za ku wahala a gidan nan. Musib yi hakuri”

Ta juya ta fara hawan stairs din daman bata sauko gaba daya. Musib ya watsawa Hurriya wani mugun kallo ya dauke ido ya bi bayan mahaifiyarsa. Zaunawa Hurriya ta yi a gurin ta rafka uban tagumi, gaba daya kwakwalwarta ta rike ce ji take kamar ba zata iya dauka ba.



*** *** ***

BAYAN WATA UKU....

Tun daga lokacin sai Hurriya da Hamad suka samu salama, ta duka Hamad kuma ya samu ta magana, ba a dukansa ba a fada masa magana marar dadi, saboda ana tsoron ya fadawa Appa, Musib da Miwan ma sai duk suka shafa musu lafiya, sai dai tsanar da Hajiya Kaltume take mata sai ya karu, har ta kai a gaban Hurriya Hajiya Kaltume take zagin Iyami sai dai ba zata yi a gaban Hamad ba, Hurriya tana jin zafin abun sosai sai dai bata taba fadawa kowa ba sai dai ta bar abun a zuciyarta. Hurriya na tsaye ita da Hamad suna wanke motar Yasir Hajiya Kaltume ta fito rike da jakarta Yasir din yana bayanta rike da makullin mota.

“A gaishe da ku, amman idan Appa ya gani karku ce ni na saka ku ku ce ku kuka saka kanku dan kar ya fara fada ya ce ban kai wankin mota ba na saka ku yi”

“Hamad ya fada masa zamu wanke maka mota ai kamin mu fara, ya ce mu je mu yi Allah ya mana albarka”

Hurriya ta amsa tana watsawa motar ruwa, domim wankin mota yana daga cikin abun da yake matukar burgeta, kuma ta taba yi sau daya a motar Appanta tun a lokacin da Amma take gidan. Hajiya Kaltume ta kallesu irin kallon nan na rasa ya zan yi da ku ta dauke kai ta nufi motar da za su shiga, tana nufar motar gabanta na kara tsananta faduwa har sai da taja ta tsaya.

“Yasir anya ba za mu fasa tafiyar nan ba? Gabana sai faduwa yake Wallahi tsoro nake ji ganin nake kamar wani abun zai sake faruwa”

Yasir ya ce.

“Babu abun da zai faru Hajiya dan Allah ki kwantar da hankalinki, ki yi imani da Allah, kuma kin ga tun da abun nan ya faru baki sake fita ba, yau kusan wata uku kenan dole ki ji haka”

Ta girgiza kai domin bata gamsu da kalaman Yasir ba.

“Ko dai mu hakura har wani lokacin?”

“Hajiya idan baki kawar da komai a ranki ba, babu ranar da zaki sake fita, rasuwa nawa aka yi baki je ba, ga haihuwa ba an yi ba daya ba amman baki fita ba, Hajiya Fatee ma tare abun nan ya same ku amman zuwanta biyar gidan nan, dan Allah ki daina tsoro babu abun da zai faru da yardar Allah”

“Toh Allah yasa”

Ta amsa tare da bude motar ta shiga ba dan ranta ya so ba, sai dan fitar ta zame mata dole ne saboda kiran da Hajiya Fatee ta yi mata tana kuka ba zata fita ba, balle kuma da ya kasance gidanta na farko da zata fara zuwa tun bayan da aka yi kidnapping dinsu, sai take ganin kamar hakan zai sake faruwa ne. A hankali Yasir ya rika jan motar suna tafiya yana dan taba mata hira, ita kuma ta kasa cewa komai sai kallon gari take har lokacin tsoro be fice ta ba, garin kuma tana ganin kamar ya sake saboda dadewa da ta yi bata fita ba.

“Bismillahi”

Ta furta yayin da ta bude motar zata fita, zuciyarta nata rawa, Yasir ya rakata har cikin falon Hajiya Fatee, yan aikin Hajiya Fatee suka fara gaisheta.

“Lafiya Kalau Ina Hajiya Fatee”

“Tana dakinta”

Hajiya Kaltume ta juya ta kalli Yasir.

“Bari na kirata ku gaisa”

“Okay”

Ya nufi kujera ya zauna, Hajiya Kaltume kuma ta nufi dakin Hajiya fatee ta tura kofar ta shiga da sallama. Kuka ya hana Hajiya Fatee amsawa sai dagowa da ta yi ta kalleta da idanuwanta da suka gama kumbura.

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, Hajiya Fatee abun har ya kai haka”

“Ya wuce, Hajiya Kaltume ina cikin bala'i da tashin hankali”

Hajiya Kaltume ta juya ta leka falon saitin da yasir yake zaune.

“Yasir ka tafi kawai idan zaka dawo daukata sai ku gaisa, amman fa da zarar na kiraka ka zo da sauri”

“Toh Hajiya”

Ya tashi ya fice cike da ladabi. Sannan Hajiya Kaltume ta koma dakin ta zauna kusa da kawarta da rabin kibar jikinta ta zube saboda tashin hankali.

“Wannan abu be yi dadi ba, yanzu miye abun yi?”

Hajiya Fatee ta share hawayenta ta kalli aminiyarta.

“Ban sani ba Hajiya Kaltume, wannan shi ne likita na uku da ya fada min haka”

“Hajiya Fatee duk laifinki, da tun farko kin yarda anje asibitin an duba lafiyarki da duk be kai ga haka ba?”

“Haba Hajiya, ina zan yarda aje asibiti a fadawa ďana abun da mutanen nan suka min? Tsoron kar ya kalleni da abin kuma kar bakinciki ya zauna masa a zuciya ya saka na ki amincewa da zuwa asibitin, kuma ni ma na san idan har ya sani ba zan samu salama ba”

Hajiya Kaltume ta rafka tagumi.

“Wallahi duk wannan Iyamin ce ta ja mana, ba zan tana yafe mata ba, ni kaina yanzu sanadinta har tsoron fita nake”

“Ni yanzu ba ta Iyami nake ba Hajiya ta kaina nake, kar asirina ya tonu, ga ni ta surukar da bata kaunata, ga makiyi babban tashin hankali kuma rashin auren nan, yau shekara goma da rasuwar Alhaji me zan fadawa duniya idan abun nan ya fito da shekaru na haka har da jikoki”

Hajiya Kaltume ta sauke ajiyar zuciya.

“Hajiya ko dai daurewa zamu akara yin allurar nan ne? Ko Allah zai saka abun ya zube”

Hajiya Fatee ta dauki robar yawu ta tsargar da yawunta cikin ta aje ta kalli Hajiya Kaltume.

“Likita nan fa ya fada min, ta farko ma da na auna arziki ne, da yanzu na wuce, ni kadai na san azabar da na sha lokacin da aka min allurar nan kuma gashi bukata bata biya ba, kuma cirewar sun ce ko na mutu ko na yi rai ne”

Hannu biyu Hajiya Kaltume ta dora saman kai ta fashe da kuka tana taya aminiyarta alhini.

“Kai wayyo Allah wannan Iyami wannan Iyami Allah ya isar mana gareki, kin aure min miji kin fitine ni yanzu kuma sanadin nan mun fada cikin bala'i, ni Wallahi ma rasa ya zan yi da matar nan da yaranta, kin ga cikinta ya shiga wata na tara kenan wani zata haifowa Alhaji, yayanta da suke gidan ma be hada kowa da su ba, birthday nan da Hurriya ta yi sarkar zinari ta miliyoyan kudi yayi mata kyauta, ni da nake matarsa be taba siya min ba, sarkar da Nafisa take ta kuri da ita yau Alhaji ya siya irinta ya mallakawa Hurriya, ga birthday Hamad tafe waya san iya abun da zai masa shi ma, kuma saboda ita yanzu ya budewa kofa kofar birthday, abun da da ya hana”

Hajiya Fatee ta daki kirji.

“Sarka Hajiya? Lallai Iyami ba zata gama da duniya lafiya ba, ta mallake shi yanzu ta bar gida ta bar muku ya ku yi kishi da ita”

“Hmm abun nan ya ishe ni, ai saboda na san kina cikin taki matsalar ne ya saka ban kawo miki kukana ba, amman ciwon matar nan yana nan a kirjina, a yanzu bana da burin da ya wuce na ga Alhaji ya fita lamarin yaran nan, kuma dukiyar da ya bata ta lalace”

“Ba ke ba, ai ko ni ba zan iya yafewa Iyami ba Hajiya, sanadinta yara kanana sana'in yayana suka daure mu a daji babu kalar wulakancin da ba su min ba, yanzu kuma ga wani abun bakinciki ya sake biyo baya, ban san ya zan yi ba”

Ta karashe zancen tare da fashewa da kuka.

“Toh ni dai ina ganin abun da ya kamata kawai mu saka a nemo mana malamin nan ko Allah zai saka mu dace”

Hajiya Fatee ta mata wani kallo galala.

“Waya zai koma a wannan dajin? Ko gawata ba za a kai ba”

“Aa ina fa? Ni ma ai ba zan yarda ba, ba komawa zamu yi ba nemansa zamu yi idan ya so shi sai ya zo ya same mu”

“Ta ina? Duka wayoyin mu suka karbe fa, ba ni da number ba, kuma da aka yi welcome din Sim din har yanzu be kira ni ba, waya sani ma ko shi ya turo a dauke mu? Mutanen nan kauye nan fa ba su da kyau”

“Kai bana tunani haka, kin ga ni fa na ga kyau aikinsa domin shi kadai ne yayi min aiki kuma aikin yayi yadda nake so har Iyami ta bar gidan nan, shekara nawa ina kashe kudi a banza ban dace ba sai a gunsa, sa zaki yi a nema mana shi waya nuna miki gurin Malamin”

“Wata kawata ce Salame”

“Toh ita zaki saka ta je ta dauko mana shi, sai mu saka gurin haduwa da shi ba dole sai ya san gidan mu ba, mu gabatar masa da bukatanmu mu basa kudin aiki, daga nan ma sai na tambaye shi ina aka kwana zancen aikin Iyami, ke kuma sai ki saka yayi miki na wannan mugun abun da yake cikinki”

Kallon rashin fahimta Hajiya Fatee ta yi mata

“Ya danne miki shi mana, ba zai taba tashi ba har ki mutu, ko baki san ana haka ba? Na Iyami ma so nake a danne shi kar ta haifa ma Alhaji mugun abu, dan na san duk wayonta be wuce Alhaji ya mutu ta ci gado ba”

Hajiya Fatee ta kalleta wata rahma na saukar mata a ruhi, jin kamar ta samu mafitar masifar da take ciki.

“Kuma kina ganin hakan zai yi?”

“Me zai hana? Ki dai ki zuba masa kudi kawai, ni ma kudin zan zuba masa, kuma a hannun Alhaji zan karbe su, kudin sarkar zinarin da ya siyawa Hurriya da kudin da ya bawa Iyami duk sai na fanshesu a hannunsa, yanzu ne za su gane sun yi kuskuren taba mace kamar ni, kuma Wallahi sai na malleke Alhaji ko ta halin yaya, sai ya dawo a tafi hannuna Iyami da ƴaƴanta sai sun ɗanɗana kuɗarsu, Iyami sai ta gane kuskuren da ta aikata na aurar min miji, sai ta yi nadamar hada shimfida da Alhaji, matsayin da ta taka a baya na tana Matar Alhaji ina Matar Alhaji sai na saka ta yi nadamar haka... Ba ita ba har Nafisa sai na sake mata sabon karatu na goge mata hadda. Dukansu sai sun dawo a tafin hannuna”

Ya daki tafin hannunta tana kashe ido alamar yanzu ta shiryawa rashin imani, da kuma fada da Iyami da Momy.




________________



Hmmmmmm Allah yasa kuna hango abubuwan da nake hangowa 🤔

Tafiyar fa duk duka yanzu aka fara.... Ku daura ɗamara ku zage damtse domin domin alkalinmin da zafinsa ya zo 😁

Kar a manta idan an karanta ayi sharing 🥰
[10/18, 6:15 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
                 

𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲

Hello Habibaties 😍🥰
Amin kara please ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy

https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy


𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣2️⃣

Musib ya aje ma Captain keys din motar Momy da ta bada umarnin a dauko masa. Kallon Keys din yayi sannan ya mika hannu ya dauka ya mike tsaye. Tsabar bacin rai zuciyarsa har zafi take kamar zata fashe, baya jin yana da sauran wata magana a yanzu kuma baya bukatar yi ma Momy sallama bayan an bata masa tayun mota a gidanta. Shi ya fara fita sannan mahaifiyarsa ta bi bayansa Momy da Musib suka biyo shi suna ba shi hakuri kamar su suka masa laifin shi dai be ce uffan ba ya matsa key hannunsa motar ta fita key ya sannan ya nufita har suka bar gidan kalma daya bata sake fitowa daga bakinsa. Ran Momy be yi dadi ba ganin ďan ďan'uwanta da take ji da shi ya fita cikin bacin rai.

“Ni abun nan ya ba ni mamaki, wai waye yayi wannan aika-aikar”

“Zai wuce Kaltume? Ai bata son kowa da alheri a gidan nan kuma ta ga mota mai tsada ina za so haka, ballantana fitowar nan da ta yi dan uwa ko daya be je ya mata barka da fitowa ba”

“Amman Momy Yasir dai ba zai yi haka ba kin san ko da ta saka shi”

“Su matan fa? Kuma shi ma ba munafurci ba ne da nuna soyayyar ido, ai ta ciki na ciki dan'uwa be taba son dan'uba ba har abada”

“Ko kuma ta aiko wani yayi ba”

Ta juyo tare da Musib suka shigo falon, ko zama ba su yi ba motar Appa ta faka a harabar ya bude ya fito ya shigo cikin falon fuska a dauke.

“Ku ba mu guri zan yi magana da mahaifiyarku”

Appa ya fada immediately after ya rufe kofar falon, Musib ya dubi Miwan sannan suka tashi suka haura sama, Momy kuma ta zauna ita ma nata ran a bace tana sauraren da wacce Appa ya zo.

“Nafisa ina son na tambaye ki, akwai laifin da Hurriya ta yi miki ko kuma Hamad?”

“Wani abun aka fada kuma?”

“Akan wani dalili zaki nemi banbanta su da sauran yayanki? Fada min banbanci dake tsakinsu da Namra ko Miwan, dukansu ba Yayana ba ne? Akan wane dalili zaki ce Hurriya sai dai ta share dakinta da kanta kuma idan zata hau stairs ko ta sauka ba ta hau kamar yadda Namra ko Musib suke yi ba?”

Momy ta rike baki.

“Oh Allah na ni Nafisa, yaushe aka yi haka? Kuma shi kenan daga fada maka zance karya da gaskiya sai ka hau ka zauna har da zuwa gurin fada ba tare da ka tsaya ka bincika ba? Shiyasa ka dauko su ka kawo min? Me yasa ba a kaiwa Kaltume ba? Ita da yake tsoronta kake sai Nafisa da aka raina itace mai dadi hawa, gashi sai mulki take mana ciki gidan ita da yaranta”

“Daga ke har ita karkashin kulawata kuke kuma karkashin ikona, dan haka duk gurin da nake ra'ayi a can yarana za su zauna, kuma ina gargadinki wannan ya zama na karshe da zan sake jin wani abu marar dadi akan Hurriya da Hamad, zan iya canja mata ban zanja yaya ba, gaba daya yarana babu na yarwa kuma bana son a batawa kowa”

“Eh amman ai ka ware wadanda kake so kake kauna, na tabbatar da nawa yayan Kaltume ko Iyami take yi ma wani abu ba zaka yi magana ba, amman da yake yayan mowa ne ai gashi nan ka shigo falo cikin bacin rai saboda an taba yan gold, ni da zaka nuna musu kauna ka dawo da uwarsu ai da duk yafi wannan nema musu yanci da kake, idan ya so sai ta rike yayanta na rike nawa”

“Abun da na ga damar aiwatarwa shi zan aiwatar, babu mai fada min gabas, na san Allah, daman ke haka kike banta zuwa da wata magana ba ki musa min ba, ban taba fada kin yi shiru kin saurareni ba sai kin fada, sa'insa da ni ba yau kika fara ba, daga ke har Kaltume babu wadda nake jin sanyinta kowacce ku da lagon da take matsawa ta bata min rai”

Momy ta fashe da kuka domin kalaman Appa sun mata zafi, ta san abun da Appa ya fada akam Iyami gaskiya ne, domin ya saba yi mata fada ko a gabansu kamar yadda su ma zai iya musu a gabanta ko kuma ya tara su gaba daya yayi musu fadan idan wani abu ya faru, su kan tanka shi su kare kansu ko maida martani amman Iyami bata cewa idan yana fada har yayi ya gama, ko daga kai ba zata yi ta kalleshi ba, wannan ta saka suke yawan yi mata kallon munafuka, hawaye shar Momy take yi daman kuma bata gama hucewa daga bacin ran abun da aka yi ma Captain ba.

“Eh sai Iyami, abar kaunarka, yanzu gashi nan ka rufe da fada akan yayanta, matarka Kaltume kuma ta takura min ta takurawa bakina, yanzu Captain ne ya zo, ka san dai yadda nake da Captain amman haka matar nan ta saka aka fasa mata tayun mota saboda bakin ciki, ban gama huce wannan haushin ba gashi nan kai kuma ka zo ka rufe ni da wani, toh Wallahi ka jawa yayanka kunne su daina munafurci, kuma ka jawa matarka matarka kunne ta fita safgata da ta bakina babu ruwanta da ni idan ba haka ba Wallahi za 'ayi tashin hankali da ba taba yi ba ko a lokacin da ka auro karamar yarinyar can Iyami”

“Ni dai na fada miki, karki sake banbanta min to ƴaƴa duk daya suke a gurina, babu wanda ya fi wani, zan iya canja mata ban canja ƴaƴa ba bana ni da kamar ƴaƴana!”

Yana kawai nan ya juya ya fice, cikin motarsa ya koma yaja ta zuwa bangare ya ajeta ya fito ya taka da kafa ya nufi bangaren Hajiya Kaltume yana shiga ita ma ya salllami yaranta suka haura sama ban da Yasir da baya gidan ma a lokacin ya fita gurin safgoginsa, Namra kuma ta fita zuwa bangarensu. Fada yayi mata sosai yana ja mata kunne akan abun da ta saka aka yi ma Momy.

“La'ilaha Illallahu ni Ummul Kultoon, yaushe kuma aka yi haka? Ni miye ruwana da Nafisa balle kuma bakinta, yanzu Fisabillahi na rasa me zan saka ayi mata sai fashe tayar baki? Abu dai kamar karamar yarinyar? Ni da nake ta kaina ma? Yaushe na fito daga daji? Kofar daki ma bana sha'awar fita balle kuma har na saka ayi wani abun, shigowar nan da ka yi ma hankalina sai da ya tashi”

“Ni dai na gargadeku, bana son wani tashin hankali kowa ya zauna lafiya kuma ya tsaya a iya matsayinsa, ku bar ni da abun da yake damuna, kullum ni ne cikin fitina kamar akaina aka fara mata aure da mata biyu”

“Mata uku dai Alhaji, yaushe ka saki yarinyar can Iyami da har zaka dawo kanmu nu kadai, musamman ni, taya za a ce na fasa tayar mota? Yara ma wa zan saka yayi wannan aiki? So take ta zugaka ka koreni a gidan kamar yadda ka kori Iyami, to Wallahi ni kam zama daram dam dam dam sai mutuwa, kuma Alhaji dan Allah ka rika bincike kamin ka fara
Showing 33001 words to 36000 words out of 46312 words