na manya, cikin jinjina kai ya ajiye k'aramin mug d'in hannunsa mai k'yau yana fad'in “ALLAH ya taimaka, Maybe kana dawowa nima zanje insha ALLAH”.
Galadima yace, “ALLAH ya kaimu”.
Daga nan sund'an cigaba da ta6a hira, a haka jakadiya ta shigo nemawa matawalle iso, yabada izinin a shigo dashi. bayan shigowarsa da yin gaisuwa sai suka d'ora hirar su uku gwanin sha'awa da birgewa. da Wanbai yazo gaida Sarki jakadiya ta sanar masa ai Galadima da matawalle suna ciki, shi komawa yay wai yafasa gaisuwar, jakadiya ta ta6e baki tana 6azgar goro da fad'in “kaikuma kasani gwandararren banza, kai koma y'ar k'autarnan ta jinin girma ba iyawa kaiba, dakasha kanu da sirrika a wajena wlhy”. duk a hankali take maganar yanda kowa bazai jitaba🤣.

Saida gari yay tangaran da haske sannan Galadima da matawalle suka fito, suka bar Sarki zaiyi shirin zuwa fada.
Koda Galadima ya dawo sashensa wajensu Munaya ya nufa, saboda jiyo kukan yaransa.
Ya iske Ashe wanka ake musu, Munaya kuma tana wankan itama, sai Samha da Sauban keta faman jijjigarsu a kafad'a, Abdurrahman kuma yana hannun laraba tana masa wanka. duk gaidashi suka shigayi, ya amsa musu cikin jinjina kai da lumshe ido, baki kam ko motsi bai yiba. Samha ta kawo masa Amaturrahman dake hannunta, bai d'auketa ba, ya dai shafa kumatun yarinyar yana murmushi, sai tayi shiru tana kallonsa kaikace tasan wanene.
Murmushinsa ya fad'ad'a yana jan d'an hancinta.
Samha tace, “Uncle Sam ALLAH Amaturrahman tafi su Abdurraheem wayo, shiyyasa nafi ji da ita”.
Murmushi yakumayi, ya shafi muskar Samha itama tareda d'an bubbugawa, hakan ya sakata fahimtar yau babu y'an maganar a kusa. Saima ya juya yay ficewarsa abinsa daga d'akin.
d'akinsa ya koma ya sake wanka da shirin fita cikin wani d'anyen boyal fari tas, anmasa surfani da golden color sai walk'iya yake da d'aukar idanu, takalmansa na ainahin masu sarauta half cover da lankwasarsu a gaba suma fari da kwalliyar Golden d'in, ya matsa gaban Mirror yana kallon kansa da d'aura a gogo, ganin komai dai-dai ya d'auki turarensa ya fesa kala-kala sannan ya zuba wayoyinsa a aljihu da d'aukar links d'in hannun rigar yafice yana k'ok'arin sakawa.
Da Sauban sukaci karo, yabisa da kallon birgewa, kai manyan kaya na matuk'ar k'awata k'yawun dirin yayansa, kuma sai akayi sa'a yana masifar sonsu, Dan ko'a India yakan sakasu fiyeda k'ananum kaya ko suit.
Zungurinsa galadima yayi yana fad'in “baka sanni bane?”.
Ajiyar zuciya Sauban ya sauke, yana sosa k'eya, “Yaa Sam please one pic.. Mana”.
Galadima ya hararesa zai cigaba da tafiya, da sauri Sauban yakuma had'e hannanyen sa alamar rok'o.
Galadima yay guntun tsaki, “kaiwai shin mikake da hotone? kullum baka gajiya da tarasu”. ya k'are maganar yana d'an dafe goshi.
Shidai Sauban ya marairaice, babu yanda Galadima ya iya dole ya yarda yamasa hoton, harda zuwa sukayi tare. Shidai Galadima ya girgiza kai kawai ya nufi sashen Munaya.
Ya isketa taci gayunta cikin doguwar riga ta popul d'in material, tayi d'as da ita, bazaka ta6a kallonta kace itace da yara uku ba, tana zaune tana bama Abdurraheem nono, sauran kuma suna hannun Samha, laraba tafita..
Zama yay kusada Munaya ya kar6i sauran yaran a hannun Samha, ya d'an rankwafa kan Munaya yana kama hannun Abduraheem data cire a nono ta gyara rigarta, da sauri ta d'ago tana kallonsa da mamakin koya manta Samha na d'akin dazai wani shige mata, shima kallonta yayi yana d'age gira d'aya fuska babu walwala.
Hakan kam saiya bama Samha damar yimusu hoto jiki na rawa, Dan ba k'aramin bada kala sukayiba😘.
Hasken camera d'in ya saka su d'agowa duk suka kalleta, wani ta sake k'yastawa ta fita da gudu.
Munaya ta saka hannu tana toshe bakinta saboda dariyar dake Neman kufce mata, shikam kwafa yay yana fad'in “zan kamaki ne Dan k'aniyarki, yara duk sunbi sun rainani”.
Dariyar Munaya ta fito Dan takasa rik'eta, hararta yayi dukda dariyar tata tamasa k'yau, yad'an rankwasheta akai, “kece kika sakasu ko? dama ai Sauban shima titsiyeni yayi”.
Daina dariyar tayi ta turo baki gaba tana tsafa inda ya rankwasheta, “yoni mizanyi da wani hotonka malam”.
“waya Sani ko sokike ki mallakeni”.
Baya Munaya tayi tana kallonsa, ya wani basar tamkar bashine yay maganarba, ya hauma yaransa wasa dukda basusan mima yakeyiba.
Dan gwarar da Abdurraheem tayi gefensa tana mik'ewa, “Humm, ko inason mallaka bazan mallaki abinda bai minba”.
Yi yay tamkar bai jita ba, yabama yaransa gaba d'aya hankalinsa.
Munaya taji haushin k'in kulatan da yayi, yakai mintuna 30 a d'akin kafin yay kissing kumatunsu ya ajiyesu. inda Munaya take tsaye jikin mirror tana kallonsu ya nufa ta d'auke kanta tana maidawa gefe.
Gabanta ya tsaya daf har tanajin hucin numfashinsa, hannunsa duka cikin aljihun rigar boyal d'insa 3Quarter, “Na dawo gareki, idan kin Isa maimaita abinda kika fad'a”.
Tasan halinsa da makomar maimaicin, shiyyasa ta ta6e baki tana cewa, “aini ba'a sakani abinda ban niyaba”.
Bakinsa ya ta6e yana murmushin gefen baki, “matsoraciya kawai”. yafad'a yana juyawa zai fita, saida yaje bakin k'ofa sannan ya kalli agogonsa, “kuzama a shiri, dana dawo....”. Bai k'arasa ba yay ficewarsa.
Da mamaki Munaya tace “daka dawo? To daka dawo za'yi mi?”. Batada mai bata amsa dan haka ta share ta koma kusada yaran.

Da hanzari Su sarkin Mota suka mik'e, aka bud'e masa mota ya shiga, sashen da aunty Mimi take suka fara zuwa, ya shiga Dan yasan tana nan tanajin haushinsa akan fitar jiya.
Aiko a falo ya isketa zaune a dining tana breakfast, hadimanta nata kaikawon gyara 6angaren, dining d'in ya nufa yaja kujera ya zauna, idonsa a kanta, ta shareshi tamkar batasan dashiba, shima baice uffanba ya d'auki spoon ya saka a plate d'in da take cin Arish, harararsa tayi, shima ya rama yana ta6e baki da basarwa ya cigaba da cin Arish d'in hankali kwance.
Kallonsa ta tsaya yi kawai da mamaki, takai hannu ta daki damtsen hannunsa, shafa wajen yayi yana bud'e baki, saikuma ya kwa6e fuska alamar shagwa6a.
Dariya Aunty Mimi tayi tana sake dukansa da fad'in “kadai girma rigimamme”.
Yay Murmushi tareda kwantar da kansa gefen kafad'arta, a hankali yace, “kin daina fushin dani to? kinsanfa babbar ya uwa”.
Murmushi tayi itama, ta shafa kansa tana fad'in “bazan iya fushi da kaiba ai my k'ani”.
Yace, “Nagode Auntyna”. yafad'a yana tashi zaune sosai.
Mug d'in tea d'in hannun ta ta mik'a masa, ya girgiza kansa.
Tace, “miyasa?”.
Iska yad'an furzo daga bakinsa, yace, “K'anwarki tamin d'ura tunda asuba Dan mugunta”.
Aunty Mimi tayi dariya, “'Dan rainin wayo, inama laifin daka samu mai maka d'urar, kama tunamin, Yaya maganar tafiyarta gida?”.
Saida ya rage fara'a sannan yace, “mungama magana da mai martaba” ya kalli agogonsa da cigaba da fad'in “yanzu zand'anje wani waje, insha ALLAH zuwa 2 to 3 zan dawo, basai yamma bane?”.
“To Alhmdllh, naji dad'i da mai martaba yasa baki, dan da wannan taurin kan naka bazaisa ka saurari kowaba”.
Mik'ewa yay yana ta6e baki, tareda cewa nayi nan, saina dawo, kudai zama cikin shiri jirgin 7:30pm zamubi”.
“ALLAH ya tsare ya bada sa'a”.
“Amin” ya amsa yana ficewa.
Aunty Mimi tayi murmushi da binsa da kallo, tana tausayin k'aninta da gwagwarmayar rayuwa ta zauna jiransa tunkan yazo duniya, ALLAH dai ya kawo iyakar komai dan shima yasamu kwanciyar hankali.


Nace, “amin aunty Mimi mu😘👍🏻”.



*******************

Koda Galadima ta fita waya ya kira, Wanda suke wayar ya tabbatar masa k'arfe 11:00 dai-dai Alhaji Shehu Darma zaibar gidansa.
Galadima yay murmushi, sannan ya kalli sarkin mota.
“Baseer!”
Sarkin mota ya amsa da “na'am Ranka ya dad'e”.
Kwantar da kansa yay jikin seat d'in yana cewa “Zamu banbanta tafiya dasu, dan haka a plaza zamu kar6i mota hannun Saleem, da ita zamu samu Shehu, itace irin motar dazai shiga”.
Cikin mamaki Sarkin mota yace, “Amma ranka ya dad'e ta Yaya? Kasanfa yanada bodyguards kuma masu had'ari”.
Murmushi Galadima yay yana d'agowa, yace, “Duk had'arinsu Muhammad Sameer Saifudden yafisu, kaidai yi abinda nace”.
Da to kawai sarkin mota ya amsa cikeda girmamawa................✍🏻



😨🙆🏽Galadima ma yazama kidnapper, readers saiku kiyaye⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀⛹🏻‍♀🤣.


_Masu nemo picture's d'in mutane suna cewa wane da wane canta matse muku, nidai banyi cover d'in RAINA KAMA ba, sannan ban fad'i kamannin mutum ko guda d'aya a buk d'inaba balle mutum yace na siffanta da Wanda kuke yawo dashi, naga wasu suna fad'ar duk maganar datazo bakinsu akan hoton babu taunawa, Ku kama kanku bansan rainin hankalinnan, yafara isata hakanan kuma, bazai yuwu kulum ina asarar data da lokacina ba sannan kuzauna kuna yankama mutane magana batare da kun duba cancantar fitarta ba, please ya Isa haka, ya isa Wanda bazai iyaba babu lali babu tilas, idan kungama wannan kunga batakai mukuba saikuma Ku tsokalo wannan, shin wane irin rayuwane hakan dan girman ALLAH🤦🏻‍♀, salon cikin Luke d'auka ko k'alk'yalin duniya?, bazaku ta6a magana akan Abu mai muhimmanci da amfaniba sai Mara amfani._






*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*😭🙏🏼
[7/22, 6:22 PM] Aysha Galadima: *_typing📲_*


💡 *_HASKE WRITERS ASSO....._*


*_♦RAINA KAMA.....!!♦_*
_(Kaga gayya)_



*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*



~BOOK 3~ 👉🏻3⃣ & 4⃣


................Suna Isa plaza Saleem ya fito, dan yana ganinsu ne ta CCTV, Galadima yay k'asa da glass 6angaren da yake, idonsa akan Saleem dake fitowa, ya k'araso yana rissinawa da gaisheshi, hannu kawai ya d'aga masa, Saleem ya mik'a masa key d'in motar yana fad'in “gashi ranka ya dad'e”.
Kansa ya girgiza masa, sannan ya bud'e baki yana fad'in “ai Kaine da kanka zakaja motar, mu zamu bika a bayane”.
Da “to” Saleem ya amsa, ya juya ga motar ya shiga.

Haka suka tafi su Galadima a gaba Saleem nabin bayansu, suna tafiya Galadima nayin waya har suka isa inda aikai musu kwatance, wajen wata ma'aikatane, motocine birjik a wajen, alamun sunada yawa a ciki, daga d'an nesa suka tsaya, kusan mintuna biyar saiga wani dattijo ya fito tsakanin motocin jikinsa na rawa, harya k'araso wajen motar su Galadima idonsa akansa yake, ta window ya lek'o, amma sai Galadima yay masa nuni daya zagaya ya shigo.
Ya zauna a d'arare yana gaishe da Galadima, cikin y'ar sakin fuska Galadima ya gyara zama yana kallonsa, “Baba Rabilu ka kwantar da hankalin, insha ALLAH zaka ku6ta kuma zaka samu y'ancinka, ni namaka wannan alk'awarin, bazaka ta6a taimakona nabari ka wulak'anta ba insha ALLAH, a hankali iyalanka da duk wani dake tare dakai zai fahimci baka mutuba, yanzu mi sukeyi cikin nan d'in?”.
Baba Rabilu ya had'iye yawu, muryarsa na rawa yace, “Ranka ya dad'e ban saniba wlhy, amma abinda na fahimta shine lallai sunfara farga dakai, dan naji jiya mai wani a cikinsu yana waya wai kaima lokaci yayi dazasu maka irinna mahaifinka, dan kana neman zamewa rayuwarsu barazana”.
Murmushi Galadima yayi, yana cije lips, “karka damu baba Rabilu, wannan ai a hannun Ubangiji yake, yanzu dai ga mota nan ankawo, saika kar6a, zakayi gaba, mukuma zamu bika a baya da y'ar tazara, inason kafinma su d'auki hanya komai zai wakana, su Ameer a shirye suke suma”.
“shikenan ranka ya dad'e, ALLAH dai yabamu nasara, kaikuma yabaka kwarin gwiwa da k'arfin zuciyar abinda ka faro, ka ruguza rundunar wad'annan azzaluman da kullum cikin zaluntar bayin ALLAH suke ba a saniba, wasu kuma sunsani tsoronsune ya hanasu magana ko d'aga murya.....”. ya k'are maganar cikin sharar hawaye’.
Shiru kawai Galadima yayi yana kallonsa, shima zuciyarsa sai suya da k'una takeyi, saidai yanata ambatar sunan ALLAH kodan neman sassaunci, ajiyar zuciya ya sauke da furzar da huci, yace “shikenan muje ko, dan zamu iya rasa damarmu”.
Jin jina kai Baba Rabilu Yayi, ya fita yana rufo k'ofar, hawayen da suka cikama Galadima idone ya sakashi d'aukar glasses d'insa ya saka yana had'iye abinda ya toshe mak'oshinsa, yagaji hakanan, buk'atarsa yanzu kawai k'arshen al'amarinnan yazo kowa ya huta, shima ya gina rayuwarsa data y'ay'ansa cikin salama.

Sun isa k'ofar gidan Alhaji Shehu Darma, amma baba Rabilu ya tsayane nesa da gidan, sai motar su Galadima Ce ta k'arasa har gate.
Mai gadi yasan Galadima, dukda bawani zuwa gidan yakeba sosai, dan haka babu wani bincik'e-bincike ya barsa ya shiga.
Gidane babba na alfarma, Wanda kallo d'aya zaka masa kasan lallai an kashe dukiya ta musamman.
Galadima yana zaune a mota bai fitoba, sarkin mota ya fita domin nema masa iso, mintuna dabasu wuce 3 ba saiga P.A d'in Alhaji Darma tare da Sarkin mota, shine ya bud'e ma Galadima mota ya fito yana mai masa barka da zuwa.
Yay masa iso har cikin gida falon Alhaji Darma na saukar bak'i masu muhimmanci. Zamansa babu jimawa aka cika masa gaba da kayan ciye-ciye, kai kace jiranshi suke, motsi Galadima bai yiba balle ya nuna alamar zaici, saima latsa wayarsa kawai yakeyi hankalinsa kwance, ga iskar AC na ratsa ga66ansa, kamar daga sama yaji ance “laaah Kaine a gidanmu yau?”.
Da farko sharewa yay yak'i koda motsawa, mikuma ya tuna saiya d'ago a nutse ya zuba k'yawawan idonsa a kanta, gabansa yad'an fad'i, wannan ai yarinyar da suka ta6a had'uwane a jirgi, sannan itace suka kuma had'uwa a airport har yayma Munaya Abu dantaji haushi, to mitakeyi ana........?
Tunaninsa ya kuma katsewa lokacin da ta tafa hannayenta guda biyu a saitin fuskarsa, firgigit ya dawo hayyacinsa, amma saiya basar kawai ya maida kansa ga wayarsa yana cigaba da danne-danne.
Tana niyyar yin magana saiga Alhaji Shehu ya shigo, Galadima yakuma saita camera d'in wayarsa danya ga yanayin da Alhaji Darma zai shiga idan ya gansu.
Ilai kuwa da mamaki ya kalli yarinyar, ya bud'e baki kamar zaiyi masifa saikuma ya had'iye yana fad'in “kekuma waya kawoki nan Rumaisa?”.
Dariya tayi cikin nuna ita ta6ararriyace zata fara zaro zance ya harareta, sannan ya nuna mata k'ofa da hannu, “wannan ai iskancine, ya za'ayi daga yin bak'o kiwanizo ki tsaya masa akai, kedai uwarki tagama lalataki, ta6ararki tayi yawa w.......”
Katseshi Galadima yay da fad'in Afuwa Alhaji, maybe itama uzurintane ya kawota”.
“Shikenan Sameer, amma abunne babu dad'i ai”.
“babu komai”. Galadima ya fad'a cikin lumshe ido.
Gaisuwa sukayi da tambayar juna Ahali, Alhaji Darma yace, “ina Haneefa? had'uwa tayi wahala, siyasa ta 6oyemu, tunda kunk'i bani dai”.
Murmushi kawai Galadima yay baice komaiba.
Alhaji Darma daduk yakasa nutsuwa da wannan zuwa na Galadima ya mik'e yana fad'in “kad'anci wani Abu Sameer, ina zuwa dan ALLAH”.
Galadima ya jinjina kai kawai, Alhaji Darma na fita ya murmusa, bodyguards biyu da suka shigo tare dashi d'aya ya fita, d'ayan harzai fice saiya dawo baya kad'an, wani Abu ya ajiyema Galadima ya fice shima da sauri.
d'auka Galadima yay ya saka a aljihu, sannan yamik'e alamun shirin tafiya, hakan ya nuna dama can abinda yazo nema kenan. A tsaye Alhaji Darma ya iskeshi, cikin mamaki yace, “Sameer yana ganka a tsayene?”.
Cikin murmushin dole Galadima yace babu komai Alhaji, zan wucene, dama hanyace ta biyo damu, shine nace bara na shigo mu gaisa an dad'e ba'a had'uba”.
“Aiko ka k'yauta, ALLAH dai ya saka da alkairi, ai kafi Haneefa da saitazo k'asar sau nawa bata tuna damuba”.
Nanma dai murmusawa Galadima yayi kawai.
Har harabar gidan Alhaji Darma ya rako Galadima, saida yaga ya shiga mota sannan hankalinsa ya kwanta, ya sauke ajiyar zuciya yana goge zufar fuskarsa data wuya.

Sarkin mota yay murmushi, “Ranka ya dad'e yanzu kam komai ya kammala, d'an shegiyarnan shima yazo hannu”.
Galadima baice komaiba sai ciza lips kawai da yayi. Guri suka kuma samu
Showing 3001 words to 6000 words out of 115198 words