kuma bayan ya gama nasa fushin bachi ya sace shi. Ta bangaren Appa ma yadda ya ga rana haka ya ga dare, kwanan Hajiya Kaltume ta bangaren be kuranye masa damuwarsa ba, sai ma ya kasa kwantar daga karshe ya koma falo ya zauna ya kunna Tv sai dai kuma babu mafitarsa a cikin kallon kamar yadda babu shi a cikin bacci sai ma karin damuwa, me yasa ya aikata shi ne abun da ya tsaya masa a rai yake ta tambayar kansa, idan kuma ya tuna da abun da yake ji idan tana gidan sai ya ga kamar yin haka shi ne daidai.
Washe gari da wuri Hajiya Kaltume ta tashi, daman duk ranar girkinta da wuri take tashi ta shirya masa abun karyawa, kasancewar bata da mai aiki tun bayan da ta dauki Iyami aiki ta aure mata miji bata sake yarda ko mai sharar gida ta sake dauka ba, sai dai ta yi komai da kanta ba kamar Momy ba da masu aiki ne suke mata komai sai dai ta ci idan kuma ranar girkinta ne sai dai ta dauki na Appa ta kai masa.
Ko da bakwai ta yi ta gama hada masa ruwan zafin tea da gasa masa bread dan ya fada mata tea kawai zai sha baya son cin komai. Yana shan tea yana hamma saboda bachi da ya gagareshi da dare da alama yana neman fansa a yanzu da safiya.
“Wai dazun ina barin bangarenka Hajiya Fatee ta kira ni”
Ya dan juyo kadan yana kalleta alamar ina saurarenki.
“Wai danta Fadeel ya samu tsabani da matarsa shi ne take son na zo”
“Allah ya kyauta...”
Yadda ya amsa mata ya karantar da ita izinin zuwa ne, daman kuma ta san ba zai hanata ba.
“Ameen zaman auren ne na su, zaman lafiya ta gagara Allah ya shirya tsakaninsu”
Appa dai be sake cewa komai ba, har ya shaye tea ya aje cup be taba bread ba. Hakan kuma be yi ma Hajiya dadi ba domin ta san damuwar ba zata wuce ta ƴaƴan Iyami ba ko kuma ta Iyamin ma gaba daya. Ta dauke cup din ta fita ba tare da ta fada masa yanzu ta tafi ba da safen nan. Ta isa bangarenta rike da cup din. A dinning din da duka matansa suke fara cin karo da shi a kowane falo idan suka fito daga bangarensa ta aje cup din sannan ta nufi dakinta, tana shiga ta raba jikinta da tufafin da ta saka da safen nan ta daura tawul ta shiga bathroom, a gaggauce ta yi wanka gudun kar ta yi latti sanin cewar inda za su je kaune dake gaba daji baya daji. Ko da ta fito ta samu Khairi zaune akan gadonta fuska a kumbure musamman bakinta.
“Ba laifin Ya Yasir ba ne Hajiya, laifin Appa ne yana mugun son yarinyar nan, ya fi kaunarta da duka sauran ƴaƴansa, dubi yadda ransa ya bace saboda na fada mata gaskiya bayan kuma gaskiyar ce”
“Hmmm ai ni ganin nake kamar ba banza uwar yaran nan ta bar Alhaji ba, ita kanta ai ba a banza ta aure min miji ba, yanzu kuma saboda yaran nan Allah kadai ya san ran mutun nawa zai ɓace a gidan nan”
“Wallahi sai na rama komai ta dade”
“Toh ki rama dai ta sigar lalama, in ba haka ba Alhaji ko Yasir su ci ubanki kin san jira kawai suke”
Ta tashi ta fice dakin tana wani zakuɗa ita ga balagaggiya. Hajiya ta shirya cikin koriyar Atamfa ta saka farin mayafi ta sauki jakarta mai kala daya da gyalen da kuma talkaminta ta saka sannan ta dauki wayarta ta kira daya daga cikin drivers din gidan ta sanar masa fitarta. Gurin da take aje kudi ta bude ta dauko kudi mai yawa ta zuba a jakarta sannan ta rufe ta rataya jakar ta fito rike da wayarta sai kamshi take zubawa irin na manyan matan masu kudi kuma masu miji da ikon gida.
“Hajiya fita zaki yi?”
Maama ta tambaya.
“Eh wani guri zamu je da Hajiya Fatee”
“Allah ya tsare, Hajiya kin ga yadda Ya Yasir ya fasa bakin Khairi”
“Na gani, ku ma sai kun yi taka tsantsan ai, ni ba dan ubansu daya ba ai sai na tsora ta na ce aurenta yake son yi”
“Lallai ya fi sonta da mu ma”
“Hmmm Allah dai ya kyauta, ki tashi sauran yan 'uwanki kar su yi latti makaranta, ni na fita”
Daga haka ta fice daga falon Maama na yi nata Allah ya tsare. Ko da ta fito direban har ya tashi motar ya juyata tana fuskantar gate domin ya san uwargidan Alhaji Haruna Mai Yadi bata daukar raini. Tana shiga motar be tsaya da ita ko'ina ba sai gidan aminiyarta Hajiya Fatee, yana aje ta ya juya a can ma ba su bata lokaci ba, Hajiya Fatee ta kira direban dake kai su kauyen ta sanar masa sun shirya, ba su yarda su tafi da motarsu ba saboda tsoron masu kidnapping da kuma tonon asiri, sai dai su dauki shatar motar kasuwa ta zo ta dauke su har gidan Hajiya Fatee ta kaisu inda za su je, kasancewarsa mijin Hajiya Fateen ya dade da rasuwa ita kadai ce a katon gidan sai yan matanta biyu da kuma masu aiki da danta Fadeel ya zuba mata.
Misalin karfe tara da rabi na safe suka kama hanyar kauyen gidan zalla dake cikin local government din Kwatarkwashi. Suna tafe suna hira Hajiya Fatee na kara fada mata yadda matar danta Afrah ke son mulkar mata ďa ta saka shi ya manta da ita. Idan ta kai aya sai Hajiya Kaltume ta dauko nata zancen na abun da ya faru tsakaninta da Alhaji a jiya. Sanar da shi da suka yi cewar suna nan tafe ya saukaka musu wucewa kai tsaye dakin da yake gabatar da tsiface-tsifacensa. Sai da ya fara yi musu maraba da zuwa sannan Hajiya Kaltume ta ciro kudi 300k ta aje masa tana masa godiya.
“Aiki yayi Malam, dan haka na zo da kaina na kawo maka goronka, kuma na yi maka godiya”
Malamin da hakoransa ke daskare da jan goro ya yi dariyar jindadi da farinciki ya jinjina kai.
“Hajiya ai na fada miki, indai muka yi aiki ba a dawo mana da shi, kuma kar tunanin kin yi kin yi baki dace ba yasa ki karaya a gurinmu, idan kin ji ana malam anjima da nisa ba ma gobe da nisa ba to kika zo nan kakarki ta yanke saka kawai”
“Na gani ai Malam Wallahi na gode, domin shekara da shekaru ina neman yadda matar nan zata bar min mijina amman abu ya garara sai an yi kamar za a rabu sai kuma ka ga ba rabuwar bace, sai yanzu Allah ya kawo karshen abun, sai dai ko yanzu ni ina jin tsoro domin na lura ya shiga damuwa matuka gaya saboda sakinta da yayi, ina jin kar ya ce zai dawo da ita domin saki daya yayi mata”
“Ina ko alama! Karki damu Hajiya, idan har mutum zai mutu ya dawo to kishiyarki zata dawo gidan, ai farraqu muka musu ita tana gabam yana yamma har abada ba zama a tsakaninsu”
Wani kalar dadi ya lullube Hajiya Kaltume.
“Haka nake so, kuma ina son a koya mata hankali so nake ka yi mata wani aikin da ba zata sake aure ba har abada, tun da ta zabi kishi da ni to ko bayan ta bar gidan mijina sai ta dandana bakincikin da nadanar auren Alhaji da ta yi, sannan be sake ta sai da ya damka mata kudi har miliyan asirin, Malam ina son a lalata duniyar da ya bata, har da gidan da ya mallaka mata idan akwai yadda za'ayi a ruguza gidan ko ma ya karbe abunsa, kuma a daureta ko kare kar ya sake sha'awarta balle har ta yi aure”
“Wato so kike a lalata duniyar da ya bata, ba wadda ya bata kawai ba, har tata duniyar da ta mallaka za a iya lalatawa idan kina so”
“Aiko idan ka yi min haka, ina mai tabbatar maka aikin Hajji bana da kai za'ayi, kuma zan maka kyautar kudi har naira miliyan daya”
Malamin ya sake yin dariya yana gyara babbar rigarsa.
“Hajiya na miki alkawari akaifa kishiyarki ba zata sake amfana da ita ba, ba duniyarta ko ta mijinki da ya bata ba, har dukiyar wani idan ya dauka ya bata ba zata taba amfanarta ba, ita da aure ko sai lahira idan ana yi, kuma yadda ba a mutuwa a dawo haka ba zata sake dawowa a gidan mijinki ba”
“Alhamdulillah”
Hajiya Kaltume ta fada tana daga hannu sama ta yi ma Allah godiya, sannan ta kalli Hajiya Fatee suka taba suna dariya. Daga bisani Hajiya Fatee ta kora masa da nata bayanin.
“Malam nima da tawa mtsalar na zo yau, suruka ce ta saka ni a gaba, ta mallake min ďan yaki ya kara aure kuma baya jin maganar kowa sai ta matarsa, ga kudi yana da shi amman ko kyauta zai yi sai abun da ta so yake bayarwa, ni so nake a raba su ya sake ta saki uku idan da dama”
Malamin ya amsa mata da kai.
“Ya sunanta, ya kuma sunan ďanki?”
“Afrah ake kiranta, shi kuma Fadeel”
Ya dauko kasa dake cikin farantin katako ya dora a cinyarsa yayi zane zane ya jinjina kai ya dago ya kalli Hajiya Fatee.
“Lallai sai kin tashi tsaye, ta mallaki danki Mallaka bata wasa ba, kuma idan ba ki yi da gaske ba abu ne mai wahala ya sake yin aure ko da kuwa ta mutu”
“Ka ji irinta ba, shedaniyar yarinyar na sha wahalar yarinyar da can babu ruwansa da ni ma, sai da na tashi tsaye, dan abun da ubansa ya bar min duk a can ya kare, ba dan Allah yasa nasa gadon yayi albarka kuma ya samu babban aiki ba da yanzu mun kade”
“Toh lallai dai gata nan ko yanzu a tsaye take akan danki”
“Dan Allah a zaunar da ita, idan da dama ma a kwantar da ita a saka ta bacci ko a sumar da shegiya”
Malamin yayi dariya
“Ai tun da kika zo nan komai zai zama tarihi Hajiya, ki bada kudin karan alkamin kawai a saka aiki”
Da sauri ta bude jakarta ta dauko kudin da ba zai wuce 30k ba ta aje masa.
“Ga wannan ban zo da kudi mai yawa ba, amman dai a fara saka aiki da wannan idan zan dawo zan ciko jaka da yardar Allah”
“Toh shi ke nan ba matala idan na gama aiki na hada abubuwa zan kira na fada muku sai ku zo ku karba ko kuma ku aiko ko kuma ni da kaina na aiko muku”
A bisa wannan suka yi masa sallama suka fito suka dawo cikin motar. Direban ya a kama hanya, ba su yi nisa da garin ba suka rage gudu ganin an tsayar da motocin dake gabansu a zatonsu sojoji ne, hankalinsu be tashi ba sai da suka fara jin harbe harbe wasu na ihu.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un Bandits ne”
Direban ya fada, da sauri Hajiya Fatee ta kalli Hajiya Kaltume da cikinta ya soma murdawa.
“Mun shiga uku mun lalace, ya zamu yi?”
“Shiyasa bana son shigowa dajin nan gari gaba daya ya lalace a yanzu”
Cewar Hajiya Kaltume ido na raina fata.
“Kai direba ya zamu yi?”
“Hajiya ni ba ku kuka kawo ni nan ba, kuma gashi motoci a bayanmu balle mu juya”
Maganar yake yana leken motocin dake bayansu ga karar bindigar sai matsosu take.
“Toh ko dai mu kira Malamin nan mu fada masa”
Hajiya Fatee da fitsari ya fara zubo mata ta kalli Hajiya Kaltume.
“Ya mana me? Soja ne shi ko dan sanda?”
“Ya turo aljannu su dauke mu mana, Hajiya mutanen nan suka kama mu ai mun shiga uku, kuma na cewa Alhaji me? Daga zuwa sulhun aure!”
Cikin tashin hankali Hajiya Fatee ta ce
“Aljannu suka dauke mu ai shikenan mun bar duniya kuma kara ma wadannan da aljannu dan su kai mu za su inda babu kowa su aje, ko su kai mu China aljanni ai ba zai dauke ka ya aje ka nan kusa ba sai wata duniyar”
Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana neman agajin Allah.
“Allah ka yafe mana Allah ka dube mu Allah Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, ni har na bata zane”
Direba ya bude kofar a hankali ya sulale ya yanki daji cikin ciyayi. Hajiya Kaltume ta saka kalma shada, Hajiya Fatee ta kama mata suka karasa suka kallon juna kowacce na kai hannu ta taba yar'uwarta. domin sun san yadda suka ci suka koshi nan ba za su iya gudu ba ko sa sun gwada hakan.
____________________
Hmmmmm masu karatu kun taba gani ko jin mugun kishi da bakar hassada irinta ta Hajiya Kaltume?
Ni dai Hurriya ta ba ni tausayi domin rayuwa gurin da baka bukatarka yana da wahala, musamman idan babu uwa a kusa.
Ta wani bangaren kuma Iyami tana da laifi daga zuwa aiki sai ki aure mijin mata? Ina laifi ki rumgume talaucinki ki shafawa kanki lafiya, yanzu wa gari ya waya...?
Mu hadu da ku page din gobe, amman kamin nan ina son na ga Comments baza-baza line by line in ji Bature...
[10/18, 5:35 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 7️⃣
Ana kiran sallah asuba ta sauko daga kan gadon ta nufi kofar dakinta ta bude ta fito, a hankali ta sauko downstairs, tana isa bakin kofar falon bata tsaya komai ba ta kai hannu zata bude kofar.
“Ina zaki je?”
Ta juyo da sauri domin bata yi tsammanin wani zai iya fitowa at this early ba.
“Fita zan yi”
Ta amsawa Namra. Cikin mamaki Namra ta wara ido.
“Asuba ne fa”
“Na sani, Hijab zan dauko na yi sallah”
“Haba Hurriya shiga dakina ki dauko nawa mana, saboda Hijab sai ki fita tun a asuba ki koma part dinku kamar wata bakuwa, ke a gida kike fa”
Hurriya ta dan sauke kai kasa daga barin kallon yayarta wadda ta bata shekara uku da haihuwa. Namra bata sake ce mata komai ta nufi kujerar da ta zauna a jiya ta dauki agogonta da assignment din da ta yi, sai da ta kusa hayewa sannan Hurriya ta rufa mata baya, cikin ladabi da natsuwa ta shiga dakin Namra ta tsaya jikin kofa, haka Hurriya take bata sakewa da mutane tana da wahalar sabo, musamman idan ta san zaka tsangwame ta ko ka yi mata fada. Namra ta juyo ta jefo mata hijab din cikin hanzari Hurriya ta cafke.
“Akwai carpet din Sallah a can?”
“Aa babu”
Namra ta dauki nata ta jefa mata Hurriya ta sake cafkewa ta juya ta fice daga dakin zuwa dakinta. Bata shiga nata dakin ba sai da ta kwankwasa kofar dakin Hamad tana kiran sunansa.
“Na tashi”
Ya amsa mata daga can ciki, sannan ta wuce dakinta ta maida kofar ta rufe. Tun bayan da ta yi Sallah bata sake fitowa ba sai da ta auna lokacin makaranta yayi mata, sannan ta bude kofar a hankali kamar wata bakuwa ta rufe ta nufo hanyar saukowa kasa gabanta har faduwa yake kar ta hadu da Musib ko dan'uwansa Miwan balle kuma Momy da ta san bata ishe ta kallo ba. Sai dai ta yi rashin sa'a Momy da duka yaranta suna falon zaune, abun da bata saka tsammani ba domin Momy bata tashi da wuri sai idan tana bangaren Appa shi ma da zarar ta kai masa abun karyawa zata sake komawa bachi kuma babu mai tashinta sai gidan maigidan ne da kansa if not kowaye ya tasheta zai gane kurensa a ranar.
“Baka fada min zaka zo ba, ai da na saka an shirya mana abinci mai kyau”
Cewar Momy tana kallon kyakkyawan saurayin dake zaune a kujerar dake facing nata, kyakkyawan saurayin farin saurayin mai jini a jika ya girgiza mata kai yana duba agogo hannunsa.
“Noo Momy na gode tafiyar ta gaggawa ce, yanzu zan kama hanya, kawai na ce bari na biyo mu gaisa ne”
Momy ta yi murmushin kasaita irin na manya mata.
“Daman na sani, abinci idan ba na Hajiya Turai baka ci na kowa”
Ya dan fadada fuskarsa da murmushim da ya kara masa kyau da haiba yana daga kai ya kalli Hurriya dake saukowa. Momy ta dan juya ta kalleta kadan ta dauke kai irin ba ki isheni kallo ba din nan.
“Momy ina kwana”
Hurriya ta gaisheta cikin ladabi Momy har ta yi kamar ba zata amsa ba sai kuma ta ci albarkacin bakonta amsa ciki ciki kamar an mata dole.
“Yaya Musib ina?”
Ya amsa, ta juya gurin dan'uwansa shi ma ta gaishe shi, sai ya amsa mata fuska a sake kamar dan'uwansa, ta kalli Namra ta gaishe ta kamin ta rufe baki Namra ta amsa tana mata an tashi lafiya, daga karshe Hurriya ta cike gaisuwarta da bakon da take kyautata zaton yana da muhimmanci a gurin Momy da yaranta ganin yadda suke ta murna da ganinsa kuma suka fito dukansu da sanyin safiyar nan suka zauna a falo just because of him.
“Ina kwana”
Ya d'auki 'yan dak'ik'u kafin ya amsa gaisuwarta, shi ma kuma ba da baki ba kai kawai ya daga mata and light smile. Binta yayi da kallo har ta wuce ta gabansa ta nufi kofar fita.
“ƴar Mijina ce, kanenta ne ka ga ya fita dazun”
Momy ta fada masa domin ta san ba zai tambaya ba, ta san kallon da yake mata be wuce na neman sanin wacece ba, dan zuwan da yake gidan jefi jefi be taba ganinta ba, haka ma bata yi masa kama da masu aikin Momy ba balle yace ko yar aiki ce, ba zai ce ya san kowa a gidan ba, amman yadda ya san familynsu musamman Momy idan har ta bawa wani damar shiga ma a falonta to yana da muhimmanci a gareta, sai dai abun da be sani ba wannan shigar ta dole ce ta cilastawar Appa ba dan Hurriya tana da muhimmanci a gareta ba.
“Yaya ance an daga bikinka”
Miwan ya tambaya yana kallonsa. Mutumen da Miwan ya kira da Yaya ya juyo ya kalleshi.
“Ka aje wannan Yaya aside ka kira ni da real sunana Jamal”
Momy ta yi murmushi mai sauti.
“Haba dai Captain dukansu fa
Showing 18001 words to 21000 words out of 46312 words
Washe gari da wuri Hajiya Kaltume ta tashi, daman duk ranar girkinta da wuri take tashi ta shirya masa abun karyawa, kasancewar bata da mai aiki tun bayan da ta dauki Iyami aiki ta aure mata miji bata sake yarda ko mai sharar gida ta sake dauka ba, sai dai ta yi komai da kanta ba kamar Momy ba da masu aiki ne suke mata komai sai dai ta ci idan kuma ranar girkinta ne sai dai ta dauki na Appa ta kai masa.
Ko da bakwai ta yi ta gama hada masa ruwan zafin tea da gasa masa bread dan ya fada mata tea kawai zai sha baya son cin komai. Yana shan tea yana hamma saboda bachi da ya gagareshi da dare da alama yana neman fansa a yanzu da safiya.
“Wai dazun ina barin bangarenka Hajiya Fatee ta kira ni”
Ya dan juyo kadan yana kalleta alamar ina saurarenki.
“Wai danta Fadeel ya samu tsabani da matarsa shi ne take son na zo”
“Allah ya kyauta...”
Yadda ya amsa mata ya karantar da ita izinin zuwa ne, daman kuma ta san ba zai hanata ba.
“Ameen zaman auren ne na su, zaman lafiya ta gagara Allah ya shirya tsakaninsu”
Appa dai be sake cewa komai ba, har ya shaye tea ya aje cup be taba bread ba. Hakan kuma be yi ma Hajiya dadi ba domin ta san damuwar ba zata wuce ta ƴaƴan Iyami ba ko kuma ta Iyamin ma gaba daya. Ta dauke cup din ta fita ba tare da ta fada masa yanzu ta tafi ba da safen nan. Ta isa bangarenta rike da cup din. A dinning din da duka matansa suke fara cin karo da shi a kowane falo idan suka fito daga bangarensa ta aje cup din sannan ta nufi dakinta, tana shiga ta raba jikinta da tufafin da ta saka da safen nan ta daura tawul ta shiga bathroom, a gaggauce ta yi wanka gudun kar ta yi latti sanin cewar inda za su je kaune dake gaba daji baya daji. Ko da ta fito ta samu Khairi zaune akan gadonta fuska a kumbure musamman bakinta.
“Subhanallahi haka Yasir ya fasa miki baki saboda yar iskar yarinyar nan?”
“Ba laifin Ya Yasir ba ne Hajiya, laifin Appa ne yana mugun son yarinyar nan, ya fi kaunarta da duka sauran ƴaƴansa, dubi yadda ransa ya bace saboda na fada mata gaskiya bayan kuma gaskiyar ce”
“Hmmm ai ni ganin nake kamar ba banza uwar yaran nan ta bar Alhaji ba, ita kanta ai ba a banza ta aure min miji ba, yanzu kuma saboda yaran nan Allah kadai ya san ran mutun nawa zai ɓace a gidan nan”
“Wallahi sai na rama komai ta dade”
“Toh ki rama dai ta sigar lalama, in ba haka ba Alhaji ko Yasir su ci ubanki kin san jira kawai suke”
Ta tashi ta fice dakin tana wani zakuɗa ita ga balagaggiya. Hajiya ta shirya cikin koriyar Atamfa ta saka farin mayafi ta sauki jakarta mai kala daya da gyalen da kuma talkaminta ta saka sannan ta dauki wayarta ta kira daya daga cikin drivers din gidan ta sanar masa fitarta. Gurin da take aje kudi ta bude ta dauko kudi mai yawa ta zuba a jakarta sannan ta rufe ta rataya jakar ta fito rike da wayarta sai kamshi take zubawa irin na manyan matan masu kudi kuma masu miji da ikon gida.
“Hajiya fita zaki yi?”
Maama ta tambaya.
“Eh wani guri zamu je da Hajiya Fatee”
“Allah ya tsare, Hajiya kin ga yadda Ya Yasir ya fasa bakin Khairi”
“Na gani, ku ma sai kun yi taka tsantsan ai, ni ba dan ubansu daya ba ai sai na tsora ta na ce aurenta yake son yi”
“Lallai ya fi sonta da mu ma”
“Hmmm Allah dai ya kyauta, ki tashi sauran yan 'uwanki kar su yi latti makaranta, ni na fita”
Daga haka ta fice daga falon Maama na yi nata Allah ya tsare. Ko da ta fito direban har ya tashi motar ya juyata tana fuskantar gate domin ya san uwargidan Alhaji Haruna Mai Yadi bata daukar raini. Tana shiga motar be tsaya da ita ko'ina ba sai gidan aminiyarta Hajiya Fatee, yana aje ta ya juya a can ma ba su bata lokaci ba, Hajiya Fatee ta kira direban dake kai su kauyen ta sanar masa sun shirya, ba su yarda su tafi da motarsu ba saboda tsoron masu kidnapping da kuma tonon asiri, sai dai su dauki shatar motar kasuwa ta zo ta dauke su har gidan Hajiya Fatee ta kaisu inda za su je, kasancewarsa mijin Hajiya Fateen ya dade da rasuwa ita kadai ce a katon gidan sai yan matanta biyu da kuma masu aiki da danta Fadeel ya zuba mata.
Misalin karfe tara da rabi na safe suka kama hanyar kauyen gidan zalla dake cikin local government din Kwatarkwashi. Suna tafe suna hira Hajiya Fatee na kara fada mata yadda matar danta Afrah ke son mulkar mata ďa ta saka shi ya manta da ita. Idan ta kai aya sai Hajiya Kaltume ta dauko nata zancen na abun da ya faru tsakaninta da Alhaji a jiya. Sanar da shi da suka yi cewar suna nan tafe ya saukaka musu wucewa kai tsaye dakin da yake gabatar da tsiface-tsifacensa. Sai da ya fara yi musu maraba da zuwa sannan Hajiya Kaltume ta ciro kudi 300k ta aje masa tana masa godiya.
“Aiki yayi Malam, dan haka na zo da kaina na kawo maka goronka, kuma na yi maka godiya”
Malamin da hakoransa ke daskare da jan goro ya yi dariyar jindadi da farinciki ya jinjina kai.
“Hajiya ai na fada miki, indai muka yi aiki ba a dawo mana da shi, kuma kar tunanin kin yi kin yi baki dace ba yasa ki karaya a gurinmu, idan kin ji ana malam anjima da nisa ba ma gobe da nisa ba to kika zo nan kakarki ta yanke saka kawai”
“Na gani ai Malam Wallahi na gode, domin shekara da shekaru ina neman yadda matar nan zata bar min mijina amman abu ya garara sai an yi kamar za a rabu sai kuma ka ga ba rabuwar bace, sai yanzu Allah ya kawo karshen abun, sai dai ko yanzu ni ina jin tsoro domin na lura ya shiga damuwa matuka gaya saboda sakinta da yayi, ina jin kar ya ce zai dawo da ita domin saki daya yayi mata”
“Ina ko alama! Karki damu Hajiya, idan har mutum zai mutu ya dawo to kishiyarki zata dawo gidan, ai farraqu muka musu ita tana gabam yana yamma har abada ba zama a tsakaninsu”
Wani kalar dadi ya lullube Hajiya Kaltume.
“Haka nake so, kuma ina son a koya mata hankali so nake ka yi mata wani aikin da ba zata sake aure ba har abada, tun da ta zabi kishi da ni to ko bayan ta bar gidan mijina sai ta dandana bakincikin da nadanar auren Alhaji da ta yi, sannan be sake ta sai da ya damka mata kudi har miliyan asirin, Malam ina son a lalata duniyar da ya bata, har da gidan da ya mallaka mata idan akwai yadda za'ayi a ruguza gidan ko ma ya karbe abunsa, kuma a daureta ko kare kar ya sake sha'awarta balle har ta yi aure”
“Wato so kike a lalata duniyar da ya bata, ba wadda ya bata kawai ba, har tata duniyar da ta mallaka za a iya lalatawa idan kina so”
“Aiko idan ka yi min haka, ina mai tabbatar maka aikin Hajji bana da kai za'ayi, kuma zan maka kyautar kudi har naira miliyan daya”
Malamin ya sake yin dariya yana gyara babbar rigarsa.
“Hajiya na miki alkawari akaifa kishiyarki ba zata sake amfana da ita ba, ba duniyarta ko ta mijinki da ya bata ba, har dukiyar wani idan ya dauka ya bata ba zata taba amfanarta ba, ita da aure ko sai lahira idan ana yi, kuma yadda ba a mutuwa a dawo haka ba zata sake dawowa a gidan mijinki ba”
“Alhamdulillah”
Hajiya Kaltume ta fada tana daga hannu sama ta yi ma Allah godiya, sannan ta kalli Hajiya Fatee suka taba suna dariya. Daga bisani Hajiya Fatee ta kora masa da nata bayanin.
“Malam nima da tawa mtsalar na zo yau, suruka ce ta saka ni a gaba, ta mallake min ďan yaki ya kara aure kuma baya jin maganar kowa sai ta matarsa, ga kudi yana da shi amman ko kyauta zai yi sai abun da ta so yake bayarwa, ni so nake a raba su ya sake ta saki uku idan da dama”
Malamin ya amsa mata da kai.
“Ya sunanta, ya kuma sunan ďanki?”
“Afrah ake kiranta, shi kuma Fadeel”
Ya dauko kasa dake cikin farantin katako ya dora a cinyarsa yayi zane zane ya jinjina kai ya dago ya kalli Hajiya Fatee.
“Lallai sai kin tashi tsaye, ta mallaki danki Mallaka bata wasa ba, kuma idan ba ki yi da gaske ba abu ne mai wahala ya sake yin aure ko da kuwa ta mutu”
“Ka ji irinta ba, shedaniyar yarinyar na sha wahalar yarinyar da can babu ruwansa da ni ma, sai da na tashi tsaye, dan abun da ubansa ya bar min duk a can ya kare, ba dan Allah yasa nasa gadon yayi albarka kuma ya samu babban aiki ba da yanzu mun kade”
“Toh lallai dai gata nan ko yanzu a tsaye take akan danki”
“Dan Allah a zaunar da ita, idan da dama ma a kwantar da ita a saka ta bacci ko a sumar da shegiya”
Malamin yayi dariya
“Ai tun da kika zo nan komai zai zama tarihi Hajiya, ki bada kudin karan alkamin kawai a saka aiki”
Da sauri ta bude jakarta ta dauko kudin da ba zai wuce 30k ba ta aje masa.
“Ga wannan ban zo da kudi mai yawa ba, amman dai a fara saka aiki da wannan idan zan dawo zan ciko jaka da yardar Allah”
“Toh shi ke nan ba matala idan na gama aiki na hada abubuwa zan kira na fada muku sai ku zo ku karba ko kuma ku aiko ko kuma ni da kaina na aiko muku”
A bisa wannan suka yi masa sallama suka fito suka dawo cikin motar. Direban ya a kama hanya, ba su yi nisa da garin ba suka rage gudu ganin an tsayar da motocin dake gabansu a zatonsu sojoji ne, hankalinsu be tashi ba sai da suka fara jin harbe harbe wasu na ihu.
“Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un Bandits ne”
Direban ya fada, da sauri Hajiya Fatee ta kalli Hajiya Kaltume da cikinta ya soma murdawa.
“Mun shiga uku mun lalace, ya zamu yi?”
“Shiyasa bana son shigowa dajin nan gari gaba daya ya lalace a yanzu”
Cewar Hajiya Kaltume ido na raina fata.
“Kai direba ya zamu yi?”
“Hajiya ni ba ku kuka kawo ni nan ba, kuma gashi motoci a bayanmu balle mu juya”
Maganar yake yana leken motocin dake bayansu ga karar bindigar sai matsosu take.
“Toh ko dai mu kira Malamin nan mu fada masa”
Hajiya Fatee da fitsari ya fara zubo mata ta kalli Hajiya Kaltume.
“Ya mana me? Soja ne shi ko dan sanda?”
“Ya turo aljannu su dauke mu mana, Hajiya mutanen nan suka kama mu ai mun shiga uku, kuma na cewa Alhaji me? Daga zuwa sulhun aure!”
Cikin tashin hankali Hajiya Fatee ta ce
“Aljannu suka dauke mu ai shikenan mun bar duniya kuma kara ma wadannan da aljannu dan su kai mu za su inda babu kowa su aje, ko su kai mu China aljanni ai ba zai dauke ka ya aje ka nan kusa ba sai wata duniyar”
Hajiya Kaltume ta fashe da kuka tana neman agajin Allah.
“Allah ka yafe mana Allah ka dube mu Allah Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un, ni har na bata zane”
Direba ya bude kofar a hankali ya sulale ya yanki daji cikin ciyayi. Hajiya Kaltume ta saka kalma shada, Hajiya Fatee ta kama mata suka karasa suka kallon juna kowacce na kai hannu ta taba yar'uwarta. domin sun san yadda suka ci suka koshi nan ba za su iya gudu ba ko sa sun gwada hakan.
____________________
Hmmmmm masu karatu kun taba gani ko jin mugun kishi da bakar hassada irinta ta Hajiya Kaltume?
Ni dai Hurriya ta ba ni tausayi domin rayuwa gurin da baka bukatarka yana da wahala, musamman idan babu uwa a kusa.
Ta wani bangaren kuma Iyami tana da laifi daga zuwa aiki sai ki aure mijin mata? Ina laifi ki rumgume talaucinki ki shafawa kanki lafiya, yanzu wa gari ya waya...?
Mu hadu da ku page din gobe, amman kamin nan ina son na ga Comments baza-baza line by line in ji Bature...
[10/18, 5:35 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 7️⃣
Ana kiran sallah asuba ta sauko daga kan gadon ta nufi kofar dakinta ta bude ta fito, a hankali ta sauko downstairs, tana isa bakin kofar falon bata tsaya komai ba ta kai hannu zata bude kofar.
“Ina zaki je?”
Ta juyo da sauri domin bata yi tsammanin wani zai iya fitowa at this early ba.
“Fita zan yi”
Ta amsawa Namra. Cikin mamaki Namra ta wara ido.
“Asuba ne fa”
“Na sani, Hijab zan dauko na yi sallah”
“Haba Hurriya shiga dakina ki dauko nawa mana, saboda Hijab sai ki fita tun a asuba ki koma part dinku kamar wata bakuwa, ke a gida kike fa”
Hurriya ta dan sauke kai kasa daga barin kallon yayarta wadda ta bata shekara uku da haihuwa. Namra bata sake ce mata komai ta nufi kujerar da ta zauna a jiya ta dauki agogonta da assignment din da ta yi, sai da ta kusa hayewa sannan Hurriya ta rufa mata baya, cikin ladabi da natsuwa ta shiga dakin Namra ta tsaya jikin kofa, haka Hurriya take bata sakewa da mutane tana da wahalar sabo, musamman idan ta san zaka tsangwame ta ko ka yi mata fada. Namra ta juyo ta jefo mata hijab din cikin hanzari Hurriya ta cafke.
“Akwai carpet din Sallah a can?”
“Aa babu”
Namra ta dauki nata ta jefa mata Hurriya ta sake cafkewa ta juya ta fice daga dakin zuwa dakinta. Bata shiga nata dakin ba sai da ta kwankwasa kofar dakin Hamad tana kiran sunansa.
“Na tashi”
Ya amsa mata daga can ciki, sannan ta wuce dakinta ta maida kofar ta rufe. Tun bayan da ta yi Sallah bata sake fitowa ba sai da ta auna lokacin makaranta yayi mata, sannan ta bude kofar a hankali kamar wata bakuwa ta rufe ta nufo hanyar saukowa kasa gabanta har faduwa yake kar ta hadu da Musib ko dan'uwansa Miwan balle kuma Momy da ta san bata ishe ta kallo ba. Sai dai ta yi rashin sa'a Momy da duka yaranta suna falon zaune, abun da bata saka tsammani ba domin Momy bata tashi da wuri sai idan tana bangaren Appa shi ma da zarar ta kai masa abun karyawa zata sake komawa bachi kuma babu mai tashinta sai gidan maigidan ne da kansa if not kowaye ya tasheta zai gane kurensa a ranar.
“Baka fada min zaka zo ba, ai da na saka an shirya mana abinci mai kyau”
Cewar Momy tana kallon kyakkyawan saurayin dake zaune a kujerar dake facing nata, kyakkyawan saurayin farin saurayin mai jini a jika ya girgiza mata kai yana duba agogo hannunsa.
“Noo Momy na gode tafiyar ta gaggawa ce, yanzu zan kama hanya, kawai na ce bari na biyo mu gaisa ne”
Momy ta yi murmushin kasaita irin na manya mata.
“Daman na sani, abinci idan ba na Hajiya Turai baka ci na kowa”
Ya dan fadada fuskarsa da murmushim da ya kara masa kyau da haiba yana daga kai ya kalli Hurriya dake saukowa. Momy ta dan juya ta kalleta kadan ta dauke kai irin ba ki isheni kallo ba din nan.
“Momy ina kwana”
Hurriya ta gaisheta cikin ladabi Momy har ta yi kamar ba zata amsa ba sai kuma ta ci albarkacin bakonta amsa ciki ciki kamar an mata dole.
“Yaya Musib ina?”
Ya amsa, ta juya gurin dan'uwansa shi ma ta gaishe shi, sai ya amsa mata fuska a sake kamar dan'uwansa, ta kalli Namra ta gaishe ta kamin ta rufe baki Namra ta amsa tana mata an tashi lafiya, daga karshe Hurriya ta cike gaisuwarta da bakon da take kyautata zaton yana da muhimmanci a gurin Momy da yaranta ganin yadda suke ta murna da ganinsa kuma suka fito dukansu da sanyin safiyar nan suka zauna a falo just because of him.
“Ina kwana”
Ya d'auki 'yan dak'ik'u kafin ya amsa gaisuwarta, shi ma kuma ba da baki ba kai kawai ya daga mata and light smile. Binta yayi da kallo har ta wuce ta gabansa ta nufi kofar fita.
“ƴar Mijina ce, kanenta ne ka ga ya fita dazun”
Momy ta fada masa domin ta san ba zai tambaya ba, ta san kallon da yake mata be wuce na neman sanin wacece ba, dan zuwan da yake gidan jefi jefi be taba ganinta ba, haka ma bata yi masa kama da masu aikin Momy ba balle yace ko yar aiki ce, ba zai ce ya san kowa a gidan ba, amman yadda ya san familynsu musamman Momy idan har ta bawa wani damar shiga ma a falonta to yana da muhimmanci a gareta, sai dai abun da be sani ba wannan shigar ta dole ce ta cilastawar Appa ba dan Hurriya tana da muhimmanci a gareta ba.
“Yaya ance an daga bikinka”
Miwan ya tambaya yana kallonsa. Mutumen da Miwan ya kira da Yaya ya juyo ya kalleshi.
“Ka aje wannan Yaya aside ka kira ni da real sunana Jamal”
Momy ta yi murmushi mai sauti.
“Haba dai Captain dukansu fa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7 Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16