to tace , tana ninke takardar fita suka yi jikin su a sanyaye da sauri mukhtar ya kulle kofar ya dawo ya zauna yace '' asim wannan wanne irin cin mutunci ne yar aiki ka ɗauke ta kenan ma?.'''
ASIM cikin halin ko in kula yace '' to bayan wannan wanne amfani za tayi min aikin ma dana bata share share ne da goge goge karta sake ƙafafuwan ta su shiga hanyar kitchen din mu.''
Hmmmm wallahi akwai ranar da zan maimaita maka wannan maganar asim ba'a raina mace ko wacce da irin baiwar da Allah ya bata karka zo kana neman hanyar da zata amince dakai nace maka nima ban san hanyar ba.
Cewar mukhtar.
ASIM yace '' wa Ni...? Allah ya kiyaye gaskiya mukhtar ka cuce ni me zanyi da wannan kwailar wallahi har ka saka zuciya'ta tana tashi ni na haɗa gado da wannan nace na haɗa gado da wa ?.''
mukhtar yace '' kayi nisa baka jin kira wallahi, amma lokaci yana nan zuwa inshallahu da za kayi amai ka lashe zancen ka , bana fatan ku rabu da mardiyya fata nake naga har jikokin ku.''
ASIM dogon tsaki yaja ya ci gaba da aikin da yake gaban sa.
wannan kenan
aginɗin wata bishiya ta zauna domin tafiya ma , ta ƙasa yin ta , zama tayi tana sauke numfashi tace '' SUHAILA gaskiya bazan iya ba , cimin mutunci zai ɗinga yi yana hulakanta ni, bani da wani gata yan uwana ba anan suke ba shekara uku fa ba kwana uku bace ba..?.''
dan Allah mardiyya ki tashi ki dena wannan zance wallahi ba ayi namijin da zai hulakan ki ba inhar ina raina, ki kyale sa ba sai kin shiga sabgar sa ba , sannan zai hulakan'ta ki ba
Cewar suhailah.
tashi tayi tana dafa ta da sauri mardiyya ta rufe idon ta sakamakon motar afiyaah da ta , tawo a guje ta fallatsa musu ruwan , da ya kwanta a gurin da suke a hankali ta buɗe idon ta kayan ta duk ya ɓaci haka kayan suhaila afiyaah ganin basu gane wace tayi musu wannan aikin ba dawowa tayi ta tsaya tare da zuge bakin glass ɗin motar ta , tace '' talakawan banza ku da kusan a kafa kuke yawo, kuka fara faɗa dani..?'' nonsense.''
Mardiyya da zuciyar ta , ta kawo har wuya bata san lokacin da ta dauki dutsai ba ta buga a glass din motar afiyaah wucewa yayi ya sauka akan goshin ta anan danan jini ya balle glsss din gaban motar ta ya gashe domin dutsai da ta dauko ba ƙarami bane.
Ihuuuuuuuuuu afiyaah ta saki tare da rufe bakin ta domin tuni bakin ta ya kumbura , har ta leɓen ta sai da ya fashe.
da sauri mardiyya ta fita a guje haka ma suhaila sai dai kafin suyi wani yunkuri security sun riƙe su, Abdulwahab da yake kusa da gurin da sauri ya ƙara so yana cewa maza ku kai su gurin police.
da yake akwai police station a cikin makarantar.
mardiyya da ranta ya ɓaci ta ture hannun mutumin da ya riƙe ta , tace '' cika ni da kaina zan kai kana?.''
cikin tsawa abdulrazak yace '' wato ke ce mara kunyar ko to za kici ubanki yau za mu nuna miki shegen birni yafi na ƙauye.''
AFIYAH fitowa tayi dakyar da sauri Abdulwahab ya riƙe ta yana cewa duk ɓarnar da sukai miki sai sun biya ki bara na kai ki asibiti.
kai kurum ta gyaɗa masa domin bata da bakin magana.
riƙe hannun ta yayi suka shiga cikin motar sa mardiyya da suhaila security suka tisa ƙ'esar su, suna tafiya da sauri mukhtar da yake kokarin buɗe motar sa yace '' officer me yake faruwa ne...?.''
Bala officer yace '' wa'yannan da kake gani yan ta'addane tsagerun makarantar nan yau to kashin su ya bushe barin wannan mara kunyar wata suka fasawa kai.''
da sauri mukhtar ya rufe motar sa yace '' subhanallahi suhaila me ya saka kukai wannan gangancin...?.''
SUHAILA tace '' wallahi tun a office din doctor take ci mana mutunci, yanzu muna tsaye nida mardiyya ta fallatsa ruwa kuma ta faɗa magana bakaken maganganu shi ne ran mardiyya ya ɓace ta jefa mata dutsai wallahi itama da tasan haka zata faru ba za ta jefa mata dutsai ba..''
Suhaila ta ƙarashe maganar ta , tana matsar kwallah.
Mardiyya kuwa ban da dana sani ba abin da take yi mukhtar yace '' a OFFICE din asim kuka haɗu?.''
Kai mardiyya ta ɗaga mai mukhtar yace '' office ka sake su wannan da kake gani bata da kirki halin tane wallahi duk abin da aka ce min zata aikata, haushi taji dan yaji asim zai aure shine ta huce akan su.''
Hadi yace '' gaskiya malam mukhtar ba za mu iya sakin su ba domin iya Abdulwahab ya san wannan maganar yana tafi kai ta asibiti amma idan zaka biyo mu ka biya duk abin da ya kashe mata shikkenan idan ta hakura a kashe case din idan bata hakura ba mi hukunta su, Saboda da hukuma a cikin makarantar nan , duk girman mutum duk ɗaurin gindin mutum idan aka kawo mana kar'ar sa zamu hukunta shi dai-dai da abin da ya aikata.''
okay muje mukhtar ya faɗa yana zaro wayar sa a aljihu, number asim ya lalubo ya dannawa asim kira har ta katsai be kira ba mai da wayar aljihu yayi ya bi bayan su.
har office din yan sanda ya bisu a bayan kan'ta suka zuba su mardiyya sai a lokacin kuka ya subbuce mata bata da gata sai Allah bata da madogara sai Allah yau ita ce a hannun hukumar makaranta , mukhtar a waje suka ce ya tsaya.
Wani dan sanda ne yace '' kunga wannan duk ba abin tashin hankali bane inhar zaku iya fansar kanku ai shikkenan kuna mata ku bari kanku ya kulle musamman ma ke yar fillo komai yaji ya ƙarashe maganar sa yana lasar bakin sa.
da sauri mardiyya ta ɗago kwata kwata bata gane yaren sa ba suhaila tace '' auzubillahi muna neman tsari da wannan bakar rayuwar wallahi idan baka iya bakin ka ba sai mun tona maka asiri mun maka kama da yan iska?.''
sai a lokacin mardiyya ta dauki hasken abin da yake nufi jikin tane ya fara rawa ta shiga uku karo na biyu kenan da aka taɓa yi mata wannan abu tsoro da farga ba duk suka cika mata zuciya
tsawa ya daka musu ya bar gurin ransa yana ɓaci beyi tsammanin ba wayayyu bane su.
a waje kuwa mukhtar ne yake ta kiran asim amma sam wayar bata shiga , mai da wayar yayi ya zura wayar sa a cikin aljihu ƙansa ya ɗago karaf suka haɗa ido da Abdulwahab da afiyaah ɗauke kai yayi yana cewa inshallah sai Ubangiji ya kawo sanadiyar rabuwar ki da abokina ya fadi haka a cikin zuciyar sa afili kuwa be nuna komai akan fuskar sa ba hannu ya bawa Abdulwahab suka gaisa yace '' ashe haka abu ya faru..?.''
wallahi kuwa ai wa'yannan yara sun nuna rashin mutunci kallo yadda sukai mata da fuska kallon fuskar afiyaah yayi ji yayi dariya tana neman kubbuce mai domin bakin ta yayi wani irin kato ya kumbura haka goshin ta ma duk halittar, ta tabi ta sauya dakyar ya iya saita ƙansa yace '' gaskiya basu kyau ta ba amma kema afiyaah ke dena tsokana Allah ma ya rufa asiri abin iya nan ya tsaya mu shiga daga ciki ko..?.''
taɓa rai tayi, tayi gaba da sauri Abdulwahab ya bita, domin baya so abin da zai saka be samu afiyaah ba.
girgiza kai kurum mukhtar yayi domin yasan halin Abdulwahab sarai ba mutumin kirki bane ,
bin bayan sa yayi suka shiga direct gurin D.P.O aka tura su, gaisawa yayi da su mukhtar sannan ya kalli AFIYAH yace '' me ya faru har suka fasa miki mota..da fuska?.''
Cikin kissa tace '' ina parking kawai naji ruwan dutsai ita wannan har cewa taka sai ta kashe ni..''
ta ƙara she maganar ta , tana nuna mardiyya.
da sauri mardiyya tace '' kiji tsoran Allah wallahi yallaɓai ita ta fara yi mana kuma ni bansan haka zata faru ba da ban yi ba tun a bakin kofar office din doctor ASIM take ci mana mutunci..''
D.o.p yace '' baku san hanyar zuwa gurin hukuma bane da zaku dauki mataki a hannun ku?.''
shiru, suka yi hankalin mardiyya a tashe yake , tsoran ta daya kar ace a gurin nan zasu kwana gobe suna da jarabawa.
Mukhtar ne yace '' yanzu dai ayi musu afuwa ke afiya kiyi hakuri komai ya huce su baki hakuri.''
wani kallo tayi mai ta dauke kai tace '' yallaɓai ni dai gaskiya abimin hakki na glass din motata ya fashe ni wallahi da ace iya glsss din motata ya tsaya da sauki kalli fuska ta yanzu dole sai na zauna nayi zaman jinya duk wani abu da nake yi ya tsaya ita zata dinga banu kudin da zan dinga cin abinci ?.''
d.p.o yace '' kiyi hakuri komai yana son masalaha kema baki san wata rana alfarmar da , za suyi miki ba kiyi hakuri ki fadi abin da kika kashe su biya ki , su gyara miki glass din motar ki.''
ya tsuna fuska tayi tace '' idan ma na faɗa iya biya za su yi kawai yallaɓai ku hukunta su , ko sharar office office ku basu da ta ajujuwan makaranta Saboda idan an biya kudi gaba za su ƙara idan kuwa jikin su ya faɗa musu ko cewa akai suyi wallahi ba za su yi ba..''
Mukhtar yace '' gaskiya ba za su yi wannan aikin ba ki fadi nawa ne na biya ?.''
D.o.p yace '' to ku zo ku hau kan kujerata sai ku yanke hukunci.''
matsar kwalla mardiyya tayi, malaman da suke yan iska ace su dinga tafiya suna share share a office din su.
AFIYAH tace '' kai hakuri yallaɓai ni dai ka duba fuskata ka tausaya min a yanke musu hukunci ni bana bukatar kudi nafi karfin abin da za su bani.
kallon mukhtar yayi da gaba ki ɗaya ransa yaka a ɓace yace '' kai me Zaka ce ?.''
Mukhtar yace '' ina nema musu sassauci kayi hakuri a basu sharar theater idan ya zama dole su yi, suyi shara ta rana daya shikkenan komai ya huce.''
yan rubuce rubuce yayi sannan yace '' ku ba ruwan ku da ita ko kallon banza wani a cikin kun ku yayi mata ke ki zo ki faɗa min sannan ku zan baku aiki ku share wannan theater ta new side ku share ta, tas.''
to suka ce nan suka saka hannu ya sallame su,
jan kunnen su mukhtar yayi sannan suka tafi hostel.
a bakin police station kuwa Abdulwahab cewa yayi '' ki bari zan gyara miki glass din yan zu hau mota ta , na kai ki gidan ku.''
AFIYAH da ranta duk yake a ɓace ba haka ta so ba tace '' a'a barshi yanzu zanyi waya a kawo min wata motar wannan bazan ƙara hawan ta ba.''
cikin rarrashi yace '' tsayawar da kikai anan be dace da ke ba kina hajiya big lady ki zo na kai ki gida ai mun zama ɗaya.''
ranta ne ya ƙara ɓace saboda a a police station kasa cewa komai yayu sannan yanzu zai zo yayi mata daɗin baki, iya uban me za tayi da wannan taga take taken sa , gwara ta taka mai burki tace '' da kata malam nace maka bana so ana dole ne ? a gaban ka komai ya faru amma sai ka rufe bakin ka kayi shiru ɓace min daga gani kar yanzu raina ya ɓaci nayi maka abin da banyi niya ba.''
Ran sane ya ɓace shi mace take fadawa haka macen da ya zamar da ita , tamkar rigar sakawar sa yan mata nawa ya buɗe aleda amma shi wata banza karuwa ke fada masa haka Allah ne kaɗai yasan irin mazan da take bi amma sai ya danne domin dole sai ya bakantawa asim rai, dole ya shiga inda asim yake shiga yace '' kiyi hakuri idan na bata miki rai dan Allah ki biyi Ni na kai ki gida..''
dankwalin kanta ta cire ta wullar a ƙasa tace '' kanka ake ji.''
kara wayar ta , tayi a kunne tana ɗagowa wata mota blue black hannu.
ƙarasa sowa inda take tayi da sauri ta buɗe motar ta shiga wanda ya kawo mata motar ta miƙa mai key din motar ta , ya amsa cikin ladabi.
aguje ya ta fita sosai take gudu tamkar wacce zata tashi sama , ranta gaba ki ɗaya a ɓace yake musamman ma da ta hau kan titi...
yau so tayi idan ta dawo, daga gurin asim zata huce club saboda akwai gagarimin party tsaki taja tana girgiza kai tare da dukan staring ɗin motar ta.
bata tsaya a ko ina ba sai a gaban tafkeken wani gida horn tayi mai gadi ya buɗe mata gate.
parking tayi, ta fito tana jan ƙaramin tsaki sosai tayi tafiya sannan ta ƙara so inda kofa take tana zuwa kusa da ita , ta buɗe shiga tayi wani irin hadaddan parlour ta shiga ba kowa a ciki.
wayar ta , ta ciro a cikin jaka ta shiga contact din ta ji tayi ta baya an rungume ta da sauri ta juyo tana cewa shegiya ashe kina nan , na zayi zatan kin fita ?.
turo dauri gaban goshi tayi tace '' ya za ayi na fita Alhaji yana nan.''
hnmmm kaji manya kece za ki iya zama batare da kin ci mace ba.
da sauri ta saka hannu a bakin afiyaah tana cewa kiyi a hankali yana nan.
me ya faru naga duk kin canza kardau wani ne yayi miki wannan dukan kinsan bariki ba tabbas.
hmmm mu zauna akwai labari.
afiyaah tace haka tana dafa kafaɗar shema'u.
Shema'u tace '' kinga mu shiga daga ciki bana so Alhaji yasan ina kawo mata cikin gidan nan kinsan fa besan me nake ba , maza zo mu shiga wancan dakin.''
Amina alhasan Muhammad opay 1k
814185374
Ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374
free page ya kusan karewa.
*JAMI'A*
Ina hajjiyo da yan kwalisa to ku garzayo OUMYASMEEN COLLECTION domin samun kaya na kerewa Sa'a ki zama fitila wajen oga ba abin da bana siyarwa cikin fara shi me sauki
Kallon shema'u tayi tace '' ke ni ba zama na zo ba wallahi raina duk a ɓace yake.''
Shema'u tace '' Please mu shiga kar yazo ya ganki anan kinsan fa na faɗa miki gani yake gaba ki ɗaya na dena mu'amala da ku, tun da ya ja kunne na wai sai na rabu da yan iskan kawayena yan bariki.''
Afiyaah ranta ne ya ƙara ɓace tace '' akwai ɗan bariki da ya huce ke , ni wallahi kina ba ni ma mamaki nifa ba ayi namijin da zan zauna yana shinfiɗa min dokoki ba , shi ya saka ma aure baya gaba na me na nema na rasa ?.''
hmmm kawai shema'u tace ta buɗe wata kofa ta shiga afiyaah bata da wani zaɓi da ya huce itama ta bi bayan'ta.
me makon ta tarar da daki ƙatuwar baranda ta tarar an mata ado me kyau ga bishiyu sai rangaji suke.
sosai ya jinjina kudin Alhaji yahuza ashe haka yake da uwar dukiya, tsakanin sa da asim wa yafi wani kenan ? ai bata taɓa zaton a wannan ɗaular kawar tata , take ba
bin bayan ta , tayi suka shiga wata kofar glsss wani hadaddan parlour suka tarar afiyaah zama tayi a ɗaya daga cikin kujerun parlour tana sauke ajiyar zuciya.
Shema'u zama tayi kusa da ita , tace '' kawata me ya faru?.''
kai shema'u ko drinks baki tare ni da shi ba kina tambaya ta me ya faru to budurwar asim ce ta , fasa min kai.
kama baki tayi da haɓa tace '' budurwar asim fa kika ce min?.''
Wallahi kawata budurwar sa , amma fa ba son'ta yake ba , kinsan waccan shegiyar uwar tasa , bata sona to ta matsa mai sai yayi aure, shi ne nace mai yayi auren contract da yarinyar nan da shekara uku ya sake ta , manufa ta yin haka kuwa bana tunanin ki shekara biyu wannan uwar tasa za tayi ciwon fa suga ne da ita rana ɗasai dai a wayi gari ta mutu kinga tana mutuwa ko arba'in ba zan bari a yi ba sai ya sake ta ya auri ni.
cikin mamaki shema'u tace '' to ke yanzu kin faɗa mai wannan maganar?.''
zaro ido afiyaah tayi tace '' ke rufa min asiri kan uba wallahi ko nice autar mata daga ni ba ko wacce mace a duniya asim ya bar ni, sai kace wata mara hankali zan faɗa mai haka.''
Shema'u tace '' Allah ya kyauta afiyaah bakya ganin kin daɓawa kanki huƙa AFIYAH namiji fa ba tabbas ne dashi ba ? karfa reshe ya juye ya koma da mujiya ni dai da lallaɓata kikai, ta yarda kika aure shi amma wannan wanne irin zance ne wai auren contract ita yarinyar zata yarda ya aure ta ya sake ta ne.''
Ke banza bafa wayayyiya bace fa ai ina sane nace ya aure ta dan baki ganta ba local da ita , wannan ko kallon inda take ba zai ba impact ma baya yi mata kallon mace bafulatana ce fulanin daji shema'u kina raina ƙwaƙwalwa'ta calculatre ce uwar lissafi komai sai na tsara shi na auna shi a ma'auni na hankali, shema'u yawo take da hijabi idan ya ganta ma kau da kansa yake bata ɗaya daga cikin matan da yake so.
afiyaah ta fadi haka cikin jin dadi tare da sheƙewa da dariya har da riƙe ciki saboda ta tuna irin muguntar da , ta shirya a wannan auren tabbas mardiyya sai ta gwammace bata san asim ba ina ma a garin su ta zauna.
Shema'u tace '' kawata inhar zan faɗa miki, kiji to karki soma yin wannan haukan baki san komai yana iya juyawa ba ? daga yadda kika san shi ya juya ya koma abin da baki taɓa zato ba ita ce miki a kayi a haka zata zauna ? ke a ina ma kika samo ta?.''
bata ɗauki maganar shema'u serious ba tace '' jami'ar birmu ɗalibar sa ce .''
kuttumar uban nan ki ga yarinya a jami'a , jami'ar ma BIRMU da take da wayayyun yan mata , da
Showing 15001 words to 18000 words out of 20501 words
to tace , tana ninke takardar fita suka yi jikin su a sanyaye da sauri mukhtar ya kulle kofar ya dawo ya zauna yace '' asim wannan wanne irin cin mutunci ne yar aiki ka ɗauke ta kenan ma?.'''
ASIM cikin halin ko in kula yace '' to bayan wannan wanne amfani za tayi min aikin ma dana bata share share ne da goge goge karta sake ƙafafuwan ta su shiga hanyar kitchen din mu.''
Hmmmm wallahi akwai ranar da zan maimaita maka wannan maganar asim ba'a raina mace ko wacce da irin baiwar da Allah ya bata karka zo kana neman hanyar da zata amince dakai nace maka nima ban san hanyar ba.
Cewar mukhtar.
ASIM yace '' wa Ni...? Allah ya kiyaye gaskiya mukhtar ka cuce ni me zanyi da wannan kwailar wallahi har ka saka zuciya'ta tana tashi ni na haɗa gado da wannan nace na haɗa gado da wa ?.''
mukhtar yace '' kayi nisa baka jin kira wallahi, amma lokaci yana nan zuwa inshallahu da za kayi amai ka lashe zancen ka , bana fatan ku rabu da mardiyya fata nake naga har jikokin ku.''
ASIM dogon tsaki yaja ya ci gaba da aikin da yake gaban sa.
wannan kenan
aginɗin wata bishiya ta zauna domin tafiya ma , ta ƙasa yin ta , zama tayi tana sauke numfashi tace '' SUHAILA gaskiya bazan iya ba , cimin mutunci zai ɗinga yi yana hulakanta ni, bani da wani gata yan uwana ba anan suke ba shekara uku fa ba kwana uku bace ba..?.''
dan Allah mardiyya ki tashi ki dena wannan zance wallahi ba ayi namijin da zai hulakan ki ba inhar ina raina, ki kyale sa ba sai kin shiga sabgar sa ba , sannan zai hulakan'ta ki ba
Cewar suhailah.
tashi tayi tana dafa ta da sauri mardiyya ta rufe idon ta sakamakon motar afiyaah da ta , tawo a guje ta fallatsa musu ruwan , da ya kwanta a gurin da suke a hankali ta buɗe idon ta kayan ta duk ya ɓaci haka kayan suhaila afiyaah ganin basu gane wace tayi musu wannan aikin ba dawowa tayi ta tsaya tare da zuge bakin glass ɗin motar ta , tace '' talakawan banza ku da kusan a kafa kuke yawo, kuka fara faɗa dani..?'' nonsense.''
Mardiyya da zuciyar ta , ta kawo har wuya bata san lokacin da ta dauki dutsai ba ta buga a glass din motar afiyaah wucewa yayi ya sauka akan goshin ta anan danan jini ya balle glsss din gaban motar ta ya gashe domin dutsai da ta dauko ba ƙarami bane.
Ihuuuuuuuuuu afiyaah ta saki tare da rufe bakin ta domin tuni bakin ta ya kumbura , har ta leɓen ta sai da ya fashe.
da sauri mardiyya ta fita a guje haka ma suhaila sai dai kafin suyi wani yunkuri security sun riƙe su, Abdulwahab da yake kusa da gurin da sauri ya ƙara so yana cewa maza ku kai su gurin police.
da yake akwai police station a cikin makarantar.
mardiyya da ranta ya ɓaci ta ture hannun mutumin da ya riƙe ta , tace '' cika ni da kaina zan kai kana?.''
cikin tsawa abdulrazak yace '' wato ke ce mara kunyar ko to za kici ubanki yau za mu nuna miki shegen birni yafi na ƙauye.''
AFIYAH fitowa tayi dakyar da sauri Abdulwahab ya riƙe ta yana cewa duk ɓarnar da sukai miki sai sun biya ki bara na kai ki asibiti.
kai kurum ta gyaɗa masa domin bata da bakin magana.
riƙe hannun ta yayi suka shiga cikin motar sa mardiyya da suhaila security suka tisa ƙ'esar su, suna tafiya da sauri mukhtar da yake kokarin buɗe motar sa yace '' officer me yake faruwa ne...?.''
Bala officer yace '' wa'yannan da kake gani yan ta'addane tsagerun makarantar nan yau to kashin su ya bushe barin wannan mara kunyar wata suka fasawa kai.''
da sauri mukhtar ya rufe motar sa yace '' subhanallahi suhaila me ya saka kukai wannan gangancin...?.''
SUHAILA tace '' wallahi tun a office din doctor take ci mana mutunci, yanzu muna tsaye nida mardiyya ta fallatsa ruwa kuma ta faɗa magana bakaken maganganu shi ne ran mardiyya ya ɓace ta jefa mata dutsai wallahi itama da tasan haka zata faru ba za ta jefa mata dutsai ba..''
Suhaila ta ƙarashe maganar ta , tana matsar kwallah.
Mardiyya kuwa ban da dana sani ba abin da take yi mukhtar yace '' a OFFICE din asim kuka haɗu?.''
Kai mardiyya ta ɗaga mai mukhtar yace '' office ka sake su wannan da kake gani bata da kirki halin tane wallahi duk abin da aka ce min zata aikata, haushi taji dan yaji asim zai aure shine ta huce akan su.''
Hadi yace '' gaskiya malam mukhtar ba za mu iya sakin su ba domin iya Abdulwahab ya san wannan maganar yana tafi kai ta asibiti amma idan zaka biyo mu ka biya duk abin da ya kashe mata shikkenan idan ta hakura a kashe case din idan bata hakura ba mi hukunta su, Saboda da hukuma a cikin makarantar nan , duk girman mutum duk ɗaurin gindin mutum idan aka kawo mana kar'ar sa zamu hukunta shi dai-dai da abin da ya aikata.''
okay muje mukhtar ya faɗa yana zaro wayar sa a aljihu, number asim ya lalubo ya dannawa asim kira har ta katsai be kira ba mai da wayar aljihu yayi ya bi bayan su.
har office din yan sanda ya bisu a bayan kan'ta suka zuba su mardiyya sai a lokacin kuka ya subbuce mata bata da gata sai Allah bata da madogara sai Allah yau ita ce a hannun hukumar makaranta , mukhtar a waje suka ce ya tsaya.
Wani dan sanda ne yace '' kunga wannan duk ba abin tashin hankali bane inhar zaku iya fansar kanku ai shikkenan kuna mata ku bari kanku ya kulle musamman ma ke yar fillo komai yaji ya ƙarashe maganar sa yana lasar bakin sa.
da sauri mardiyya ta ɗago kwata kwata bata gane yaren sa ba suhaila tace '' auzubillahi muna neman tsari da wannan bakar rayuwar wallahi idan baka iya bakin ka ba sai mun tona maka asiri mun maka kama da yan iska?.''
sai a lokacin mardiyya ta dauki hasken abin da yake nufi jikin tane ya fara rawa ta shiga uku karo na biyu kenan da aka taɓa yi mata wannan abu tsoro da farga ba duk suka cika mata zuciya
tsawa ya daka musu ya bar gurin ransa yana ɓaci beyi tsammanin ba wayayyu bane su.
a waje kuwa mukhtar ne yake ta kiran asim amma sam wayar bata shiga , mai da wayar yayi ya zura wayar sa a cikin aljihu ƙansa ya ɗago karaf suka haɗa ido da Abdulwahab da afiyaah ɗauke kai yayi yana cewa inshallah sai Ubangiji ya kawo sanadiyar rabuwar ki da abokina ya fadi haka a cikin zuciyar sa afili kuwa be nuna komai akan fuskar sa ba hannu ya bawa Abdulwahab suka gaisa yace '' ashe haka abu ya faru..?.''
wallahi kuwa ai wa'yannan yara sun nuna rashin mutunci kallo yadda sukai mata da fuska kallon fuskar afiyaah yayi ji yayi dariya tana neman kubbuce mai domin bakin ta yayi wani irin kato ya kumbura haka goshin ta ma duk halittar, ta tabi ta sauya dakyar ya iya saita ƙansa yace '' gaskiya basu kyau ta ba amma kema afiyaah ke dena tsokana Allah ma ya rufa asiri abin iya nan ya tsaya mu shiga daga ciki ko..?.''
taɓa rai tayi, tayi gaba da sauri Abdulwahab ya bita, domin baya so abin da zai saka be samu afiyaah ba.
girgiza kai kurum mukhtar yayi domin yasan halin Abdulwahab sarai ba mutumin kirki bane ,
bin bayan sa yayi suka shiga direct gurin D.P.O aka tura su, gaisawa yayi da su mukhtar sannan ya kalli AFIYAH yace '' me ya faru har suka fasa miki mota..da fuska?.''
Cikin kissa tace '' ina parking kawai naji ruwan dutsai ita wannan har cewa taka sai ta kashe ni..''
ta ƙara she maganar ta , tana nuna mardiyya.
da sauri mardiyya tace '' kiji tsoran Allah wallahi yallaɓai ita ta fara yi mana kuma ni bansan haka zata faru ba da ban yi ba tun a bakin kofar office din doctor ASIM take ci mana mutunci..''
D.o.p yace '' baku san hanyar zuwa gurin hukuma bane da zaku dauki mataki a hannun ku?.''
shiru, suka yi hankalin mardiyya a tashe yake , tsoran ta daya kar ace a gurin nan zasu kwana gobe suna da jarabawa.
Mukhtar ne yace '' yanzu dai ayi musu afuwa ke afiya kiyi hakuri komai ya huce su baki hakuri.''
wani kallo tayi mai ta dauke kai tace '' yallaɓai ni dai gaskiya abimin hakki na glass din motata ya fashe ni wallahi da ace iya glsss din motata ya tsaya da sauki kalli fuska ta yanzu dole sai na zauna nayi zaman jinya duk wani abu da nake yi ya tsaya ita zata dinga banu kudin da zan dinga cin abinci ?.''
d.p.o yace '' kiyi hakuri komai yana son masalaha kema baki san wata rana alfarmar da , za suyi miki ba kiyi hakuri ki fadi abin da kika kashe su biya ki , su gyara miki glass din motar ki.''
ya tsuna fuska tayi tace '' idan ma na faɗa iya biya za su yi kawai yallaɓai ku hukunta su , ko sharar office office ku basu da ta ajujuwan makaranta Saboda idan an biya kudi gaba za su ƙara idan kuwa jikin su ya faɗa musu ko cewa akai suyi wallahi ba za su yi ba..''
Mukhtar yace '' gaskiya ba za su yi wannan aikin ba ki fadi nawa ne na biya ?.''
D.o.p yace '' to ku zo ku hau kan kujerata sai ku yanke hukunci.''
matsar kwalla mardiyya tayi, malaman da suke yan iska ace su dinga tafiya suna share share a office din su.
AFIYAH tace '' kai hakuri yallaɓai ni dai ka duba fuskata ka tausaya min a yanke musu hukunci ni bana bukatar kudi nafi karfin abin da za su bani.
kallon mukhtar yayi da gaba ki ɗaya ransa yaka a ɓace yace '' kai me Zaka ce ?.''
Mukhtar yace '' ina nema musu sassauci kayi hakuri a basu sharar theater idan ya zama dole su yi, suyi shara ta rana daya shikkenan komai ya huce.''
yan rubuce rubuce yayi sannan yace '' ku ba ruwan ku da ita ko kallon banza wani a cikin kun ku yayi mata ke ki zo ki faɗa min sannan ku zan baku aiki ku share wannan theater ta new side ku share ta, tas.''
to suka ce nan suka saka hannu ya sallame su,
jan kunnen su mukhtar yayi sannan suka tafi hostel.
a bakin police station kuwa Abdulwahab cewa yayi '' ki bari zan gyara miki glass din yan zu hau mota ta , na kai ki gidan ku.''
AFIYAH da ranta duk yake a ɓace ba haka ta so ba tace '' a'a barshi yanzu zanyi waya a kawo min wata motar wannan bazan ƙara hawan ta ba.''
cikin rarrashi yace '' tsayawar da kikai anan be dace da ke ba kina hajiya big lady ki zo na kai ki gida ai mun zama ɗaya.''
ranta ne ya ƙara ɓace saboda a a police station kasa cewa komai yayu sannan yanzu zai zo yayi mata daɗin baki, iya uban me za tayi da wannan taga take taken sa , gwara ta taka mai burki tace '' da kata malam nace maka bana so ana dole ne ? a gaban ka komai ya faru amma sai ka rufe bakin ka kayi shiru ɓace min daga gani kar yanzu raina ya ɓaci nayi maka abin da banyi niya ba.''
Ran sane ya ɓace shi mace take fadawa haka macen da ya zamar da ita , tamkar rigar sakawar sa yan mata nawa ya buɗe aleda amma shi wata banza karuwa ke fada masa haka Allah ne kaɗai yasan irin mazan da take bi amma sai ya danne domin dole sai ya bakantawa asim rai, dole ya shiga inda asim yake shiga yace '' kiyi hakuri idan na bata miki rai dan Allah ki biyi Ni na kai ki gida..''
dankwalin kanta ta cire ta wullar a ƙasa tace '' kanka ake ji.''
kara wayar ta , tayi a kunne tana ɗagowa wata mota blue black hannu.
ƙarasa sowa inda take tayi da sauri ta buɗe motar ta shiga wanda ya kawo mata motar ta miƙa mai key din motar ta , ya amsa cikin ladabi.
aguje ya ta fita sosai take gudu tamkar wacce zata tashi sama , ranta gaba ki ɗaya a ɓace yake musamman ma da ta hau kan titi...
yau so tayi idan ta dawo, daga gurin asim zata huce club saboda akwai gagarimin party tsaki taja tana girgiza kai tare da dukan staring ɗin motar ta.
bata tsaya a ko ina ba sai a gaban tafkeken wani gida horn tayi mai gadi ya buɗe mata gate.
parking tayi, ta fito tana jan ƙaramin tsaki sosai tayi tafiya sannan ta ƙara so inda kofa take tana zuwa kusa da ita , ta buɗe shiga tayi wani irin hadaddan parlour ta shiga ba kowa a ciki.
wayar ta , ta ciro a cikin jaka ta shiga contact din ta ji tayi ta baya an rungume ta da sauri ta juyo tana cewa shegiya ashe kina nan , na zayi zatan kin fita ?.
turo dauri gaban goshi tayi tace '' ya za ayi na fita Alhaji yana nan.''
hnmmm kaji manya kece za ki iya zama batare da kin ci mace ba.
da sauri ta saka hannu a bakin afiyaah tana cewa kiyi a hankali yana nan.
me ya faru naga duk kin canza kardau wani ne yayi miki wannan dukan kinsan bariki ba tabbas.
hmmm mu zauna akwai labari.
afiyaah tace haka tana dafa kafaɗar shema'u.
Shema'u tace '' kinga mu shiga daga ciki bana so Alhaji yasan ina kawo mata cikin gidan nan kinsan fa besan me nake ba , maza zo mu shiga wancan dakin.''
Amina alhasan Muhammad opay 1k
814185374
Ku turo da shedar biya ta wannan number 08141785374
free page ya kusan karewa.
*JAMI'A*
Ina hajjiyo da yan kwalisa to ku garzayo OUMYASMEEN COLLECTION domin samun kaya na kerewa Sa'a ki zama fitila wajen oga ba abin da bana siyarwa cikin fara shi me sauki
https://chat.whatsapp.com/DSd6g96hO2F41IG6k43rEl?mode=ems_copy_t
*Episode 6*
Kallon shema'u tayi tace '' ke ni ba zama na zo ba wallahi raina duk a ɓace yake.''
Shema'u tace '' Please mu shiga kar yazo ya ganki anan kinsan fa na faɗa miki gani yake gaba ki ɗaya na dena mu'amala da ku, tun da ya ja kunne na wai sai na rabu da yan iskan kawayena yan bariki.''
Afiyaah ranta ne ya ƙara ɓace tace '' akwai ɗan bariki da ya huce ke , ni wallahi kina ba ni ma mamaki nifa ba ayi namijin da zan zauna yana shinfiɗa min dokoki ba , shi ya saka ma aure baya gaba na me na nema na rasa ?.''
hmmm kawai shema'u tace ta buɗe wata kofa ta shiga afiyaah bata da wani zaɓi da ya huce itama ta bi bayan'ta.
me makon ta tarar da daki ƙatuwar baranda ta tarar an mata ado me kyau ga bishiyu sai rangaji suke.
sosai ya jinjina kudin Alhaji yahuza ashe haka yake da uwar dukiya, tsakanin sa da asim wa yafi wani kenan ? ai bata taɓa zaton a wannan ɗaular kawar tata , take ba
bin bayan ta , tayi suka shiga wata kofar glsss wani hadaddan parlour suka tarar afiyaah zama tayi a ɗaya daga cikin kujerun parlour tana sauke ajiyar zuciya.
Shema'u zama tayi kusa da ita , tace '' kawata me ya faru?.''
kai shema'u ko drinks baki tare ni da shi ba kina tambaya ta me ya faru to budurwar asim ce ta , fasa min kai.
kama baki tayi da haɓa tace '' budurwar asim fa kika ce min?.''
Wallahi kawata budurwar sa , amma fa ba son'ta yake ba , kinsan waccan shegiyar uwar tasa , bata sona to ta matsa mai sai yayi aure, shi ne nace mai yayi auren contract da yarinyar nan da shekara uku ya sake ta , manufa ta yin haka kuwa bana tunanin ki shekara biyu wannan uwar tasa za tayi ciwon fa suga ne da ita rana ɗasai dai a wayi gari ta mutu kinga tana mutuwa ko arba'in ba zan bari a yi ba sai ya sake ta ya auri ni.
cikin mamaki shema'u tace '' to ke yanzu kin faɗa mai wannan maganar?.''
zaro ido afiyaah tayi tace '' ke rufa min asiri kan uba wallahi ko nice autar mata daga ni ba ko wacce mace a duniya asim ya bar ni, sai kace wata mara hankali zan faɗa mai haka.''
Shema'u tace '' Allah ya kyauta afiyaah bakya ganin kin daɓawa kanki huƙa AFIYAH namiji fa ba tabbas ne dashi ba ? karfa reshe ya juye ya koma da mujiya ni dai da lallaɓata kikai, ta yarda kika aure shi amma wannan wanne irin zance ne wai auren contract ita yarinyar zata yarda ya aure ta ya sake ta ne.''
Ke banza bafa wayayyiya bace fa ai ina sane nace ya aure ta dan baki ganta ba local da ita , wannan ko kallon inda take ba zai ba impact ma baya yi mata kallon mace bafulatana ce fulanin daji shema'u kina raina ƙwaƙwalwa'ta calculatre ce uwar lissafi komai sai na tsara shi na auna shi a ma'auni na hankali, shema'u yawo take da hijabi idan ya ganta ma kau da kansa yake bata ɗaya daga cikin matan da yake so.
afiyaah ta fadi haka cikin jin dadi tare da sheƙewa da dariya har da riƙe ciki saboda ta tuna irin muguntar da , ta shirya a wannan auren tabbas mardiyya sai ta gwammace bata san asim ba ina ma a garin su ta zauna.
Shema'u tace '' kawata inhar zan faɗa miki, kiji to karki soma yin wannan haukan baki san komai yana iya juyawa ba ? daga yadda kika san shi ya juya ya koma abin da baki taɓa zato ba ita ce miki a kayi a haka zata zauna ? ke a ina ma kika samo ta?.''
bata ɗauki maganar shema'u serious ba tace '' jami'ar birmu ɗalibar sa ce .''
kuttumar uban nan ki ga yarinya a jami'a , jami'ar ma BIRMU da take da wayayyun yan mata , da
Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4Chapter 5Chapter 6 Chapter 7