ta tura kofar falon Amma ta shiga. Hamad na kwance kan kujera yana kallon remote a hannunsa.
“Hamad wai Appa sakin Amma yayi? Wai rabuwa suka yi? Yaya Khairi ta fada min”
Tana maganar yana kuka even though bata gama tabbatarwa ba. Hamad ya tashi zaune yana kallonta.
“Ai ke ce mahaukaciya shiyasa baki gane ba”
A nan Huriyya ta samu damar fashewa da kuka mai karfi, ta juya da sauri ta nufi bangaren mahaifinta.
*** *** ***
“Ah Ah Alhaji ina ce Kaltume ce Babba a gidan nan? Me zai hana su zauna a bangarenta?”
Appa ya mike tsaye.
“A nan nake son su zauna, kuma nan za su zauna ko kin yarda ko baki yarda ba, domin ke da su duk a karkashin ikona kuka kuma a gidana”
“Aa Alhaji gaskiya ban ci ƙashi ba ba zan ci aman tsoka ba! Har ina? Yara da girmansu da komai a kawo min su? Da wani abun arziki ne ai matarka take tarewa ta karbe sai a yanzu da yake wahala ce za a kawo min”
Appa ya nuna kansa.
“ƴaƴane wahala Nafisa? Ke dai har abada ba zaki taba zama matar kirki, har abada mai hali be taba fasa halinsa ba, kowa yana girma yana kara hankali da hali na gari amman ban da ke”
“Daman ni ban taba haske a idonka ba, masu haske Iyami ce da Kaltume, ka san ni ka san halina ni bana son a shiga sabgata ina bangarena babu ruwana da kowa, akan me yanzu za a dauko yayar sarauniyar gida mace da ta hana ka ganin martaba a kawo min”
Alhaji Haruna ya nuna ta da yatsansa.
“Sau daya tak bakinki ya sake furta wata magana marar dadi akan Iyami da yayanta sai mugun saba miki, ni na zabi su zauna a nan kuma a nan din za su zauna, idan baki son zama da ƴaƴana jinina ƙofar gidan a bude take..!”
Momy ta aje numfashi da karfi.
“Bismillah ga dakuna nan su zabi wanda suke so su zauna, gidan naka ne yaya naka ne ni ma taka ce Allah ya ba mu hakurin zama”
Fuuuu! Appa ya fice daga falon nata cikin mugun bacin rai. Namra da Musib suka bishi da kallo su kansu sun manta when last su ga mahaifinsu a cikin bacin rai irin wannan sai yau.
“Tsakani da Allah takurawa ce dawowarsu a nan, musamman ma dan iska yaron nan Hamad ni ubansa zan ci Wallahi”
Cewar Musib yana jin haushin hukuncin da mahaifinsu ya yanke. Bakinciki ya hana Momy sake cewa komai ta kai hannu ta dauki sarkar zinarinta dake kan aje a hannun kujera ta mike tsaye ta nufi upstairs, kamin ta isa dakinta ma wani aiki ne saboda izza da isa kamar wadda bata son taka kasa haka take tafiya.
Bakin gadonta ta zauna ta rike da sarkar sai cika take tana batsewa, ita dai ta san tana daga kafa akan kishi da matan Alhaji Haruna domin ganin take babu sa'arta a cikinsu Hajiya Kaltume dai yar talakawa ce arzikin na Alhaji Haruna Mai Yadi ne, Iyami ma haka rufin asirinsu na Alhaji Haruna ne domin har gidan da iyayenta suke ciki a yanzu shi ya siya musu shi yake dauke da nauyinsu.
Kuma Iyami ba sa'arta bace a shekaru, kuma ta fi Hajiya Kaltume zama makaskanciya a idonta domin ita ga aiki ta zo yi a gidan ta aure Alhaji Haruna, ba dan ma da kaddarar aure ta hana ba kuma yara sun shiga tsakani ba wata kila da ba zata iya hakurin sharing miji daya da yar aikin gida ba, kallon da take yi ma Amma bata da ajin da zata yi kishi da ita sai idan abun ya motsa.
Ita dai abun da ta fi tsana shi ne a shiga sabgarta, idan ta shiga sha'aninta na masu arziki har mantawa take da Hajiya Kaltume da Amma, a yanzu kuma kawo mata Hurriya da Hamad da Appa ya dage sai shi ne abun bacin ranta a yanzu, domin da su zauna a gurinta kara ya dawo da uwarsu ta rainin abunta, sam sam Momy bata son yayan kowa idan ba nata ba, bata mutanta kowa sai masu kumbar susa, idan baka da arziki har ganin take kamar baka cika mutum ba.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 6️⃣
Da tunanin Amma Appa ya dawo apartment dinsa, tsansar biyayyarta da yadda take gujewa bacin ransa da nuna kulawa akan duk wani abu da ya shafe shi. Ya tabbatar da ita ce ba sai ya bukaci a bawa Hurriya abinci ba, matukar ta san uwar yaran bata gidan zata yi kokarin kwatantan kyautata musu kuma ta ja su a jiki, haka ma da ita ce ya zo mata da zancen dawowa ƴaƴan abokiyar zamanta a bangarenta zata yi marhabun ta karba da hannu biyu ko da kuwa bata son haka ba zata nuna har ya gani ba, duk wani abu da Amma ta san Appa yana son kokarin raya shi kaunar abun take ba ta bata masa rai ba.
Hannayensa hade a bayansa yake tafiyar fuskarsa a yanutse zuciyarsa a hargitse yana jin kamar ya fashe da kuka gaba daya ya rasa me ke samunsa ya rabu da matarsa rabuwar ta haifar masa da rashin kwanciyar hankali da bacin rai, zamanta a gidan kuma masifa ce a gidansa masifar da be san ta micece ba domin shi dai ya san matarsa bata masa laifi ba, be san dalilin da ya saka ya tsane ta ba. Kukan Hurriya ne abun da ya fara masa maraba da zuwa a lokacin da ya kunna kai cikin falonsa, kuka take sosai irin kukan nan da ya hana gilashin idonta tsaya saboda hawayen da ke cika shi, ta rike gilashin a hannu lipa dinta da jikinta sai rawa suke, dishe-dishe ta ga alamar shigowar mutum bata bukatar saka gilashi domin tantance waya shiga, ta san tsayinsa da yanayin tafiyarsa ta haddace komai. Shi ya taho da sauri ita ma ta nufo inda yake da sauri tana rike da gilashin dayan hannunta kuma yana lalabensa.
“Appa. ..apa... Appa... Appa wai ka rabu da Amma?... Sakin Amma ka yi?”
“A gurin wa kika ji wannan maganar Hurriya? Waya fada miki haka cikin daren nan?”
“Yaya Khairi.... Appa da gaske? Appa why? Yanzu mu kadai ne zamu rasa uwa a nan Appa! Me Amma ta yi?”
Tambaya take tana wani irin kuka numfashi na fitar mata da karfi kamar ranta zai fita. Idon Appa ya cika da hawaye
“Bata yi komai ba Hurriya, be kamata ki shiga cikin magana irin wannan ba, zauna a nan ina zuwa”
Ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita, ya juya ya fita gaba daya abubuwa sun rike masa har ji yake wani abu na juya masa cikin kai, kamar za a haukata shi haka yake ji. Bangaren Hajiya Kaltume ya nufa tun a tsakar falon ya fara kiran Khairi rai a matukar bace daman ciwon sakin Amma da ya kama shi, ga bacin ran da Momy ta saka masa yanzu kuma Khairi ta kara masa wani ta hanyar batawa Hurriya. Umm Khairi ta fito daga dakin Hajiya tare da Maama Umm Ruman na biye da su a baya, Umm Salma da Yasir kuma suka fito a nasu dakuna duk suka sauko kasa.
“Alhaji Lafiya?”
Cewar Hajiya Kaltume da ta riga su saukowa gabanta har faduwa yake.
“Akan wane dalili Umm Khairi zata fadawa Hurriya sakin mahaifiyarta aka yi? Ita mahaifiyar bata fada ba sai ke yar iya? Wannan ba rashin hankali da rashin tarbiya ba ne? Ki shiga cikin maganar iyayenki?”
Ya juya gurin Hajiya Kaltume.
“Kin ga abun da kika hanyo ko? Kin maida yaran nan kawayenki da maganar da ya dace da wanda be dace ba duk fada kike a gabansu, har suna jin sun isa sun kai su saka baki a zaman takewar mahaifinsu, sai na koya miki hankali sai na koya miki hankali Ummul Khairi”
Jikinta ya dauki rawa domin ta san halin Appansu idan hau yana wuyar saukowa. Yasir ya karbawa Appa.
“Iskanci ne da rainin hankali, ta fi uban kowa baki da bakin iyayi a gidan nan kamar wata babbar mace, yau sai kin fadi wanda ya aike ki”
Hajiya Kaltume na jin haka ta yi saurin zunguje Khairi.
“Ba zaki bada hakuri ba yar iskar yarinya? Idan kuma ba haka ba ne sai ki fadi yadda aka yi ai ko?”
“Appa Wallahi karya take min, yarinyar nan munafukace sai dai idan labe ta yi, ko kuma so take ta hada min sheri”
Tana rufe baki Yasir ya fara dukan bakin nata ya saka hannnunsaya kama lips din ya jan sai da ta ti ihu sannan ya rufe ta da duka gaba daya, Hajiya Kaltume ta fara kokarin kwatar yarta Appa kuma ya fice daga falon ba tare da ya hana Yasir dukan Khairi ba.
“Ai fa an taba yar gata yar gaban goshi yar lasa da halshe, kai dan Allah karka kashe min ƴa saboda ƴar wasu da ba zata amfana maka komai ba”
Hajiya Kaltume na masifa tana kwatar Khairi dake ta rusar ihu, Maama da Salma sai haushi suke ji saboda ana dukan yar'uwarsu Ruma ce kadai take jin abun da yayarta ta yi bata yi daidai ba.
A bangaren Hurriya Appanta na fita sai ta tsagaita kukanta ta share hawayen da suka ki tsaya mata ta saka gilashin da zai bata ganin kofar fita dakin daidai ta mike tsaye ta fito daga bangaren mahaifinta ta dawo na su bangaren tana tafe tana hawaye har ta isa. Sai ta ta tura kofar falon ta bude sai kuma ta kasa shiga domin jin take kamar Amma ma mutuwa ta yi ba barin gidan ba bata taba sanin haka kewa take ba sai yau da ta yi kewar mahaifiyarta. Kusan da ita da wanda ba shi da lakka a jiki duk daya domin tun a yanayin tafiyarta zaka fahimci zuciyarta ta karaya salulu ta shigo falon ta zauna kan kujera har lokacin Hamad na zaune a inda ta barshi, sai dai a yanzu fuskarsa na nuna danuwar dake zuciyarsa domin ya bata rai sosai ba kamar dazun ba d ya bar abun a cikin zuciyarsa. Fashewa Hurriya ta yi da kuka tana girgiza kai ji take kamar ace mata ba gaske ba ne, da ace ta san sakin Amma Appanta yayi babu abun da zai hana ta binta, da ba zata yarda ta zauna a gidan ba, a yanzu kam ta yarda ita wawuya ce da bata yi saurin ganewa ba, domin tana da saurin yarda idan aka fada mata abu dauka take ko da kuwa ba gaskiya ba ne. Kukanta ne ya saka Hamad hawaye yana ta dantse baki yana boye cikarsa domin zuciyarsa kawowa take kamar wani zaki, amman sai duk da hakan sai ya gagara rike kansa shi ma ya fasa kuka, ita da shi suka zama kamar wadanda aka cewa Amma ta mutu ta bar su.
“Hurriya Hamad”
Kusan a tare suka dago suka kalli kofar gefen Dinning din kofar da Appa ke tsaye, kofar cikin falon Amma ce dake basu damar shiga bangaren Appansu. Hurriya ta tashi da sauri ta nufi inda yake tana kuka sosai Hamad kuma ya dauke ido alamar baya son ganin Appa.
“Wannan kuka sai kace an yi mutuwa? Haba karku saka kanku a damuwa tsakanin halshe ra hokora ma ana basawa balle kuma mutum da mutum, dan tsabani muka samu shi ne Amma ta tafi gida, amman da zarar al'amurra sun daidaita zata dawo”
Hurriya ta kasa magana sai kuka take, Hamad kuma ya mike tsaye ya share hawayensa ya nufi sama.
“Karka shiga, ba a nan zaku kwana ba, na yi magana da Momynku a can zaku kwana ku zo muje”
Be jira cewarsu ba ya kama hannun Hurriya zuciyarsa na masa babu dadi, daman can shu baya son kukan wani ko ganin wani a damuwa balle kuma yaransa, sanin cewar shi ne silar damuwar ya saka shi jin babu dadi gaba daya abubuwan sun zo masa ta yadda be yi zato ba. Ganin Appa ya nufi kofar fita falon tare da Hurriya ya saka Hamad ya bi bayansu, sai da suka fita harabar gidan gaba daya, sannan Appa ya tsaya ya tsayar da yarsa ya daga kanta ta kalleshi.
“Haka zamu shiga bangaren Momynki kina ta kuka Hurriya? Dan Allah ku yi hakuri idan ba so kuke ni ma na yi kukan nan ba, ba ku san abun da yake cikin zuciyata ba, ina cikin wani irin tashin hankali da rudani marar misaltuwa”
Kai kawai ta iya daga masa ta saka hannayensa ta share hawayenta tana ta aikin hade kukan dake neman ya gagari tsayawa a iya bakinta da idonta.
“Ammanku ba mutuwa tayi ba, zaku iya zuwa ku ganta a duk lokacin da kuke so, ita zata iya zuwa ta ganku, Hamad na san kai ne mai zuciya ka sakawa kanka hakuri dan Allah ko dan yar'uwarka”
Ko saitin gurin da Appa yake tsaye Hamad be kalla ba, yadda ya dauke kai yana kallon wani gurin sai ka rantse da Allah ba da shi Appa yake magana ba, domin a yau kam ba shi da abokin tsana kamar Appansa saboda sanin cewar ya rabu da Amma, ko da kuwa ba zai iya fadar abun da ya faru tsakaninsu ba, hausawa suka ce mai lalabe a duhu balle an haska masa, a banza yayi fushi balle an taba shi. Appa ya dauke kai ya rika hannun Hurriya suka cigaba da tafiyar, da kansa ya shiga falon, be zarce ko ko'ina ba sai Stairs kai tsaye ya nufi dakunan da suke gefen bedroom din Momy kamar yadda suke a kowane bangare, ya san dakin Namra da na Musib da Miwan dan haka be taba dakunansu ba ya nufi wani dakin ba dabam ya tura kofar dakin sannan ya saki hannun Hurriya daki ne dake dauke da furniture na mutum daya domin Appa ya saka an zuba furniture an gyara ko wane daki duk kuwa da kasancewar wasu dakunan babu kowa, ba dan komai ba sai dan irin haka ko kuma idan an yi baki ko ma idan yaransa sun yi sha'awar canja daki daga wani zuwa wani. Hurriya ta daga kafarta ta shiga cikin dakin ta isa bakin gadon da zai wadaci mutum daya ta juyo ta zauna ta a hankali tana kallon Appanta dake jan kofar dakin. Gam... Kofar na amsawa gabanta ya yanke ya fadi, gaba daya sai ta ji kamar wata duniyar aka kawo ta, sai ta ji kamar wani gidan da bata san kowa ba kuma bata da gatan kowa a ciki aka kawota. Rabon da ta shiga bangaren Momy ma an dade, babu ruwanta da bangare sai da dalili ita ma Momy bata shiga nasu bangaren ita ta ware kanta dabam a gidan. Dayan dakin dake kusa da na Hurriya Appa ya budewa Hamad
“Nan zai mana Hamad?”
Ya daga kai sannan ya saka kai ya shige dakin da kansa ya turo kofar dakin ba tare da ya jira mahaifinsa ya rufe masa ba. Appa ya sauke ajiyar zuciya ya juya ya sauka, Namra da Musib suka hada ido suna mamakin yadda Appa ya shigo da Hurriya be ma bari ta zo da kanta ba.
“Musib ina Miwan?”
“Ya fita da magariba nan Appa”
“Namra da Musib dan Allah a zauna lafiya, yaran nan kanenku ne, jini daya ne ku da su, bana son na ji wani tashin hankali ko fada, Hamad dai kun riga kun san halinsa ba sai an fada muku ba, duk wani abun da zai yi ku kawar da ido ni kaina da nake mahaifinsa hakuri nake da shi, Hurriya kuma kun san babu ruwanta da fita dan Allah a zauna lafiya”
Nasiha yake musu amman zuciyarsa cike take da kunci da damuwa narar misaltuwa. Appa ya amsa cike da ladabi
“In Shaa Allahu Appa”
Ya dan motsa kansa kadan alamar gamsuwa sannan ya nufi kofar fita.
“Sai da safe Appa mu kwana lafiya”
“Allah yasa”
Ya amsa sannan ya fice. Yana sakin kofar falon Musib yayi kwafa ya mike tsaye ya nufi stairs Namra ta bi bayansa, ita ta shige dakin Momy Musib kuma ya nufi dakin da zuciyarsa ta raya nasa Hurriyya na ciki. Ya tura kofar dakin kamar abun arziki ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta idonta shar da hawaye.
“Yar gatan Appa, da kansa ya riko hannunsa ya kawo ki, kuma saboda ke yayi ta fada da Momy”
Uffan Hurriya bata ce masa ba, har ya gaji da tsayuwa ya bar mata kofar a bude yayi tafiyarsa. Runtse ido ta yi tana jin wani sabon kuka na zo mata, ta dawo a rakube gurin ta ta san cewar zata sha azaba da wahalar zama, da ma ace bangaren Hajiya Kaltume aka ajeta ko ba komai zata samu sauki ta wani bangaren saboda Yasir, amman a na bangaren ta san babu mai sonta, gaba daya sai ta ji ta zama wata marainiya ashe ba sai da rashin uwa da uba ake maraici ba. Musib na barin kofar dakin Hurriya ya nufi dakin Hamad ya tura, kwance ya hango shi saman gadon ya baya kofar baya, kuma budewar da Musib yayi be saka Hamad juyo dan ya duba ko waye ba. Wani mugun kallo da tsana irin ta yan uba Musib ya jefi kanensa da shi, sannan ya bar kofar dakin shi ma be rufe masa ba, Hamad na jin alamar an tafi ya juyo ya sauko saman gadon ya iso gurin kofar ya rufe ta da karfi ya saka key, Musib da be jima da barin bakin kofar ba ya juyo ya kalli kofar jin yadda aka bugata da karfi.
“Zaka sha wahala yaro”
Yayi kwafa ya nufi dakin Momy sai wani huci yake kamar mace, daman shi ne mai kishin da matan ubansa a gidan sai dai yana boye abun a zuciyarsa, yadda yake jin kiyayyar Iyami da Hajiya Kaltume ko Momynsa bata jin kiyayyarsu haka domin ita sai idan kishin ya motsa mata ne take kula su ko kula wani abu da ya shafesu.
Daren sai ya zamewa Hamad da Hurriya dabam, sanin cewar rabuwa mahaifiyarsu ta yi da mahaifinsu ya hana Hurriya rutsawa har safe, sai ta raya daren da kuka Hamad
Showing 15001 words to 18000 words out of 46312 words
“Hamad wai Appa sakin Amma yayi? Wai rabuwa suka yi? Yaya Khairi ta fada min”
Tana maganar yana kuka even though bata gama tabbatarwa ba. Hamad ya tashi zaune yana kallonta.
“Ai ke ce mahaukaciya shiyasa baki gane ba”
A nan Huriyya ta samu damar fashewa da kuka mai karfi, ta juya da sauri ta nufi bangaren mahaifinta.
*** *** ***
“Ah Ah Alhaji ina ce Kaltume ce Babba a gidan nan? Me zai hana su zauna a bangarenta?”
Appa ya mike tsaye.
“A nan nake son su zauna, kuma nan za su zauna ko kin yarda ko baki yarda ba, domin ke da su duk a karkashin ikona kuka kuma a gidana”
“Aa Alhaji gaskiya ban ci ƙashi ba ba zan ci aman tsoka ba! Har ina? Yara da girmansu da komai a kawo min su? Da wani abun arziki ne ai matarka take tarewa ta karbe sai a yanzu da yake wahala ce za a kawo min”
Appa ya nuna kansa.
“ƴaƴane wahala Nafisa? Ke dai har abada ba zaki taba zama matar kirki, har abada mai hali be taba fasa halinsa ba, kowa yana girma yana kara hankali da hali na gari amman ban da ke”
“Daman ni ban taba haske a idonka ba, masu haske Iyami ce da Kaltume, ka san ni ka san halina ni bana son a shiga sabgata ina bangarena babu ruwana da kowa, akan me yanzu za a dauko yayar sarauniyar gida mace da ta hana ka ganin martaba a kawo min”
Alhaji Haruna ya nuna ta da yatsansa.
“Sau daya tak bakinki ya sake furta wata magana marar dadi akan Iyami da yayanta sai mugun saba miki, ni na zabi su zauna a nan kuma a nan din za su zauna, idan baki son zama da ƴaƴana jinina ƙofar gidan a bude take..!”
Momy ta aje numfashi da karfi.
“Bismillah ga dakuna nan su zabi wanda suke so su zauna, gidan naka ne yaya naka ne ni ma taka ce Allah ya ba mu hakurin zama”
Fuuuu! Appa ya fice daga falon nata cikin mugun bacin rai. Namra da Musib suka bishi da kallo su kansu sun manta when last su ga mahaifinsu a cikin bacin rai irin wannan sai yau.
“Tsakani da Allah takurawa ce dawowarsu a nan, musamman ma dan iska yaron nan Hamad ni ubansa zan ci Wallahi”
Cewar Musib yana jin haushin hukuncin da mahaifinsu ya yanke. Bakinciki ya hana Momy sake cewa komai ta kai hannu ta dauki sarkar zinarinta dake kan aje a hannun kujera ta mike tsaye ta nufi upstairs, kamin ta isa dakinta ma wani aiki ne saboda izza da isa kamar wadda bata son taka kasa haka take tafiya.
Bakin gadonta ta zauna ta rike da sarkar sai cika take tana batsewa, ita dai ta san tana daga kafa akan kishi da matan Alhaji Haruna domin ganin take babu sa'arta a cikinsu Hajiya Kaltume dai yar talakawa ce arzikin na Alhaji Haruna Mai Yadi ne, Iyami ma haka rufin asirinsu na Alhaji Haruna ne domin har gidan da iyayenta suke ciki a yanzu shi ya siya musu shi yake dauke da nauyinsu.
Kuma Iyami ba sa'arta bace a shekaru, kuma ta fi Hajiya Kaltume zama makaskanciya a idonta domin ita ga aiki ta zo yi a gidan ta aure Alhaji Haruna, ba dan ma da kaddarar aure ta hana ba kuma yara sun shiga tsakani ba wata kila da ba zata iya hakurin sharing miji daya da yar aikin gida ba, kallon da take yi ma Amma bata da ajin da zata yi kishi da ita sai idan abun ya motsa.
Ita dai abun da ta fi tsana shi ne a shiga sabgarta, idan ta shiga sha'aninta na masu arziki har mantawa take da Hajiya Kaltume da Amma, a yanzu kuma kawo mata Hurriya da Hamad da Appa ya dage sai shi ne abun bacin ranta a yanzu, domin da su zauna a gurinta kara ya dawo da uwarsu ta rainin abunta, sam sam Momy bata son yayan kowa idan ba nata ba, bata mutanta kowa sai masu kumbar susa, idan baka da arziki har ganin take kamar baka cika mutum ba.
[10/18, 5:34 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: https://chat.whatsapp.com/GJ9hOtbWbfDKmq8NrKsDIG
☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
𝗣𝗮𝗴𝗲 6️⃣
Da tunanin Amma Appa ya dawo apartment dinsa, tsansar biyayyarta da yadda take gujewa bacin ransa da nuna kulawa akan duk wani abu da ya shafe shi. Ya tabbatar da ita ce ba sai ya bukaci a bawa Hurriya abinci ba, matukar ta san uwar yaran bata gidan zata yi kokarin kwatantan kyautata musu kuma ta ja su a jiki, haka ma da ita ce ya zo mata da zancen dawowa ƴaƴan abokiyar zamanta a bangarenta zata yi marhabun ta karba da hannu biyu ko da kuwa bata son haka ba zata nuna har ya gani ba, duk wani abu da Amma ta san Appa yana son kokarin raya shi kaunar abun take ba ta bata masa rai ba.
Hannayensa hade a bayansa yake tafiyar fuskarsa a yanutse zuciyarsa a hargitse yana jin kamar ya fashe da kuka gaba daya ya rasa me ke samunsa ya rabu da matarsa rabuwar ta haifar masa da rashin kwanciyar hankali da bacin rai, zamanta a gidan kuma masifa ce a gidansa masifar da be san ta micece ba domin shi dai ya san matarsa bata masa laifi ba, be san dalilin da ya saka ya tsane ta ba. Kukan Hurriya ne abun da ya fara masa maraba da zuwa a lokacin da ya kunna kai cikin falonsa, kuka take sosai irin kukan nan da ya hana gilashin idonta tsaya saboda hawayen da ke cika shi, ta rike gilashin a hannu lipa dinta da jikinta sai rawa suke, dishe-dishe ta ga alamar shigowar mutum bata bukatar saka gilashi domin tantance waya shiga, ta san tsayinsa da yanayin tafiyarsa ta haddace komai. Shi ya taho da sauri ita ma ta nufo inda yake da sauri tana rike da gilashin dayan hannunta kuma yana lalabensa.
“Appa. ..apa... Appa... Appa wai ka rabu da Amma?... Sakin Amma ka yi?”
“A gurin wa kika ji wannan maganar Hurriya? Waya fada miki haka cikin daren nan?”
“Yaya Khairi.... Appa da gaske? Appa why? Yanzu mu kadai ne zamu rasa uwa a nan Appa! Me Amma ta yi?”
Tambaya take tana wani irin kuka numfashi na fitar mata da karfi kamar ranta zai fita. Idon Appa ya cika da hawaye
“Bata yi komai ba Hurriya, be kamata ki shiga cikin magana irin wannan ba, zauna a nan ina zuwa”
Ya nufi kujera da ita ya zaunar da ita, ya juya ya fita gaba daya abubuwa sun rike masa har ji yake wani abu na juya masa cikin kai, kamar za a haukata shi haka yake ji. Bangaren Hajiya Kaltume ya nufa tun a tsakar falon ya fara kiran Khairi rai a matukar bace daman ciwon sakin Amma da ya kama shi, ga bacin ran da Momy ta saka masa yanzu kuma Khairi ta kara masa wani ta hanyar batawa Hurriya. Umm Khairi ta fito daga dakin Hajiya tare da Maama Umm Ruman na biye da su a baya, Umm Salma da Yasir kuma suka fito a nasu dakuna duk suka sauko kasa.
“Alhaji Lafiya?”
Cewar Hajiya Kaltume da ta riga su saukowa gabanta har faduwa yake.
“Akan wane dalili Umm Khairi zata fadawa Hurriya sakin mahaifiyarta aka yi? Ita mahaifiyar bata fada ba sai ke yar iya? Wannan ba rashin hankali da rashin tarbiya ba ne? Ki shiga cikin maganar iyayenki?”
Ya juya gurin Hajiya Kaltume.
“Kin ga abun da kika hanyo ko? Kin maida yaran nan kawayenki da maganar da ya dace da wanda be dace ba duk fada kike a gabansu, har suna jin sun isa sun kai su saka baki a zaman takewar mahaifinsu, sai na koya miki hankali sai na koya miki hankali Ummul Khairi”
Jikinta ya dauki rawa domin ta san halin Appansu idan hau yana wuyar saukowa. Yasir ya karbawa Appa.
“Iskanci ne da rainin hankali, ta fi uban kowa baki da bakin iyayi a gidan nan kamar wata babbar mace, yau sai kin fadi wanda ya aike ki”
Hajiya Kaltume na jin haka ta yi saurin zunguje Khairi.
“Ba zaki bada hakuri ba yar iskar yarinya? Idan kuma ba haka ba ne sai ki fadi yadda aka yi ai ko?”
“Appa Wallahi karya take min, yarinyar nan munafukace sai dai idan labe ta yi, ko kuma so take ta hada min sheri”
Tana rufe baki Yasir ya fara dukan bakin nata ya saka hannnunsaya kama lips din ya jan sai da ta ti ihu sannan ya rufe ta da duka gaba daya, Hajiya Kaltume ta fara kokarin kwatar yarta Appa kuma ya fice daga falon ba tare da ya hana Yasir dukan Khairi ba.
“Ai fa an taba yar gata yar gaban goshi yar lasa da halshe, kai dan Allah karka kashe min ƴa saboda ƴar wasu da ba zata amfana maka komai ba”
Hajiya Kaltume na masifa tana kwatar Khairi dake ta rusar ihu, Maama da Salma sai haushi suke ji saboda ana dukan yar'uwarsu Ruma ce kadai take jin abun da yayarta ta yi bata yi daidai ba.
A bangaren Hurriya Appanta na fita sai ta tsagaita kukanta ta share hawayen da suka ki tsaya mata ta saka gilashin da zai bata ganin kofar fita dakin daidai ta mike tsaye ta fito daga bangaren mahaifinta ta dawo na su bangaren tana tafe tana hawaye har ta isa. Sai ta ta tura kofar falon ta bude sai kuma ta kasa shiga domin jin take kamar Amma ma mutuwa ta yi ba barin gidan ba bata taba sanin haka kewa take ba sai yau da ta yi kewar mahaifiyarta. Kusan da ita da wanda ba shi da lakka a jiki duk daya domin tun a yanayin tafiyarta zaka fahimci zuciyarta ta karaya salulu ta shigo falon ta zauna kan kujera har lokacin Hamad na zaune a inda ta barshi, sai dai a yanzu fuskarsa na nuna danuwar dake zuciyarsa domin ya bata rai sosai ba kamar dazun ba d ya bar abun a cikin zuciyarsa. Fashewa Hurriya ta yi da kuka tana girgiza kai ji take kamar ace mata ba gaske ba ne, da ace ta san sakin Amma Appanta yayi babu abun da zai hana ta binta, da ba zata yarda ta zauna a gidan ba, a yanzu kam ta yarda ita wawuya ce da bata yi saurin ganewa ba, domin tana da saurin yarda idan aka fada mata abu dauka take ko da kuwa ba gaskiya ba ne. Kukanta ne ya saka Hamad hawaye yana ta dantse baki yana boye cikarsa domin zuciyarsa kawowa take kamar wani zaki, amman sai duk da hakan sai ya gagara rike kansa shi ma ya fasa kuka, ita da shi suka zama kamar wadanda aka cewa Amma ta mutu ta bar su.
“Hurriya Hamad”
Kusan a tare suka dago suka kalli kofar gefen Dinning din kofar da Appa ke tsaye, kofar cikin falon Amma ce dake basu damar shiga bangaren Appansu. Hurriya ta tashi da sauri ta nufi inda yake tana kuka sosai Hamad kuma ya dauke ido alamar baya son ganin Appa.
“Wannan kuka sai kace an yi mutuwa? Haba karku saka kanku a damuwa tsakanin halshe ra hokora ma ana basawa balle kuma mutum da mutum, dan tsabani muka samu shi ne Amma ta tafi gida, amman da zarar al'amurra sun daidaita zata dawo”
Hurriya ta kasa magana sai kuka take, Hamad kuma ya mike tsaye ya share hawayensa ya nufi sama.
“Karka shiga, ba a nan zaku kwana ba, na yi magana da Momynku a can zaku kwana ku zo muje”
Be jira cewarsu ba ya kama hannun Hurriya zuciyarsa na masa babu dadi, daman can shu baya son kukan wani ko ganin wani a damuwa balle kuma yaransa, sanin cewar shi ne silar damuwar ya saka shi jin babu dadi gaba daya abubuwan sun zo masa ta yadda be yi zato ba. Ganin Appa ya nufi kofar fita falon tare da Hurriya ya saka Hamad ya bi bayansu, sai da suka fita harabar gidan gaba daya, sannan Appa ya tsaya ya tsayar da yarsa ya daga kanta ta kalleshi.
“Haka zamu shiga bangaren Momynki kina ta kuka Hurriya? Dan Allah ku yi hakuri idan ba so kuke ni ma na yi kukan nan ba, ba ku san abun da yake cikin zuciyata ba, ina cikin wani irin tashin hankali da rudani marar misaltuwa”
Kai kawai ta iya daga masa ta saka hannayensa ta share hawayenta tana ta aikin hade kukan dake neman ya gagari tsayawa a iya bakinta da idonta.
“Ammanku ba mutuwa tayi ba, zaku iya zuwa ku ganta a duk lokacin da kuke so, ita zata iya zuwa ta ganku, Hamad na san kai ne mai zuciya ka sakawa kanka hakuri dan Allah ko dan yar'uwarka”
Ko saitin gurin da Appa yake tsaye Hamad be kalla ba, yadda ya dauke kai yana kallon wani gurin sai ka rantse da Allah ba da shi Appa yake magana ba, domin a yau kam ba shi da abokin tsana kamar Appansa saboda sanin cewar ya rabu da Amma, ko da kuwa ba zai iya fadar abun da ya faru tsakaninsu ba, hausawa suka ce mai lalabe a duhu balle an haska masa, a banza yayi fushi balle an taba shi. Appa ya dauke kai ya rika hannun Hurriya suka cigaba da tafiyar, da kansa ya shiga falon, be zarce ko ko'ina ba sai Stairs kai tsaye ya nufi dakunan da suke gefen bedroom din Momy kamar yadda suke a kowane bangare, ya san dakin Namra da na Musib da Miwan dan haka be taba dakunansu ba ya nufi wani dakin ba dabam ya tura kofar dakin sannan ya saki hannun Hurriya daki ne dake dauke da furniture na mutum daya domin Appa ya saka an zuba furniture an gyara ko wane daki duk kuwa da kasancewar wasu dakunan babu kowa, ba dan komai ba sai dan irin haka ko kuma idan an yi baki ko ma idan yaransa sun yi sha'awar canja daki daga wani zuwa wani. Hurriya ta daga kafarta ta shiga cikin dakin ta isa bakin gadon da zai wadaci mutum daya ta juyo ta zauna ta a hankali tana kallon Appanta dake jan kofar dakin. Gam... Kofar na amsawa gabanta ya yanke ya fadi, gaba daya sai ta ji kamar wata duniyar aka kawo ta, sai ta ji kamar wani gidan da bata san kowa ba kuma bata da gatan kowa a ciki aka kawota. Rabon da ta shiga bangaren Momy ma an dade, babu ruwanta da bangare sai da dalili ita ma Momy bata shiga nasu bangaren ita ta ware kanta dabam a gidan. Dayan dakin dake kusa da na Hurriya Appa ya budewa Hamad
“Nan zai mana Hamad?”
Ya daga kai sannan ya saka kai ya shige dakin da kansa ya turo kofar dakin ba tare da ya jira mahaifinsa ya rufe masa ba. Appa ya sauke ajiyar zuciya ya juya ya sauka, Namra da Musib suka hada ido suna mamakin yadda Appa ya shigo da Hurriya be ma bari ta zo da kanta ba.
“Musib ina Miwan?”
“Ya fita da magariba nan Appa”
“Namra da Musib dan Allah a zauna lafiya, yaran nan kanenku ne, jini daya ne ku da su, bana son na ji wani tashin hankali ko fada, Hamad dai kun riga kun san halinsa ba sai an fada muku ba, duk wani abun da zai yi ku kawar da ido ni kaina da nake mahaifinsa hakuri nake da shi, Hurriya kuma kun san babu ruwanta da fita dan Allah a zauna lafiya”
Nasiha yake musu amman zuciyarsa cike take da kunci da damuwa narar misaltuwa. Appa ya amsa cike da ladabi
“In Shaa Allahu Appa”
Ya dan motsa kansa kadan alamar gamsuwa sannan ya nufi kofar fita.
“Sai da safe Appa mu kwana lafiya”
“Allah yasa”
Ya amsa sannan ya fice. Yana sakin kofar falon Musib yayi kwafa ya mike tsaye ya nufi stairs Namra ta bi bayansa, ita ta shige dakin Momy Musib kuma ya nufi dakin da zuciyarsa ta raya nasa Hurriyya na ciki. Ya tura kofar dakin kamar abun arziki ya tsaya daga bakin kofa yana kallonta idonta shar da hawaye.
“Yar gatan Appa, da kansa ya riko hannunsa ya kawo ki, kuma saboda ke yayi ta fada da Momy”
Uffan Hurriya bata ce masa ba, har ya gaji da tsayuwa ya bar mata kofar a bude yayi tafiyarsa. Runtse ido ta yi tana jin wani sabon kuka na zo mata, ta dawo a rakube gurin ta ta san cewar zata sha azaba da wahalar zama, da ma ace bangaren Hajiya Kaltume aka ajeta ko ba komai zata samu sauki ta wani bangaren saboda Yasir, amman a na bangaren ta san babu mai sonta, gaba daya sai ta ji ta zama wata marainiya ashe ba sai da rashin uwa da uba ake maraici ba. Musib na barin kofar dakin Hurriya ya nufi dakin Hamad ya tura, kwance ya hango shi saman gadon ya baya kofar baya, kuma budewar da Musib yayi be saka Hamad juyo dan ya duba ko waye ba. Wani mugun kallo da tsana irin ta yan uba Musib ya jefi kanensa da shi, sannan ya bar kofar dakin shi ma be rufe masa ba, Hamad na jin alamar an tafi ya juyo ya sauko saman gadon ya iso gurin kofar ya rufe ta da karfi ya saka key, Musib da be jima da barin bakin kofar ba ya juyo ya kalli kofar jin yadda aka bugata da karfi.
“Zaka sha wahala yaro”
Yayi kwafa ya nufi dakin Momy sai wani huci yake kamar mace, daman shi ne mai kishin da matan ubansa a gidan sai dai yana boye abun a zuciyarsa, yadda yake jin kiyayyar Iyami da Hajiya Kaltume ko Momynsa bata jin kiyayyarsu haka domin ita sai idan kishin ya motsa mata ne take kula su ko kula wani abu da ya shafesu.
Daren sai ya zamewa Hamad da Hurriya dabam, sanin cewar rabuwa mahaifiyarsu ta yi da mahaifinsu ya hana Hurriya rutsawa har safe, sai ta raya daren da kuka Hamad
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16