har ya gaji, bakinsa baki kirin ido kamar an daka tarugu tsabar ja, jiki a murda kamar gashin kansa, kana ganinsa ka ga rikakken dan ta'adda.
“Kai ne kake neman Hajiya Fatee?”
Hajiya Kaltume ta tambaya cikin karfi hali domin zuciyarta har wani zillo take.
“Ni ne Allah ya taimakeki, Hajiya Wallahi ina cikin matsala ne, su kuma wadan nan watsatsin masu aikin kullum na zo sai su hana ni shiga, ba dan ina ganin mutumcin Hajiya Fatee ba da yanzu na farka cikin mai gadin nan Wallahi, sai dai Hajiya tana da kima a idona kamar uwa take a gurina ba zan iya haka ba”
Magana yake da irin muryar mazan nan da shaye shaye ya gama canja kalar muryarsu ta koma mai ban tsoro. Hajiya Kaltume ta yi murmushin karfin hali.
“Ka kyauta haka ake so ai, ya sunan ka?”
“Sunana Isiyaku, amman dai wasu kan ce min Danja yan sunanayen nan dai na zamani Hajiya”
“Toh Amman me kake so gurin Hajiya?”
A take ya fara kuka kamar wani yaro ko wawa kukan da babu hawaye sai zallar iskanci.
“Hajiya Gyatuma aka kwatar a asibiti, kuma ba ni da ko sisin na magani, ita Hajiya Fatee ta sani ba na wani aiki bana sana'ar komai tun da na bar gidan nan ban sake samun wani aikin ba, ina cikin matsala bana da gata sai Allah sai Hajiya Fatee so nake ta taimaka min da kudin magani, kar gyatuma ta mutu Wallahi Allah akwai matsala idan ta mutu ba a taimaka min ba, duk mai hannu a ciki sai na ci uwatar...”
Yana fada yana hada hannu biyu ya buga, Hajiya Kaltume ta dan ja baya sannan ta kalli mai aikin ta ce.
“Zaki iya tafiya”
Sai da mai aikin ta yi nisa sannan ta taka kafarta ta fito daga cikin gidan ta taka nesa da gate din yadda mai gadin ba zai ji abun da zata fada ba. Sannan ta tsaya ta kalli Danja ta ce.
“Nawa ne kudin maganin?”
“Toh Hajiya dubu talatin ne, amman dai ko dubu biyu ko biyar aka taimaka min da su duk taimako ne”
“Kana da account”
“Akwai account Hajiya amman bana da shi aka Wallahi, kwanyar ce mun sha miyar kuka, daddawa duk ta kwashe basirar, tuwon dawa ma haka ake baza mana shi a ture, kai mun ci wuya Wallahi ga talaucin nan har yanzu be bar mu ba”
Hajiya Kaltume ta yi dariya har lokacin tsoro be fice ta ba, domin muryarsa ma abar tsoro ce balle kuma ka kalleshi.
“Kana da waya?”
Ya dan sosa kansa ya shafa aljihu.
“Wayar ce Hajiya ko an siya idan ka ji eh ya ne tana damun cikinka dole mu siyar mu siye abinci, line ma dari da hansi na siyar da shi shekaranjiya”
“Toh yanzu idan ina son magana da kai za mu yi kenan?”
“Ki fada min gidanki kawai zan zo na sameki har dakinki”
“Aa ni da Hajiya Fatee duk ba mu gama warkewa daga damuwar da muka shiga ba, baka san yan ta'adda suka kama mu ba?”
“Kai na ji Hajiya, zuwana talatin gidan nan sai ace min bata nan, wai wasu ne suka kamata, da an fada min ba za a biya sisi ba zan karbota ni sai a ba ni kudin, akwai mutanenmu fa masu harkar kuma ni Wallahi jan wuya ne, bana inda bana iya shiga, karfe be fasa ni bundiga bata kama ni sai dai ayi min tambo, danjar nan da kika ji ance Hajiya ni fa danja ne, uban fitina kuma bana tsoron kowa”
“Kai zaka iya aikata komai kenan Danja?”
“Zan iya komai Hajiya mun zubar da hannaye mun cire kafa, rai ma mun wulgar da shi barzahu, Allah dai ya shirya mu kawai”
“Shiyasa Hajiya take tsoron ka, ni ma ina gudun na janyo ka jiki na jawa kaina matsala”
“Kai... Kuturi”
Ya rike baki.
“Wai Hajja Fatee tsorona take? Ita din ai uwa ce ba za a mata komai ba, wani ma be isa ya mata ba balle kuma ni, ba dan ita ba da yanzu na barar da hanjin masu aikin nan nata, alkur'ane da yanzu ka ga hanta ya lilo shushushushushuuuuuuu”
Ya nuna yadda hantar zata rika raea idan ya sareta.
“Toh yanzu dai zan shiga gida, zan aiko mai aiki da number wayata idan ka samu waya sai ka kira ni mu yi magana, amman dan Allah ka daina damun Hajiya Fatee da yawan zuwa”
“An gama amman Hajiya yanzu akwai wani abu nan? Ina fatar ke ma kina da yan abubuwa yan timatinmai eh... Eh.. Kin dai gane”
“Zan aiko mai number tare da kudin da zaka hau babur ka koma”
Tana fadin haka ta yi gaba tana nufi gate zata koma ciki, shi kuma ya bita da kirari yana daga mata hannu.
“Chau chau chau chachachau lafiya lau ne Hajiya, Allah dai ya kara miki kwanciyar hankali ya kara miki ƙiba kai kana ganin Hajiyar nan ka san akwai manyan kaya, Allah ya kara sutura”
Cikin gidan Hajiya Kaltume ta koma ta shiga dakin Hajiya Fatee ta samu biro ta mikawa Hajiya Fatee domin ita bata iya rubutun ba.
“Rubuta masa number ta a nan”
“Numberki kuma? Me ya faru? Karki jawa kanki matsala fa irin wadannan ba su jin magana”
“Ke dai rubuta babu komai, ke na ke yi ma jihadin ai, wayo yake masa”
Hajiya Fatee ta karba ta rubuta mata number ta mika mata. Hajiya Kaltume ta bude jakarta ta dauko 3k ta hade ta takardar ta fita falo ta bawa mai aikin ta umarce ta da ta kai masa. Sannan ta juyo ta dawo dakin tana tambayar Hajiya Fatee ya aka karkare da Salame.
“Na kirata na mata bayani, ta ce ai ya canja line saboda rufe masa wacan da masu gidan line suka yi, amman yanzu zata turo min sabuwa numbersa kuma zata kira ta masa bayani”
“Haka nake son ji, to yanzu ki kwnatar da hankali ki kira ki fada masa ya shirya komai na sa ya zo garin nan zamu aika da mota a dauko shi a kawo mana har gida, daga nan sai mu gabatar masa da matsakarmu”
“Amman kina ganin zai yarda ya zo?”
“Hajiya Fatee miye kudi ba zai yi ba? Muradi dai abashi kudi shi kuma ya biya mana bukata kawai”
“Ni dai Allah yasa cikin nan ya tausu, idan ba haka na zan shiga uku ga shegiyar suruka zata ji dadi”
“Komai zai wuce Hajiya Fatee ki kwanatar da hankali”
Cewar Hajiya Kaltume ga aminiyarta tana murmushi.
IYAMI POV. .
“Iyami ba a zama haka, ke kanki kin san mijinki yana sonki, ga yaya yanzu kuma ga cikin nan da kika shiga watan haihuwa, kamata yayi ki nemi taimako idan ma wani asirin aka yi masa aka rabaku a karya shi, ki koma dakinki bana son ki haihu a gida Wallahi”
Amma ta yunkura da katon cikinta ta tashi zaune daker tana kallon Hindu dake maganar.
“Hindu, Wallahi ban taba yi ba, su kansu da suke ganin kamar asiri na yi ma Alhaji yake ta so na ko na malleke shi, ban taba bada naira biyar na ce a mallake min Alhaji ba, tsantsar biyayya ne kawai da kawar da kai da kuma jin maganar duk abun da ya fada, ni yanzu ko zaki dora wuka a wuyana ba zan iya fada miki sunan Malami daya da na sani ba a garin nan, ban taba yi ba, Gwaggo ma bata taba ta yi ba mu ba mu da kowa sai Allah”
“Na sani, to ai tambaya ake kin ga har na tsarin jikinki sai ki sha kuma ki bawa yayanki, domin su ma ba barinsu zata yi ba”
“Ni dai ba zan iya ba, na kai kukana ga Allah shi zai min magana, ko yanzu ai ba yadda suke so suka samu ba, duk wata sai ya aiko min da abinci da kudi saboda cikin nan, yanzu kuma kina ganin yadda aka cika harabar gidan nan da itace saboda na shiga watan haihuwar, na san idan ra'ayinsu za a bi ba zasu so haka ba, yarana kuma idan ya auna lokaci ya kan aiko da su su gan ni na gansu, an rabu ne kawai amman kamar ana tare, idan Allah yayi zan koma sai ki ga na koma kamar yadda ban saka ran auren Alhaji ba Allah yayi kuma aka yi auren”
“Toh Allah yasa haka shi ya fi alheri, amman dai da kin tafi ba a san inda za a dace ba”
“Allah ya hada mu da dacewar”
“Ameen”
Ta amsa ba dan ta jidadin yadda Iyami ta ki amincewa da zuwan ba.
[10/20, 6:26 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣5️⃣
Salame na turo number Malamin Hajiya Fatee ta kira shi a waya, suka gaisa ta fada masa abubuwan da suka faru ya jajanta mata, ya kara mata da cewar shi ma layinsa aka rufe shiyasa bata ji shi ba. Hajiya Kaltume ya karba suka gaisa sannan ta dora masa da banin abun da ya sami Hajiya Fatee, daga karshe suka yanke ranar da zai shigo garin. Sannan Hajiya Fatee ta iya fita dakinta ta samu ruwan tea ta sha domin bata iya cin komai. Hajiya Katume bata jima a gidan ba Fadeel ya shigo gaishe da mahaifiyar, da zai fita Hajiya Kaltume ta bukaci ya sauke ta gida.
*** *** ***
Ba kadan ran Momy ya ba ce ba, jin cewar Captain ya zo gidan tana bachi, kuma ya fita da bacin rai saboda Hurriya.
“Oh to wai miye na siya mata gilashin ma?”
Namra ta aje spoon din hannunta.
“To nidai ranar da ya zo last na ganta da shi cirko cirko, gilashinta a kasa tana lalabe to shi ne yau take fada min ai marinta yayi saboda sun yi karo”
“Ai gara da mareta ma, yarinyar nan bata da hankali, sannan yanzu ya zo ta ki ta karbi box din wata kila ba zai sake dawowa gidan nan ba kuma, ta ja min ya fara fushi da ni kenan”
“Shi ma fa Captain din nan ya cika zuciya ga zafin hannu, amman dai bata kyauta ba da bata karba ba”
“Bar yar iska bata san su waye iyayensa ba ne shiyasa, shi ma dai miye na kawo mata glass ko makancewa ta yi iya ruwansa”
“Kila ya ga be kyauta ba, ko kuma...”
Momy ta kalleta da duba kyama.
“Ko kuma me? Allah ya kiyaye ai ko mata sun kare duniya Captain ba zai yi komai da wannan yar tatsitsiyar yarinyar na duka ma nawa take shekaranjiya ta yi 16yrs fa, kuma shi da yake da matar da zai aura”
“Toh ba sai idan anyi auren ba, wannan me bakar zuciyar? Ba kowa ce zata iya zama da shi ba”
“Ai ko fasawa aka yi sai dai ya aureki, daman Hajiya Turai ta so a hada wannan zumunci shi din ne ya ki, kuma kin san basa masa dole ”
“Ni”
Namra ta nuna kanta domin bata taba jin makamacin haka daga bakin Momy ba.
“Ke fa mun sha yin maganar da Hajiya Turai ai, amman shi Jameel din ne be yarda ba, yanzu dai ya samu wadda yake so an huta”
Namra bata ce komai ba ta maida idonta kan abincin da take ci tana motsa shi a hankali kamar mai tunani. Momy kuma ta tashi daga dinning din tana ta masifa saboda Namra bata tasheta daga bacci ba.
“Kiransa zan yi yanzu Allah yasa ya daga, kar wannan yar filfilwar ta jazamin masifa ni Nafisa”
Nan ma Namra bata ce komai b ta cigaba da motsa abinci tana tauna wanda yake bakinta ta kasa hadewa sai tunani take. Kamin ta juyo ta kalli falon da aka bude, Hurriya ce ta shigo kanta ba dankwali rabin kan nata a tsire.
“Yi sauri ki dauki abun da zaki dauka ki fice kamin Momy ta fito, dan na san sai ta miki fadan kin karbar box din da Captain ya baki”
“Abinci zan zuba”
Ta nuna abinci tana kallon stairs gabanta sai tsananta faduwa yake.
“Zo ki zuba”
Ta nufi dinning din da sauri ta dauki plate ta zuba abincin mutum biyu ita da Hamad ta saka naman kaza a sama ta dauki spoon biyu ta saka.
“Ke da Hamad zaku ci?”
“Eh”
“Dazun shi ya hana ki karbar glass din ko?”
“Na ga ya bata rai yana hararata, na san idan na karna zai iya min masifa kuma yayi fada ni, ko ya dukeni”
“Ke dai Hamad ya raina ki ya maida ke kamar kanwarsa, ko dan ya ganshi babba ke kuma ba ki ba”
Hurriya ta yi dariya mai sauti ta shiga Kitchen ta dauko tray ta dora ruwa da lemu a kai sannan ta fito ta dauki plate din abincin ta dora a tray ta dauka ta fice da sauri. A harabar Apartment din Hajiya Kaltume ta dawo ta zauna a balcony kusa da Hamad ta aje tray.
“Hamad zo mu ci abinci”
Ya kalli abinci sai ya bata rai.
“Waya ce ki hade? Waye zai ci abinci da ke to?”
“To ai ni ina sauri ne, Yaya Namra ta ce Momy nemana take zata min fada saboda ban karbi abun da bakonta ya ba ni ba”
“Toh ina ruwana ki je ki zuba wani”
Ya saka hannu ya dauke abincin da ba zai iya cinyewa shi kadai ba ta dora a cinyarsa.
“Idan ba zaka ci da ni ba, ba sai ka je ka debo na ka ba?”
“Ba zan ce ba, ni ki daina ba ni umarni”
“Wannan dai nawa ne ka ba ni abinci na Hamad”
Yayi mata kunne ne shege yana ta cin abinci ko kallonta be yi ba. Har ta tashi zata tafi debar wani sai kuma wata zuciyar tace mata Momy na nan falo, sai ta koma ta zauna ta dauki lemun ta sha tana ta kallonsa yana cin abinci. Ita ma dai kamar mantawa ta yi Hamad be cin abinci da kowa kuma be cin ragin kowa har da na Appansa da na Amma. Hakura ta yi ta saka masa ido ta can kuma ta ji ba zata iya ba tunawa da ta yi baya son gashi idan yana cin abinci sai ta cigaba da sifar kan tana kallonsa wai ko zai ji kyama ya aje abinci. Instead of yayi haka sai ya kifar da plate din ya riko gashin kan nata a daidai lokacin da Mota ta faka harabar Hajiya Kaltume. Da wani irin karfi yake fisgar gashi da karfi bata san lokacin da ta fara ihu tana rike hannunsa ba. Da sauri Fadeel ya bude motar be ko tsaya kashewa ba ya fito ya nufi inda suke daker ya banbanre hannun Hamad Hurriya ta koma bayansa da sauri tana kuka.
“Kai wannan ai sai ka tsinke mata gashin ka rage mata sadaki, miya hada ku?”
Hurriya bata iya magana saboda kuka, Hamad kuma ba gwanin maida magana ba ne daman sai cika yake kamar wani zaki. Hajiya Kaltume tana kawowa kusa da su ta ce
“Ai haka suke, uwa daya uba daya amman baya raga mata, basa zaman lafiya kamar Annabi da Kahiri suke”
Cikin mamaki Fadeel ya kalli Hamad.
“Wai kanwarsa ce yake mata wannan jan gashi haka?”
“Ita ce yayar ai, dan ka ganshi da girma shi ne kanen ai, baya ragawa kowa a gidan”
Hamad ya juyo yana watsawa hara Hajiya Kaltume dake korawa Fadeel bayani saboda ta tabo shi tun da ta ce be ragama kowa.
“Idan ba kai ba, wake fada da mata? Ba yayarka ba ce?”
Ya juyo ya kalli Hurriya da ta boya bayansa.
“Ke kuma ki rika kiyaye, yi hakuri ki daina zama babu dankwali ba kyau”
“Ai Allah yasa ma aljannu da ifiritai da shaidan duk su tattara su shige a cikin kan nata, ita ma ai ba karamar marar jin magana ba ce”
Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume dake fadar haka tare da yin gaba da bar su a gurin. Ta share hawayenta ta kalli Hamad sannan ta kalli Fadeel.
“Ina wuni”
Dariya yayi.
“Lafiya Kalau, Allah ya tsare gaba Hurera ko?”
“Hurriya”
Ta gyara masa.
“Yeah ki rufe kanki”
“Toh”
Ya juya ta sauka balcony din ya nufi motarsa dake kunne har lokacin sai da ya shiga motar daga mata hannu sai kallonta yake sannan yayi reverse ya fice.
Two Week Later....
Hajiya Fatee ta gyara zama ta kalli kawarta kamin ta kalli Malamin da suka sauka a garage din gidan.
“To yanzu Malam akwai yadda za'ayi a danne cikin nan kar ya bayyana? Kuma wannan tofe tofen yawun da kin cin abinci da nake ga kasala duk na daina shi?”
Malamin dake sanye da babbar riga ya kalli Hajiya Fatee yana murmushi.
“Za'a iya sosai kowa, ba yau na saba ba, za a iya danne cikin nan har tsawon shekarun da kike so”
“Alhamdulillah, ina son a danne min shi har nan da shekara dari, na san dai ba zan yi shekara dari a duniya ba”
“Ko kuma nan da lokacin da zaki yi aure ba, Hajiya yadda kike da surar nan Maa Shaa Allah, ai sai idan mutum be samu dama ba, shekarunki ba ba za a ce kin yi ba, ai na san ba za a rasa namema ba ko?”
Maganar yake yana dariya kamar wata abokiyar wasarsa.
“Aa kai aure kuma? Wake ta aure yanzu? Aa mun bar wa yara, ni dai yanzu bukatata a fara danne cikinki, idan an samu nasara hakan yayi sai a shiga yi Farraqu tsakanin yaron nan Fadeel da Matarsa Afrah domin ina kwana da bakincikinta a kullum Wallahi”
.“Babu Matsala Hajiya, za a danne ciki, matukar ba a daga dutsen da zamu saka layar mu rufe ba, cikin nan ba zai taba tashi ba har abada, amman fa zaki zuba kudi kam”
“Karka damu zan biya ka ko nawa ne, ammam dan Allah a saka dutsen a inda ba za a iya dagawa ba”
“Aljannu za mu saka su yi aikin, karki damu”
Hajiya Fatee ta kalli Kaltume suka yi murmushin jindadi sannan Hajiya Kaltume ta kora da nata bayanin.
“To ni Malam na ji shiru, kasan na baka kudi akan za ayi ma Iyami aiki ina son komai nata ya lalace amman har yanzu ba labari, kuma ni yanzu so nake a mallake min kowa a gidan nan daga mijina har Nafisa ikon kowa ya dawo karkashina, ina son Alhaji ya zama be iya aiwatar da komai sai abun da na fada masa, kuma ina son a shiga tsakaninsa da
Showing 42001 words to 45000 words out of 46312 words
“Kai ne kake neman Hajiya Fatee?”
Hajiya Kaltume ta tambaya cikin karfi hali domin zuciyarta har wani zillo take.
“Ni ne Allah ya taimakeki, Hajiya Wallahi ina cikin matsala ne, su kuma wadan nan watsatsin masu aikin kullum na zo sai su hana ni shiga, ba dan ina ganin mutumcin Hajiya Fatee ba da yanzu na farka cikin mai gadin nan Wallahi, sai dai Hajiya tana da kima a idona kamar uwa take a gurina ba zan iya haka ba”
Magana yake da irin muryar mazan nan da shaye shaye ya gama canja kalar muryarsu ta koma mai ban tsoro. Hajiya Kaltume ta yi murmushin karfin hali.
“Ka kyauta haka ake so ai, ya sunan ka?”
“Sunana Isiyaku, amman dai wasu kan ce min Danja yan sunanayen nan dai na zamani Hajiya”
“Toh Amman me kake so gurin Hajiya?”
A take ya fara kuka kamar wani yaro ko wawa kukan da babu hawaye sai zallar iskanci.
“Hajiya Gyatuma aka kwatar a asibiti, kuma ba ni da ko sisin na magani, ita Hajiya Fatee ta sani ba na wani aiki bana sana'ar komai tun da na bar gidan nan ban sake samun wani aikin ba, ina cikin matsala bana da gata sai Allah sai Hajiya Fatee so nake ta taimaka min da kudin magani, kar gyatuma ta mutu Wallahi Allah akwai matsala idan ta mutu ba a taimaka min ba, duk mai hannu a ciki sai na ci uwatar...”
Yana fada yana hada hannu biyu ya buga, Hajiya Kaltume ta dan ja baya sannan ta kalli mai aikin ta ce.
“Zaki iya tafiya”
Sai da mai aikin ta yi nisa sannan ta taka kafarta ta fito daga cikin gidan ta taka nesa da gate din yadda mai gadin ba zai ji abun da zata fada ba. Sannan ta tsaya ta kalli Danja ta ce.
“Nawa ne kudin maganin?”
“Toh Hajiya dubu talatin ne, amman dai ko dubu biyu ko biyar aka taimaka min da su duk taimako ne”
“Kana da account”
“Akwai account Hajiya amman bana da shi aka Wallahi, kwanyar ce mun sha miyar kuka, daddawa duk ta kwashe basirar, tuwon dawa ma haka ake baza mana shi a ture, kai mun ci wuya Wallahi ga talaucin nan har yanzu be bar mu ba”
Hajiya Kaltume ta yi dariya har lokacin tsoro be fice ta ba, domin muryarsa ma abar tsoro ce balle kuma ka kalleshi.
“Kana da waya?”
Ya dan sosa kansa ya shafa aljihu.
“Wayar ce Hajiya ko an siya idan ka ji eh ya ne tana damun cikinka dole mu siyar mu siye abinci, line ma dari da hansi na siyar da shi shekaranjiya”
“Toh yanzu idan ina son magana da kai za mu yi kenan?”
“Ki fada min gidanki kawai zan zo na sameki har dakinki”
“Aa ni da Hajiya Fatee duk ba mu gama warkewa daga damuwar da muka shiga ba, baka san yan ta'adda suka kama mu ba?”
“Kai na ji Hajiya, zuwana talatin gidan nan sai ace min bata nan, wai wasu ne suka kamata, da an fada min ba za a biya sisi ba zan karbota ni sai a ba ni kudin, akwai mutanenmu fa masu harkar kuma ni Wallahi jan wuya ne, bana inda bana iya shiga, karfe be fasa ni bundiga bata kama ni sai dai ayi min tambo, danjar nan da kika ji ance Hajiya ni fa danja ne, uban fitina kuma bana tsoron kowa”
“Kai zaka iya aikata komai kenan Danja?”
“Zan iya komai Hajiya mun zubar da hannaye mun cire kafa, rai ma mun wulgar da shi barzahu, Allah dai ya shirya mu kawai”
“Shiyasa Hajiya take tsoron ka, ni ma ina gudun na janyo ka jiki na jawa kaina matsala”
“Kai... Kuturi”
Ya rike baki.
“Wai Hajja Fatee tsorona take? Ita din ai uwa ce ba za a mata komai ba, wani ma be isa ya mata ba balle kuma ni, ba dan ita ba da yanzu na barar da hanjin masu aikin nan nata, alkur'ane da yanzu ka ga hanta ya lilo shushushushushuuuuuuu”
Ya nuna yadda hantar zata rika raea idan ya sareta.
“Toh yanzu dai zan shiga gida, zan aiko mai aiki da number wayata idan ka samu waya sai ka kira ni mu yi magana, amman dan Allah ka daina damun Hajiya Fatee da yawan zuwa”
“An gama amman Hajiya yanzu akwai wani abu nan? Ina fatar ke ma kina da yan abubuwa yan timatinmai eh... Eh.. Kin dai gane”
“Zan aiko mai number tare da kudin da zaka hau babur ka koma”
Tana fadin haka ta yi gaba tana nufi gate zata koma ciki, shi kuma ya bita da kirari yana daga mata hannu.
“Chau chau chau chachachau lafiya lau ne Hajiya, Allah dai ya kara miki kwanciyar hankali ya kara miki ƙiba kai kana ganin Hajiyar nan ka san akwai manyan kaya, Allah ya kara sutura”
Cikin gidan Hajiya Kaltume ta koma ta shiga dakin Hajiya Fatee ta samu biro ta mikawa Hajiya Fatee domin ita bata iya rubutun ba.
“Rubuta masa number ta a nan”
“Numberki kuma? Me ya faru? Karki jawa kanki matsala fa irin wadannan ba su jin magana”
“Ke dai rubuta babu komai, ke na ke yi ma jihadin ai, wayo yake masa”
Hajiya Fatee ta karba ta rubuta mata number ta mika mata. Hajiya Kaltume ta bude jakarta ta dauko 3k ta hade ta takardar ta fita falo ta bawa mai aikin ta umarce ta da ta kai masa. Sannan ta juyo ta dawo dakin tana tambayar Hajiya Fatee ya aka karkare da Salame.
“Na kirata na mata bayani, ta ce ai ya canja line saboda rufe masa wacan da masu gidan line suka yi, amman yanzu zata turo min sabuwa numbersa kuma zata kira ta masa bayani”
“Haka nake son ji, to yanzu ki kwnatar da hankali ki kira ki fada masa ya shirya komai na sa ya zo garin nan zamu aika da mota a dauko shi a kawo mana har gida, daga nan sai mu gabatar masa da matsakarmu”
“Amman kina ganin zai yarda ya zo?”
“Hajiya Fatee miye kudi ba zai yi ba? Muradi dai abashi kudi shi kuma ya biya mana bukata kawai”
“Ni dai Allah yasa cikin nan ya tausu, idan ba haka na zan shiga uku ga shegiyar suruka zata ji dadi”
“Komai zai wuce Hajiya Fatee ki kwanatar da hankali”
Cewar Hajiya Kaltume ga aminiyarta tana murmushi.
IYAMI POV. .
“Iyami ba a zama haka, ke kanki kin san mijinki yana sonki, ga yaya yanzu kuma ga cikin nan da kika shiga watan haihuwa, kamata yayi ki nemi taimako idan ma wani asirin aka yi masa aka rabaku a karya shi, ki koma dakinki bana son ki haihu a gida Wallahi”
Amma ta yunkura da katon cikinta ta tashi zaune daker tana kallon Hindu dake maganar.
“Hindu, Wallahi ban taba yi ba, su kansu da suke ganin kamar asiri na yi ma Alhaji yake ta so na ko na malleke shi, ban taba bada naira biyar na ce a mallake min Alhaji ba, tsantsar biyayya ne kawai da kawar da kai da kuma jin maganar duk abun da ya fada, ni yanzu ko zaki dora wuka a wuyana ba zan iya fada miki sunan Malami daya da na sani ba a garin nan, ban taba yi ba, Gwaggo ma bata taba ta yi ba mu ba mu da kowa sai Allah”
“Na sani, to ai tambaya ake kin ga har na tsarin jikinki sai ki sha kuma ki bawa yayanki, domin su ma ba barinsu zata yi ba”
“Ni dai ba zan iya ba, na kai kukana ga Allah shi zai min magana, ko yanzu ai ba yadda suke so suka samu ba, duk wata sai ya aiko min da abinci da kudi saboda cikin nan, yanzu kuma kina ganin yadda aka cika harabar gidan nan da itace saboda na shiga watan haihuwar, na san idan ra'ayinsu za a bi ba zasu so haka ba, yarana kuma idan ya auna lokaci ya kan aiko da su su gan ni na gansu, an rabu ne kawai amman kamar ana tare, idan Allah yayi zan koma sai ki ga na koma kamar yadda ban saka ran auren Alhaji ba Allah yayi kuma aka yi auren”
“Toh Allah yasa haka shi ya fi alheri, amman dai da kin tafi ba a san inda za a dace ba”
“Allah ya hada mu da dacewar”
“Ameen”
Ta amsa ba dan ta jidadin yadda Iyami ta ki amincewa da zuwan ba.
[10/20, 6:26 PM] Nana 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲 1: ☆❁ 𝗛𝗨𝗥𝗜𝗬𝗬𝗔 ❁☆
𝐁𝐲 𝐊𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚 𝐂𝐚𝐧𝐝𝐲
Pease ku yi following dina a Arewabook. @khadeejacandy
https://www.arewabooks.com/u/khadeejacandy
𝗣𝗮𝗴𝗲 1️⃣5️⃣
Salame na turo number Malamin Hajiya Fatee ta kira shi a waya, suka gaisa ta fada masa abubuwan da suka faru ya jajanta mata, ya kara mata da cewar shi ma layinsa aka rufe shiyasa bata ji shi ba. Hajiya Kaltume ya karba suka gaisa sannan ta dora masa da banin abun da ya sami Hajiya Fatee, daga karshe suka yanke ranar da zai shigo garin. Sannan Hajiya Fatee ta iya fita dakinta ta samu ruwan tea ta sha domin bata iya cin komai. Hajiya Katume bata jima a gidan ba Fadeel ya shigo gaishe da mahaifiyar, da zai fita Hajiya Kaltume ta bukaci ya sauke ta gida.
*** *** ***
Ba kadan ran Momy ya ba ce ba, jin cewar Captain ya zo gidan tana bachi, kuma ya fita da bacin rai saboda Hurriya.
“Oh to wai miye na siya mata gilashin ma?”
Namra ta aje spoon din hannunta.
“To nidai ranar da ya zo last na ganta da shi cirko cirko, gilashinta a kasa tana lalabe to shi ne yau take fada min ai marinta yayi saboda sun yi karo”
“Ai gara da mareta ma, yarinyar nan bata da hankali, sannan yanzu ya zo ta ki ta karbi box din wata kila ba zai sake dawowa gidan nan ba kuma, ta ja min ya fara fushi da ni kenan”
“Shi ma fa Captain din nan ya cika zuciya ga zafin hannu, amman dai bata kyauta ba da bata karba ba”
“Bar yar iska bata san su waye iyayensa ba ne shiyasa, shi ma dai miye na kawo mata glass ko makancewa ta yi iya ruwansa”
“Kila ya ga be kyauta ba, ko kuma...”
Momy ta kalleta da duba kyama.
“Ko kuma me? Allah ya kiyaye ai ko mata sun kare duniya Captain ba zai yi komai da wannan yar tatsitsiyar yarinyar na duka ma nawa take shekaranjiya ta yi 16yrs fa, kuma shi da yake da matar da zai aura”
“Toh ba sai idan anyi auren ba, wannan me bakar zuciyar? Ba kowa ce zata iya zama da shi ba”
“Ai ko fasawa aka yi sai dai ya aureki, daman Hajiya Turai ta so a hada wannan zumunci shi din ne ya ki, kuma kin san basa masa dole ”
“Ni”
Namra ta nuna kanta domin bata taba jin makamacin haka daga bakin Momy ba.
“Ke fa mun sha yin maganar da Hajiya Turai ai, amman shi Jameel din ne be yarda ba, yanzu dai ya samu wadda yake so an huta”
Namra bata ce komai ba ta maida idonta kan abincin da take ci tana motsa shi a hankali kamar mai tunani. Momy kuma ta tashi daga dinning din tana ta masifa saboda Namra bata tasheta daga bacci ba.
“Kiransa zan yi yanzu Allah yasa ya daga, kar wannan yar filfilwar ta jazamin masifa ni Nafisa”
Nan ma Namra bata ce komai b ta cigaba da motsa abinci tana tauna wanda yake bakinta ta kasa hadewa sai tunani take. Kamin ta juyo ta kalli falon da aka bude, Hurriya ce ta shigo kanta ba dankwali rabin kan nata a tsire.
“Yi sauri ki dauki abun da zaki dauka ki fice kamin Momy ta fito, dan na san sai ta miki fadan kin karbar box din da Captain ya baki”
“Abinci zan zuba”
Ta nuna abinci tana kallon stairs gabanta sai tsananta faduwa yake.
“Zo ki zuba”
Ta nufi dinning din da sauri ta dauki plate ta zuba abincin mutum biyu ita da Hamad ta saka naman kaza a sama ta dauki spoon biyu ta saka.
“Ke da Hamad zaku ci?”
“Eh”
“Dazun shi ya hana ki karbar glass din ko?”
“Na ga ya bata rai yana hararata, na san idan na karna zai iya min masifa kuma yayi fada ni, ko ya dukeni”
“Ke dai Hamad ya raina ki ya maida ke kamar kanwarsa, ko dan ya ganshi babba ke kuma ba ki ba”
Hurriya ta yi dariya mai sauti ta shiga Kitchen ta dauko tray ta dora ruwa da lemu a kai sannan ta fito ta dauki plate din abincin ta dora a tray ta dauka ta fice da sauri. A harabar Apartment din Hajiya Kaltume ta dawo ta zauna a balcony kusa da Hamad ta aje tray.
“Hamad zo mu ci abinci”
Ya kalli abinci sai ya bata rai.
“Waya ce ki hade? Waye zai ci abinci da ke to?”
“To ai ni ina sauri ne, Yaya Namra ta ce Momy nemana take zata min fada saboda ban karbi abun da bakonta ya ba ni ba”
“Toh ina ruwana ki je ki zuba wani”
Ya saka hannu ya dauke abincin da ba zai iya cinyewa shi kadai ba ta dora a cinyarsa.
“Idan ba zaka ci da ni ba, ba sai ka je ka debo na ka ba?”
“Ba zan ce ba, ni ki daina ba ni umarni”
“Wannan dai nawa ne ka ba ni abinci na Hamad”
Yayi mata kunne ne shege yana ta cin abinci ko kallonta be yi ba. Har ta tashi zata tafi debar wani sai kuma wata zuciyar tace mata Momy na nan falo, sai ta koma ta zauna ta dauki lemun ta sha tana ta kallonsa yana cin abinci. Ita ma dai kamar mantawa ta yi Hamad be cin abinci da kowa kuma be cin ragin kowa har da na Appansa da na Amma. Hakura ta yi ta saka masa ido ta can kuma ta ji ba zata iya ba tunawa da ta yi baya son gashi idan yana cin abinci sai ta cigaba da sifar kan tana kallonsa wai ko zai ji kyama ya aje abinci. Instead of yayi haka sai ya kifar da plate din ya riko gashin kan nata a daidai lokacin da Mota ta faka harabar Hajiya Kaltume. Da wani irin karfi yake fisgar gashi da karfi bata san lokacin da ta fara ihu tana rike hannunsa ba. Da sauri Fadeel ya bude motar be ko tsaya kashewa ba ya fito ya nufi inda suke daker ya banbanre hannun Hamad Hurriya ta koma bayansa da sauri tana kuka.
“Kai wannan ai sai ka tsinke mata gashin ka rage mata sadaki, miya hada ku?”
Hurriya bata iya magana saboda kuka, Hamad kuma ba gwanin maida magana ba ne daman sai cika yake kamar wani zaki. Hajiya Kaltume tana kawowa kusa da su ta ce
“Ai haka suke, uwa daya uba daya amman baya raga mata, basa zaman lafiya kamar Annabi da Kahiri suke”
Cikin mamaki Fadeel ya kalli Hamad.
“Wai kanwarsa ce yake mata wannan jan gashi haka?”
“Ita ce yayar ai, dan ka ganshi da girma shi ne kanen ai, baya ragawa kowa a gidan”
Hamad ya juyo yana watsawa hara Hajiya Kaltume dake korawa Fadeel bayani saboda ta tabo shi tun da ta ce be ragama kowa.
“Idan ba kai ba, wake fada da mata? Ba yayarka ba ce?”
Ya juyo ya kalli Hurriya da ta boya bayansa.
“Ke kuma ki rika kiyaye, yi hakuri ki daina zama babu dankwali ba kyau”
“Ai Allah yasa ma aljannu da ifiritai da shaidan duk su tattara su shige a cikin kan nata, ita ma ai ba karamar marar jin magana ba ce”
Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume dake fadar haka tare da yin gaba da bar su a gurin. Ta share hawayenta ta kalli Hamad sannan ta kalli Fadeel.
“Ina wuni”
Dariya yayi.
“Lafiya Kalau, Allah ya tsare gaba Hurera ko?”
“Hurriya”
Ta gyara masa.
“Yeah ki rufe kanki”
“Toh”
Ya juya ta sauka balcony din ya nufi motarsa dake kunne har lokacin sai da ya shiga motar daga mata hannu sai kallonta yake sannan yayi reverse ya fice.
Two Week Later....
Hajiya Fatee ta gyara zama ta kalli kawarta kamin ta kalli Malamin da suka sauka a garage din gidan.
“To yanzu Malam akwai yadda za'ayi a danne cikin nan kar ya bayyana? Kuma wannan tofe tofen yawun da kin cin abinci da nake ga kasala duk na daina shi?”
Malamin dake sanye da babbar riga ya kalli Hajiya Fatee yana murmushi.
“Za'a iya sosai kowa, ba yau na saba ba, za a iya danne cikin nan har tsawon shekarun da kike so”
“Alhamdulillah, ina son a danne min shi har nan da shekara dari, na san dai ba zan yi shekara dari a duniya ba”
“Ko kuma nan da lokacin da zaki yi aure ba, Hajiya yadda kike da surar nan Maa Shaa Allah, ai sai idan mutum be samu dama ba, shekarunki ba ba za a ce kin yi ba, ai na san ba za a rasa namema ba ko?”
Maganar yake yana dariya kamar wata abokiyar wasarsa.
“Aa kai aure kuma? Wake ta aure yanzu? Aa mun bar wa yara, ni dai yanzu bukatata a fara danne cikinki, idan an samu nasara hakan yayi sai a shiga yi Farraqu tsakanin yaron nan Fadeel da Matarsa Afrah domin ina kwana da bakincikinta a kullum Wallahi”
.“Babu Matsala Hajiya, za a danne ciki, matukar ba a daga dutsen da zamu saka layar mu rufe ba, cikin nan ba zai taba tashi ba har abada, amman fa zaki zuba kudi kam”
“Karka damu zan biya ka ko nawa ne, ammam dan Allah a saka dutsen a inda ba za a iya dagawa ba”
“Aljannu za mu saka su yi aikin, karki damu”
Hajiya Fatee ta kalli Kaltume suka yi murmushin jindadi sannan Hajiya Kaltume ta kora da nata bayanin.
“To ni Malam na ji shiru, kasan na baka kudi akan za ayi ma Iyami aiki ina son komai nata ya lalace amman har yanzu ba labari, kuma ni yanzu so nake a mallake min kowa a gidan nan daga mijina har Nafisa ikon kowa ya dawo karkashina, ina son Alhaji ya zama be iya aiwatar da komai sai abun da na fada masa, kuma ina son a shiga tsakaninsa da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15 Chapter 16