________________________📖 Shiru na ƴan wasu sakanni kafin ya motsa bakin sa
"Na so ki tare yau sedai baze yiwu ba tunda munyi dare but be ready gobe da safe insha Allah zan zo mu wuce".
Tsrewa, yau, gobe da safe, wucewa, gaba ɗaya bata gane ma'anar wannan kalaman ba.
It may sound funny ko kuma a ɗauka rainin hankali ne but dagaske a wannan lokacin manta ma'anar su tayi, sam bata gane me yake nufi ba haka yasa tayi saurin yin magana
"Wucewa, gobe, zuwa ina?".
Seda ya kalle ta sosai kafin ya kau da kai trying not to look at her face again, tun lokacin da ya ga ƙwayar idon ta a ƙauyen su yaji yana sha'awar sake gani, so yake ya tantance wane kala ne da eyeballs ɗin ta tunda ya tabbatar ba baƙa bace sedai baya san ta ɗau hakan da wata manufa shiyasa yake kauda Kai
"Nace ki tattara abubuwan da kuke buƙata na iya suttura zaki koma gidan auren ki gobe insha Allah".
Zuwa yanzu kam she's speechless dan ba zata ce bata gane me kuma yake nufi ba yanzu tunda gwari gwari yayi mata, ita kam ta rasa a wane layi zata ajiye wannan auren nata, da neman auren da ɗaurawa duk cikin kwana ɗaya zuwa biyu aka yi su, yanzu kuna ga tariya, a al'adar malam bahaushe dangin amarya kan haɗu su rakata gidan auren ta cikin soyayya da ƙauna amma ita gata ana batun tariyar daga ita se mijin ta da ƴaƴan ta, lallai auren ta wani iko ne na Ubangiji.
A hankali ta saci kallon sa cikin son furta abinda take so sedai bata san ya akayi ta tsinci harshen ta da furta abinda ba shi ne a zuciyar ta ba
"Allah yasa zamu ga goben da rai da lafiya".
Ameen ya faɗa daga nan kuma suka cigaba da zaman shiru, ita bata ce komai ba shi ma haka, tsayin lokaci har ta gaji da zaman ta gyara amma bashi da niyyar cewa komai
"Ki taso yaran mu tafi".
"Mu tafi, ina kenan bayan dare kuma yayi, its almost ten fa".
"And me kike nufi da zaman da kike yi a nan?".
Wani irin tuƙuƙin takaici ne ya cika mata maƙogaro, daga ɗazu zuwa yanzu ta fahimci mutumin nan wani bahago ne na daban, ko saboda ba wani kusanci ne tsakanin su na daban ba a office maybe shiyasa bata San hakan ba tuntuni.
Bata ce komai ba ta fita daga motar tare da maida murfin ta rufe masa ta wucewar ta cikin gida tana gunguni ita kaɗai.
Seda ya ga shigar ta gidan sannan ya tashi motar ya fita daga layin cike da sanyin jikin da gajiya ta haifar masa, wannan dogon tuƙin da yayi jiya da yau sam be saba masa ba shiyasa gaba ɗaya jikin sa yayi masa nauyi.
Kulle motar yayi ya fita batare da ya kula ganin ta da yayi tsaye ba, da sauri tabi bayan sa har tana haɗawa da gudu saboda takunsa irin na cikakkun maza ne masu isasshiyar lafiya
"Yaya Abdu, ya Abdu".
Yana jin ya tsaf amma yayi mata banza hakan yasa ta kuma kwasa da gudu tasha gaban sa lamarin da ya tilasta masa tsayuwar dole sedai tuni ya sake ɗin ke fuska tsaf kamar wanda be taɓa sanin wani abu wai shi annurin dariya ko murmushi ba a duniya.
"Dama Anna ce ke neman ka, tuntuni nake kiran wayar ka in faɗa maka yaƙi shiga, gashi ita kuma se kuka take da kiran sunan yaya nafi wuni guda yau taƙi cin komai".
"Kije ki faɗawa baba".
"Zuwa yanzu ya kwanta yaya Abdu, Please ka taimaka kazo muje kayi mata magana ko zata ji, na bata baki amma taki saurara ta".
Sam baya son kallon ta sabida irin shigar dake jikin ta, duk da kasancewar dare ne amma gidan nasu tarwai yake da haske da ko allura ce ta faɗi tsaf mutum ze tsugunna ya ɗau abar sa ya tashi.
Tun ba yau ba yasan ita da yayar ta nafisa Allah ya ji ƙan rai kamar gabas da yamma ne, sam bata inda suka yi kamanceceniya se ko ta fuska da kuma jini shiyasa ko da sam be sake mata fuska balle ta samu damar kawo masa raini bare kuma yanzu da yake jin kowa ma daidai yake dashi.
"Kije zan zo in nayi wanka, nayi gumi da yawa I can't go to her a haka".
Ya faɗa yana wuce ta cikin tafiyar nan tasa me cike da karfi da isa, bin bayan sa tayi da kallo cike da maɗaukakin shauƙi, lumshe ido tayi tare da rungume hannuwan a ƙirji inda take ji kamar shine ta rungume, wannan maganar da ya mata ji take kamar an mata albishir da shiga aljanna.
Tun yayar ta na da rai take so da ƙaunar yaya Abdu sedai tayi ta ƙoƙarin dannewa, yanzu kuwa da babu yayar ta bata tunanin akwai abinda ze tsayar da ita kuma.
A saɗaɗe ta juya zuwa part ɗin su, bakin ƙofa ta tarar da anna tsaye, da sauri ta riƙo hannun ta suka ƙara sa ciki kafin ta dube ta
"Yaya, cewa yai baze zo ba?".
"Yace zezo amma se yayi wanka, dawowar sa kenan baze iya zuwa gare ki a haka ba".
"Kai masha Allah bari maza in shafa rob ɗin nan a ido na ɗan suyi ja su dinga hawaye, insha Allah buƙatar mu zata biya bari ki gani".
Tsohuwa Anna ta faɗa tana murza Rob a fuskar ta, duk yadda idanun ta ke hawaye be sa ta fasa ba se da ta saka sosai ta yadda in ka kalle ta zaka ce ta daɗe tana kuka dan yadda fuskar ta tayi jajir kasancewar ta fara haka ma idanun ta suka yi ja suka tasa.
A can ɓangaren Hajiya Babba kuwa da sauri shuraiha dake tsaye jikin window riƙe da curtains tana kallon abinda ke faruwa tsakanin Abu Aulad da Nuriyya ta saki uban ashariya
"Kan uba".
Ta faɗa da sauri tana sakin curtains ɗin, bata tsaya wata wata ba ta zura bedroom slippers ɗin ta tayi waje without minding cewa kayan bacci ne a jikin ta ba, burin ta a lokacin shine ta kai gare su taji me suke tattaunawa a wannan tsohon daren.
Baza tayi sanyar da wata can daban zata ƙwace mata Abdallah ba bayan an gama kwaɗaita mata shi tare da lasa mata zuma a baki yanzu kuma a ce za'a janye, ina ba zata yarda ba.
Sedai kash ko kafin ta kai ga fita daga part ɗin su tuni ya shige nasa part ɗin ita kuma Nuriyya ta koma nasu hakan yasa ko da ta fito compound ɗin bata tadda kowa ba se ma'aikata dake ɗan kai kawo dan wasun su ma tuni sun nemi makwanci.
Haka ta koma part ɗin nasu tana cizon yatsa, taso taji me waccan karuwar ke faɗa masa wanda har ya tsaya saurara haka sedai kash bata samu ji ba, ya zama dole ta tunzura Hajiya Babba ayi ayi ai bikin su ko hankalin ta ya kwanta, daga lokacin da ta sami wannan damar a lokacin ita kanta Hajiya babbar zata raina kanta dan kallon ta kawai take itama da tata tsarin da buƙatar akan Abdallah ɗin.
A hankali yake rage kayan jikin sa cike da gajiya, wanka yake buƙata yake kusan sanyi dan yadda yake jin jikin sa na ƙaiƙayi shine kawai abinda se yi yaji sauƙi.
Singlet ɗin jikin sa yake ƙoƙarin cirewa se kuma ya fasa sanadin hango inuwa da yayi jikin labulen sa alamun akwai wani laɓe a ta wajen.
Cikin nutsuwa ya shiga takawa har ya kai wajen yasa hannu ya yaye curtains ɗin da suka rufe tagar, tsaye take cikin shaiɗanun kayan da dasu da babu a jikin ta basu da wani banbanci, suna haɗa ido ta sake masa wani arnen murmushi cike da barikanci kafin cikin kwarkwasa ta shiga lauya jikin ta tana magana da wata seducive voice
"Sannu da zuwa Abu Aulad, ga dukkan alamu ka gaji, don't mind I can takeaway all your stresses, yanzu dai muje kayi wanka ko super man?".
Kamarw anda garwashin wuta ya taɓa haka yayi watsi da hannun da takai jikin sa, ya rabbal alameen be san ya zai yi da rayuwar sa a cikin wannan gidan da a wajen sa gara kabari dashi ba.
Wani irin birkitaccen mafi ya watsa mata da yasa ta yin katantanwa ta faɗi can gefe kanta ya bugu da jikin Centre table ɗin dake falon, cikin wata irin zuciya da ta ciwo shi ya bita yasa ƙafa ta taka sangalalin hannun ta har se da yayi ƙarar dake shaida alamar in har bata sami fracture ba to tabbas ƙashin nan ya fita daga bigiren sa.
Wani wahalallen ihu ta saki da be wani fita da karfi ba saboda tsabar wahala yasa a take Muryar ta ya shaƙe, cikin wani dakusasshen Muryar da ɓacin rai ya haifar masa ya shiga yi mata concrete warning
"This is the first and last time da zan kuma ganin ki a part ɗina, na rantse da Ubangijin da ya busa min rai da second time na kuma ganin ki zan iya ɗaukar ranki dan ko banza an rage mugun iri, annoba kuma jinin shaiɗan, before the count of three ki fice min ɗaga ɗaki in ba haka ba wallahi rataye kibzan yi jikin fanka, fitsararriyar fasiƙa kawai mara kunya da tsoron Allah".
Ai ko kafin ya gama bayanin sa tuni ta tarkata hannun ta tayi waje da mugun sauri dan a yadda ta gan shi da kuma rashin imanin da ya gwada mata ta tabbatar ze iya rataye tan kamar yadda ya faɗa.
Da numfarfashi da komai takai kanta part ɗin ta zube kan kujera tana maida numfashi, wani irin zufa ne ke keto mata na wahala da azabar da take sha a jikin ta, bata taɓa sanin haka zafin karaya yake ba se yau.
Ƙwalla take zubar wa tana bin hannun da kallo yayinda cikin ranta take shan mugayen alwashi kala kala a kan shi, tun da ta riga ta ɗora ido a kan shi takuma kwaɗaitu da shi ta rantse ita kuma se ta same shi, in kuwa ba haka ba to tabbas sedai ayi biyu babu uku ba ko ɗaya ma'ana indai ba zata same shi b ato sedai kowace mace ta rasa.
Da sauri ta runtse idon ta lokacin da ta auno shi a idanun ta tare da wata mace, inaaa, ba'a haifi macen da zata amfane shi ba, ada dai tayi wannan imanin amma a yanzu zata iya yin komai in tace komai tana nufin komai wajen ganin ta saka kyakkyawar barrier tsakanin sa da duk wata ƴa mace kowace ita kuwa.
Ranar haka ta kwanan cikin azaba da raɗaɗin zuci da na jiki, ga dai jinya ya kwantar da ita kuma wai batare da ya bari ta amfanu da komai daga gare shi ba, ita da ta samu abinda taje nema to da sauki ba karya ta ba ko kashe ta yayi ba zata damu ba tunda ta cika burin ta.
A ɓangaren Abu Aulad ma haka ya kwana a zaune cikin wani irin yanayin da baze fassaru ba, be san da wane suna ze Kira gidan da yake ciki ba haka be san da wane suna ze kirayi mutanen cikin sa ba, be taɓa sanin bawa kan zaɓi mutuwa kan rayuwar sa ba se a kan shi, da ace kisan kai ba haram bane a musulunci da tuni ya daɗe da sheƙe kan sa ya huta.
Tun tasowar sa be san wani abu wai shi farin ciki ba, kullum cikin baƙin ciki da damuwa yake tun fara wayo sa har kawo yanzu da yake shekarun sa na cikakken namiji mai ji da sabon jini da ƙuruciya.
Rayuwar sa a hagunce ta faro kuma har kawo yanzu a haka take, be san se yaushe ne ze samu daidaito na rai, ruhi da rayuwa ba balle har ya samu salama, a duk sanda yaga mutane na rayuwa suna dariya da nishaɗi ya kan tsinci kansa da ayyana dama shine, so da yawa yasha kusan yin saɓo in ya zauna tunani dan ya kan dinga aiyana me yayi wa Allah da yasa ƙaddarar jarabawar tazo a haka, me yasa ba wata daban ba.
Kiran sallar asuba da ake yi ne yasa shi miƙewa yana dafe kan sa dake sara masa ya shiga toilet, daga tsayen da yake ya sakarwa kansa ruwa masu sanyi sanye da wandon shaddar da singlet ɗin batare da ya cire ba, tsayin lokaci Sannan ya gabatar da wanka ya ɗaura alwala ya fito.
Jallabiya ya zura a jikin sa tare da ɗaukar tasbah ɗin sa ya wuce masallaci, seda aka idar da sallah har gari yayi haske kafin ya taho gida.
Jiri yake gani dan rabon shi da abinci tun na safen jiya kafin su tafi ƙauye ga kuma rashin bacci sedai kasancewar tsayayyen namiji ba wanda ze fahimci hakan se wanda yayi masa sani na sosai.
Wata jallabiyar ya canja kawai ya ɗau key ɗin motar sa zuwa gidan su, ɗauko ta ze yi dan se yayi hakan hankalin sa ne kwnata, mutanen gidan su are so cunning, gwara tun kafin su farga yayi outsmarting ɗin su ya shayar dasu mamaki ya kuma basu tsoro ba kuma ta kowace hanya ba se ta kawo macen da ya nema wa kan sa auren ta cikin gidan.
Ya sani in da mace a tare dashi abubuwa da yawa zasu masa sauƙi sedai matsalar shine shin itama irin su ce, wane assurance yake dashi na ba zata zama kamar su ba, shin in aka mata tayi da zunzurutun kudi ko matsayi zata karɓa ko kuwa?!.
Wannan sune tarin abubuwan da tuntuni suke hana shi aure sedai a yanzu da yayi ba wai ze saki jiki da ita bane, hasalima auren su na da wa'adin da ya ɗibar masa wanda yana cika ze sauta, zaman sa shi kaɗai ya fiye masa dan be yarda da kowa ba baya kuma jin ze yarda ɗin.
Yaro ya samu ya aika gidan, tana cikin sawa Ifty rigar school ta jiyo Muryar yaron na faɗin aiken da aka turo shi
"Wai salma ta fito inji Abdallah".
Sedai rigar ta kubce ta faɗi daga hannun ta saboda yadda zuciyar ta ta doka da jin sunan sa, hannun ta na rawa ta sake ɗaukar rigar ta shiga kici kicin sa mata sedai ta kasa saboda ruɗewar da tayi, Hajiya ce ta amsawa yaron da gata nan fitowa saboda jiya ta zauna tayi mata bayanin komai dan kamar mahaifiyar haka ta ɗauki Hajiya saboda ba ƙaramin taimako tayi mata ba a rayuwar ta.
Ɗakin Hajiya ta shigo ta karɓi shirya Ifty dan tuni ta gana da Ibty
"Je ki bashi uzuri daga nan ki nemo yara su fara fitar miki da jakunkunan, in an kwana biyu insha Allah zan zo in ga mazaunin ki, tashi kije".
Jiki ba laka ta fita, zaune cikin motar ta same shi ƙafar sa duka biyu a waje ya lumshe idanun sa tare da jingina kan sa da makarin kujerar, seda ta tattaro duk dauriyar dake gare ta kafin ta iya gaida shi
"Barkada safiya".
Saukar Muryar ta yasa ya buɗe idon sa, kallo ɗaya yayi mata ya kau da kai tare da maida ƙafafun sa cikin motar ya fara ƙoƙarin kunna ta
"Kayi haƙuri Ban ƙara sa shirya Ifty ba amma yanzun nan zamu ƙarasa, Bari in Sami yaro ya fitar min da jakunkunan".
Fasa kunna motar yayi ya koma ya kwanta kamar ɗazu ita kuma ta matsa ta sami wani almajiri suka koma ciki tare, ko da ta shiga tuni Hajiya ta gama shirya Ifty tare da haɗa musu launch box ɗin su, manyan jakunkunan kayan su dake shaƙe ta fara jawowa tana fitarwa tsakar gida almajirin na fita dasu har suka gama, kallon ɗakin take cike da matsanancin kewar sa da zata yi kafin kuma ta maida kallon ta kan Hajiya, matar da tayi mata halaccin da har abada ba zata manta ba, a rayuwa da ita da bana Husaila sun mata abinda in har ta manta to ita ɗin butulu ce cikakiya.
Nasiha sosai Hajiya ta yi mata da har tasa ta kuka ba dan komai ba se dan kewar mahaifiyar ta da kakarta da ta taso mata, ta sani da suna nan su zasu yi mata wannan nasihar.
Haka Hajiya ta rakata har mota, ko da suka je tuni ya zuba jakunkunan a booth ɗin motar sa ita kawai yake jira.
Duk yadda yake moody be san lokacin da ya saki fuska ba da Ifty ta ƙarasa tana ɗane shi Ibty kuma na gaida shi, haka ya ɗauke su duk biyu ya riƙe yana kallon su cike da shauƙi yana sauraren shirmensu har Hajiya ta gama mata nasihar da zata yi suka idasa bakin motar, har ƙasa ya tsugunna ya gaida Hajiya abinda yayi salma matuƙar daɗi a rai.
Hala suka ɗau hanya zuwa gidan da bata sani ba tana cike da kewar rabuwa da Hajiya da ragowar ƴan uwan zaman hayar ta da basu san da maganar auren ba ma se yau da safe amma duk da haka suka bita da fatan alkhairi.
Har bakin ƙofar party ɗin mahaifin sa ya kai motar sannan ya fita ya zagaya ya buɗe mata itama ta fito a ɗarare sannan ya buɗe wa su Ibty baya suka fito, hannu yasa ya ɗau Ifty yayinda ya riƙewa Ibty hannu ya nufi falon mahaifin nasa ta rufa masa baya itama.
Gana ɗaya mutanen ɗakin suka zuba musu ido zuciyoyin marasa gaskiya na dukan uku uku, masu gaskiya kuma na musu kallon rashin fahimta.
"Barka da safiya baba, ga salma matata da ƴaƴan ta kuma nawa".
A zabure mutane shida dake falon suka miƙe tsaye kowanne da kalar tambayar da yake jefowa
"What?, Me?, Kutumar uba?, Mata?, How comes?, Haba da Allah!.
Wannan sune ruwan tambayoyin da suka dinga yawo a falon cikin ihun muryoyi daban daban yayinda Abu Aulad ya saki hannun Ibty ya saka hannun ya jawo salma cikin jikin sa ya rungume.........................✍🏻.
Tooooooooh jama'a, gamu a ƙarshen free page da izinin Ubangiji, ko yaya paid pages zasu kasance?!.
Shin wacece Abu Aulad ya karyawa hannu jiya da dare?!
Wacece shuraiha?, Wai ma tsaya ita kanta Hajiya babbar wacece, meye alaƙarta da Abu Aulad?!
Jarumi, jarumi!, Shin kun Tuna shi?! Wanne shi?.
Nuriyya ƙanwar nafisa ƴa a wajen Anna, ko meye ƙudurin ta kan Abu Aulad?!.
Yace be yarda da kowa ba se kan shi kaɗai, what about Haisam?!.
Haisam, Haisam, anya shima babu wani ƙulli kuwa a under
Showing 24001 words to 27000 words out of 27225 words
________________________📖 Shiru na ƴan wasu sakanni kafin ya motsa bakin sa
"Na so ki tare yau sedai baze yiwu ba tunda munyi dare but be ready gobe da safe insha Allah zan zo mu wuce".
Tsrewa, yau, gobe da safe, wucewa, gaba ɗaya bata gane ma'anar wannan kalaman ba.
It may sound funny ko kuma a ɗauka rainin hankali ne but dagaske a wannan lokacin manta ma'anar su tayi, sam bata gane me yake nufi ba haka yasa tayi saurin yin magana
"Wucewa, gobe, zuwa ina?".
Seda ya kalle ta sosai kafin ya kau da kai trying not to look at her face again, tun lokacin da ya ga ƙwayar idon ta a ƙauyen su yaji yana sha'awar sake gani, so yake ya tantance wane kala ne da eyeballs ɗin ta tunda ya tabbatar ba baƙa bace sedai baya san ta ɗau hakan da wata manufa shiyasa yake kauda Kai
"Nace ki tattara abubuwan da kuke buƙata na iya suttura zaki koma gidan auren ki gobe insha Allah".
Zuwa yanzu kam she's speechless dan ba zata ce bata gane me kuma yake nufi ba yanzu tunda gwari gwari yayi mata, ita kam ta rasa a wane layi zata ajiye wannan auren nata, da neman auren da ɗaurawa duk cikin kwana ɗaya zuwa biyu aka yi su, yanzu kuna ga tariya, a al'adar malam bahaushe dangin amarya kan haɗu su rakata gidan auren ta cikin soyayya da ƙauna amma ita gata ana batun tariyar daga ita se mijin ta da ƴaƴan ta, lallai auren ta wani iko ne na Ubangiji.
A hankali ta saci kallon sa cikin son furta abinda take so sedai bata san ya akayi ta tsinci harshen ta da furta abinda ba shi ne a zuciyar ta ba
"Allah yasa zamu ga goben da rai da lafiya".
Ameen ya faɗa daga nan kuma suka cigaba da zaman shiru, ita bata ce komai ba shi ma haka, tsayin lokaci har ta gaji da zaman ta gyara amma bashi da niyyar cewa komai
"Ki taso yaran mu tafi".
"Mu tafi, ina kenan bayan dare kuma yayi, its almost ten fa".
"And me kike nufi da zaman da kike yi a nan?".
Wani irin tuƙuƙin takaici ne ya cika mata maƙogaro, daga ɗazu zuwa yanzu ta fahimci mutumin nan wani bahago ne na daban, ko saboda ba wani kusanci ne tsakanin su na daban ba a office maybe shiyasa bata San hakan ba tuntuni.
Bata ce komai ba ta fita daga motar tare da maida murfin ta rufe masa ta wucewar ta cikin gida tana gunguni ita kaɗai.
Seda ya ga shigar ta gidan sannan ya tashi motar ya fita daga layin cike da sanyin jikin da gajiya ta haifar masa, wannan dogon tuƙin da yayi jiya da yau sam be saba masa ba shiyasa gaba ɗaya jikin sa yayi masa nauyi.
Kulle motar yayi ya fita batare da ya kula ganin ta da yayi tsaye ba, da sauri tabi bayan sa har tana haɗawa da gudu saboda takunsa irin na cikakkun maza ne masu isasshiyar lafiya
"Yaya Abdu, ya Abdu".
Yana jin ya tsaf amma yayi mata banza hakan yasa ta kuma kwasa da gudu tasha gaban sa lamarin da ya tilasta masa tsayuwar dole sedai tuni ya sake ɗin ke fuska tsaf kamar wanda be taɓa sanin wani abu wai shi annurin dariya ko murmushi ba a duniya.
"Dama Anna ce ke neman ka, tuntuni nake kiran wayar ka in faɗa maka yaƙi shiga, gashi ita kuma se kuka take da kiran sunan yaya nafi wuni guda yau taƙi cin komai".
"Kije ki faɗawa baba".
"Zuwa yanzu ya kwanta yaya Abdu, Please ka taimaka kazo muje kayi mata magana ko zata ji, na bata baki amma taki saurara ta".
Sam baya son kallon ta sabida irin shigar dake jikin ta, duk da kasancewar dare ne amma gidan nasu tarwai yake da haske da ko allura ce ta faɗi tsaf mutum ze tsugunna ya ɗau abar sa ya tashi.
Tun ba yau ba yasan ita da yayar ta nafisa Allah ya ji ƙan rai kamar gabas da yamma ne, sam bata inda suka yi kamanceceniya se ko ta fuska da kuma jini shiyasa ko da sam be sake mata fuska balle ta samu damar kawo masa raini bare kuma yanzu da yake jin kowa ma daidai yake dashi.
"Kije zan zo in nayi wanka, nayi gumi da yawa I can't go to her a haka".
Ya faɗa yana wuce ta cikin tafiyar nan tasa me cike da karfi da isa, bin bayan sa tayi da kallo cike da maɗaukakin shauƙi, lumshe ido tayi tare da rungume hannuwan a ƙirji inda take ji kamar shine ta rungume, wannan maganar da ya mata ji take kamar an mata albishir da shiga aljanna.
Tun yayar ta na da rai take so da ƙaunar yaya Abdu sedai tayi ta ƙoƙarin dannewa, yanzu kuwa da babu yayar ta bata tunanin akwai abinda ze tsayar da ita kuma.
A saɗaɗe ta juya zuwa part ɗin su, bakin ƙofa ta tarar da anna tsaye, da sauri ta riƙo hannun ta suka ƙara sa ciki kafin ta dube ta
"Yaya, cewa yai baze zo ba?".
"Yace zezo amma se yayi wanka, dawowar sa kenan baze iya zuwa gare ki a haka ba".
"Kai masha Allah bari maza in shafa rob ɗin nan a ido na ɗan suyi ja su dinga hawaye, insha Allah buƙatar mu zata biya bari ki gani".
Tsohuwa Anna ta faɗa tana murza Rob a fuskar ta, duk yadda idanun ta ke hawaye be sa ta fasa ba se da ta saka sosai ta yadda in ka kalle ta zaka ce ta daɗe tana kuka dan yadda fuskar ta tayi jajir kasancewar ta fara haka ma idanun ta suka yi ja suka tasa.
A can ɓangaren Hajiya Babba kuwa da sauri shuraiha dake tsaye jikin window riƙe da curtains tana kallon abinda ke faruwa tsakanin Abu Aulad da Nuriyya ta saki uban ashariya
"Kan uba".
Ta faɗa da sauri tana sakin curtains ɗin, bata tsaya wata wata ba ta zura bedroom slippers ɗin ta tayi waje without minding cewa kayan bacci ne a jikin ta ba, burin ta a lokacin shine ta kai gare su taji me suke tattaunawa a wannan tsohon daren.
Baza tayi sanyar da wata can daban zata ƙwace mata Abdallah ba bayan an gama kwaɗaita mata shi tare da lasa mata zuma a baki yanzu kuma a ce za'a janye, ina ba zata yarda ba.
Sedai kash ko kafin ta kai ga fita daga part ɗin su tuni ya shige nasa part ɗin ita kuma Nuriyya ta koma nasu hakan yasa ko da ta fito compound ɗin bata tadda kowa ba se ma'aikata dake ɗan kai kawo dan wasun su ma tuni sun nemi makwanci.
Haka ta koma part ɗin nasu tana cizon yatsa, taso taji me waccan karuwar ke faɗa masa wanda har ya tsaya saurara haka sedai kash bata samu ji ba, ya zama dole ta tunzura Hajiya Babba ayi ayi ai bikin su ko hankalin ta ya kwanta, daga lokacin da ta sami wannan damar a lokacin ita kanta Hajiya babbar zata raina kanta dan kallon ta kawai take itama da tata tsarin da buƙatar akan Abdallah ɗin.
A hankali yake rage kayan jikin sa cike da gajiya, wanka yake buƙata yake kusan sanyi dan yadda yake jin jikin sa na ƙaiƙayi shine kawai abinda se yi yaji sauƙi.
Singlet ɗin jikin sa yake ƙoƙarin cirewa se kuma ya fasa sanadin hango inuwa da yayi jikin labulen sa alamun akwai wani laɓe a ta wajen.
Cikin nutsuwa ya shiga takawa har ya kai wajen yasa hannu ya yaye curtains ɗin da suka rufe tagar, tsaye take cikin shaiɗanun kayan da dasu da babu a jikin ta basu da wani banbanci, suna haɗa ido ta sake masa wani arnen murmushi cike da barikanci kafin cikin kwarkwasa ta shiga lauya jikin ta tana magana da wata seducive voice
"Sannu da zuwa Abu Aulad, ga dukkan alamu ka gaji, don't mind I can takeaway all your stresses, yanzu dai muje kayi wanka ko super man?".
Kamarw anda garwashin wuta ya taɓa haka yayi watsi da hannun da takai jikin sa, ya rabbal alameen be san ya zai yi da rayuwar sa a cikin wannan gidan da a wajen sa gara kabari dashi ba.
Wani irin birkitaccen mafi ya watsa mata da yasa ta yin katantanwa ta faɗi can gefe kanta ya bugu da jikin Centre table ɗin dake falon, cikin wata irin zuciya da ta ciwo shi ya bita yasa ƙafa ta taka sangalalin hannun ta har se da yayi ƙarar dake shaida alamar in har bata sami fracture ba to tabbas ƙashin nan ya fita daga bigiren sa.
Wani wahalallen ihu ta saki da be wani fita da karfi ba saboda tsabar wahala yasa a take Muryar ta ya shaƙe, cikin wani dakusasshen Muryar da ɓacin rai ya haifar masa ya shiga yi mata concrete warning
"This is the first and last time da zan kuma ganin ki a part ɗina, na rantse da Ubangijin da ya busa min rai da second time na kuma ganin ki zan iya ɗaukar ranki dan ko banza an rage mugun iri, annoba kuma jinin shaiɗan, before the count of three ki fice min ɗaga ɗaki in ba haka ba wallahi rataye kibzan yi jikin fanka, fitsararriyar fasiƙa kawai mara kunya da tsoron Allah".
Ai ko kafin ya gama bayanin sa tuni ta tarkata hannun ta tayi waje da mugun sauri dan a yadda ta gan shi da kuma rashin imanin da ya gwada mata ta tabbatar ze iya rataye tan kamar yadda ya faɗa.
Da numfarfashi da komai takai kanta part ɗin ta zube kan kujera tana maida numfashi, wani irin zufa ne ke keto mata na wahala da azabar da take sha a jikin ta, bata taɓa sanin haka zafin karaya yake ba se yau.
Ƙwalla take zubar wa tana bin hannun da kallo yayinda cikin ranta take shan mugayen alwashi kala kala a kan shi, tun da ta riga ta ɗora ido a kan shi takuma kwaɗaitu da shi ta rantse ita kuma se ta same shi, in kuwa ba haka ba to tabbas sedai ayi biyu babu uku ba ko ɗaya ma'ana indai ba zata same shi b ato sedai kowace mace ta rasa.
Da sauri ta runtse idon ta lokacin da ta auno shi a idanun ta tare da wata mace, inaaa, ba'a haifi macen da zata amfane shi ba, ada dai tayi wannan imanin amma a yanzu zata iya yin komai in tace komai tana nufin komai wajen ganin ta saka kyakkyawar barrier tsakanin sa da duk wata ƴa mace kowace ita kuwa.
Ranar haka ta kwanan cikin azaba da raɗaɗin zuci da na jiki, ga dai jinya ya kwantar da ita kuma wai batare da ya bari ta amfanu da komai daga gare shi ba, ita da ta samu abinda taje nema to da sauki ba karya ta ba ko kashe ta yayi ba zata damu ba tunda ta cika burin ta.
A ɓangaren Abu Aulad ma haka ya kwana a zaune cikin wani irin yanayin da baze fassaru ba, be san da wane suna ze Kira gidan da yake ciki ba haka be san da wane suna ze kirayi mutanen cikin sa ba, be taɓa sanin bawa kan zaɓi mutuwa kan rayuwar sa ba se a kan shi, da ace kisan kai ba haram bane a musulunci da tuni ya daɗe da sheƙe kan sa ya huta.
Tun tasowar sa be san wani abu wai shi farin ciki ba, kullum cikin baƙin ciki da damuwa yake tun fara wayo sa har kawo yanzu da yake shekarun sa na cikakken namiji mai ji da sabon jini da ƙuruciya.
Rayuwar sa a hagunce ta faro kuma har kawo yanzu a haka take, be san se yaushe ne ze samu daidaito na rai, ruhi da rayuwa ba balle har ya samu salama, a duk sanda yaga mutane na rayuwa suna dariya da nishaɗi ya kan tsinci kansa da ayyana dama shine, so da yawa yasha kusan yin saɓo in ya zauna tunani dan ya kan dinga aiyana me yayi wa Allah da yasa ƙaddarar jarabawar tazo a haka, me yasa ba wata daban ba.
Kiran sallar asuba da ake yi ne yasa shi miƙewa yana dafe kan sa dake sara masa ya shiga toilet, daga tsayen da yake ya sakarwa kansa ruwa masu sanyi sanye da wandon shaddar da singlet ɗin batare da ya cire ba, tsayin lokaci Sannan ya gabatar da wanka ya ɗaura alwala ya fito.
Jallabiya ya zura a jikin sa tare da ɗaukar tasbah ɗin sa ya wuce masallaci, seda aka idar da sallah har gari yayi haske kafin ya taho gida.
Jiri yake gani dan rabon shi da abinci tun na safen jiya kafin su tafi ƙauye ga kuma rashin bacci sedai kasancewar tsayayyen namiji ba wanda ze fahimci hakan se wanda yayi masa sani na sosai.
Wata jallabiyar ya canja kawai ya ɗau key ɗin motar sa zuwa gidan su, ɗauko ta ze yi dan se yayi hakan hankalin sa ne kwnata, mutanen gidan su are so cunning, gwara tun kafin su farga yayi outsmarting ɗin su ya shayar dasu mamaki ya kuma basu tsoro ba kuma ta kowace hanya ba se ta kawo macen da ya nema wa kan sa auren ta cikin gidan.
Ya sani in da mace a tare dashi abubuwa da yawa zasu masa sauƙi sedai matsalar shine shin itama irin su ce, wane assurance yake dashi na ba zata zama kamar su ba, shin in aka mata tayi da zunzurutun kudi ko matsayi zata karɓa ko kuwa?!.
Wannan sune tarin abubuwan da tuntuni suke hana shi aure sedai a yanzu da yayi ba wai ze saki jiki da ita bane, hasalima auren su na da wa'adin da ya ɗibar masa wanda yana cika ze sauta, zaman sa shi kaɗai ya fiye masa dan be yarda da kowa ba baya kuma jin ze yarda ɗin.
Yaro ya samu ya aika gidan, tana cikin sawa Ifty rigar school ta jiyo Muryar yaron na faɗin aiken da aka turo shi
"Wai salma ta fito inji Abdallah".
Sedai rigar ta kubce ta faɗi daga hannun ta saboda yadda zuciyar ta ta doka da jin sunan sa, hannun ta na rawa ta sake ɗaukar rigar ta shiga kici kicin sa mata sedai ta kasa saboda ruɗewar da tayi, Hajiya ce ta amsawa yaron da gata nan fitowa saboda jiya ta zauna tayi mata bayanin komai dan kamar mahaifiyar haka ta ɗauki Hajiya saboda ba ƙaramin taimako tayi mata ba a rayuwar ta.
Ɗakin Hajiya ta shigo ta karɓi shirya Ifty dan tuni ta gana da Ibty
"Je ki bashi uzuri daga nan ki nemo yara su fara fitar miki da jakunkunan, in an kwana biyu insha Allah zan zo in ga mazaunin ki, tashi kije".
Jiki ba laka ta fita, zaune cikin motar ta same shi ƙafar sa duka biyu a waje ya lumshe idanun sa tare da jingina kan sa da makarin kujerar, seda ta tattaro duk dauriyar dake gare ta kafin ta iya gaida shi
"Barkada safiya".
Saukar Muryar ta yasa ya buɗe idon sa, kallo ɗaya yayi mata ya kau da kai tare da maida ƙafafun sa cikin motar ya fara ƙoƙarin kunna ta
"Kayi haƙuri Ban ƙara sa shirya Ifty ba amma yanzun nan zamu ƙarasa, Bari in Sami yaro ya fitar min da jakunkunan".
Fasa kunna motar yayi ya koma ya kwanta kamar ɗazu ita kuma ta matsa ta sami wani almajiri suka koma ciki tare, ko da ta shiga tuni Hajiya ta gama shirya Ifty tare da haɗa musu launch box ɗin su, manyan jakunkunan kayan su dake shaƙe ta fara jawowa tana fitarwa tsakar gida almajirin na fita dasu har suka gama, kallon ɗakin take cike da matsanancin kewar sa da zata yi kafin kuma ta maida kallon ta kan Hajiya, matar da tayi mata halaccin da har abada ba zata manta ba, a rayuwa da ita da bana Husaila sun mata abinda in har ta manta to ita ɗin butulu ce cikakiya.
Nasiha sosai Hajiya ta yi mata da har tasa ta kuka ba dan komai ba se dan kewar mahaifiyar ta da kakarta da ta taso mata, ta sani da suna nan su zasu yi mata wannan nasihar.
Haka Hajiya ta rakata har mota, ko da suka je tuni ya zuba jakunkunan a booth ɗin motar sa ita kawai yake jira.
Duk yadda yake moody be san lokacin da ya saki fuska ba da Ifty ta ƙarasa tana ɗane shi Ibty kuma na gaida shi, haka ya ɗauke su duk biyu ya riƙe yana kallon su cike da shauƙi yana sauraren shirmensu har Hajiya ta gama mata nasihar da zata yi suka idasa bakin motar, har ƙasa ya tsugunna ya gaida Hajiya abinda yayi salma matuƙar daɗi a rai.
Hala suka ɗau hanya zuwa gidan da bata sani ba tana cike da kewar rabuwa da Hajiya da ragowar ƴan uwan zaman hayar ta da basu san da maganar auren ba ma se yau da safe amma duk da haka suka bita da fatan alkhairi.
Har bakin ƙofar party ɗin mahaifin sa ya kai motar sannan ya fita ya zagaya ya buɗe mata itama ta fito a ɗarare sannan ya buɗe wa su Ibty baya suka fito, hannu yasa ya ɗau Ifty yayinda ya riƙewa Ibty hannu ya nufi falon mahaifin nasa ta rufa masa baya itama.
Gana ɗaya mutanen ɗakin suka zuba musu ido zuciyoyin marasa gaskiya na dukan uku uku, masu gaskiya kuma na musu kallon rashin fahimta.
"Barka da safiya baba, ga salma matata da ƴaƴan ta kuma nawa".
A zabure mutane shida dake falon suka miƙe tsaye kowanne da kalar tambayar da yake jefowa
"What?, Me?, Kutumar uba?, Mata?, How comes?, Haba da Allah!.
Wannan sune ruwan tambayoyin da suka dinga yawo a falon cikin ihun muryoyi daban daban yayinda Abu Aulad ya saki hannun Ibty ya saka hannun ya jawo salma cikin jikin sa ya rungume.........................✍🏻.
Tooooooooh jama'a, gamu a ƙarshen free page da izinin Ubangiji, ko yaya paid pages zasu kasance?!.
Shin wacece Abu Aulad ya karyawa hannu jiya da dare?!
Wacece shuraiha?, Wai ma tsaya ita kanta Hajiya babbar wacece, meye alaƙarta da Abu Aulad?!
Jarumi, jarumi!, Shin kun Tuna shi?! Wanne shi?.
Nuriyya ƙanwar nafisa ƴa a wajen Anna, ko meye ƙudurin ta kan Abu Aulad?!.
Yace be yarda da kowa ba se kan shi kaɗai, what about Haisam?!.
Haisam, Haisam, anya shima babu wani ƙulli kuwa a under
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9 Chapter 10