Cikin annashuwa da ďaukin gani Momy take kallonta.
“Ai har ina cewa maybe ba zaki biyo ba, na ga Yamma ta yi”
Matar dake kawar da kai daga barin kallon aikin Momy dake jera mata kayan da aka shirya mata ta kalli Momy.
“Ai kin san halin Captain shi ya fi son tafiyar dare”
“Tare da shi kuka zo kenan? Amman be shigo ba?”
“Yana waje, waya yake”
“Oh Soyyayar da bata karewa, ai dai an kusa auren nan a huta, ke ma ki samu hutawa Ammy”
“Toh sai a taya mu da Addu'a Allah ya daidaita tsakaninsu”
Tana maganar tare da kai hannu ta dauko plate din grapes din da aka rolling ta cire ledar ta fara ci.
“Tsabani suka samu ne?”
Cikin mamaki Momy ta bukaci sani. Kamin ta bata amsa sai da ta juya ta kalli kofar dakin Momy da daya daga cikin masu aikinta taja.
“Wai har cikin daki kike barin masu aikinki suna shigowa?”
“Toh ya zan yi Hajiya Turai? Kin san dai ba zan yi aiki da kaina ba, dole su zan saka”
“Ai ni iyakacina da mai aiki falo sai kitchen da haraba, har yaushe mai aiki ta yi matsayin shigo min bedroom? Kina gani ai idan kika je gidana, su Larai ke kula min da daki”
“Toh ni wa zan saka? Ke ai kina rikon su Larai da Aliya”
“Wannan yar mijin na ki da kika fada min ta dawo nan hutu ta zo yi? Idan ma baki sonta sai ki duba a cikin dangi ki dauko wadda zata iya kula miki da daki, amman ba dai masu aiki ba”
“Zan duba a dangi, yar miji ina sakata za ace bana kaunarta”
Hajiya Turai ta yi murmushi mai sauti tana mamakin sakarcin Momy domin a gurinta abun da Momy take fada ko take gi sakarci ne.
“Ke ma dai ban da abun ki Hajiya Nafisa waya taba son ɗa ko ƴar kishiya? Ai ba wani boye boye, ba zan hana ka aure ba amman fa ba zan so matarka da ƴaƴanta ba”
“Ai Wallahi Hajiya Turai ba karamin sa'a kike yi ba, da yayana baya sha'awar aure-aure, ba kamar nawa mijin ba, domin ni ko a yanzu da ya saki Iyami tunani nake ko dai ta dawo ko kuma ya auro wata”
“Shi ne banbancin tashi a gidan arziki da kuma cintar arzikin, da ace mijinki ma kamar tashin Engr ne, da ba zai yi wannan aure-aurenba, ai talauci mugun abu ne, da zarar sun ga sun yi kudi sai su ga babu abun da ya dace da su kamar aure, amman Engr kam ai rayuwarta turawace da shi, babu ruwansa da wannan hange-hange”
“Wallahi ya huta, da alama ma ďana halinsa zai gado”
Hajiya Turai ta tabe tana girgiza kai cike da kasaita.
“Hmmm Captain? Ai idan ba Allah ya sauya masa hali ba, da wahala ma ya iya zaman da mata, yanzu ma addu'a muke kar ya ce ya fasa auren, shiyasa na ce ban yarda ya zauna ko'ina ba sai a kusa da ni”
Momy ta kasa dariya.
“Haba dai Hajiya Turai”
“Hajiya Nafisa kin manta halin ďan naki? Wannan mugun fushi da bakar zuciyar ta Captain tsoro take ba ni, komai aka yi masa a duniya ba a masa daidai, ko kallonsa kika yi zai iya cewa kallon ya wuce kima ya fara masifa ko ma ya ce hararasa kika yi, yadda kika san shaidan aka nade aka saka masa a zuciya haka, abu kadan sai masifa sai fushi baya iya controlling kansa, ga zafin hannu a family babu wanda be san halinsa ba, ita kanta yarinyar da zai aura yanzu, ba dan tana hakuri da shi ba da yanzu rabu da ita, da inda abun ya zo da sauki ita mai sanyi hali ce kuma tana gudun zuciyarsa”
“Toh ai sai a kiyaye, haka Allah yake son ganin kayansa, Captain murdaden mutum ne iya masa sai Allah”
“Ina ta addu'a dai Allah ya sauke masa wannan mugun fushi da bakar zuciyar, idan ba haka ba zaman auren ba zai jima ba, kuma ya fada min idan yayi wannan auren ba zai sake yi ba har abada, wai ko matarsa mutuwa ta yi ko suka rabu a haka zai zauna har karshen rayuwarsa, ni kuwa ba fatan haka nake ba, ni da nake son na yi ta ganin jikoki a makwafin ƴaƴan da Allah be ba ni ba”
“Gaskiya kam, muma muna son gani ai balle kuma ke da shi kadai kika haifa...”
Hajiya Turai na taba kayan marmarin suna hira da Momy har time ya fara ja, hakan kuma be saka sun yanke hirar ba har sai da Namra ta shigo turo kofar dakin ta shigo.
“Momy Hajiya ta iso”
Momy ta yatsina fuska domin ta san wace
Hajiyar ake magana, wato Hajiyar Binta surukarta uwar da ta haifi mijinta.
“Toh shi ne kuma sai an fada min? Kin san ai ba nan take fara zuwa ba sai ta gama da ko'ina take lekowa nan, to miye damuwata da ita, je ki fadawa masu aiki su kai mata abinci”
"Okay”
Ta juya ta fita. Momy ta yi tsargi da fuska.
“Idan ban je na gaisheta ba, sai ki ga ya shigo yana ta bala'i, alhalin ba so take ba, idan ta zo bata sauka bangaren kowa sai na Iyami, kuma sai ta fara shiga bangaren Kaltume sannan take leko nan”
“ikon Allah haka take ita kuma! Allah kyauta rayuwarku sai ku Hajiya Nafisa”
Cewar Hajiya Turai da kamar gatse tana jin ita duk ba zata iya daukar wannan ba, domin kowa yana da yancinsa. Namra na fitowa bedroom din Momy ta nufi dakin Hurriya ta tura kofar dakin, Hurriya na ji an taba kofar ta yi saurin juya fuskarsa ta boye kukanta.
“Hurriya Hajiyarki ta iso, Appa ya aiko Ya Musib ya fadawa Momy”
Hurriya ta share hawayenta da sauri ta juyo, sai gata ta sauko daga saman gadon bata ko kula Namra ba ta ratsa gefenta ta fice da gudu, duk wata dokar sauka ko hawa stairs na Momy manta su Hurriya ta yi a lokacin saboda zumudin zuwan Kakarta Hajiya Binta a gidan, kamar yau ne zata fara ganinta a gidan haka Hurriya ta ji. Da sauri ta bude kofar fita falon Momy bata kula komai ba ta saka kai zata fice, da mugun karfi ta ji kanta ya daki wani abu mai karfi har sai da ta yi baya kamar zata fadi. Dagowar da zata yi ta duba me ta buga domin be yi mata kama da karfe ko icce ba, ta ji an wanke mata fuska da lafiyayen marin da ya haddasa mata ganin wadansu kananan taurari, gilashin da yake mafaka ne a idonta ya fadi kasa, sai hudu da buji suka mamaye ilahirin idanuwanta. Sai ta tsaya cak irin tsayin da ta saba yi a duk lokacin da wani bakon al'amari ya ziyarceta.
Gafen fuskarta ya hau zugi yayi ja, idanuwanta suka masa tantance mutunen da ke tsaye a gabanta, fafadane ta ga hakan a cikin hudun idanuwanta, dogo ne irin tsayin da ta tsaya iyakar kirjinsa. A hankali ta sulale ta kai kasa ta saka hannayenta tana lalaben gilashinta hawaye na kwankwaso mata kofa. Lalabe ta yi ta yi amman ta kasa jin gilashin, kamar yadda ta duka haka ta mike tsaye a hankali ta juya ta lalabi kofar falon ta fara tafiya.
“Hurriya... Me ya same ki”
Namra ta tambaya tana nufota da sauri ta kama hannayenta ta rike domin hawaye take kamar an bude kofar fanfo.
“Ya... Ya... Namra... Gilashi... Na...”
Namra bata tsaya komai ba ta rika hannunta ta juya da ita suka fita tana janye da hannunta, har lokacin Mutumen da ya mareta yana a gurin tsaye ko yatsansa be motsa ba. Namra ta kalleshi kamin ta sako hannun Hurriya ta fara duba gilashin, can gefe ta hango shi ta nufi gurin da sauri ta dauko mata.
“Har gefen ido daya ya fashe daga sama, me ya faru Hurriya”
Ta saka mata gilashin da kanta, lokaci daya ganinta ya dawo fashewar da gilashin yayi ba irin wadda zai hanata gani ba ne, daga sama ne ya fashe shi ma kuma kadan. Hurriya ta daga ido ta kalli mutumen da be mata uzuri ba ya wanke fuskarta mai tsada da mari. Hawaye be daina mata zuba ba, hakan kuma be hana idanuwanta ganin mutumen da kyau, dubansa ta yi ta dube shi, ta sake dubansa sannan ta sauke idonta kasa ta ratsa gefensa ta fara sauka kasa. Slowly ya juya ya kalleta kamar mai son gasgata wani abu ko karyatawa.
“Bata gani sai da gilashi, me ya faru Yaya?”
Ya juyo ya kalli Namra a fusace.
“Aza min bindiga sai na fada miki”
Jinin jikinta ta sha ta kauce ta ba shi hanya ya shiga ciki, ita kuma ta ja kofar sannan ta bi bayan Hurriya domin gaishe da Hajiya Binta, kamar yadda Appa ya sabarwa kowa a gidan ko baka cikin gidan idan mahaifiyarsa ta zo matukar kana cikin garin sai ka zo ka gaisheta...
[10/18, 5:16 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣3️⃣
Da kallo ya bi Hurriya da Hamad har suka fice sannan ya kalli Hajiya Kaltume ya dauke kai ya nufi stairs. Yana shiga dakinsa abun da ya fara yi shi ne duba gurin da ya aje gilasan Hurriya, amman be ga ko daya ba, a nan ya fara tunanin ko ya canja musu gurin ajiya ya manta, haka ya bi komai na dakin ya duba ba gilasan babu alamarsu, fitowar yayi mamaki duk ya cika fuskarsa ya sauka kasa sai ya samu mahaifiyarsa a gurin da ya barta zaune sai dai wannan karon waya take amsawa, gefenta ya zauna a hannu kujera har sai da ta gama wayar sannan ya tambaye ko ta dauka.
“Me zan yi da gilasai kuma? Komai dai ni, ubanka ya dora min laifi matan ubanka su adabe ni kai kuma yanzu ka zarge ni da satar gilasan Hurriya saboda ga Kaltume makiyiyarta ko?”
Maganar Hajiya bata masa dadi ba kuma ya san duk wani kalami da zai dora bayan nata a yanzu ba zai fahimtar da ita. Dan haka ya tashi ba tare da ya sake cewa komai ba ya nufi dakin yan'uwa daya bayan daya ya bi yana tambayarsu kowacce tace masa bata dauka ba, Khairi har da hadawa da rantsuwa saboda ta fi kowa rashin tsoron Allah.
‘Toh ko Hurriya ta zo ta dauka ko Hamad ban sani ba?’
Ya tambayi kansa, sai dai ya san ba su taba masa haka ba, idan tana bukatar abu zata yi masa magana kuma idan ma ta dauka zata fada masa. Fitowa yayi daga bangaresu ya nufi bangaren Momy, kamar ance masa juya ka gani, yana juya ya kalli bangaren Appa sai ya hango Hurriya tsaye tare da Appanta ta rike hannunsa tana ta bata rai da alama makiya take masa kan wani abu. Fasa nufar bangaren Momy yayi sai ya nufi bangaren mahaifinsa domin tambayarta ko ta dauko gilashin be sani ba.
“Appa dan Allah daga wannan ba zaka sake yi ba”
Ta fada cike da shagwaba tana kara rike hannunsa.
“Haramun ne, ba kyau Hurriya ni bana sha'awar irin abubuwan nan”
Appa ya fada yana kallon Yasir da ya iso gurin fuska a sake.
“Me take so Appa?”
“Birthday kuma ka sa be da kyau ba al'adar mu ba ce hausawa wannan dabi'un turawa ne”
“Oh Appa yanzu kai ya waye fa, ba wani abun ba ne kawai dai ana samun tsabanin fahimta ne ga mutane, kuma yanzu zamani ya canja ba kamar lokacin baya ba”
“Ko zamani ya canja ni ban canja ba Yasir, abun da duk ba tarbiya ba bana sha'awar”
“Appa sau daya zamu yi fa, daga wannan ba zaka sake ba? Appa please kawaye na duk ana musu sai ni”
Tana maganar tana son yin kuka Appa yayi murmushi.
“Shi ke nan na ji, za a dafa shimkafa fara ayi sadaka”
Ta buga kafa daya a kasa tana kukan da babu hawaye, Yasir kuma ya saka dariya.
“Appa dan Allah dai Appa”
Ba kasai Hurriya take zuwa masa da bukata ba, kusan duk wata bukata da take gabatar masa da ita kidayayyyiya ce, hakan ya sak idan ta zo masa sai ya biya mata ko dan tausayinta da yake na lalurar dake tare da ita, balle kuma yanzu da tausayinta ya ninku a zuciyarsa saboda rashin Amma a gidan, sai yake ganin yaransa kamar wasu marayu da uwarsu ta mutu ta bar su.
“Na ji amman daga wannan ba za'a sake ba?”
Ta amsa da sauri tana tsalle.
“Na yarda Appa na yarda Allah ya saka da alheri, Appa Allah ya biya maka bukatunka na alheri ya rabaka da Hajiya Lafiya ya kara buda maka a kasuwanci ya kyautata karshenka”
Ta masa kwatankwacin addu'ar da Amma take masa idan yayi mata wani abun kyautata da ta ji dadi. Appa ya shafa kansa yana jin zuciyarsa da tausayin da be san na minene ba. Yasir ma murmushi yayi yana taya ta murna yadda Appansy ya amince da wuri.
“Bari mu fara neman Gift din da zamu bawa mai birthday”
“Har da kyauta ake badawa?”
Appa ya tambaya sai Yasir ya amsa masa.
“Eh Appa idan mutum yayi birthday ana ba shi kyau sosai ma, kowa da kalar abun da yake ba shi”
“Oh toh saboda ki ci kudinmu kike son yi birthday kenan?”
Cewar Appa yana kallonta da zolaya, sai ta saka dariya kamar ba ita ta rufe idonta.
“Appa ba da kai ba an yafe maka”
Shi ma dariyar yayi, ya bita da kallo domin tuni ta nufi bangaren Momy domin labartawa Hamad cewar Appa ya yarda zai mata birthday kamin ya isa gurin hawaye ya cika idonta domin ta saba idan aka mata albishir Amma take fara fadawa sai dai a yau babu Amma a gidan kuma ta san babu wanda zai taya ta farinciki da murna sai dan'uwanta. Tana ahiga falon sai ta ja ta tsaya tana kallon Musib da ya hada hannayen Hamad ya rike yana zabga masa mari.
“Ba zaka yi magana ba? Waye yaje ma fadawa Appa karya da gaskiya ya zo ya rufata ta fada? Tsakanin kai da Hurriya”
“Ni ce”
Ta amsa kai tsaye domin ba zata jure ganin ana duka dan'uwanta ba da yaki yayi magana kuma ya ki yayi kuka sai dai idanuwansa sun kada sun yi ja sosai sai wani cika yake yana batsewa alamar zuciyarsa ta gama kawowa.
“Okay zo nan bakar mufuka wato daga dawowarku za ku fara hada Momy fada da Appa ko?”
Bata zo ba kamar yadda ya bukata sai dai kuma bata matsa daga inda take tsaye ba ssi hawayen da ta shigo da su suka fara sauko mata, Hamad ya juya ya kalleta har lokacin be ce komai ba, daman tun shigowarsa falon Musib ya rike shi wai sai ya fada masa waya fadawa Appa gulma har ya shigo yana mata fada ta yi kukan, Hamad ta kafiya ya ki magana hakan ya saka Musib dukansa. Musib ya saki hannun Hamad ya nufi gurin da Hurtiya take tsaye ya fara kai mata duka sai ta boye fuskarta ta fara kuka, yadda Hamad ya nufo gurin da suke tsaye sai ka dauka zai yi dambe yayansa Musib ne, ficewa yayi daga falon Musib na kokarin rikoshi ya fisge ya fice da gudu, be zame ko'ina ba sai gurin da Garden din gidan yake ya samo manya manyan duwatsu ya dauko har uku ya fito da su ya nufi gurin da Motar Momy take ta fara jefan gilashin a take ya fasa mata gilashin mota ya koma dayan bangaren ya sake jefawa. Kamin yayi na uku Appa da Yasir da suke tsaye a gurin da Hurriya ta bar su, suka iso gurin da sauri domin sun lura da lokacin da ya dauko duwatsu sun san ba za'ayi mai kyau ba, Yasir yayi saurin rike Hamad.
“Kai miye haka?”
Sai a lokacin Hamad ya fashe da kuka yana maida magana.
“Ya Musib ya yi min mari hudu, kuma gashi can yana dukan Hurriya, wai ya ce mun yi munafurci mun hada Momt da Appa fada”
Appa da ransa ya bace saboda abun da Hamad aikata, a take abun da ya fada ya gusar da bacin ran abun da Hamad yayi. Ya nufi falon fuska a hade Yasir dake rike da Hamad har lokacin yana ta zillo sai ya sake kwaso wasu duwatsun ya fasa motar ya bi bayan Appa. Da karfi Appa ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Hurriya duke kusa da kofar ta rufe fuskarta tana kuka marar sauti.
“Musib...!”
Appa ya aika masa da wani irin kira da karfin murya mai razanarwa. Musib dake boye kitchen ya fito baki kofar kitchen din yana amsa kiran muryarsa na rawa.
“Na'am...”
Appa ya taka ya karasa har inda yake ya dauke shi da mari. Daidai lokacin da Momy ta sauko tare da Namra.
“Akwai wanda na taba duka cikinku? Akan wani dalili zaka dokesu? Kai da ya kamata ka ga wasu musguna musu ku shigar musu kai zaka saka hannu da kanka ka dokesu? Karka sake! Ina gargadinka ba su ba Hurriya da Hamad kadai ba duka yayana kar ka sake saka hannu ka dake su”
Appa ya juyo ya kalli Momy dake tsaye kamar hoto tsabar mamaki ya ce.
“Na rantse da Allah idan wani ya sake dokar min ƴaƴa sai na masa abun da zai yi bakinciki da na kasance ubansa, ban doka ba ba zan yarda wani ya dokar min ba”
“Saboda ƴaƴan Iyami ne?”
Momy ta tambaya tana jin wani tuƙuƙi a zuciyarta, shi kuma ya amsa mata ba dan suna ƴaƴan Iyami kaɗai ɓa sai dai baya daukar a zalinci kowa, amman saboda ta ji haushi sai ya amsa mata da haka.
“Eh saboda suna Ƴaƴan Iyami...”
Yana fadar hakan ya juya ya fice daga falon, a nan ma Yasir da har lokacin yana rike da Hamad dake ta jan numfashi da karfi saboda zuciya, ya rufa masa baya tare da Hamad din, Hurriya kuma da ta tuni kuka yayi mata bankwana ya tafi ya barta tsaye tana kallon dramar da ake ta bi Appa da kallo kamin ta juyo ta kalli Momy.
“Ba hakka, haka ne... Daman ance maza ke bude wata kofar wani lokacin yau na gani, kuma ya bude muku kofa,
Showing 30001 words to 33000 words out of 46312 words
Cikin annashuwa da ďaukin gani Momy take kallonta.
“Ai har ina cewa maybe ba zaki biyo ba, na ga Yamma ta yi”
Matar dake kawar da kai daga barin kallon aikin Momy dake jera mata kayan da aka shirya mata ta kalli Momy.
“Ai kin san halin Captain shi ya fi son tafiyar dare”
“Tare da shi kuka zo kenan? Amman be shigo ba?”
“Yana waje, waya yake”
“Oh Soyyayar da bata karewa, ai dai an kusa auren nan a huta, ke ma ki samu hutawa Ammy”
“Toh sai a taya mu da Addu'a Allah ya daidaita tsakaninsu”
Tana maganar tare da kai hannu ta dauko plate din grapes din da aka rolling ta cire ledar ta fara ci.
“Tsabani suka samu ne?”
Cikin mamaki Momy ta bukaci sani. Kamin ta bata amsa sai da ta juya ta kalli kofar dakin Momy da daya daga cikin masu aikinta taja.
“Wai har cikin daki kike barin masu aikinki suna shigowa?”
“Toh ya zan yi Hajiya Turai? Kin san dai ba zan yi aiki da kaina ba, dole su zan saka”
“Ai ni iyakacina da mai aiki falo sai kitchen da haraba, har yaushe mai aiki ta yi matsayin shigo min bedroom? Kina gani ai idan kika je gidana, su Larai ke kula min da daki”
“Toh ni wa zan saka? Ke ai kina rikon su Larai da Aliya”
“Wannan yar mijin na ki da kika fada min ta dawo nan hutu ta zo yi? Idan ma baki sonta sai ki duba a cikin dangi ki dauko wadda zata iya kula miki da daki, amman ba dai masu aiki ba”
“Zan duba a dangi, yar miji ina sakata za ace bana kaunarta”
Hajiya Turai ta yi murmushi mai sauti tana mamakin sakarcin Momy domin a gurinta abun da Momy take fada ko take gi sakarci ne.
“Ke ma dai ban da abun ki Hajiya Nafisa waya taba son ɗa ko ƴar kishiya? Ai ba wani boye boye, ba zan hana ka aure ba amman fa ba zan so matarka da ƴaƴanta ba”
“Ai Wallahi Hajiya Turai ba karamin sa'a kike yi ba, da yayana baya sha'awar aure-aure, ba kamar nawa mijin ba, domin ni ko a yanzu da ya saki Iyami tunani nake ko dai ta dawo ko kuma ya auro wata”
“Shi ne banbancin tashi a gidan arziki da kuma cintar arzikin, da ace mijinki ma kamar tashin Engr ne, da ba zai yi wannan aure-aurenba, ai talauci mugun abu ne, da zarar sun ga sun yi kudi sai su ga babu abun da ya dace da su kamar aure, amman Engr kam ai rayuwarta turawace da shi, babu ruwansa da wannan hange-hange”
“Wallahi ya huta, da alama ma ďana halinsa zai gado”
Hajiya Turai ta tabe tana girgiza kai cike da kasaita.
“Hmmm Captain? Ai idan ba Allah ya sauya masa hali ba, da wahala ma ya iya zaman da mata, yanzu ma addu'a muke kar ya ce ya fasa auren, shiyasa na ce ban yarda ya zauna ko'ina ba sai a kusa da ni”
Momy ta kasa dariya.
“Haba dai Hajiya Turai”
“Hajiya Nafisa kin manta halin ďan naki? Wannan mugun fushi da bakar zuciyar ta Captain tsoro take ba ni, komai aka yi masa a duniya ba a masa daidai, ko kallonsa kika yi zai iya cewa kallon ya wuce kima ya fara masifa ko ma ya ce hararasa kika yi, yadda kika san shaidan aka nade aka saka masa a zuciya haka, abu kadan sai masifa sai fushi baya iya controlling kansa, ga zafin hannu a family babu wanda be san halinsa ba, ita kanta yarinyar da zai aura yanzu, ba dan tana hakuri da shi ba da yanzu rabu da ita, da inda abun ya zo da sauki ita mai sanyi hali ce kuma tana gudun zuciyarsa”
“Toh ai sai a kiyaye, haka Allah yake son ganin kayansa, Captain murdaden mutum ne iya masa sai Allah”
“Ina ta addu'a dai Allah ya sauke masa wannan mugun fushi da bakar zuciyar, idan ba haka ba zaman auren ba zai jima ba, kuma ya fada min idan yayi wannan auren ba zai sake yi ba har abada, wai ko matarsa mutuwa ta yi ko suka rabu a haka zai zauna har karshen rayuwarsa, ni kuwa ba fatan haka nake ba, ni da nake son na yi ta ganin jikoki a makwafin ƴaƴan da Allah be ba ni ba”
“Gaskiya kam, muma muna son gani ai balle kuma ke da shi kadai kika haifa...”
Hajiya Turai na taba kayan marmarin suna hira da Momy har time ya fara ja, hakan kuma be saka sun yanke hirar ba har sai da Namra ta shigo turo kofar dakin ta shigo.
“Momy Hajiya ta iso”
Momy ta yatsina fuska domin ta san wace
Hajiyar ake magana, wato Hajiyar Binta surukarta uwar da ta haifi mijinta.
“Toh shi ne kuma sai an fada min? Kin san ai ba nan take fara zuwa ba sai ta gama da ko'ina take lekowa nan, to miye damuwata da ita, je ki fadawa masu aiki su kai mata abinci”
"Okay”
Ta juya ta fita. Momy ta yi tsargi da fuska.
“Idan ban je na gaisheta ba, sai ki ga ya shigo yana ta bala'i, alhalin ba so take ba, idan ta zo bata sauka bangaren kowa sai na Iyami, kuma sai ta fara shiga bangaren Kaltume sannan take leko nan”
“ikon Allah haka take ita kuma! Allah kyauta rayuwarku sai ku Hajiya Nafisa”
Cewar Hajiya Turai da kamar gatse tana jin ita duk ba zata iya daukar wannan ba, domin kowa yana da yancinsa. Namra na fitowa bedroom din Momy ta nufi dakin Hurriya ta tura kofar dakin, Hurriya na ji an taba kofar ta yi saurin juya fuskarsa ta boye kukanta.
“Hurriya Hajiyarki ta iso, Appa ya aiko Ya Musib ya fadawa Momy”
Hurriya ta share hawayenta da sauri ta juyo, sai gata ta sauko daga saman gadon bata ko kula Namra ba ta ratsa gefenta ta fice da gudu, duk wata dokar sauka ko hawa stairs na Momy manta su Hurriya ta yi a lokacin saboda zumudin zuwan Kakarta Hajiya Binta a gidan, kamar yau ne zata fara ganinta a gidan haka Hurriya ta ji. Da sauri ta bude kofar fita falon Momy bata kula komai ba ta saka kai zata fice, da mugun karfi ta ji kanta ya daki wani abu mai karfi har sai da ta yi baya kamar zata fadi. Dagowar da zata yi ta duba me ta buga domin be yi mata kama da karfe ko icce ba, ta ji an wanke mata fuska da lafiyayen marin da ya haddasa mata ganin wadansu kananan taurari, gilashin da yake mafaka ne a idonta ya fadi kasa, sai hudu da buji suka mamaye ilahirin idanuwanta. Sai ta tsaya cak irin tsayin da ta saba yi a duk lokacin da wani bakon al'amari ya ziyarceta.
Gafen fuskarta ya hau zugi yayi ja, idanuwanta suka masa tantance mutunen da ke tsaye a gabanta, fafadane ta ga hakan a cikin hudun idanuwanta, dogo ne irin tsayin da ta tsaya iyakar kirjinsa. A hankali ta sulale ta kai kasa ta saka hannayenta tana lalaben gilashinta hawaye na kwankwaso mata kofa. Lalabe ta yi ta yi amman ta kasa jin gilashin, kamar yadda ta duka haka ta mike tsaye a hankali ta juya ta lalabi kofar falon ta fara tafiya.
“Hurriya... Me ya same ki”
Namra ta tambaya tana nufota da sauri ta kama hannayenta ta rike domin hawaye take kamar an bude kofar fanfo.
“Ya... Ya... Namra... Gilashi... Na...”
Namra bata tsaya komai ba ta rika hannunta ta juya da ita suka fita tana janye da hannunta, har lokacin Mutumen da ya mareta yana a gurin tsaye ko yatsansa be motsa ba. Namra ta kalleshi kamin ta sako hannun Hurriya ta fara duba gilashin, can gefe ta hango shi ta nufi gurin da sauri ta dauko mata.
“Har gefen ido daya ya fashe daga sama, me ya faru Hurriya”
Ta saka mata gilashin da kanta, lokaci daya ganinta ya dawo fashewar da gilashin yayi ba irin wadda zai hanata gani ba ne, daga sama ne ya fashe shi ma kuma kadan. Hurriya ta daga ido ta kalli mutumen da be mata uzuri ba ya wanke fuskarta mai tsada da mari. Hawaye be daina mata zuba ba, hakan kuma be hana idanuwanta ganin mutumen da kyau, dubansa ta yi ta dube shi, ta sake dubansa sannan ta sauke idonta kasa ta ratsa gefensa ta fara sauka kasa. Slowly ya juya ya kalleta kamar mai son gasgata wani abu ko karyatawa.
“Bata gani sai da gilashi, me ya faru Yaya?”
Ya juyo ya kalli Namra a fusace.
“Aza min bindiga sai na fada miki”
Jinin jikinta ta sha ta kauce ta ba shi hanya ya shiga ciki, ita kuma ta ja kofar sannan ta bi bayan Hurriya domin gaishe da Hajiya Binta, kamar yadda Appa ya sabarwa kowa a gidan ko baka cikin gidan idan mahaifiyarsa ta zo matukar kana cikin garin sai ka zo ka gaisheta...
[10/18, 5:16 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣3️⃣
Da kallo ya bi Hurriya da Hamad har suka fice sannan ya kalli Hajiya Kaltume ya dauke kai ya nufi stairs. Yana shiga dakinsa abun da ya fara yi shi ne duba gurin da ya aje gilasan Hurriya, amman be ga ko daya ba, a nan ya fara tunanin ko ya canja musu gurin ajiya ya manta, haka ya bi komai na dakin ya duba ba gilasan babu alamarsu, fitowar yayi mamaki duk ya cika fuskarsa ya sauka kasa sai ya samu mahaifiyarsa a gurin da ya barta zaune sai dai wannan karon waya take amsawa, gefenta ya zauna a hannu kujera har sai da ta gama wayar sannan ya tambaye ko ta dauka.
“Me zan yi da gilasai kuma? Komai dai ni, ubanka ya dora min laifi matan ubanka su adabe ni kai kuma yanzu ka zarge ni da satar gilasan Hurriya saboda ga Kaltume makiyiyarta ko?”
Maganar Hajiya bata masa dadi ba kuma ya san duk wani kalami da zai dora bayan nata a yanzu ba zai fahimtar da ita. Dan haka ya tashi ba tare da ya sake cewa komai ba ya nufi dakin yan'uwa daya bayan daya ya bi yana tambayarsu kowacce tace masa bata dauka ba, Khairi har da hadawa da rantsuwa saboda ta fi kowa rashin tsoron Allah.
‘Toh ko Hurriya ta zo ta dauka ko Hamad ban sani ba?’
Ya tambayi kansa, sai dai ya san ba su taba masa haka ba, idan tana bukatar abu zata yi masa magana kuma idan ma ta dauka zata fada masa. Fitowa yayi daga bangaresu ya nufi bangaren Momy, kamar ance masa juya ka gani, yana juya ya kalli bangaren Appa sai ya hango Hurriya tsaye tare da Appanta ta rike hannunsa tana ta bata rai da alama makiya take masa kan wani abu. Fasa nufar bangaren Momy yayi sai ya nufi bangaren mahaifinsa domin tambayarta ko ta dauko gilashin be sani ba.
“Appa dan Allah daga wannan ba zaka sake yi ba”
Ta fada cike da shagwaba tana kara rike hannunsa.
“Haramun ne, ba kyau Hurriya ni bana sha'awar irin abubuwan nan”
Appa ya fada yana kallon Yasir da ya iso gurin fuska a sake.
“Me take so Appa?”
“Birthday kuma ka sa be da kyau ba al'adar mu ba ce hausawa wannan dabi'un turawa ne”
“Oh Appa yanzu kai ya waye fa, ba wani abun ba ne kawai dai ana samun tsabanin fahimta ne ga mutane, kuma yanzu zamani ya canja ba kamar lokacin baya ba”
“Ko zamani ya canja ni ban canja ba Yasir, abun da duk ba tarbiya ba bana sha'awar”
“Appa sau daya zamu yi fa, daga wannan ba zaka sake ba? Appa please kawaye na duk ana musu sai ni”
Tana maganar tana son yin kuka Appa yayi murmushi.
“Shi ke nan na ji, za a dafa shimkafa fara ayi sadaka”
Ta buga kafa daya a kasa tana kukan da babu hawaye, Yasir kuma ya saka dariya.
“Appa dan Allah dai Appa”
Ba kasai Hurriya take zuwa masa da bukata ba, kusan duk wata bukata da take gabatar masa da ita kidayayyyiya ce, hakan ya sak idan ta zo masa sai ya biya mata ko dan tausayinta da yake na lalurar dake tare da ita, balle kuma yanzu da tausayinta ya ninku a zuciyarsa saboda rashin Amma a gidan, sai yake ganin yaransa kamar wasu marayu da uwarsu ta mutu ta bar su.
“Na ji amman daga wannan ba za'a sake ba?”
Ta amsa da sauri tana tsalle.
“Na yarda Appa na yarda Allah ya saka da alheri, Appa Allah ya biya maka bukatunka na alheri ya rabaka da Hajiya Lafiya ya kara buda maka a kasuwanci ya kyautata karshenka”
Ta masa kwatankwacin addu'ar da Amma take masa idan yayi mata wani abun kyautata da ta ji dadi. Appa ya shafa kansa yana jin zuciyarsa da tausayin da be san na minene ba. Yasir ma murmushi yayi yana taya ta murna yadda Appansy ya amince da wuri.
“Bari mu fara neman Gift din da zamu bawa mai birthday”
“Har da kyauta ake badawa?”
Appa ya tambaya sai Yasir ya amsa masa.
“Eh Appa idan mutum yayi birthday ana ba shi kyau sosai ma, kowa da kalar abun da yake ba shi”
“Oh toh saboda ki ci kudinmu kike son yi birthday kenan?”
Cewar Appa yana kallonta da zolaya, sai ta saka dariya kamar ba ita ta rufe idonta.
“Appa ba da kai ba an yafe maka”
Shi ma dariyar yayi, ya bita da kallo domin tuni ta nufi bangaren Momy domin labartawa Hamad cewar Appa ya yarda zai mata birthday kamin ya isa gurin hawaye ya cika idonta domin ta saba idan aka mata albishir Amma take fara fadawa sai dai a yau babu Amma a gidan kuma ta san babu wanda zai taya ta farinciki da murna sai dan'uwanta. Tana ahiga falon sai ta ja ta tsaya tana kallon Musib da ya hada hannayen Hamad ya rike yana zabga masa mari.
“Ba zaka yi magana ba? Waye yaje ma fadawa Appa karya da gaskiya ya zo ya rufata ta fada? Tsakanin kai da Hurriya”
“Ni ce”
Ta amsa kai tsaye domin ba zata jure ganin ana duka dan'uwanta ba da yaki yayi magana kuma ya ki yayi kuka sai dai idanuwansa sun kada sun yi ja sosai sai wani cika yake yana batsewa alamar zuciyarsa ta gama kawowa.
“Okay zo nan bakar mufuka wato daga dawowarku za ku fara hada Momy fada da Appa ko?”
Bata zo ba kamar yadda ya bukata sai dai kuma bata matsa daga inda take tsaye ba ssi hawayen da ta shigo da su suka fara sauko mata, Hamad ya juya ya kalleta har lokacin be ce komai ba, daman tun shigowarsa falon Musib ya rike shi wai sai ya fada masa waya fadawa Appa gulma har ya shigo yana mata fada ta yi kukan, Hamad ta kafiya ya ki magana hakan ya saka Musib dukansa. Musib ya saki hannun Hamad ya nufi gurin da Hurtiya take tsaye ya fara kai mata duka sai ta boye fuskarta ta fara kuka, yadda Hamad ya nufo gurin da suke tsaye sai ka dauka zai yi dambe yayansa Musib ne, ficewa yayi daga falon Musib na kokarin rikoshi ya fisge ya fice da gudu, be zame ko'ina ba sai gurin da Garden din gidan yake ya samo manya manyan duwatsu ya dauko har uku ya fito da su ya nufi gurin da Motar Momy take ta fara jefan gilashin a take ya fasa mata gilashin mota ya koma dayan bangaren ya sake jefawa. Kamin yayi na uku Appa da Yasir da suke tsaye a gurin da Hurriya ta bar su, suka iso gurin da sauri domin sun lura da lokacin da ya dauko duwatsu sun san ba za'ayi mai kyau ba, Yasir yayi saurin rike Hamad.
“Kai miye haka?”
Sai a lokacin Hamad ya fashe da kuka yana maida magana.
“Ya Musib ya yi min mari hudu, kuma gashi can yana dukan Hurriya, wai ya ce mun yi munafurci mun hada Momt da Appa fada”
Appa da ransa ya bace saboda abun da Hamad aikata, a take abun da ya fada ya gusar da bacin ran abun da Hamad yayi. Ya nufi falon fuska a hade Yasir dake rike da Hamad har lokacin yana ta zillo sai ya sake kwaso wasu duwatsun ya fasa motar ya bi bayan Appa. Da karfi Appa ya tura kofar falon ya shiga sai ya samu Hurriya duke kusa da kofar ta rufe fuskarta tana kuka marar sauti.
“Musib...!”
Appa ya aika masa da wani irin kira da karfin murya mai razanarwa. Musib dake boye kitchen ya fito baki kofar kitchen din yana amsa kiran muryarsa na rawa.
“Na'am...”
Appa ya taka ya karasa har inda yake ya dauke shi da mari. Daidai lokacin da Momy ta sauko tare da Namra.
“Akwai wanda na taba duka cikinku? Akan wani dalili zaka dokesu? Kai da ya kamata ka ga wasu musguna musu ku shigar musu kai zaka saka hannu da kanka ka dokesu? Karka sake! Ina gargadinka ba su ba Hurriya da Hamad kadai ba duka yayana kar ka sake saka hannu ka dake su”
Appa ya juyo ya kalli Momy dake tsaye kamar hoto tsabar mamaki ya ce.
“Na rantse da Allah idan wani ya sake dokar min ƴaƴa sai na masa abun da zai yi bakinciki da na kasance ubansa, ban doka ba ba zan yarda wani ya dokar min ba”
“Saboda ƴaƴan Iyami ne?”
Momy ta tambaya tana jin wani tuƙuƙi a zuciyarta, shi kuma ya amsa mata ba dan suna ƴaƴan Iyami kaɗai ɓa sai dai baya daukar a zalinci kowa, amman saboda ta ji haushi sai ya amsa mata da haka.
“Eh saboda suna Ƴaƴan Iyami...”
Yana fadar hakan ya juya ya fice daga falon, a nan ma Yasir da har lokacin yana rike da Hamad dake ta jan numfashi da karfi saboda zuciya, ya rufa masa baya tare da Hamad din, Hurriya kuma da ta tuni kuka yayi mata bankwana ya tafi ya barta tsaye tana kallon dramar da ake ta bi Appa da kallo kamin ta juyo ta kalli Momy.
“Ba hakka, haka ne... Daman ance maza ke bude wata kofar wani lokacin yau na gani, kuma ya bude muku kofa,
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11 Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16