MATAR SOJAA 1 to 33
Posted on October 23, 2015
[25/08 2:17 PM] Aishat muh’d: 1
Matar sojaa
Tuluka tuluka babbar doya ……tuluka tuluka babbar doya yara wasu yara su uku zasukai kamani shekara shabiyar15 suna tika uban gudu suna kuma ihu suna cewa tuluka tuluka babban doyan …….chan na hango wata yarinya itamadai zatai 15 amma tafisu kiba kana ganinta kaga kosassiyar yarinya yar duma duma da ita.jikinnan nata mulmul kaman dabino tanada matsakaicin tsawo dai dai ita iya abinda na iya hango muku kenan amma bari inta matso kusa nafada muku suffarta
Gudu itama take tana wlh yau sainaci durun uwarku wacece tuluka ina yaya hamma yace adena cemin tuluka wlh bazan yarda ba gudusu ke suna ance tuluka din idan kin isa kibiyomu kiba tahanaki gudu wooyiiii
Ai sai suka kara birkitata takara gudu …. gudu har suka fara fita wajen kauyensu sunkai kan titi suka tsallake ita kuma tsabagen ta zuciya ga fushi yasa ko kallon titin batai ba ta shige
Ji kake kiiiiiiiiii mota ta taka birki wanda saida yasa yarinyar tsorata ta koma baya dagudu taga motan ya sauka gefen titi wazata gani yayanta hamma yafito a mazauni na kusa na mai tuki a gaba duk ta tsorata jikinta na rawa ya karaso ya daure fuska yace BESSHA baki ganin hanya ne?saboda rawan kai da rashin natsuwa irin naki ko inda kin mutu fa?tai gulu gulu da eye tace yaya kayakuri su atine ne suke cemin wai tuluka yace to karya sukayi tafara kuka tace ni wlh ba tuluka bace yace wuce kitafi gida kicema mama anjima zan shigo tace to tana kumbure kumbure tai kwafa tace wlh duk randa nakamasu atine na lahira sai ya fisu jin dadi kawai ta kece da gudu takoma cikin kauyen su
Maman shakur
[25/08 2:31 PM] Aishat muh’d: 2
Matar sojaa
Koda ta koma kauye bataje gidaba gidan gwaggo taje ta shiga ko sallama babu tahau jikin goggo tana kuka goggo tace yarnan lpy tace goggo basu su suu antine bane suke cemin tuluka ba goggo tace ya isa yi shiru dena kuka kinji ta share mata hawaye tace karki damu har gidansu zanje nacimusu mutunshi ya isa hakadai ta lallabata tadena kukan tafara mata lbr tace bessha yaufa jikana zaizo tace kut nidai goggo nafison gidan nan dagani sai ke.koma waye banasonshi wlh bazan yardaba hakanan yanzu nidashi zaki dinga rabama kayan dadi da nikadai ce ke cinyewa goggo tace to ya isa idan yazo zan koreshi tai murmushi…..tace yauwa goggo na saisa nake sonki mema zakiyi dashi bani ina miki komiba barima nai miki shara sai kiban kudin iloka ko tace eh tai maza tai shara ta gyara gidan tass goggo tace gaskiya sai kinyi wanka zan baki tun jiya rabonki da wanka tana kumbure kumbure taje tayi wankan tace bari naje gida nasa kaya ta karbi naira hamsin din da goggo tabata sai gida lokacin ma mangariba tayi
Maman shakur
[25/08 2:51 PM] Aishat muh’d: 3
Matar sojaa
Tana kaiwa gida ta shigo sadaf sadaf kaman mara gaskiya taje daki lokacin mama na salla taje tai alwala itama tai salla tana gamawa mama ta daure fuska ina kikaje tace wurin goggo mama tace karya kike tundazu da safe babanki yatura akiraki baki nan tafara kame kame tace mama wlh dama dama mama tamata tsawa tace dama me tafara kwalalo ido tace mama ba su atine bane sukecimin tuluka mama tace shine kika bisu kukai dambe ko tace mama wlh binsu nayi amma sunma gudu ..mama tace ba aiki nasaki da safe ba kika gudu kika fita bessha wai mesa bakijin magana kin girma amma har yanzu kwakwalwan yara gareki tace mama yakuri mama ta cigaba da mata fada anahaka yaya hamma ya shigo yace maiya faru mama tafada mishi yace akan titi naganta lokacin mumma kusa bigeta ina cikin motan jikan goggo dayazo yau yarinyar nan kinga yanda take tikan gudu kuwa mama takai mata mari tace wlh bessha nagaji dake kin gunduren barikin sojoji zan kaiki soja ya horaki….mama nafado sunan soja ta tsorata tafara bata hakuri a rayuwanta babu abunda take tsoro kaman soja duk inda taga soja da kaki a jikinshi bata iya zuwa wurin ta dinga kuka kenan.saboda soja ne ya karyama dantala saurayinta kafa ranan yai sata a gabanta taga wani soja babu imani ya dinga dukan dan tala harda karya mishi kafa.gashi mama na yawan bata lbr mugancin sojoji da kuma yanda sukeda karfi ga daure fuska ancema wai basa dariya.tadawo daga tunanin da take tace mama dan girman allah kiyakuri karki kaini barikin sojoji a horani allah kome kikeso zandingayi nadena yawo daga yanzu nai alkawari tana magana tana kuka mama tace baki isaba yarinya gobe nida baban ki zamu kaiki ta tashi ta shiga uwar daka takoma wurin yaya tanamai kuka dayake tsakanin wa da kani sai allah ya sharemata hawaye yace kinyi alkawari kin dena tace eh yace to muje muba mama hakuri suka bita yasa baki har mama ta hakura ta tashi ta rungume mama tana murna
Kubiyoni dan jin asalin labarin
Maman shakur
[25/08 10:07 PM] Aishat muh’d: 4
Matar sojaa
Malam husaini shine mahaifin da karima sune iyayen bessha mutane masu mutunci da amana ga sanin yakamata allah ya azurtasu uku hamma sai amina da yar autar gida mafadaciya sarkin tsiwa mai tsoron soja kuma wato BESSHA….bessha yarinya ce kakkyawa ta karshe baka ce amma mai sheki black beauty tanada dara daran ido farare tas ga dan karamin bakinta lips dinta pink hancinnan nata dogo kaman kan biyu ya karama fuska kyau ha dimple dinta guda
biyu.intai dariya da daddare sai kaga hakoranta sunyi haske tsabagen farinsu gashi allah ya hore mata gashi har gadon baya saida ita gashinta ba baki bane yana jajja jajja yanda kasan gashin turawa ,wanda ya kwanta gaban goshintanema baki yarinya badai kyauba.dalilin dayasa kawayenta kece mata tuluka kuwa tanada kibanta daidai ita baza a kirata ramammiyaba bul bul take cikin yan matan kauyen duk ta fisu kiba gata akwai diri dukda 15 take bai hana dirin fitowaba akwai lafiyan hips saima tana tafiya kaga kaman da gangan take juyasu dan suna daukan ido dukiyan fulani kuwa na mamanta ta gado dan haka mama kedasu sun cika kirjinta kaman suma magana.
Goggo dakukaji tana fada ba yar uwarsu bace kawai zaman
tarene.akwai wani rana tana cikin tafiya taga goggo ta dauko kaya akai ta karbi kayan takai mata gida ta sharemata gidan to tundaga nan wani irin soyayya ta shiga tsakanin goggo da bessha har agida ansani dan wani zubin har kwana takeyi achan.
Maman shakur
[26/08 12:30 PM] Aishat muh’d: 5
Matar sojaa
Goggo dai wata dattijuwar azikice zatakai 75 year yaronta daya kachal aduniya alhj umar yanada mata mai suna hj amina suma yaronsu daya basir shekaranshi 30 a duniya goggo na matukar son jikanta saboda shikadai allah yabata kullum burinta yay aure yahaifi yara dayawa taga zuri’ar tai ta bunkasa shikuma basir bayidama plan din aure a gabanshi yanzu akasan waje yay karatu sojanshi bayan yagamane yadawo yana aiki a barrack din abuja achan yake zama kakkayawane ajin farko farine shi tas ga hanci ga ido ga wani saje daya ajiye kaman balarabe yahadu iya haduwa saida bayadi magana sosai baya yawan dariya kullum fuskar a daure gashi ya tsani raini bayason rashin kunya
Yaje wurin goggo ne musamman saboda har kuka takira tayi wai baya zuwa wajenta shine yadau hutun sati biyu yatafi.yace goggo da rigima dad yayi yayi da ita takoma birni nan cikin kano amma taki kuma yanzu tana damunshi yaje shinefa ya tattara ya tafi.wanan kenan
Washe gari na wayewa kaman dagaske bessha tai aikinta tsaf taje wurin mama tai fuskan tausayi mama dan Allah naje wurin goggo? Mama tace jeki amma karki biya ko’ina kinajina ko tace naji mama harta fita ta dawo tace mama achan zanyi wanka mama tace to shikenan tafi.tawuce aguje sai gidan goggo
Maman shakur
[26/08 12:53 PM] Aishat muh’d: 6
Matar sojaa
Tana shiga gidan goggo ta tsaya a bakin kofa tace goggo kin kori jikan nakiko?goggo tace haba bessha ta kidan barshi ya kwana biyu sai yatafi ai kaman ta karama bessha gishiri tafara bubbuga kafa akasa tana ihu wlh goggo bazan yardaba allah sai yabar gidanan ke goggo nane nikadai kawai yazo dan yayi kwadayi will goggo bazan yardaba salon duk kayan dadin dazaki kawo kirabamana nidashi allah bazan yardaba tana ihu harda hawaye
Firgigit ya farka daga bacci dayakeyi sabofa kukan dayaji a firgice ya sauko daga kan gado yazira jallabiya yafita tsakar gidan yana goggo lpy
Bessha ta juyo ta kalleshi dukda yamata kwarjini gashi kakkyawa kaman bature bai hana ta murgudamai baki tace eh gidanmu zaka barmana ba goggon ka bane goggo nane kuma wlh kotakawo madara mai sanyi(ice cream) bazan bari
tabakaba.goggo tace bessha bakida kunya bai girmekiba tawani kada ido ta girgiza kirji tace mai ruwana
Basir sakin baki yayi yana kallonta yar karaman yarinya da inda yay aure da wuri yahaifi kamanta shine takemai rashin kunya…….ji yayi takara cewa nace ka dauko kayanka kabarmin gidan goggo na ko tawani girgiza kirji subhanallah shine kalman da basir yafada dan yanda kirjin suka girgiza a gabanshi saida ya hadiye miyau……chan yawani daure fuska yace ke bakida hankaline nikikema rashin kunya?:evil::evil::evil: dukda ta matukar tsorata dashi amma ta martuke tace anyima din nidai kabarmin innata ta murguda baki ai baisan lokacin dayayo kanta ya kifa mata mari saida taga star hudu saboda azaba ya kara yau kanta da gudu ta labe bayan goggo tana hawaye shikuma ya tsaya yana huci ….goggo tace maisa bakijin magana bessha tsaran wasan kine tace eh din nidai yatafi nafijin dadin nikadai ke cin kayan dadinki wlh wlh wlh saiyabar gidannan ba tsammani taji andamkota an felfella mata mari anyi ball da ita dago idon dazatayi taga yaya hamma ne ne yace dama bakida kunya abokina kikema rashin kunya kin rika ko ?wuyanki ya isa yanka zan gyara miki zama…. goggo tace bar dukanta hamma bessha ya kuri yi shiru kinji yakusa yafiya azuciye ta mike saida takai zaure tace goggo dagayau bazan kara zuwa gidankiba munbata tunda kinfison jikanki kanni tana kuka tafice
Maman shakur
[27/08 6:25 AM] Aishat muh’d: 7
Matar soja
Tana komawa gida ta zauna a tsakar gidansu ta cika fam sai kumbure kumbure takeyi.
Mama na fitowa taga bessha zaune tana kumbure kumbure tai mamaki dataganta ware haka dan tasan intaje wurin goggo har dare wani zubin tana kaiwa,mama ta karasa wajen ta tace auta lpy naga kinata fushi??? ai kaman jira take kawai kuka yazomata tace mama ba ba ba goggo banebaaaaa tana magana kaman ta yara hade da shagwaba , mama tace mai goggo tayi?tace mama tafison jikanta kanni kuma bazan kara zuwa gidanba tana magana tana kuka
,mama tace yau anganku a rana keda goggo ki maiyafaru??tace mama wai kawai dannace ta kori jikanta nikadai da ita muyi zamanmu shine taki .mama ta kalleta tace auta hankali banda abunki ya za’ayi kice ta kori jikanta uhmmm nikinmaga aikina zanje nayi ba’ashiga tsakanin ki da goggon ki anjima zaku shirya kubani kunya tamike tatafi tana murmushi tace Allah kenan kawai yahada goggo da bessha wanda cikinsu babu wanda zai iya rintsawa batare dayaga dayaba nasan anjiman nan kodai taje ko kuma goggon tabiyota su shirya shakuwar dake tsakanin su yabaci mama duk tunanin nan a ranta takeyi.
Bangaren goggo kuwa taji shiru har wajajen karfe 5 bataga besshan taba duk tadamu tacee nasan ana fushi dani bari naje nai biko ta tashi tana kokarin sa hijab ne basir ya shigo yace sai ina goggo?? tace zanje nai bikon yata dakasa muka bata yawani daure fuska kaman dagaske yace mata allah raka taki gona yajuya yatafi dakinshi….azuciyarshi yana murna danshi har ga allah yarinyar na burgeshi haka kawai ,tuntuni yana kofar gidansu shida hamma suna fira yanaso yaga koda giftawar tane amma baiganiba yagaji sukai sallama da hamma yatafi.saisa yaji dadi dayaga goggo zataje bikonta
Maman shakur
[27/08 7:31 AM] Aishat muh’d: 8
Matar sojaa
Goggo na shiga gidan da sallamanta bessha ta tashi ta juya baya tana ni karma kimin magana ba ruwana dake
Mama na gefe tana dariya tace oo goggo yau munganku a rana
goggo ta harareta da sigan wasa takoma kan bessha tace haba bessha ta zomuje gidana musa labule kinji tace ni bazaniba sai jikanki yatafi…goggo takara marairaicewa harda rage murya tace bessha to kiyakuri kidan bari yayi sati biyu kachal sai mu koreshi tace ni goggo bazan yardaba sati biyu yay yawa tace haba bessha ta kiyakuri yayi satin biyu kinji yar albarka allah nunamin auranki nayi albidir har barmani choge zan kira ta kadamin kwarya na taka zoma muje gidana nabaki farin madara kuma ke kadai zanba bazan ba basir ba kinji dan kisan nafi sonki dakyar goggo ta lallbata suka tafi gidan
Suna kaiwa goggo ta dauko ice cream tabata tanasha suna fira goggo tana kara lallabata bayan tagama shan ta gyarama goggo gidan taimata shara sai wuraren isha tace goggo natafi goggo tace tsaya kici abinci tace goggo nakoshi madara mai sanyi tacika min ciki tafito ta tafi .tana kaiwa zaure tahau tsaki mtsww nama manta ban karbi tocula ba tana kokarin zujawa ta koma wurin goggo dan karban touch taji anriketa gam ta bala’in tsorata tana kokarin yin ihu ya taushe mata baki sai alokacin ya kunna touch taga ashe jikan goggo ne ta daure fuska
Ya cire hanunshi daga bakinta tace mallam lpy?:evil::evil:yace ke ni kikema rashin kunya ko ina wasa dake eh azuciye yake mata magana sai ta tsorata dan karya daketa tace tobana baka hakuriba kuma ma aikai ke cemin tuluka yace to ai ba karya nayiba ke tuluka ce maganar tai bala’in bata mata rai har hawaye ya ciko idonta tace wlh niba tuluka bace jikina daidai ni banda wani kiba ,yace eh naji bakida wani kiba amma kinfi duka sa’o inki na kauyenan kiba kinga saisa kika dawo tuluka…sai alokacin hawayen idonta ya idda saukowa daga idonta.yace duk randa kika karamin koda kallon banzane sai na bata miki rai mara kunya fitsararriya tuluka kawai ya hankadata tabigi bango tako bare baki tana kuka goggo taji ihu bessha tai maza ta fito tana bessha lpy dama baki tafiba taganta tsugunne tana kuka ta tattabata lpy bessha ta dago tace goggo ba jikanki bane ya dakeni yakuma nushine a jikiba ,goggo ta rafka salati tana yanzu basirun ne yamiki haka wlh zai gamu dani muje na sameshi ta tasata agaba har bakin kofan dakinshi goggo nacewa basiru oya fito kabata hakuri inba hakaba zan sabama dan zalinci yarinya karama zaka daka harda nushi bessha tace goggo kuma harda murdamin hannu goggo tace assha muga hannun dafatan bai jimiki ciwoba .yana daki yana jinsu shi abunma dariya yake bashi yay banza dasu goggo tagama maganganun ta lallaba bessha tabata biscuit tace tafi gida gobe zai gane
Maman shakur
[27/08 7:51 AM] Aishat muh’d: 9
Matar sojaa
Yau kusan kwana uku bessha bata bari su hadu ita da basir dan tasan tamai karya inya kamata zata gane.duk idan tazo gidan tanacin sa’a bayanan kuma tana gama aiki taci abincin goggo saita gudu gida.
Yau tazo sunata fira da goggo ita tana wanke tsakar gidan da ruwa goggo dama tana daki zaune tsautsayi yasa goggo tace bari nafito bessha naga yanda tsakar gidan yayi…bessha tace goggo ki zauna inna gama tsakar gidan yabushe sai kifito kigani goggo ta kuke dole saita gani tako fito kaman abu kaman wasa goggo na fitowa santsin dan madinan dake kafanta ya kwasheta tai wani irin mummunan faduwa jikake timmmm bessha batasan lokacin data wurgar da tsintsiyan taje wuri goggo tana kuka goggo sannu tashi dan allah saida nace karki taho amma me tana juyo goggo taga bakin goggo ya karkace ko motsin kirki batayi bessha tana girgiza goggo tana goggo dan allah mike goggo taga goggo ko motsawa ta kasa aguje ko takalmi batasaba tafita waje kiran basir dama yau taji hamma nafadama mama zaikai jikan goggo rafi.tana tuna haka tai hanyar rafi aguje tana kuka tana zuwa tahangosu suna zaune takarasa tana kuka tafada jikin basir tana kuka mai ban tausayi jikinshi yay wani yarrrr ya tureta yace lpy?? ta dago jajayen idonta tace goggo tafadi tamutu bata
magana.hamma yace wai mesa bakida hankaline bessha goggon ce ta mutu tace wlh yaya ba karya nayiba kuzo muje kugani aguje dukansu sakayi hanyar gida
Suna shiga gidan suka hango goggo akasa aguje basir yakarasa kanta duk ya rude yace goggo dan allah karki mutu goggo nafiso kiga aurena kiga tattaba kunnen ki dakika damu kinaso kigani kafin ki mutu duk ya rude harda kuka bessha ma tana gefe sai rusar kuka take yaya hamma ne chan ya lura kaman kirjinta na buguwa yay maza yakarasa wajen yataba kirjinta yaga yana bugawa yace basir da ranta goggo nada ranta
Maman shakur
[27/08 8:34 AM] Aishat muh’d: 10
Matar sojaa
Da sauri basir yatashi shima yataba kirjinta yaga tana numfashi yay maza yaciro wayanshi daga aljihunshi yay dialing number dad dinshi ringing daya biyo ya dauka
Hello my son sojana ya kake??
Yace dad ba lpy
Dad yace maiyafaru??
Da muryar kuka yace dad goggo tafadi akasa kuma kaman tasamu stroke.dad yamafi danshi rudewa yace maza maza sata amota ka shigo da ita kano yanzu nikuma zanje asibiti naima likitoci magana muna jiranku yace ok dad ya kashe wayan yatashi yaje yabude garejin gidan yafito da mota shida hamma suka ciccibi goggo suka kaita cikin mota bessha itama tafito wai zata bisu hamma yace ba inda za’a dake ta durkushe a wurin tana wani irin kuka kaman zata mutu tabama basir tausayi amma hakanan zata hakura asibiti ba wurin zuwan yara bane suka shiga mota sukadau hanya sai garin kanon dabo
Bessha tasha kuka hakanan tamike ta tafi gida tana kuka tana shiga mama tazo a rude tana lpy auta ? tace mama goggooooo mama tace maiyasami goggo tace faduwa tayi kaman ta mutu amma jikanta da hamma sun sata a mota sunkaita asibiti a kano shine sukaki zuwa dani tana magana tana kuka mama ta jawota jikinta tana lallashi tace kiya kuri zata warke kidena kukan nan karki ciwo ga jikinki yay zafi kinji kiyimata addu’a zata warke.tana kuka tace mama wlh in goggo tamutu bansan yanda zanyiba wlh mama inasonta sosai mama taciga da lallashi tace bazama tamutuba.
Bangaren su basir suna kaiwa aka karbi goggo likitoci suka dukufa akanta ana ceto lafiyanta amma hakan bai samuba dan goggo tariga tasamu paralyze
Wani doc abokin dad ne yafito yace kubiyoni office su
Showing 1 words to 3000 words out of 18889 words