ya ganshi to daman idan anaso Ayi maka hukunci a palace din to dama either akaika chamber din subira ko kuma Imad chamber su biyu nan suna da matsaloli


Hurriya kam banza tayi dashi ta cigaba da aikinta don a wurin ta baida amsa ita dama she hate useless talks ta gama gyara gadon tass Imad da yake tsaye yana fuming don bacin ran da yake ciki zai iya karyata idan har batai wasa ba ba’a taba yi mashi irin abinda akayi mashi ba yau tun kam daga yarintar shi

Ta shigo mashi daki ba tare da izininshi ba sannan ta tadashi daga baccin da yake mai matukar dadi don ta raina mashi wayau wai kuma da brush ta tadashi sannan bata gaishe shi ba and again yana mata magana tayi banza dashi ko bata iya turanci ba bata iya durkusawa ta fara bashi hakuri tana kuka tana rike mashi kafa


Amman shine takeyin kamar ma batasan dashi a wurin ba gaskiya yarinyar nan must have a dead wish because she’s playing with fire

Wata tsawa ya buga mata yace ke bakiji ana maki magana ba ko kurma ce Hurriya a hankali ta juyo ta zuba mashi idanunta masu matukar kyau da kaifi kallonta yake tundaga gashin kanta da yake a bude har zuwa fuskarta mai matukar kyau da annuri yace Do you want to die sai kuma ya tuna ba Lallai tanajin turanci ba magana yafaryi mata cikin muryarshi mai dadi kuma da dadin sauraro yace wacece ke? Dan tsotsar bakinta tayi sannan tace Hurriya Faisait Hamood sabuwar mai aikin ka


Kin aikata laifuka don haka zaki amshi hukunci da ya kamata yana maganar with arrogance ne and full of himself

Hurriya kallonshi take ba tare da ko kyaftawa ba tunda yake babu mai aikin da taba kallonshi ido cikin ido kowa acikinsu yana shakkar shi Amman banda Hurriya wadda take kallonshi kamar yadda Ammar ke kallonshi cikin muryar ta mai dadi da sanyi sai kuma maganar ta wanda yake nuna cewar tana da wani yare na daban tace babu inda nayi laifi tunda nazo a dokokin ance ba ruwana dakai kuma na kiyaye kuma ance bakasan hayaniya kuma banyi ihu ba ance idan kana Bacci kada in tadaka da magana kuma banyi magana nayi amfani da wancan abune wurin tada ka

Sharrudan da aka gaya mata duka ta fada mashi shiru yayi yana kallon bakinta wanda yake da kyau da bakin lining a kasa wanda kamar ita ta zanashi Amman haka hallitar bakinta yake

Zama yayi saman sofa ita kuma ta fara share wurin da vacum cleaner Ammar ya shigo yana wata irin dariya yana nuna Imad wanda ya rasa miye zaice Hurriya kallonshi tayi taga kamar su daya don suma identical twins ne kamar Neela da liya murmushi yayi mata sannan yayi mata wink bayan tagama komai zata fita tazo wucewa kenan Imad ya tadiyeta ta fadi goshinta da hannunta na buguwa da kyar ta tashi.


🌚Masarautar Qamar

By Khadija (KMU)

19&20

Da kyar ta tashi  kallonshi tayi da idanunta masu wani kaifi Dukansu kasa gane expression din fuskarta sukayi she looks fierce and scary ta iya hiding emotion don fuskarta baka iya lura da farin ciki ko sadness ko happiness ta kware wurin hiding emotion dinta don haka fuskarta is neutral saidai idanunta ne suke bashi warning sannan ta sanya kafa ta tafi Because she was done ko mopping din batayi yayi da kanshi.



Ammar dariya ke cinshi Amman ganin zallar bacin rai a fuskar shi ya sanya yace Husain waye ya tabaka banza imad yayi dashi ya tashi yaje ya kwanta saman gado ya runtse idonshi

Ganin mulki da sarautar tashi ta matso ya sanya ammar ya fita idan ya sauko sai ya dawo

Hurriya ranta bace yake Mai mutane suka dauki duniya ne itadai abinda ta sani a rayuwarta da mai kudi da talaka duk Abu dayane da yaro da babba duk Abu dayane da makaho da mai ido duk abu daya ne saboda duka suna amsa sunansu mutane batasan yawan tunani don haka ta nufi dayar chamber din


Chamber zinariya kowa kallonta yake kuma ba wanda tayi ma magana abinda ya kaita shi takeyi don Allah ya taimaketa aikin kitchen ne

Aiki sukeyi sosai don abinci akeyi kala kala wasu suna gyara inda aka bata wasu kuma  suna jera fruits a trays

Hurriya kam wanke wanke kawai takeyi tana kifewa

Sun dade suna aiki a wurin kafin a kamalla  Hurriya wuri ta samu tadan zauna

Shugabar dake a wurin ta kalli Hurriya tace ku tashi kuje kukai abinci kuma ku tsaya har agama ci saboda idan suna bukatar wani abu

Hurriya kallonta tayi ido cikin ido sannan tace bazanje ba daganan nagama aiki sai kuma abincin dare zanzo Amman ba zan kai abinci ba

Shiru kitchen din ya dauka kowa yana kallonta baki bude


Hurriya ba inda suka tsaya sai inda takeyin wanki tunawa tayi bata wanke kayanta ba don haka ta shiga dakin ta dauko kayan saida ta cire kudinta da sarkokinta da wayarta ta adanasu sannan ta nufi wurin wankin

Wata yar karamar yarinya tazo wurin Hurriya kallon Hurriya tayi tace inason ki tayi dariya yan hakoranta na fitowa yarinyar tace kinsan miyasa nike sonki Hurriya ta girgiza kai tana kallon yarinyar tace Aa yarinyar dariya tayi sannan tace saboda kina da kyau shiru Hurriya tayi tana kallonta yarinyar tace kinsan mi ?kinfi kowa kyau a masarautar Qamar

Sai kuma ta bata fuska alamar tanaso tayi kuka tace amman banason in rasaki kamar yadda na rasa fareedaa shiru Hurriya tayi don bata gane inda zancen yarinyar ya dosa ba Hurriya wadda bata iya lallashi ba tace kiyi shiru ki daina kuka sannan ta matsa daga gefen yarinyar ta fara wankin

Hurriya duk tafi jin dadin aikin wanki kowa hidimar gabanshi yake ba wanda ya damu da wani don haka ba ruwanta da bata miyaun bakinta wurin magana


Kayanta ta fara wankewa sannan ta cigaba da wankin da ake kawo mata wanki take sosai ga sanyi

Duk sanyi bai dameta ba kamar yunwar da ta dameta don duk yau bataci komai ba wata irin yunwa takeji


Imad kallon wayarshi yake wadda banda ringing ba abinda takeyi tun dazu khaleed ke kiranshi non-stop Amman yaki dauka saboda his new Maid has ruined his entire day saidai he made a vowed to ruined her life the way she ruined his mood she really messed with the wrong person wani kiran ne ya kara shigo mashi cikin yanayi na mulki da kuma izza ya dauka shiru yayi batare da yace komai ba


Khaled yace kaifa dan rainin wayau ne kaifa kadai muke jira tun dazu don Allah kayi sauri cikin yanayi na mulki Imad yace please I will be there in the next five minutes
Ya kashe wayar sannan ya tashi ya shiga toilet dinshi ya dade a toilet din kafin ya fito sannan ya shirya cikin hadaddun English wears dinshi wadanda sukayi mashi kyau

Imad na fitowa ya iske Ammar da yake zaune a falon da yake link da bedroom dinshi yana kallon football babu wanda yake da access din shigowa wurin anyhow sai hassan dinshi wato twin brother dinshi

Ammar tasowa yayi ya kalki danuwanshi wanda suke da matukar kama sannan ya bashi side hug

Tunda ya kalleshi yasan cewar mood dinshi ba Daidai bane don haka yace twin mi yake faruwa dakai ne

Don’t tell me har yanzu saboda sabuwar maid dinka kake wannan frowning face din dariya Ammar yayi mai kulewa sannan yace haba young prince kada fa ka bada mu ka saki ranka mana don Allah

Zamuyi maganinta ta isa ta taba min husain dina ta zauna lafiya kada kacwani damu i will punish her myself

Dadin baki Ammar ya rinkayi mashi har ya samu Imad yayi dariyar da bai shirya ba daman dariyar tashi a iyakar ta wurin Ammar din sai kuma kannenshi shi kuma Ammar daman baida matsala yana da fara’a sosai

Fitowa sukayi tare wanda duk bala’en ka baka iya ganesu saboda matukar kamar su don wata irin kama sukeyi ba kadan ba they are identical twins kamarsu har tayi yawa

Duk inda suka wuce durkusawa ake ana cewa Allah ya taimake ku Allah ya kara maku nasara har suka fito inda motoci suke parked iri iri cikin hanzari aka bude masu

bayan wata red Bentley flying spur sannan bakaken convoy suka biyo bayansu


Hurriya kallon kala biyun da idan tagama wankesu to shikenan tagama wankin
tayi kololuwa wurin gajiya don daurewa kawai takeyi ga yunwa da take nukurkusarta

Tsotsar bakinta tayi sannan ta maida hankalita ta cigaba da wanki shanya taje tayi har ta fara tafiya taji ana mai kyau mai kyau mai kyau tana haki har ta iso inda Hurriya take tasha gabanta Hurriya kallonta tayi kamar zatayi magana sai kuma tayi shiru yar kyakyawar yarinya karama wadda ta zauna kusada Hurriya kafin ta fara wanki dazu tace ina maki magana shine ki kayi shiru Hurriya again batace mata komai ba dariya wasba tayi sannan tace mata sunana wasba kefa ? Hurriya ko kallon inda take batayi ba ta kama gabanta.


Wasba kallon inda Hurriya ta bari tayi sannan tayi murmushi ta nufi gidansu dake cikin masarautar.



Hurriya kam tundaga nesa taga bakin dakin wurin ya cika yayi fam cike da mamaki ta karaso tana kallon mutanen da suka cika famm kamar hadin baki kuma suna ganinta sauran mutanen duka suka juyo suna kallonta

Hurriya kam takawa ta cigabayi a hankali tana karasowa don ita haka Allah yayi ta idanun mutane basu takura mata saidai su kara mata confidence don haka ta tsakiyar su ta ratsa don duk kallon da ake mata ko ajikinta saidai wata fitinanniyar tsawa da aka buga mata wadda ta shiga duk wanda yake wurin Hurriya ita kanta tsawar ta shigeta saidai ta maze ta dago idonta cike da rainin wayau ta zuba ma wanda ya jefeta da tsawar tana zuba mashi idanunta masu masifar kyau.

Kallonta yake tundaga tafukan kafafunta har zuwa kan dogon bakin gashinta kallonta yake yana hadiye miyau da kyar

Hurriya kam lura da irin kallon da yake mata mai cike da zallar iskanci ya sanya tayi tsoki tace dan akuya maye ta nufi inda zai sadata da kofa saidai bata ida karasawa ba taji an kifa mata bulala mai matukar zafi

Juyowa tayi aiko taganshi tsaye yana kallonta da idanunshi wadanda basu da kyaun gani

Kallonta yayi sannan yace ke tsinaniya yar gidan matsiyata da ubanwa kike takama dashi duk masarautar nan da har zaki kona ma barira fuska tsotsar bakinta tayi sannan ta kalleshi ido cikin ido tace da ubanka nike takama a masarautar nan tana kallonshi shima yana kallonta wani irin kwarjini takeyi mashi don kwata kwata taki sauke idonta har lokacin idonshi na cikin nashi


Kowa kallon dramarsu yake ana jiran kaura ya jawota yayi mata dukan da bazata iya gane ko kanta ba bare har ta zagi kaura ko ta kona mashi budurwa

Shikam kaura he was lost in thought because he had never seen a beautiful human being like her she’s beautiful beyond words she’s just beautiful yadda take komai yake sanya mashi ganin kyauwunta gyara tsayuwar shi yayi domin ya bugeta kawai saiga kuyanga daga sashen Imad

Kallonsu tayi tace mi yake faruwa ganin duk sunyi shiru ya sanya ta kalli Hurriya tace muje hakimi na kiranki Hurriya ba wanda ta kalla acikin su tabi kuyangar

Suna zuwa suka shiga chamber hakimin wanda yana can ciki kwance a saman sofa

Abinci ya gama ci sannan ya sanya aka fidda mashi kwanonin abinci wayarshi yake latsawa kafin bacci ya daukeshi mai matukar dadin gaske


Hurriya kam tunda ta sanya aka gaya mashi Amman har lokacin bataji anyi mata iso ba don haka taje balcony ta zauna tayi shiru tana kallon masu wucewa


Duk kuyangin dake wucewa kallonta suke da mamaki irin kujerar prince kika zauna tabb kina ruwa ba wanda ta kula bare tayi mashi magana

Lumshe idonta tayi sannan tayi crossing legs dinta banda yunwa ba abinda takeji don duk wunin ranar bata sanya ma cikinta komai

Baccin gajiya da taji ya fara daukarta ya sanya ta tashi ta koma ciki kitchen din ta shiga wanda tayi sa’a ba kowa kallon kulolin abinci tayi wanda aka jera abinci ne a table din kitchen island ba tare da bata lokaci ba ta shiga budewa abinci ne kala kala ga yankakun fruits wani plate mai kyau ta jawo ta zuba abincin ta faraci ahankali saida taci ta koshi don wanda ta rage baifi ace loma daya ba wanda har ta koshi sosai


Mama RaBI ta shigo kitchen din tare da zubaida dukansu bude baki sukayi da mamaki suna kallon Hurriya da tagama cin abincinta hankali kwance salati mama rabi ta farayi tana kallonta sannan tace waye ya baki izinin cin abincin nan kinsan abinci waye kuwa kallonta Hurriya tayi da idanunta masu haske ba tare da tace komai ba ta dauki ruwan da yake jere a saman tray din ta fita.


Mama RaBI kam ba’a tabayi mata irin abinda Hurriya tayi mata ba
Kallon zubaida tayi wadda har lokacin bakinta bude yake sannan tace wai ina aka samo wannan shegiyar yarinyar ne mama rabi kinga wani kallon banza datayi maki sannan ta juya ta tafi shiru mama rabi tayi sannan ta Sauke ajiyar zuciya tace lallai yaro baisan wuta ba sai ya taka sannan ta kyalkyace da dariya zubaida wata dariyar gefen baki tayi itama sannan suka bar wurin

Mama RaBI taji haushi sosai da hakimi bai basu fuska
Ko kara bai basu damar wani ya kaimashi bare munafunci da tsaegumi
Da wallahi sai tagaya ma Imad kaskantaciyar mai-aikin shi taci mashi abinci kwata tayi sannan tace ajuri zuwa rafi watarana tulu zai fashe


Hurriya tafiyar ta Tayi wanda gari har ya fara duhu magrib ta gabato saida tayi tafiya mai nisan gaske sannan tazo bangarensu ta shiga

Ta gaji sosai don ba abinda take bukata irin tayi wanka tayi bacci kallon bintu da take zaune tana hamma tayi wanda dama ga dukkan alamu Hurriya take jira



Wuri ta samu ta zauna Bintu ta kalleta tace sannu Hurriya kindawo ne kinci abinci ? Daga mata kai Hurriya tayi batace ma Bintu komai ba

Bintu kallonta tayi hamma tayi sannan tace saida safe daman jiran dawowar ki nike bari in tafi har ta juya tajiyo sautin muryar Hurriya daga bayanta tace kinci abinci da wata irin murna Bintu tajuyo tace naci a hankali Hurriya ta zaro naira dari biyu ta mika mata

Bintu amsa tayi tana kallon Hurriya domin jin karin bayani lumshe idonta Hurriya tayi sannan ta tsotsi bakinta saida ta dauki lokaci sannan ta bude idonta masu kyau ta zuba ma bintu su tace idan kina bukatar wani abu ki siya can kasan makoshin tace ki kula da kanki sannan ta kara rufe idonta kamar mai bacci


Bintu murmushi tayi tana kallon Hurriya da zallar kauna a idonta wadda idonta suke rufe dan tsalle Bintu tayi kamar karamar yarinya tace Ina kaunar ki Hurriya sannan ta juya ta tafi dakinsu

Saida Hurriya taji tafiyarta sannan ta mike ta nufi babban kitchen din da ake dafa ko wani irin abinci

Dubawa tayi ko zata ga matar jiya saidai akasin haka baba haule reza tagani don duk tafi kowa zama kusa da ita don haka ta nufi wurinta da bokitin baba haula reza kallo daya zakayi mata kasan cewar masifarfa ce ta ajin karshe

Hurriya bokoti ta ajiye ahankali sannan ta kalleta in a commanding tone tace ruwa zaki zuba min

Baba haule reza ta dago idonta a kankance ta fara surfa mata ashariya Hurriya bata janye idonta daga kallonta ba kuma batace mata kala ba



Har saida tagama kumfar bakinta kowa kallon baba haule reza yayi acikin kitchen din sannan kowa ya cigaba da hidimar shi don inda sabo ta saba



Hurriya saida ta tabattar da cewar baba haule tagama masifarta sannan ta zaro naira dari ta ajiye mata tana kulleta da idonta

Baba haule kam kamar an daure mata baki don dauke darin tayi a inda Hurriya ta ajiye tana saka kudin cikin skirt dinta

Bokitin ta janyo ta zuba ma Hurriya ruwan zafi masu yawan gaske ba tare da Hurriya tace kala ba taja bokitin ta nufi toilet ta gasa jikinta sosai da ruwan zafi.

[12/02, 4:53 PM] Khadyn Sp: 🌚Masarautar Qamar
A story about a mysterious palace

By Khadija (KMU)

Page 21&22

Bata wani dauki lokaci sosai ba ta fito daga toilet din tana mai ya mutsa fuskarta don duk batajin dadi don kayan dake jikinta sune ta maida dalili kam da akwai zanen tatoo a bayanta bata kaunar ko wani dan mutum yaga tatoo din sam she’s not comfortable cikin masarautar Qamar don kwata kwata batada yancin dan adam kuma ita a rayuwarta ba abinda takeso irin yanci don haka ta tashi a rayuwarta tunda ta taso ba wanda ya taba depriving right dinta tanada ko wani irin freedom


Tana da matukar tsafta don kaya basu iya mata 24hrs ajikinta bare kuma ace kuma tayi wanka ta maimaita kaya saidai da ace ta fita da daurin zani wanda duk zanen dake bayyane a bayanta zai bayyana ga idon mutane gwara ta maida kayanta

Don haka da kayan ajikinta ta fito sannan tayi alwala ta shiga dakin




Cikin natsuwa ta Cire kayan jikinta kallon inner wears din da ta siya dazu dasu sabulun wanka da brush tayi har da turare mai sanyi kamshi batasan ana kasa haja ba sai dazu da safe inda har tazo wucewa taga haule reza ta kasa kaya masu kyau har ta wuce ta dawo haule reza ba abinda bata saidawa saida Hurriya ta bata kudi sosai wurin siyen abinda takeso don saida ta tabbatar duk abinda take bukata ta siya sannan ta nufi bangaren Imad

under wears ta sanya masu kyau sannan ta shirya cikin wata blue half gown da iyakarta gwiwar kafarta ta tsaya

doguwar hijab dinta ta sanya sannan ta kabbara sallah rama sallolinta tayi duka bayan tagama sallarh ta kishingida jikin katifar ta lumshe idonta ba bacci take ba Amman dai tayi lamo


Sunanta taji ana
Showing 21001 words to 24000 words out of 38837 words