baka san a ina ta sha ba!?
Ga wadda za ku tambaya nan?”
Tayi maganar tana nuna Hudan.
Cikin karkarwar jiki Hudan tace
“Ban san a ina ta sha ba”
Dasauri cikin katseta tace
“Ai tare kuke! Dan haka dole
kinga ta sha wani abun.”
Cikin rashin fahimta Hudan tace
“Ina cikin had’awa Ya Aslam coffe ta zo tace zata sha, sai
na zuba mata a cup
That was the only thing da naga ta sha daganan ta fara tar..........”
Shiruuu, tayi ta kasa k’arasawa sai kuma a rikice ta d’ago tana kallon Mammy wadda ita ma itan take kallo kafin ta matso kusa da ita tace
“Hudan we all know
ba kya k’aunar Aslam!!!
Da kika zo kashe shi kika san kin yi poisioning coffe d’insa! Me ye laifin Ummi da zaki had’a har da ita ki bari ta sha?”
Cikin tsananin tashin hankali Hudan take kallonta zata yi magana Mammyn ta katse ta ta hanyar sake cewa
“Ko jifan tsuntsu biyu kike son yi da dutse d’aya?
Because it’s obvious yanzu babu abunda zai sake shiga tsakanin Maryam da Abba!”
Wani kalar kuka da Hudan take yi sai da ta kusan shid’ewa!
Zata yi magana Mammy ta sake cewa
“Wachche irin zuciya ce da ke Hudan? Na tabbatar idan kika rok’i Aslam kika ce ya sakeki tsaf z........”
Da mugun k’arfi Aslam wanda ya zo iya wuya yace
“Mammy!!!”
Wanda gaba d’ayansu sai da suka razana! Kowa ya d’auke wuta……..
A hankali Abba wanda tun lokacin da Mammy ta fara magana ya runtse idanuwan ya bud’e ya kamo hannun Aslam yace
“Za a iya ganinta ko?”
Sai da ya d’an dedeta kansa tukunna yace
“Eh” ba tare da ya kalleshi ba
dan wani kalar kallon kallo suke yiwa juna shi da Mammy wanda da ace Mammyn ta san kallon da Aslam d’in yake yi mata to daa ba zata yarda ta bar kwayar idanunta a cikin nasa ba.
D’akin da aka shiga da ita sanda aka kawota nan Abba ya shiga dan basu ga lokacin da aka fito da ita ba.
Sai a sannan Mommy ta matso ta jaa hannun Aslam suka fice daga wajen gaba d’aya.
Suna fita Mammy ta sake juyowa kan Hudan a karo na biyu tace
“Yau wallahi mai kwatar ki a hannuna sai Allah,
kin san ya Ummi take a wajena kuwa......”
Banda kallon Mammy ba abunda Mom take yi tana wani irin kuka, so take tayi magana amman ta ma kasa.
Cikin fushi Mammy ta yi kan Huda kamar zata shak’ota.
Damk’ar hannunta d’in da Dad yayi ne ya sa ta juyo tana kallonsa!
Ba tare da ya kalleta ba
ya jaa hannunta da mugun k’arfi ya fita da ita……
Sai da ya sakata a mota ya cewa driver ya maida ta gida tukunna ya juya ya koma ciki ba tare da ya bi takan bak’ak’en maganganun da take jefa mishi ba.
Mammy kamar zata mutu haka ta ji, wato bashi da time d’in da zai yi mata magana sai in zai wulak’antata sannan a gaban mutane ko kuma in ba su kad’ai bane to ya kan kulata.
Gashi yanzu Arshaad shima ya fara, tsabar wulak’anci ga ta ga shi amman iya gaisuwace kawai take shiga tsakaninsu, d’azu taje d’akinsa har sau biyu baya nan
a na ukun kuwa da tayi sa a yana nan tana shiga ya mik’e ya fita ya barta kamar ba uwar da ta tsugunna ta haifesa ba,
bama fa ta san ya dawo ba sai a gidan kawai ta ganshi!
Takaici da b’acin rai kamar ta d’aura hannu aka tayi ta kurma ihu........
A kwance ya ganta da oxygen da wasu na’urori tana janyo numfashi da kyar!
A hankali ya k’arasa wajen ya tsaya a dede kanta yace
“Ummi”
Sai kuma wasu zafafan hawaye suka shiga sintiri a kan kyakkyawar fuskarshi.
A hankali ta shiga bud’e idanunta…
Tun tana ganinsa dishi dishi har ta d’an fara ganinsa sosai
dan haka ta fara k’ok’arin mik’ewa.
Da sauri yace
“Nooo..
Stay still”
Sai kuma ya juya ya janyo wani stool ya zauna a kai ya kama hannunta ya rik’e.
A hankali ta d’an jaa oxygen d’in k’asa, tace
“Naji Likitan yana cewa poision na sha ko?
Wai hanjina sun tsitstsinke.”
A hankali Abba ya kawar da kansa yayi amfani da free hand d’insa ya share hawayen fuskarsa kafin ya juyo yace
“You are going to be okay”
Murmushi ta yi a hankali tace
“K’arya fa ba halin ka bane
Abba”
This time around kuka ne ya kufce masa…
A hankali ya kamo hannunta ya d’ago ya kai setin bakinsa yayi kissing hannun
cikin kuka yace
“Ki yi hak’uri Ummi.
Dan Allah ki yi hak’uri.
Na nuna miki k’iyayya,
ni kaina naji ina jin haushin kaina ballantana ke.”
Murmushi tayi
a hankali tace
“Ko sau d’aya ban tab’a jin haushin abunda kake min ba Abba
remember
tun muna Yara
na sha gaya maka
‘ko menene idan kayi burgeni yake yi’
dan haka kar kayi tunanin na rik’e ka a zuciyata!
Zuciyata iya kar k’aunarka da tsananin son ka ta sani
bata san wani abu akasa sin haka ba”
Ta k’arashe maganar tana d’an murmushi.
Kuka ne sosai ya kufcewa Abba.
A hankali take d’an matsar hannunsa wanda yake rik’e da nata tace
“Good bye Abba,
ka kulamin da su Shuraim dan Allah, har da Hudata itama
ka cigaba da kula min da y’ay’ana.”
Cikin tsananin kuka yace
“Ummi ki yi shiru..
Fad’ar Likita ba fad’ar Ubangiji bace ba. Ki yi shiru da waennan maganganun dan Allah.”
A hankali tace
“Lokacina yayi!
Tun ba yau ba na fara jin hakan a jikina.”
Shiruu ta d’anyi kafin ta lumshe idanunta ta bud’e a hankali tana ganin dishi dishi tace
“Ina takaicin
Ba zaka dinga tunani a matsayin masoyiyarka ba
bayan raina! Sai dai
a matsayin wadda ta sanya rayuwarka a k’unci
ta saka ka tunani da bak’in ciki. Da ace za a bani chance d’in da zan iya komawa farko
to da na fita a rayuwarka kayi farin ciki daga farkonta har k’arshe.”
Cikin katseta yace
“Ummi mun wuce wannan wajen, na fad’a miki
na riga na yafe miki na manta da komai.
Ba zan tab’a tunoki a matsayin wadda ta sanya rayuwata k’unci ba sai a matsayin ki na matata!
Amaryata!
Uwar y’ay’ana!
K’anwata
sannan
masoyiyata
wadda take tsananin so na.”
A hankali ya matso da bakinsa ya d’aura a kan goshinta
yayi kissing yana kuka
ya d’an d’ago yana kallon idonta yace
“I love you, Zainab”
Wasu zafafan hawayene suka shiga zubo mata,
a hankali tace
“Now I’ll have a nice nap!
In sha Allah.
Thank you.”
Kasa ci gaba da zaman yayi dan haka ya mik’e da sauri ya fita a d’akin yana kuka sosai.
Yana fita Hudan Shuraim da Sudais suka shigo.
Tana jin kukan su ta fahimci sune suka shigo
dan zuwa yanzu ba
sosai take gani ba.
A hankali ta bud’e musu hannuwanta alamun su je gareta. Da sauri kuwa suka nufeta suna zuwa tayi hugging d’insu gaba d’aya….
A hankali suka cikata suka matsa gefe suna kuka.
Cikin kuka Huda tace “Ummi wallahi ban san poison bane ba”
A hankali Ummin ta katseta ta hanyar cewa
“Shhh”.
Sai da ta ga ta d’anyi shiru
sannan tace
“Magana d’aya zuwa biyu nake so in gaya muku…
Ku had’a kanku ku so junanku ku rik’e zumunci a duk inda kuke ku rik’e amana
dan Allah
sannan kar ku cuci wani..”
A hankali Granpa ya turo k’ofar ya shigo
Idanuwanshi sun yi jajawur!
Tun lokacin da Gramma ta fad’a mishi ta fito sam sai ya gagara sukuni
shiyasa shima kawai ya yanke shawarar zuwa asibitin. Yana hanya ma lokacin da Aslam ya kira shi ya fad’a mishi abunda Likita yace.
Da kyar ya taka da y’ar sandarshi ya k’arasa bakin gadon.
Inda Abba ya tashi nan ya zauna tukun
a hankali yace
“Ummi”
Juyowa ta yi sanann ta d’an d’ago hannunta tana k’ok’arin kama nasa.
A hankali ya kamo hannun nata da nashi hannayen duka biyu ya rik’e.
Inda su Shuraim suke a tsaye yanzu tun shigowar Granpa ta d’an kalla kafin tace “ku bamu guri”.
Har sun juya za su fita suka ji tace “Allah yayi muku albarka”
Sai da suka juyo gaba d’ayansu tukunna suka ce “Ameen Ummi”
Sannan suka juya suka fita suna wani irin kuka.
A hankali ta maida idonta inda take Jin Granpa tace
“Daddie, dama inada niyyar bada sak’o a baka koda ace baka zo ba.
Na gode kuma naji dad’in zuwanka.
Maganata ta farko
Itace
Godiya!
Kasancewar ka Uncle kuma Uba a gareni
Is one of the luckiest thing da kuma nake alfahari da a rayuwata.
Tun tasowata har kawo yanzu bana jin akwai abunda na tab’a nema na rasa shi, baka
rage ni da komai ba
akoda yaushe k’ok’ari kawai kake yi kaga nayi dariya na samu abunda nake so!
Na gode kwarai Daddie
bana jin aduniyar nan a kwai d’iyar da tayi sa’ar samun uba mai tsananin kaunarta kamar ni.”
Runtse hannunta da yake a cikin nashi hannayen yayi
hawaye ya fara sintiri akan tsohuwar fuskarshi.
A hankali dan muryarta tayi low zuwa yanzu
ta ci gaba da magana
“Sai magana ta biyu
Shawara ce zan baka!
Iyaye da manya suna ganin kamr duk abunda babba yayi shine dai dai
alhalin wasu lokutan wani babban yana yin abunda ko d’an shekara tara ba zai aikata ba saboda ya san ba dede bane ba
amman tsoro da fargabar gayawa wannan babban gaskiya sai a sanya ido ayi shiru a nad’e hannu a koma gefe a taru ayita tafka b’arna!”
Shiruu, ta d’anyi tana k’ok’arin jawo numfashi kafin tace
“Same thing da yake going a estate d’inmu kenan…
Ka yi hak’uri da abunda zan fad’a yanzu
Kai da kanka da hannunka ka hargitsa estate d’innan wanda yanzu abunda ya faru yau yasa na tabbatar da hakan kuma inajin takaicin rashin sanin k’arshen wannan bala’i da musiba da ta shigo mana ko kuma ince muke ciki tsundum ba tare da mun sani ba.
Granpa dan Allah dan Annabi
the first thing da zan rok’eka shine
ka daina nuna bambanci!
Yanzu ni
ba a maganata
amman in baka tashi ka tsaya ka gyara tsagwaran bambancin da kake nunawa a tsakanin Aslam Auwal da Arshaad ba to
akwai matsala babba!.
Bani da tantama bani da shakku akan Aslam akaso ayi poisioning yau ni kuma na sha ba tare da na sani ba!
Ban ce Arshaad ko Auwal bane ba amman dai na san dole a cikin estate d’in mu ne
wanda na tabbatar ata dalilin kyautar gidan da kayi mishi ne
da kuma ragowar abubuwan da kake tayi tun haihuwarshi har kawo yanzu,
sannan ina so ka san
wallahi tallahi ba Huda bace ba”.
Numfashinta da ya fara sark’e wa ne yasa ta yi shiru ta hau kokawar janyowa….
Da sauri Granpa ya mik’e ya fara kiran
“Doctor!!”
Ruk’o hannunshi tayi tace
“One last thing
abunda nake so
abunda idan kayi min zan ji dad’i shine
Granpa dan girman Allah
da manzonsa
ka yi hak’uri ka daure
ka yarda sannan ka taimaka wa Abba ya maida Maryam!
Ka yi accepting d’inta ita da Huda
Dan Allah Granpa
sannan ka tayani neman yafiyar mutum uku
Maryam Aisha da Huda!
Although na san su Maryam sun yafe min
amman Ina buk’atar ka sake nema min yafiyarsu”
Tana gama fad’in haka numfashinta ya fara sama
maganar ma da take son sake yi ta sark’e harshenta ya fara fidda maganar da ba ita ba!
Da sauri Granpa ya sake cewa
“Doctor!!”
Da k’arfi yana zubarda hawaye da k’ok’arin barin wajen amman sai yaji still ta sake rik’e hannunshi tak’i saki.
Juyowa yayi suka had’a ido yaga yadda idanuwanta suke shirin k’afewa tana ta
faman kokawa da numfashinta!
Da sauri ya k’arasa yayi cupping fuskarta
yana kallon idonta yace
“Ashhadu allailaha illallah”
A hankali tace
“Ashhadu allailaha illallah”
Wani kuka ne ya taho mishi yanayi yace
“Wa ashhadu anna muhammadrasulullah”
Cikin jan numfashi da kyar tace
“Wa ashhadu anna muhammadrasulullah”
Dai dai nan Doctor nurse da ragowar ahalin MT gaba d’aya suka shigo d’akin ata dalilin kiran Doctor d’in da Granpa yayi….
Cikin tsananin kuka dan har idanuwanta sun k’afe
yace
“Salllallahu alaihi wa sallam”
A hankali yaji ta maimaita
daga nan dip! Komai nata ya tsaya ta chak! Ta daina k’ok’arin janyo numfashin da take ta faman yi yana wahalar da ita
K’arar naurar da aka jojjona mata shima ya chanja…….
Kifawa Granpa yayi abkanta yana tsananin kukan da rabonshi da yi tun ranar da Yaya da Doctor suka rasu..........
A hankali Likitan ya k’araso ya hau dudduba ta, chaan! Ya
d’ago agogon hannunsa ya duba kafin ya juya ya kalla nurse d’in da suka shigo tare yace mata
“Time of death!
1:30am”.
Kuka gaba d’ayansu suka saka lokaci guda, babu mai lallashin wani.
A hankali nurse d’in tace “su d’an bata guri zata gyarata ta saka mata auduga kar iska ya shiga kafin zuwa gobe tunda ta san dole zatayi kwanan keso”
……………..
A waje suka samu Arshaad da Aslam suna zaune kowa yayi jugum.
Daman tunda suka ji Granpa ya kwala kiran Doctor sun san menene
shiyasa ma suka k’i shiga
yanzu kuma fitowar su kowa yana kuka ya sake tabbatar musu.
Da sauri Aslam ya mik’e ya fice a wajen haka shima Arshaad d’in dan basu san wa za su fara lallashi ba! Kowa ka ganshi kuka yake yi masu hawaye nayi
hatta Granpa ya kasa tsaida hawayensa.
Cikin mintuna 15 nurse d’in ta fito ta mik’a musu kayanta da ta saka a box tace
“An gama.
Saura rufe bill, daga nan
su wuce da ita”
A take Dad ya bita ya gama komai har file
sanann ya dawo suka turata kanainaye cikin farin bedsheet har mota shi da Daddy, su Mommy da Mom suka shigar da ita suna kuka.
Mom ce ta zauna a baya ta d’aura kan ta a kan cinyarta tana wani irin kuka kamar ranta zai fita.
Mommy kuma a gaba Dad yana tuk’i, a haa suka kama hanyar MT..
Aslam shi ya ja su Huda da Shuraim da Abba
Arshaad kuma suka tafi tare da Daddy
Granpa kuma driver d’in da ya kawoshi ya maida shi tare da Gramma.
A hanya Granpa bai bari sun k’arasa ba ya kira Abba yace mishi “dan Allah a wuce da ita estate idan ba damuwa”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
65
Mikiya Writers Association.
Direct side d’in Granpa aka nufa da gawar Ummi.
Kafin zuwa asuba Mommy da Gramma suka yi mata wanka suka shiryata.
Haka nan suka sakata a gaba suka dinga yi mata karatu da tofi tun jiyan dama suke yi
su biyar har Huda Shuraim da Sudais, suna yi suna kuka.
Ana idar da sallah
aka sanar jana’iza k’arfe 9:00am a masallacin estate, daga nan gaba d’ayan su kowa ya nufi side d’in Granpa.
Shiruu! Haka b’angaren ya kasance amman kowa da Al’quraninsa, masu hawaye suna yi suna karatun…..
Har zuwa lokacin da gari ya waye jama’a suka fara taruwa,
mak’ofta da suka ji ana ta lek’awa estate d’in ana gaisuwa, sai k’awayensu da family friends da suka ji ta wayoyi…..
K’arfe tara tana yi mazan suka shigo domin fita da gawar
sai a sannan abun ya dawo sabo! Abun tausayi
especially yadda Huda Shuraim da Sudais suka k’amk’ame gawar suna kuka kamar ransu zai fita!
Da kyar Arshaad ya janye Sudais
Auwal kuma wanda Daddy yaje ya d’auko ba da jimawa ba ya janye Shuraim
Aslam kuma yaja Huda!
Tukunna su Daddy suka saka gawar a makara aka fita da ita waje domin a sallaceta……
K’arfe tara aka gabatar da jana’iza aka mik’a Ummi gidanta na gaskiya.
Ta samu halarta d’umbin jama’a maza da mata
dan kamar yadda mak’abarta ta cika haka ma cikin estate d’in.
Suna dawowa Granpa ya cewa Abba “Su zauna anan (estate d’in) ayi zaman makoki
ba sai sun koma chan gidansu ba......
Washegari,
Sumayya Ummu da Baban su Sakina suka zo suka yi ma Huda da Abba gaisuwa.
Ranar sadakar uku,
Huda tana d’akin Gramma dan a nan take ita da su Shuraim
ta ji wayarta tana k’ara!
Tana d’auka Auwal yace
“Ta yi bak’o yana waje a bakin estate, wai ya zo mata gaisuwa, yace ‘sunan shi
Junaidu’ Ta sanshi
a barshi ya shigo?”.
Bata san lokacin da ta diro daga kan gadon ba
tace
“Eh Ya Auwal na sanshi sosai yayana ne!
A barshi ya shigo.”
Daga nan ta zari hijabinta
ta yi waje tana adduar Allah yasa Ya Junaidun ne da gaske.
Bata samesu a compound d’in Granpa ba daman bata yi expecting hakan ba!
Dan haka ta fice daga gidan
ta nufi tsakiyar main compound na estate d’in.
A inda ake parking motoci ta hango Auwal sanye cikin bak’ar jallabiya fuskarsa tayi fayau! Idanuwansa da suka ci kuka sun yi jaa sun k’ank’ance
yayi tsananin rama sannan kana ganinshi ka san bashi da lafiya….
A tsaye tare da wani ya juya baya sanye cikin shadda fara d’inkin boda da bak’ar hula
ya jingina a jikin booth d’in wata bak’ar mota Jeep!
Yanayin takalmi da shadda da kuma hular kansa kad’ai sun isa su sa ka san cewa kud’i sun zauna…
Da Auwal suka fara had’a ido
yana shirin yin magana
a hankali yaji tace
“Ya Junaidu”
Shiruu yayi da maganar da yake yi kafin ya gyara tsayuwarshi daga nan kuma ya juyo gaba d’ayanshi yana murmushi…..
Kusan daskarewa Huda tayi,
a hankali hawaye na gangarowa akan kumatunta ta ce
“Ya junaidu”
Murmushi yayi yace
“Na’am Huda”
Cikin share hawayenta tace
“Where have you been? Yaushe ka dawo?
Me ya faru?
How have you been..”
Murmushi ya saki mai d’an had’a da dariya kafin ya shafa k’asumbar da ya tara tayi mishi tsananin kyau yace
“Ya muka ji da hak’uri?”
A hankali ta sunkuyar da kanta tace “Alhamdulillah”
Cikin sanyin murya.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace
“Allah ya ji k’anta yasa chan tafi nan”
A hankali ita da Auwal suka ce “Ameen”
Kafin Auwal d’in ya juya ya yi mishi sallama ya wuce.
Gyara tsayuwarshi yayi yana kallonta kafin yace
“How are you?.”
Congratulations
you have finally found your Dad”
Jijjiga kai tayi sanann tace “Thank you”
Tana mai d’ago da kanta sannan ta sake jeho mishi tambayar
“Where have you been?”
Dede nan Arshaad wanda dawowar sa kenan daga airport d’auko Aaima suka k’araso wajen shi da Aaima.
Murmushi Junaidu yayi kafin yace “Arshaad!”
Da sauri Huda ta juya dan ita bama taga tahowarsu ba.
A hankali ta k’arasa inda Aaima take ta rik’e mata hannu tana kallonta kafin ta yi hugging d’inta.
Bata iya ce mata komaiba
Har ta cika ta ta d’ago.
Ahankali Aaima da muryarta ta d’an dishe tsabar kuka tace
“Ya hak’urin mu?”
“Alhamdulillah” Huda tace
Daga nan Aaima ta d’an d’ago ta kalli Junaidu wanda
ya kafe Arshaad da ido
tace
“Ina wuni”
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya juyo ya kalleta a hankali
Showing 45001 words to 48000 words out of 100703 words
Ga wadda za ku tambaya nan?”
Tayi maganar tana nuna Hudan.
Cikin karkarwar jiki Hudan tace
“Ban san a ina ta sha ba”
Dasauri cikin katseta tace
“Ai tare kuke! Dan haka dole
kinga ta sha wani abun.”
Cikin rashin fahimta Hudan tace
“Ina cikin had’awa Ya Aslam coffe ta zo tace zata sha, sai
na zuba mata a cup
That was the only thing da naga ta sha daganan ta fara tar..........”
Shiruuu, tayi ta kasa k’arasawa sai kuma a rikice ta d’ago tana kallon Mammy wadda ita ma itan take kallo kafin ta matso kusa da ita tace
“Hudan we all know
ba kya k’aunar Aslam!!!
Da kika zo kashe shi kika san kin yi poisioning coffe d’insa! Me ye laifin Ummi da zaki had’a har da ita ki bari ta sha?”
Cikin tsananin tashin hankali Hudan take kallonta zata yi magana Mammyn ta katse ta ta hanyar sake cewa
“Ko jifan tsuntsu biyu kike son yi da dutse d’aya?
Because it’s obvious yanzu babu abunda zai sake shiga tsakanin Maryam da Abba!”
Wani kalar kuka da Hudan take yi sai da ta kusan shid’ewa!
Zata yi magana Mammy ta sake cewa
“Wachche irin zuciya ce da ke Hudan? Na tabbatar idan kika rok’i Aslam kika ce ya sakeki tsaf z........”
Da mugun k’arfi Aslam wanda ya zo iya wuya yace
“Mammy!!!”
Wanda gaba d’ayansu sai da suka razana! Kowa ya d’auke wuta……..
A hankali Abba wanda tun lokacin da Mammy ta fara magana ya runtse idanuwan ya bud’e ya kamo hannun Aslam yace
“Za a iya ganinta ko?”
Sai da ya d’an dedeta kansa tukunna yace
“Eh” ba tare da ya kalleshi ba
dan wani kalar kallon kallo suke yiwa juna shi da Mammy wanda da ace Mammyn ta san kallon da Aslam d’in yake yi mata to daa ba zata yarda ta bar kwayar idanunta a cikin nasa ba.
D’akin da aka shiga da ita sanda aka kawota nan Abba ya shiga dan basu ga lokacin da aka fito da ita ba.
Sai a sannan Mommy ta matso ta jaa hannun Aslam suka fice daga wajen gaba d’aya.
Suna fita Mammy ta sake juyowa kan Hudan a karo na biyu tace
“Yau wallahi mai kwatar ki a hannuna sai Allah,
kin san ya Ummi take a wajena kuwa......”
Banda kallon Mammy ba abunda Mom take yi tana wani irin kuka, so take tayi magana amman ta ma kasa.
Cikin fushi Mammy ta yi kan Huda kamar zata shak’ota.
Damk’ar hannunta d’in da Dad yayi ne ya sa ta juyo tana kallonsa!
Ba tare da ya kalleta ba
ya jaa hannunta da mugun k’arfi ya fita da ita……
Sai da ya sakata a mota ya cewa driver ya maida ta gida tukunna ya juya ya koma ciki ba tare da ya bi takan bak’ak’en maganganun da take jefa mishi ba.
Mammy kamar zata mutu haka ta ji, wato bashi da time d’in da zai yi mata magana sai in zai wulak’antata sannan a gaban mutane ko kuma in ba su kad’ai bane to ya kan kulata.
Gashi yanzu Arshaad shima ya fara, tsabar wulak’anci ga ta ga shi amman iya gaisuwace kawai take shiga tsakaninsu, d’azu taje d’akinsa har sau biyu baya nan
a na ukun kuwa da tayi sa a yana nan tana shiga ya mik’e ya fita ya barta kamar ba uwar da ta tsugunna ta haifesa ba,
bama fa ta san ya dawo ba sai a gidan kawai ta ganshi!
Takaici da b’acin rai kamar ta d’aura hannu aka tayi ta kurma ihu........
A kwance ya ganta da oxygen da wasu na’urori tana janyo numfashi da kyar!
A hankali ya k’arasa wajen ya tsaya a dede kanta yace
“Ummi”
Sai kuma wasu zafafan hawaye suka shiga sintiri a kan kyakkyawar fuskarshi.
A hankali ta shiga bud’e idanunta…
Tun tana ganinsa dishi dishi har ta d’an fara ganinsa sosai
dan haka ta fara k’ok’arin mik’ewa.
Da sauri yace
“Nooo..
Stay still”
Sai kuma ya juya ya janyo wani stool ya zauna a kai ya kama hannunta ya rik’e.
A hankali ta d’an jaa oxygen d’in k’asa, tace
“Naji Likitan yana cewa poision na sha ko?
Wai hanjina sun tsitstsinke.”
A hankali Abba ya kawar da kansa yayi amfani da free hand d’insa ya share hawayen fuskarsa kafin ya juyo yace
“You are going to be okay”
Murmushi ta yi a hankali tace
“K’arya fa ba halin ka bane
Abba”
This time around kuka ne ya kufce masa…
A hankali ya kamo hannunta ya d’ago ya kai setin bakinsa yayi kissing hannun
cikin kuka yace
“Ki yi hak’uri Ummi.
Dan Allah ki yi hak’uri.
Na nuna miki k’iyayya,
ni kaina naji ina jin haushin kaina ballantana ke.”
Murmushi tayi
a hankali tace
“Ko sau d’aya ban tab’a jin haushin abunda kake min ba Abba
remember
tun muna Yara
na sha gaya maka
‘ko menene idan kayi burgeni yake yi’
dan haka kar kayi tunanin na rik’e ka a zuciyata!
Zuciyata iya kar k’aunarka da tsananin son ka ta sani
bata san wani abu akasa sin haka ba”
Ta k’arashe maganar tana d’an murmushi.
Kuka ne sosai ya kufcewa Abba.
A hankali take d’an matsar hannunsa wanda yake rik’e da nata tace
“Good bye Abba,
ka kulamin da su Shuraim dan Allah, har da Hudata itama
ka cigaba da kula min da y’ay’ana.”
Cikin tsananin kuka yace
“Ummi ki yi shiru..
Fad’ar Likita ba fad’ar Ubangiji bace ba. Ki yi shiru da waennan maganganun dan Allah.”
A hankali tace
“Lokacina yayi!
Tun ba yau ba na fara jin hakan a jikina.”
Shiruu ta d’anyi kafin ta lumshe idanunta ta bud’e a hankali tana ganin dishi dishi tace
“Ina takaicin
Ba zaka dinga tunani a matsayin masoyiyarka ba
bayan raina! Sai dai
a matsayin wadda ta sanya rayuwarka a k’unci
ta saka ka tunani da bak’in ciki. Da ace za a bani chance d’in da zan iya komawa farko
to da na fita a rayuwarka kayi farin ciki daga farkonta har k’arshe.”
Cikin katseta yace
“Ummi mun wuce wannan wajen, na fad’a miki
na riga na yafe miki na manta da komai.
Ba zan tab’a tunoki a matsayin wadda ta sanya rayuwata k’unci ba sai a matsayin ki na matata!
Amaryata!
Uwar y’ay’ana!
K’anwata
sannan
masoyiyata
wadda take tsananin so na.”
A hankali ya matso da bakinsa ya d’aura a kan goshinta
yayi kissing yana kuka
ya d’an d’ago yana kallon idonta yace
“I love you, Zainab”
Wasu zafafan hawayene suka shiga zubo mata,
a hankali tace
“Now I’ll have a nice nap!
In sha Allah.
Thank you.”
Kasa ci gaba da zaman yayi dan haka ya mik’e da sauri ya fita a d’akin yana kuka sosai.
Yana fita Hudan Shuraim da Sudais suka shigo.
Tana jin kukan su ta fahimci sune suka shigo
dan zuwa yanzu ba
sosai take gani ba.
A hankali ta bud’e musu hannuwanta alamun su je gareta. Da sauri kuwa suka nufeta suna zuwa tayi hugging d’insu gaba d’aya….
A hankali suka cikata suka matsa gefe suna kuka.
Cikin kuka Huda tace “Ummi wallahi ban san poison bane ba”
A hankali Ummin ta katseta ta hanyar cewa
“Shhh”.
Sai da ta ga ta d’anyi shiru
sannan tace
“Magana d’aya zuwa biyu nake so in gaya muku…
Ku had’a kanku ku so junanku ku rik’e zumunci a duk inda kuke ku rik’e amana
dan Allah
sannan kar ku cuci wani..”
A hankali Granpa ya turo k’ofar ya shigo
Idanuwanshi sun yi jajawur!
Tun lokacin da Gramma ta fad’a mishi ta fito sam sai ya gagara sukuni
shiyasa shima kawai ya yanke shawarar zuwa asibitin. Yana hanya ma lokacin da Aslam ya kira shi ya fad’a mishi abunda Likita yace.
Da kyar ya taka da y’ar sandarshi ya k’arasa bakin gadon.
Inda Abba ya tashi nan ya zauna tukun
a hankali yace
“Ummi”
Juyowa ta yi sanann ta d’an d’ago hannunta tana k’ok’arin kama nasa.
A hankali ya kamo hannun nata da nashi hannayen duka biyu ya rik’e.
Inda su Shuraim suke a tsaye yanzu tun shigowar Granpa ta d’an kalla kafin tace “ku bamu guri”.
Har sun juya za su fita suka ji tace “Allah yayi muku albarka”
Sai da suka juyo gaba d’ayansu tukunna suka ce “Ameen Ummi”
Sannan suka juya suka fita suna wani irin kuka.
A hankali ta maida idonta inda take Jin Granpa tace
“Daddie, dama inada niyyar bada sak’o a baka koda ace baka zo ba.
Na gode kuma naji dad’in zuwanka.
Maganata ta farko
Itace
Godiya!
Kasancewar ka Uncle kuma Uba a gareni
Is one of the luckiest thing da kuma nake alfahari da a rayuwata.
Tun tasowata har kawo yanzu bana jin akwai abunda na tab’a nema na rasa shi, baka
rage ni da komai ba
akoda yaushe k’ok’ari kawai kake yi kaga nayi dariya na samu abunda nake so!
Na gode kwarai Daddie
bana jin aduniyar nan a kwai d’iyar da tayi sa’ar samun uba mai tsananin kaunarta kamar ni.”
Runtse hannunta da yake a cikin nashi hannayen yayi
hawaye ya fara sintiri akan tsohuwar fuskarshi.
A hankali dan muryarta tayi low zuwa yanzu
ta ci gaba da magana
“Sai magana ta biyu
Shawara ce zan baka!
Iyaye da manya suna ganin kamr duk abunda babba yayi shine dai dai
alhalin wasu lokutan wani babban yana yin abunda ko d’an shekara tara ba zai aikata ba saboda ya san ba dede bane ba
amman tsoro da fargabar gayawa wannan babban gaskiya sai a sanya ido ayi shiru a nad’e hannu a koma gefe a taru ayita tafka b’arna!”
Shiruu, ta d’anyi tana k’ok’arin jawo numfashi kafin tace
“Same thing da yake going a estate d’inmu kenan…
Ka yi hak’uri da abunda zan fad’a yanzu
Kai da kanka da hannunka ka hargitsa estate d’innan wanda yanzu abunda ya faru yau yasa na tabbatar da hakan kuma inajin takaicin rashin sanin k’arshen wannan bala’i da musiba da ta shigo mana ko kuma ince muke ciki tsundum ba tare da mun sani ba.
Granpa dan Allah dan Annabi
the first thing da zan rok’eka shine
ka daina nuna bambanci!
Yanzu ni
ba a maganata
amman in baka tashi ka tsaya ka gyara tsagwaran bambancin da kake nunawa a tsakanin Aslam Auwal da Arshaad ba to
akwai matsala babba!.
Bani da tantama bani da shakku akan Aslam akaso ayi poisioning yau ni kuma na sha ba tare da na sani ba!
Ban ce Arshaad ko Auwal bane ba amman dai na san dole a cikin estate d’in mu ne
wanda na tabbatar ata dalilin kyautar gidan da kayi mishi ne
da kuma ragowar abubuwan da kake tayi tun haihuwarshi har kawo yanzu,
sannan ina so ka san
wallahi tallahi ba Huda bace ba”.
Numfashinta da ya fara sark’e wa ne yasa ta yi shiru ta hau kokawar janyowa….
Da sauri Granpa ya mik’e ya fara kiran
“Doctor!!”
Ruk’o hannunshi tayi tace
“One last thing
abunda nake so
abunda idan kayi min zan ji dad’i shine
Granpa dan girman Allah
da manzonsa
ka yi hak’uri ka daure
ka yarda sannan ka taimaka wa Abba ya maida Maryam!
Ka yi accepting d’inta ita da Huda
Dan Allah Granpa
sannan ka tayani neman yafiyar mutum uku
Maryam Aisha da Huda!
Although na san su Maryam sun yafe min
amman Ina buk’atar ka sake nema min yafiyarsu”
Tana gama fad’in haka numfashinta ya fara sama
maganar ma da take son sake yi ta sark’e harshenta ya fara fidda maganar da ba ita ba!
Da sauri Granpa ya sake cewa
“Doctor!!”
Da k’arfi yana zubarda hawaye da k’ok’arin barin wajen amman sai yaji still ta sake rik’e hannunshi tak’i saki.
Juyowa yayi suka had’a ido yaga yadda idanuwanta suke shirin k’afewa tana ta
faman kokawa da numfashinta!
Da sauri ya k’arasa yayi cupping fuskarta
yana kallon idonta yace
“Ashhadu allailaha illallah”
A hankali tace
“Ashhadu allailaha illallah”
Wani kuka ne ya taho mishi yanayi yace
“Wa ashhadu anna muhammadrasulullah”
Cikin jan numfashi da kyar tace
“Wa ashhadu anna muhammadrasulullah”
Dai dai nan Doctor nurse da ragowar ahalin MT gaba d’aya suka shigo d’akin ata dalilin kiran Doctor d’in da Granpa yayi….
Cikin tsananin kuka dan har idanuwanta sun k’afe
yace
“Salllallahu alaihi wa sallam”
A hankali yaji ta maimaita
daga nan dip! Komai nata ya tsaya ta chak! Ta daina k’ok’arin janyo numfashin da take ta faman yi yana wahalar da ita
K’arar naurar da aka jojjona mata shima ya chanja…….
Kifawa Granpa yayi abkanta yana tsananin kukan da rabonshi da yi tun ranar da Yaya da Doctor suka rasu..........
A hankali Likitan ya k’araso ya hau dudduba ta, chaan! Ya
d’ago agogon hannunsa ya duba kafin ya juya ya kalla nurse d’in da suka shigo tare yace mata
“Time of death!
1:30am”.
Kuka gaba d’ayansu suka saka lokaci guda, babu mai lallashin wani.
A hankali nurse d’in tace “su d’an bata guri zata gyarata ta saka mata auduga kar iska ya shiga kafin zuwa gobe tunda ta san dole zatayi kwanan keso”
……………..
A waje suka samu Arshaad da Aslam suna zaune kowa yayi jugum.
Daman tunda suka ji Granpa ya kwala kiran Doctor sun san menene
shiyasa ma suka k’i shiga
yanzu kuma fitowar su kowa yana kuka ya sake tabbatar musu.
Da sauri Aslam ya mik’e ya fice a wajen haka shima Arshaad d’in dan basu san wa za su fara lallashi ba! Kowa ka ganshi kuka yake yi masu hawaye nayi
hatta Granpa ya kasa tsaida hawayensa.
Cikin mintuna 15 nurse d’in ta fito ta mik’a musu kayanta da ta saka a box tace
“An gama.
Saura rufe bill, daga nan
su wuce da ita”
A take Dad ya bita ya gama komai har file
sanann ya dawo suka turata kanainaye cikin farin bedsheet har mota shi da Daddy, su Mommy da Mom suka shigar da ita suna kuka.
Mom ce ta zauna a baya ta d’aura kan ta a kan cinyarta tana wani irin kuka kamar ranta zai fita.
Mommy kuma a gaba Dad yana tuk’i, a haa suka kama hanyar MT..
Aslam shi ya ja su Huda da Shuraim da Abba
Arshaad kuma suka tafi tare da Daddy
Granpa kuma driver d’in da ya kawoshi ya maida shi tare da Gramma.
A hanya Granpa bai bari sun k’arasa ba ya kira Abba yace mishi “dan Allah a wuce da ita estate idan ba damuwa”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
65
Mikiya Writers Association.
Direct side d’in Granpa aka nufa da gawar Ummi.
Kafin zuwa asuba Mommy da Gramma suka yi mata wanka suka shiryata.
Haka nan suka sakata a gaba suka dinga yi mata karatu da tofi tun jiyan dama suke yi
su biyar har Huda Shuraim da Sudais, suna yi suna kuka.
Ana idar da sallah
aka sanar jana’iza k’arfe 9:00am a masallacin estate, daga nan gaba d’ayan su kowa ya nufi side d’in Granpa.
Shiruu! Haka b’angaren ya kasance amman kowa da Al’quraninsa, masu hawaye suna yi suna karatun…..
Har zuwa lokacin da gari ya waye jama’a suka fara taruwa,
mak’ofta da suka ji ana ta lek’awa estate d’in ana gaisuwa, sai k’awayensu da family friends da suka ji ta wayoyi…..
K’arfe tara tana yi mazan suka shigo domin fita da gawar
sai a sannan abun ya dawo sabo! Abun tausayi
especially yadda Huda Shuraim da Sudais suka k’amk’ame gawar suna kuka kamar ransu zai fita!
Da kyar Arshaad ya janye Sudais
Auwal kuma wanda Daddy yaje ya d’auko ba da jimawa ba ya janye Shuraim
Aslam kuma yaja Huda!
Tukunna su Daddy suka saka gawar a makara aka fita da ita waje domin a sallaceta……
K’arfe tara aka gabatar da jana’iza aka mik’a Ummi gidanta na gaskiya.
Ta samu halarta d’umbin jama’a maza da mata
dan kamar yadda mak’abarta ta cika haka ma cikin estate d’in.
Suna dawowa Granpa ya cewa Abba “Su zauna anan (estate d’in) ayi zaman makoki
ba sai sun koma chan gidansu ba......
Washegari,
Sumayya Ummu da Baban su Sakina suka zo suka yi ma Huda da Abba gaisuwa.
Ranar sadakar uku,
Huda tana d’akin Gramma dan a nan take ita da su Shuraim
ta ji wayarta tana k’ara!
Tana d’auka Auwal yace
“Ta yi bak’o yana waje a bakin estate, wai ya zo mata gaisuwa, yace ‘sunan shi
Junaidu’ Ta sanshi
a barshi ya shigo?”.
Bata san lokacin da ta diro daga kan gadon ba
tace
“Eh Ya Auwal na sanshi sosai yayana ne!
A barshi ya shigo.”
Daga nan ta zari hijabinta
ta yi waje tana adduar Allah yasa Ya Junaidun ne da gaske.
Bata samesu a compound d’in Granpa ba daman bata yi expecting hakan ba!
Dan haka ta fice daga gidan
ta nufi tsakiyar main compound na estate d’in.
A inda ake parking motoci ta hango Auwal sanye cikin bak’ar jallabiya fuskarsa tayi fayau! Idanuwansa da suka ci kuka sun yi jaa sun k’ank’ance
yayi tsananin rama sannan kana ganinshi ka san bashi da lafiya….
A tsaye tare da wani ya juya baya sanye cikin shadda fara d’inkin boda da bak’ar hula
ya jingina a jikin booth d’in wata bak’ar mota Jeep!
Yanayin takalmi da shadda da kuma hular kansa kad’ai sun isa su sa ka san cewa kud’i sun zauna…
Da Auwal suka fara had’a ido
yana shirin yin magana
a hankali yaji tace
“Ya Junaidu”
Shiruu yayi da maganar da yake yi kafin ya gyara tsayuwarshi daga nan kuma ya juyo gaba d’ayanshi yana murmushi…..
Kusan daskarewa Huda tayi,
a hankali hawaye na gangarowa akan kumatunta ta ce
“Ya junaidu”
Murmushi yayi yace
“Na’am Huda”
Cikin share hawayenta tace
“Where have you been? Yaushe ka dawo?
Me ya faru?
How have you been..”
Murmushi ya saki mai d’an had’a da dariya kafin ya shafa k’asumbar da ya tara tayi mishi tsananin kyau yace
“Ya muka ji da hak’uri?”
A hankali ta sunkuyar da kanta tace “Alhamdulillah”
Cikin sanyin murya.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace
“Allah ya ji k’anta yasa chan tafi nan”
A hankali ita da Auwal suka ce “Ameen”
Kafin Auwal d’in ya juya ya yi mishi sallama ya wuce.
Gyara tsayuwarshi yayi yana kallonta kafin yace
“How are you?.”
Congratulations
you have finally found your Dad”
Jijjiga kai tayi sanann tace “Thank you”
Tana mai d’ago da kanta sannan ta sake jeho mishi tambayar
“Where have you been?”
Dede nan Arshaad wanda dawowar sa kenan daga airport d’auko Aaima suka k’araso wajen shi da Aaima.
Murmushi Junaidu yayi kafin yace “Arshaad!”
Da sauri Huda ta juya dan ita bama taga tahowarsu ba.
A hankali ta k’arasa inda Aaima take ta rik’e mata hannu tana kallonta kafin ta yi hugging d’inta.
Bata iya ce mata komaiba
Har ta cika ta ta d’ago.
Ahankali Aaima da muryarta ta d’an dishe tsabar kuka tace
“Ya hak’urin mu?”
“Alhamdulillah” Huda tace
Daga nan Aaima ta d’an d’ago ta kalli Junaidu wanda
ya kafe Arshaad da ido
tace
“Ina wuni”
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya juyo ya kalleta a hankali
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6Chapter 7Chapter 8Chapter 9Chapter 10Chapter 11Chapter 12Chapter 13Chapter 14Chapter 15Chapter 16 Chapter 17Chapter 18Chapter 19Chapter 20Chapter 21Chapter 22Chapter 23Chapter 24Chapter 25Chapter 26Chapter 27Chapter 28Chapter 29Chapter 30Chapter 31Chapter 32Chapter 33Chapter 34