Beauty and wellness*
*Duk masu son sanin mayukan da azsu dace da skin dinsu to A lame skin Beauty and wellness zaku samu.*
*07036662633*
Ranar talata da daddare bayan Abida ta yi barci. Na lallaba na kira wayarsa domin na kai matukar gajiya wajen takura da yanayin da ya jefamu.
Bugu biyu ya dauka murya babu amo ya yi sallama.
Na amsa sai kuma na yi shiru. Na kasa ce wa kanzil.
Murya a dashen ya ce "Me ya hana ki barci Bili?"
Maimakon na amsa sai na jefa masa tambaya na ce "Ni kam mai yake faruwa ne. Tun zuwan da ka yi last gabadaya ka canja mini, na gama iya nazarina ban hango inda muka samu sabani ko na bata maka ba. Amma ina ta ganin changes masu yawa a tare da kai. Tun ina yi maka uzzirin ko yanayin rayuwa ne har na fahimci kawai dan ka ga na damu da kai ne shiyasa zaka yi amfani da hakan wajen gigita nutsuwata!
Na kammala maganata cikin yanayin damuwa ainun.
Ya numfasa ya kaurara murya ya ce *Bilkisu".*
Na kasa amsawa domin ban saba jin ya kama cikakken sunana ba, yafi ce wa Bilki ko Bily.
Ya zarce da fadin "Gaskiyar maganar ban ji dadin wulakanta ni da yayanku ya yi a gidanku ba!
Gabana ya takarkara ya tsinke. Na kasa hakaito wanne a cikin yayan nawa yake batu a kansa?
Ban kai ga ganowa ba ya ce " Bilki tuni na fahimci mafi yawa y'anuwanki basu sona tare da ke. Na gama tunanina ban samu gamshasshen dalilin da zai sa su washe ni irin haka ba. Amma daga ranar da muka yi ido hudu da Asad Funtua na gane shi suke marawa baya, haka nan muzanta ni da ya yi a gabanki ya tabbatar mini da ce wa sonki yake yi, an kuma shirya yaudarata ne shi ya sanya aka karbi iyayena da hannu bibbiyu."
Raina ya baci sosai. Da rawar murya na ce "Wa ya shirya yaudarar naka ni ko iyayena Sahal?"
Jin na harzuka da yawa sai ya yi maza ya sassauta ya ce "Ai idan muna magana a tsakaninmu iya ni da ke ta shafa, babu maganar iyayenmu a ciki don kuwa ba abokan wasanmu bane. Ke kike mini wasa da hankali. Domin yadda kika manta da ni daga isowar yayanki wajen da muke zaune ya tabbatar mini da cewar kema kina sonsa, kinsan kuwa duk yadda iyayenku zasu so ni ba kamar dansu ba ko?"
Na sauke nannauyar ajiyar zuciya na ce "Ba a mini dole akan lamarinka ba, da yawuna ka turo aka tambayar maka izinin neman aurena, menene zai tayar maka hankali akan Yaya Asad?"
Da azama ya ce "Soyayyarki da na ga ni cikin idanuwansa da gangar jikinsa ce ta dame ni".
A tausashe na ce "Indai ba a nawa idanuwan ka ga soyayyarsa ba, ban ga abin damuwa ba, domin kuwa na riga na zabe ka".
Maimakon ya ji dadin kalamaina ya gasgata ni, ya huce. Sai ya numfasa ya ce "Indai nine zabinki to zan turo a yi maganar aurenmu idan ba haka ba, to kuwa sai dai idan hakan ya zama lisisin korata. Ni ba zan iya jure zullumin da nake ciki akan wannan tafkeken dansandan ba".
Na murmusa na ce "Me yasa ka karaya haka? Me yasa ka rasa jarumtar gwarazan maza?"
Murya babu amo ya ce "saboda Baba babba ne ubansa. Kin sani, na sa ni kuma still baba babban ne mai bada aurenki, idan kuwa haka ne ko ban ce komai kin san ína da hujjoji da zasu karya dukkan confidence dina."
Na numfasa na ce "Dukkan sisters dina da aka aurar sai da suka kammala jamia, ni fa yanzu ne na gama shekarar farko ma, ka yarda kai ne zabina".
Ina rufe baki ya ce " Allah ya bamu alheri! Cikin fishi ya furta hakan, sannan ya katse kiran.
Na daure ban kira shi ba . Kwanaki biyu Muna cikin takaddama. Kan dole na hakura na bi ra'ayinsa na amince mu yi auren tunda shine samun masalaaha a tsakaninmu.
Domin gabadaya ya fittitke akan ko dai mu yi auren ko kuma na ya yi gaba ba zai yarda na cigaba da yaudararsa ba.
Bamu koma makaranta ba sai da ya turo aka yi maganar aure tare da kawo dukkan abubuwan da ake yi ja al'ada. A sanya aure watanni hudu masu zuwa wanda ya yi daidai da kammala zangon farko na aji biyu.
Mahaifana duka biyu basu wani so lamarin ba, domin kowa da dalilin da ya hana shi zumudi.
Baba karami so ya yi ace a cikin yayan Baba babba ne zai aure ni, yayin da mami take kuncin ga Munira nan da kammala digiri ba a yi mata aure ba sai ni dan bakar mugunta irin ta Baba babba.
Ni dai na kame bakina ban ce mata komai ba, amma nasan koma menene nice da alhakin komai tunda sai da baba babban ya tambaye ni, na amince Sannan ya basu damar zuwa da maganar aure.
Ansar na zugata, yayin da Yaya Sulaiman ya ce "Mami huce ki daina damuwa dan ta riga Munira da Abida aure ai ba wani abin bane. Kowa da yadda aka tsara masa rayuwarsa, kawai yi hakuri ki bita da addu'ar dacewa". A lokacin ya zo hutu.
Kan dole ta hakura amma ba dan ta so ba.
Murna da zumudi da Sahal ke cikinsu ba zai yiwu na iya hakaitosu ba. Domin gabadaya ya ninka kulawar da yake yi mini, yayin da ni kuma na takura gabadaya na kasa samun nutsuwa a zuciyata. Haka siddan nake jin tamkar na yiwa kaina garaje. Na rasa da wa zan tattauna, na rasa wa zan tunkara ko na samu na fita daga takura da na samu kaina a ciki.
Ana jibi zamu koma makaranta. Da hantsi na ji ana ta kiciniya a harabar gidanmu. Da yake dakinmu na sashen baba babba muna ganin harabar ta taga. Da yake bana iya barci a dalilin nauyin da zuciyata ta yi mini a kwanakin nan. Ya sanya na sauka daga gadona na isa jikin tagar na yaye labulen kadan dan kada haske ya isa ga fuskar Abida ta tashi ta rufar mini da bala'i. Tunda aka saka ranar aurena ta sake botsare mini fiye da kwanakin baya. Ba gaba take yi da ni ba, a a kawai ta sake kamewa daga shiga dukkan shirgina, yana wahalar gaske ta yi mini magana a karan kanta, amma idan na yi mata zata amsa ko da a takaice ne. Haka nan shekaranjiya bayan an kawo kudin aurena.
Ta kalle ni jikinta a sanayaye ta ce "Ina miki fatan alheri a cikin hukuncin da kika yankewa kanki. Ina miki fatan kada ki yi kuka a hannun Sahalu"
Daga haka ta bude littafin Jiki magayi ta hau bitarsa da haka Har barci ya sure ta.
Na saki ajiyar zuciya mai nauyi ina cigaba da leken yadda ake ta daura tampol tare da shimfida tabarmai . Tsawon lokaci ina tsaye ina kallo tare da cankecanken me za'a yi haka a gidan na hidima bamu sani ba?
Na tabbatar da mutuwa ce ba zan ga ana yin aikin cikin walwala da nutsuwa ba.
Nan da nan aka kammala shimfida aka shiga ajiye kulolin abinci kalakala tare da lemounan kwalba na maltina da su coke.
Na sake shiga mamaki, sai na yi tamkar na tashi Abida sai na fasa domin tashinta a barci bata dauke shi da sauki ba. Yana cikin zunubin da idan aka yi mata sai an biya ta da wani abu, ko ku yi ta buga dabi.
Kafin ka ce kwabo kuma sai shigowa ake yi ana ta zama, na gane wasu da yawa abokan Yaya Faruk ne. Yayin da ban gane wasu da yawa ba.
Ina tsaye ina kallon ikon Allah kawai sai na ga Yaya Faruk ya shigo ya zauna cikin alhini, sai mika masa hannu ake yi ana yi masa jaje tare da fatan Allah yasa hakanne alheri.
Kaina ya sake kullewa, a fili na furta "Menene yake faruwa ne?"
Gabadaya wajen sai hada hada suke suna cin abinci ana ta hira yayin da Yaya Faruk ya tagumi cikin takurarren yanayi.
Can Kuma na ji ya hau fadin "Ba fa hira da nishadi na kiraku mu yi ba. Na gayyatoku ne ku taya ni alhinin rasa sarauniyar shaiba".
Suka dauki hayaniya kowa na fadin "Rashin rabo ya sanya bai fahimci Dingishin kwado da wuri ba.
Ni kuwa gabadaya na ji jiwa na katantawa da ni, kaina ya kulle dakin ya shiga juya mini tamkar an mayar da kasan ya koma sama.
Hawaye ya balle mini. Wani irin abu ya sake tokare mini a kirjina. Hakan ya saka damuwar da nake ciki ta rubanya tsananta. Bansan ya aka yi ba na ware baki na fashe da matsanancin kuka, hawaye da majina suka dinga sintiri a fuskata.
A kidime Abida ta tashi ta zauna a tsakiyar gadonta.
Murya a dashe kuma a firgice ta ce "Me ya faru, mutuwa aka rafkane Bilki? Hayaniya nake ji sosai".
Ta duro a gigice dan taga abin da yake wanzuwa har ya sani kuka sosai.
Bata ga komai ba, illah Yaya Faruk da jamaarsa suna ta cin abinci da alamu walima ake yi duk da shi din bata ganshi da kuzari ba.
Ta saki labulen yayin da ni kuma na yi kasa na zauna dabas a kasan tayal ina cigaba da kokawa ainun.
Ta yi shiru amma gabadaya jikinta ya saki. Ta zauna kusa da ni a tausashe tamkar ba Abida ba ta ce "Na hada ki da darajar ma'aiki ki fada mini me ya sanya ki kuka irin haka? Ta ruko hannuna na dama ta dora a saitin inda zuciyarta take. Wani irin bugu take yi fiye da kima. Ta zuba mini idanuwanta da barci da firgici suka jirgitasu. Na yi kasa da kaina ina gunjin kuka. Ta rike hannuna sosai tabbacin hakuri take ba ni duk da bata furta hakan da baki ba.
Da rawar murya na ce "Yaya Faruk ne Abida! Na furta hakan cikin rushewa da kuka fiye da wanda nake yi.
Ta zabura ta fita ko mayafi bata saka kan doguwar rigar barcinta cotton ba.
Da Yaya Sulaiman ta yi kicibis.
Ya shigo diban ruwan da lemo a fridge din momi.
A matukar razane ta ce "Me yake faruwa ne a gidan nan Yaya Sulaiman? Ina Yaya Faruku?"
Ya amsa da ce wa "Ga shi can ana masa jajjabin an kasa shi a soyayyarsa da Bilki!
Tausayinsa ya tsirgawa Abida ta sani yana son Bilki, ta kuma sani tunda ya gane Yaya Asad shima an jarrabe shi akan sonta shiyasa ya shiriritar da maganar tun kafin su fahimci Yaya Asad na sonta shi ya fahimci hakan.
Gabadaya dukkansu uku tausayinsu take ji, amma a yau na Yaya Faruk yafi tsananta.
Bilki kuwa haushin yadda ta rufe ido ta kasa zaben mutum guda a cikin yayyen nasu ya dakushe tausayinta.
Ta koma ta zauna a bakin gado tana hurar da iskar damuwa. Kamar ba zata yi magana ba, sai kuma ta ce "Bilkisu ki rufe mini baki, tun ban miki sanadin da zaki yi kuka fiye da hakan ba. Wanne irin kasafi ne haka? Menene zaki yi kuka akan Yaya Faruk alhalin ba dole aka yi miki kika zabi waninsa kika bar shi ba.
Ko makaho ya zauna da ke da Faruku sai ya gane yana tsananin sonki, amma kika runtse idanuwanki kika bar shi. Yanzu kuma ki ce zaki yi kuka dan yana bayyanawa duniya alhinin asarar rashinki da ya yi!
A matukar kufule take wannan maganar.
Tashin hankali ya yi mini kawanya. Zullumi da fargaba suka saka na yi zurzuru cikin lokaci kalilan. Na rarrafa na isa gaban gadon da take zaune na durkushe gabanta na ruko dukkan hannuwanta biyu, murya na rawa na ce "Abida ki yi mini adalci, ki ji tausayina ko iya na yau ne a rayuwata.
Na rasa gane me nake ciki, kaina na shirin fashewa, zuciyata na shirin tarwatsewa Wallahi ina jina cikin bala'in da ya yi mini dauri tamkar huhun goro!
Ta sassauta amma bata furta komai ba.
Na ce "Ki yi alkalanci na gaskiya Abida kin sani ina sonki, kin sani da ke nake son na yi sharing damuwata anan duniya dan Allah kada ki rufe mini wannan damar a wannan tsukun da nake ciki na cankacakare"
Ta cigaba da yi mini zuru hakan da na gani na alamta mini hankalinta na kaina tare da abin da zan furta.
Hawaye na zuba na ce "Abida tsakaninki da Allah Yaya Faruk ya taba tsayawa kai da fata akan yana sona, so na gaske?"
Ban jira amsarta ba na ce "Na sani kun fi kusa da shi a kaina, amma ban zaci zaki yi mini irin wannan son kan ba Abida. Ya kike so na yi? So kike na ce wa baba babba Yaya Faruk nake so ya aura masa ni alhalin shi da yake namiji bai yi hakan ba? Bayan matarsa yana da halin ya auro uku ba ni kawai ba amma tsananin tsoronta, ya hana shi kuzari akan sha'anina. Amma ke da kika fahimce ni, irin fahimtar da babu wanda ya yi mini irinta sai kuma ki hau gaba da ni akan lamarin da bani da laifi a cikinsa ko kankani! Akan me zaki rufe mini kofofin tattauna halin da nake ciki Abida? Akan me zaki yi mini irin wannan alkalancin akan lamarina da ya Faruk?"
Na fada ina rushewa da matsanancin kuka domin tsakanina da Allah gabadaya na daburce na kidime ban san ina son yaya Faruk over ba sai a ranar.
Ta sassauta kwarai da gaske ta busar da iskar damuwa ta ce "Yaya Faruk mutum ne mai matukar karamci da sadaukarwa, yana sonki, yana da burin ya aure ki, so yake ki kammala sakandire sai ya bayyana ta yadda ba zaku dade kuna dating ba zaku yi aure. Kwatsam sai aka jarrabi yayansa da sonki, irin son da ya kasa boyuwa a kirjinsa da gangar jikinsa. Hakan da Yaya Faruk ya fahimta ya sanya ya zabi ya bar lamarinki a zuciyarsa gudun kada shaidan ya kawo musu yamutsi! Amma ke gabadaya kin tattara kin rufe kofar da Yaya Asad zai same ki, kin ga ai dole Yaya Faruk ya shimfida tabarmai a yi masa jajen asarar da suka taffka ta biyu babu "
Na kasa cewa komai sai kukan da na cigaba da yinsa ainun.
Murya ba amo Abida ta sake cewa "Dole na ji babu dadi akan sha'aninki mana.
Na yarda Yaya Faruk bai zo ya nuna kansa da gaske ba. Yaya Usman fa? Yaya Asad fa? Wanne irin hannunka mai sandane bai yi miki ba? Har mai suna ya yi miki alhalin bai sanya sunana ba, kinsan kuwa na fiki cancantar ya mini cibina ba dan cikinmu guda ba sai dan tun filazal ni ce tasa ke ta Yaya Faruk ."
Na zuba mata ido hawaye na cigaba da tsere akan fuskata.
Yayin da ta numfasa ta ce "Dan haka ki rufe mini baki da wannan kukan domin dai ke kika yiwa kanki zabin da kike ganin kin gamsu da shi. Ba kuma zai yiwu ki hana zuciyata taya y'anuwana yanuwana bakin cikin asarar rasa ki da suka yi ba, hakanan ba zaki iya cire mini takaicin yadda kika zabi zumuncinmu ya yi rauni ba.
Dan kuwa da wani cikinsu kika aura zan yi mu'amala mai k'arfi da gidanki fiye da ace bare kike aure".
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: https://www.instagram.com/deenah_cakes_and_more?igsh=c2lnZjk5Z3pjYjNw&utm_source=qr
*Deenah cakes and more -Kano*
*09038055790*
*IG @Deenah cakes and more*
*Snacks such as*
*Birthday cakes*
*Cupcakes
*Samosa*
*Springrolls*
Meatpie
*Frozen snacks*
*Event snacks*
*Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
12
Na sake ruko hannunta na ce "Saboda hakan sai na rasa hakkin da nake da shi na zumunci? Shike nan har kawancenmu ma sai ya shiga tasgado Abida? Yanzu ba zaki sake a gidana ba dan ban auri siblings din ki ba? Ashe haka kike da son kai mai yawa ban sani ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Bilkisu kada ki juya mini manufata, kin sani sarai da abin da muke fata ya tabbata a tsakaninki da wani cikinsu, yadda gidanki zai zama dandali a wajena ko ban biki mun tare ba, to kuwa zan mayar da gidan ne wajen zuwana da hutawata domin dukkanku nawa ne sabanin idan ke ce tawa zan dinga yin kaffa kaffa domim ko iyayenmu ma ba zasu yarda na yi ta yi miki jele mai yawa ba."
Da rawar murya na ce "Kira Yaya Faruk na fada masa ina sonsa ya je wajen baba babba sai a mayarwa da Sahal kayansa a dawo da auren kansa".
Ta zuba mini ido ta ce "Ai hakan ba mai yiyuwa ba ne. Ban ji a jikina Yaya Faruk mijinki bane har abada kuwa. Dama Yaya Asad kika ce. Dan kuwa Yana sonki fiye da Yaya Faruk. Nima kuma ina taya shi sonki, ina matukar son a ce ya yi amarya da ke. Da bakinsa ya ce mini da ace ubangiji zai kaddara ki zama matarsa da ya tabbatar dukkan niimomi sun tabbata a gare shi. Idan har zai zauna ya fada mini hakan ni da nake kanwarsa na tabbatar son da yake yi miki mai girma ne."
Na yi kasa da kaina na kasa furta kalma ko guda domin ni kam ban taba jin sonsa ba, asalima haushinsa ne ya sake cushe mini makoshi ta yadda ya zama sanadin da yaya Faruk ya shatawa soyayyata layi. A matukar raunane na ce "Ni dai sai idan Yaya Faruk ne! Na fada zuciyata a kuntace domin har cikin kasan zuciyata nake jin sonsa.
Ta ce "ai maganarki ta yi k'arfin da ba za'a canja da wani ba. Baba babba ne ya karbi komai yanzu kuma sai ya koma ya fadawa iyayen Sahal ya fasa bashi aurenki haka siddan babu dalilinsa na yin haka. Sannan kuma a ji ya daura aurenki da wani cikin yayansa. Anya ko duniya bata yi zundensa ba, mu da kanmu ai dole mu kalubalance shi da zama dattijon kawai".
A matukar raunane na ce "To ki dawo da amincin da yake tsakaninmu Abida. Ki daina share ni.
Showing 30001 words to 33000 words out of 42772 words
*Duk masu son sanin mayukan da azsu dace da skin dinsu to A lame skin Beauty and wellness zaku samu.*
*07036662633*
Ranar talata da daddare bayan Abida ta yi barci. Na lallaba na kira wayarsa domin na kai matukar gajiya wajen takura da yanayin da ya jefamu.
Bugu biyu ya dauka murya babu amo ya yi sallama.
Na amsa sai kuma na yi shiru. Na kasa ce wa kanzil.
Murya a dashen ya ce "Me ya hana ki barci Bili?"
Maimakon na amsa sai na jefa masa tambaya na ce "Ni kam mai yake faruwa ne. Tun zuwan da ka yi last gabadaya ka canja mini, na gama iya nazarina ban hango inda muka samu sabani ko na bata maka ba. Amma ina ta ganin changes masu yawa a tare da kai. Tun ina yi maka uzzirin ko yanayin rayuwa ne har na fahimci kawai dan ka ga na damu da kai ne shiyasa zaka yi amfani da hakan wajen gigita nutsuwata!
Na kammala maganata cikin yanayin damuwa ainun.
Ya numfasa ya kaurara murya ya ce *Bilkisu".*
Na kasa amsawa domin ban saba jin ya kama cikakken sunana ba, yafi ce wa Bilki ko Bily.
Ya zarce da fadin "Gaskiyar maganar ban ji dadin wulakanta ni da yayanku ya yi a gidanku ba!
Gabana ya takarkara ya tsinke. Na kasa hakaito wanne a cikin yayan nawa yake batu a kansa?
Ban kai ga ganowa ba ya ce " Bilki tuni na fahimci mafi yawa y'anuwanki basu sona tare da ke. Na gama tunanina ban samu gamshasshen dalilin da zai sa su washe ni irin haka ba. Amma daga ranar da muka yi ido hudu da Asad Funtua na gane shi suke marawa baya, haka nan muzanta ni da ya yi a gabanki ya tabbatar mini da ce wa sonki yake yi, an kuma shirya yaudarata ne shi ya sanya aka karbi iyayena da hannu bibbiyu."
Raina ya baci sosai. Da rawar murya na ce "Wa ya shirya yaudarar naka ni ko iyayena Sahal?"
Jin na harzuka da yawa sai ya yi maza ya sassauta ya ce "Ai idan muna magana a tsakaninmu iya ni da ke ta shafa, babu maganar iyayenmu a ciki don kuwa ba abokan wasanmu bane. Ke kike mini wasa da hankali. Domin yadda kika manta da ni daga isowar yayanki wajen da muke zaune ya tabbatar mini da cewar kema kina sonsa, kinsan kuwa duk yadda iyayenku zasu so ni ba kamar dansu ba ko?"
Na sauke nannauyar ajiyar zuciya na ce "Ba a mini dole akan lamarinka ba, da yawuna ka turo aka tambayar maka izinin neman aurena, menene zai tayar maka hankali akan Yaya Asad?"
Da azama ya ce "Soyayyarki da na ga ni cikin idanuwansa da gangar jikinsa ce ta dame ni".
A tausashe na ce "Indai ba a nawa idanuwan ka ga soyayyarsa ba, ban ga abin damuwa ba, domin kuwa na riga na zabe ka".
Maimakon ya ji dadin kalamaina ya gasgata ni, ya huce. Sai ya numfasa ya ce "Indai nine zabinki to zan turo a yi maganar aurenmu idan ba haka ba, to kuwa sai dai idan hakan ya zama lisisin korata. Ni ba zan iya jure zullumin da nake ciki akan wannan tafkeken dansandan ba".
Na murmusa na ce "Me yasa ka karaya haka? Me yasa ka rasa jarumtar gwarazan maza?"
Murya babu amo ya ce "saboda Baba babba ne ubansa. Kin sani, na sa ni kuma still baba babban ne mai bada aurenki, idan kuwa haka ne ko ban ce komai kin san ína da hujjoji da zasu karya dukkan confidence dina."
Na numfasa na ce "Dukkan sisters dina da aka aurar sai da suka kammala jamia, ni fa yanzu ne na gama shekarar farko ma, ka yarda kai ne zabina".
Ina rufe baki ya ce " Allah ya bamu alheri! Cikin fishi ya furta hakan, sannan ya katse kiran.
Na daure ban kira shi ba . Kwanaki biyu Muna cikin takaddama. Kan dole na hakura na bi ra'ayinsa na amince mu yi auren tunda shine samun masalaaha a tsakaninmu.
Domin gabadaya ya fittitke akan ko dai mu yi auren ko kuma na ya yi gaba ba zai yarda na cigaba da yaudararsa ba.
Bamu koma makaranta ba sai da ya turo aka yi maganar aure tare da kawo dukkan abubuwan da ake yi ja al'ada. A sanya aure watanni hudu masu zuwa wanda ya yi daidai da kammala zangon farko na aji biyu.
Mahaifana duka biyu basu wani so lamarin ba, domin kowa da dalilin da ya hana shi zumudi.
Baba karami so ya yi ace a cikin yayan Baba babba ne zai aure ni, yayin da mami take kuncin ga Munira nan da kammala digiri ba a yi mata aure ba sai ni dan bakar mugunta irin ta Baba babba.
Ni dai na kame bakina ban ce mata komai ba, amma nasan koma menene nice da alhakin komai tunda sai da baba babban ya tambaye ni, na amince Sannan ya basu damar zuwa da maganar aure.
Ansar na zugata, yayin da Yaya Sulaiman ya ce "Mami huce ki daina damuwa dan ta riga Munira da Abida aure ai ba wani abin bane. Kowa da yadda aka tsara masa rayuwarsa, kawai yi hakuri ki bita da addu'ar dacewa". A lokacin ya zo hutu.
Kan dole ta hakura amma ba dan ta so ba.
Murna da zumudi da Sahal ke cikinsu ba zai yiwu na iya hakaitosu ba. Domin gabadaya ya ninka kulawar da yake yi mini, yayin da ni kuma na takura gabadaya na kasa samun nutsuwa a zuciyata. Haka siddan nake jin tamkar na yiwa kaina garaje. Na rasa da wa zan tattauna, na rasa wa zan tunkara ko na samu na fita daga takura da na samu kaina a ciki.
Ana jibi zamu koma makaranta. Da hantsi na ji ana ta kiciniya a harabar gidanmu. Da yake dakinmu na sashen baba babba muna ganin harabar ta taga. Da yake bana iya barci a dalilin nauyin da zuciyata ta yi mini a kwanakin nan. Ya sanya na sauka daga gadona na isa jikin tagar na yaye labulen kadan dan kada haske ya isa ga fuskar Abida ta tashi ta rufar mini da bala'i. Tunda aka saka ranar aurena ta sake botsare mini fiye da kwanakin baya. Ba gaba take yi da ni ba, a a kawai ta sake kamewa daga shiga dukkan shirgina, yana wahalar gaske ta yi mini magana a karan kanta, amma idan na yi mata zata amsa ko da a takaice ne. Haka nan shekaranjiya bayan an kawo kudin aurena.
Ta kalle ni jikinta a sanayaye ta ce "Ina miki fatan alheri a cikin hukuncin da kika yankewa kanki. Ina miki fatan kada ki yi kuka a hannun Sahalu"
Daga haka ta bude littafin Jiki magayi ta hau bitarsa da haka Har barci ya sure ta.
Na saki ajiyar zuciya mai nauyi ina cigaba da leken yadda ake ta daura tampol tare da shimfida tabarmai . Tsawon lokaci ina tsaye ina kallo tare da cankecanken me za'a yi haka a gidan na hidima bamu sani ba?
Na tabbatar da mutuwa ce ba zan ga ana yin aikin cikin walwala da nutsuwa ba.
Nan da nan aka kammala shimfida aka shiga ajiye kulolin abinci kalakala tare da lemounan kwalba na maltina da su coke.
Na sake shiga mamaki, sai na yi tamkar na tashi Abida sai na fasa domin tashinta a barci bata dauke shi da sauki ba. Yana cikin zunubin da idan aka yi mata sai an biya ta da wani abu, ko ku yi ta buga dabi.
Kafin ka ce kwabo kuma sai shigowa ake yi ana ta zama, na gane wasu da yawa abokan Yaya Faruk ne. Yayin da ban gane wasu da yawa ba.
Ina tsaye ina kallon ikon Allah kawai sai na ga Yaya Faruk ya shigo ya zauna cikin alhini, sai mika masa hannu ake yi ana yi masa jaje tare da fatan Allah yasa hakanne alheri.
Kaina ya sake kullewa, a fili na furta "Menene yake faruwa ne?"
Gabadaya wajen sai hada hada suke suna cin abinci ana ta hira yayin da Yaya Faruk ya tagumi cikin takurarren yanayi.
Can Kuma na ji ya hau fadin "Ba fa hira da nishadi na kiraku mu yi ba. Na gayyatoku ne ku taya ni alhinin rasa sarauniyar shaiba".
Suka dauki hayaniya kowa na fadin "Rashin rabo ya sanya bai fahimci Dingishin kwado da wuri ba.
Ni kuwa gabadaya na ji jiwa na katantawa da ni, kaina ya kulle dakin ya shiga juya mini tamkar an mayar da kasan ya koma sama.
Hawaye ya balle mini. Wani irin abu ya sake tokare mini a kirjina. Hakan ya saka damuwar da nake ciki ta rubanya tsananta. Bansan ya aka yi ba na ware baki na fashe da matsanancin kuka, hawaye da majina suka dinga sintiri a fuskata.
A kidime Abida ta tashi ta zauna a tsakiyar gadonta.
Murya a dashe kuma a firgice ta ce "Me ya faru, mutuwa aka rafkane Bilki? Hayaniya nake ji sosai".
Ta duro a gigice dan taga abin da yake wanzuwa har ya sani kuka sosai.
Bata ga komai ba, illah Yaya Faruk da jamaarsa suna ta cin abinci da alamu walima ake yi duk da shi din bata ganshi da kuzari ba.
Ta saki labulen yayin da ni kuma na yi kasa na zauna dabas a kasan tayal ina cigaba da kokawa ainun.
Ta yi shiru amma gabadaya jikinta ya saki. Ta zauna kusa da ni a tausashe tamkar ba Abida ba ta ce "Na hada ki da darajar ma'aiki ki fada mini me ya sanya ki kuka irin haka? Ta ruko hannuna na dama ta dora a saitin inda zuciyarta take. Wani irin bugu take yi fiye da kima. Ta zuba mini idanuwanta da barci da firgici suka jirgitasu. Na yi kasa da kaina ina gunjin kuka. Ta rike hannuna sosai tabbacin hakuri take ba ni duk da bata furta hakan da baki ba.
Da rawar murya na ce "Yaya Faruk ne Abida! Na furta hakan cikin rushewa da kuka fiye da wanda nake yi.
Ta zabura ta fita ko mayafi bata saka kan doguwar rigar barcinta cotton ba.
Da Yaya Sulaiman ta yi kicibis.
Ya shigo diban ruwan da lemo a fridge din momi.
A matukar razane ta ce "Me yake faruwa ne a gidan nan Yaya Sulaiman? Ina Yaya Faruku?"
Ya amsa da ce wa "Ga shi can ana masa jajjabin an kasa shi a soyayyarsa da Bilki!
Tausayinsa ya tsirgawa Abida ta sani yana son Bilki, ta kuma sani tunda ya gane Yaya Asad shima an jarrabe shi akan sonta shiyasa ya shiriritar da maganar tun kafin su fahimci Yaya Asad na sonta shi ya fahimci hakan.
Gabadaya dukkansu uku tausayinsu take ji, amma a yau na Yaya Faruk yafi tsananta.
Bilki kuwa haushin yadda ta rufe ido ta kasa zaben mutum guda a cikin yayyen nasu ya dakushe tausayinta.
Ta koma ta zauna a bakin gado tana hurar da iskar damuwa. Kamar ba zata yi magana ba, sai kuma ta ce "Bilkisu ki rufe mini baki, tun ban miki sanadin da zaki yi kuka fiye da hakan ba. Wanne irin kasafi ne haka? Menene zaki yi kuka akan Yaya Faruk alhalin ba dole aka yi miki kika zabi waninsa kika bar shi ba.
Ko makaho ya zauna da ke da Faruku sai ya gane yana tsananin sonki, amma kika runtse idanuwanki kika bar shi. Yanzu kuma ki ce zaki yi kuka dan yana bayyanawa duniya alhinin asarar rashinki da ya yi!
A matukar kufule take wannan maganar.
Tashin hankali ya yi mini kawanya. Zullumi da fargaba suka saka na yi zurzuru cikin lokaci kalilan. Na rarrafa na isa gaban gadon da take zaune na durkushe gabanta na ruko dukkan hannuwanta biyu, murya na rawa na ce "Abida ki yi mini adalci, ki ji tausayina ko iya na yau ne a rayuwata.
Na rasa gane me nake ciki, kaina na shirin fashewa, zuciyata na shirin tarwatsewa Wallahi ina jina cikin bala'in da ya yi mini dauri tamkar huhun goro!
Ta sassauta amma bata furta komai ba.
Na ce "Ki yi alkalanci na gaskiya Abida kin sani ina sonki, kin sani da ke nake son na yi sharing damuwata anan duniya dan Allah kada ki rufe mini wannan damar a wannan tsukun da nake ciki na cankacakare"
Ta cigaba da yi mini zuru hakan da na gani na alamta mini hankalinta na kaina tare da abin da zan furta.
Hawaye na zuba na ce "Abida tsakaninki da Allah Yaya Faruk ya taba tsayawa kai da fata akan yana sona, so na gaske?"
Ban jira amsarta ba na ce "Na sani kun fi kusa da shi a kaina, amma ban zaci zaki yi mini irin wannan son kan ba Abida. Ya kike so na yi? So kike na ce wa baba babba Yaya Faruk nake so ya aura masa ni alhalin shi da yake namiji bai yi hakan ba? Bayan matarsa yana da halin ya auro uku ba ni kawai ba amma tsananin tsoronta, ya hana shi kuzari akan sha'anina. Amma ke da kika fahimce ni, irin fahimtar da babu wanda ya yi mini irinta sai kuma ki hau gaba da ni akan lamarin da bani da laifi a cikinsa ko kankani! Akan me zaki rufe mini kofofin tattauna halin da nake ciki Abida? Akan me zaki yi mini irin wannan alkalancin akan lamarina da ya Faruk?"
Na fada ina rushewa da matsanancin kuka domin tsakanina da Allah gabadaya na daburce na kidime ban san ina son yaya Faruk over ba sai a ranar.
Ta sassauta kwarai da gaske ta busar da iskar damuwa ta ce "Yaya Faruk mutum ne mai matukar karamci da sadaukarwa, yana sonki, yana da burin ya aure ki, so yake ki kammala sakandire sai ya bayyana ta yadda ba zaku dade kuna dating ba zaku yi aure. Kwatsam sai aka jarrabi yayansa da sonki, irin son da ya kasa boyuwa a kirjinsa da gangar jikinsa. Hakan da Yaya Faruk ya fahimta ya sanya ya zabi ya bar lamarinki a zuciyarsa gudun kada shaidan ya kawo musu yamutsi! Amma ke gabadaya kin tattara kin rufe kofar da Yaya Asad zai same ki, kin ga ai dole Yaya Faruk ya shimfida tabarmai a yi masa jajen asarar da suka taffka ta biyu babu "
Na kasa cewa komai sai kukan da na cigaba da yinsa ainun.
Murya ba amo Abida ta sake cewa "Dole na ji babu dadi akan sha'aninki mana.
Na yarda Yaya Faruk bai zo ya nuna kansa da gaske ba. Yaya Usman fa? Yaya Asad fa? Wanne irin hannunka mai sandane bai yi miki ba? Har mai suna ya yi miki alhalin bai sanya sunana ba, kinsan kuwa na fiki cancantar ya mini cibina ba dan cikinmu guda ba sai dan tun filazal ni ce tasa ke ta Yaya Faruk ."
Na zuba mata ido hawaye na cigaba da tsere akan fuskata.
Yayin da ta numfasa ta ce "Dan haka ki rufe mini baki da wannan kukan domin dai ke kika yiwa kanki zabin da kike ganin kin gamsu da shi. Ba kuma zai yiwu ki hana zuciyata taya y'anuwana yanuwana bakin cikin asarar rasa ki da suka yi ba, hakanan ba zaki iya cire mini takaicin yadda kika zabi zumuncinmu ya yi rauni ba.
Dan kuwa da wani cikinsu kika aura zan yi mu'amala mai k'arfi da gidanki fiye da ace bare kike aure".
[8/24, 12:53 PM] Surayya Dee: https://www.instagram.com/deenah_cakes_and_more?igsh=c2lnZjk5Z3pjYjNw&utm_source=qr
*Deenah cakes and more -Kano*
*09038055790*
*IG @Deenah cakes and more*
*Snacks such as*
*Birthday cakes*
*Cupcakes
*Samosa*
*Springrolls*
Meatpie
*Frozen snacks*
*Event snacks*
*Wannan littafin na kudine pay* *1k via 2384876855*
*Surayya Ibrahim Zenith Bank.*
*A tura shaidar biya ta wadannan lambobin*
# 08032773332#
# 09069067488#
*Littafi na d'aya zai zo kyauta a WhatsAp yayin da na biyu da na uku zai zo a Telegram da arewa ga wadanda suka biya kudin karatu*.
*DINGISHIN KWADO*
*BY*
*SURAYYA DEE*
*MARUBUCIYAR*
*HALIN YAU*
*SABO DA KAZA*
*BAK'AR TA'ADA*
12
Na sake ruko hannunta na ce "Saboda hakan sai na rasa hakkin da nake da shi na zumunci? Shike nan har kawancenmu ma sai ya shiga tasgado Abida? Yanzu ba zaki sake a gidana ba dan ban auri siblings din ki ba? Ashe haka kike da son kai mai yawa ban sani ba?"
Ta girgiza kai ta ce "Bilkisu kada ki juya mini manufata, kin sani sarai da abin da muke fata ya tabbata a tsakaninki da wani cikinsu, yadda gidanki zai zama dandali a wajena ko ban biki mun tare ba, to kuwa zan mayar da gidan ne wajen zuwana da hutawata domin dukkanku nawa ne sabanin idan ke ce tawa zan dinga yin kaffa kaffa domim ko iyayenmu ma ba zasu yarda na yi ta yi miki jele mai yawa ba."
Da rawar murya na ce "Kira Yaya Faruk na fada masa ina sonsa ya je wajen baba babba sai a mayarwa da Sahal kayansa a dawo da auren kansa".
Ta zuba mini ido ta ce "Ai hakan ba mai yiyuwa ba ne. Ban ji a jikina Yaya Faruk mijinki bane har abada kuwa. Dama Yaya Asad kika ce. Dan kuwa Yana sonki fiye da Yaya Faruk. Nima kuma ina taya shi sonki, ina matukar son a ce ya yi amarya da ke. Da bakinsa ya ce mini da ace ubangiji zai kaddara ki zama matarsa da ya tabbatar dukkan niimomi sun tabbata a gare shi. Idan har zai zauna ya fada mini hakan ni da nake kanwarsa na tabbatar son da yake yi miki mai girma ne."
Na yi kasa da kaina na kasa furta kalma ko guda domin ni kam ban taba jin sonsa ba, asalima haushinsa ne ya sake cushe mini makoshi ta yadda ya zama sanadin da yaya Faruk ya shatawa soyayyata layi. A matukar raunane na ce "Ni dai sai idan Yaya Faruk ne! Na fada zuciyata a kuntace domin har cikin kasan zuciyata nake jin sonsa.
Ta ce "ai maganarki ta yi k'arfin da ba za'a canja da wani ba. Baba babba ne ya karbi komai yanzu kuma sai ya koma ya fadawa iyayen Sahal ya fasa bashi aurenki haka siddan babu dalilinsa na yin haka. Sannan kuma a ji ya daura aurenki da wani cikin yayansa. Anya ko duniya bata yi zundensa ba, mu da kanmu ai dole mu kalubalance shi da zama dattijon kawai".
A matukar raunane na ce "To ki dawo da amincin da yake tsakaninmu Abida. Ki daina share ni.
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11 Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15