falon na Hajiya Kaltume yana cike da yayanta da kuma yayan yan'uwanta da ma ita kanta sai hira ake har da Namra. Kamar ta Allah haka Hajiya Kaltume ta washe baki tana maraba da zuwan Hajiya Binta.
“Sannu da zuwa Hajiya, ai da ma baki zo ba, ga kafafuwa suna ciwo ni kaina idan na warware ai sai na zo na gaishe ki, kuma ai kin kira waya haka ma ya wadatar”
“Aa kara dai na zo, fatar na same ku lafiya”
“Lafiya Kalau Alhamdulillah, ya ciwon kafafuwan yayi sauki?”
“Alhamdulillah”
Sama sama dai suka yi ta gaisawa Appa na zaune kusa da Hajiyarsa daga kasa, Hajiya Kaltume kuma na daga kan kujera ita da duka yaranta, Hurriya da Hamad ne kadai a kasa domin haka Amma ta koya musu idan babba yana kan gado ko kujera to su kuma su zauna a kasa, kar su zauna tare da shi ko kuma a yadda yake zaune. Da hira ta yi hira ne Hajiya Kaltume ta dauko zancen wahalar da suka sha a dajin tana fadar yadda aka rika mistreated dinsu kamar wasu dabbobi.
“Shiyasa ake son a samu soji masu kishin kasa da za su iya yakarsu idan ba haka ba, kasar nan da wahala ta gyaru domin Shugabannin ma sun zama sai a hankali”
Cewar Yasir. Cikin murmushi Hajiya Binta ta kalli Hamad ta ce.
“Da yardar Allah Hamad soja zai yi, wannan fushi da zuciyar ta soja ce”
Hamad ya girgiza kai.
“Aa ba soja nake so ba?”
Namra ta ce.
“To me kake so? Wannan zuciyar taka Hamad ai soja ya dace da kai”
“Aa ni Likitan idanu nake son zama, idan na kware zan yi ma Hurriya aiki ta, ita ma ta rika gani kamar kowa”
Tsit katon falon na Hajiya Kaltume yayi domin babu wanda ya za ci abun da zai fito daga bakin Hamad kenan. Hurriya ta yi murmushi tana masa kallo irin na so da kaunar dan'uwa, ita kanta ba yi zaton Hamad yana sonta kuma ya kula da damuwarta har haka ba.
“Come here my friend”
Yasir ya mika masa hannu, sai ya taso ya iso gurin Yasir din Yasir ya rumgume yana buga bayansa.
“Yayi kyau babban mutum”
Cikin jindadi da alfahari Appa ya kalli Hamad ya ce.
“Da yardar Allah da yardar Allah, Hamad ba zaka yi karatu a kasar nan ba, waje zan kai ka ka sha ilmin akan idanuwa har ka gaji, da ikon Allah wannan kudirin naka sai ya cika ko da bana raye”
Hajiya Kaltume da ta rasa abun da zata yi ta kalli Appa da murmushin dole.
“Za a karya dokar fitar da yara waje karatu kenan Alhaji akan Hamad?”
“In Shaa Allah, ba shi kadai ba Hurriya ma ba zata yi karatu a kasar nan ba, yadda take da kokarin nan waje ya kamata ta yi karatu, kuma ko ba ni ba Principal dinsu ya fada min suna sa ran da zarar ta gama secondary school zata samu scholarship mai kyau a manya kasasshe saboda kokarinta da yadda take cin gasa ta bangaren lissafi”
“Maa Sha Allahu, Allah ya nuna mana yara masu albarka Allahu akbar Allah dai yayi albar....ya bar zumunci”
Sai ta kasa karasa da Allah yayi albarka ta canja zuwa Allah ya bar zumunci, domin ta san hausawa sun ce addu'ar makiyi karɓaɓɓiya ce, ita ko ba zata so su yi albarka ba. Gashi abun da Appa ya fada cewar yaran Iyami za su karatu a waje ya daki zuciyarta mugun daka irin dakan da ace mashi ne, babu abun da zai hana ya bullo ta bayanta, yanayinta ma gaba daya sai ya sauya hankalinta yayi mugun tashi, ba dan ta yaki zuciyarta ba wata kila ma da ta rasa sukuninta har kowa ya gane halin da take ciki.
“Allah sarki dan'uwa mai kaunar yar'uwarsa, duk da fadan nan da kuke da rashin jituwa wannan soyayyar da kaunar tana nan a zuciyarsa, Allah ya kara hada kanku, ya shirya mana”
Kowa ya amsa addu'ar da Hajiya Binta ta yi da Ameen ban da Hajiya Kaltume da gume ma ya karye mata kamar wadda aka kwancewa zane a kasuwa. Daga bangaren Hajiya Kaltume Hajiya Binta ta fito ta shiga bangaren Momy suka gaisa sannan ta fito tana jin kewar Iyami. Sai addu'a take ma Appa idan dawowar Iyami alheri ce Allah ya daidaita tsakaninsu, ya kasa amsawa da ameen bayan kuma abun da yake nema kenan a zuciyarsa. Mota daya suka shiga Hurriya bayan ta dauko mayafinta, ita da Hajiya suka zauna a back seat, Appa da Hamad kuma suka shiga gaba, Appa yana jan motar suka fi daga gidan.
After mintuna goma da tafiyar Hajiya Binta, Momy ta fito tare da bakuwarta da kuma ɗanta da be ci komai ba a cikin abubuwan da Momy ta saka a shirya musu, Miwan na bayansu tare da dan'uwansa Musib sun yi ma bakuwar Momy da ďanta rakiya ban da Namra da har yanzu tana can bangaren Hajiya Kaltume.
“Captain ai yana yawan zuwa nan, duk lokacin da zai zo garin na ba ya tafiya sai ya shigo, ina jindadin haka Wallahi”
Hajiya Turai ta yi murmushi.
“Ai danki idan yana son mutum to ya huta, Allah ya hada jininku”
“Sosai kam, Allah dai ya nuna mana lokacin auren nan mu rakwashe”
Cewar Momy, Mutumen da aka ta maganar akansa be ce uffan ba ya fara sauko Entrance din hannu dafe a kirjinsa yana murza a hankali domin ba karamin zafi ya ji ba a lokacin da suka yi karo da Hurriya, taku daya biyu uku hudu yayi kamin ya ja ya tsaya yana kallon yadda tsaddadiyar motarsa ta yi ta kasa gaba daya, saboda tayun motar da aka succe duka hudu. Ya juyo ya kallesu.
“Waya taba motar nan?”
“Wace motar?”
Kusan a tare suka kalli motar Musib yayi sauri sauka ya karasa gurin motar da mamaki.
“Lafiya kalau kuka zo da ita?”
“Idan bata da lafiya zamu zo da ita ne? What kind of stupid question is this!”
“Subhanallahi, garin ya haka ta faru!”
Cewar Momy tana saukowa ta nufi gurin motar. Miwan ya ce
“Gaskiya wannan succe tayun aka yi”
“To waya aikata haka? Wannan dai rainin wayo ne da neman mutum yayi magana ace ya cika masifa”
Ya fada da karfi wani karin bacin dai na tunkarosa, cikin bakinciki ya sauka ta isa gurin motar. Momy ta kai hannu ta dafa karjikinsa.
“Kwantar da hankalinka Captain, a cikin yaran nan dai wani ba zai yi gigin yi maka haka ba, akwai dai matsalar da aka samu”
Momy na rufe Hajiya Turai ta miko masa hannu kamar wani karamin yaro dan yaye.
“Captain shigo ka zauna, sai mu shiga wata motar”
Ya sauke ajiyar zuciya tare da jan dagon numfashi ya fi sau goma, sannan ya shuri motar da kafarsa da karfi.
“Duk wanda yayi min haka da gangan yayi, saboda a bata min rai”
“Toh waye zai maka haka Captain? Dan Allah karka bata ranka, na gano, yanzu haka ba zai wuce bakar matar can ba Kaltume, domin na dade da lura da yar bakinciki ce ta karshe”
Momy tana maganar tana jin kamar ta yi tsalle taje ta shake wuyan Hajiya Kaltume.
“Oh kekam baki zaune cikin mutane kwarai Hajiya Nafisa, rayuwa a gidanku tana da wahala”
Momy ta amsawa Hajiya Turai tana kwafa.
“Barta na san yadda zan yi maganinta, da ni take zancen, Captain yi hakuri shigo ka huta sai ka dauki motata ku tafi da ita, idan an gyara wannan Musib zai kai maka ita gida”
Jameel ya juyo ya nufo hanyar falon, sai duk suka dugunzuma suka biyo bayansa, ban da Hajiya Turai da bata matsa daga inda take tsaye ba tun bayan da suka fito daga falon. Cikin natsuwa da kamala ya shiga falon, sai ka rantse ba shi ne ya gama bacin rai a waje ba, zaunawa yayi ya hade hannayensa ya sadda kai kasa ya rufe ido yana motsa bakinsa a hankali, kokari yake na ganin be bar bacin ransa ya ninku a zuciyarsa ba...
[10/20, 6:25 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣4️⃣
Namra ta dago ta dubi kofar shigowa falon tana amsa sallama, sai ta mike tsaye da sauri tana kallon Captain da mamaki, zuwansa a yanzu ya bata mamaki tsabanin baya da bata mamakin zuwansa domin ya saba zuwa gidan a duk lokacin aiki ya kawo shi ko ziya, tana mamakin zuwansa ne kasa da wata uku da faruwar abun da ya fusata shi, wato fasa masa tayun mota da Hamad yayi suke zaton Hajiya Kaltume ce ta saka aka aikata haka. Ba kasafai yake sake zuwa gurin da aka bata masa rai ba, idan ma zai sake komawa a gurin sai ya dauki lokaci mai tsawo har an manta da shi yake sake zuwa, wannan ya saka duk wani makusancinsa da yake son alaka da shi ta daure ko da iyayensa yake kokarin kiyaye duk wani abu da zai batawa dan gatan Ammy kuma ďa daya tilo ga Alhaji Aliyu Turaki. Wata kila haduwar jinin da Allah ya saka tsakanin Momy da ďan Yayanta ya wuce yayi mata haka. Fuska ba yabo ba fallasa ya shigo falon hannayensa duka biyu suna bayansa.
“Sannu da zuwa Ya... Captain”
Tunawa da ta yi baya son ace masa Yaya ya saka ta kasa karasa sai ta kiranshi da sunan da kowa yake kiransa.
“Yauwa hutawa kike?”
“Eh bari na kira Momy tana ciki”
Tana juyawa ya dakatar da ita.
“No Wait... Ina yarinyar nan take Namra?”
Ta juyo tana wara alamar bata fahimce wadda yake tambaya ba.
“Wata fara haka mai dan tsayi marar jiki, mai saka glasses”
“Oh Hurriya, tana bangaren Hajiya a kirata”
Ya daga mata kai, sai ta aje remote din hannunta ta nufi kofar fitar ta fice da sauri, da mamaki da tunanin dalilin kiran Hurriya ta isa bangaren Hajiya Kaltume, sai ta ci karo da Hurriya tana rike da tiyo tana watsawa motar Yasir ruwa, Hamad kuma na ta kada kumfa.
“Hurriya”
“Uhmm”
Ta juyo ta kalleta.
“Wai ki zo ana kiranki Captain...”
“Waye Captain...?”
“Ina wani wadda na ganku tsaye a bakin kofar Momy har na dauko miki glashinki da ya fashe? Kin tuna”
Hurriya ta yi shiru ta dan bata fuska, kuma ta kasa amsawa Namra da ta tuna ko ba ta tuna ba.
“Wanda ya mareki?”
Hamad ya tambaya, Hurriya ta daga masa kai Namra ta zaro ido domin bata saka ran marinta yayi ba, ta san dai akwai abun da yake faruwa.
“Au daman marinki yayi? Ikon Allah me kika masa?”
“Wucewa na zo yi ban gani ba muka yi karo shi ne ya mare ni har gilashina ya fashe”
“Ni kuma na fasa masa tayun mota duk biyu da wuka”
Namra ta rufe baki with mamaki. Hurriya ma masa kallon rashin jindadi fadar da yayi a yanzu.
“Daman kai ka fasa tayun nan? An kusan yaki a gidan nan fa saboda an fasa tayun Captain, Allah ya tsare ka Momy bata sani ba, da sai ka zama abun tausayi”
“Ni ina ruwana”
Ya fada yana turo baki.
“Captain akwai zafin zuciya ko shi zai iya maka hukunci babu ruwansa da alakarka a gidan nan, to yanzu dai shi ya ce a kiraki”
Hurriya ta ake tiyon kasa ta nufi fanfon ta kashe sannan ta bi bayan Namra, Hamad kuma ya cire hannayensa daga cikin kumfan da yake kadawa ya bi bayan Hurriya. Ita dai bata san ta masa laifi a yanzu ba balle ta yi zaton mari ne ko cin mutumci, sai idan kuma cewa za'ayi ta haifar masa da ciwon kirji saboda kanta ya bugi kirjinsa. Namra ce ta fara shiga sannan Hurriya sai kuma Hamad dake bayanta. Yana tsaye a gurin da Namra ta barshi sai dai wannan karon gefen kujerar da Namra ta tashi yake kallo ma'ana kofar falon ta koma gefensa na dama sabanin dazun da ya bata baya.
“Gata nan”
Namra ta fada, sannan ta zauna Hurriya ta karaso inda yake ta tsaya gabansa ta kalleshi sau daya ta sauke kai kasa, Hamad kuma yake tsaye kusa da kofar falon yana kallon ya ga abun da za'ayi ma yar'uwarsa. Captain ya maido ta hannayensa gaba ya mika mata box din da ke hannunsa da hannunsa na dama ba tare da ya ce komai ba. Ko be fada mata ba, ta san box din glasse ne domin shi dabam yake ta ka ganshi kana ganewa balle kuma ita da take 5&6 da glass. A hankali ta dago ta kalli fuskarsa bayan ta kalli gilashin sannan ta kalli Hamad ya watsa mata harara duk ya bi ya bata rai, domin har yanzu haushi Captain din yake ba shi, daman kuma shi be iya tsana ba idan ya tsane ka sai Allah ke kasa ku sake shiri da shi. Captain ya karkarata da kansa kadan ya kalli Hamad da sai a lokacin da ya san da shi tsaye a gurin sai kuma ya kalli Hurriya. Ita ma ta kalleshi ta dauke kai ta nufi kofar fita daga falon ba tare da ta ce masa Komai ba balle kuma har ta karba, sai da ta fara ficewa sannan Hamad ya bi bayanta yaja kofar falon ya rufe. Captain ya matse box din gilashin dake hannunsa da mugun karfi ya daga kansa sama ya rufe ido.
“Allah ya sassauta min kar na kashe yarinyar nan....”
‘Tab ka kasheta Wallahi kai ma sai an kashe ta dan gata be fi gata ba, ita ma yar gatan banbanta ce’
Namra ta fada a ranta a fili kuma sai ta ce.
“Glasse ne?”
Ya sauke kan ya kalleta.
“Wuka ce”
“Gilashin da Appa yake siya mata mai kyau ne daga waje ake kawo mata”
Ta fada a zahiri a badini kuma sai ta ce.
‘Captain dai kamar ka fi kowa iya bakar magana’
Kamar ta san zai kara mata.
“Wannan a bula na dauko shi”
“Tambaya ce kawai, daman ai na san Hamad ba zai bari ta karba ba, amman ka ba ni zan bata hakuri sai na bata daga baya”
Ya kai dayan hannunsa yana zagayen gilashin da shi.
“Waye Hamad?”
“Kanenta ne wanda ka ga ya tsaya jikin kofa har ta kalleshi, shi ne ya fasa maka tayun mota saboda ka mareta, ni ma ban sani ba sai yanzu yake fada”
Murmushi yayi mai sauti, ya dago ya kalleta ya sake yin murmushi mai cike da mamaki.
“Wow... Nice...”
“Haka ya kamata dan'uwa ya zama, mai kokarin kare yan'uwansa i like him”
Ya fada after yayi taking few seconds yana kallon wani bangare na falon, because he know yayi missing wani part na shi da be taba samu ba, wato yan'uwa da suka hada uwa ko uba ko ma uwa da uban gaba daya.
“Amman haka ba zai hana a hukunta shi ba, they have to pay for what they did”
Ya juya ya fice daga falon ba tare da ya nemi a kira masa Momy ba, daman kuma ba dan ita ya zo ba wannan karon, ya zo ne domin baya Hurriya gilashin da ya siyo Saudiya saboda ya fasa nata, and that slap da yayi mata ya tsaya masa after ya bar gidan saboda lura da yayi da bata gani sai da gilashin kamar yadda Namra ta tabbatar masa tun a wacan ranar. Namra ta san me yake nufi they instead of he, wato Hurriya saboda ta ki karbar gilashin Hamad kuma saboda ya fasa masa tayun mota. Sai da ta leka ta ga tashin motarsa sannan ta saki curtains din tana fadin.
“Ban da kai Captain ana kyauta dole ne, ko ni ce ai ba zan karba ba, ka yi zafin hannu ba wani uzuri da an maka abu sai zafin zuciya”
Ta nufi upstairs, sai da ta fara leka dakin Momy ta ga har lokacin bachi take sai ta ja mata kofar a hankali ta nufi dakinta.
HAJIYA KALTUME POV.
“Yanzu kina da number Salame?”
“Eh ina da ita, ai ko shekaran jiya ta zo gidan nan, har take min zancen Malamin ni dai ban tanka ta ba, domin damuwata ta isheni kar na yi abun kunya”
“Kunya Hajiya fatee? Tofar da yawu, har abada ba zamu taba kunyar duniya ba lahirar ma muna fatan nasara, saka number ki kirata ki ce ta turo miki number Malamin ko kuma idan ta samu lokaci ta shigo sai ku yi magana”
Hajiya Kaltume na rufe baki Hajja Fatee ta dauki waya ta shiga laleben number Salame. Knocking aka yi har sau biyu sannan Hajiya Fatee ta amsa.
“Waye?”
“Hajiya Yaron nan ne ya sake dawowa fa, kuma mai Baba mai gadi ya ce yayi yayi da shi amman ya ki tafiya shi sai ya ganki”
Hajiya Fatee ta hanye wayar ta rafka tagumi.
“Oh wannan fitinanne yaro ba zai bar ni da abun da ya ishe ni ba”
“Waye haka?”
“Wallahi wani yaro ne na dauka aikin ba fulawa ruwa, ashe barawo, ni ban sani ba, irin yaran nan yan sare sare, wata rana suka zo nemansa har da fasa mana gida aka ayi, tun daga lokacin sai na sallame shi, amman yaron nan ya ki ya rabu da ni, duk lokacin da wani abun ya same shi sai ya zo ya fada ko mai dadi ko marar dadi, ko kuma ya ce ya zo gaishe ni, yanzu ya bi ya fitine ni yau sati biyu kullum sai ya zo wai mahaifiyarsa bata da lafiya ni yake son gani”
“Ikon Allah toh ke Hajiya irin wadannan yaran ai suna da amfani wata rana”
“Hmmm baki san yadda suke fitinar mutum ba ne, ga su da shegen na ci idan sun ga samu”
“Bari na yi magana da shi, ki kira Salame yanzu”
Hajiya Kaltume ta mike tsaye tabur tabur ta fice daga dakin, Hajiya Fatee kuma ta shiga kiran Salame da wayarta.
“Ina yake?”
Hajiya Kaltume ta tambayi one of masu yi ma Hajiya Fatee aiki da ta zo sanar da Hajiya.
“Yana can gate”
“Muje na ganshi”
Mai aikin ta wuce gaba Hajiya ta sauko tana bin bayanta har suka fita falon suka isa gate ta tambayi mai gadin ina yake.
“Yana waje Hajiya kullum sai ya zo kuma ita Hajiya ta ce kar a barshi ya shigo”
Ya bude mata karamar kofar gate din ta leka waje ta ganshi zaune daf da gate din, a take gabanta ya yanke ya fadi domin ya tuna mata da lokacin da suke cikin daji hannun yan ta'adda, ga fuskarsa duk tambo alamar ya sha sara
Showing 39001 words to 42000 words out of 46312 words
“Sannu da zuwa Hajiya, ai da ma baki zo ba, ga kafafuwa suna ciwo ni kaina idan na warware ai sai na zo na gaishe ki, kuma ai kin kira waya haka ma ya wadatar”
“Aa kara dai na zo, fatar na same ku lafiya”
“Lafiya Kalau Alhamdulillah, ya ciwon kafafuwan yayi sauki?”
“Alhamdulillah”
Sama sama dai suka yi ta gaisawa Appa na zaune kusa da Hajiyarsa daga kasa, Hajiya Kaltume kuma na daga kan kujera ita da duka yaranta, Hurriya da Hamad ne kadai a kasa domin haka Amma ta koya musu idan babba yana kan gado ko kujera to su kuma su zauna a kasa, kar su zauna tare da shi ko kuma a yadda yake zaune. Da hira ta yi hira ne Hajiya Kaltume ta dauko zancen wahalar da suka sha a dajin tana fadar yadda aka rika mistreated dinsu kamar wasu dabbobi.
“Shiyasa ake son a samu soji masu kishin kasa da za su iya yakarsu idan ba haka ba, kasar nan da wahala ta gyaru domin Shugabannin ma sun zama sai a hankali”
Cewar Yasir. Cikin murmushi Hajiya Binta ta kalli Hamad ta ce.
“Da yardar Allah Hamad soja zai yi, wannan fushi da zuciyar ta soja ce”
Hamad ya girgiza kai.
“Aa ba soja nake so ba?”
Namra ta ce.
“To me kake so? Wannan zuciyar taka Hamad ai soja ya dace da kai”
“Aa ni Likitan idanu nake son zama, idan na kware zan yi ma Hurriya aiki ta, ita ma ta rika gani kamar kowa”
Tsit katon falon na Hajiya Kaltume yayi domin babu wanda ya za ci abun da zai fito daga bakin Hamad kenan. Hurriya ta yi murmushi tana masa kallo irin na so da kaunar dan'uwa, ita kanta ba yi zaton Hamad yana sonta kuma ya kula da damuwarta har haka ba.
“Come here my friend”
Yasir ya mika masa hannu, sai ya taso ya iso gurin Yasir din Yasir ya rumgume yana buga bayansa.
“Yayi kyau babban mutum”
Cikin jindadi da alfahari Appa ya kalli Hamad ya ce.
“Da yardar Allah da yardar Allah, Hamad ba zaka yi karatu a kasar nan ba, waje zan kai ka ka sha ilmin akan idanuwa har ka gaji, da ikon Allah wannan kudirin naka sai ya cika ko da bana raye”
Hajiya Kaltume da ta rasa abun da zata yi ta kalli Appa da murmushin dole.
“Za a karya dokar fitar da yara waje karatu kenan Alhaji akan Hamad?”
“In Shaa Allah, ba shi kadai ba Hurriya ma ba zata yi karatu a kasar nan ba, yadda take da kokarin nan waje ya kamata ta yi karatu, kuma ko ba ni ba Principal dinsu ya fada min suna sa ran da zarar ta gama secondary school zata samu scholarship mai kyau a manya kasasshe saboda kokarinta da yadda take cin gasa ta bangaren lissafi”
“Maa Sha Allahu, Allah ya nuna mana yara masu albarka Allahu akbar Allah dai yayi albar....ya bar zumunci”
Sai ta kasa karasa da Allah yayi albarka ta canja zuwa Allah ya bar zumunci, domin ta san hausawa sun ce addu'ar makiyi karɓaɓɓiya ce, ita ko ba zata so su yi albarka ba. Gashi abun da Appa ya fada cewar yaran Iyami za su karatu a waje ya daki zuciyarta mugun daka irin dakan da ace mashi ne, babu abun da zai hana ya bullo ta bayanta, yanayinta ma gaba daya sai ya sauya hankalinta yayi mugun tashi, ba dan ta yaki zuciyarta ba wata kila ma da ta rasa sukuninta har kowa ya gane halin da take ciki.
“Allah sarki dan'uwa mai kaunar yar'uwarsa, duk da fadan nan da kuke da rashin jituwa wannan soyayyar da kaunar tana nan a zuciyarsa, Allah ya kara hada kanku, ya shirya mana”
Kowa ya amsa addu'ar da Hajiya Binta ta yi da Ameen ban da Hajiya Kaltume da gume ma ya karye mata kamar wadda aka kwancewa zane a kasuwa. Daga bangaren Hajiya Kaltume Hajiya Binta ta fito ta shiga bangaren Momy suka gaisa sannan ta fito tana jin kewar Iyami. Sai addu'a take ma Appa idan dawowar Iyami alheri ce Allah ya daidaita tsakaninsu, ya kasa amsawa da ameen bayan kuma abun da yake nema kenan a zuciyarsa. Mota daya suka shiga Hurriya bayan ta dauko mayafinta, ita da Hajiya suka zauna a back seat, Appa da Hamad kuma suka shiga gaba, Appa yana jan motar suka fi daga gidan.
After mintuna goma da tafiyar Hajiya Binta, Momy ta fito tare da bakuwarta da kuma ɗanta da be ci komai ba a cikin abubuwan da Momy ta saka a shirya musu, Miwan na bayansu tare da dan'uwansa Musib sun yi ma bakuwar Momy da ďanta rakiya ban da Namra da har yanzu tana can bangaren Hajiya Kaltume.
“Captain ai yana yawan zuwa nan, duk lokacin da zai zo garin na ba ya tafiya sai ya shigo, ina jindadin haka Wallahi”
Hajiya Turai ta yi murmushi.
“Ai danki idan yana son mutum to ya huta, Allah ya hada jininku”
“Sosai kam, Allah dai ya nuna mana lokacin auren nan mu rakwashe”
Cewar Momy, Mutumen da aka ta maganar akansa be ce uffan ba ya fara sauko Entrance din hannu dafe a kirjinsa yana murza a hankali domin ba karamin zafi ya ji ba a lokacin da suka yi karo da Hurriya, taku daya biyu uku hudu yayi kamin ya ja ya tsaya yana kallon yadda tsaddadiyar motarsa ta yi ta kasa gaba daya, saboda tayun motar da aka succe duka hudu. Ya juyo ya kallesu.
“Waya taba motar nan?”
“Wace motar?”
Kusan a tare suka kalli motar Musib yayi sauri sauka ya karasa gurin motar da mamaki.
“Lafiya kalau kuka zo da ita?”
“Idan bata da lafiya zamu zo da ita ne? What kind of stupid question is this!”
“Subhanallahi, garin ya haka ta faru!”
Cewar Momy tana saukowa ta nufi gurin motar. Miwan ya ce
“Gaskiya wannan succe tayun aka yi”
“To waya aikata haka? Wannan dai rainin wayo ne da neman mutum yayi magana ace ya cika masifa”
Ya fada da karfi wani karin bacin dai na tunkarosa, cikin bakinciki ya sauka ta isa gurin motar. Momy ta kai hannu ta dafa karjikinsa.
“Kwantar da hankalinka Captain, a cikin yaran nan dai wani ba zai yi gigin yi maka haka ba, akwai dai matsalar da aka samu”
Momy na rufe Hajiya Turai ta miko masa hannu kamar wani karamin yaro dan yaye.
“Captain shigo ka zauna, sai mu shiga wata motar”
Ya sauke ajiyar zuciya tare da jan dagon numfashi ya fi sau goma, sannan ya shuri motar da kafarsa da karfi.
“Duk wanda yayi min haka da gangan yayi, saboda a bata min rai”
“Toh waye zai maka haka Captain? Dan Allah karka bata ranka, na gano, yanzu haka ba zai wuce bakar matar can ba Kaltume, domin na dade da lura da yar bakinciki ce ta karshe”
Momy tana maganar tana jin kamar ta yi tsalle taje ta shake wuyan Hajiya Kaltume.
“Oh kekam baki zaune cikin mutane kwarai Hajiya Nafisa, rayuwa a gidanku tana da wahala”
Momy ta amsawa Hajiya Turai tana kwafa.
“Barta na san yadda zan yi maganinta, da ni take zancen, Captain yi hakuri shigo ka huta sai ka dauki motata ku tafi da ita, idan an gyara wannan Musib zai kai maka ita gida”
Jameel ya juyo ya nufo hanyar falon, sai duk suka dugunzuma suka biyo bayansa, ban da Hajiya Turai da bata matsa daga inda take tsaye ba tun bayan da suka fito daga falon. Cikin natsuwa da kamala ya shiga falon, sai ka rantse ba shi ne ya gama bacin rai a waje ba, zaunawa yayi ya hade hannayensa ya sadda kai kasa ya rufe ido yana motsa bakinsa a hankali, kokari yake na ganin be bar bacin ransa ya ninku a zuciyarsa ba...
[10/20, 6:25 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣4️⃣
Namra ta dago ta dubi kofar shigowa falon tana amsa sallama, sai ta mike tsaye da sauri tana kallon Captain da mamaki, zuwansa a yanzu ya bata mamaki tsabanin baya da bata mamakin zuwansa domin ya saba zuwa gidan a duk lokacin aiki ya kawo shi ko ziya, tana mamakin zuwansa ne kasa da wata uku da faruwar abun da ya fusata shi, wato fasa masa tayun mota da Hamad yayi suke zaton Hajiya Kaltume ce ta saka aka aikata haka. Ba kasafai yake sake zuwa gurin da aka bata masa rai ba, idan ma zai sake komawa a gurin sai ya dauki lokaci mai tsawo har an manta da shi yake sake zuwa, wannan ya saka duk wani makusancinsa da yake son alaka da shi ta daure ko da iyayensa yake kokarin kiyaye duk wani abu da zai batawa dan gatan Ammy kuma ďa daya tilo ga Alhaji Aliyu Turaki. Wata kila haduwar jinin da Allah ya saka tsakanin Momy da ďan Yayanta ya wuce yayi mata haka. Fuska ba yabo ba fallasa ya shigo falon hannayensa duka biyu suna bayansa.
“Sannu da zuwa Ya... Captain”
Tunawa da ta yi baya son ace masa Yaya ya saka ta kasa karasa sai ta kiranshi da sunan da kowa yake kiransa.
“Yauwa hutawa kike?”
“Eh bari na kira Momy tana ciki”
Tana juyawa ya dakatar da ita.
“No Wait... Ina yarinyar nan take Namra?”
Ta juyo tana wara alamar bata fahimce wadda yake tambaya ba.
“Wata fara haka mai dan tsayi marar jiki, mai saka glasses”
“Oh Hurriya, tana bangaren Hajiya a kirata”
Ya daga mata kai, sai ta aje remote din hannunta ta nufi kofar fitar ta fice da sauri, da mamaki da tunanin dalilin kiran Hurriya ta isa bangaren Hajiya Kaltume, sai ta ci karo da Hurriya tana rike da tiyo tana watsawa motar Yasir ruwa, Hamad kuma na ta kada kumfa.
“Hurriya”
“Uhmm”
Ta juyo ta kalleta.
“Wai ki zo ana kiranki Captain...”
“Waye Captain...?”
“Ina wani wadda na ganku tsaye a bakin kofar Momy har na dauko miki glashinki da ya fashe? Kin tuna”
Hurriya ta yi shiru ta dan bata fuska, kuma ta kasa amsawa Namra da ta tuna ko ba ta tuna ba.
“Wanda ya mareki?”
Hamad ya tambaya, Hurriya ta daga masa kai Namra ta zaro ido domin bata saka ran marinta yayi ba, ta san dai akwai abun da yake faruwa.
“Au daman marinki yayi? Ikon Allah me kika masa?”
“Wucewa na zo yi ban gani ba muka yi karo shi ne ya mare ni har gilashina ya fashe”
“Ni kuma na fasa masa tayun mota duk biyu da wuka”
Namra ta rufe baki with mamaki. Hurriya ma masa kallon rashin jindadi fadar da yayi a yanzu.
“Daman kai ka fasa tayun nan? An kusan yaki a gidan nan fa saboda an fasa tayun Captain, Allah ya tsare ka Momy bata sani ba, da sai ka zama abun tausayi”
“Ni ina ruwana”
Ya fada yana turo baki.
“Captain akwai zafin zuciya ko shi zai iya maka hukunci babu ruwansa da alakarka a gidan nan, to yanzu dai shi ya ce a kiraki”
Hurriya ta ake tiyon kasa ta nufi fanfon ta kashe sannan ta bi bayan Namra, Hamad kuma ya cire hannayensa daga cikin kumfan da yake kadawa ya bi bayan Hurriya. Ita dai bata san ta masa laifi a yanzu ba balle ta yi zaton mari ne ko cin mutumci, sai idan kuma cewa za'ayi ta haifar masa da ciwon kirji saboda kanta ya bugi kirjinsa. Namra ce ta fara shiga sannan Hurriya sai kuma Hamad dake bayanta. Yana tsaye a gurin da Namra ta barshi sai dai wannan karon gefen kujerar da Namra ta tashi yake kallo ma'ana kofar falon ta koma gefensa na dama sabanin dazun da ya bata baya.
“Gata nan”
Namra ta fada, sannan ta zauna Hurriya ta karaso inda yake ta tsaya gabansa ta kalleshi sau daya ta sauke kai kasa, Hamad kuma yake tsaye kusa da kofar falon yana kallon ya ga abun da za'ayi ma yar'uwarsa. Captain ya maido ta hannayensa gaba ya mika mata box din da ke hannunsa da hannunsa na dama ba tare da ya ce komai ba. Ko be fada mata ba, ta san box din glasse ne domin shi dabam yake ta ka ganshi kana ganewa balle kuma ita da take 5&6 da glass. A hankali ta dago ta kalli fuskarsa bayan ta kalli gilashin sannan ta kalli Hamad ya watsa mata harara duk ya bi ya bata rai, domin har yanzu haushi Captain din yake ba shi, daman kuma shi be iya tsana ba idan ya tsane ka sai Allah ke kasa ku sake shiri da shi. Captain ya karkarata da kansa kadan ya kalli Hamad da sai a lokacin da ya san da shi tsaye a gurin sai kuma ya kalli Hurriya. Ita ma ta kalleshi ta dauke kai ta nufi kofar fita daga falon ba tare da ta ce masa Komai ba balle kuma har ta karba, sai da ta fara ficewa sannan Hamad ya bi bayanta yaja kofar falon ya rufe. Captain ya matse box din gilashin dake hannunsa da mugun karfi ya daga kansa sama ya rufe ido.
“Allah ya sassauta min kar na kashe yarinyar nan....”
‘Tab ka kasheta Wallahi kai ma sai an kashe ta dan gata be fi gata ba, ita ma yar gatan banbanta ce’
Namra ta fada a ranta a fili kuma sai ta ce.
“Glasse ne?”
Ya sauke kan ya kalleta.
“Wuka ce”
“Gilashin da Appa yake siya mata mai kyau ne daga waje ake kawo mata”
Ta fada a zahiri a badini kuma sai ta ce.
‘Captain dai kamar ka fi kowa iya bakar magana’
Kamar ta san zai kara mata.
“Wannan a bula na dauko shi”
“Tambaya ce kawai, daman ai na san Hamad ba zai bari ta karba ba, amman ka ba ni zan bata hakuri sai na bata daga baya”
Ya kai dayan hannunsa yana zagayen gilashin da shi.
“Waye Hamad?”
“Kanenta ne wanda ka ga ya tsaya jikin kofa har ta kalleshi, shi ne ya fasa maka tayun mota saboda ka mareta, ni ma ban sani ba sai yanzu yake fada”
Murmushi yayi mai sauti, ya dago ya kalleta ya sake yin murmushi mai cike da mamaki.
“Wow... Nice...”
“Haka ya kamata dan'uwa ya zama, mai kokarin kare yan'uwansa i like him”
Ya fada after yayi taking few seconds yana kallon wani bangare na falon, because he know yayi missing wani part na shi da be taba samu ba, wato yan'uwa da suka hada uwa ko uba ko ma uwa da uban gaba daya.
“Amman haka ba zai hana a hukunta shi ba, they have to pay for what they did”
Ya juya ya fice daga falon ba tare da ya nemi a kira masa Momy ba, daman kuma ba dan ita ya zo ba wannan karon, ya zo ne domin baya Hurriya gilashin da ya siyo Saudiya saboda ya fasa nata, and that slap da yayi mata ya tsaya masa after ya bar gidan saboda lura da yayi da bata gani sai da gilashin kamar yadda Namra ta tabbatar masa tun a wacan ranar. Namra ta san me yake nufi they instead of he, wato Hurriya saboda ta ki karbar gilashin Hamad kuma saboda ya fasa masa tayun mota. Sai da ta leka ta ga tashin motarsa sannan ta saki curtains din tana fadin.
“Ban da kai Captain ana kyauta dole ne, ko ni ce ai ba zan karba ba, ka yi zafin hannu ba wani uzuri da an maka abu sai zafin zuciya”
Ta nufi upstairs, sai da ta fara leka dakin Momy ta ga har lokacin bachi take sai ta ja mata kofar a hankali ta nufi dakinta.
HAJIYA KALTUME POV.
“Yanzu kina da number Salame?”
“Eh ina da ita, ai ko shekaran jiya ta zo gidan nan, har take min zancen Malamin ni dai ban tanka ta ba, domin damuwata ta isheni kar na yi abun kunya”
“Kunya Hajiya fatee? Tofar da yawu, har abada ba zamu taba kunyar duniya ba lahirar ma muna fatan nasara, saka number ki kirata ki ce ta turo miki number Malamin ko kuma idan ta samu lokaci ta shigo sai ku yi magana”
Hajiya Kaltume na rufe baki Hajja Fatee ta dauki waya ta shiga laleben number Salame. Knocking aka yi har sau biyu sannan Hajiya Fatee ta amsa.
“Waye?”
“Hajiya Yaron nan ne ya sake dawowa fa, kuma mai Baba mai gadi ya ce yayi yayi da shi amman ya ki tafiya shi sai ya ganki”
Hajiya Fatee ta hanye wayar ta rafka tagumi.
“Oh wannan fitinanne yaro ba zai bar ni da abun da ya ishe ni ba”
“Waye haka?”
“Wallahi wani yaro ne na dauka aikin ba fulawa ruwa, ashe barawo, ni ban sani ba, irin yaran nan yan sare sare, wata rana suka zo nemansa har da fasa mana gida aka ayi, tun daga lokacin sai na sallame shi, amman yaron nan ya ki ya rabu da ni, duk lokacin da wani abun ya same shi sai ya zo ya fada ko mai dadi ko marar dadi, ko kuma ya ce ya zo gaishe ni, yanzu ya bi ya fitine ni yau sati biyu kullum sai ya zo wai mahaifiyarsa bata da lafiya ni yake son gani”
“Ikon Allah toh ke Hajiya irin wadannan yaran ai suna da amfani wata rana”
“Hmmm baki san yadda suke fitinar mutum ba ne, ga su da shegen na ci idan sun ga samu”
“Bari na yi magana da shi, ki kira Salame yanzu”
Hajiya Kaltume ta mike tsaye tabur tabur ta fice daga dakin, Hajiya Fatee kuma ta shiga kiran Salame da wayarta.
“Ina yake?”
Hajiya Kaltume ta tambayi one of masu yi ma Hajiya Fatee aiki da ta zo sanar da Hajiya.
“Yana can gate”
“Muje na ganshi”
Mai aikin ta wuce gaba Hajiya ta sauko tana bin bayanta har suka fita falon suka isa gate ta tambayi mai gadin ina yake.
“Yana waje Hajiya kullum sai ya zo kuma ita Hajiya ta ce kar a barshi ya shigo”
Ya bude mata karamar kofar gate din ta leka waje ta ganshi zaune daf da gate din, a take gabanta ya yanke ya fadi domin ya tuna mata da lokacin da suke cikin daji hannun yan ta'adda, ga fuskarsa duk tambo alamar ya sha sara
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14 Chapter 15Chapter 16