ƴaƴansu.
       Har mota ƙannensa da Momy sukai masa rakkiya, Gebrail ma motar ya shiga zai bisa har airport dan yanason ya tambayi kuɗi a wajensa. Solomon dai nata faman cin maganin da shi Yoohan ɗinma bai san yanayi ba. Sai da motocin suka fice sannan suka koma cikin gidan.

      Hawaye sosai Aymah ta dingayi dan kewar gidace sosai ta dawo mata sabuwa fil. Daga ƙarshe ma sai ta koma gado ta kwanta abinta. Tun tana tunanin mafita akan wannan auren har barci yay awon gaba da ita batare data shirya hakanba.
       Barcin kusan awa guda da rabi tayi kafin ta tashi, koba komai taji sakayau bakamar ɗazunba. Ganin lokacin walha ya wuce sai kawai ta shiga toilet tai uzirinta ta fito. A ranta take ayyanawa bazatai zaman takura kai ba, gara ta fitama ta zagaya gidan kar masu gidan su ɗauka ko tsoronsu takeji su sami nayi a kanta. A falo taci karo da breakfast da Blessing ta kawo mata tun ɗazun. Ta matsa gaban tray ɗin tana buɗe kwanikan. gasashen plantain ne, sai miyar ƙwai da ruwan tea da farfesun kifi. Ba yunwar take jiba. dan haka ta ɗauki gasashshen plantain ɗin guda biyu tasa miya a gefe ta zauna taci, koda ta gama saita ɗauka trayn gaba ɗaya ta fito da shi.
      Tunda ta fara sakkowa daga steps ɗin benan duk suka zuba mata idanu. Babu wanda bai yaba ƙyawunta ba a cikin ransa. Tare da ganin dacewarta da Yoohan ɗin nasu. Miracle ce ta fara jan tsaki tana kauda kanta gefe. Karaf kuwa a idon Aymah dake sakkowa. Wani ɓoyayyen murmushi ta saki a ranta tana ayyana ‘kece zaki fara ɗaukar lesson kenan ƴar lukuta’. A fili kam saita dubi Blessing data hangota tazo wajen da saurin domin amsar tiren hannunta. Yanda Blessing ɗin ta gaidata da girmamawa haka itama ta amsa mata da girmamawa tana miƙa mata tiren..
          Cikin falon ta ƙarasa fuskarta ɗauke da ɗan murmushi, ta zauna a kujerar data rage. Su mama debora ta fara gaidawa, suka amsa mata fuska a ɗaure. Bata damuba ta gaida Momy, ita dai babu yabo babu fallasa ta amsa. Daga haka ta gaida su Momy Favour da suka amsa mata sukam da fara'a, har suna tambayarta ya baƙunta?. ko kallon inda su Joy suke batai ba, sai da su Victoria na gaisheta ne ta amsa musu da kulawa tana tambayarsu ya school?.
       Wani wawan tsoki Miracle ta sake ja tana miƙewa tana wani fifita fuska da hannu alamar wulaƙanci dai.
     Tana zuwa saitin Aymah tasa ƙafa ta taɗeta batare da kowa ya lura da yanda akai ba, sai ganin Miracle sukai a ƙasa wanwar bakinta ya daki gefen centre table aiko ya fashe.............✍

Tofa, mutuniyarku zata fara taro mana world cup a gidan Pastor goshpower😱😣😂.


yanzu haka an kusa kai ƙarhe, gamai buƙata zai iya garzayawa ya biya zafafa kar agama shanye romo babu shi😋😋😋.

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.


No. 49

_____________

_Ina ma’abota karance karance littafin hausa? Wanda ke nishadantar wa ya fadakar? Kana ya tsunduma ku a kogin lobayyar kauna..?_

_*REAL FEEDO* hazikar marubuciyar nan ta zo muku da wani gangariyar littafi mai suna: *BA AMO...!* *BA AMO* wani nazartaccen littafi ne daya zo da wani irin salo na daban..._

_Labarin *BA AMO* ya faru akan wata yarinya da d'an sarkin garin su, yarinyar gidan su gidan yawa ne...Baban su yana auri saki ya tara 'ya'ya da mata da yawa. Tirqashi! To ita yarinya sunan ta KHAIRAT... Tun farko dangin mahaifin su sun tsani mahaifiyar tasu,Bayan ya auro ta, Ta haifi yara mata zallah suna kiran ta da uwar mata kuma kwata-kwata basa kaunar ita da 'ya'yan nata. To ita yarinya ta gama karatun ta.... wato KHAIRAT.. shekarun ta 22 matan gidan nasu suna mata gorin tayi kwantai tak'i aure. Kwatsam wata rana yarinyar ta samu labarin d'an sarkin garin su ya bude sabon company ya fara daukan sabbin ma'aikata, 🧚🏻‍♂️😍cikin ikon Allah ta zuwa ta samu aiki. Ta fara zuwa aikin ta, a karshe su kansu da suka fahimci kwazan ta da nutsuwar ta samu karin matsayi. To a lokacin ne kuma Yarima da PA dinsa suka sami matsala aka kore ta a ma'aikata sai aka daura ita Khairat d'in a matsayin P.A dinsa. Tafiyar tasu batama yi nisa ba! Aka yi makiya suka yi masu sharrin wai karuwar sa ce, har labarin yaje gun mai martaba. Itama Khairat d'in labarin yaje ga mahaifin ta har ya nemi korar ta daga gidan sa, da kyar aka lallashe shi ya hakura.._

_Tab rungutsumi din fa kenan🤮Ya zata kaya ne ga YAREEMAH GA KHAIRAT..a roof d’aya? Ya rabbi😢 labarin kauna yayi.. Amma fa Za’a sha rikici.. Karku manta khairat daga gidan yawa tafito🥺Ga basuda wani hali.. Shin sarki zai yadda da Khairat amatsayin personal assistant din yareemah ko kuwa.? Duk wannan ruguntsumi n REAL FEEDO ce kadai zata iya warware mana.._

_BA AMO::::: (Ba Labari...)_

_DOMIN MALLAKAR NAKI/‘NAKA sai ku baza idanu domin free ne yana nan yana yawo a kowane group_😘😘


___________

No. 49

............Kusan duk falon sai da kowa ya miƙe saboda uban ihun da Miracle ta ƙwallo. Hannunta ɗaya riƙe da baki ɗaya riƙe da ƙafarta data bugi kujera. Duk kanta suka nufa cike da tashin hankali.
       Banda Aymah data wani ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya tamkar ba itace ta aikata tsiyar ba. Cikin mintuna ƙalilan bakin Miracle ya suntume, gashi an ɗagata ta kasa taka ƙafar sai faman ihu take tana kiran Jesus. Tayi yare tayi turanci hawaye shaɓe-shaɓe da fuska.
        Abu kamar wasa sai ga jikin Miracle ya rine da zazzɓi dan harga ALLAH taji faɗuwar musamman data kasance a bazata tazo mata. Gata masha ALLAH tanada jiki. Ko a kwalar rigar Nu'aymah, dan saida ta gama shan ƙamshinta sannan ta ɗan matsa gab da Mira da aka kwantar a doguwar kujera dake kusa da inda Aymah take zaune ana jiran Doctor yazo ya dubata. Da wani salon iskanci tace, “Ayyah Aunty Orrobo sorry yeah, wannan baki haka kamar shantu? Gobe kam ya sake yin tsaki batare da ya tantance inda zaiyi ba”. Babu wanda yaji mita faɗa a maganarta ta ƙarshe bayan sannu da taima Mira. Dan kuwa da hausa tayi, yanda kuma ta kwaɓe fuska sai ka ɗauka duk tausayin Mira ɗinne takeyi.
      A gefe kuma suna ganin Aymah ba wani turancin kirki takeji ba shiyyasa ta ƙarasa sannu wa Miracle ɗin da hausa. Haka suka cigaba da zama har isowar Doctor, ya duba Miracle ɗin sai ga sakamakon targaɗe a ƙafar data buge. Dole yace su shirya a kaita asibiti dan a duba ƙafar da ƙyau, a kuma yimata ɗinki a gefen bakinta da ya shafce.

        Tun bayan wucewar su Miracle da Gebrail da Joy suka tafi rakawa asibiti Aymah ta koma sama dan lokacin sallar zuhur yayi. Dariya ta dinga sheƙawa tunda ta shigo kamar wata zararriya. Sai da tayi mai isarta sannan ta ɗauro alwala tana faɗin, ‘Duk wanda ya shirya match dani ai ya sani nima da shirina nake. Babu ta yanda za'ayi na zauna mushirikai su hau kaina suci tuwo. Wasa kam yanzu aka fara a wanga gida dan na kula basusan wacece Zainabu jikar Hajjo ɗiyar baba malam ba’.
           Sallarta ta gabatar a nutse, tana idarwa ta ɗauki Al-qur'ani ta hau karatu cikin zazzaƙar muryarta. Blessing ce ta shigo kawo mata lunch, sai dai a falo ta ajiye bata shigoba. Ta matso jikin ƙofar danta sanar mata ga abinci nan kunnenta ya jiye mata zazzaƙar muryar Nu'aymah na raira karatun littafi mai tsarki. Tsayawa cak tayi daga yunƙurin knocking ɗin tana sake matsar da kunnenta dan taji sosai. Kamar wasa sai gashi ta share mintuna kusan goma tana saurarenta. Sai da taji tsoron kar wanu ya shigo ya ganta ne sannan tai saurin barin sashen.
      Oho, Aymah batasan tanayiba. Karatunta ta sha na kusan awa ɗaya sannan tai addu'a ta miƙe. Sosai takejin kewar ahalinta, musamman ma Muhammad abokin dambenta. Gudun kar damuwa taima ranta yawa yasa ta fito falon danta ɗanyi ko kallo ne. Sai da ta fara duba abincin da Blessing ta ajiye, duk da taga shinkafa da miya hakan bai sata jin zataci ba. Itafa gaskiya bazata jura cin abincinsu ba. Ya dawo zata faɗa masa ita zatana girkintane kawai. Da wannan tunanin ta maida kulolin ta rufe. Saurarrakin biscuits ɗin data ci ɗazun ta ɗebo. ta dawo cikin kujera ta kunna tv a ranta tana mamakin yanda koda yaushe suke cikin wutar nepa. A maimakon kallon ma sai tai ta Searching tashoshi tana duba masu amfanin da riƙe Numbers ɗinsu a kanta. Hakan ya jata lokaci mai tsayi har aka kira la'asar. Salla taje tayi, ta sake wanka. Tsaf ta fito tana baza ƙamshi ta sauka ƙasa.
       Yanzunma duk a falin ta iskesu an dawo da Mira data sha ɗauri a ƙafa da hannunta data kulje, kunburin bakin kam ya ƙara faɗi dan ya kusa shanye rabin kumatunta. Batare da Nu'aymah ta duba ko inda take ba tacema su Destiny suzo su rakata taga gidan. Harara mama debora ta zuba musu da musu gargaɗi da idanu. Amma duk sai suka maƙe kafaɗa suka miƙe. Tsaf Aymah na lura da komai, dan haka tai murmushi kawai (Mama debo karfa kizama next level🤣lol).
           Suna fita Joy tace, “Yarinyar nan na kula da rawan kai ta shigo gidan nan, wlhy ni sai nagama kamar itace ta sama Mira ƙafa ta faɗi fa?”.
      Gebrail da ya bi Aymah da kallo kamar idanun zasu zubo ƙasa yay saurin waigowa yana duban Joy ɗin. “Hy madam banda ƙarya fa, dan kawai tana rayuwanta kai tsaye sai ace tana rawan kai?. Kufa ɗazun kuke gulman hausawa bagidadawa ne. Sai kuma gashi ita ta ƙaryataku yanzun tunda ta nuna kanta a buɗe yake. Da kun sone ta ƙunshe kanta a ɗaki komi? Mtsoww amebo girl”.
       Zumbur Joy ta miƙe kansa, Momy ta daka musu tsawa. Dan ciwon kai suke neman ƙara mata bayan wanda take ciki. Saboda akan idonta Aymah ta sakama Miracle ƙafa. Amma tai shiru saboda wani dalilinta. Tsaki Joy taja da yima Gebrail alamar zasu haɗune da yatsunta. Shima sai ya ɗage kafaɗa da taɓe baki irin na I don't care ɗin nan.
      Wani irin tafasa zuciyar mira ta ringayi, ga abin faɗa a bakinta amma babu damar cewa. Ita kanta yanzu maganar Joy ta sakata ƙara tariyo a yanda ta faɗin. Tunda tasan lafiyar ALLAH take tafiya babu kuma komai a gabanta. Aiko tabbas saita damalmala kan yarinyar nan bisa tiles ɗin gidan nan bara ta warke dai.
       Su mama debora nata cancana maganar da Joy ta faɗa akan tunanin Aymah ce ta kada Mira. Yayin da su Maman Favour keta ƙoƙarin kare Nu'aymah ɗin akan Joy ɗin ta faɗi dai son zuciyarta ne kawai.
      Oho, Nu'aymah batasan sunayi ba, tana can sunata zagaya lungu da saƙo na gidan ita da su Victoria. A ƙarshe suka yada zango cikin garden ɗin gidan da yay mugun tafiya da tunanin Aymah. Musamman ma swimming pool ɗin da ruwan cikinsa sky Blue da keta ɗaukar idanun mai kallo. Sun ɓata lokaci sosai a garden ɗin, dan har sai da duhun magriba ya fara rufa sannan suka fito.
     Yanzun kam babu kowa a falon kowa ya shige, sai masu aiki biyu maza dake gyarawa. Sashenta tai wucewarta suma su Favour suka nufi ɗakinsu.

___________★★★__________

            A kano kam shiru kakeji babu wani abu daya sake faruwa bayan jin labarin inda su Abdallah suke. Ashe Abdallah saudia yay komawarsa, Naseer kuwa yana anan cikin garin kano sai a yau yazo gidan. Kowa yayi mamakin ganinsa hankali kwance saɓanin yanda sukayi tunanin samunsa.
            Dominma ya ƙara tabbatar musu da hankalin nasa a kwance yake sai da ya shiga kowanne sashe yay musu bangajiyar biki. Da yamma su Abba Musbahu zasu koma Lagos harda shi cikin ƴan rakkiya airport.
     Bayan ya dawo ne shi da malam ƙarami da suka kaisu ya samu gaisawa da baba malam daya shigo. Yanda babu wanda ya tambayesa ina yaje cikin su hajjo haka baba malam ma baice masa komaiba. Sai dai a ƙasan ransa mamakin yanda babu wata damuwa tattare da Naseer ɗin yakeyi. ‘To mi hakan ke nufi?’ ya tambayi kansa acan ƙasan zuciya. babu mai basa amsa, dan haka yaja bakinsa ya tsuke ko Umm baima wannan maganaba. Bai san itama abinda Naseer ɗin yayi yana cikin ranta ba, tayi shiru ne kamar yanda kowa yayi ne kawai itama.

___________★★★★__________

        Lafiya lau Nu'aymah tai barcinta a sashen ita kaɗai batare dajin ko ɗar ba na tsoro. Dan haka sam dama ba ɗabi'arta bace ba kowa ya sani. Abinda kawai yayta cimata rai shine kaɗaici da kewar ahalinta. Gashi bata da ko ƴar waya balle ta kirasu taji koda muryarsu. Sai damuwa akan waɗan nan mutanen gidan data fahimci sam babu mai ƙaunarta a cikinsu. Sai dai kowa da nasa salon kallon data lura yana mata. Yaran nan su Victoria ne kawai babu ruwansu, sai su maman Destiny. Amma har masu aikin gidan tana fahimtar kallon ƙyama da suke binta da shi duk da kuwa duk suna mata gaisuwa da girmamawa. Lallai kuwa dolene ta ɗaura ɗammarar zama mara jin magana, inba hakaba wahala zata sha tunda ta fahimci shi daya ajiyeta bamai zama bane. Yazama lallai kenan itace zataima kanta yaƙi da kanta basai ta jira daga wurinsa ba. Da waɗan nan tunane-tunanen tai barci a wannan daren, hakan yasa washe gari bata fita a sashen nata ba sai bayan sallar zuhur.
       Yau kam babu kowa a falon sai Abraham kawai yana kallon cartoon, yanda yaron bai tanka mata ba haka itama bata kulashi ba tai ficewarta. Kai tsaye garden ta nufa abinta. Shiru wajen babu komai sai kukan tsuntsaye da iska mai daɗi dake kaɗawa. Ta zauna a bakin pool ɗin tare da zira ƙafafunta ciki tana lumshe idanu saboda sanyin ruwan. Haka ta zauna tsahon lokaci a wajen rabin hankalinta duk yana ga tunani, kamar ance ta waiga sai idanunta caraf akan Gebrail da ita kanta batasan adadin lokacin daya ɗauka a wajenba. Kanta ta ɗauke daga dubansa tana sake tsuke fuska. Yayinda shi kuma ya shiga takowa inda take yana wani rangaji irin na gayu marasa jin magana. A mamakinta sai kawai ganinsa tai ya zauna daf da ita shima ya zura ƙafafunsa cikin ruwan.
          Kallonsa tai da wani irin takaici, shiko ya saki murmushi. Kafin ya furta maganar dake bashinsa taja baya ta fidda ƙafafunta tana jan wani shegen tsaki........ Da sauri yace, “Ayya sorry my aunty, i......”
      Wani shegen kallon da tai masa ne ya sakashi haɗiye abinda ke bakinsa. Ta zira takalmanta ta fice daga garden ɗin gaba ɗaya. Ta kula yaron nan yana son shigar mata hanci, to lallai zata fyatoshi kuwa da gaggawa tunda shi ɗan bunsuru ne.
      Gebrail kam da kallo ya bita a wani irin yanayi yana lashe laɓɓansa, harga ALLAH tun ganin Aymah a wajen dinner ya rikice, dan yarinyar da shekarunsa ta dace bawai yayansa ba.

         Takaicin da take ciki na Gebrail yasata ko ganin hanya batayi take tafiya kawai ta bayan garden ɗin. Dan jitai sam batama buƙatar shiga cikin gidan balle ta sake karo da wani takaicin kuma. Cak ta tsaya saboda jin ana magana ƙasa-ƙasa kamar cikin tashin hankali. Tai saurin komawa baya kaɗan ta maƙe jikin rassan flowers ɗin da suka sarƙe wayar garden ɗin. Ƙafafunsu kawai take gani banda fuska saboda karewa da bishiyan ayaba tayi, saboda da turanci suke haɗawa a maganar ya bata damar jin wani abu a ciki.
     Wanda ke maganar yace, “Boss! Nima ganin hoton nan ya matuƙar tadamin hankali, dan bamu saniba koma bashi kaɗai baneba, tunda wannan ma a tsakkiyar file ɗin nan na companyn na samesa”. Cikin tsananin tashin hankali taji wanda aka kira boss ɗin ya fara magana da yare, kafin ya kuma dawo yi da turanci kamar zai haɗiye harshensa. “Tabbas akwai damuwa idan hoton nan ya shiga idon wani, dan zai iya zama silar buɗewar ɓoyayyen sirrina da babu wani mahaluki daya sanshi bayan mutum huɗu, suma ɗin ba komai suka saniba akai sai abinda na sanar musu. SB kayi gaggawar ɓatar da hoton nan, sannan dolene a cikin watannan mubi kaf takardun nan mu bincikesu dama gidan gaba ɗaya, sai mun tabbatar da babu wani makamancin irin wannan hoton sannan hankalina zai kwanta, zan shigo Lagos ɗin nima amma bari sai tafiya mai tsaho ta sam....”. Sai kuma ya sake komawa yin maganar da yare wancan na amsa masa.
       Gani tai ɗaya na takowa alamar zai fito. Tai azamar sake maƙewa a wajen dan taɗau alwashin sai taga kosu ɗin su wanene?.
       Har yayo nisa taji wancan ya tsaidashi, da turanci yace, “Kaga bani hoton nan kar a sami kuskure, zan ƙonashi ni da kaina kawai”. Batare da wancan ɗin yayi musu ba ya miƙa masa yana faɗin, “Okay sir”. Daga haka ya juyo zai fita.
       Da kallo Aymah ta bisa harya ɓacema idanunta, bata sanshiba, dan babushi a cikin duk waɗanda aka nuna mata a cikin gidan. Jin ana takowa za'a fito ya sata sake komawa
Showing 168001 words to 171000 words out of 303604 words