kaina ba. Shiyasa na toshe dukkan ƙofar da za'a mini auren zumunci.
Tunda har yaya Faruku bai furta so ko wani yin motsi mai ƙarfi akan akan soyayyata da shi ba, ai kuwa sai dai a yi a bar ni, babu wanda zan so, in ba shi ba a cikinsu.
A kai a kai Sahal yake zuwa zance. Duk ranar da zai zo bana cikin sukuni, girki kwalliya duk na musamman ne. Abida kuwa bata sake cewa komai akan lamarinsa ba. Da gaske ta runtse idanuwanta daga lamarinmu. Sai dai akai akai take yi mini habaicin na ƙi ƴan-uwana ko karar zumunci ban iya ba.
Ranar da ƴan kirkin suke kusa ta leƙa su gaisa, ranar da take a botsare ko tunkararta bana yi. Yaya Munirah dai duk sadda ya zo sai ta je sun zanta akan shirye shiryensu na tafiya call to bar a jihar Kano.
Wata ranar juma'a da yamma muna tare da Sahal na ci kwalliya ta burge wa. Sai jifan juna muke yi da wani irin murmushi da yake fitowa daga ƙasan zuciya. Ina samun nutsuwar zuciya idan ina tare da shi. Ina jin farin ciki mai daɗin gaske. Domin tunda ga ƙasa zuciyar nake jin farin ciki da zumudi.
Muna haka yaya Faruku ya shigo harabar gidan.
Kai tsaye ya iso inda muke ya mikawa Sahal hannu suka gaisa. Cikin barkwanci ya ce "Dama na matsu na ganka na ga mai ka taka ne daga zuwanka ka rushe gwamnatina a wajen Bilkisu tashi guda?".
Kunya ta kama shi ya ce "Yayanmu ba rushe ka na yi ba, girma ka ci ka matsa mini kaɗan".
Yaya Faruku ya faɗaɗa murmushinsa ya ce " Tunda kasan ba ƙarfina kafi ba shike nan, na zama surukinka, ka riƙe mini ita amana domin ita ɗin mai haƙuri ce kuma mai nutsuwa ce."
Cikin kunya Sahal ya ce "Da ikon Allah zan rike ta da kyautatawa".
Daga haka ya kalle ni, Ni kuma cikin nauyi na ce "Yaya Faruku barka da yini."
Ya amsa yana faɗin ai na ɗauka kin zama kurma". Ya wuce cikin gida.
Ya numfasa ya ce "Yaya Faruku mutumin kirki ne Bilkisu".
Na ce "Sosai fa"
Muka cigaba da hira cikin shauki domin ban ƙi mu tabbata muna hira cikin wannan yanayin mai dadi da walwala ba.
A wannan dogon hutun mun sake shaƙuwa domin tsallaken kwana ɗaya kacal yake yi. Wani zubin ma kullum ne sai ya zo ko tsoron titi ba ya yi.
Ranar wata Laraba da ba na mantawa da yammaci lis muna hirarmu a inda muka saba zama wato harabar gate dinmu daga gefe, domin mu a gidanmu ba'a yarda da hirar falo. Sai dai a filin Allah ƙarkashin bishiyoyi da furannai.
Ba zato yaya Asad ya bayyana shi kaɗai babu ƴan rakiya daga dukkan alamu a jirgi ya iso Kaduna. Sai kuma ya iso Funtua tunda haka yake yi matukar zai zo ganin gida.
Ya hango ni, ya dunfaromu cikin saurinsa domin shi mutum ne mai hanzari ga shi ƙarfaffa na gaske. Zuciyata ta buga, bansan me ya sanya nake matuƙar nutsuwa idan na ganshi ba, hakanan a duk sadda idanuwana suka hango shi ko da ban ji kalaman bakinsa ba sai zuciyata ta harba da tsananin gaske. Na kan rasa wannan kasafi sai dai na fi tunanin tsoronsa da ya gina a zuciyata tun ina mitsitsiyata. Duk da a yanzu kirki yake yi mini tare da tarairayata fiye da ƴar ɗakinsa sarkin rikici Abida.
Yana isowa na mike tsaye murya a dashe na ce "Baban Bilkisu sannu da zuwa. Ya su Nana da Anti?"
Maimakon ya amsa da baki sai ya cire hularsa tare da ƙamewa ya kuma sara mini tamkar dai yadda ya taɓa yi mana ni da Baba babba shekarun baya.
Daɗi ya ratsa ni har zuciyata domin gaisuwa ce mai ƙololuwar daraja bare kuma ace mai ɗamara ne ya yiwa farar hula irina da ba ni da wani muƙamin komai sai dan girmamawa kawai.
Murmushi ya subuce mini, na ce "Baban Bilkisu na gode da karamcinka".
Ya taya ni murmushi fararen haƙoransa suka haska baƙar fuskarsa.
Ya ce "So nake Bilki ta manta batun duniyar yaya Asad ta yi ta ganinsa a cikin mutanen da suke sonta tare da kambaba dukkan lamarinta."
Na ƙayalkyale da dariya na ce "Ai tunda ka mini takwara na yafe maka, na manta komai na gane na sha gaban Abida. Amma fa ni gaskiya har gobe yaya Faruku ne best"
Ya yi waiwaye ya ce "Idan autar momi ta ji wannan maganar ai kin kunyata ni Maigado".
Na sake yin dariya na ce "Ai gaskiya na furta".
Daidai lokacin Sahla ya gaishe shi cikin nutsuwa domin ya lura ma tamkar bai lura da shi ba, ko kuma mun manta da shi gaba-daya.
Ya amsa gaisuwar babu yabo babu fallasa sai dai ko kadan babu raha ko karramawa. Ya wuce cikin gida ya barmu.
Hirar da bata yiwu ba ke nan. Domin mintina biyar ya ƙara ya mike tare da faɗin "Zan wuce ina son na isa Zaria da wuri. Baba ya ce zan raka shi dubiya bayan maghriba".
Ban kawo komai a raina ba na ce "To"
Muka yi sallama ya tafi a sanyaye.
Na shiga falon Momi na tarar da shi tare da su Baba suna taya shi rarrashin Abida domin tunda ta gaishe shi bata sake kula shi ba, duk yadda take tatsarsa a dalilin bai mata takwara ba, sai ni ya yiwa, bai sa ta huce da shi ba har lokacin.
Na zauna na ce "Wato Allah ya so ni da ba zamu yi kishi ba Abida."
Ta galla mini harara tare da ce wa "Yo ai ke tsare mini gaban da kika yi ko kishiya sai haka. Kowa Bilkisu, kowa Maigado, duk wanda suke jama'atane a da kin kwace mini su a yanzu. Abin kaicon kuma naki mutanen kin riƙe su gam tsabar haɗama."
Gaba-daya aka kwashe da dariya, yayin da ta gintse tata dariyar da take neman ƙwace mata.
Baba ya ce "Abida ƙanwar Bilki kina sanya ni nishadi, idan kuna makaranta sai na ta jina tamkar wanda ya rasa wani abu. Domin kullum kuna ɗebe mini kewa na yi ta tuno da ƙuruciyarku."
Yaya Asad ya ce "Yaran nan kun samu duniya, Allah yasa lahirarku ta zarce hakan."
Wannan karon Abida ce ta yi dariya tare da ce wa "Kai Yaya!
Ya murmusa ya ce "To me zan ce? Gaba-daya kun tattare soyayyar ya'yan fari da ya'yan karshe ku kaɗai. Fatan Allah yasa kuna ibada tuƙuru yadda lahirarku ma zata yi muku daɗi fiye da nan"
Ya nisa ya ce "Wai ina Muni ban ji ɗuriyarta ba".
Baba ya ce "jiya ta je Katsina yayarsu bata jin daɗi shine ta je ta ɗan kula mata da yara kafin tafiyarsu Kano ta taso".
A ladabce ya ce "Allah ya bata lafiya, amma mun yi waya bata faɗa mini bata da lafiya ba".
Baba ya ce "ka manta zurfin cikinta ne? Kasan kuma ce wa zata yi, kana nesa ba zata tayar maka da hankali ba tunda ba kashirban take ba '".
Bamu tashi ba sai da aka fara kiran sallar magarib. Ni da Abida muka yi sashinmu dan bawa baba babba damar ganawa da baban Bilkisu sosai. Tunda ya mini takwara na koma ce kishi hakan a gabansa ko ba'a gabansa ba. Na kuma fahimci yana son sunan domin da karsaahi haɗi da kazangi yake amsawa.
Daren ranar shiru Sahal bai ƙira ni ba, tunda tara da rabi ta yi na shiga tunanin ko lafiya domin da zarar tara ta yi idan muka fara waya muna kaiwa goman dare ko fiye da haka tamkar da akan iska muke magana ba kuɗi ba.
Da goma ta yi sai na kasa haƙuri na buga masa, amma har ta katse bai ɗauka ba, kuma bai katse dan ya biyo baya ba. Ban shiga mamaki ba sai da aka shafe mintina talatin bai bugo ya gabatar da uzzirin baya kusa ko yana tare da iyayensa ba. Gabadaya na daburce, na sake ƙira a karo na uku sai na ji an kashe wayar ma bakiɗaya. Da yake fashin sallah nake yi, sai na takure a kan gado gaba daya na rasa jin daɗin zuciyata. Yayin da tuni Abida ta yi barcinta cikin nutsuwa. Idan akwai abin da yake burge ni da Abida to rashin sanyawa kai damuwar duniya ne. Samsam bata yarda ta yi sabo da abin da zai dame ta. Kusan kullum sai ta ce mini soyayya lalura ce kabiran. Kafin ta yi barci ma da ta lura da yanayina sai da ta ja tsaki ta ce "Ya miki sabo da kalaman da kaso saba'in cikin ɗari na daɗin baki ne ba na gaskiya ba. Da zarar an haɗaku zaman aure hirar mintina goma ma sai an wayi gari ba zai iya ware wa cikin lokacinsa ya yi da ke ba, a yanzu kuma ya yi miki sabo da doguwar hirar da idan baki ji daga gare shi ba zaki kidime ki kasa sukuni. Me za'a yi da soyayya irin taki ne Bilki?"
Da nasan gaskiya ta faɗa sai na kasa amsa mata domin ba ni da bakin yi mata musu ko raddi dan idan ta kaikaice ta fara cashe mini sai ta sanya ni kuka na gaske. Sannan zata juya ta yi kwanciyarta, cikin nutsuwa zan ga tana sauke numfashi tabbacin barci mai cike da nutsuwa take yi.
Da ƙyar na yi barci ina ta saƙesaƙe ko jinya ce ta kwantar da shi tunda a kullum sai ya ce mini ba zai iya barci bai ji muryata ba. Shiyasa ma baya ƙirana sai ya yi sallar Isha domin da zarar mun gama waya barci yake yi muryatace abu na ƙarshe da yake ji a ko wanne dare.
Ina idar da sallar asuba na sake ƙiran layinsa amma shiru kake ji a kashe take.
Na shiga damuwa duk yadda nake son komawa barci ranar ban samu sukunin komawa ba.
Sai da muka karya muka yi sashen Momi hannuna ɗauke da ledar alawa da biskit masu tsada cikin wanda Sahal yake kawo mini na ɗiba na zuba a leda da yawa da mufin na bawa baban Bilkisu ya kaiwa Hafcy. Muka tarar shi kadai yana karyawa kuma ya yi haramar komawa. Muka gaishe shi ya amsa tare da faɗin "Na shiga gaida Mami da Baba ƙarami baku tashi ba".
Abida ce ta amsa da ce wa "ki ce ban tashi ba kawai, amma ita bakam ta yi bata cikin hayyacinta saurayinta ya yi mata fushi tun daren jiya ta rasa walwala da kuzari ".
Ga mamakina sai na ga ya ɓata rai, bacin ran da ya bayyana har a fuskarsa. Da farko tamkar zai share sai kuma ya kasa hadiyewa ya ce "Har haka kika bari ya mamaye ki ne Bilki? Ni ba dan kar na zama babban kwabo ba da sai na ce miki kin fishi ƙarfi da karsashi, gabadaya fa siffar mata gare shi wannan yaron, dan dai kina sonsa ne, autar momi ta yi gaskiya zubin makirai ne da shi, kin kasa ganewa, bansan me yasa ba zaki gane gaskiyar lamari ba, yanzu saboda Allah Maigado menene aibun auren mai mata ne?"
Zuciyata ta harba da tsananin gaske.
Amma saboda yadda Abida ta kasa ta tsare tana kallonmu nasan ba iya kallon kawai take yi ba, har da nazari. Domin kamewa ta yi tana kallonmu cikin tsananin nutsuwa.
Dan haka cikin rawar murya haɗi da kuka na ce "To shine ya tunkare ni da sunan soyayya ban da shi babu wani, sannan mai matar ai bai zo ba, bare ace na jingina masa aibu."
Bansan ya aka yi ba Abida ta yi fit ta ce "Sau dubu nawa zasu zo? Yaya Faruku fa?"
Takaicinta ya shake ni, na rushe da kuka sosai na ce "Da yaushe ya taba tare ni da sunan soyayya ta gaskiya ba ta wasa ba?"
Kafin ta amsa mini Baban Bilkisu ya ce "Kin fita gaskiya. Faruku bai zo da gaske ba, amma akwai wadanda suke son ki da gaske kina tankwabarwa, abokin nan nawa da gaske yake yi, bayan shi akwai wani da zaki amince ya tabbatar mini ko yaushe a shirye yake domin kin yi masa irin sosai ɗin nan".
Abida ta numfasa ta ce "oh Yaya Asad!
Ya yi biris da ita domin sosai ya ɗaure fuska dan haka dole ta kame bakinta ta tsuke.
Ya numfasa ya ce " share hawaye ki ki daina kuka kin ji, ba wacce aka yiwa auren dole a gidan nan, matukar ina raye kema ba za'a yi miki ba, ina miki fatan alheri tsakaninki da yaron".
Daga haka ya mike ya zura hannu a aljihunsa ya ciro ƙudi ya damƙawa Abida ya ce "ke da ita, ku sayi abin da kuke so idan zaku koma makaranta."
A sanyaye ta yi masa godiya. Ni kuwa na kasa yin godiyar.
Ya ce "To mu je ku raka ni mu yi sallama da su Baba."
Na miƙe na zare abin hannuna wanda na stones ne, na sake zaro ribbon din kaina na jefa a ledar alawaer na ce "ga shi ka kaiwa Hafcy, ka faɗa mata I realy miss her silly questions."
Ya murmusa ya ce "Kullum sai ta yi hirarki, kullum sai ta ce "Anty Maigado zata. Ga shi Maigado ba mai fahimta ba ce".
Zuciyar tawa ta sake karaya,.nauyi mai yawa ya kama ni. Na saci kallon Abida na ga itama kallona take da dukkan nutsuwarta.
Haka muka bi bayansa ba tare da mun iya tofawa ba.
Ya yi sallama da kowa, iyayenmu suka bishi da sanya albarka tare da nema masa tsarewar Ubangiji akan dukkan lamarinsa.
Har waje muka bishi ni da Abida.
Bana manta kallon da ya kafe ni da shi, amma bai ce ƙala ba, illah faɗin "ku kula da kanku Allah ya sake haɗamu da alheri."
Abida ta rike hannunsa ta ce"Ka kula da kanka yaya! Su Baba na buƙatarka, matarka da ƴaƴanka na buƙatarka, muma muna sonka, kada ka saka damuwa mai yawa akan lamarin wanda baya bukatarka ko ba shi da asara idan ka haɗu da jinya ".
Ya zuba mata ido irin sosai tare da ruƙo dukkan hannuwanta murya cike da rauni ya ce "Zan kiyaye autar momi! Sai dai bana son ki zama mai son kai, ko tursasawa ga rayuwar wani ta hanyar kyara da ƙaranta mu'amala. Kina da hazaƙa, kina da saurin fahimtar al'amurra. Na roki kada ki yi ƙullaci ko kushe wanda Maigado take so "
Ta amsa da ce wa "To" a takaice.
Jikina ya sake sanyi sosai domin na gaskata sona yake yi. Sai dai tabbas bai yi mini ba, duk yadda yake a tsaye kuma ƙarfaffa. Amma bana son auren zumunci, bana son auren mai mata bana son baƙin namiji.
Ya shiga motar da ta zo daukarsa suka tafi.
Abida ta yi gaba ta bar ni da sanyin jiki. Da ƙyar na ja ƙafafuwana na bi bayanta. Shariyar Abida da rashin samun wayar Sahal suka yi mini rubdugu. Yini guda ina ɗaki sai juyi nake yi na rasa sukuni a jika da zuciyata.
Da na idar da sallar la'asar na dauki wayar na sake ƙiran layinsa a karo na barkatai. Cikin sa'a ta shiga, gaba-daya na ji wani irin salama ta shige ni. Sai dai har ta katse ba'a ɗauka ba. Na sauke ina sake gaskata lallai akwai matsala. Sai dai tunanina bai haƙaito mini menene dalilin faruwar haka ba.
Ina ta kokawa da zuciyata akan kada na sake ƙiransa. Ba zato sautin da na sanya masa na real love by massari ta hau tashi. Kamar zan share amma na kasa sharewar.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
11
Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks
*Lafazi writer's*
Jiki na bari na amsa kiran. Ba wani karkasashi ya ce "Na ga tarin missed call dinki, hidima ta sha kaina ban samu sukunin kiranki back ba".
Na yi sororo da waya a hannuna. Domin a yadda na dauka babu hudimar da zata hana ya nemi ji daga gare ni, mussaman wayar dare da ta zame mana kaida.
Tsawon lokacin ban samu sukunin lalubar kalma ko guda ba.
Ya numfasa ya zarce da ce wa "Bilki so nake ki bani dama na turo a tsayar da maganar aure a tsakaninmu. Don so nake yi, na takaitawa kaina zullumi da fargabar rasa ki".
Gabana ya takarkara ya fadi. Aure kuma? Ban ci karfin karatuna ba, duk yadda nake son Sahal ban hakaito na yi aure a lokacin ba, domin dukkan sisters dinmu ba a aurar da su ba sai da suka kammala digiri. Ga Yaya Munira ma bata yi a aure ba sai ni?"
Da rawar murya na ce "Aure yanzu?'
Ga mamakina sai kawai ya katse wayar gabadaya. Ba tare da ya ce uffan ba.
Na rike wayar ina kallonta tamkar wacce zata fahimtar da ni dalilin sauyin da nake ga ni a tare da Sahal.
Gabadaya na sake rikicewa, na kasa gane mai yake yi mini dadi a duniyata. Kwanakin biyun da suka biyo baya masu tsauri ne domin gabadaya Sahal ya yi watsi da ni. Na kasa tattauna halin da nake cikin da kowa. Abida ce abokiyar hirar, sai dai ban isa na tunkareta da maganarsa ba. To ban fada mata matsalata da shi ba kullum a cikin yi mini habaci da shaguben son da nake yi masa ya zarce wanda yake yi mini take. Bare yanzu da take mini fushi akan ban so brothers dinta ba.
To ina kuma ga na bude baki na tabbtar mata damuwar da nake kwana na yini a cikinta Sahal ne sababinta.
Cikin rashin karsashi nake hada kayana na komawa makaranta tunda a sati mai zuwa hutunmu zai kare.
Kwanaki biyu ke nan da nutsuwa ta yi mini tutsu sosai a dalilin kullum lamarina da Sahal na sake cakalkalewa. Na gama tunanina nasan ban yi masa komai ba. Haka kuma nasan bamu samu sabanin ra'ayi ba.
Haka siddan matsalakan ya dauki zazzafan fushi da ni, dan kawai yasan zuciyata ta shaku da shi, ta kuma kambaba sha'aninsa.
*Lame.Ng Skin
Showing 27001 words to 30000 words out of 42772 words
Tunda har yaya Faruku bai furta so ko wani yin motsi mai ƙarfi akan akan soyayyata da shi ba, ai kuwa sai dai a yi a bar ni, babu wanda zan so, in ba shi ba a cikinsu.
A kai a kai Sahal yake zuwa zance. Duk ranar da zai zo bana cikin sukuni, girki kwalliya duk na musamman ne. Abida kuwa bata sake cewa komai akan lamarinsa ba. Da gaske ta runtse idanuwanta daga lamarinmu. Sai dai akai akai take yi mini habaicin na ƙi ƴan-uwana ko karar zumunci ban iya ba.
Ranar da ƴan kirkin suke kusa ta leƙa su gaisa, ranar da take a botsare ko tunkararta bana yi. Yaya Munirah dai duk sadda ya zo sai ta je sun zanta akan shirye shiryensu na tafiya call to bar a jihar Kano.
Wata ranar juma'a da yamma muna tare da Sahal na ci kwalliya ta burge wa. Sai jifan juna muke yi da wani irin murmushi da yake fitowa daga ƙasan zuciya. Ina samun nutsuwar zuciya idan ina tare da shi. Ina jin farin ciki mai daɗin gaske. Domin tunda ga ƙasa zuciyar nake jin farin ciki da zumudi.
Muna haka yaya Faruku ya shigo harabar gidan.
Kai tsaye ya iso inda muke ya mikawa Sahal hannu suka gaisa. Cikin barkwanci ya ce "Dama na matsu na ganka na ga mai ka taka ne daga zuwanka ka rushe gwamnatina a wajen Bilkisu tashi guda?".
Kunya ta kama shi ya ce "Yayanmu ba rushe ka na yi ba, girma ka ci ka matsa mini kaɗan".
Yaya Faruku ya faɗaɗa murmushinsa ya ce " Tunda kasan ba ƙarfina kafi ba shike nan, na zama surukinka, ka riƙe mini ita amana domin ita ɗin mai haƙuri ce kuma mai nutsuwa ce."
Cikin kunya Sahal ya ce "Da ikon Allah zan rike ta da kyautatawa".
Daga haka ya kalle ni, Ni kuma cikin nauyi na ce "Yaya Faruku barka da yini."
Ya amsa yana faɗin ai na ɗauka kin zama kurma". Ya wuce cikin gida.
Ya numfasa ya ce "Yaya Faruku mutumin kirki ne Bilkisu".
Na ce "Sosai fa"
Muka cigaba da hira cikin shauki domin ban ƙi mu tabbata muna hira cikin wannan yanayin mai dadi da walwala ba.
A wannan dogon hutun mun sake shaƙuwa domin tsallaken kwana ɗaya kacal yake yi. Wani zubin ma kullum ne sai ya zo ko tsoron titi ba ya yi.
Ranar wata Laraba da ba na mantawa da yammaci lis muna hirarmu a inda muka saba zama wato harabar gate dinmu daga gefe, domin mu a gidanmu ba'a yarda da hirar falo. Sai dai a filin Allah ƙarkashin bishiyoyi da furannai.
Ba zato yaya Asad ya bayyana shi kaɗai babu ƴan rakiya daga dukkan alamu a jirgi ya iso Kaduna. Sai kuma ya iso Funtua tunda haka yake yi matukar zai zo ganin gida.
Ya hango ni, ya dunfaromu cikin saurinsa domin shi mutum ne mai hanzari ga shi ƙarfaffa na gaske. Zuciyata ta buga, bansan me ya sanya nake matuƙar nutsuwa idan na ganshi ba, hakanan a duk sadda idanuwana suka hango shi ko da ban ji kalaman bakinsa ba sai zuciyata ta harba da tsananin gaske. Na kan rasa wannan kasafi sai dai na fi tunanin tsoronsa da ya gina a zuciyata tun ina mitsitsiyata. Duk da a yanzu kirki yake yi mini tare da tarairayata fiye da ƴar ɗakinsa sarkin rikici Abida.
Yana isowa na mike tsaye murya a dashe na ce "Baban Bilkisu sannu da zuwa. Ya su Nana da Anti?"
Maimakon ya amsa da baki sai ya cire hularsa tare da ƙamewa ya kuma sara mini tamkar dai yadda ya taɓa yi mana ni da Baba babba shekarun baya.
Daɗi ya ratsa ni har zuciyata domin gaisuwa ce mai ƙololuwar daraja bare kuma ace mai ɗamara ne ya yiwa farar hula irina da ba ni da wani muƙamin komai sai dan girmamawa kawai.
Murmushi ya subuce mini, na ce "Baban Bilkisu na gode da karamcinka".
Ya taya ni murmushi fararen haƙoransa suka haska baƙar fuskarsa.
Ya ce "So nake Bilki ta manta batun duniyar yaya Asad ta yi ta ganinsa a cikin mutanen da suke sonta tare da kambaba dukkan lamarinta."
Na ƙayalkyale da dariya na ce "Ai tunda ka mini takwara na yafe maka, na manta komai na gane na sha gaban Abida. Amma fa ni gaskiya har gobe yaya Faruku ne best"
Ya yi waiwaye ya ce "Idan autar momi ta ji wannan maganar ai kin kunyata ni Maigado".
Na sake yin dariya na ce "Ai gaskiya na furta".
Daidai lokacin Sahla ya gaishe shi cikin nutsuwa domin ya lura ma tamkar bai lura da shi ba, ko kuma mun manta da shi gaba-daya.
Ya amsa gaisuwar babu yabo babu fallasa sai dai ko kadan babu raha ko karramawa. Ya wuce cikin gida ya barmu.
Hirar da bata yiwu ba ke nan. Domin mintina biyar ya ƙara ya mike tare da faɗin "Zan wuce ina son na isa Zaria da wuri. Baba ya ce zan raka shi dubiya bayan maghriba".
Ban kawo komai a raina ba na ce "To"
Muka yi sallama ya tafi a sanyaye.
Na shiga falon Momi na tarar da shi tare da su Baba suna taya shi rarrashin Abida domin tunda ta gaishe shi bata sake kula shi ba, duk yadda take tatsarsa a dalilin bai mata takwara ba, sai ni ya yiwa, bai sa ta huce da shi ba har lokacin.
Na zauna na ce "Wato Allah ya so ni da ba zamu yi kishi ba Abida."
Ta galla mini harara tare da ce wa "Yo ai ke tsare mini gaban da kika yi ko kishiya sai haka. Kowa Bilkisu, kowa Maigado, duk wanda suke jama'atane a da kin kwace mini su a yanzu. Abin kaicon kuma naki mutanen kin riƙe su gam tsabar haɗama."
Gaba-daya aka kwashe da dariya, yayin da ta gintse tata dariyar da take neman ƙwace mata.
Baba ya ce "Abida ƙanwar Bilki kina sanya ni nishadi, idan kuna makaranta sai na ta jina tamkar wanda ya rasa wani abu. Domin kullum kuna ɗebe mini kewa na yi ta tuno da ƙuruciyarku."
Yaya Asad ya ce "Yaran nan kun samu duniya, Allah yasa lahirarku ta zarce hakan."
Wannan karon Abida ce ta yi dariya tare da ce wa "Kai Yaya!
Ya murmusa ya ce "To me zan ce? Gaba-daya kun tattare soyayyar ya'yan fari da ya'yan karshe ku kaɗai. Fatan Allah yasa kuna ibada tuƙuru yadda lahirarku ma zata yi muku daɗi fiye da nan"
Ya nisa ya ce "Wai ina Muni ban ji ɗuriyarta ba".
Baba ya ce "jiya ta je Katsina yayarsu bata jin daɗi shine ta je ta ɗan kula mata da yara kafin tafiyarsu Kano ta taso".
A ladabce ya ce "Allah ya bata lafiya, amma mun yi waya bata faɗa mini bata da lafiya ba".
Baba ya ce "ka manta zurfin cikinta ne? Kasan kuma ce wa zata yi, kana nesa ba zata tayar maka da hankali ba tunda ba kashirban take ba '".
Bamu tashi ba sai da aka fara kiran sallar magarib. Ni da Abida muka yi sashinmu dan bawa baba babba damar ganawa da baban Bilkisu sosai. Tunda ya mini takwara na koma ce kishi hakan a gabansa ko ba'a gabansa ba. Na kuma fahimci yana son sunan domin da karsaahi haɗi da kazangi yake amsawa.
Daren ranar shiru Sahal bai ƙira ni ba, tunda tara da rabi ta yi na shiga tunanin ko lafiya domin da zarar tara ta yi idan muka fara waya muna kaiwa goman dare ko fiye da haka tamkar da akan iska muke magana ba kuɗi ba.
Da goma ta yi sai na kasa haƙuri na buga masa, amma har ta katse bai ɗauka ba, kuma bai katse dan ya biyo baya ba. Ban shiga mamaki ba sai da aka shafe mintina talatin bai bugo ya gabatar da uzzirin baya kusa ko yana tare da iyayensa ba. Gabadaya na daburce, na sake ƙira a karo na uku sai na ji an kashe wayar ma bakiɗaya. Da yake fashin sallah nake yi, sai na takure a kan gado gaba daya na rasa jin daɗin zuciyata. Yayin da tuni Abida ta yi barcinta cikin nutsuwa. Idan akwai abin da yake burge ni da Abida to rashin sanyawa kai damuwar duniya ne. Samsam bata yarda ta yi sabo da abin da zai dame ta. Kusan kullum sai ta ce mini soyayya lalura ce kabiran. Kafin ta yi barci ma da ta lura da yanayina sai da ta ja tsaki ta ce "Ya miki sabo da kalaman da kaso saba'in cikin ɗari na daɗin baki ne ba na gaskiya ba. Da zarar an haɗaku zaman aure hirar mintina goma ma sai an wayi gari ba zai iya ware wa cikin lokacinsa ya yi da ke ba, a yanzu kuma ya yi miki sabo da doguwar hirar da idan baki ji daga gare shi ba zaki kidime ki kasa sukuni. Me za'a yi da soyayya irin taki ne Bilki?"
Da nasan gaskiya ta faɗa sai na kasa amsa mata domin ba ni da bakin yi mata musu ko raddi dan idan ta kaikaice ta fara cashe mini sai ta sanya ni kuka na gaske. Sannan zata juya ta yi kwanciyarta, cikin nutsuwa zan ga tana sauke numfashi tabbacin barci mai cike da nutsuwa take yi.
Da ƙyar na yi barci ina ta saƙesaƙe ko jinya ce ta kwantar da shi tunda a kullum sai ya ce mini ba zai iya barci bai ji muryata ba. Shiyasa ma baya ƙirana sai ya yi sallar Isha domin da zarar mun gama waya barci yake yi muryatace abu na ƙarshe da yake ji a ko wanne dare.
Ina idar da sallar asuba na sake ƙiran layinsa amma shiru kake ji a kashe take.
Na shiga damuwa duk yadda nake son komawa barci ranar ban samu sukunin komawa ba.
Sai da muka karya muka yi sashen Momi hannuna ɗauke da ledar alawa da biskit masu tsada cikin wanda Sahal yake kawo mini na ɗiba na zuba a leda da yawa da mufin na bawa baban Bilkisu ya kaiwa Hafcy. Muka tarar shi kadai yana karyawa kuma ya yi haramar komawa. Muka gaishe shi ya amsa tare da faɗin "Na shiga gaida Mami da Baba ƙarami baku tashi ba".
Abida ce ta amsa da ce wa "ki ce ban tashi ba kawai, amma ita bakam ta yi bata cikin hayyacinta saurayinta ya yi mata fushi tun daren jiya ta rasa walwala da kuzari ".
Ga mamakina sai na ga ya ɓata rai, bacin ran da ya bayyana har a fuskarsa. Da farko tamkar zai share sai kuma ya kasa hadiyewa ya ce "Har haka kika bari ya mamaye ki ne Bilki? Ni ba dan kar na zama babban kwabo ba da sai na ce miki kin fishi ƙarfi da karsashi, gabadaya fa siffar mata gare shi wannan yaron, dan dai kina sonsa ne, autar momi ta yi gaskiya zubin makirai ne da shi, kin kasa ganewa, bansan me yasa ba zaki gane gaskiyar lamari ba, yanzu saboda Allah Maigado menene aibun auren mai mata ne?"
Zuciyata ta harba da tsananin gaske.
Amma saboda yadda Abida ta kasa ta tsare tana kallonmu nasan ba iya kallon kawai take yi ba, har da nazari. Domin kamewa ta yi tana kallonmu cikin tsananin nutsuwa.
Dan haka cikin rawar murya haɗi da kuka na ce "To shine ya tunkare ni da sunan soyayya ban da shi babu wani, sannan mai matar ai bai zo ba, bare ace na jingina masa aibu."
Bansan ya aka yi ba Abida ta yi fit ta ce "Sau dubu nawa zasu zo? Yaya Faruku fa?"
Takaicinta ya shake ni, na rushe da kuka sosai na ce "Da yaushe ya taba tare ni da sunan soyayya ta gaskiya ba ta wasa ba?"
Kafin ta amsa mini Baban Bilkisu ya ce "Kin fita gaskiya. Faruku bai zo da gaske ba, amma akwai wadanda suke son ki da gaske kina tankwabarwa, abokin nan nawa da gaske yake yi, bayan shi akwai wani da zaki amince ya tabbatar mini ko yaushe a shirye yake domin kin yi masa irin sosai ɗin nan".
Abida ta numfasa ta ce "oh Yaya Asad!
Ya yi biris da ita domin sosai ya ɗaure fuska dan haka dole ta kame bakinta ta tsuke.
Ya numfasa ya ce " share hawaye ki ki daina kuka kin ji, ba wacce aka yiwa auren dole a gidan nan, matukar ina raye kema ba za'a yi miki ba, ina miki fatan alheri tsakaninki da yaron".
Daga haka ya mike ya zura hannu a aljihunsa ya ciro ƙudi ya damƙawa Abida ya ce "ke da ita, ku sayi abin da kuke so idan zaku koma makaranta."
A sanyaye ta yi masa godiya. Ni kuwa na kasa yin godiyar.
Ya ce "To mu je ku raka ni mu yi sallama da su Baba."
Na miƙe na zare abin hannuna wanda na stones ne, na sake zaro ribbon din kaina na jefa a ledar alawaer na ce "ga shi ka kaiwa Hafcy, ka faɗa mata I realy miss her silly questions."
Ya murmusa ya ce "Kullum sai ta yi hirarki, kullum sai ta ce "Anty Maigado zata. Ga shi Maigado ba mai fahimta ba ce".
Zuciyar tawa ta sake karaya,.nauyi mai yawa ya kama ni. Na saci kallon Abida na ga itama kallona take da dukkan nutsuwarta.
Haka muka bi bayansa ba tare da mun iya tofawa ba.
Ya yi sallama da kowa, iyayenmu suka bishi da sanya albarka tare da nema masa tsarewar Ubangiji akan dukkan lamarinsa.
Har waje muka bishi ni da Abida.
Bana manta kallon da ya kafe ni da shi, amma bai ce ƙala ba, illah faɗin "ku kula da kanku Allah ya sake haɗamu da alheri."
Abida ta rike hannunsa ta ce"Ka kula da kanka yaya! Su Baba na buƙatarka, matarka da ƴaƴanka na buƙatarka, muma muna sonka, kada ka saka damuwa mai yawa akan lamarin wanda baya bukatarka ko ba shi da asara idan ka haɗu da jinya ".
Ya zuba mata ido irin sosai tare da ruƙo dukkan hannuwanta murya cike da rauni ya ce "Zan kiyaye autar momi! Sai dai bana son ki zama mai son kai, ko tursasawa ga rayuwar wani ta hanyar kyara da ƙaranta mu'amala. Kina da hazaƙa, kina da saurin fahimtar al'amurra. Na roki kada ki yi ƙullaci ko kushe wanda Maigado take so "
Ta amsa da ce wa "To" a takaice.
Jikina ya sake sanyi sosai domin na gaskata sona yake yi. Sai dai tabbas bai yi mini ba, duk yadda yake a tsaye kuma ƙarfaffa. Amma bana son auren zumunci, bana son auren mai mata bana son baƙin namiji.
Ya shiga motar da ta zo daukarsa suka tafi.
Abida ta yi gaba ta bar ni da sanyin jiki. Da ƙyar na ja ƙafafuwana na bi bayanta. Shariyar Abida da rashin samun wayar Sahal suka yi mini rubdugu. Yini guda ina ɗaki sai juyi nake yi na rasa sukuni a jika da zuciyata.
Da na idar da sallar la'asar na dauki wayar na sake ƙiran layinsa a karo na barkatai. Cikin sa'a ta shiga, gaba-daya na ji wani irin salama ta shige ni. Sai dai har ta katse ba'a ɗauka ba. Na sauke ina sake gaskata lallai akwai matsala. Sai dai tunanina bai haƙaito mini menene dalilin faruwar haka ba.
Ina ta kokawa da zuciyata akan kada na sake ƙiransa. Ba zato sautin da na sanya masa na real love by massari ta hau tashi. Kamar zan share amma na kasa sharewar.
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: *Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
11
Deenah cakes and more -Kano
09038055790
IG @Deenah cakes and more
Snacks such as :
Birthday cakes
Cupcakes
Samosa
Springrolls
Meatpie
Frozen snacks
Event snacks
*Lafazi writer's*
Jiki na bari na amsa kiran. Ba wani karkasashi ya ce "Na ga tarin missed call dinki, hidima ta sha kaina ban samu sukunin kiranki back ba".
Na yi sororo da waya a hannuna. Domin a yadda na dauka babu hudimar da zata hana ya nemi ji daga gare ni, mussaman wayar dare da ta zame mana kaida.
Tsawon lokacin ban samu sukunin lalubar kalma ko guda ba.
Ya numfasa ya zarce da ce wa "Bilki so nake ki bani dama na turo a tsayar da maganar aure a tsakaninmu. Don so nake yi, na takaitawa kaina zullumi da fargabar rasa ki".
Gabana ya takarkara ya fadi. Aure kuma? Ban ci karfin karatuna ba, duk yadda nake son Sahal ban hakaito na yi aure a lokacin ba, domin dukkan sisters dinmu ba a aurar da su ba sai da suka kammala digiri. Ga Yaya Munira ma bata yi a aure ba sai ni?"
Da rawar murya na ce "Aure yanzu?'
Ga mamakina sai kawai ya katse wayar gabadaya. Ba tare da ya ce uffan ba.
Na rike wayar ina kallonta tamkar wacce zata fahimtar da ni dalilin sauyin da nake ga ni a tare da Sahal.
Gabadaya na sake rikicewa, na kasa gane mai yake yi mini dadi a duniyata. Kwanakin biyun da suka biyo baya masu tsauri ne domin gabadaya Sahal ya yi watsi da ni. Na kasa tattauna halin da nake cikin da kowa. Abida ce abokiyar hirar, sai dai ban isa na tunkareta da maganarsa ba. To ban fada mata matsalata da shi ba kullum a cikin yi mini habaci da shaguben son da nake yi masa ya zarce wanda yake yi mini take. Bare yanzu da take mini fushi akan ban so brothers dinta ba.
To ina kuma ga na bude baki na tabbtar mata damuwar da nake kwana na yini a cikinta Sahal ne sababinta.
Cikin rashin karsashi nake hada kayana na komawa makaranta tunda a sati mai zuwa hutunmu zai kare.
Kwanaki biyu ke nan da nutsuwa ta yi mini tutsu sosai a dalilin kullum lamarina da Sahal na sake cakalkalewa. Na gama tunanina nasan ban yi masa komai ba. Haka kuma nasan bamu samu sabanin ra'ayi ba.
Haka siddan matsalakan ya dauki zazzafan fushi da ni, dan kawai yasan zuciyata ta shaku da shi, ta kuma kambaba sha'aninsa.
*Lame.Ng Skin
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10 Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15