Ki daina mini fishi Ubangiji ne shaidar ina cikin takurarren yanayi a dalilin auren da zan yi da kuma fishinki!
Ta numfasa ta ce"Na huce maigado. Amma kin sani tun filazal jinina bai hadu da yaron nan ba, nima zan roke ki. Ki yiwa Allah ki yi mini adalci kada ki saka ni mu'amala da shi, kada ku samu sabani ki fada mini domin zan sake tsanarsa ba kuma zan ba ki shawara mai dadi ba a kansa. Idan kuwa hakane to kawai mu yi zumuncinmu da harkarmu a tsakaninmu amma kada na shiga cikin aurenki na roke ki, da sunan Ubangiji ki yi mini wannan alfarmar dan so nake aurenki ya yi k'arko ya kuma yi albarka". Da kuka sosai na ce "Ba zan fada miki ba, ba zan saka ki ba tunda na gane ba kya son shiga din. Amma ki sani wannan matakin zai iya zama nakasu a zuciyata, domin kinsan yadda na saba sharing damuwata da ke. "
Ta numfasa ta ce "Ina fatan matsalolin da zaki shiga a gidan aurenki su zama kadan ne kuma masu sauki sosai."
Har aka yi sallar azahar muna tare cikin wani irin yanayi mun yi jigum jigum kowa na ta sake saken zuci, ba kuma mu sanyawa cikinmu komai ba.
Taron Yaya Faruk kuma sai lokacin ya tashi bayan sun yi jam'in sallah. Kowa ya kama gabansa suna ta yi masa tsiyar ya zama ragon namiji tunda ya bari wani ya shigo har cikin gudansu ya ci shi da yaki.
Can muka jiyo shi daga falon momi yana dokawa Abida kira.
Bansan ya aka yi ta kasa amsawa ba domin da gaske jikinta ya yi sanyi irin tubus din nan.
Ba a jima ba muka ji ana kwankwasa kofar ɗakinmu. Murya a dashe ta ce "Bismillah.
Ya turo kofar ya lek'o, da kansa kadan har ya fara hargagin tana jin yadda yake kiranta amma ta yi mukus alhalin ta ji shi. Ganinmu tare a zaune ga alamun kuka nake yi sosai ya sanya ya shigo d'akin gabad'aya ba tare da ya shirya ba.
A matukar gigice ya ce "Me ya samu sarauniyar shaiba ko dai zuciyarki na taya ni alhinin da tawa zuciyar ke ciki na gagarumar asarar rashinki ?".
Yana rufe baki na sake fashewa da kuka mai sauti tamkar dai ba shafe lokaci mai tsayi na yi ina kukan ba.
Ya sake rikice wa ainun domin tunda nake da Yaya Faruk a hankalina wannan ranar ne karon farko da ya kai hannunsa jikina.
Dukkan hannuwansa ya saka ya ruko nawa hannun dake cikin na Abida.
Ya kasa cewa komai domin idanuwansa sun kada sun yi ja matuka da gaske.
Ni da shi muka tsurawa juna ido, tuni nawa idanuwan suke zubar da hawaye yayin da nasa suka cika da kwalla taf.
Soyayyata baro baro a idanuwansa da gangar jikinsa gabadaya. Domin ya yi laushi da alamun rashin kuzarin da yake zuciyarsa ya shafi gangar jikinsa gabadaya. Duk yadda yake da hayaniya da kwarafniya sai da kawo kudin aurena ya yi masa bugun da ya yi matukar kasarra shi ya zama irin yanayina na rashin hayaniya da shiru shiru.
Murya na rawa na ce "Me yasa haka Yaya Faruk? Me yasa ka mini haka? Jamila ta fini tasiri da kyallin goshi a zuciyarka da idanuwanka ko?"
Idanuwansa na cikin nawa ya shiga girgiza kai murya ba amo ya ce "Ina ko kusa, ba haka bane Bilkina. Kawai ba a kaddara mini cikin littafin kaddarata cewar ke matata ce ba. Amma Allah da ya haliccemu ya sani na soki, ina kan sonki. Ba kuma zan daina sonki ba sarauniyar shaiba muddin ina zukar numfashi".
Daga haka ya kasa jarumtar sake cewa uffan illah rungeme ni da ya yi tsamtsam. Gabadaya jikina ya hau tsuma na kasa kwacewa domin na lura gabadaya ya manta cewar ni din ba Abida ba ce da idan ya rungeme ta irin haka shaidan ba zai kawo musu caffa ba dan kuwa muharramarsa alhalin ni kuwa so da begen juna ne a tsakaninmu.
Da kyar na yi jarumtar zamewa na koma gefe ina kuka sosai, abin mamaki sai na ga shima hawaye na zubar masa haka ma Abida. Na sake kaduwa domin Abida tana da matukar taurin rai abin da zai sa zuciyarta ta karaya to kuwa lallai babba ne.
Bai ce komai ya juya ya bar dakin, da alamu ma gidan ya bari gabadaya.
Daga ni har Abida mun koma wasu iri tamkar wadda aka yi mana mutuwar kwatsam. Na kuma gane a yanzu tana tausayina, ta kuma daina jin haushina domin ta daina kyarata kullum a tausashe take yi mini magana. Har muka koma makaranta bamu wani wartsake gabadaya ba.
Sahal da kansa ya gane ina cikin takurarren yanayi. Domin gabadaya bana mararain amsa masa waya kamar yadda nake yi a lokutan baya.
Har zangon karatunmu ya fara nisa, sannan na warware na cigaba da sauraran Sahal cikin dadin rai.
Domin shima na gamsu yana sona gabadaya ya rasa sukuni a dalilin sauyin da yake ga ni a tare da ni, kullum yana zarya tsakanin Zaria da Kano.
Sannu a hankali muka kammala wannan zangon cikin nasara.
Muka koma gida muka tarar an kammala komai na siyayyar aurena wanda Yaya Asad ne ya siya kayan daki tunda ga kan gado da setin kujera na alfarma. Hatta su firij da talabijin. Ya ce lokaci ya yi da su Baba zasu fara hutawa da hidimarmu, su fara shan yayan itace da suka shuka bayan dogon kulawa da suka yi da wannan dashen.
Gidan maza sun kawo lefe da ya amsa sunan lefe domin kuwa ba karamin dukiya aka zuba ba. Ba yadda za'a yi ka ce angon bai fara aiki ko kuma ba sana'a mai k'arfi a hannunsa ba.
A bakin Ansari na ji sati uku masu zuwa ne aure. Na riga kuma na sani Zaria zan zauna domin Baban Zaria ya bashi wani karamin gida a cikin Hanwa ya zauna dan kada karatuna ya samu tasgado.
Duk yadda nake son Sahal amma na kasa jin doki da farincikin auren. Da zarar na ga giftawar Yaya Faruk da yadda ya zama sukuku sai na ji komai ya fita a kaina.
Mahaifiyata kuwa takanas ta samo mini maganin sanyi daga Kano. Itama hanyarsa aka yi mata domin daga Chad ake kawo saiwowin. Kwanaki biyu kacal da fara shan maganin na fara jin marata sakayau. A farko ban mayar da hankalina wajen shan ba, amma jin na samu sauyi a jikina nan da nan ya sanya na mayar da hankali nake sha, mussaman yadda nake jin matsalolin da sanyi ke jefa mace a ciki. Hadakar bandakin makaranta kadai ya isa ya sanya infection yi mana katutu.
Haka wani hakkin daka mai kyau kullum sai ta tsare ni na sha a cikin yogurt ko Madara. Tun a lokacin na gasgata kayan Bojuwa Herbs masu asalin kyau ne ga rahusa.
08032773332 tuntubi wannan layin don samun naki kayan gyaran na mutanen Chad.
Saiwowin dahuwar kaza ta siya ta hada ta dafa mana tare da ita. Na dinga tunanin wai har yanzu mami suna yin harkar nan ne?
Abida da Basma Maska ne kadai suka yi mini kawance, duk da Basma a kano take karatunta na jamia hakan bai sa kawancenmu ya yi rauni ba. Tare da mahaifiyarta da kanwarta suka zo. Da yamma suka koma, suka barta sai washagari zata tafi.
Ranar 15/7 aka daura aurena da Sahal Sulaiman Mashi a babban masallacin juma'a na Funtua.
Yaya Asad da dukkan iyalinsa sun zo daga Enugu.
Anty Rukayya kuwa matarsa Dispenser, oven da microwave ta kawo ban da kayan souvenirs masu uban yawa dan kuwa har da farantan tangaran da kofina mai dauke da sunana da na ango. Courtesy Mr& Mrs Asad Funtua family. Sosai bikinmu ya yi armashi. Matar Yaya Faruk kuwa tamkar ta zuba ruwa a kasa ta sha dan tsananin murnar da take ciki.
Lafiya lau aka yi hidimar bikina cikin walwala da nutsuwa.
Ban sake gane Abida tana sona tamkar yadda nake sonta ba sai ranar da za'a kai ni dakin aurena. Tun safiyar ranar take kuka, sai da tayarwa da dukkan wanda suke gidan hankali domin gaskiyar magana ba wanda ake so a gidanmu irin Abida. Duk yadda take a baude da kuma tsautsaren ra'ayi tana da wani iri jini mai tasiri. Kowa sonta yake yi tare da kaffa kaffa da ita, ba iyayenmu ba, ba kuma a tsakaninmu ba.
Da akace na fito za'a tafi ta rike ni gam nima kuma na riketa na ki tashi. Yaya Faruk da ya ga zamu batawa su baba babba lokaci tunda zuwa zasu yi su juyo sai ya shigo dakin namu. Ya saka hannu ya janye ta ya sakata a jikinsa yana fadin "Ai ba rabuwa kuka yi ba autar momi. Ina ce nan da sati hudu ma hutun zai kare ki koma Zaria ku hadu ku cigaba da rayuwa tare?"
Bata ce masa komai ba. Ta cire zoben hannunta wanda na gold ne ta kamo yatsana na hannun dama ta sanya mini. Ta ce forget me not Bilkina. Sannan duk ranar da na haihu to kawai ki kaddara kin sake haihuwa dan na san kafin nan, kin haifo mini nawa, hakurin da kika yi da ni a tsawon rayuwarmu ba zai tafi a banza ba, zan miki alherin da zaki tabbata kina sona. Fatan alheri mai yawa! Sai kuma kuka ya sake kwace mata.
Ina kuka sosai Yaya Faruk ya fita da ni. Domin bayan ii rabuwata da gida ba karamin raunana zuciyata ta yi da soyayyata da na gani a tare da Abida ba.
A motar baba babba C.R.V. muka tafi. Yaya Faruk ne mai tuki sai Baba babba da baba karami. Duk yadda su baba suka so Yaya Asad ya shigo a tafi da shi tunda ya riga ya dauki girma yana hurar da su dawainiya ya sanya suma suke jagorantar da shi akan sha'aninmu. Kansa a kasa ya ce "Allah ya kaiku lafiya Baba. Ga Faruku nan duk daya ne. Ya leko ya ce "Ki zama mai hakuri, ki sake ninka hakurinki. All the best maigado!
Daga haka ya matsa gefe. Cikin nutsuwa Yaya Faruk ya ja motar muka tafi.
Gidan Baba. Zaria aka kai ni. Baba babba ya rike hannuna ya damkawa wan mahaifin Sahal kuma waliyinsa amanata. Shi kuwa ya saka hannu ya rike hannuna gamgam.
Yana fadin "na karbi amaana in sha Allah y'arku tana amintaccen hannu."
Tarba ta karrmawa ya yi mana, iyalinsa kuma suka baibauemu da abinci da na sha, duk ni kaina kasa yake kuma a kunshe cikin mayafi . Basu wani jima ba suka tafi suka bar ni a gidan Baban Zaria. Zuciyata sai tsallen bad'ake take yi, yanzu shike nan na bar gidanmu gabadaya sai dai na je da bakunta? Iyayena da kansu suka dauko ni suka kawo ni wani gidan da nufin na zama cikin ahalinsu muddin rai. A raina na dinga jin lallai al'amarin aure ba karami bane a addini da rayuwa ba.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
*Lafazi writer's*
13
Message Amreesh spices & more on WhatsApp. https://wa.me/message/Y7KSRJ7PDQSCC1
*Fatan alheri ga*
*Haj Dr Safiya Saulawa*
*Haj Zahra Shehu*.
Sai da aka yi sallar isha sannan Baban zaria da matarsa da ake kira da Mama suka kai ni gidana da babu nisa tsakaninmu da su. Unguwar kusa ne kwarai da jamiaar.
A gidan muka tarar da shi tare da amininsa Lawal.
Addua sosai Baba ya yi mana tare da jaddawa Sahal girman hakkina da yake kansa.
Haka nima ya ta nanata mini na kulla abota da hakuri da kuma juriya, sanna na gane biyayyar da aka kallafa mini na yi masa umarnine daga Ubangiji. Dan haka duk abin da zan yi masa na hidima na yi min Allah dan kuwa shi ya shirya tsarin aure da kansa. Mama ta shigar da ni cikin dakina ta zaunar da ni akan gadona tana ta yi mini fatan Ubangiji yasa na zama tsohuwar gidan.
Basu wani jima ba suka tafi suka bar ni a sabon gidana da zan fara sabuwar rayuwa a cikinsa.
Jin ana kiran sallar magahariba ya sanya suka tafi, su Sahal suka rakasu wajen mota suna ta godiya da ban gajiya gasu Baba, sai da motarsu ta bace musu. Basu shigo ciki ba suka wuce masallaci dan sauke farali.
Bayan an idar suka shigo da ledoji da alamu sun siya tun dazu a mota suka barsu.
A guggurje ya yi barkwancinsa tare da ajiye mini bandir din yan 200 wai kudin siyen baki.
Ya yi mini sallama ya wuce, dan hanyar Katsina zai kama a daren nan.
Da kazangi ya dawo ya zauna daf da ni ya rungume ni yana shakar kamshina. Gabadaya na takura, bansan meyasa ban ji tsumin da na ji a lokacin da Yaya Faruk ya rungume ni ba a yanzu.
Tabbas jikina ya shiga bakon yanayi da bai saba ba, ban sani ba ko tsananin alhinin rabuwa da ahalina tare da fargabar yadda zan shiga cikin sabon ahali ne oho.
Cikin nutsuwa ya ware mayafin da na lulluba da shi. Ya mikar da ni ya ce "Zo mu je falo mu ci abinci. "
Tsire ne mai kyau sai yogurt da kuma ruwan roba masu sanyi.
Duk yadda nake jin yunwa ban iya cin naman ba, sai yogurt din na sha, shima ba wani mai yawa ba.
Bai wani sake ba, sai da ya dawo daga sallar isha.
Ya sake janmu sallar nafila ya yi mana adduar zaman lafiya da albarkar rayuwaa.
Da rawar Jiki ya mannu da ni ya ce "Yau ranace ta mussaman a tarihin rayuwarmu gabadaya. Ina fatan Ubangiji ya sanya albarka a dukkan zaman da zamu yi."
Murya babu amo na ce ",ameen".
Duk yadda nake jin bakunta ta kewaye ni sai da ya hilace ni ya dangana ni da lafiyayyen gadonmu da ya sha shimfida ta alfarma.
Cikin gaggawa yake yin komai, gabadaya ya dinga sarrafa ni, ya jima yana shafata tare da kissing dina. Bai samu nutsuwa ba sai da ya tabbatar ya isa inda ya dade yana fatan ya isa. Bai wani jima ainun ba. Yayin da ni ban wani gane komai ba sai radadi.
Na kalle shi yana ta numfarfashi, daga haka barci ya yi awon gaba da shi. Na jima ina ta sake saken zuci ban kuma isa na hakaito mai nake sake sake a akansa ba.
Na duba wayata na ga shadayan dare. Na mike na shiga bayi dan yin wanka. Domin Mami ta ce mini kada na bari na dinga barci da janaba in ba dole ko lalura ba.
Na gasa kaina sannan na yi wanka. Har na kammala na shirya bai motsa ba. Na lallaba na kwanta a gefensa.
A haka nima barci ya yi awon gaba da ni.
Bamu makara sallar asuba ba, sai dai da muka koma din sai wajen goma muka farka a dalilin dukkanmu mun tara gajiya, na fito daga wanka ina shiryawa cikin nutsuwa, shi kuma yana daga kwance yana kallona cikin murmushi.
Daidai lokacin kuma ya fita ya karbo abin karin kumallo da aka aiko mana daga gidansu.
Funkaso ne da kunun gyada. An zuba cikin kyawawan kwanuka.
Kaitsaye dakin ya shigo da kwandon. Ya zuba mini ido ina sanye cikin guda daga cikin kyawawan material din Malaysia, mai kalar siminti da yarfin kwanduwar kwai.
*Contact umm Nihla for all your *Malaysian fabrics.
*Malaysian Batik and more*
*All are unique and classy*
*Available wholesale and retail*
.......
Ya ce "Billy kin kara kyau sosai
Na murmusa cikin kunya na ce "Na gode ".
Ya wuce bayi yana ce wa "bari nima na yi wanka kada tazarar da kika yi mini a kyau ya sake tsananta."
Na murmusa ba tare da na ce kanzil ba.
Bai wani jima ba,¹0 pop-up ya fito daure da tawul na yi maza na dauke kaina. Bai ce komai ba ya fice zuwa daya dakin da yake a matsayin nasa.
Na hanzarta canja zanin gadon da duk ya baci da jinin budurci na canja wani. Na shiga bandaki na kama duk inda ya baci na wanke, na yarfe sannan na ninke na baza shi akan kyauren bandakin.
Ya shigo sanye cikin yadi mai taushi shudi kalar sararin Subhana(sky blue).
Sosai ya yi kyau zuciyata ta doka da tsananin gaske, take raunin da soyayyarsa ta yi a dalilin Yaya Faruk ya kau, mai kyaune irin wanda nake so duk da dai siriri ne irin sosai din nan, na tabbatar sirintarsa tana karawa tsayinsa kaimi. Sabuwar soyayyarsa ta sake yun mmkuro mini tana sake bin dukkan sassan jikina tana mamaya da k'arfin gaske.
Idona ya kada kwallar shauki ta cikasu taf.
Da hanzari ya iso inda nake. Ya ce "sannu da aikin lada Bily. Allah ya yi miki albarka! Mu je mu karya yunwa nake ji sosai."
Gabadayanmu kamshi muke yi. A plate daya ya zuba mana abincin. Ya turo mini kofin shayi gabana tare da ce wa "zuba sugar da su madara yadda zasu yi miki".
Ban ce komai ba, domin kaina a kasa yake, kunya da bakunta ke dawainiya da ni gabadaya.
Cikin nutsuwa da walwala muka karya duk da ni kunya ta yi mini dabaibayi.
Bai fita ba sai da aka yi sallar azahar. Ya yi tafi masallaci ya ce zai shige gida ya gaidasu Baba.
Na idar da tawa sallar. Na dauko wayata da take kashe tun daren jiya.
Na kunna, na jinkirta ta daidiata.
Mami na fara kira, ta amsa da walwalar da take alamta mini ta yi kewata sosai.
Har na ji dadin yadda ta mu'amalance ni. Ta dinga fadin nasan kina da hakuri da shanye damuwa, ki yi kokarin ninka hakurinki Bilki, hakurin nan dai shine aure, shine ma rayuwa gabadaya. Murya babu amo na ce "To Mami na gode Allah ya kara miki lafiya da hakuri. Ta amsa da fadin "ameen, amma ai ni bana hakurin da zan cutu, a sha'anin aure ne kawai nake dukkan hakuri domin zawarci bashi da dadi Bilkisu!
Ko a gaban uwarka da ubanka zaka yi shi kuwa bare ni marainiya ce, tun ba'a aurar da ni ba na rasa uwarta, mahaifina kuwa
Showing 33001 words to 36000 words out of 42772 words
Ta numfasa ta ce"Na huce maigado. Amma kin sani tun filazal jinina bai hadu da yaron nan ba, nima zan roke ki. Ki yiwa Allah ki yi mini adalci kada ki saka ni mu'amala da shi, kada ku samu sabani ki fada mini domin zan sake tsanarsa ba kuma zan ba ki shawara mai dadi ba a kansa. Idan kuwa hakane to kawai mu yi zumuncinmu da harkarmu a tsakaninmu amma kada na shiga cikin aurenki na roke ki, da sunan Ubangiji ki yi mini wannan alfarmar dan so nake aurenki ya yi k'arko ya kuma yi albarka". Da kuka sosai na ce "Ba zan fada miki ba, ba zan saka ki ba tunda na gane ba kya son shiga din. Amma ki sani wannan matakin zai iya zama nakasu a zuciyata, domin kinsan yadda na saba sharing damuwata da ke. "
Ta numfasa ta ce "Ina fatan matsalolin da zaki shiga a gidan aurenki su zama kadan ne kuma masu sauki sosai."
Har aka yi sallar azahar muna tare cikin wani irin yanayi mun yi jigum jigum kowa na ta sake saken zuci, ba kuma mu sanyawa cikinmu komai ba.
Taron Yaya Faruk kuma sai lokacin ya tashi bayan sun yi jam'in sallah. Kowa ya kama gabansa suna ta yi masa tsiyar ya zama ragon namiji tunda ya bari wani ya shigo har cikin gudansu ya ci shi da yaki.
Can muka jiyo shi daga falon momi yana dokawa Abida kira.
Bansan ya aka yi ta kasa amsawa ba domin da gaske jikinta ya yi sanyi irin tubus din nan.
Ba a jima ba muka ji ana kwankwasa kofar ɗakinmu. Murya a dashe ta ce "Bismillah.
Ya turo kofar ya lek'o, da kansa kadan har ya fara hargagin tana jin yadda yake kiranta amma ta yi mukus alhalin ta ji shi. Ganinmu tare a zaune ga alamun kuka nake yi sosai ya sanya ya shigo d'akin gabad'aya ba tare da ya shirya ba.
A matukar gigice ya ce "Me ya samu sarauniyar shaiba ko dai zuciyarki na taya ni alhinin da tawa zuciyar ke ciki na gagarumar asarar rashinki ?".
Yana rufe baki na sake fashewa da kuka mai sauti tamkar dai ba shafe lokaci mai tsayi na yi ina kukan ba.
Ya sake rikice wa ainun domin tunda nake da Yaya Faruk a hankalina wannan ranar ne karon farko da ya kai hannunsa jikina.
Dukkan hannuwansa ya saka ya ruko nawa hannun dake cikin na Abida.
Ya kasa cewa komai domin idanuwansa sun kada sun yi ja matuka da gaske.
Ni da shi muka tsurawa juna ido, tuni nawa idanuwan suke zubar da hawaye yayin da nasa suka cika da kwalla taf.
Soyayyata baro baro a idanuwansa da gangar jikinsa gabadaya. Domin ya yi laushi da alamun rashin kuzarin da yake zuciyarsa ya shafi gangar jikinsa gabadaya. Duk yadda yake da hayaniya da kwarafniya sai da kawo kudin aurena ya yi masa bugun da ya yi matukar kasarra shi ya zama irin yanayina na rashin hayaniya da shiru shiru.
Murya na rawa na ce "Me yasa haka Yaya Faruk? Me yasa ka mini haka? Jamila ta fini tasiri da kyallin goshi a zuciyarka da idanuwanka ko?"
Idanuwansa na cikin nawa ya shiga girgiza kai murya ba amo ya ce "Ina ko kusa, ba haka bane Bilkina. Kawai ba a kaddara mini cikin littafin kaddarata cewar ke matata ce ba. Amma Allah da ya haliccemu ya sani na soki, ina kan sonki. Ba kuma zan daina sonki ba sarauniyar shaiba muddin ina zukar numfashi".
Daga haka ya kasa jarumtar sake cewa uffan illah rungeme ni da ya yi tsamtsam. Gabadaya jikina ya hau tsuma na kasa kwacewa domin na lura gabadaya ya manta cewar ni din ba Abida ba ce da idan ya rungeme ta irin haka shaidan ba zai kawo musu caffa ba dan kuwa muharramarsa alhalin ni kuwa so da begen juna ne a tsakaninmu.
Da kyar na yi jarumtar zamewa na koma gefe ina kuka sosai, abin mamaki sai na ga shima hawaye na zubar masa haka ma Abida. Na sake kaduwa domin Abida tana da matukar taurin rai abin da zai sa zuciyarta ta karaya to kuwa lallai babba ne.
Bai ce komai ya juya ya bar dakin, da alamu ma gidan ya bari gabadaya.
Daga ni har Abida mun koma wasu iri tamkar wadda aka yi mana mutuwar kwatsam. Na kuma gane a yanzu tana tausayina, ta kuma daina jin haushina domin ta daina kyarata kullum a tausashe take yi mini magana. Har muka koma makaranta bamu wani wartsake gabadaya ba.
Sahal da kansa ya gane ina cikin takurarren yanayi. Domin gabadaya bana mararain amsa masa waya kamar yadda nake yi a lokutan baya.
Har zangon karatunmu ya fara nisa, sannan na warware na cigaba da sauraran Sahal cikin dadin rai.
Domin shima na gamsu yana sona gabadaya ya rasa sukuni a dalilin sauyin da yake ga ni a tare da ni, kullum yana zarya tsakanin Zaria da Kano.
Sannu a hankali muka kammala wannan zangon cikin nasara.
Muka koma gida muka tarar an kammala komai na siyayyar aurena wanda Yaya Asad ne ya siya kayan daki tunda ga kan gado da setin kujera na alfarma. Hatta su firij da talabijin. Ya ce lokaci ya yi da su Baba zasu fara hutawa da hidimarmu, su fara shan yayan itace da suka shuka bayan dogon kulawa da suka yi da wannan dashen.
Gidan maza sun kawo lefe da ya amsa sunan lefe domin kuwa ba karamin dukiya aka zuba ba. Ba yadda za'a yi ka ce angon bai fara aiki ko kuma ba sana'a mai k'arfi a hannunsa ba.
A bakin Ansari na ji sati uku masu zuwa ne aure. Na riga kuma na sani Zaria zan zauna domin Baban Zaria ya bashi wani karamin gida a cikin Hanwa ya zauna dan kada karatuna ya samu tasgado.
Duk yadda nake son Sahal amma na kasa jin doki da farincikin auren. Da zarar na ga giftawar Yaya Faruk da yadda ya zama sukuku sai na ji komai ya fita a kaina.
Mahaifiyata kuwa takanas ta samo mini maganin sanyi daga Kano. Itama hanyarsa aka yi mata domin daga Chad ake kawo saiwowin. Kwanaki biyu kacal da fara shan maganin na fara jin marata sakayau. A farko ban mayar da hankalina wajen shan ba, amma jin na samu sauyi a jikina nan da nan ya sanya na mayar da hankali nake sha, mussaman yadda nake jin matsalolin da sanyi ke jefa mace a ciki. Hadakar bandakin makaranta kadai ya isa ya sanya infection yi mana katutu.
Haka wani hakkin daka mai kyau kullum sai ta tsare ni na sha a cikin yogurt ko Madara. Tun a lokacin na gasgata kayan Bojuwa Herbs masu asalin kyau ne ga rahusa.
08032773332 tuntubi wannan layin don samun naki kayan gyaran na mutanen Chad.
Saiwowin dahuwar kaza ta siya ta hada ta dafa mana tare da ita. Na dinga tunanin wai har yanzu mami suna yin harkar nan ne?
Abida da Basma Maska ne kadai suka yi mini kawance, duk da Basma a kano take karatunta na jamia hakan bai sa kawancenmu ya yi rauni ba. Tare da mahaifiyarta da kanwarta suka zo. Da yamma suka koma, suka barta sai washagari zata tafi.
Ranar 15/7 aka daura aurena da Sahal Sulaiman Mashi a babban masallacin juma'a na Funtua.
Yaya Asad da dukkan iyalinsa sun zo daga Enugu.
Anty Rukayya kuwa matarsa Dispenser, oven da microwave ta kawo ban da kayan souvenirs masu uban yawa dan kuwa har da farantan tangaran da kofina mai dauke da sunana da na ango. Courtesy Mr& Mrs Asad Funtua family. Sosai bikinmu ya yi armashi. Matar Yaya Faruk kuwa tamkar ta zuba ruwa a kasa ta sha dan tsananin murnar da take ciki.
Lafiya lau aka yi hidimar bikina cikin walwala da nutsuwa.
Ban sake gane Abida tana sona tamkar yadda nake sonta ba sai ranar da za'a kai ni dakin aurena. Tun safiyar ranar take kuka, sai da tayarwa da dukkan wanda suke gidan hankali domin gaskiyar magana ba wanda ake so a gidanmu irin Abida. Duk yadda take a baude da kuma tsautsaren ra'ayi tana da wani iri jini mai tasiri. Kowa sonta yake yi tare da kaffa kaffa da ita, ba iyayenmu ba, ba kuma a tsakaninmu ba.
Da akace na fito za'a tafi ta rike ni gam nima kuma na riketa na ki tashi. Yaya Faruk da ya ga zamu batawa su baba babba lokaci tunda zuwa zasu yi su juyo sai ya shigo dakin namu. Ya saka hannu ya janye ta ya sakata a jikinsa yana fadin "Ai ba rabuwa kuka yi ba autar momi. Ina ce nan da sati hudu ma hutun zai kare ki koma Zaria ku hadu ku cigaba da rayuwa tare?"
Bata ce masa komai ba. Ta cire zoben hannunta wanda na gold ne ta kamo yatsana na hannun dama ta sanya mini. Ta ce forget me not Bilkina. Sannan duk ranar da na haihu to kawai ki kaddara kin sake haihuwa dan na san kafin nan, kin haifo mini nawa, hakurin da kika yi da ni a tsawon rayuwarmu ba zai tafi a banza ba, zan miki alherin da zaki tabbata kina sona. Fatan alheri mai yawa! Sai kuma kuka ya sake kwace mata.
Ina kuka sosai Yaya Faruk ya fita da ni. Domin bayan ii rabuwata da gida ba karamin raunana zuciyata ta yi da soyayyata da na gani a tare da Abida ba.
A motar baba babba C.R.V. muka tafi. Yaya Faruk ne mai tuki sai Baba babba da baba karami. Duk yadda su baba suka so Yaya Asad ya shigo a tafi da shi tunda ya riga ya dauki girma yana hurar da su dawainiya ya sanya suma suke jagorantar da shi akan sha'aninmu. Kansa a kasa ya ce "Allah ya kaiku lafiya Baba. Ga Faruku nan duk daya ne. Ya leko ya ce "Ki zama mai hakuri, ki sake ninka hakurinki. All the best maigado!
Daga haka ya matsa gefe. Cikin nutsuwa Yaya Faruk ya ja motar muka tafi.
Gidan Baba. Zaria aka kai ni. Baba babba ya rike hannuna ya damkawa wan mahaifin Sahal kuma waliyinsa amanata. Shi kuwa ya saka hannu ya rike hannuna gamgam.
Yana fadin "na karbi amaana in sha Allah y'arku tana amintaccen hannu."
Tarba ta karrmawa ya yi mana, iyalinsa kuma suka baibauemu da abinci da na sha, duk ni kaina kasa yake kuma a kunshe cikin mayafi . Basu wani jima ba suka tafi suka bar ni a gidan Baban Zaria. Zuciyata sai tsallen bad'ake take yi, yanzu shike nan na bar gidanmu gabadaya sai dai na je da bakunta? Iyayena da kansu suka dauko ni suka kawo ni wani gidan da nufin na zama cikin ahalinsu muddin rai. A raina na dinga jin lallai al'amarin aure ba karami bane a addini da rayuwa ba.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
*Lafazi writer's*
13
Message Amreesh spices & more on WhatsApp. https://wa.me/message/Y7KSRJ7PDQSCC1
*Fatan alheri ga*
*Haj Dr Safiya Saulawa*
*Haj Zahra Shehu*.
Sai da aka yi sallar isha sannan Baban zaria da matarsa da ake kira da Mama suka kai ni gidana da babu nisa tsakaninmu da su. Unguwar kusa ne kwarai da jamiaar.
A gidan muka tarar da shi tare da amininsa Lawal.
Addua sosai Baba ya yi mana tare da jaddawa Sahal girman hakkina da yake kansa.
Haka nima ya ta nanata mini na kulla abota da hakuri da kuma juriya, sanna na gane biyayyar da aka kallafa mini na yi masa umarnine daga Ubangiji. Dan haka duk abin da zan yi masa na hidima na yi min Allah dan kuwa shi ya shirya tsarin aure da kansa. Mama ta shigar da ni cikin dakina ta zaunar da ni akan gadona tana ta yi mini fatan Ubangiji yasa na zama tsohuwar gidan.
Basu wani jima ba suka tafi suka bar ni a sabon gidana da zan fara sabuwar rayuwa a cikinsa.
Jin ana kiran sallar magahariba ya sanya suka tafi, su Sahal suka rakasu wajen mota suna ta godiya da ban gajiya gasu Baba, sai da motarsu ta bace musu. Basu shigo ciki ba suka wuce masallaci dan sauke farali.
Bayan an idar suka shigo da ledoji da alamu sun siya tun dazu a mota suka barsu.
A guggurje ya yi barkwancinsa tare da ajiye mini bandir din yan 200 wai kudin siyen baki.
Ya yi mini sallama ya wuce, dan hanyar Katsina zai kama a daren nan.
Da kazangi ya dawo ya zauna daf da ni ya rungume ni yana shakar kamshina. Gabadaya na takura, bansan meyasa ban ji tsumin da na ji a lokacin da Yaya Faruk ya rungume ni ba a yanzu.
Tabbas jikina ya shiga bakon yanayi da bai saba ba, ban sani ba ko tsananin alhinin rabuwa da ahalina tare da fargabar yadda zan shiga cikin sabon ahali ne oho.
Cikin nutsuwa ya ware mayafin da na lulluba da shi. Ya mikar da ni ya ce "Zo mu je falo mu ci abinci. "
Tsire ne mai kyau sai yogurt da kuma ruwan roba masu sanyi.
Duk yadda nake jin yunwa ban iya cin naman ba, sai yogurt din na sha, shima ba wani mai yawa ba.
Bai wani sake ba, sai da ya dawo daga sallar isha.
Ya sake janmu sallar nafila ya yi mana adduar zaman lafiya da albarkar rayuwaa.
Da rawar Jiki ya mannu da ni ya ce "Yau ranace ta mussaman a tarihin rayuwarmu gabadaya. Ina fatan Ubangiji ya sanya albarka a dukkan zaman da zamu yi."
Murya babu amo na ce ",ameen".
Duk yadda nake jin bakunta ta kewaye ni sai da ya hilace ni ya dangana ni da lafiyayyen gadonmu da ya sha shimfida ta alfarma.
Cikin gaggawa yake yin komai, gabadaya ya dinga sarrafa ni, ya jima yana shafata tare da kissing dina. Bai samu nutsuwa ba sai da ya tabbatar ya isa inda ya dade yana fatan ya isa. Bai wani jima ainun ba. Yayin da ni ban wani gane komai ba sai radadi.
Na kalle shi yana ta numfarfashi, daga haka barci ya yi awon gaba da shi. Na jima ina ta sake saken zuci ban kuma isa na hakaito mai nake sake sake a akansa ba.
Na duba wayata na ga shadayan dare. Na mike na shiga bayi dan yin wanka. Domin Mami ta ce mini kada na bari na dinga barci da janaba in ba dole ko lalura ba.
Na gasa kaina sannan na yi wanka. Har na kammala na shirya bai motsa ba. Na lallaba na kwanta a gefensa.
A haka nima barci ya yi awon gaba da ni.
Bamu makara sallar asuba ba, sai dai da muka koma din sai wajen goma muka farka a dalilin dukkanmu mun tara gajiya, na fito daga wanka ina shiryawa cikin nutsuwa, shi kuma yana daga kwance yana kallona cikin murmushi.
Daidai lokacin kuma ya fita ya karbo abin karin kumallo da aka aiko mana daga gidansu.
Funkaso ne da kunun gyada. An zuba cikin kyawawan kwanuka.
Kaitsaye dakin ya shigo da kwandon. Ya zuba mini ido ina sanye cikin guda daga cikin kyawawan material din Malaysia, mai kalar siminti da yarfin kwanduwar kwai.
*Contact umm Nihla for all your *Malaysian fabrics.
*Malaysian Batik and more*
*All are unique and classy*
*Available wholesale and retail*
.......
Ya ce "Billy kin kara kyau sosai
Na murmusa cikin kunya na ce "Na gode ".
Ya wuce bayi yana ce wa "bari nima na yi wanka kada tazarar da kika yi mini a kyau ya sake tsananta."
Na murmusa ba tare da na ce kanzil ba.
Bai wani jima ba,¹0 pop-up ya fito daure da tawul na yi maza na dauke kaina. Bai ce komai ba ya fice zuwa daya dakin da yake a matsayin nasa.
Na hanzarta canja zanin gadon da duk ya baci da jinin budurci na canja wani. Na shiga bandaki na kama duk inda ya baci na wanke, na yarfe sannan na ninke na baza shi akan kyauren bandakin.
Ya shigo sanye cikin yadi mai taushi shudi kalar sararin Subhana(sky blue).
Sosai ya yi kyau zuciyata ta doka da tsananin gaske, take raunin da soyayyarsa ta yi a dalilin Yaya Faruk ya kau, mai kyaune irin wanda nake so duk da dai siriri ne irin sosai din nan, na tabbatar sirintarsa tana karawa tsayinsa kaimi. Sabuwar soyayyarsa ta sake yun mmkuro mini tana sake bin dukkan sassan jikina tana mamaya da k'arfin gaske.
Idona ya kada kwallar shauki ta cikasu taf.
Da hanzari ya iso inda nake. Ya ce "sannu da aikin lada Bily. Allah ya yi miki albarka! Mu je mu karya yunwa nake ji sosai."
Gabadayanmu kamshi muke yi. A plate daya ya zuba mana abincin. Ya turo mini kofin shayi gabana tare da ce wa "zuba sugar da su madara yadda zasu yi miki".
Ban ce komai ba, domin kaina a kasa yake, kunya da bakunta ke dawainiya da ni gabadaya.
Cikin nutsuwa da walwala muka karya duk da ni kunya ta yi mini dabaibayi.
Bai fita ba sai da aka yi sallar azahar. Ya yi tafi masallaci ya ce zai shige gida ya gaidasu Baba.
Na idar da tawa sallar. Na dauko wayata da take kashe tun daren jiya.
Na kunna, na jinkirta ta daidiata.
Mami na fara kira, ta amsa da walwalar da take alamta mini ta yi kewata sosai.
Har na ji dadin yadda ta mu'amalance ni. Ta dinga fadin nasan kina da hakuri da shanye damuwa, ki yi kokarin ninka hakurinki Bilki, hakurin nan dai shine aure, shine ma rayuwa gabadaya. Murya babu amo na ce "To Mami na gode Allah ya kara miki lafiya da hakuri. Ta amsa da fadin "ameen, amma ai ni bana hakurin da zan cutu, a sha'anin aure ne kawai nake dukkan hakuri domin zawarci bashi da dadi Bilkisu!
Ko a gaban uwarka da ubanka zaka yi shi kuwa bare ni marainiya ce, tun ba'a aurar da ni ba na rasa uwarta, mahaifina kuwa
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12 Chapter 13Chapter 14Chapter 15