wani rissinar da kai kamar gaske. A ranta tace, ‘Munafuki dan ka gansa a wajen kake wani acting like mutumin ƙwarai. Zanyi maganinka ne ai, bara na gama da na sama da kai’.
Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe tare da leƙowa. a marairaice yace, “Please Brother na shigo muje tare?”.
Wata banzar harara Yoohan ya watsa masa. Saurin barin jikin motar yay yana ɓata fuska. A ransa kuwa wani irin wutar son Aymah ce ke ruruwa masa a zuciya tare dajin zafin Yayan nasa mai share kukansa a koda yaushe wajen magance masa bukatunsa. Da ƙyar ya iya nufar garden inda abokansa suke zaune da giyar da zasu sha ransa duk a ƙuntace. Dan tabbas yanaji a ransa bazai iya haƙuri ya barma Yayan nasa zuƙeƙiyar yarinyarnan datai dai-dai da burinsa ba. Shi musilincinta ko yarenta duk ba damuwarsa ba. Itaɗin yake so, so irin wanda ke shiga ɗin nan farat ɗaya a zuciya batare da yayi shawara da mai zuciyar ba. Dan a kallo ɗaya da yayma Aymah a wajen dinner tai masa shigar corona virus a zuciya. Bakuma tayi sanya ba wajen mamaye dukan zuciyarsa da ilahirin jikinsa. Dan haka koda bala'i sai ya mallaketa, sai ya ɗanɗani zumarta, sai ya ɗanɗana mata tashi kuma. Yanaji a ransa zata soshi fiye da Brother Yoohan inhar ya bayyana masa abinda ke cikin zuciyarsa game da ita..............✍
😸Wa yaga kwamatsala ɗan Nageriya da mulkin Amuruka😜.
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[6/14, 2:54 PM] +234 901 860 0202: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
_Ina mata masu son ingattun kayan kamshi: Na kece raini? Kayan mata masu sa kishiya k’wafa? Bikin dangin miji ba za’a baki yankan albasa ba da wankin tumatir? To matso kusa domin HAJARA COLLECTION ta kawo muku kayayyaki na gyara ciki da wajen mace, Wanda suka kunshi:_
_Khumrahs: Sudaniyya, Chadian, Dufr, Fara da brown, Kai harda masu flavours... _
_Akwai turaren wuta irin su sandal, Hawi, Alut, Gab gab da sauran su.._
_Akwai turaren tsugunno dana jiki original gangariya tafiyayye dan gaske_
_Hajara collection ta kawo muku air fresheners, Mopping sprays da turaren wanki..._
_TANA BADA KAYANTA AKAN FARASHIN SARI KO SAYA DAYA DAYA, SANNAN TANA TURA KAYANTA A KOINA AFADIN NIGERIA_
_AVAILABLE IN WHOLESALE/RETAILS. Nationwide deliveries. 100% tested and trusted...!!!_
_Kyau, inganci, Rahusa... Sai kayan HAJARA COLLECTION....!_
_idan anje siya ace daga zafafa biyar.. Akwai special package da Za’a hada maka masu kamshi🥰😍🧚🏻♂️_
______________
No. 52
............Motar tayi shiru, bakajin komai saina fitar sassanyan ac da sautin karatun al-qur'ani daya saka can ƙasa. A hankali yake tuƙin kamar baya so. Fuskar nan babu ko alamun yasan minene ma murmushi. Duk da Aymah tasan shiɗin ba mutum bane mai fara'a aɗan zaman da sukayi, sai duk tajita a takure da yanda yay matuƙar tsuke fuskar.
Sake lafewa tai abinta cikin kujera ƙamshin motar da sanyin ac na kuma saka mata kasala. A zahiri zakace idanunta a rufe suke, sai dai sam ba haka bane. Ta ƙasan ido take ƙare masa kallo daki-daki kamanin balarabiyar nan ta hoto na sake bayyana tattare da shi. A ranta kuwa rayawa take, ‘Dolene kayi ƙyau, ashe kanada alaƙa da larabawa. Ga papan ma duk da kasancewarsa ɗan African, Africa ɗin ma Najeriya, Najeriyarma kudanci shiɗin ƙyaƙyƙyawa ne tabbas’.
Yoohan dake ji a jikinsa kallonsa akeyi ya ɗan juyo ya kalleta. Duk da idanunta a rufe suke ya fahimci ba barci take ba. Dan inba ita ɗinba babu wanda zai kallesa tunda a mota suke, motarma mai tinted glass. Baice komaiba ya cigaba da tuƙinsa kamar baya son suje inda zasu ɗin.
Sun isa haɗaɗen shagon sayayyar da Abujawan da kansu keji da shi, (bazan faɗi suna ba, danni na dainama masu shaguna talla yanzun🙄, duk maison a ringa saka sunan shagonsa a littafi yazo ya biya kuɗi koda baturene😎😏).
Sai da ya gama dai-daita fakin ya buɗe motar zai fita sannan Nu'aymah ta buɗe idanu. Batasan wannan cinkushe fuskar dan haka cikin neman tsokanar data iya tai saurin faɗin, “Ni dai gaskiya bazan shiga da kaiba wani yazata kidnapping ma'aikatan mukazoyi”.
Jin abinda ta faɗa ɗinne ya hanashi zura ɗayar ƙafar da yay niyya dan har ya sauke ɗaya a ƙasa. Juyowa yay yana kallonta. Ta cika kumatu da iska tana tura baki. “Yoni ka daina kallona da waɗan nan idanun iya gaskiyata na faɗa. tayaya dan ALLAH zan bika, kaga fuskarka kuwa? Yasin kamar ta shekau na dajin sambisa. Dan haka yi gaba zan biyoka a baya”.
Duk yanda yaso daurewa ya gaza, ya kauda kansa gefe murmushi na suɓuce masa. A ransa yana jinjina rashin jin yarinyar nan da rashin tsoro. A fili kam sai ya ƙarasa fita yana faɗin, “Silly girl sakko, kafin in jehoki ƙasa”.
Baki ta murguɗa tana buɗe ƙofar ta fito. Cikin ƙunƙuni tace, “Kaima dai nakusa fara kiranka Silly boy ɗin nan daka ishi mutan da shi”. Ta ƙare maganar tana ƙarasawa inda yake tsaye yana gyara p-cap ɗin da a yanzu itadai ta gansa da ita. Dan da suka fito kansa babu hula. Kallonsa tai ta ɗauke kanta, a ranta kuwa tana yaba yanda p-cap ke masa ƙyau idan ya sanya. Musamman a yanzu da komai na jikinsa ya kasance baƙi, hularce kawai fara.
“Malama kallon da kikemin ya isheni”. Taji maganarsa a bazata. Sai dai yayi gaba kamar bashine ya faɗa ba. Murya taɗan ɗaga kaɗan yanda zai jita tace, “Kai da wane idon kasan ina kallonka?”.
Tsayawa yay tare da juyowa gaba ɗayansa. Ita kuma ta riga da tazo gab da shi sai tai ƙoƙarin yin baya ganin zasuyi karo. Tako tafi gaba ɗayanta zatasha ƙasa. Da sauri ya bita ya tallafo ƙugunta ta dawo jikinsa. A yanda ƙirjinta ke bugawa ya tabbatar masa taji tsoron faɗuwar sosai. Samun kansa yay dajin dariya na taho masa. Ya ɗanyi kamar zai saketa, tai wani uban tsalle ta mamuƙesa zata saki ihu yay azamar danne bakin da ɗayan hannunsa yana kallon yanda tsirarun mutane dake shiga da fita cikin wajen suna kallonsu. Wasu na dariya wasu na gulma.
Idanunsa ya rumtse da sauri yana faɗin, “Shikenan kin tara mana mutane hankalinki ya kwant...” Ai baima kai ƙarsheba ta fincike jikinta tana turesa. Sai kuma tai saurin komawa bayansa ta ɓuya ganin da gaske kallon nasu akeyi. Gaba ɗaya kunya ta dabaibayeta kamar ta nutse ƙasa takeji.
“ALLAH ne ya rama min”. Ya juya da wani salo yana yin manar a cikin kunnenta kamar bashi ya faɗa ɗin ba. Da sauri tabi bayansa tana tura baki gaba. Sai dai da alama bakin tsuwar ya mutu kam.
Kamar yanda ƙa'idar shiga wajen take sai da akai bincikesu sannan suka shiga, sai dai yanzu kam a jere suke tafiya gwanin sha'awa. Batare da ya kalleta ba yace, “Mizaki saya?”.
“Duka shagon”. Ta bashi amsa itama batare data kallesa ba.
Shima da yake ya iya baƙar maganar sai cewa yay, “Okay sai muje a saidama Shekau ɗin da kikace Kano muzo musai shagon da kuɗin”.
Babu shiri taja birki harda riƙe ƙugu. Shima tsayawar yay ya tura duka hannayensa cikin aljihun yana kallonta fuska a ciskule. “Ai wlhy sai dai a saida garinku, dan kano tafi ƙarfin shekau”.
“Trouble maker”.
Ya faɗa yanayin gaba. Bayansa tabi tana ƙunƙuni, sai dai bajin abinda take faɗan akeba. A haka suka shiga wajen kayan ƙwalam da maƙulashe. Irin kalolin biscuits da kayan ƙwaɗayin dataga ya tara a gida yaketa ɗiba yanzun ma, hakan yasa ta dinga binsa da kallo kawai tana gulmarsa a cikin zuciya, (wai maƙwaɗaici ne🤣).
Sai da ya kusan cika keken sannan ya kalleta. “Kifa ɗeba naki, dan ba ƙara cimin nawa zakiyi ba yarinya”. Idan ba ita datasan shine yayi maganarba babu yanda za'ai ace shi yayita. Dan ya ɗauke kansa ya cigaba da harkar gabansa.
Leɓe Aymah ta ciza, a ranta take raya ‘zakaga mugunta kuwa yau ɗan balarabe’ komawa baya tayi itama ta jawo nata keken. Ta shiga lodar chocolates da kayan ciye-ciye iri-iri. Wanima ko saninsa batayiba balle tasan zaiyi daɗi ko bazaiyiba. Saida ta cika kwandon nan dam da kayan ƙwaɗayi kawai har tana turawa da ƙyar tsabar mugunta. Tana a layin ƙarshe zata ɗauki wani roban chewing gum taji ƙamshin turaren da ya sakata waige-waige da sauri. Cikin kwandon ta jefa chewing gum ɗin tai saurin fitowa a lungun tana leƙe. Babu ko mai alamarsa, sai dai tabbas wannan ƙamshin shi kaɗai ta sani da shi. Duk da zuciyarta na ayyana mata wanine bashi ba ta kasa aminta. Sai ƙara kutsa kai take kowanne layi dan dubashi. Wani irin mugun bugawa ƙirjinta yayi jin an riƙo mata hannu. Ta waigo da sauri sai taga Yoohan ne.
“Miye kike nema haka?”.
Yay maganar babu wasa a fuskarsa. Sannan muryarsa a kausashe kamar wanda yake cikin fushin da ɓacin rai. Kanta ta girgiza masa tana ƙoƙarin maida ƙwallar da suka cika mata ido. Bai sake cemata komaiba yaja hannun nata suka bar wajen. Duk da taga bai maidata wajen kayanta data bariba, ba tai magana ba. A mamakinta saita hangi kayan can wajen bada kuɗi ana loda musu a ledoji. Suna isowa matar fuskarta faɗaɗe da murmushi tace, “Doctor ATM”. Zarowa yay a wallet ya miƙa mata batare da yace komaiba. Ta amsa idanunta akan Nu'aymah dake sake waige-waigen ko zata gansa anan.
“Amaryar Doctor Good evening ”. Maganar matar ta maidota hankalinta. A taƙaice ta amsa mata duk da ta fahimci akwai sanayya tsakaninta da Yoohan ɗin. Ta ɗan dubesa lokacin da ma'aikatan wajen ke kwashe ledojin zasu kai masu mota. Har yanzun fuskarsa babu sauƙi. Gashi ya wani riƙe mata hannu gam kamar za'a saceta. ATM ɗin ya amsa yaja hannunta suka fita.
A can wajen motar da sukazo taga anata loda kaya harma da wanda bataga sanda aka sayaba ita dai. Batayi magana ba dan bataga fuskaba. Saima buɗe mata murfin yayi yay mata alamar ta shiga. Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe mata. Ta mazauninsa ya zagaya, taga ya buɗe lokar motar ya ciri kuɗi ya maida ya rufe. Batasan waya bamawa ba, sai dai bai jimaba ya dawo suka fice a wajen.
A lokacin anata kiraye-kirayen sallar magriba. Gudu yake yanzu sosai, kai tsaye anguwar su Abban Abdallah ya nufa. Daɗi ya kama Aymah sai dai ta haɗiye abinta a ciki har suka isa. Anata hada-hadar shiga sallar magriba a massallacin ƙofar gidan. Horn ɗaya kuwa yayi maigadi dake ƙoƙarin fitowa zaije salla yay murmushi yana komawa ya buɗe musu. Shiga Yoohan yay da motar har ciki yay fakin Aymah nata mamakin ƙarfin halinsa.
“Kije ciki zanje nai salla”. Yay maganar yana buɗe motar ya fita. Ai tuni ma ta rigashi fitar. Sai hangota yay ta tsilla da gudu hanyar shiga cikin gidan. Da kallo kawai ya bita harta buɗe ƙofar falon ta shige.
Ya ɗan lumshe idanunsa ya buɗe yana nufar hanyar fita gate ɗin da hanzari jin za'a tada salla.
Da uban ihu Nu'aymah ta shiga tana ƙwalama su Amal kira. Aiko kamar jira suma sai gasu da gudun sun fitowa suna ihun murnar ganinta. Momy na salla take jiyo ihun nasu. Sai da sukayi mai isarsu sannan suka sarara. Ɗakin Amal ɗin suka nufa inda Yusrah da Adawiya dataƙi fitowa suke hutunsu da basusan dalilinsa ba balle ranar komawa kano.
Duk da idon Aymah ya ga Adawiya dake kwance a kan gado tana danna waya sai tai tamkar bata ganta ba ta cigaba da biyema su Yusrah dake mata sherin wai ta canja saboda daɗin aure ko sun sami baby ne?. Shaƙiyanci sukaitama juna suna sheƙa dariyar dake sake ƙullar da Adawiya. Dan suma su Amal ɗin ta ishesu. Kullum haka take yini a gidan cikin ɗacin rai, bata shiga sabgarsu basa shiga tata. Momy tayi faɗan harta gaji ta zuba musu idanu.
Sallar suma sukayi, kafin su idar Adawiya tabar ɗakin ta koma falo. Bayan sun idar cikin dabara Aymah take tambayarsu Amal yaushe Yusrah zata tare tunda taga Yah Ab bai koma ba. Da mamaki sosai Amal tace, “Yah Ab ɗin da ya koma Saudia tun randa aka ɗaura miki aure. Kuma Yusrah ai tace bazata tare a gidansa ba saboda fitinar Adawiya”.
Bayanin Amal ya matuƙar ɗaure kan Aymah, dan ita dai tabbas-tabbas tanaji a ranta da Yah Ab sukai gamo a inda suka baro. Sai dai batasan dalilinsa na ɓoye mata kansa ba. Danne wannan tunanin tayi a zuciyarta ta fuskanci Yusrah datai kamar bataji mi suke magana a kai ba.
“Yusrah! Miyasa baƙya son zama da Yah Ab wai dan ALLAH?”.
Murmushi Yusrah tayi tana ƙoƙarin miƙewa daga wajen gaba ɗaya, Aymah tai saurin maidata ta zauna. “ALLAH babu inda zakije sai kin amsamin tambaya ta”.
“Humm Aymah kenan, ba amsa tambayarki bace mai wahala, hujjar amsata. Ni bancema kowa bana son Yah Ab ba ai. Kawai dai zaman aurene banason yi da shi. Fatan da nakeson muyi ni da ku kawai shine ya maida Adawiya ɗakinta. Indan ba hakaba kuwa tsugunne bata ƙareba a family ɗinmu wlhy. Adawiya na son Yah Ab sosai duk da nasan tabbas Nu'aymah kin fita sonsa. Amma ke yanzun wannan babin ya shafe a gareki dan dama ƙaddarace tazo muku da wannan yanayin”.
“Amma Yusrah.…..”
“No Aymah karki sake cewa komai dan ALLAH. Mu ajiye wannan maganar haka kawai. Ku tashima muje dan ga kamar momy can ta fito”.
Badan Nu'aymah taso ba tai shiru.
A falo kam zaman Adawiya babu jimawa Abba da Yoohan suka shigo falon Omar biye da su. Ɗago kanta tayi da nufin yima Abba sannu idanunta ya sauka akan Yoohan da shi koma kallon inda take baiyi ba. Ganin har zasu wuce batai magana ba Abbah yace, “Adawiya baki iya gaisuwa ba ne? Ko bakiga mijin ƴar uwarkiba Nu'aymah?”.
Da gaske gaban Adawiya sai da ya faɗi. Bakinta na rawa ta gaida Yoohan. Sau ɗaya ya amsa tare da mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Binsa da kallo kuwa ta cigaba da yi harya shige falon Abbah.
A fili tace, ‘Dama Aymah ba ƙabila akace ta aura ba? Naga kuma balarabe?’. Bata da mai bata wannan amsar dan haka tai shiru tana saƙe-saƙenta a cikin zuciya har Momy ta fito tana tambayarta ihun mi takeji ɗazun. Tana cikin sanar ma Momyn ne su Aymah suka fito. Zuwa Nu'aymah tai ta rungume Momy cike da murna.
Momy dake dariya tace, “Ja'ira, an girma ba'asan an girma ba”.
Dariya ta sakeyi su Amal na taya ta. Adawiya dai tai muƙuy kamar bata falon abin duniya ya gama isarta a rai game da ganin mijin Nu'aymah..
Tura Amal momy tayi ta kira Uwaliya mai aikin da aka kawoma Nu'aymah daga kano. Ashe dama ita suka biyo ɗauka batare da Yoohan ya sanar mata ba. Ba wata tsohuwa bace ba. Zata iya kai kimanin shekaru talatin da bakwai dai. Sun gaisa da Nu'aymah momy tai musu bayanin juna. Har cikin zuciya Aymah taji son zama da Uwaliya kuwa. Dan haka cikin jin daɗi ta miƙe domin zuwa falon Abbah ta gaidashi shima.
Basu bar gidanba sai goma saura. Sun tafi da Uwaliya. Su Amal ma sun mata alƙawarin zuwa next week dan dama Abbah ne ya hanasu wai karsuje su tada mata hankali. Amma yanzu daya ganta babu wata damuwa yace zai barsu suje ɗin amma sai weekend insha ALLAH.
Papa kawai suka samu a harabar gidan zaune. Sai su Solomon da suma ke tasu hirar acan gehe. Ita dai tana gaida papan ciki suka wuce da Uwaliya. Shi kuma ya nufi inda papan yake zaune.
Basu sami kowa a falon ba. Gidan ma shiru alamar duk sun kwanta. Ta fahimci ɗabi'arsu ce barcin wuri, musamman ma yaran saboda makaranta. Da kuma su ɗin kansu daya kasance duk suna fita aiki da safe. Uwaliya nata kalle-kalle ita dai har suka ƙarasa sashensu. Sarai Aymah taga Momy acan ƙofar sashenta zaune. Amma sai tai kamar bata ganta ba suka shige abinsu.
A falo suka yada zango. Kusan zaman mintuna ashirin sai gashi ya shigo tare da su Solomon da suka
Showing 180001 words to 183000 words out of 303604 words
Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe tare da leƙowa. a marairaice yace, “Please Brother na shigo muje tare?”.
Wata banzar harara Yoohan ya watsa masa. Saurin barin jikin motar yay yana ɓata fuska. A ransa kuwa wani irin wutar son Aymah ce ke ruruwa masa a zuciya tare dajin zafin Yayan nasa mai share kukansa a koda yaushe wajen magance masa bukatunsa. Da ƙyar ya iya nufar garden inda abokansa suke zaune da giyar da zasu sha ransa duk a ƙuntace. Dan tabbas yanaji a ransa bazai iya haƙuri ya barma Yayan nasa zuƙeƙiyar yarinyarnan datai dai-dai da burinsa ba. Shi musilincinta ko yarenta duk ba damuwarsa ba. Itaɗin yake so, so irin wanda ke shiga ɗin nan farat ɗaya a zuciya batare da yayi shawara da mai zuciyar ba. Dan a kallo ɗaya da yayma Aymah a wajen dinner tai masa shigar corona virus a zuciya. Bakuma tayi sanya ba wajen mamaye dukan zuciyarsa da ilahirin jikinsa. Dan haka koda bala'i sai ya mallaketa, sai ya ɗanɗani zumarta, sai ya ɗanɗana mata tashi kuma. Yanaji a ransa zata soshi fiye da Brother Yoohan inhar ya bayyana masa abinda ke cikin zuciyarsa game da ita..............✍
😸Wa yaga kwamatsala ɗan Nageriya da mulkin Amuruka😜.
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[6/14, 2:54 PM] +234 901 860 0202: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 52
_________________
_*HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION._*
_Ina mata masu son ingattun kayan kamshi: Na kece raini? Kayan mata masu sa kishiya k’wafa? Bikin dangin miji ba za’a baki yankan albasa ba da wankin tumatir? To matso kusa domin HAJARA COLLECTION ta kawo muku kayayyaki na gyara ciki da wajen mace, Wanda suka kunshi:_
_Khumrahs: Sudaniyya, Chadian, Dufr, Fara da brown, Kai harda masu flavours... _
_Akwai turaren wuta irin su sandal, Hawi, Alut, Gab gab da sauran su.._
_Akwai turaren tsugunno dana jiki original gangariya tafiyayye dan gaske_
_Hajara collection ta kawo muku air fresheners, Mopping sprays da turaren wanki..._
_Akwai herbal organic soap wato sabulun gyaran jiki na maida tsohuwa yarinya.._
_Sannan Hajia hajara collection tana gyaran jiki.. Tana kuma siyarwa da kayan gyaran jiki na dilke set, Fata tai luwai luwai kamar ta jarirai.._
_Akwai special bridal spa wato gyaran jikin Amarya... Duk Amarya mai son tadinga kamshi har bayan shudewar bikinta to ta nemi hajara collection.._
_Akwai duk wasu nau’in kayayyakin turare masu kamsasa unguwa baki d’aya, Ki mopping tiles suyi sati suna kamshi, Kayan Haj hajara collection akwai inganci sosai._
_Akwai page dinta a favebook mai suna *GIDAN KAMSHI* ga mai son zuwa ya duba hajarta, Ko kuma ya tuntubeta a number wayarta kamar haka: 09032069304_
_Adireshi: KANO NIGERIA, MARIRI dake Kan titin MAIDUGURI RD. KANO STATE.._
_TANA BADA KAYANTA AKAN FARASHIN SARI KO SAYA DAYA DAYA, SANNAN TANA TURA KAYANTA A KOINA AFADIN NIGERIA_
_AVAILABLE IN WHOLESALE/RETAILS. Nationwide deliveries. 100% tested and trusted...!!!_
_Kyau, inganci, Rahusa... Sai kayan HAJARA COLLECTION....!_
_idan anje siya ace daga zafafa biyar.. Akwai special package da Za’a hada maka masu kamshi🥰😍🧚🏻♂️_
______________
No. 52
............Motar tayi shiru, bakajin komai saina fitar sassanyan ac da sautin karatun al-qur'ani daya saka can ƙasa. A hankali yake tuƙin kamar baya so. Fuskar nan babu ko alamun yasan minene ma murmushi. Duk da Aymah tasan shiɗin ba mutum bane mai fara'a aɗan zaman da sukayi, sai duk tajita a takure da yanda yay matuƙar tsuke fuskar.
Sake lafewa tai abinta cikin kujera ƙamshin motar da sanyin ac na kuma saka mata kasala. A zahiri zakace idanunta a rufe suke, sai dai sam ba haka bane. Ta ƙasan ido take ƙare masa kallo daki-daki kamanin balarabiyar nan ta hoto na sake bayyana tattare da shi. A ranta kuwa rayawa take, ‘Dolene kayi ƙyau, ashe kanada alaƙa da larabawa. Ga papan ma duk da kasancewarsa ɗan African, Africa ɗin ma Najeriya, Najeriyarma kudanci shiɗin ƙyaƙyƙyawa ne tabbas’.
Yoohan dake ji a jikinsa kallonsa akeyi ya ɗan juyo ya kalleta. Duk da idanunta a rufe suke ya fahimci ba barci take ba. Dan inba ita ɗinba babu wanda zai kallesa tunda a mota suke, motarma mai tinted glass. Baice komaiba ya cigaba da tuƙinsa kamar baya son suje inda zasu ɗin.
Sun isa haɗaɗen shagon sayayyar da Abujawan da kansu keji da shi, (bazan faɗi suna ba, danni na dainama masu shaguna talla yanzun🙄, duk maison a ringa saka sunan shagonsa a littafi yazo ya biya kuɗi koda baturene😎😏).
Sai da ya gama dai-daita fakin ya buɗe motar zai fita sannan Nu'aymah ta buɗe idanu. Batasan wannan cinkushe fuskar dan haka cikin neman tsokanar data iya tai saurin faɗin, “Ni dai gaskiya bazan shiga da kaiba wani yazata kidnapping ma'aikatan mukazoyi”.
Jin abinda ta faɗa ɗinne ya hanashi zura ɗayar ƙafar da yay niyya dan har ya sauke ɗaya a ƙasa. Juyowa yay yana kallonta. Ta cika kumatu da iska tana tura baki. “Yoni ka daina kallona da waɗan nan idanun iya gaskiyata na faɗa. tayaya dan ALLAH zan bika, kaga fuskarka kuwa? Yasin kamar ta shekau na dajin sambisa. Dan haka yi gaba zan biyoka a baya”.
Duk yanda yaso daurewa ya gaza, ya kauda kansa gefe murmushi na suɓuce masa. A ransa yana jinjina rashin jin yarinyar nan da rashin tsoro. A fili kam sai ya ƙarasa fita yana faɗin, “Silly girl sakko, kafin in jehoki ƙasa”.
Baki ta murguɗa tana buɗe ƙofar ta fito. Cikin ƙunƙuni tace, “Kaima dai nakusa fara kiranka Silly boy ɗin nan daka ishi mutan da shi”. Ta ƙare maganar tana ƙarasawa inda yake tsaye yana gyara p-cap ɗin da a yanzu itadai ta gansa da ita. Dan da suka fito kansa babu hula. Kallonsa tai ta ɗauke kanta, a ranta kuwa tana yaba yanda p-cap ke masa ƙyau idan ya sanya. Musamman a yanzu da komai na jikinsa ya kasance baƙi, hularce kawai fara.
“Malama kallon da kikemin ya isheni”. Taji maganarsa a bazata. Sai dai yayi gaba kamar bashine ya faɗa ba. Murya taɗan ɗaga kaɗan yanda zai jita tace, “Kai da wane idon kasan ina kallonka?”.
Tsayawa yay tare da juyowa gaba ɗayansa. Ita kuma ta riga da tazo gab da shi sai tai ƙoƙarin yin baya ganin zasuyi karo. Tako tafi gaba ɗayanta zatasha ƙasa. Da sauri ya bita ya tallafo ƙugunta ta dawo jikinsa. A yanda ƙirjinta ke bugawa ya tabbatar masa taji tsoron faɗuwar sosai. Samun kansa yay dajin dariya na taho masa. Ya ɗanyi kamar zai saketa, tai wani uban tsalle ta mamuƙesa zata saki ihu yay azamar danne bakin da ɗayan hannunsa yana kallon yanda tsirarun mutane dake shiga da fita cikin wajen suna kallonsu. Wasu na dariya wasu na gulma.
Idanunsa ya rumtse da sauri yana faɗin, “Shikenan kin tara mana mutane hankalinki ya kwant...” Ai baima kai ƙarsheba ta fincike jikinta tana turesa. Sai kuma tai saurin komawa bayansa ta ɓuya ganin da gaske kallon nasu akeyi. Gaba ɗaya kunya ta dabaibayeta kamar ta nutse ƙasa takeji.
“ALLAH ne ya rama min”. Ya juya da wani salo yana yin manar a cikin kunnenta kamar bashi ya faɗa ɗin ba. Da sauri tabi bayansa tana tura baki gaba. Sai dai da alama bakin tsuwar ya mutu kam.
Kamar yanda ƙa'idar shiga wajen take sai da akai bincikesu sannan suka shiga, sai dai yanzu kam a jere suke tafiya gwanin sha'awa. Batare da ya kalleta ba yace, “Mizaki saya?”.
“Duka shagon”. Ta bashi amsa itama batare data kallesa ba.
Shima da yake ya iya baƙar maganar sai cewa yay, “Okay sai muje a saidama Shekau ɗin da kikace Kano muzo musai shagon da kuɗin”.
Babu shiri taja birki harda riƙe ƙugu. Shima tsayawar yay ya tura duka hannayensa cikin aljihun yana kallonta fuska a ciskule. “Ai wlhy sai dai a saida garinku, dan kano tafi ƙarfin shekau”.
“Trouble maker”.
Ya faɗa yanayin gaba. Bayansa tabi tana ƙunƙuni, sai dai bajin abinda take faɗan akeba. A haka suka shiga wajen kayan ƙwalam da maƙulashe. Irin kalolin biscuits da kayan ƙwaɗayin dataga ya tara a gida yaketa ɗiba yanzun ma, hakan yasa ta dinga binsa da kallo kawai tana gulmarsa a cikin zuciya, (wai maƙwaɗaici ne🤣).
Sai da ya kusan cika keken sannan ya kalleta. “Kifa ɗeba naki, dan ba ƙara cimin nawa zakiyi ba yarinya”. Idan ba ita datasan shine yayi maganarba babu yanda za'ai ace shi yayita. Dan ya ɗauke kansa ya cigaba da harkar gabansa.
Leɓe Aymah ta ciza, a ranta take raya ‘zakaga mugunta kuwa yau ɗan balarabe’ komawa baya tayi itama ta jawo nata keken. Ta shiga lodar chocolates da kayan ciye-ciye iri-iri. Wanima ko saninsa batayiba balle tasan zaiyi daɗi ko bazaiyiba. Saida ta cika kwandon nan dam da kayan ƙwaɗayi kawai har tana turawa da ƙyar tsabar mugunta. Tana a layin ƙarshe zata ɗauki wani roban chewing gum taji ƙamshin turaren da ya sakata waige-waige da sauri. Cikin kwandon ta jefa chewing gum ɗin tai saurin fitowa a lungun tana leƙe. Babu ko mai alamarsa, sai dai tabbas wannan ƙamshin shi kaɗai ta sani da shi. Duk da zuciyarta na ayyana mata wanine bashi ba ta kasa aminta. Sai ƙara kutsa kai take kowanne layi dan dubashi. Wani irin mugun bugawa ƙirjinta yayi jin an riƙo mata hannu. Ta waigo da sauri sai taga Yoohan ne.
“Miye kike nema haka?”.
Yay maganar babu wasa a fuskarsa. Sannan muryarsa a kausashe kamar wanda yake cikin fushin da ɓacin rai. Kanta ta girgiza masa tana ƙoƙarin maida ƙwallar da suka cika mata ido. Bai sake cemata komaiba yaja hannun nata suka bar wajen. Duk da taga bai maidata wajen kayanta data bariba, ba tai magana ba. A mamakinta saita hangi kayan can wajen bada kuɗi ana loda musu a ledoji. Suna isowa matar fuskarta faɗaɗe da murmushi tace, “Doctor ATM”. Zarowa yay a wallet ya miƙa mata batare da yace komaiba. Ta amsa idanunta akan Nu'aymah dake sake waige-waigen ko zata gansa anan.
“Amaryar Doctor Good evening ”. Maganar matar ta maidota hankalinta. A taƙaice ta amsa mata duk da ta fahimci akwai sanayya tsakaninta da Yoohan ɗin. Ta ɗan dubesa lokacin da ma'aikatan wajen ke kwashe ledojin zasu kai masu mota. Har yanzun fuskarsa babu sauƙi. Gashi ya wani riƙe mata hannu gam kamar za'a saceta. ATM ɗin ya amsa yaja hannunta suka fita.
A can wajen motar da sukazo taga anata loda kaya harma da wanda bataga sanda aka sayaba ita dai. Batayi magana ba dan bataga fuskaba. Saima buɗe mata murfin yayi yay mata alamar ta shiga. Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe mata. Ta mazauninsa ya zagaya, taga ya buɗe lokar motar ya ciri kuɗi ya maida ya rufe. Batasan waya bamawa ba, sai dai bai jimaba ya dawo suka fice a wajen.
A lokacin anata kiraye-kirayen sallar magriba. Gudu yake yanzu sosai, kai tsaye anguwar su Abban Abdallah ya nufa. Daɗi ya kama Aymah sai dai ta haɗiye abinta a ciki har suka isa. Anata hada-hadar shiga sallar magriba a massallacin ƙofar gidan. Horn ɗaya kuwa yayi maigadi dake ƙoƙarin fitowa zaije salla yay murmushi yana komawa ya buɗe musu. Shiga Yoohan yay da motar har ciki yay fakin Aymah nata mamakin ƙarfin halinsa.
“Kije ciki zanje nai salla”. Yay maganar yana buɗe motar ya fita. Ai tuni ma ta rigashi fitar. Sai hangota yay ta tsilla da gudu hanyar shiga cikin gidan. Da kallo kawai ya bita harta buɗe ƙofar falon ta shige.
Ya ɗan lumshe idanunsa ya buɗe yana nufar hanyar fita gate ɗin da hanzari jin za'a tada salla.
Da uban ihu Nu'aymah ta shiga tana ƙwalama su Amal kira. Aiko kamar jira suma sai gasu da gudun sun fitowa suna ihun murnar ganinta. Momy na salla take jiyo ihun nasu. Sai da sukayi mai isarsu sannan suka sarara. Ɗakin Amal ɗin suka nufa inda Yusrah da Adawiya dataƙi fitowa suke hutunsu da basusan dalilinsa ba balle ranar komawa kano.
Duk da idon Aymah ya ga Adawiya dake kwance a kan gado tana danna waya sai tai tamkar bata ganta ba ta cigaba da biyema su Yusrah dake mata sherin wai ta canja saboda daɗin aure ko sun sami baby ne?. Shaƙiyanci sukaitama juna suna sheƙa dariyar dake sake ƙullar da Adawiya. Dan suma su Amal ɗin ta ishesu. Kullum haka take yini a gidan cikin ɗacin rai, bata shiga sabgarsu basa shiga tata. Momy tayi faɗan harta gaji ta zuba musu idanu.
Sallar suma sukayi, kafin su idar Adawiya tabar ɗakin ta koma falo. Bayan sun idar cikin dabara Aymah take tambayarsu Amal yaushe Yusrah zata tare tunda taga Yah Ab bai koma ba. Da mamaki sosai Amal tace, “Yah Ab ɗin da ya koma Saudia tun randa aka ɗaura miki aure. Kuma Yusrah ai tace bazata tare a gidansa ba saboda fitinar Adawiya”.
Bayanin Amal ya matuƙar ɗaure kan Aymah, dan ita dai tabbas-tabbas tanaji a ranta da Yah Ab sukai gamo a inda suka baro. Sai dai batasan dalilinsa na ɓoye mata kansa ba. Danne wannan tunanin tayi a zuciyarta ta fuskanci Yusrah datai kamar bataji mi suke magana a kai ba.
“Yusrah! Miyasa baƙya son zama da Yah Ab wai dan ALLAH?”.
Murmushi Yusrah tayi tana ƙoƙarin miƙewa daga wajen gaba ɗaya, Aymah tai saurin maidata ta zauna. “ALLAH babu inda zakije sai kin amsamin tambaya ta”.
“Humm Aymah kenan, ba amsa tambayarki bace mai wahala, hujjar amsata. Ni bancema kowa bana son Yah Ab ba ai. Kawai dai zaman aurene banason yi da shi. Fatan da nakeson muyi ni da ku kawai shine ya maida Adawiya ɗakinta. Indan ba hakaba kuwa tsugunne bata ƙareba a family ɗinmu wlhy. Adawiya na son Yah Ab sosai duk da nasan tabbas Nu'aymah kin fita sonsa. Amma ke yanzun wannan babin ya shafe a gareki dan dama ƙaddarace tazo muku da wannan yanayin”.
“Amma Yusrah.…..”
“No Aymah karki sake cewa komai dan ALLAH. Mu ajiye wannan maganar haka kawai. Ku tashima muje dan ga kamar momy can ta fito”.
Badan Nu'aymah taso ba tai shiru.
A falo kam zaman Adawiya babu jimawa Abba da Yoohan suka shigo falon Omar biye da su. Ɗago kanta tayi da nufin yima Abba sannu idanunta ya sauka akan Yoohan da shi koma kallon inda take baiyi ba. Ganin har zasu wuce batai magana ba Abbah yace, “Adawiya baki iya gaisuwa ba ne? Ko bakiga mijin ƴar uwarkiba Nu'aymah?”.
Da gaske gaban Adawiya sai da ya faɗi. Bakinta na rawa ta gaida Yoohan. Sau ɗaya ya amsa tare da mata kallo ɗaya ya ɗauke kansa. Binsa da kallo kuwa ta cigaba da yi harya shige falon Abbah.
A fili tace, ‘Dama Aymah ba ƙabila akace ta aura ba? Naga kuma balarabe?’. Bata da mai bata wannan amsar dan haka tai shiru tana saƙe-saƙenta a cikin zuciya har Momy ta fito tana tambayarta ihun mi takeji ɗazun. Tana cikin sanar ma Momyn ne su Aymah suka fito. Zuwa Nu'aymah tai ta rungume Momy cike da murna.
Momy dake dariya tace, “Ja'ira, an girma ba'asan an girma ba”.
Dariya ta sakeyi su Amal na taya ta. Adawiya dai tai muƙuy kamar bata falon abin duniya ya gama isarta a rai game da ganin mijin Nu'aymah..
Tura Amal momy tayi ta kira Uwaliya mai aikin da aka kawoma Nu'aymah daga kano. Ashe dama ita suka biyo ɗauka batare da Yoohan ya sanar mata ba. Ba wata tsohuwa bace ba. Zata iya kai kimanin shekaru talatin da bakwai dai. Sun gaisa da Nu'aymah momy tai musu bayanin juna. Har cikin zuciya Aymah taji son zama da Uwaliya kuwa. Dan haka cikin jin daɗi ta miƙe domin zuwa falon Abbah ta gaidashi shima.
Basu bar gidanba sai goma saura. Sun tafi da Uwaliya. Su Amal ma sun mata alƙawarin zuwa next week dan dama Abbah ne ya hanasu wai karsuje su tada mata hankali. Amma yanzu daya ganta babu wata damuwa yace zai barsu suje ɗin amma sai weekend insha ALLAH.
Papa kawai suka samu a harabar gidan zaune. Sai su Solomon da suma ke tasu hirar acan gehe. Ita dai tana gaida papan ciki suka wuce da Uwaliya. Shi kuma ya nufi inda papan yake zaune.
Basu sami kowa a falon ba. Gidan ma shiru alamar duk sun kwanta. Ta fahimci ɗabi'arsu ce barcin wuri, musamman ma yaran saboda makaranta. Da kuma su ɗin kansu daya kasance duk suna fita aiki da safe. Uwaliya nata kalle-kalle ita dai har suka ƙarasa sashensu. Sarai Aymah taga Momy acan ƙofar sashenta zaune. Amma sai tai kamar bata ganta ba suka shige abinsu.
A falo suka yada zango. Kusan zaman mintuna ashirin sai gashi ya shigo tare da su Solomon da suka
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34Chapter 35Chapter 36Chapter 37Chapter 38Chapter 39Chapter 40Chapter 41Chapter 42Chapter 43Chapter 44Chapter 45Chapter 46Chapter 47Chapter 48Chapter 49Chapter 50Chapter 51Chapter 52Chapter 53Chapter 54Chapter 55Chapter 56Chapter 57Chapter 58Chapter 59Chapter 60Chapter 61 Chapter 62Chapter 63Chapter 64Chapter 65Chapter 66Chapter 67Chapter 68Chapter 69Chapter 70Chapter 71Chapter 72Chapter 73Chapter 74Chapter 75Chapter 76Chapter 77Chapter 78Chapter 79Chapter 80Chapter 81Chapter 82Chapter 83Chapter 84Chapter 85Chapter 86Chapter 87Chapter 88Chapter 89Chapter 90Chapter 91Chapter 92Chapter 93Chapter 94Chapter 95Chapter 96Chapter 97Chapter 98Chapter 99Chapter 100Chapter 101Chapter 102