zai kira saiya fasa, gashi yanason jin Yaya yaransa da jikin Abdurraheem, ya danna kiran yana cizar lips d'in nasa daya zame masa jiki🙄😏.
_______________
Muna zaune a d'akin mu ni da Ayusher, Feena da sukazo, tirene a tsakkiyarmu munacin d'an wake da Maman yaa Hameed tayi yau dan aikintane, wayata na hannun Feena tana kallon pictures kiran ya shigo, kallona tayi ta kalli wayar ta kwashe da dariya tana mik'omin.
Muduka kallonta mukayi da mamaki, na kar6i wayar ina fad'in, “kekam kokin fara zarewane?”.
Bata bani amsaba, saima dariyarta take cigaba dayi, na kalli wayar nima, a dai-dai nan kiran ya tsinke, sunan mai kiranne ya d'auki hankalina, *_“Rabin raina!”_* na fad'a a saman lips, ni dai banyi saving number kowa hakaba, yanzu na fahimci abinda yabama Feena dariya kenan.
Daga can Galadima yay tsaki, yana jefar da wayar ya mik'e zuwa gaban mirror, saidai kuma zuciyarsa takasa hak'ura, sukda haushin kansa da yakeji na kiranta da yayi, to amma ai dan yaransama yayi, shine zatak'i d'aga masa waya? zuciyarsa tace idan kuma bata kusafa? Kokuma yaran ne suka d'auke mata hankali da kuka.
Iska ya furzo daga bakinsa, dan tuna hakan zata iya yuwuwa kuma, saiya mik'e ya d'auki wayar, lallai yau Munaya takafa tarihi a rayuwarsa, ko Momma idan yay mata kira d'aya bata d'agaba yakan hak'ura saita kirashi, inhar baya mantaba baita6a kiran
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5 Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39