yi Difaring ni kuma naga duk wata Sabuwar Wahalace nace ya barshi zan rika kokartawa.

Hakanan na ke zuwa da Katon ciki gaba ina tafiya a tale kamar wata yar kaciya, aikin gidana kam tuni na yaye shi sai in Habiba tazo ne ta kan taimakamin Tunda cikina yana cikin Watannin fitowarsa Duniya ne.
Assadiq duk bayan sati biyu ya ke zuwa ya ganni, in kuma yana wajen aiki ko da yaushe muna tare da juna ta waya.
Ba abunda zan ce ma Anty Surayya sai Godiya domin ta nuna min dukkan kauna, ita ta yi masa maganar Kudin kayan jariri ya ba kuma bata ta sDiyamin komai har da kayan da zan yi Fitan suna dashi.
Kuma sai da ta turomin kayan na zaba duk da kuma nace basai ta yi hakan ba, zata kirani bayan kwana Biyu taji lafiyata ita ta kara karfafan gwiwan ma kada nace zan zauna a gida na cigaba da zuwa makaranta na Saboda hakan zai taimakamin na samu sauki wajen Haihuwa.
Amma na lissafe da wattanin Cikina ta kuma bani tabbacin Adda zata zo ta zauna dani, Da ya ke ma Addan na ta fama da Ciwo yanzu Amma ita kuma sai ta yi lafiya.
Da watan azumin nan babu abunda Assadiq bai ijemin na kayan abinci ba, sai ma ina kyauta da shi kuma sai da na tambayeshi ya bani izini.
Na dibarma Adda Fati kayan abinci har maman suhailat na ba ta, ta na Godiya Ummi dai ban bata ba, tunda Tuni huld'a a tsakanin mu ta jima da yankewa sai dayan matar ne na ba ma wa kawai.
Sannan na Diba nace Habiba ta kai samaru dogon gida wajen maman boy, tunda yace a yi sadaka ga mabukata ne.
Da ya ke ba su yadani ba Lokaci bayan Lokaci suna kawo min ziyara ne, ni ce ma dai sau daya na taba zuwa anguwan tun bayan aurena da komawar Amma gadan mallam mamman.
Bamu muka gama jarabawa ba sai da aka shiga goman karshe na watan azumin Ramadan, Assadiq yazo sau biyu ya dubani ya kuma yi min Weekend, sai dai abun da ke bani mamaki ya rage zuwa Gusai Kamar baya ina tsoron kada ace saboda ni Umma ta raba shi da matarsa.
Ina so na tambayesa ammh kuma wata zuciyar na hanani ganin kamar ba Hurumina ba ne, kada kuma yaga na tsallako abunda bai shafeni ba.
Hatta kayan Sallar da zan yi fitar Idi da shi yace yana Gusai Big sis duk ta karba kudi ni da Sultana tace zata siyamana.
Jin ya ambaci sunan Sultana sai na samu salama araina nace suna tare kenan har yanzu, na manta ko basa tare kanwa take a garesa zai iya yi mata komai da yaya ke yiwa kannensa.
Salla saura kwana uku Assadiq ya kirani yace gobe yana tafe na shirya tare zamu wuce gusai chan zamu yi sallah.
Duk da har acikin Raina ban so hakan ba , sai dai ban iya ce masa komai ba da yaga na damu sai ya fara lallashina yana nuna min kada na damu yan'uwansa ne ya zama Dole mu'amala ta irin wannan salla ko wata Hidima ta rika had'amu ta hakane har watarana zamu samu Fahimtar juna.

Ba ni da yarda zan yi, hakanan na kira su Adda Fati ina gayamusu ita kuma tace miye aciki naje cikin Dangin mijina na yi sallah Tunda haka ya ke so, Adda Rukayya ce da muka yi waya ta rika masifan kada naje a wulakantani fa, tunda ai Adda Fati ta gayamata yadda komai ya Faru.
Sai na nuna mata ba wanda zai min wulakanci matukar Assadiq na tare dani, har Amma sai da na kira na gayamata ita dai Fatan alheri kawai ta yi mana. Kafin ya iso duk na had'a abunda zan Bukata da yamma ya iso dakyar na iya Dama masa kuni, shima sai ya tsinke zubarwa na yi Maman Suhaihat ce ta bashi abun bude baki tunda ni azumin da na yi duka duka bai wuce goma ba.
Washegari kuma Tun safe muka Dauki Hanya Tunda da Motarsa ya zo,  da na gaji da zama yaga ina ta faman Mutsu mutsu sai muka Tsaya ya Budemin baya na shiga yace na kwanta na Huta shi kuma ya koma gidan Gaba yacigaba da Tukinsa.
Da wuri muka isa gusai Shashen Umma muka fara sauka, kuma kamar yadda na Lura kowa yasan da zuwana Tunda shi Assadiq din ya tabbatar musu anan zamu yi sallah.
Na dauka zuwa wannan Lokacin Umma ta sauko ashe abun ba haka ba ne, da muka shigo ta na zaune afalonta ita da Sultana suna Sauraran wa'azi a tashar Sunna Tv.
Sultana na Sanye da Atamfa Doguwar riga ta na ganinmu mun shigo Umma tace ta tashi ta shiga ciki.
Zan durkusa na gaisheta Assadiq yace na zauna saman kujera daman kuma in nace zan duka to aiki ne babba na jama kaina.
Dagani har Assadiq Umma bata amsa gaisuwarmu ba.
Sai ma wani kallo da ta yi mana ta Dauke kai.
Dagani har shi sai muka yi shuru muka kasa mgana , ni kaina a kasa ina ta fama da faduwar gaba.
Shi kuma yana Tunanin Fushin Umma zuwa yanzu ya yi yawa gaskiya.
Shi a ganinsa tunda ya gane kuskurensa to ta yafe masa kamar yadda Abba ya yi, sannan ta zaunar da shi su yi mgana ta Fahimtar juna.
Zuwa lokacin Har chan shinkafi su san da Labarin auransa kuma sun kikkirasa sun yi masa Fatan alheri.

Baba Shitu kuma mahaifin Sultana shi da kanshi ya kirasa ya fad'a masa abunda Sadiq bai sani ba ita Sultanan ta kirashi ta na kuka ta na fad'amai wai Sadiq yaci Amanarta sai da ya yi mata Fata fata sannan.
Kuma ba wanda yasan Umma ta barota da gidan mijinta ta dawo gabanta da zama ya'yanta na zugata.
Abba kuma har alokacin bai ce mata komai ba Sadiq ya kirasa ya na gayamasa Umma bata Daukan wayansa ko zai yi mata mgana?
Abba yace ya kara bata Lokaci ta Huce Tukunnah.
Kamar daga sama naji Umma tace"Ke bakar Annoba tashi ki fita zan yi mgana da d'ana."
Haka ta fad'a kai Tsaye Lokaci d'aya ta na Hararana.
Da Sauri na mike har sai da bayana ya amsa, Shima mikewar ya yi Umma ta dakamai Tsawa kafin tace"Koma to ka zauna Bita zai zai."
Ba shi da yadda zai yi sai ya koma ya zauna sannan ya kalleni ya na fad'in"Ki shiga bangaren Innani ko bangarem mama"
Ban ce komai ba na kama Hanyar Fita shi kuma sai ya daga murya ya na fadin"Kin ji ko?
Sai na juyo ina daga masa kai idanuwana fal da kwallah.
Na jima a haraban gidan na rasa ina zani sai da na gama kukana na share kwalla sannan na nufi bangaren Mama.
Kaamar Daga sama ta ganni farko Siyama ce zaune a falo  ammh yarinyar nan kallo wulakanci ta yi min sai ni ce na gaisheta sannan nace mata wajen Mama nazo, shima sai da taga dama sannan ta tashi ta shiga ciki ta yi ma Maman mgana sai ga su sun fito tare.
Ita da Fara'a muka gaisa fad'i ta ke yi" yanzu kuka iso kenan? Ina shi magajin gidan?
Kaina na kasa nace"Ya na wajen Umma, shi yace na zo nan na zauna."
Mama ta jinjina kai kafin tace"Allah sarki sannun ku da zuwa ya nauyin jiki? Kai wannan cikin naki akwai girma wa ya ga Runduna."
Kaina na kasa ban yi mgana ba, sai faman hira take min ta min Tambayoyi ni kuma bani da sakewa yasa na ke amsata daya daya.
Ni ce naga ko ruwa ba ta bani ba sai nace mata zan sha ruwa.
Cikin yake tace"Af nafa manta ku bakwa azumi,  Siyama"
Sai ta fara kwalama Siyama kira sai gashi ta fito ta na wani Tura baki Mama tace ta kawomin Ruwa.
A wulakance ta kawomin Ruwan gora kuma don mugunta mai sanyi, ba ta ko Duba Halin da ni ke ciki ba.
Kuma babu ko karamin kofin da zan sha, Kuma gashi ina jin kishi hakanan na sha kad'an na ijiye.
Daga karshe da Mama taga na kasa sakin baki na bata labari sai ta shige ciki su ka barni anan kamar wata almajira.
Gashi Fitsari ya matseni na rasa yadda zan yi, ina zaune kawai ina ta sharan kwallah na tausayin kaina a baya ina Murnan na fita daga cikin Tsaka mai wuya ashe tsuguuno bata karemin ba.

******
A falon Umma kuwa bayan Fitata sai da Umma ta gama shanya Sadiq zaune a gabanta sannan ta gyara zama ta kalleshi Lokaci d'aya ta na fadin"Abubakar dago nan ka kalleni."
Ba musu ya dago yana kallonta Fuskarta ba Fara'a tace"Wacece ni hala a wajen ka?
Cikin mamakin Tambayarta yace"Ke din mahaifiyata ce."
Wani mirmishi Umma ta yi kafin ta daga baki ta kira sunan Sultana ta amsa sai gashi ta fito.
Gaban Umma ta durkusa ta na cewa gata, Umma ta kalleta yadda duk ta rame a tsaye, suma cikin satin da ya fita suka gama WEac Sai neco.
Duk ta rame ta Lalace sannan ba ta da wani Walwala bata da aiki sai kuka.
Itace ya kamata ta share mata hawaye Tunda dai ba ta da wata Uwar da ta wuceta.
Nuna masa ita ta yi kafin tace"Ita kuma miye nata matsayin a wajen ka?
Sai da ya dago ya na kallon sultana wacce ta kauda kai gefe kamar bata son kallonsa.
Cikin sanyin murya yace"Ita d'in kanwata ce sannan kuma matata."
Umma ta jinjina kai kafin tace"Shine ka maida maganata banzaa ko Sadiq? Ba na gayamaka ka zaba ko sultana ko wanchar bakar Annobar ba? Ammh Saboda Alhaji ya baka Dama sai ka saka kafa ka shure mganata ka yi tafiyarka tare da matarka kana so ka nuna min abunda ka ke nufi ko?
Zai yi mgana ta daga masa hannu a Fusace ta na cigaba fad'in"Bana son jin komai daga bakin ka, yanzu zaka gayamin meneme manufarka? Tunda ka tafi ka barni da yarinya kuma baka min wata mgana ba, in ka zab'i wancan ne sai ka sakarmin yarinya domin tasan ta fara Iddarta."
Baki ya saki kafin yace"Me ya kawo kuma mganar Saki anan wajen kuma Umma?
Umma ta balla masa Harara kafin tace"Bansani ba, sallamamme mara Tunani ai na riga na fada maka baka isa ba. Indai ka zabi zama da wannan Annobar to sai ka sakarmin y'a kaji ma na gayamaka."
Shuru ya yi kansa na kasa kafin yace"Umma ba maganar saki Tsakanina da Sultana ballatana Siya, dukkansu ban aure su domin na sake su ba."
Umma ta harzuko kamar zata dakesa ta na fadin"To wlh ahir dinka, kai da dauko bala'in sai dai ya kare maka ammh bazan bari diyata ta zauna da kai ba, tunda ka zabi Ita Bakar Annoba to ka shirya sakar min yarinya kaji ma na rantse."
Cikin mamaki yace"Umma kada ki yi saurin Rantsuwa fa?
Umma tace"Nace wlh tallahi Rantsuwan d'an musulmi in baka saki wannan annobar matar da ka jajibo ba, to auren ka da Sultana na Haramtashi."
Baki sake yace"Umma kada ki zo ki yi kafarra gwara ki janye rantsuwan ki domin na baki tabbacin dukkansu ina son su ba kuma zan iya Rabuwa da d'aya saboda d'aya ba."
Mamakinsa ya kama Umma daman ai tasan halinsa ba'a kadashi a mgana.
A fusace tace"Sai kuma ka yi, tashi ka bani waje ni na riga na gama mgana."
Kin tashi ya yi sai ma ya gyara zama yana fadin"Umma ki yi hakuri don Allah, nasan na yi ba daidai ba ammh tunda nagane kuskurena sai ki yi min afuwa don Allah."
Umma saboda ma tagaji da jin mganarsa sai kawai ta kallo sultana ta na fadin"Ke tashi ki karamin karan Tibin nan ki shiga ciki."
Ba musu Sultana ta mike Idanuwanta har sun tasa saboda kuka ta kara karan talabijin din ta wuce salau salau ta koma cikin daki Sadiq ya bita da kallo.

Kafin ya girgiza kai kawai, bai tab'a Tunanin haka yarinyar ta yi nisa ba sai yanzu, tun bayan Faruwar abun bata bari sun yi mgana ba ya yi ta kiranta bata dauka ba, har Texts ya tura mata na ban hakuri duk da shi a ganinsa bai yi mata wani laifi ba ammh yarinyar nan ta yi masa banza.
Sai cikin satin nan yaga ta turo masa sakon wai ta jisa shuru ta na jiransa.
To alokacin ya dauka ta sauko ne za su yi magana sai ya kirata kawai sai ta rika latsa masa Busy.
Shi kuma da ya Fahimci ba ta da kunya sai ya kyaleta shekaranjiya kuma sai gashi ta kara Turo masa wai tana so tasan matsayinta.
Bai yi mamaki ba daman Big sis tace su Sadiya ke kara zugata ita da Umma.
Kuma daman yasan kowa acikin su musamman Sajida da saboda munafunci bakinta ya yi tsini uwar gulma.
In ta zauna ta na Biye musu ita ta sani shi dai Allah na gani akan abunda ya aikata na raya sunna ma'aiki, kuma yace yasan bai kyauta ba kuma ya ba da Hakuri ammh yarinyar nan na neman kuresa.
Kawai sai ya tura mata da sakon cewa amsar matsayinta na wajenta, duk matsayin da ta yi ma kanta shi a wajensa daidai ne, kuma ya na da tabbacin su suka zugata ta Rubuta masa haka.
Bai hakura ba, ballatana ya Saduda haka ya zauna ya na ta ba ma Umma Hakuri ita ko ta na zaune ta na masa wani kallo.
Sai da taji yace"Umma yanzu in kika ce sai na saki Siya  ina kike so taje da wannan Tsohon cikin? Kuma fa bai hallasta saki da ciki a irin wannan Lokacin ba."
Umma ta daga masa hannu a Fusace kafin ta mike taje ta kashe talabijin da kanta sannan ta Dawo ta zauna ta na fadin"Maimata abunda ka ce yanzu."
Kansa na kasa ya maimaita Umma ta fara fad'a ta na fadin"Ah ba Siya ba Siyoyo kaji min mara kunya, ina ruwana da cikin jikinta kai ke da matsala dashi, abun takaici ma mallam wai ka rasa waxaka aura sai bazawara wacce ta gama yawon dakuna? Kuma nasan kasan  bakar Annoba ce, kowa na gudunta ammh da ya ke kai shashasha ne sakarai sai ka kwasa ka kawo mana cikin zuru'ar mu ko?
Ta fad'a ta na kallonsa cikin Takaicinsa.
Sadiq daman yasan haka zata Faru sai ya yi shuru ya na jin Umma ta na ta zagin Hasiya ta na aibata ta.
Ita kam ai sha kumdum ne bazai iya kare Siya a gabanta ba.
Ammh dai bazai ki gayamata abunda Allah yace ba.
Cikin sanyin murya yace"Umma miye Laifin zawarawa ? Su ba Mutane ba ne? Sannan me yasa a ke son ware su daga cikin mata? Ai suma Mutane ne kuma ba su suka kaddaro ma kansu mutuwar aure ba kaddaran Allah ne, Umma ko acikin ya'yan ki suma Allah zai iya jarbtan daya daga cikin su da Mutuwar aure in wannan ya faru sai ki ce mene?
Umma ta yi hangam da baki ta na kallon Sadiq ya na cigaba da fadin"Kuma Umma sunan nan da kike kiran siya da shi bai kamata ba, ba kyau musulmi ya rika aibata musulmi  dan'uwansa balle kuma ya yi masa Dariyan kaddaransa  dalili shine shima bai wuce kaddaran haka ta fada masa ba, kuma Umma duk fa karya ce ba wani Canfi a addinin mu, bamu san shi ba, Qur'ani ya koya mana sanin Tauhidi da iklasi kuma ni a iya ilimin da na ke da shi nasan cewa Wani abu bai isa ya samu wani bawa ba face abunda Ubangiji ya Shirya masa."
Umma sai kallonsa ta ke yi kamar ta kai masa duka, Sai da taga ya kara wani gyara zama zai kara shiryamata magana Fusace ta dakar dashi da cewa"Kai dalla gafarachan, ni zaka zo ka zauna da d'an iliminka na cikin cokali kana gayamin nima za'a iya sakar min ya'ya su zama zawarawa ?
Cikin mamaki yace"Ni fa ba."
"Ka rufemin baki nace ko? Karya na yi maka ba haka ka zauna anan wajen kana fad'amin ba, tashi ka fita ni bazan gani ba Tunda mace ta saka ka fara musu da uwarka da yan'uwanka daman Tuni ka nuna musu iyakarsu ai sai kaje ita ta zame maka uwa da yan'uwa"
Zai kara magana Umma ta mike ta na fadin"Kada ka fita di'n , ni bari na bar maka falon."
Jiki a sabule ya fita daga bangaren Umma Abba baya nan ammh sun yi waya yana nan dawowa.
Ya dauka ina bangaren Innani sai da yaje yaga ba na nan daga ita sai Farida.
Daman sanda aka yi wannan Cases din bata nan taje ganin gida chan Shinkafi.
Innani ta rika ina ta saka dashi shi kuma yana mata cin magani.
Kula da hakan da ta yi ne yasa tace"Nifa tuni na Saduda na bi Allah Tunda Sulaimanu ya yi min nasiha ina ni ina ja da Abunda Allah yace ayi, Uhm ni wai ita sulsanan Salamatu ta rike ta ta ce bazata koma gidan ka ba ne magajin gida?
Kai Tsaye yace"Haka tace"
Innani ta yi shuru kafin tace"Ba abun na yi mgana ba yanzu sai ace na so bare naki d'an gida."
Kai Tsaye Assadiq yace"To gwara ki yi shurun zai fi miki alheri."
Daga haka suka cigaba da Hirarsu tace ina Matar tasa yace yana ga tana bangaren Mama.
Innani ta tabe fuska kafin tace"Da ba nan ka kawomin ita ba, wai ni yaushe ne zata haihu har yanzu shuru ban ji an ce ta sauka ba?
Sadiq yace"Ki tayata da addu'a Innani ta na watan haihuwanta ne"
Innani ta fara jero addu'o'in Ga Hasiya Sadiq na amsa mata da Ameen
Da yaji dadi kai Tsaye yace"Ke zaki zo mata ma zaman arba'in na Jego."
Innani ta washe baki ta na fadin"Allahu akbar Allah ya nuna min ranar da wannan albarka zata sauka a gidan Magajin gida.
Ya jima a bangarenta sai da Abba ya kirasa yace ya dawo sannan ya yi mata sallama ta na ce masa ya kawo mata Hasiya bangarenta ta zauna har ta na rage murya ta na fad'in Tunda salamatu dai ta cire Allah a ranta ba mutumtata Baiwar Allah zata yi ba. shi dai bai ce komai ba sai Dariya kawai da ya yi.
Bai nemeni ba, sai da yaje shashen Abba suka gaisa ya kuma zauna ya karanta masa komai da Umma ta tareshi da shi.
Abba ya yi mirmishi kafin yace"Rabu da ita, ina mai tabbatar maka itace zata yi kaffara ammh kamar yadda na fad'amaka ba wacce zaka saka saboda wata."
Sadiq yace"To Abba ya zan yi? Umma taki fahimtata."
Abba yace"To ka nemi matarka ka lallasheta mana."
Da sauri yace"Duk su Sajida sun gama zugata bata ko daukan wayata, Allah
Showing 42001 words to 45000 words out of 116366 words