da fita ba ishaq ya shigo ganin salman yasa yasaki wani murmushi😏 tare da tsugunnawa ya gaida sarki, cikin sanyin murya ya amsa ishaq yace salman yanaganka a tsaye? Salman ya kalleshi sannan ya d'auke kai tare dacewa sarki nabarka lafiya, sarki bai amsaba salman kam da sauri yai waje.

Ishaq yace Abba Allah yasa dai d'an kanin nan nawa ba laifi yama ba? Inkuwa laifi yai ina bada hakuri a maimakon shi, sarki yace kyale sokon yaro zanyi maganinsa, sannan kafad'ama fulani ta fara nemo yarinyar dazai aura dan in bai kawo wace zai auraba nan da wata 1 to ba shakka aure zan mai.

Ishaq yace to ranka ya dade, sannan shima ya fita zuciyarshi fal farinciki lalai yau sunada karamin party.



Salmah kam tagama aikin gida takoma d'aki ta d'auko littafinta kenan taji yaro na sallama sai dai kafin tafita goggo ta fita tace yaro ya akai? Yaron yace wai ana sallama da salmah inji Muftahu tace muftahu? Wanne kenan? Yace muftahu mai babban shagon can tace au toh nagane, je kace gatannan yanzu zata iso, yace to tare da yin waje.

Goggo ta taho dasauri tana washe baki takaraso dakin salmah dake zaune duk taji abinda sukai da yaron, goggo tace tashi 'yar nan alkairi yasamemu😁 salmah tace name fa? Goggo tace gidan ku kina nufi bakiji me mukai da yaron can ba😠? Salmah tace au nad'auka sa'a yake nema( kanwarta da akai aure wata 4 dasuka wuce).

Goggo tace kaji min 'yar rainin hankali sa'ar datai aure za'azo nema? Tace kin manta ne goggo kwanaki.....ta katseta rufemin baki yar iskar banza to ke ake nema kuma muftahu ne mai katan shagon can salma tad'an tabe baki tace goggo kinsan fa ni yaya kamal nakeso, goggo tace lalai dalla rufemin baki kamalo ba kamalu ba kinsan Allah salma😠 tashi kafin na fasa miki baki.

Kasa tai dakanta tare da jan hijab dinta tai waje tana turo baki.



Muftahu kam ansha shadda da hula ga motarsa Civic ya ajiyeta yana tsaye ya juya baya, yanajin motsin kofa ya juyo yana murmushi takalleshi tare da d'auke kai tace ina wuni? Yacw lafiya lau *Salmat*😊 tace salmat? Yace eh mana ni haka zan dinga kiranki ta juya kai tare da yin shiru, yace salmat plz nazo da magana mai girma hope zaki fahimceni? Ta juyo tare da kakaro murmushi tace am sorry muftahu nasan kasan inada Wanda zan aura.


Muftahu yace salmat, kamal ba baida niyar auranki, inba haka ba shekararsa nawa acan? Kaf 'yan layin nan gulmar abin suke mahaifinki yabarki kina jiran d'an uwansa bayan kila shi yamanta daku.
Salma kam ranta yagama b'aci batare datace komai ba tai hanyar gida ta bude kofar tai dakin ta da sauri tafad'a kan gado ahankali hawaye yafara zubo mata.
...




By Ayusher Mohd📚
[10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄




*NA AYUSHER MOHD*



NO.5⃣

Tanajin motsin umma a waje amma abin haushi ko tazo ta tambayeta meya faru, Abbanta nadawo wa tamike da sauri taje tagaidashi umma da goggo nazaune bayan ya amsa, goggo tace dazun korar muftahun kikai shima? Salma tai kasa dakai, Abba yace wai ke Basira meyasa bakyaji? Na dade da fad'a miki bana san kina takurama salmah, ko kin manta matar da kamal ce? Tace yahkuri Alhaji ganinai tanata zama a gida ba kamal ba labarinsa.

Abba yace kada ki manta yanda muke da mahaifin kamal mu 2 ne a d'akin mu shine yayana kuma baki isa kisa zumuncin mu yai rauni ba, Goggo tace Allah yabaku hakuri, Alhaji nad'auka salma kamar 'ya take a gurina tunda nina raineta, Allah bai bani 'da ba.....

Da sauri umma ta katseta tace Goggo kidaina wannan maganar, sannan takalli salma tace ke kuma tashi ki bamu guri, salma ta mike duk jikinta yai sanyi tai d'akinta.

Umma takalli goggo tace kiyi hakuri hajiya, Alhaji bai kamata ka mata fad'a agaban wannan 'yar ba, Alhaji yace ai basira ce na dade ina mata magana bata ji, amma yanzu abar maganar nan zan kira kamal inji menene ya tsayar dashi dan ni kaina nasan gaskiya basira take fad'a, yana kai nan yai waje, umma tashiga ba goggo hakuri.


Yau salma na zaune a class suna d'aukan lectures hankalinta nakan karatun da akeyi har malamin yagama koyarwa ya fita zama tai a theater room din tana duba littafinta.

Ganin mutum tai ya zauna a saman desk din datake ta d'ago cikin mamaki tare da matsawa, mamaki ne ya kamata ta zaro ido sannan gabanta ya fad'I ta mike zata wuce hannu yasa ya fizgota tare da maidata inda take yace 'yar gidan Amadu ina zaki batare da uzinina ba? Tace izini? Yace eh ko kinfi karfi? Tai shiru tare da ture hannunshi tace wai menene dalilinka nasan shiga harkata? Yace I won't leave you har sai kin janye maganarki na tausayi daga kaina, in kuwa ba haka ba I promise you sai kinyi dana sani mai karfi.

Salma tai wani murmurshi😏 duk daba ganinta yake ba tace in naki fa?yace then mark my word😠, tace prince I am not afraid of u, yace u are not? Ta daga kai alamar yes yai murmushi yace then I will have to make you, yana kai nan yai waje.


Wata doguwar ajiyar zuciya ta rike hannunta dake rawa murya taji cikin sanyin ance salmah kiyi hakuri ki kuma ba salman hakuri, tad'ago cikin mamaki Najib tagani tace mena mai? Yace bakiyi komai ba amma salman ba abinda yatsana irin yaji ance yana ba mutum tausayi, ya juya ya fita, ta bishi da kallo tare da runtse ido tace yazanyi yaya kamal? 😞


Batafi 1 hr ba zee tashigo dasauri tace salma me kikayi? Salma tace name fa? Tace an kafe sunan ki a notice board an baki suspension na 2 weeks na dasauri ta mike cikin kidema tace suspension? Ni *SALMAH AHMAD MOHD* ? Zee tace wlh sunan ki akasa tace menayi? Tafad'a hawaye na zubo wa daga idanta tace akan me? Zee tace kema kinsani ai, salma tace I have to go an ask dan salman yace a bani suspension dan ni ba 'yar kowa bace sai abani?

Zee tace ki rufa mana asiri kar kisa a koreki daga skul din gaba daga, hannu tasa akai tafara kuka zee ta dafata tana rarrashinta.


Dakyar ta tsayar da hawayenta tare da d'aukar jakarta tace zee na wuce gida kuma plz karki fad'a a gida abinda yafaru tace to salmah.


A hankali take sauka daga steps din gun zuciyarta nakan tunanin abinda ke faruwa har ta iso titi tana jiran mota.


Motace tazo kusa da ita tai parking tad'ago jajjayen idanunta, ahankali aka zuge glass d'in bayan motar, tana kallan wanda ke ciki haushi da wata muguwar tsanarsa suka mata yawa tadan matsa daga gun ahankali motar takara matsowa gun salman yace sorry limamiya I really pity you☹yanzu what can we do🤔? Jitai kamar tasa ihu d'an bakin ciki kalamansa amma me? Daurewa tai tace u don't have to pity me bawani abin bane dan anban suspension just take it as nasamu rest daga ganin mutanen dana tsani gani tana kainan ta matsa tafara tafiya da kafa.

Salman yai kwafa haushin kalamanta suka kamashi yakalli driver dinsa yace dalla wuce mutafi yace to ranka ya dade.


Salman na isa gida yana fitowa daga mota wanI bawa yazo yace sarki na nemanka, yace to tare dayin hanyar fadar sarki.


Zaune suke su 2 sarki ya kalleshi yace ka kyauta da wulakantani dakai salman yace Abba bangane ba? Yace ai ni ka wulakanta tunda bakaji kunyar sawa abawa d'aliba suspension ba wlh salman sai kasan kayi kuskuren b'atamin suna dasauri ya d'ago yace Abba yarinyarce fa.......yace just keep silent ka kuma bani guri sanda ishaq ya fad'amin zancen nan I thought karya yakema amma yanzu na tabbatar dan haka mike kaban guri😠.


Cikin sanyin jiki salman ya mike yana fita yai hanyar dakin ishaq sai dai yana tsaye daga waje yanajin shewar su ishaq da kannansa maza 4 suna murna kowa nacewa kai yarima ka birgeni, ishaq yace ai na dade da fad'a muku salman d'an karamin kwarone a gurina, ragowar sai jin jina mai suke ahankali ya juya yai bangarensa kansa na sarawa yana shiga d'aki ya zube ya shiga murkususu rike da kirji da kai dakyar yasha magani yashiga karanta *INA LILAHI WA INA ILAIHI RAJI'UN* ahankali yafara jin relief.



By Ayusher Mohd📚




☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄




*NA AYUSHER MOHD*



NO.6⃣

Kuka sosai takeyi yi abinda ya kara tunzurata umma na zaune a waje tana goge kubewa amma ko ta tambayeta, ta dade tana kuka ganin ba mai lalasarta yasa ta mike tare da fitowa tad'au kwandam wanka tai toilet umma ta bita da kallo.


Qur'ani ta d'auko tashiga karantawa ahankali tafara jin sanyi na ziyarta zuciyarta, jin motsin Abba yasa ta fito da sauri takarasa tare da mai sannu da zuwa yai murmushi tare da cewa 'yar Abba meya sami idanunki? Tai kasa dakai yakamo hannunta yace muje inji matsalar 'yata tunda duk gidan ba mutanen da zasu tambayeki.

A falo suka zauna yace menene salma? Tace Abba aran wayarka nakira yaya kamal yace to naji amma fad'amin menene? Tace bakomai Abba banajin dadi ne, yace ayya sannu ko muje asibiti? Tace A'a Abba naji sauki yace to sannu sannan yamika mata wayarsa ta amsa tare da mikewa tabar falon.


D'aki tashiga tareda yima kamal flashing sau 6 tamai amma abin haushi bai biyoba, daga baya tai deciding ta kirashi sai dai shima no answer tadanyi tsaki tace kila yana wanI sabgar ne☹.....nace hmmm.



Ishaq ne zaune gaban sarki, sarki ya kalleshi yace nasani ishaq kaimesan d'an uwankane, ishaq yai kasa dakai cikin sanyin murya yace Abba yazamuyi da matsalar yarinyar daya kora daga makaranta? Abin na damuna😞, gashi mutane an fara gulmar abin ina tsoron kar hakan yajama salman tsana daga mutane😕.



Sarki yace ni kaina abin na damuna amma bari insa akira waziri inji yazamuyi, ishaq yai murmushi😏 ba b'ata lokaci sarki yasa akira waziri nan ishaq yafad'amai abinda ke faruwa.

Waziri yai shiru can yace yarinyar ya take? Ishaq ya shiga yin bayani akan binciken dayasa ayi akan salma da kyawawan halin yarinyar, waziri ya nisa yace mezai hana muyi haka? Sarki yace me? Mu nunama mutane bawai korarta yasa akai ba dalili ba matar dazai aurace yakesan abata lokacin shirye shirye tahakan ne kowa zaisan salman ba mutum ne mara mutunci ba mai wulakanta mace, sarki yai shiru yana tunani.

Ishaq kam baiso ba amma saboda san ya wulakanta salman jin yarinyar 'yar talakace ba jinin sarauta ba ko 'yar masu kudi yasa yace waziri ka kawo shawara Abba ya kagani? Sarki yace kasa a kara bincike akanta waziri banaso salman ya auri matar da bazata rufamai asiri ba waziri yace to ranka ya dade angama, ya mike yai waje.


Salman kam yau weekend bacci yake sosai sai azahar yai wanka ya fito, al'adar gidan ne aje gaida duk matan gidan da ranar asabar hakan yasa salman ya fito bangaren hajiya karama(Amarya)yafara zuwa, bawani shiri sukeba gaisawa kawai sukai ya mike ya fita ta bishi da harara itakam gadarar yaron na bata haushi gashi ita d'anta namiji shekararashi 7😠.

Bangaren Hajiya babba yaje(ta tsakiya) sun gaisa cikin sakin fuska sannan ya fito saidai yasani itama ba sanshi takeba.


Yakarasa bangaren fulani itakam yasan halinta sarai amma ita gani take baisan komai ba cikin farinciki tasa aka damomai fura tace salman sha fura dan musamman saboda kai nasa aka dama yai murmushi yace nagode fulani tace sai kace wani bare? Kaifa d'ana ne yace haka ne😏.

Bayan ya fito yakoma d'akinshi ya kwanta tare da runtse ido kaf 'yan gidan yasani 'yan uwansa mata 2 ne kesansa kuma sunyi aure sai yara dabasusan rayuwar gidan ba.

Shima kuma kallan kowa yake tunda haryau bai manta abinda sukai mai ba yana yaro har sarkin kuwa☹.




By Ayusher Mohd📚


[10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄




*NA AYUSHER MOHD*



NO.7⃣


Salma kwance akan gado sam ta kasa barci sai juyi take rashin mutuncin da prince ya mata ne ke dawowa kwakwalwarta dasauri ta mike zaune tare dayin kwafa tace a fili yaron nan da ace nasanshi dasai na rama rashin mutuncin dayamin😠wata zuciyar tace kinsan shi mana sai dai in tsoro kike😀, dasauri ta tashi tsaye tace tsoro? Nidin? Inji tsoron wannan banzan? Alla ya sauwake🤔, haka tai ta shirme a d'aki sai 12 tasamu tai bacci.


Waziri ne zaune agaban sarki yace ranka ya dade daga gun malam nake anyi istihara akan al'amarin nan ba shakka wannan auran alheri zai jawoma salman mai yawa, sannan maganar yarinyar kawai dai 'yar talakace amma halinta kaf 'yan unguwar sun shaida kyan halinta.

Sarki yai shiru can yai murmushi yace Alhamdulila, waziri yace ga kyau dan 'yan unguwar sunce kyanta dayanda maza ke binta yasa take saka nikaf, sarki yace naji dadin binciken nan zancen talauci kuma ai ba wanI abu bane da talaka da mai kud'I duk daya suke agun Allah.

Waziri ya kara tsugunawa yace Allah yajada ran mai martaba, yanzu insanar dashi?sarki yace a'a kasan halin salman taurin kai, kafiya in har yaji to da matsala, waziri yace ai halinku d'aya ranka ya dade yafad'a yana murmushi, sarki yai gyaran murya hakan yasa waziri yace tuba nake ranka ya dade.

Sarki yace yanzu kuje kai da yayana kusamu mahaufinta kuji ko an mata miji, waziri yace bamu zamu kirashi ba? Sarki yace a'a ai mu muke nema, waziri yace angama rnka ya dade yafad'a tare da mikewa.

Sarki yai murmushi shi kanshi yakosa yaga salman ya nutsu, haka kawai yakejin farin cikin zancen auran nan.




Waziri yasa asanar da Amadu zasu shigo da yamma, duk da Abba baisan meke faruwa ba jin ance wai wani mutumi kesan ganinsa akan wata muhimmiyar magana, haka kawai Abba yasamu kanshi da fad'awa d'an aikin in ba damuwa su hadu a sharad'a inda yayansa yake cike da mamaki d'an aiken yace ba damuwa.


Nan Abba ya koma gida yaI wanka yasa manyan kaya, umma takalleshi tace meke faruwa? Yace nikaina bansani ba amma kibari inje indawo nikainan bansan menene ba kawai dai naji dan aiken yace mutumin kamar yanada hadi da gidan sarauta, tai shiru tace to Allah yasa alkairi ne yace Ameen Basira bata dawoba? Tace eh yace salma fa? Najita shiru, umma takauda kai tace inazan sani? Yai tsaki yace sai kiyi tayi ai hakan jiya 'yarnan fuskarta duk ta canza amma wai bakisan menene ba? Yai waje cikin fishi.


Dakin salma ya shiga tana zaune rike da hoton yaya kamal tanajin salamar Abba tai saurin boye hoton yakalleta cike da tausayi yace zan fita tace to Abba d'aurin aure? Yacs a'a tace adawo lafiya yacs amin tare dayin waje, yana tausayinta sosai dan jiya ya duba yaga adadin kiran datama kamal amma bai kira ba shikam dan dai bayanda zaiyi ne amma shikanshi yanaso 'yarsa tai aure.



Yayan Amadu wato Mustapha jin sakon kaninsa yasa aka gyara falon baki tare da siyo lemuka, bayan Amadu ya isone bada dade wa ba kira ta shigo wayar Amadu ya amsa jiyai ance bakin dazasu zone muna sharada gidan wa zamuce? Nan Amadu yashiga kwatanta musu har suka gane.


Su Amadu na zaune da yayansa suna hira suka dingajin hayaniya a waje cikin mamaki mustapha ya mike ya fito Amadu na bayanshi.


Mamakine yakamasu ganin motoci guda 6 sun jeru a kofar gidansa ga fadawa a tsatsaye Mustapha yace hala wani taro nasarauta za'ayi Amadu yace ko kuma hawa ba? Naga in gidan sarauta zasuyi aure suna hawa, nan sukai murmushi tare da juyawa ji sukai ance banan ne gidan Mustafa ba yayan Amadu? Atare suka juyo suka kalli bafaden dayai maganar, Amadu yadaure yace nan amma meke faruwa? Ahankali aka bude motoci biyun tsakiya kowace waziri da yayan sarki Modibo suka fito.


Mustafa da Amadu sukai kuri suna kallo ga kutane sun cika gun, jisukai wani bafade yace a waje zaku barsu? Dasauri Mustafa yace ahhhh ku ku shigo.


Waziri da Modibo suka nufi gidan shikam Amadu jiyai kamar yayi mutuwar tsaye tunaninsa d'aya laifi yayi kawai.

Sun zauna su kuma su Abba sun tsugunna suna kwasar gaisuwa,modibo yaI murmushi yace haka ake neman aure a tsugunne? Cikin sauri mustafa da Amadu suka d'ago ido? Tare da kallan juna sukace aure?Waziri yace kuzauna mana, nan suka zame suka zauna, modibo yace muna namawa Salman d'an gidan sarki auren 'yarku salma, cikin kidima Abba yace eye? Waziri yace eh muna neman alfarma, sai dai in kun mata miji to fa wannan ba yanda zamuyi, Abba yai shiru zufa tashiga keto mai, yakali mustafa shima zufar yake, Abba yadaure yace salma? Waziri yace ita fa, Abba yace ku gafarceni ranku ya dade amma....dasauri mustafa ya katseshi yace mun baku indai Salma ce😬 waziri yace amma kuwa muna godiya, yace a'a ai mune da godiya, Modibo yace to *Alhamdulila* munji dadi sosai sai dai munada magana, Nan su Abba suka d'ago, Modibo yacee bamasan auran ya wuce wata d'aya Abba yace wata 1? Waziri yace eh sannan munaso ku taimakemu karku mata komai nakayan d'aki mustafa yace amma ina ake haka? Modibo yace wannan gudumawar sarkine na amsawa dakukai zaku bamu 'yarku, mustafa yace toh😳.

Nan modibo ya ciro bandir din dubo d'aya guda 3 ya ajiye yace wannan kudin mun gani muna so ne kenan kudin gaisuwa cike da tsoro Abba yakalli kudin zaiyi magana mustafa yarigashi yace mun gode amma kudin nan yayi yawa, guda d'aya zamu d'auka sannan inkun tsaida ranar auran sai a turo afad'amin nan sukaita godiya suka mike.


Abba ya zube a gun yace yaya yazamuyi da kamal? Mustafa yace kamal basan auran salma yake ba tunda haryakai wannan lokacin batare daya dawo ba bayan nasan yagama karatu, Abba yace salma fa? Datake tsananin sansa? Yace intai aure zataso mijinta kasan zuciyar mace ai.




Hmmmmmm babar magana🤔


By Aysuher Mohd📚
[10/16, 11:16 AM] ‪+234 803 681 7247‬: ☄☄☄☄☄☄☄
💥 *NI DA PRINCE*💥
☄☄☄☄☄☄☄




*NA AYUSHER MOHD*



NO.8⃣


Abba tare suka taho da mustafa dakuma matarsa, salma na kwance a kasa inda tai sallah batasan sanda bacci ya dauketa ba.


Mafarki take mai dadi, wai gata rike da hannun wani sai dai bataga fuskarshi ba sun je bakin ruwa sun zauna, yasa hannunsa a kafad'arta tare da kwantar da kanta a jikin kafad'arsa murmushi take sosai, tareda jin wani sanyin shaukin kauna na ratsata, a cikin bacci taji anacewa ke! Ke firgigit ta mike tare da kallan umma dake tsaye akanta, umma
Showing 3001 words to 6000 words out of 36779 words