*ASM Bk2001* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 1 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI Wani mugun bugu kirjin Fatuu ya fara yi tamkar ana mata luguden ta6are ganin abunda ke faruwa ta cikin glass d'in hannuwanta har wani kerma suke saboda tsabar rud'ewa da razana don abune wanda bata ta6a ganin Haisam d'in yayi ma wata Mace ba tunda take dashi, lokaci guda ta tambayi kanta wacece wannan? Kasa jurewa tayi ta bud'e Motar ta fita ta tsaya a jikin kopar tana k'are mata kallo can ta furta "AUNTY FANAN.....!" yadda ta furta da matukar razana, Ji tayi sam kafafunta suna niyyar kasa daukarta saboda kermar da suke yi ga wani irin bugu da kirjinta keyi mata saboda tsabar razana, tambayar dake ta faman kai kawo acikin zuciyarta itace, mike tsakanin Ya Handsome da Fanan da har yake mata hakan? Ko k'annanshi da suke uwa d'aya uba d'aya bata ga yana masu hakan ba sai ita da take Cousin d'inshi, to ko dae dama soyayya suke da ita ne? Damm! k'irjinta yay mata wani Mugun bugu yin wannan tunanin lokaci guda kuma taji fitsari ya d'aure mata mara yana niyyar zubo mata da sauri ta nufi gida ko kopar motar bata rufe ba ga wani duhu da take gani da kyar ta shiga gidan don har wani jiri jiri take gani tsabar rud'ewa da kuma fargaba, toilet ta shiga tayo fitsarin tana fitowa ta nufi d'akinta ko ta kan ta duba gwaggo bata bi ba tana shiga ta fad'a saman gadonta ta duk'unk'une wuri guda sai faman zare ido take........ Nufar gaban Motar sukae hannunsu cikin na juna Fanan ta kalli wadda ke a mazaunin driver itama da gani hutu ya zauna mata duk da ba fara bace irin fatar jikinta za'a iya kiranta da chocolate fuskarta lumi tana da kyau ba laifi, da Murmushi Fanan tace "Khairat meet mah Babe" itama Murmushin take ta mik'o mashi hannu tace "Hi Haisam it's nice meeting u" aikuwa da sauri Fanan ta ka6e hannun tace "he don't do dat" dariya sosae khairat d'in tayi dama tsokanace kawae ba wani abu ba don tasan irin Mugun son da take ma Haisam dole ne tai kishinshi sosae, gaisawa sukai da haisam tace "so ga heartbeat d'inka na kawo maka sai a bani tukuici" fuskarshi da Murmushi yace ta fad'i abunda take so tace "bawani abu babba nike so ba just babynka zaka kawo man ta kwana gidanmu don nayi ta kwanan man but she refused" kallon Fanan d'in yay ta d'an yamutsa baki ta girgiza mashi kai alamar bazata je ba ta kwantar da kanta a shoulder d'inshi, khairat tace "so now da babe d'inki ke gefenki shine zaki gujeni ko, it's owk zamu koma india inda zan rama ne" k'ayataccen murmushinta mai k'ara mata kyau sosae ta saki tace "kar ki damu Babe zai kawo ni in spending day" yar harara ta wurga mata tace bata so tana kokarin tashin Motar Fanan na d'aga mata hannu tace sai sunyi Magana daga haka taja ta tafi, wani kallo mai wuyar fassarawa yayi mata ta nok'e kai tana dariya har jerarrun hakoranta farare tass suka bayyana yace "Why baki sanar dani about your coming today?" cikin muryarta ta yan gayu tace "am so eager to see u babe shiyasa na baka huge suprise" ta k'arasa Maganar tana kashe mashi ido, hannu ya kai yaja dogon hancinta tayi yar k'ara yace su shiga ciki har zasu juya tace mashi Zarah fa Hajiya ta gaya mata sun fita outing tare sai lokacin ma ya tuna da Fatun na acikin Motar har ya juya ya hango kopar a bud'e ba tare daya kawo komae ba yace yana tunanin ta shiga gida ma, still hannunsu na cikin na juna suka nufi Motar tace ya zagaya d'ayan side d'in ita ta shiga side d'in driver tajasu suka idasa gidan bayan Officer CD ya bud'e masu gate, bayan sun shige ya rufe gate d'in ya dawo kan bencin daya tashi ya kalli d'ayan Officer yace "ita wanccan d'in wacece wai, ba itace naga dazun an kawo a jeep d'in nan ba?" yace mashi "eh itama jikar Hajiyarce baka ganin kalanta na zuwa" "Itama ta wurin Hajiya Maryam d'ince kenan?" kai ya d'aga mashi alamar eh yace "Ma sha Allah amman duk tafi yan uwanta kyau gaskiya ni ban ta6a ganinta ba sai yau" Officer ya amsa mashi da eh ai bata cika zuwa ba kuma yanzu tana karatu a kasar waje ne, tana ruke da hannun Haisam suka shiga falon Hajiya lokacin tana zaune kan kujera tana kallon tv, Fanan ce tayi sallama hajiya ta maido idonta kansu tana kallonsu da Murmushi suka nufi 2 seater suka zauna Hajiya tace "ina ta nemo ka" yana Murmushi yace "mun dawo ne" "Ai ce man tayi in ta raka k'awarta bazata shigo ba har sai ta nemo ka wai,nace to Allah ya bada sa'a da yake ma akwae gidajen radio isassu maji cigiyarta in an tsinceta" d'an kallon fanan d'in yay still murmushi take kanta a saman kafad'arshi Hajiya taci gaba "sai kawae ganinta nayi kaman daga sama fa ni abun mamaki ma ya ban har saida na kira uwar tata nai mata korafin baza'a sanar mutum zai zo ba a shirya masa take ce man wai ita ta hana a sanar mana tana so ne ta bamu mamaki nace aikau ta bamu mamakin gashi tazo ma tak'i cin Abinci wai sai kazo zaka bata a baki nace ai sai taita jiranka tunda ita ba ranar da zata girma da hakan" shidae Murmushi kawae yake can ya mik'e ya d'agata ganin zasu nufi Dining area yasa tace mashi "but Babe u need to take bath ka dawo daga wani wuri nasan ka gaji" girgiza mata kai yay suna nufar dining table d'in yaja kujera ya zaunar da ita yace "eat first" yaja kujeran gabanta shima ya zauna k'in ci tayi wai sai dae ya bata a baki tayi missing hakan dole a bakin ya rink'a bata cike da kulawa, bata wani ci mai yawa ba tace ta koshi yace bai yarda ba tace ai ta d'an ci agidansu khairat tunda acan suka fara sauka sannan ya kyaleta, k'ara kama hannun juna sukai suka nufi cikin Falon zasu fita yace ma Hajiya zaije yay wanka tace to,ganin zasu fita tare tace ma Fanan bazata jirashi ya dawo ba ta mak'e mata kafad'a wai zata je ta za6ar mashi kaya ne, d'an ta6e baki Hajiyar tay tace adawo lafiya. Jama'a ina Fatuu??? Tunda ta kwanta bata mik'e ba sai faman sak'e sak'e take aranta ga wata irin fargaba data mamayeta ,fitowa gwaggo tay daga dakinta idanunta suka sauka kan takalman Fatuu dake ajiye a bakin kopa da mamaki aranta tace wannan ai takalman da Fatuu ta fita dasu ne ta dawo ne, nufar d'akin tayi tana kwala mata kira tana jin muryar gwaggon ta rufe fuskarta da gyalenta dake yashe gefe yabar saman kanta, d'aga labulan tayi ta hangota a kwance har lokacin da mamaki akan fuskarta ta kira sunanta amman bata amsa ba har saida ta k'ara kiranta sannan ta amsa tace "yaushe kuka dawo ne?" daga yadda take tace "yanzu ba dad'ewa Kawu shi6ado na gaidaki sun bada sak'on dawon Fura da Nono ma akawo maki yana Mota" da kyar take Maganar hakan yasa gwaggon cewa "To lafiya kika wani dukunkune saman gado?" shiru ta d'anyi tana tunanin abunda zata ce mata can tace "banjin dad'i ne kaman zazza6i zai kamani nike ji shiyasa ma dana shigo ban maki Magana ba" shiru gwaggon tayi tana k'are mata kallo kafin tace "ina shi yayan naki yake?" "Muna dawowa yaga sun yi bak'i ya tsaya wurinsu shine ni kuma na shigo" jinjina kai tayi tace "halan kinyi wasa da ruwa ne ko, nasan halinki sarai baki ganin ruwa ki k'yale" sai lokacin ta cire gyalen fuskarta ta bayyana ta kalli gwaggon tace "a'a wllh ai Ya Handsome bazai barni ba kawae dai banjin dadin jikinne" "To Allah ya sawake ki tashi kici Abinci sai kisha Magani" tace "na k'oshi da Abincin bari dae insha maganin kaina ciwo yake man sosae" tana gama Maganar ta saukko daga gadon da k'yar ta tunkari kopa gwaggo ta saki labulan ta koma d'akinta ta d'aukko mata Maganin ta fito ta bata, ganin yamma tayi sosae yasa tace ta shiga Falo ta zauna Magriba ta kusa ba'ason kwanciya a irin wannan lokacin in tayi Salla sai ta kwanta tace mata to. Bayan sun shiga Parlon Haisam sosae Fanan ta yaba da tsarin parlon, Haisam yace ta zauna bari yaje yay wanka ya juya zai nufi hanyar Bedroom kawae sai ji yay tace "should i come and help?" cak ya tsaya ya juyo yay mata wani kallo tasa dariya daga haka ya juya yana shiga Corridor ta d'an d'aga Murya tace "Soon i would be doing dat to u Babe" girgiza kai kawae yay ba tare daya juyo ba ya tura kopar Bedroom din ya shige, bayan wani lokaci ta mik'e ta nufi Bedroom d'in sanin yana toilet, bin d'akin tayi da kallo kafin ta nufi Closet d'inshi ta bud'e dan dudduba kayan tayi ta za6o mashi wanda zai sa ta d'aura su a gefen gado ta koma gaban Dressing mirror ta jawo drawer chest ta sama ta daukko kwalin agoguna data gani ta fiddo wadda zata hau da kayan ta daurata samansu kafin ta mayar da kwalin daga haka ta juya ta fito falo, bai dau wani dogon lokaci ba saboda Magrib tayi ya fito sanye da bathrobe yana ganin kayan data ajiye mashi yay wani kayataccen Murmushi, bai dau wani dogon lokaci ba ya gama shiryawa cikin kayan ya fita tana zaune kan L-shape idanunta akan tv tana kallo jin fitowarshi yasa ta mik'e ta nufeshi tana mashi Murmushi ya kama hannunta suka fita, saida ya rakata har bakin entrance d'in falon Hajiya sannan ya juya ya wuce Masallaci da aka fara kiran salla itama tana shiga d'akin Hajiya ta wuce don tace bata zama ko wane d'aki sai nan lokacin Hajiya ta kabbara salla ta wuce Toilet tayo wanka ta fito d'aure da farin towel, trolley d'in kayanta ta d'aura gefen gado ta bud'e ta fiddo riga da wando marasa nauyi rigar off shoulder ce blue sai wandon baki,bayan ta shirya ta d'aukko d'aya daga cikin hijjaban Hajiya dake cikin wardrobe tasa itama ta kabbara sallar, bayan an gama sallar isha gaba d'aya suna zaune a falon suna fira Fanan na manne jikin Haisam sai kace mage Hajiya tace "wai ni ina yar tafiya ne tunda kuka dawo banji d'uriyarta ba sun gaisa da Auntynta Fanan kuwa ma?" Fanan d'in tace "No ban ganta ba ta shiga gida ne bayan sun tsaya so bata zo wurina ba" Hajiya tace "aikuwa yakamata a aika masu da abubuwancen tunda kace d'aya ledar furar tasu ce ga kuma kifi shima a d'ibar mata Dije ta ga tsarabar Dam bari Saude ta je ta kai masu" tana rufe baki Fanan tace "ki kawo mu kai masu mana sai in gaisa da granny d'inta" Saude ta k'wala ma kira bayan ta fito ta gaisar dasu gaba d'aya Fanan na Murmushi ta amsa mata, umarnin ta d'ebo rabin kifin a leda sannan ta d'aukko leda d'aya ta fura da nono ta bata, ba 6ata lokaci ta kawo mata, mik'ewa Fanan tayi ta nufi Bedroom ta yafo d'an madaidaicin veil ta dawo hannunta ruk'e da wata yar babbar leda mai handle tace ma Haisam su je yace taje ita kad'ai cike da shagwa6a tace ita da bata san gidan ba Hajiya na dariya tace "ka rakata mana ita da ke bak'uwa" kafeta yay da idanu yana mata wani kallo ya d'an lumshe ido kafin ya yunkura ya mik'e yace suje ta d'auki ledojin ta bashi d'aya ya rike tace ma Hajiya sai sun dawo, lokacin da suka isa kopar gidan tsayawa yayi yace ta shiga zai jirata amman tak'i wai ita da ba'a sani ba bashi ne zai gabatar da ita ba yace to ta shiga tace zai shigo tace to, suna a Falo gwaggo na zaune kan kujera idonta akan tv Fatuu kuma na kwance kan darduma dake shimfide kan Carpet tun bayan data gama salla tai kwance wurin da k'yar gwaggo ta samu ta dan ci Abinci kad'an don duk jin bakinta take ba dad'i, da zazzak'ar muryarta ta kwad'a sallama har saida gaban Fatuu ya fad'i, amsawa gwaggo tayi ta tashi ta nufi hanyar fita ta tsaya bakin kopa tana kallonta har saida gabanta ya d'an fadi ganin wadda tay sallamar a d'arare tace "Maraba ki shigo" k'arasowa tayi gaban gwaggon ta aje ledojin hannunta tace, "Ina tare da Ya Haisam zai shigo" ta fad'a da hausarta mai dad'i gwaggo na jin hakan da sauri tace "to to ba wani abu kice ya shigo" juyawa tayi da d'an d'aga murya tace "Babe Come in" da sallama ya shigo gwaggo ta idasa fitowa tana amsa mashi tay masu nuni da cikin Parlon tace su shiga,cire takalmanshi yay ya shiga Fanan ma ta daukki ledojin tabi bayanshi suka zauna tare saman 3 seater gwaggo ma ta zauna saman 1 seater, cikin cool voice d'inshi ya gaida gwaggon ta amsa tayi mashi ya gajiyar tafiya da godiyar ziyara Fanan ma ta gaidata da fara'a itama tana mata dariya ta amsa shiru ta d'an biyo baya sai Murmushi suke ma juna can gwaggon tace"ban wayeki ba ko bak'in da Fatuu tace an yi ne" "Eh nine na zo daga Lagos" gwaggo tace "to yar wajen Hajiya Maryam ce kenan, to babbar ce ko k'aramar ni sunanku had'e man yake wllh" ta fad'a tana dariya Fanan d'in tace "Fanan ce babban", "Ah kice Amarya ce kenan" tana dariya tace "eh nine" tana rufe baki Haisam dake latsa waya ya d'an bugeta da hannunshi ta juya da sauri tace mashi "What?" shiru yay bai d'ago ba bai kuma ce mata komae ba gwaggo na dariya tace "ai kwanaki can muna fira da Hajiya take gaya man anyi baikon ku tuni amman sai kin gama karatu za'ai bikin, ko kin ma gama ne?" "Yea but zan koma akwae wani exam da zamu yi shine final", "To ma sha Allah, Allah ya bada sa'a" tace Amin, kokarin mikewa gwaggon tayi tana Fad'in ta barsu ko ruwa Fanan din tace "ba wani abu granny yanzu munsha ruwa harda Abinci" gwaggo tace "amman dae yakamata kisha na zumunci ko" tana dariya tace to abata, bayan gwaggo ta kawo mata ruwan da lemu ta fara kokarin zuba mata a Cup tana ta barshi zata zuba tace a'a ai ita bak'uwa ce ba'a barta da aiki ba, bayan tasha ta aje cup tace ma Gwaggo ga kayan sis Zarah gwaggo na dariya tace tsarabar tafiya tace eh ta nuna nata tace wannan ita ta kawo mata gwaggon tayi mata godiya sosae tace Allah ya bar zumunci, kallon inda Fatuu ke kwance tayi tace "itane ke bacci" gwaggo tace "eh tun d'azun take ta faman kwanciya tunda ta dawo wai bata jin dad'in jikinta kuma kanta na yi mata ciwo" ta kai hannu tana kokarin tashin Fatun Fanan na ta kyaleta gobe sun gaisa, duk abunnan da suke kaf tana jinsu jikinta ya mutu murus a inda take ba kamar data ji Maganar aure dake tsakaninsu yanzu ta tabbatar da abunda zuciyarta ke zargi, kenan ita ba sonta yake ba? Wannan tambayar ita ta tsaya mata har wani tuk'arta take a k'irji kaman zata yi amai, tadata gwaggo ta shiga yi tana Fad'in bari dae ta tashi su gaisa bata tunanin baccin yayi wani nisa tana cikin tashin nata taji wani amai ya taho mata da sauri ta tashi tsaye hannunta dafe da bakinta tayi hanyar fita Falon da gudu,tana fita ta nufi hanyar Toilet saidae tana kaiwa saitin kitchen ya zubo mata da k'arfi ta durkushe anan tana kwara shi sai kace yan hanjin cikinta zasu fito, a rud'e Fanan da gwaggo suka bi bayanta suka nufeta da sauri Fanan ta duk'a ta dafata tana Fad'in "Sannu Sis Zarah" gwaggo ma sannun take ta mata duk Fanan tabi ta rud'e, da k'yar aman ya tsaya tasa hannu guda ta dafe gaban kanta tana nishi da karfi yayin da d'ayan hannun ke dafe da k'irjinta Fanan ta kalli gwaggo tace "granny pls ki bamu ruwa" da sauri tace to ta nufi kitchen ta d'aukko wata yar roba taje bakin fanfo ta taro ruwan, bayan ta kawo mata tallabo kan fatun tayi ta zuba mata a baki tace ta kuskure bakin kafin ta wanke mata fuskar, d'agata tayi ta nufi cikin parlon da ita gwaggo kuma ta fara gyara wurin, sauran ruwan roban data sha ta daukko ta bud'e murfin ta kafa mata abaki tace tasha, sosae tasha ruwan don kirjinta wani irin zafi yake mata, "Sannu sis Zarah" kai ta d'aga mata tana kokarin kwanciya, bayan ta kwanta matsawa Fanan tayi gefenta ta zauna tana d'an tatta6a jikinta ta tambayeta ko cikinta ya lalace ne fatun ta girgiza mata kai alamar a'a, duk wannan abun Haisam na zaune yana kallonsu ko lokacin da take yin aman yana ji, dawowa gwaggo tayi ta zauna inda ta tashi Fanan ta tambayeta tasha Magani ne tace eh ta bata paracetamol d'azun da tace kanta na ciwon, ta6a jikinta ta sake yi jin da d'an zafi yasa ta kalli Haisam tace tana tunanin Malaria ce ke damunta abunda yafi ayi mata allura kawae, kai ya d'aga mata ya mik'e yace bari ya d'aukko mota suje su siyo tace ok, bayan ya d'aukko Motar horn yayi mata ta mik'e da sauri tace ma gwaggo bari suje su dawo tace to, komawa tayi kusa da Fatun bayan sun fita ta zauna tana mata sannu ita dae kai kawae take d'aga mata, bayan kaman minti 30 suka dawo Fanan ce kawae ta shigo shi Haisam yana waje cikin Mota duk ciwon da Fatun keyi ya dameshi ganin lafiya lau suka dawo da ita amman har yayi tsanani haka, Artemether da paracetamol injection suka siyo, had'a allurar ta shiga yi bayan ta gama tayi mata har saida gwaggon tayi mamakin yadda ta tsaya tayi mata allurar don ita in zata yi mata wani lokacin sai tayi fama da ita da can ma da bata girma ba haka wani lokacin sai tasa Amadu ya ruke mata ita, bayan ta gama ta tambayi inda dustbin yake gwaggo ta mik'e ta amsa taje ta yado su ta dawo Fanan tace ma gwaggo yakamata taje d'aki ta shiga Net saboda sauro tace to, mik'ar da ita tayi suka nufi hanyar fita gwaggo na biye dasu ta tambayi ina d'akin da zata kaita gwaggo ta nuna mata dakinta suna shiga ta nufi gado da ita ta taimaka mata ta kwanta sai faman sannu take ce mata kai kawae take d'aga mata ita kanta Fatun bata san mi take ji game da Fanan d'in ba ita kawae abunda ya dameta shine Ya Handsome bai sonta ba zai Aureta ba, a hankali kwalla suka fara ziraro mata daga kwancen ta juya masu baya yadda bazasu ga Fuskar tata ba, "Granny ni zan tafi Ya Haisam na jirana gobe in sha Allah zanzo in yi mata second dose" godiya sosae gwaggo ta shiga yi mata tana cewa Allah yasaka da Alkhairi ya bar zumunci ta amsa da Amin juyawa tayi ta dafa jikin Fatuu tace "Sis Zarah Allah baki lpy kinji" kai ta d'aga mata kawae ta juya ta tafi gwaggo tayi mata rakiya har zaure saida ta lek'a ta k'ara yi ma Haisam godiya kafin ta komo daki wurin Fatuu, a gefen gadon ta zauna tana kallonta yayin da take ta sak'e sak'e aranta game da silar ciwon Fatun tsoronta kar ace abunda take tunani ne sanin inda suka je ciwon na iya tasar mata, yin wannan tunanin yasa da sauri ta girgiza kai a fili tace "in sha Allahu bama shi bane" dafata tayi tace mata sannu ta d'aga mata kai ta tambayeta ko tana son wani abu ta girgiza mata kai alamar a'a tace "to tashi ki rage kayan jikinki bari in je in d'aukko maki wanda zaki canza" bayan taje d'akinta ta d'aukko mata kayan bacci da taimakon gwaggon ta tashi ta canja kafin ta koma ta kwanta gwaggo ta lullube mata rabin jikinta tasa mata Net. Bayan sunyi parking Motar a parking space suka fito sukai ma juna irin rukon nan na turawa wato a sak'ala hannu suka nufi part d'in Hajiya, lokacin da suka shiga ba kowa a falon hakan yasa suka wuce bedroom dinta lokacin har ta kwanta amman bata yi bacci ba wutar d'akin ma a kunne take da alama jiransu take, jin motsin shigowarsu yasa ta d'ago ta kallesu suka nufeta suna Murmushi suka zauna a bakin gadon, "Ai nayi zaton Zarah ta rik'e ki acan zaki kwana don nasan dole zatayi farinciki da zuwanki" da sauri Fanan ta girgiza mata kai da yar damuwa tace "Sis zarah ba lpy dat's why we stayed a bit long" yunkurawa Hajiya tayi ta tashi zaune da mamaki kan Fuskarta tace "Ba lpy kuma miya sameta" fad'i mata abunda ya faru Fanan din tayi harda uban aman da tayi Hajiya tasa salati ta kalli Haisam dake saurarensu tace "dama bata lpy kuka dawo" kai ya girgiza "No lafiyanta lou wai bayan ta shiga gida tace ma grandma d'inta tana jinta abnormal and kanta na mata ciwo sosae" jinjina kai Hajiya tayi da yar damuwa akan fuskarta tace "tohhh, Allah ya kyauta yasa ba mutanenta bane kuwa tunda anje wurin ruwa" cikin rashin fahimta duk suka kalleta Fanan ta tambayeta suwaye mutanenta, "Jinn nike nufi" waro ida Fanan tayi a rud'e tace "Ajanu!" yadda tayi Maganar har saida Hajiya ta d'anyi dariya ta jinjina mata kai alamar eh, "Dama tana dasu?" Haisam daya kasa hakuri ya tambaya, Hajiyar tace "Eh mana amman basu kada ita yanzu saidai su sata ciwo, tama dad'e gaskiya bata yi ciwon da take irin nasu ba" jinjina kai yay taci gaba da cewa "ai na Mahaifiyarta ne suka komo kan Fateemar amman basu cutar da ita gaskiya sai rashin ji da suka saka mata" wani d'an guntun Murmushi haisam d'in yay ya furta "the whole things make sense now", "but su dama basu son aje wurin ruwa?" Fanan da duk alamun tsoro ya bayyanar mata ta tambaya dariya hajiya tasa tace "ai kinsan su ko ina akwae su ba iya wurin ruwan ba saidae akwae inda zaki ga sunfi zama kaman toilet to wurin ruwan ma matattararsu ce, kai bamma tunanin su ne gaskiya k'ilan dai ta de6o sanyi ne kawae shine ya tado mata zazzabin" jinjina kai Fanan tayi tace Allah dai ya bata lafiya hajiya ta amsa mata da Amin, mik'ewa Haisam yay yace zaije ya kwanta Hajiya tace "Allah ya bamu Alkhairi" kokarin mikewa Fanan ta fara yi tace bari ta rakashi yace tay zamanta tace ko bakin kopa ne, suna fitowa yace ta koma sai kawae ta jingina bayanta da bango tana mashi wani kallo mai cike da tsantsar kauna hannu ya kai ya d'an shafi cheek d'inta da wata irin Murya ya furta mata "I luv u Sweetheart" hannu tasa ta dafa hannun nashi tana Murmushi tace "dat's my breath babe" yar dariya yayi ya fara kokarin wucewa ta kamo hannunshi ta baya ya juyo da narkakkun idanu tace "Gud nyt nd Dream of me" lumshe ido yay kafin yace "Always" d'ago hannun tay tayi mashi kiss a bayan hannun kafin ta saki ya tafi, saida ya kai bakin kopar fita ya juya ya kalleta yay mata alamar ta shiga cikin d'aki da kanshi,blowing kiss tai mashi kafin ta d'aga hannu tay mashi bye bye ta juya ta shige.......... Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM2002* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 2 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ..........Washe gari da suka tashi ta d'an ji sauk'in jikin nata kawae yanzu fargaba ce tafi damunta hakan yasa duk bata jin dad'in kirjinta bayan tayi sallar Asuba komawa tay tayi lamo kan gado sai sak'e sak'e take aranta, yanzu shikenan ta rasa ya Haisam, tana ji tana gani zai yi auranshi ya tafi ya barta, haka dai take ta tunane tunane tana matse k'wallan dake zubo mata ba tare da gwaggo ta ankare ba don ita duk tunaninta bacci Fatun ta koma, Wuraren k'arfe tara saura tazo ta tashe ta tayi karin kumallo, bayan taje tayo brush ta zauna don yin breakfast d'in saidai sam tama kasa cin komae don bata jin dad'in bakinta gwaggo dake zaune gabanta ta lura da hakan tace mata ta daure in taci sai tafi jin dad'in jikinta ta dai d'aga mata kai kawae, da k'yar ta d'an tuttura ta mik'e zata kwashe kayan gwaggon tace ta bassu taje ta kwanta in ta gama zata d'auke, bayan ta gaman ta kwashe komae ta kai Kitchen bata dawo d'akin ba saida ta had'a ma fatun ruwan wanka a toilet tace ta daure taje tayi ko ta ji k'arfi, d'akinta ta koma ta cire kayan jikinta ta d'aura towel ta yafa mayafi kafin ta fito ta nufi toilet walking slowly don duk jikinta ba k'arfi, bayan ta fito doguwar rigar material kawae ta zura ta haye gado taci gaba da tunane tunanenta, Wuraren k'arfe 11 Fanan ta farka tun bayan sallan Asuba data koma tana saukko da k'afafunta k'asa idanunta suka sauka akan wata yar guntuwar farar takarda dake ajiye kan bedside drawer, hannu ta kai ta d'auki takardar tana duba rubutun dake jiki kamar haka, _Went to work_ _Luv u_ Shine rubutun dake ajiki Murmushi ta saki sanin Haisam ne ya ajiyeta, baki ta kai paper d'in ta manna mata kiss had'i da furta Luv u too Babe,maidata tayi inda ta d'auketa ta ajiye ta wuce toilet don yin wanka bayan ta fito ta shirya cikin skinny jeans blue da farar top bayan ta gama shiryawa ta dauki wayarta ba tare data rufe kanta ba ta saki brown gashinta ya zuba gefe da gefen fuskarta ta nufi Parlor ganin ba Hajiya a falon yasa ta nufi d'akin Saude tana kwance kan katifa tana huta gajiyar aikin gidan data gama bada jimawa ba, zazzak'ar muryarta saude ta jiyo tana yi mata sallama hakan yasa ta tashi zaune da sauri suka had'a ido ta sakar mata Murmushi itama sauden Murmushin take mata don ba k'aramin burgeta take ba, "Ina kwana" Saude ta gaidata ta nufo inda take ta zauna gefen katifar da Murmushi tace "kin tashi lpy ya aiki" tace "Alhamdulillah" shiru suka d'anyi kowa Murmushi ne akan fuskarshi can Fanan d'in tace "Hajiya ta fita?" "Eh bata dad'e da fita ba taje wurin aiki ne" jinjina kai tayi sauden ta kuma cewa "ga breakfast can na shirya maki a kan table", " Owk thanks", "Babe ya shigo kuwa yayi breakfast?" ta tambaya tana kallon sauden,shiru ta d'anyi don bata gane babe d'in da take nufi ba gane hakan yasa fanan d'in cewa "I mean Ya Haisam" da sauri tace mata "eh ya shigo d'azun da shirin zuwa aiki ya shiga d'akin Hajiya kafin ya fito ya tafi, "yayi breakfast?" kai ta girgiza mata "a'a ai bai yin breakfast yake tafiya gaskiya sai dai wani lokacin in hajiya ta matsa mashi yake dan yi shima dai kad'an" jinjina kai tayi tace "har yanzu baison cin abinci ko?" yar dariya Saude tayi kafin tace "eh to gaskiya yana ci amman fa ba sosae ba shima dai sai Hajiya ta matsa mashi yake d'an ci da d'an yawa" jinjina kai ta sake yi ta fara kokarin tashi Saude tace "Breakfast d'in zakiyi inzo in zuba maki?", "No don't worry zanyi serving kaina" "Don Allah ki bari kar aikin yayi maki yawa" d'an waro ido tayi alamar mamaki tace "miye ne aiki ciki just serving Myself ai kene mai yin aiki so just relax" tayi Maganar tana mata alamar ta kwanta da hannu ta juya ta nufi kopa Saude ta bita da ido tana Murmushi aranta take ayyana kirkin yarinyar yayi yawa sam ba halinsu d'aya da yar'uwarta ba, tana fitowa bata nufi dining don sai taji bata son yin breakfast d'in ita kad'ai, Bedroom d'in Hajiya ta koma ta d'aura boyfriend jacket bak'a mai d'an ratsin fari ta yafa d'an k'aramin bak'in gyale ta fito, gidansu Fatuu ta nufa wayarta ruk'e a hannunta tana zuwa bakin gate ta tsaya suka gaisa da su Officer tana ta Murmushi suma duk suka washe mata baki bayan ta wuce ne su kau yabonta, tana shiga gidan ta tsaya bakin kopa ta rafka sallama da zazzakar muryarta "Salamu Aleeikum" tana niyyar k'ara yin wata gwaggo ta fito daga cikin d'akinta tana amsa mata sallamar suna ganin juna suka saki Murmushi gwaggon ta nufeta tana Fad'in "Ah ya kika tsaya anan ki shigo mana y'ata" nufota tayi suka had'e a tsakar gidan d'an side hug tay ma gwaggo tace "ina kwana granny" da fara'a tace "lafiya lou y'ata ya gajiyar tafiya kuma" "Babu shi" ta bata amsa gwaggon na niyyar ce mata su shiga falo tace "ina Sis Zarah ya jikinta fa" tace mata da sauki sosae tana cikin d'aki "owk bari in ganta" tare suka juya suka nufi d'akin gwaggo Fatuu da duk abunda suke tana jinsu tana jin sun nufo d'akin tayi saurin juyawa yadda baza'a ga fuskarta ba ta runtse idanunta sosae, suna shiga d'akin Fanan ta nufi gadon ta zauna a gefe ta kai hannu tace "Sis Zarah" shiru bata amsa ba hakan yasa ta kalli gwaggo tace ko tana bacci ne, ita kanta gwaggon ta d'anyi mamakin ganinta haka don lokacin da Fanan d'in tayi sallama tasan ba a haka take kwance ba idonta biyu har suna ma d'an Magana da ita, matsawa tayi gaban gadon ta kira sunanta da d'an karfi ba yadda ta iya dole ta amsa mata sanin gwaggon tasan ba bacci ta barta tana yi ba, "Ki tashi ku gaisa da Auntynki da tazo nasan jiya ba lalle ma in kin gane wacece ba kina cikin ciwo" d'an jimm tayi kafin a hankali ta yunk'ura ta tashi zaune ta kalli Fanan dake ta faman yi mata Murmushi murya can ciki tace mata "ina kwana, anzo lafiya" hannu ta kai ta dafa shoulder d'inta tace "Lafiya, ya jikinki" amsa mata tayi da sauki tace Allah ya bata lpy, ganin yadda take ta faman yi mata Murmushi yasa itama da kyar ta d'anyi mata na yak'e, "How are u Feeling Now?" ta tambayeta k'asa k'asa tace mata "da sauki sosae kawae bana jin karfin jikinne" still hannunta na asaman kafad'arta tace mata ta kwanta, komawa tayi ta kwanta dama bata so tashin ba cike da kulawa take kallonta kafin ta maido kallon kan gwaggo dake zaune ta tambayeta tayi breakfast tace mata eh ta d'an ci kad'an, fira suka shiga yi da gwaggon kai kace dama can sun saba tace ko ta kawo mata wani abu taci bata kaiga d'aura abincin rana ba tace mata a'a ta barshi can gwaggon ta mik'e tace bari taje ta d'aura girki fanan d'in tace mata ba damuwa bayan ta fita wayarta ta shiga latsawa tana yi tana d'an d'agowa ta kalli Fatuu can ta kai hannu ta dafa kafafunta tace "Sis Zarah am really worried about ur condition, Allah ya baki lafiya kinji" a hankali ta ware idonta kan Fanan d'in dake kallonta cike da damuwa wani iri taji don ita kanta bata ta6a tunanin zasu kasance haka da Fanan ba yadda suka shak'u sosae har ta k'agara ta ganta a zahiri saboda yadda take nuna mata k'auna bata ta6a tunanin zuwanta zai jefata a matsala haka ba, a hankali wasu yan siraran hawaye suka zubo mata tana k'okarin gogewa fanan d'in ta matsa da sauri tana Fad'in ta daina kuka zata samu lafiya bada jimawa ba in sha Allah wai akace rashin sani yafi dare duhu, wayartace ta fara ringing takai idonta kan screen d'in ganin mai kiran nata yasa ta saki Murmushin da tun bata d'auka ba Fatuu ta yanke wanda ya kirata, cikin murya mai cike da tsantsar kauna bayan ta d'auka tace, "Hlo Babe, how Work?" ta tambaya, on the other hand ya bata amsa da lafiya kafin ya tambayi tana ina tace mashi tazo ganin Zarah ne ya tambayi ya jikinta tace da sauki, "am on my coming back now" ya fad'a, d'an ware ido tay ta cire wayan daga kunnanta ta duba time kafin ta maida tace mashi amman still Working hours ne ya akai zai dawo yace saboda bata yi breakfast ba yar dariya tayi tace waye ya fad'a mashi bata yi breakfast ba yace a jikinshi ya ji, cigaba da fira sukae cike da kauna har ta tambayeshi ya taho da gaske yace eh yana driving ma suke wayan, duk Maganganun da turanci suke wayar fatuu na saurarensu a hankali ta juya ta kalli d'ayan bangaren d'akin ta shiga yin kuka sosae ta rufe bakinta da hannunta guda don kar sautin ya fita, har ya kawo kopar gidansu Fatun suna waya ta mik'e ta d'an ta6a kafafun Fatun tace zata je ta dawo, kai kawae ta d'aga mata ta juya da sauri ta fice, tana fita kopar gida taga Motarshi ta nufi d'ayan side d'in ta bud'e ta shiga suna had'a ido suka sakar ma juna Murmushi ya kamo hannunta ya rike yaja Motar da d'ayan suka tafi, suna shiga Falon Hajiya Dining suka wuce da kanshi yay serving nasu don shima bai ci komae ba awurin aiki cike da tsantsar kauna suka shiga ciyar da juna koda ya tashi komawa wurin aikin bayan sun gama marairaice mashi tayi wai ya tafi da ita gidan is so boring yace ai Hajiya bazata dad'e ba zata dawo amman ta k'iya dole yace taje ta shirya su tafi, bada jimawa sosae ba ta fito sanye cikin bak'ak'en Suit na mata kafafunta sanye da ankle strap farare irin takalman nan masu tsini sosae masu rufe diddigen k'afa da igiya sama da ake d'aure k'afa kanta ta yafa k'aramin bak'in gyale hannunta ruke da farar clutch bag data hau da rigar cikin da kuma takalmanta yayinda kunnanta ke sanye da yan kunne fashion silver masu matsiyacin kyau hannunta na hagu d'aure da agogon diamond sai d'aukar ido take ba k'aramin kyau tayi ba, idanunshi akanta ya d'an lumshe su yana binta da wani kalan kallo ta nufo shi tana tafiya irin ta wayayyun yan boko tana zuwa gabanshi ta tsaya tana Facing d'inshi tana wani kashe mashi ido yay d'an Murmushi kafin ya kai hannu ya kama kunnanta yace dama tazo da shirin takura mashi kenan ko ta fad'a jikinshi tana dariya a lokacin idanunshi suka sauka kan gashinta dake kwance kan gadon bayanta hannu ya kai ya cire gyalen ya nad'e gashin yadda bazai fito ba kafin ya d'agota ya fara nad'a mata gyalen, Allah sarki ashe ga inda Haisam ya iya nad'a gyale da Fatuu ke tambayarshi ya akai shi da yake namiji ya iya lokacin daya ta6a nada mata har tace kumatunta sunyi kaman an tura biredi, kama hannunta yay a nutse suka tafi. Bayan Azahar Amadu ya shigo cikin gida daga Makaranta don yanzu a Poly yake Karatu don tuni ya kammala Secondary d'inshi kuma Haisam ne ke d'aukar nauyin karatun nashi shi da Tk don shima ya dasa HND bayan ya gama ND din da yake, d'akinshi ya bud'e don yanzu koparshi na a cikin gidan aka maidota lokacin da Haisam yasa aka gyara masu gidan sai aka k'ara ma zauren girma, yana shiga d'akin gwaggo ta fito daga cikin Kitchen ganin kopar d'akin nashi a bud'e ne yasa ta kwala mashi kira tace ya dawo ne don bata ji shigowarshi ba, fitowa yay ya nufo inda take tsaye yace "Eh na dawo in ci abinci in d'an huta don sai k'arfe hud'u nike da lecture" kai ta d'aga yace "ba yau zaki fara aikin rana bane naga baki shirya ba kuma lokaci yayi" da yar damuwa tace "to na tafi aiki Fatuu ba lafiya, har yanzu fa jikinta bai mata dadi wllh ina lura da ita har kuka take tayi" ajiyar zuciya ya sauke yace "amma ba kince jiya har Allura an mata ba?' "Eh anyi mata amman ai kasan ciwo ke shiga lokaci d'aya sauki sai a hankali ko, kuma ni wllh damuwata kar ace ciwon da nike tunani ne" sanin ko wane ciwo take nufi yasa Amadun cewa "in sha Allahu ba shi bane ma, amman ina ganin ki tafi aikin ni bari sai in fasa komawar kawae" tace "ayi haka bazaka samu Matsala ba?" "A'a ba wata matsala dama komawar k'ila wa k'ala ce don ba lalle ma lecturer d'in yazo ba haka yake sai anata jiranshi ya kira waya yace bazai zo ba" jinjina kai tay tace "k'ilan uzuri ne ke masa yawa kasan hidindimun rayuwa, bari to in mik'o maka Abincin sai inje in shirya don ya kamata inje tunda yau Monday akwae tsare tsaren da zamuyi" tana k'arasa Maganar ta juya ta shige kicin,bayan ta mik'o mashi abincin ta zuba ma Fatuu ta kaimata saida ta matsa mata ta d'an tsakura tace mata ta k'oshi bata jin dad'in bakinta dole ta kyaleta ta hau shirin tafiya aiki bayan itama taci Abincin. Lokacin da suka isa wurin aikin tun da suka fito daga cikin Mota ake ta faman binsu da ido dan duk wanda ya kallesu sai ya k'ara wasu da suka kafesu da idanu ko kyaftawa basa yi, da suka shiga cikin wurin wad'anda suka san Haisam da basu iya hakuri bayan sun gaisa dashi sai suce wai sabuwar Ma'aikaciya suka yi ne anan ya gabatar masu da ita a matsayin wife to be d'inshi, fatan alkhairi aka shiga yi mashi yayin da wasu ke fad'in perfect match har kiran Mutane aka rink'a yi suzo ga Fiancee d'in Zakee tanata fara'a take gaisawa da mutane, bayan sun gama gaisuwar Office d'in su Nana ya wuce da ita wanda babban Office ne don su hud'u ne aciki duk mata biyu matan aure ne sai su Nanar da wata sune marasa aure, Nana zaune tana lallatsa Computer jikinta sanye da doguwar rigar atampa gyalenta akan kafad'a taji an d'anyi knocking kopar kafin aka turota hakan yasa ta kai idanunta wurin, Fanan ce ta fara shigowa ai suna yin ido biyu da Nana zumbur ta mik'e ta dafe k'irji tace "innalillahi, wa innahu min sulaimanu wa inna hu bismillah..." tana rufe baki Haisam ya shigo tana ganinshi ta sauke nannauyar ajiyar zuciya don ta fahimci tare suke tace "Haba Zakee irin wannan ai sai ka fara shigowa kai da muka sani, ni wllh nayi zaton gamo nai yo kawae ana bud'e kopa sai inga Mutum irin wannan ta shigo tana man dariya" sauran yan Office d'inne suka sa dariya taci gaba da cewa "kad'an ya rage ban saki fitsari ba" ita dai Fanan Murmushi kawae take haka ma Haisam, "Zakee bakuwa muka yi, daga ni dae sis d'inka ce ko?" tay tambayar tana kokarin zama ta nuna ma Fanan kujera tace ta zauna, maida kallonta tay kan Haisam tace "Zakee na tambayeka baka ban amsa ba" yace "Yea she's my sis and My wife to be also" waro ido Nana tayi da sauri ta kalli fanan d'in sauran abokan aikinta ma suka kalleta ita dai sai faman sakin Murmushi take, kallon Haisam Nana tayi tace "Haba mana shiyasa ba wata mace dake gabanka ashe ashe hurul ayn zaka aura, kace duk kallon gwaggon birai kake mana Zakee" gaba d'aya suka saka dariya harda Fanan, taci gaba "Tubarkallah ma sha Allah, gaskiya had'in nan yayi ba'a Magana, duk kun dace abokan rayuwa wllh Allah yasa Alkhairi ya kaimu lokacin musha biki ya kuma maida mu damshin ku duk da dai ita Amaryar tamu bansan halinta ba" Fanan na dariya tayi mata godiya tace ai duk halinsu d'aya Nanar tace to ta zauna anan ta tantance in halinsu d'aya, dole anan Office d'in nasu ya barta aikuwa sun sha fira da Nana harda ma sauran yan Office d'in sun matuk'ar yabawa da halinta na rashin ji da kai, sai gab da za'a tashi sannan Nana ta rakata Office din Haisam wanda babban Office ne mai d'auke da duk wani abu da zaka samu a hadaddan Office na babban ma'aikaci yana da dan falo wanda anan Secretary d'inshi yake, ana yin la'asar suka baro wurin aikin saida Nana ta rakota har Mota tace tana jiranta tazo mata wuni gida tace in sha Allah Babe zai kawo ta, saida suka biya shopping mall suka yi shopping yawanci duk kayan ciye ciye ne suka siya kafin suka nufi gida. Tun bayan da gwaggo ta tafi aiki take kwance tana ta tunane tunanen rayuwarta da Haisam, a yanzu ne komai nashi ke bala'en burgeta a hankali take kai hannu tana goge kwallan dake zubo mata wanda sam ta kasa tsaidasu ga wani irin kadaici da take ji don tasan da yanzu tana gidan Hajiya ba kaman da gwaggo bata nan, da ta tuna yana tare da Fanan sai taji wani irin kunci a zuciyarta har wani zafi k'irjinta ke mata da kyar ta yunkura tayi sallar la'asar ko Addu'a ta kasa yi don ta rasa wace Addu'a ma zatayi, mik'ewa tay ta cire hijab d'in ta koma kan gado ta koma duniyar tunani tana ta juye juye tana goge kwalla, tana cikin wannan halin Haulatu tazo gidan a bakin shagon Amadu daya bude bayan ya dawo daga Masallaci ta tsaya ta gaidashi ta tambayeshi Fatuu na nan ko ta wuce islamiyya yace mata tana nan ciki kwance ai bata Lafiya tun jiya jin haka yasa ta nufi cikin gidan da sauri har tana yin tuntu6e a bakin kopar shiga, d'akin Fatuu ta nufa tana zuwa ta fad'a ciki da sallama ta nufi gadon Fatuu na jin sallamarta ta yunkura da sauri ta tashi zaune fuska jage jage da hawaye ga gashinta ya kwance yay mata rumfa, a rud'e Haulat ta nufeta tana Fad'in"Subhanallahi, wai ciwon har ya kai haka k'awata, ni wllh bansan baki Lafiya ba tun d'azun naso zuwa to sai innarmu ta tafi unguwa tabar man kula da gidan, yanzu ma islamiyya zani inata tunanin k'ilan ma kin tafi ina tambayar Kawu Amadu shine yake ce man wai baki lafiya tun jiya baku ma samu zuwa Daurar ba ko?" kaman jira Fatuu take tana jin ta fad'i hakan ta fashe da kuka mai sautin gaske ta matso ta kama hannuwan Haulat cikin kuka tace "Haulat na bani munyi kuskuren fahimta wllh" a kid'ime ganin yadda Fatun take a hargitse tace "kuskuren mi?" "Ya Handsome bai sona Haulat, bai ta6a sona ba wllh" zaro ido Haulat tayi murya na rawa tace "a..amman ke ya akai kika san hakan ko kin mashi Magana ne ya fad'i maki hakan?" cikin kuka tace "a'a ashe wai yana da wadda yake so kuma ma har ansa masu rana da ta gama karatu za'ai aurensu,yauwa ba kinsan wannan Aunty Fanan d'in ba yar uwarsu mai karatu a india to itace, jiya muna dawowa muka iske tazo baki ga yadda ta rungumeshi ba da suka had'u shima baki ga yadda yake farincikin ganinta ba, da daddare suka zo tare wai kawo man tsarabar da muka yo, da tayi ma gwaggo bayanin kanta shine gwaggon tace ko itace akai masu baiko tace mata eh ashe ita gwaggo ta sani sun ta6a yin Maganar da Hajiya, Wllh Haulat baki ji yadda naji ba wani abu mai zafi kaman wuta naji a kirjina ga kaina da yayi wata sarawa nan da nan amai ya taho man baki ga aman da nayi ba kaman yan hanjina zasu fito kuma su duk sunyi tunanin ban lafiya ne har allura suka je suka siyo ita da Ya Handsome tai man" kasak'e Haulat tayi tana sauraranta kamar gunki gabanta na fad'uwa don duk gani take itace sanadin shigar Fatun halin da take ciki..... Daidai gidansu Fatuu ya parker bike d'inshi Fanan dake bayanshi ta saukko jikinta sanye da workout outfit da alama Gym zasu tafi tare, Cire Helmet din dake kanta tayi ta mik'a ma Haisam ya amsa ta juya zata shiga gidan Amadu dake cikin shago yana ganinta ya fito da sauri don jiya da daddare bayan ya shiga gida gwaggo ta bashi labarin zuwan nata harda allurar data yi ma Fatuu, da Fara'a ya gaidata ta amsa yayi mata anzo lpy tana ta sakar mashi Murmushi, bayan ta wuce ya gaishe da Haisam kafin ya koma shago, tana shiga ta kwad'a sallama da zazzakar muryarta jin ba'a amsa ba yasa ta k'ara yin sallamar tana shiga cikin gidan a lokacin suka ji sallamar Haulat ta mik'e tana bari ta duba ita kuwa Fatuu tana jin sallamar ta gane ko wacece hakan yasa ta kwanta da sauri ta juyama kopa baya ta lullu6e fuskarta tana goge kwallar fuskar, d'aga labulen d'akin Haulat tayi ta lek'a kanta tana amsa sallamar saidae a susuce ta k'arasa amsawar baki bud'e take kallon fanan dake mata Murmushi ganin tak'i ce mata komae yasa tace mata "Sannu Gwaggo fa" a dabarbarce don bata yi tunanin zataji tayi hausa ba cikin yar in ina tace "g..gwaggo ta... ina tunanin ta tafi aiki" tace "Ok Zarah fa" da hannu ta nuna mata cikin d'akin alamar tana ciki ta nufo dakin har saida tace mata zata shiga kafin da sauri taja gefe ta shige, gadon da Fatuu ke kwance ta nufa ta zauna a bakin gadon cike da kulawa tace "Sis Zarah" shiru bata amsa mata ba ta d'aga kai ta kalli haulat tace "ko tana bacci?" da sauri tace "e..nima ban dad'e dana shigo ba na ganta haka" "Ok amman ina son nayi mata injection ne zamu fita bansan ko zamu dawo da wuri ba" haulat da tayi mata k'uri tace "to bari in tada ta" matsawa tayi ta fara kwala mata kira ba yadda Fatun ta iya dole ta yunkura ta tashi zaune a hankali ta d'an kalli Fanan din ta sakar mata Murmushi tace "Sannu sis Zarah hope u'r feeling better" dan daga mata kai tayi kafin kaman an mata dole ta gaidata ta amsa had'i da dafa kafadarta tace bari tai mata second dose d'inta kai kawae Fatun ta d'aga mata ba tare da 6ata lokaci ba ta fiddo allurar da syringe daga cikin jacket din data rufe jikinta da ita ta had'ata tayi mata, cike da kulawa tace "zamu je Gym da Babe do you need something?" wani abu fatun taji ya daki kirjinta hakan yasa ta d'an kauda kanta ta girgiza mata Fanan din tace to ta koma ta kwanta Allah ya bata lafiya daga haka ta juya har takai bakin kopa ta juyo ta kalli Haulat tace "U'r Haulat right?" da sauri haulat ta d'aga mata kai kaman kadangaruwa Fanan d'in tace "I heard u'r Zara's best friend nayi farincikin ganinki" tayi Maganar tana mik'a mata hannu a d'arare haulat ta kama hannun wani kalan taushi data ji har saida ta had'iye miyau kutt, "zanzo gidanku in gaisa da mom naki in Zarah ta samu lpy" da sauri haulat tace mata to ta d'an yake baki ita ala dole Murmushi take, janye hannun tayi tace mata ta tafi, ai tana fita Haulat bata san lokacin da a zuciyarta ta furta "Bura ubannan Astagfurullah", juyawa tayi ta kalli Fatuu suka yi ma juna k'uri da alama wutar kowa ta d'auke, a sanyaye Haulat ta koma ta zauna ganin kallon da fatuu ke binta dashi idanunta sun cika da kwalla yasa tace " itace ko?" kai ta d'aga mata alamar eh, shuru sukai kowa da abunda yake sak'awa can Haulat taji Fatuu tace "Yanzu Haulat ya za'ayi" a d'an firgice Haulat tace "Uhyumm" matsowa Fatuu tayi ta kama hannuwanta kwalla suka fara zubo mata tace "Don Allah ki bani shawara Haulat yanzu ya zanyi, wllh inason Ya Handsome in ban aureshi ba zuciyata zata iya bugawa yanzu haka bakiji yadda nike ji ba kaman ana hura man wuta ga wani bugu da take man mara dad'i" tana kai Maganar ta d'ago hannun Haulat d'in ta d'aura kan kirjinta kwalla naci gaba da zubowa, wani wahalallan miyau Haulat ke had'ewa ta k'ura ma Fatuu idanu ba tare data ce mata komae ba, "Haulat don Allah ki taimaka man kinga dama kin saba bani shawara in ina cikin mawuyacin hali kuma duk inkika bani tana man aiki don Allah ki fad'i man abunda zanyi yanzu?" nannauyar ajiyar zuciya ta sauke kafin tace "kin yarda in na baki shawara tana maki aiki? Da sauri ta d'aga mata kai alamar eh, taci gaba "to zan baki shawara amman da farko ina mai baki hakuri akan halin da kike ciki don duk ni naja maki dana yanke hukunci ba daidai ba batare da nayi la'akari da wani lokacin ko a Novel d'in muna yin hasashe yazo bai zama gaskiya ba....." katseta Fatuu tayi "ki bar d'aura ma kanki laifi ai dama kince nima ina sonshi kuma bazan gane ba sai naga ina niyyar rasashi to abunda ya faru yanzu kenan ni dai ki bani shawarar kawae" wata ajiyar zuciyar Haulat ta kara yi kafin cike da k'arfin hali tace "Shawarar da zan baki itace................. Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM2003* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 3 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* "........KIYI HAKURI FATUU...." Fuzge hannunta tayi kaman wadda Shock yaja tunkan haulat d'in ta rufe baki tana fitar da numafashi da sauri sauri tace"Hakuri! ya zaki ce in yi hakuri bacin na gaya maki ina sonshi,ni dai bazan iya hakuri ba Haulat ki taimaka ki gaya man yadda zanyi in ba haka ba na gaya maki zuciyata bugawa zatayi" nan da nan idanun Haulat suka ciko tabb da kwalla ganin wai Fatuu ce a wannan halin ita da sam so bai gabanta bata da burin daya wuce tayi Karatu amman lokaci guda komae ya canja so yayi mata mugun kamu, duk gani take laifinta ne hakan, kamo hannun Fatun tayi cikin karewar murya tace "da inada shawarar da tafi wannan da na baki k'awata don nima banson ganinki cikin irin wannan mawuyacin halin to amman ya zamuyi dole saidae fa hakurin tunda dai kinga har ansa masu biki", cikin muryar kuka tace "to ko in fad'i mashi ina sonshi don Allah ya Aure ni nima?" D'an girgiza kai Haulat tayi jin wata Magana ta Fatuu wadda daga ji bata yi tunani wurin fad'inta ba, Gyara zama Haulat tayi tace "duk da bansan ya kike ji acikin zuciyarki ba amman zan iya fahimta daga yanayinki tabbas nasan kina cikin mawuyacin hali, amman fa kisani in kika ce zaki hakan to fa ba k'aramin kuskure zaki yi ba kizo ki k'ara jefa kanki wani halin don karshe nasan ba samun biyan buk'ata zaki ba, ke da kanki kince yayi farincikin zuwanta sosae kinga alamar yana sonta kenan sannan yanzu a gabanki ta fad'i cewa an gaya mata ni aminiyarki ce wa kike tunanin ya fad'i mata hakan in ba Ya Haisam d'in ba, kinga kenan duk wani abu game damu yana sanar mata ko daga kanki ma ai zaki gane yadda ta sanki sosae tun kafin ta ganki a zahiri to baki tunanin in kin gaya mashi zai iya sanar da ita kuma in tasan hakan mi kike tunanin zai faru? Duk fa yadda kike ganin kaman tana da kirki wllh tasan da wannan Maganar za'a samu matsalane babba don ba yarda za'ai ace bata kishin Ya Haisam baima yuwuwa wllh kuma tana iya sanar da Hajiya k'arshe in Maganar ta dawo kunnan gwaggo mi kike tunanin zai faru? kiyi tunani Fatuu kowa na iya yi maki kallon mara hankali ma " "Amman ai ba lalle in yaji irin wannan Maganar ba ya sanar da itan" k'ara girgiza kai Haulat tayi don ta fahimci Fatuu bata cikin hayyacinta shiyasa bata ganin hakan a wani abu tace "to kina tunanin in kin fad'i mashin Auren naki zaiyi, ni na tabbatar hakuri zai baki Ya nuna maki yana da wadda zai Aura kiyi tunani bafa zai ta6a aurenku ba ku biyu, ai ko danginsu ma bazasu ta6a yarda ba kar fa ki manta yar'uwarshi ce waye zai goyi bayan ayi mata kishiya a cikinsu bafa mai son kishiya Fatuu sai dole, duk da halin da kike ciki kar ki bari tunaninki ya gushe kizo kuma ki abunda zaki danasani ki daure ki cije ki yak'i zuciyarki ta fitar da Ya Haisam daga cikinta shine abunda yafi Alkhairi" bin ta da ido kawae Fatun keyi yayin da cikin ranta take juya Maganar Haulat d'in lokaci guda ta tuno da Farha da Abubuwan data rink'a yi mata lokacin data fara ganinta da kuma wani zuwa da suka k'ara yi yanzune ta gano dalilin da yasa hakanan ta d'auki karan tsana ta d'aura mata ashe kishi take taya yar'uwarta, ganin tayi shiru yasa Haulat cigaba da tausarta tana k'ara nuna mata had'arin dake tattare da abunda take tunanin yi na sanar mashi, K'arshe dai saidae fasa zuwa islamiyyar Haulat tayi sai gab da Magrib ta bar gidan duk jikinta yay sanyi lakwas, Tun bayan da Haulat d'in ta tafi tay zaune saman gado ta had'e kafafunta ta d'aura ha6arta idonta akan bangon d'akin tana ta nazarin Maganganun Haulat tabbas tasan in har Gwaggo taji wannan Maganar kashinta ya bushe k'arshe ma tana iya cewa zata maida ita ruga, tsorone ya kama wani 6angare na zuciyarta yayinda wani 6angaren keta k'ara azalzala mata son Haisam tana a hakan aka kira sallar Magrib amman ta kasa tashi taje tayi sai can bayan an gama ta daure ta saukko daga gadon ta fita don yo alwala, bayan ta gama sallar jin jikinta sam bai mata dad'i ne yasa ta mik'e ta cire rigar jikinta ta d'aura towel ta yafa gyale saman kanta ta nufi toilet don yin wanka, bayan ta fito tana cikin shiryawa ta jiyo sallamar Fanan dam kirjinta yay irin bugun da yakeyi duk in taji sallamar tata, a bakin kopar d'akin ta k'ara yin sallama a hankali Fatun ta amsa ta d'aga labulen ganinta tsaye yasa ta washe baki tana mata dariya ta nufeta tana Fad'in"am so happy seeing u'r recovering Sis Zarah" tayi Maganar hannunta guda kan shoulder d'in Fatuu, d'an guntun Murmushi ta daure tayi mata ta tambayeta wanka tayi ne Fatun ta d'aga mata kai, kama hannunta tayi suka nufi gefen gado ta aje ledojin dake a d'ayan hannunta tace gashi taci tasan bata jin dad'in bakinta, ita dae fatun shiru tayi hakan yasa Fanan ta bud'e leda d'aya ta fiddo shawarma bayan ta warware ta kai bakin Fatuu tana Murmushi tace "ki daure kici kinji, ina son inga kin samu lafiya kin koma normal condition naki cos am not happy seeing u like dis" d'an d'aga ido Fatuu tayi ta kalleta ta jinjina mata kai alamar tabbatar mata da abunda ta fad'a, alamar ta bud'e bakin tayi mata da nata bakin kaman bazata bud'e ba sai kuma ta d'an bude kad'an tasa mata ta gatsi yar kad'an, ganin tana kokarin k'ara bata yasa ta kai hannu zata amsa amman sai ta girgiza mata kai tace "in na baki bazaki ci sosae ba" ba yarda Fatuu ta iya haka ta rink'a bata tana ci har ce mata tayi ta k'oshi amman tak'i k'yaleta har saida Fatuu ta ruk'e hannunta tana yamutsa fuska sannan ta k'yaleta ta bud'e d'ayar ledar ta fiddo ice cream shima ta fara bata a bakin d'an kad'an tasha ta kauda kai tana Fad'in ruwa take son sha, tambayarta tayi inda ruwan yake Fatun ta mik'e tace zata je tasha, a tare suka fito ta shiga Falo ta d'aukko ruwan ita kawae so take Fanan d'in ta tafi amman saida ta rakota har Parlorn tayi mata tsaye saida tasha ruwan, bayan sun fito tace mata tazo Ya Haisam na waje yaganta ya damu da ciwon da take sosae, bata ce komae ba ta bita dama akwae gyale asaman kanta, lokacin da suka fita yana saman bike zaune yana latsa wayarsa tunda suka tunkareshi gabanta ke bugawa da sauri da sauri suna zuwa gabanshi cike da farinciki Fanan tace mashi ga Zarah ta fara samun sauk'i, idonshi akanta yana d'an Murmushi yace mata ya karfin jikin tace da sauki yace Allah ya bata lpy ta amsa da Amin, ce mashi tayi saida Safe yace Ok ta juya zata tafi Fanan tay saurin kama hannunta suka tafi tare saida ta kaita cikin gidan tace mata saida safe ta juya, da hanzari ta nufi d'akinta tana shiga ta fad'a saman gado tasa wani irin marayan kuka mai cin rai ganin Haisam din ya k'ara dagula mata lissafi, k'afartace ta ta6a ledar da Fanan ta kawo mata aikuwa ta mik'e ta d'auki ledojin tai wurgi dasu k'asa har ice cream d'in data bata ya zubo hakan bai isa ba ta rarumi filo shima ta wurgoshi k'asa, ita yanzu shikenan ta rasa Ya Handsome, duk Rayuwar da take hango ma kanta zata yi dashi watace zata yi hakan, a zuciyarta take ta raya hakan, sosae tasa kuka mai sauti tana cikin wannan halin gwaggo ta dawo don bata bari sai lokacin tashi ba saboda Fatun na ranta, tana shigowa gidan d'akin Fatun ta nufa tun kafin ta k'arasa ta jiyo kukanta aikuwa da sauri har tana tuntu6e baiwar Allah ta fad'a dakin, ganin halin da take ciki ba k'aramin tashi hankalinta yay ba nufarta tayi tana tambayar mike damunta ta d'agota tana kallon fuskarta da tayi jage jage da hawaye nan da nan itama idonta ya ciko da kwalla don ganin halin da take ciki yasa ta tabbatar ma kanta da zargin da take yi game da ciwon Fatun, hannunta ta kamo ta d'aura kan kirjinta tana Fad'in "Gwaggo k'irjina zafi, zai 6are ki taimaka man" nan da nan kwallan suka fara zubo mata ta hau yi mata Addu'oi tana tofa mata, A hankali ta fara jin sauk'in k'irjin don a halin da take ciki ganin Mutum a kusa da ita wani sauk'i ne, lamo tayi a jikin gwaggo tana maida numfashi gwaggon na cigaba da tofa mata Addu'oin tana shafa kanta, ganin ta natsu tay shiru yasa ta d'an leka fuskarta cikin harshen fulatanci ta tambayeta da sauk'i ta daga mata kai alamar eh sannu tayi mata taci gaba da shafa kanta tana adduoin can ta d'ago kanta tace bari in zubo maki Abinci da sauri ta girgiza mata kai alamar a'a tace "to ayi ciwo ba cin abinci Fatuu ki daure ki d'an ci ko ba yawa" Murya a disashe tace "naci shawarma" da d'an mamaki ta tambayeta inda ta samu shawarmar ta d'aga yatsa ta nuna mata ledojin dake yashe a k'asa tace "Aunty Fanan ta kawo" jinjina kai tayi tace "to amman kin ci d'in da gaske?" "Eh itama ta bani a baki" d'an Murmushi gwaggon tayi tace "Allah sarki, wllh ban ta6a ganin mace irinta ba Allah ya bata komae amman sam bata da girman kai bata d'auki duniya da zafi ba gashi nan tun yanzu ta fara cin ribar hakan Allah ya bata Abokin rayuwa Nagari, gaba d'aya naji masu dad'i Allah ubangiji ya albarkace su da zuria ta gari kaman yadda suke" k'asa k'asa Fatun tace Amin idanunta sun ciko da kwalla amman bata bari sun zubo ba, mik'ewa gwaggo tayi ta d'aukko ledar ta dawo ta zauna tace "to tashi ki d'an k'ara" tayi Maganar tana fiddo sauran abubuwan dake ciki wanda duk snacks ne da sauri ta girgiza mata kai don ita ko k'amshinsu ma bata son ji ganin tak'i ci ne yasa gwaggo ta fita taje ta d'ebo mata Abinci ta tasata gaba saida taci ba wani mai yawa ba, bayan ta gama tace mata tayi sallar isha tunda an fara kira sai ta kwanta inta yi bacci zata k'ara samun sauki ta amsa mata da to, tana gama sallar akan abun sallar ta kwanta tayi lamo tana ta tunane tunane itama gwaggo sallar taje tayi tana son tayi wanka amman kuma tana son taje wani wuri hakan yasa ta bari in ta dawo tayi don kar dare yayi sosae saida ta leka d'akin Fatun ta ganta a kwance duk a tunaninta bacci take ta juya ta nufi kopar gida lokacin Amadu ya dawo daga Masallaci yana kokarin bud'e shago ganin gwaggon ya nufeta yace "wani wuri zaki ne?" da yar damuwa tace "eh zanje wurin Malam tanimu ne inason gaya mashi game da halin da Fatuu take ciki ko zai yi mata Addu'a" yace "jikin har yanzu kenan, d'azun na dubata sau biyu duk a kwance nike isketa inna tambayeta ya jikin sai tace man da sauki" "Eh ai kasan irin wannan ciwon dama haka yake yanzu da sauki anjima ba sauki, yanzu fa dana dawo baka ga halin dana isketa ba da alama sun rik'e mata k'irji ne tana ta cewa zafi take ji kaman zai 6are" girgiza kai yay yace "Allah ubangiji ya bata Lafiya mai d'orewa, muje to in raka ki" Tace "A barta ita kadae kuwa, ko ka shiga gidan in je in dawo sai ka bud'e shagon" amsa mata yay da to ya wuce itama ta tafi, bata k'arasa gidan bama ta had'e dashi a hanya ya dawo daga Masallaci suka tsaya suka gaisa kafin tayi mashi bayanin halin da Fatun take ciki,sosae ya jajanta mata yace zuwa gobe da safe a zo a amsar mata ruwan Addu'a yace da za'a samu zam zam ma da yafi tace bari taje zata sa Amadu yaje ya siyo sai a aiko dashi ya amsa da to ta tambayi abunda za'a bada na sadaqa yace ba sai ta bada wani abu Allah ya bata Lafiya, tayi mashi godiya sosae da Addu'a kafin ta tafi. Tana komawa gidan ta iske Amadun a d'akin Fatuu yana zaune k'asa kusa da ita Addua ya gama yi mata yana d'an yi mata fira sama sama take tanka mashi, sak'on yaje ya siyo zam zam d'in ta bashi tace in ya dawo ya wuce ya kaima Malam Tanimun, wannan shi ake kira da cuta daban Magani daban don ma dai Maganin ta wani bangaren zai taimaka don ba abunda yafi karfin Addu'a. Bayan sun isa gida saida ya raka Fanan har d'akin Hajiya lokacin tana zaune kan Sallaya ta gama sallar Magrib tana jiran isha suna shigowa cike da tsokana tace "Luv birds an dawo" nufarta Fanan tayi tana dariya ta zauna kusa da ita ta kwantar da kanta kan kafad'arta, gaisawa yay da Hajiya yace zaije yay wanka Hajiya tace ya bari yay sallar isha sai yayi yanzu ana iya kiran salla yana wanka ya amsa mata da Ok ya nufi bakin gado ya zauna, "Wai nikam ya jikin Fateema ne?" Hajiya ta tambaya Fanan tace "tana samun sauk'i sosae sunje yanzu" jinjina kai Hajiya tayi kafin tace "Allah ya k'ara sauki" amsawa sukae da Amin harda Haisam d'in, bada jimawa ba kuma aka fara kiran isha ya mik'e yace zaije Masallaci Fanan ta d'aga hannu cike da kauna tana mashi bye bye har ya kama kopa zai bud'e tace "Babe kai man Addu'a in baka twins nine Months after we get married" hannu Hajiya ta kai zata bugi bakinta ta fad'a jikinta tana dariya shima dariyar yay ya fice, bayan angama sallar part d'inshi ya nufa yayi wanka ya shirya kafin ya dawo part d'in Hajiyar lokacin itama Fanan din tayi wanka ta shirya cikin kayan bacci riga da wando milk masu santsi kanta tasa hula itama milk ta saki brown gashinta, atare gaba d'ayansu suka nufi Dining don cin dinner, kaman sauran lokutta suka rink'a ciyar da junansu har Hajiya nama Haisam tsiyar yadda yake cin abinci yanzu don yaga Fanan ita daya raina sai taita fama dashi yak'i ci sosae sai ya gadama, dariya Fanan d'in tayi tace baison 6acin ranta ne hajiya tace sai nata yake so ko, bayan sun gama falon suka koma suna kallo Fanan dai na manne dashi lokacin da Hajiya ta mik'e tace ita dae bacci take ji shima tashi yay ya mik'ar da Fanan d'in ya rakata har cikin dakin, saida yaga ta kwanta ya manna mata kiss a gefen fuskarta yay masu saida Safe ya nufi hanyar fita idon Fanan akanshi yana kama handle d'in kopar ta d'aga murya tace "I luv u nd I can't do without u Babe" juyowa yay ya sakar mata k'ayataccen murmushi kafin ya fice Hajiya dake zaune gefen gadon ta ta6e baki tana girgiza kai Fanan taja duvet ta rufe fuskarta tana dariya. Allah sarki gwaggo tsakar dare har tashi tayi tayi salla tayi ma Fatuu Addu'ar Allah ya yaye mata lalurar da take fama da ita sosae tayi mata Addu'oi,Washe gari da Asuba ta tada Fatun tayi salla bayan ta gama ta koma ta kwanta itama gwaggon komawa tayi saida gari ya waye ta tashi don ta had'a masu breakfast lokacin da Amadun yazo amsar nashi tace mashi in ya gama yaje wurin Malam tanimu ya amso mata sak'on yace to, a d'akin nata ta kai kayan breakfast d'in ta tashi Fatuu tace ta lalla6a taje ta wanko baki, bayan ta dawo ta had'a mata tea mai kauri tace ta daure ta sha zata ji dadin jikinta, ba laifi taci abun breakfast d'in sosae don ta danji dad'in jikinta ba kaman jiya ba, suna cikin yin karin kumallon Amadu ya kawo ruwan addu'ar ya fad'i mata yace a bata tasha safe da dare sai kuma a shafe mata fuskarta da kirjin nata daya rik'e, sosae gwaggo taji dad'i bayan ya tafi ta bud'e marfin gorar ta mik'a ma Fatuu tace "kiyi bismilla kisha" zuru tayi tana yi mata kallon rashin Fahimtar abunda take batan ganin hakan yasa tace "ruwan Addu'a ne ganin halin da kike ciki jiya da daddare naje na fad'a mashi shine yace zai maki Addu'a yau da safe aje a amsa" kasa Magana tayi tana dai ta kallonta ita kuma gwaggon ganin kallon da take matan yasa ta yin tunanin suna iya hanata sha hakan yasa ta matsa tana niyyar kwafa mata robar a baki Fatun tasa hannu ta amsa ta kai bakinta bayan tasha ta mik'a mata ta zuba a hannunta ta shafa mata kaman yadda aka ce, "Yauwa in sha Allahu zaki ji kinsamu sauki ki koma ki kwanta" gwaggo ta fad'a da d'an Murmushi don taji dadin yadda Fatuu tasha ruwan Addu'ar, mik'ewa tayi ta hau gadon tay lamo ta shiga duniyar tunani zuciyarta na raya mata Ya Handsome na can suna shan soyayyarsu da Fanan ita tana nan tana ta fama, runtse idonta tayi yar siririyar kwalla ta zubo mata tasa hannu ta goge batare data bud'e idon ba. Misalin karfe sha biyu saura gwaggo na cikin Kitchen Fatuu ta fito ta tsaya a bakin Kitchen d'in tana ganinta ta nufota tace "Sannu kin tashi" kai ta d'aga mata tace "to ya jikin?" "Da sauki sosae" ta bata amsa a sanyaye, "Alhamdulillah, Allah ya k'aro sauki, halan kin gaji da kwanciyar?" kai ta sake d'aga mata tace "to ki shiga Falo ki zauna ko ki kunna kallo", "Ki kawo in yi wanke wanke in baki yi ba" ta fad'a idonta akan gwaggon duk bata jin dad'in yadda ta saka ta damuwa, "Har kin samu sauk'in da zaki iya yin aiki kije ki zauna zanyi, so nike in gama amfani da abubuwan da suka 6aci sai in had'a in wanke gaba d'aya" tace "ki kawo zan iya" gwaggon tace to don dama tafi son taga ta dawo kamar da, tana cikin yin wanke wanken Fanan tayi sallama ta shigo jikinta sanye da Maroon skirt babba mai tattara a sama sai rigar brown da ratsin maroon kanta ta yafa Maroon d'in veil kafafunta sanye da flat shoe brown ta matukar yin kyau, suna had'a ido da Fatuu data d'aga kai ta kalli kopan shigowan tana ganinta ta saki Murmushi ta nufeta tana Fad'in "am so Happy sis Zarah kinsamu lpy ko" kai ta d'aga mata kafin a hankali tace mata ina wuni ta amsa still da fara'a, gwaggo ce ta fito daga cikin Kitchen tana fadin"Muryar wa nike ji kaman y'ata Fan...fanna ko haka sunan yake ni shige man yake wllh" tana dariya ta gyara mata sunan tace yauwa bazata kara mantawa ba, "Naga Sis Zarah ta samu lpy nayi farinciki" da jin dad'in Maganarta gwaggo tace "aikuwa Alhamdulillah sauki ya fara samuwa, ki shigo falo" ta kai maganar tana nuna mata kopar falon, "No let me help her" tayi Maganar tana tattare hannun rigarta alamar zata taya Fatuu wanke wanken da sauri gwaggo tace "Don Allah ki kyaleta ta idasa ita tace zata yi bama ni na bata tayi ba" tace "ba wani abu zamu gama tare, inata so mu had'u da ita muyi fira sosae and nazo kuma bata lafiya" d'an girgiza kai gwaggo tayi aranta tana Fad'in wace irin yarinyace wannan,ganin tana niyyar duk'awa yasa da sauri tace bari in kawo maki kujera to tunda kin matsa sai kinyi, bayan ta kawo mata kujerar tace ta curo agogon hannunta kar ruwa ya shiga ya lalace ta cire ta mik'a mata harda wayarta, bayan ta zauna d'auraya ta shiga yi mata tana kifewa a cikin kwando tana d'an yi mata firar india akai akai take d'agowa ta kalleta da Murmushi a fuskarta itama fatun sai ta d'an yi mata a haka har suka gama Fatuu tace mata ta shiga falo tace to, bayan ta kai kayan kicin ta dawo ta wanke wurin itama ta nufi Parlon tana niyyar zama kan kujera Fanan dake zaune kan 3 seater tace tazo ta zauna kusa da ita batare data ce komae ba taje ta zauna, gallery d'in wayarta ta shiga ta d'an kwanto gefen Fatun tana nuna mata videos d'insu ita da friends dinta da suke karatu tare acan india, tun dai Fatun na dar dar harta saki jiki abunda ya bata dariya ta d'anyi wani kuma tayi Murmushi suna haka gwaggo ta shigo zama tayi kan 1 seater fuskarta da Murmushi don taji dad'in ganin yadda Fatuu ta d'an saki jiki, d'agowa Fanan tayi tace ma gwaggon "sannu granny kinata aiki ko inzo in tayaki?" d'an bud'a ido tay tace "ai ba wani aiki bane Abinci ne nike yi kuma ban tunanin ma kin ta6a cin abunda nike dafawa balle har ki iya tayani" da d'an mamaki kan fuskarta ta tambayeta miye take dafawa tace mata dambu, a hak'ik'ance tace "I know dambi mana...." tun kan ta k'arasa gwaggo tasa dariya fatuu ma saida ta d'anyi, "To ai y'ata Fanan tun wurin fad'in sunan nashi ma kinga ya nuna baki sanshi ba" da sauri tace "Serious granny na ta6a cin dambin ba shine kaman cous cous ba?" kai gwaggo ta daga"tabbas shine amman ba dambi sunanshi ba dambu ake cewa Fanan d'in tace yauwa shi to take nufi, "Ai da har ina tunanin in sama maki wani abun kici bansan kin iya cin shi ba" girgiza mata kai tayi tace "zanci sosae na dad'e banci shi ba Mom na mana" mik'ewa gwaggo tayi tana Fad'in to bari taje tayi sauri ta gama ko don d'iyarta taci, Fanan d'in na Dariya jin Maganar gwaggon, kiran sallar Azahar aka fara suka tashi ita da Fatun suka je d'akinta su kai salla bayan sun gama suka dawo falon lokacin gwaggo ta kawo masu dambun na Masara ne yaji zogale sai kamshi ke tashi, tare ta zubo masu a babban plate don tasan ko ta zubo masu kowa da nashi karshe Fanan din sai tace a had'a masu, sosae taji dad'in dambun duk yadda Fatuu taso k'in ci da yawa ta hanata tace in bata cin abinci sosae koda ta samu lafiya karfin jikinta bazai dawo ba, ba yadda ta iya haka ta rink'a turawa ba don tana wani jin dadinshi ba, koda suka cinye gwaggo tace a k'aro masu cewa Fanan tayi eh sam bata nuna bak'unta kai kace yar 'uwarsu ce ma, k'in ci Fatuu tayi bayan an k'aro tace ita ta koshi dole ta kyaleta taci gaba da ci ita kadae, tana cikin ci Hajiya tayi sallama gwaggo dake zaune itama tana cin dambun ta mik'e da sauri ta fita tana Fad'in "Maraba da Hajiya" ta amsa mata da yauwa tana nufota Saude na bayanta itama gwaggo tayi mata sannu da zuwa ta gaisheta da fara'a ta amsa mata tace su shigo, suna shiga idon Hajiya ya sauka kan Fanan da ta tura dambu a baki tana mata dariya Hajiya ta ruk'e ha6a tace "Oh su shanshani kafan yawo ana nan ana kwalama ashe, to Allah ya jikanka dambu ki dai bi a hankali in ba haka ba ya shaqe ki" tayi Maganar tana kokarin zama kan kujera gwaggo dake Dariya tace "Mutum da gidansu ai ba kwalama take ba" Fanan d'in ta gyad'a kai alamar atoh,nuna ma Saude kujera gwaggo tayi tace ta zauna tayi tsaye ta nufi wurin ta zauna, gaisawa suka shiga yi suka yi mata ya mai jiki tace da sauki kallon fatuu dake zaune kan carpet gefen Fanan tayi shiru tace "Oh sannu Fateema kinji, Allah ubangiji ya yaye maki wannan lalura baki d'aya ki huta wannan zuwa Dam bai yi dad'i ba sam" gwaggo dake d'an Murmushi tace "to ya za'ai haka Allah ya kaddara" hajiya tace "hakane amman dae da sauki sosae ko?" "Eh jiyane dana dawo dae na iske abun yayi tsanani har tana kirjinta zai 6are to sai nayi mata Addu'oi na kuma je wurin Malam tanimu na fad'a mashi halin da ake ciki shine ya bukaci ruwan zam zam yayi mata Addu'oi yau da safe aka amso tasha na shafa mata kaman yadda yace Allah cikin ikonsa ta samu sauki sosae wllh" gaba d'ayansu duk suka girgiza kai alamar tausayawa ita dae Fatuu zuru tayi tana binsu da ido don ta fahimci ciwon da suke tunanin yana damunta, mik'ewa gwaggo tayi tace bari a zubo masu dambu Hajiya ta tambayeta na miye tace na Masara ne tace to a zubo masu kad'an don ta kwana biyu bata ci shiba, wuri daban daban ta zubo masu ita da Saude Hajiya na ganin haka tace maimakon ta zubo masu wuri guda sai sun cinye masu abinci dama ga wata acicin nan sai turawa take Fanan na jin haka tasa dariya suma duk dariyar suke, bayan sun gama Hajiya ta tambayi gwaggo bazata aiki bane yau tace tana son zuwa amman tana tunanin yanayin jikin Fatuu don jiya yadda ta dawo ta sameta hankalinta ba k'aramin tashi yay ba, Fanan na jin haka tace taje aikinta zasu zauna tare Hajiya tace "to ku taho can gida mana in ta dawo ba sai ta dawo ba" girgiza kai Fanan tayi tace "ban komawa fushi nake da Babe" Dariya Hajiya tayi tace "Saboda yau yak'i zuwa dake aikin kika yi fushi dashi" kai ta d'aga alamar eh, tace "hum dama dae zaki iya duk cika baki ne" gwaggo dake dariya tace "ai y'ata kishinki yake shiyasa bai je dake ba" bayan sun gama gaba d'aya suka nufi gidan Hajiya........... Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2004* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 4 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* Koda suka je zama sukayi a parlor suna kallo suna fira sai dae Fatuu bata wani saki jiki sosae ba sama sama take Magana ganin yanayinta yasa Hajiya tace taje d'akinta ta kwanta Fanan ta kama hannunta suka tafi, kwantawa tayi saman gadon Hajiyar Fanan kuma ta wuce Toilet don tayi wanka lokacin data fito har bacci ya kwashe Fatuu itama kayan shan iska tasa ta kwanta gefenta tana son ta kira Haisam don taga missed call d'inshi lokacin data fito daga toilet amman sai kawae ta daure ta kyaleshi wai don yasan tayi fushi, tana ta latsa wayarta har bacci itama ya kwasheta, sai da akayi la'asar Hajiya ta shigo yin salla ta tashesu suma suyi sallar, da daddare bayan isha suna zaune a falo Fatuu duk ta k'agara ta koma gida don bata son Haisam ya dawo tana gidan, har cewa tayi zata tafi Hajiya tace ta bari in Dijen ta dawo ai zata kira ita kuma Fanan cewa tayi ta kwana anan kawae mana ita dae murmushin yak'e kawae tayi, suna zaunen Haisam ya shigo da sallama duk suka d'aga kai suka kalleshi Hajiya ta amsa mashi yayin da k'irjin Fatuu yay mata wani irin bugu tana yin arba da fuskarshi sai dae kuma ta kasa daina kallonshi wani irin fresh taga yayi mata, nufosu yay Fanan ta kauda kanta yana ganin haka yaja ya tsaya Hajiya dake kallonsu na masu Murmushi don tasan yadda sukai da Fanan d'in da safe, juyawa yay zai koma da sauri Hajiya tace "ka rufa man asiri ban shirya yin jinya ba daga kawo man ziyara" ita kuwa Fanan d'in mik'ewa tayi da sauri sauri gudu gudu ta nufeshi tana zuwa ta fad'a bayanshi ta k'ank'ameshi ta yadda bazai iya cigaba da tafiya ba, ruk'e hannuwanta yay ya juyo yana kallonta ta zo6ara baki ya kai hannu ya d'an ja lips d'inta ta saki yar k'ara sai lokacin yay Murmushi ya kama hannunta suka nufo cikin falon, wani irin abu Fatuu taji ya tokare mata k'irji nan da nan zuciyarta ta karye taji kwalla na niyyar zubo mata da sauri ta juyar da kanta ta kalli tv, gefen Fatuu inda ta taso ya kaita ta zauna shi kuma ya zauna saman hannun Sofa har lokacin suna ruk'e da hannun juna kallon Hajiya yay ya gaidata ta amsa tana Murmushi a hankali ya juya ya kalli Fatuu daidai itama ta juyo saida ta had'iye wani abu mai d'aci kafin da k'yar ta iya gaidashi ya amsa yay mata ya jiki tace da sauki, maida kallon yay kan Fanan yace ta gama fushin Hajiya tace "to ai ni bansan wane ma irin fushi ne wannan ba" turo baki Fanan tay ta kwantar da kanta gefen jikinshi tace ita dama ba fushi tayi dashi ba ai, Hajiya tace to kanta dai ta k'aryata ba ita ba duk suka yi dariya, janyeta yay ya mik'e yace zaije yay wanka baiwar Allah Fatuu daurewa kawae take ita kadae tasan abunda take ji yanzu ta tabbatar ma kanta ba k'aramin son juna suke ba, kasa jure zaman tayi ta mik'e tace zata je gida tasan yanzu gwaggo ta dawo Hajiya tace ta lura dae gidan take son tafiya to ta bari taci abinci Fanan ma tace ta bari in sunci dinner sai su rakata ita da Babe Hajiya tace lokacin ma tasan dijen ta dawo, kasa yi ma su musu tay ta koma ta zauna bada jimawa sosae ba Haisam ya shigo ya shirya cikin jallabiya dark ash mai gajeren hannu yana shigowa Fanan ta mik'e ta kama hannun Fatuu tace mashi suje table Zarah nason tafiya gida jinjina kai yay suka nufi dining area da tun bayan gama sallar isha Saude ta shirya komae, kaman yadda suka saba haka suke cin abincin baiwar Allah Fatuu daurewa kawae take idonta akan abincin gabanta da Fanan ta zuba mata ji take kaman ta rushe da kuka, bata wani ci da yawa ba sai faman jujjuya cokali take can ta mik'e tace ta k'oshi fanan tace ta daure ta k'ara bata ci sosae ba tace amai take ji ne hakan yasa Hajiya tace ta k'yaleta fanan d'in tace to ta jirasu a falo su gama ta d'aga mata kai kawae, a tare suka rakota suna ta hirarsu irin ta masoya har wani d'an fad'a mashi a jiki take, lokacin da suka k'araso kopar gidan su biyu suka shiga shi ya tsaya a waje zai jirata, gwaggo bata dad'e da shiga gidan ba suka shigo fanan na dariya tace ta maido yar ajiya tak'i ta kwanan mata itama gwaggon dariya take tay mata godiya sosae ta tafi, kallon Fatuu dake zaune kan kujera tayi tace mata ya jikin ta amsa mata da sauki ta mik'e zata wuce d'akinta gwaggon tace ta tsaya ta zubo mata Abinci sai taje ta kwanta tace taci acan daga haka ta wuce d'akinta tana shiga ta nufi gado ta fada samanshi tayi rubda ciki sai lokacin kukan da take ta rik'ewa ya samu zubowa,wani irin son Ya Handsome take ji acikin ranta bata da buri yanzu sai na auranshi to amman ta yaya shi da baisan ma tana yi ba gashi yanzu tabbas ta gasgata Maganar Haulat na ba k'aramin son juna suke ba shida Fanan, sak'e sak'e taci gaba da yi tana neman mafita har gwaggo ta lek'o ganinta haka yasa tayi tunanin tayi bacci ne shiga tayi cikin d'akin tay mata Addu'oi duk fatun na jinta bayan ta gama ta gyara mata kwanciya lokacin da zata fita daga d'akin ta kashe mata hasken wuta kafin ta fita. Tun daga wannan ranar Fatuu bata k'ara yadda wani abu ya kaita gidan Hajiya ba don ta fahimci in taga Haisam k'ara shiga mawuyacin hali take, k'iri k'iri ta hakura da ganinshin abunda bata ta6a tunani ba a rayuwarta wato guje ma ganin Ya Handsome d'inta mutumin da ko tafiya yay a k'agare take daya dawo don duk sai tajita ba daidai ba in bai nan, duk abunnan ba wanda ya fahimci halin da take ciki su a tunaninsu lalurar da suke zato ke damunta ita gwaggo bata ma san cewa Fatun bata san da Maganar baikon dake tsakaninsu ba sanin irin shak'uwar dake tsakaninta dasu duka bama kamar Haisam, itama kuma Fanan bata san Fatun bata sani ba, Ranar Asabar ya kama kwanan Fanan shidda da zuwa Fatuu na cikin d'akinta don yanzu ta d'aura aure da zaman d'aki ba kaman in gwaggo bata nan in tana nan ne wani lokacin inta matsa mata take zuwa Parlor ta kunna tv saidae sunan tana yin kallonne amman hankalinta na wani wuri tunane tunane sun zamar mata jiki duk tazama wata so silent Magana saita kama take yi, shigowa gwaggo tayi da sallama ta d'aga kai ta kalleta kafin a hankali ta amsa mata ta nufi gefen gadon ta zauna fatun ta yunk'ura ta mik'e zaune, "Sannu ya karfin jikin?" amsa mata tayi da sauki, tace "Yanzu ya kike jin jikinne ina yafi damunki?" shiru ta d'anyi idonta akanta kafin a hankali tace "ba ko ina" itama gwaggon shiru tay kaman mai nazarinta hakan yasa Fatun duk'ar da kanta tana wasa da yatsunta, "In ba abunda ke damunki yanzu miyasa kika k'i sakin jikin ki kaman da?" da yar damuwa tay Maganar, damm gabanta ya d'an fad'i ta d'ago idanunta har sun canja kala a sanyaye tace "kawae banjin dad'in jikinne kaman ba nawa ba" jinjina kai gwaggon tayi tace "a hankali zaki warware amman wannan k'umshewar da kike cikin d'aki hada shi ke k'ara maki rashin dad'in jikin, ki daure ki rink'a sakin jikin kina fitowa" kai ta d'aga mata tace Allah ya bata Lafiya daga haka ta mik'e zata fita sai kuma ta tsaya ta juyo tace "ko gidan Hajiya ki daure ki rink'a zuwa kinga yarinyar nan Fanan kullum sai tazo dubaki duk ta damu da halin da kike ciki in taga kinje zata ji dad'i, da zaki iya ma kiyi d'an wani abu ki kai mata nasan zata ji dad'i sosae taga kema kin damu da ita kaman yadda ta damu dake" wani irin fad'uwa gabanta yay hakanan ita bata tsani Fanan ba amman data ji muryarta ko anyi Maganarta sai gabanta ya fad'i ganin gwaggon ta kafeta da ido ne yasa tace to mi zata yi mata, tace "yauwa to ko wainar fulawa ce akwae komae na yi kije waje wurin Amadu sai ki amso kwai nasan ba k'aramin dad'inta zata ji ba tunda ita ba ruwanta komae ci take" ta k'arasa Maganar tana nufar kopa, zaune tayi tay shiru bayan gwaggon ta fita, ba wai wainar ke bata son yi mata ba kawae ita gidan Hajiyar ne bata son zuwa don karshenta zata tado ma kanta wata matsalar ne can dai ta saukko daga kan gadon ta fita, ba tare da 6ata lokaci ba gwaggo ta taimaka mata wurin had'a k'ullun wainar ta yi shi mai d'an yawa yadda suma zasu ci, suya Fatuu ta fara cikin Kitchen gwaggo kuma ta yanka mata cabbage da sauran kayan ci, bayan ta soya mai d'an yawa gwaggo tace tay sauri ta shirya ta kaimata ita bari taci gaba da yin suyar, wanka taje tayo har ta wuce kitchen gwaggo ta kirata tazo bakin kitchen d'in ta tsaya tace "nace ko ki saka kayan data kawo maki dinnan suna nan na saka maki acikin kayanki" kai kawae ta d'aga mata ta wuce, kayan na nan yadda suke cikin leda tunda ta kawo su Fatun bata ta6a su ba, d'aukar ledar tayi ta koma bakin gado ta zazzagesu ta fara d'agasu tana dubawa, sari kala ukku ne riga da wando da mayafinsu rigar iya gwuiwa ce sai kuma doguwar riga har k'asa itama kuma tana da wando da mayafi kayan sun matukar had'uwa daka kallesu zaka gane ainihin na india ne sun mata kyau saidae yanayin da take ciki yasa ta kasa yin murnar kayan dama kwanaki can baya Haisam ya ta6a kawo mata irinsu kala biyu da yaje Lagos yace Fanan tace a bata sai yanzu ta fahimci dalilin dayasa yake yawan zuwa Lagos wani lokacin harda wurin Fanan yake zuwa in tazo,wasu sky blue ta d'auka zata sa ta mayar da sauran cikin ledar,bayan ta gama shiryawa tsaye tay gaban mirror tana kallon kanta kayan sunyi mata kyau sosae sai salki stones din jiki ke saki ba don yanayin da kayan suka risketa aciki ba da ba abunda zai hana har rawar india tayi,jiki a sanyaye ta yafa mayafin kayan ta nufi kicin bayan ta sanya takalma masu d'an tudu don bata saka flat shoes shiyasa ma bata dasu sai yan na sawa a tsakar gida, lokacin data je kicin d'in gwaggo har ta had'a wadda zata kaimata tana ganinta ta washe bakin jin dad'in ganin yan matanta yau ta fito tsaf da ita duk da ba wata kwalliya tayi ba iya mai kawai ta shafa sai kayan data sa sosae ta shiga yabon kayan tana sunyi mata kyau sosae ita dae shiru tay tana bin ta da ido, d'aukko mata kwanon dinner set mai d'an girma dake a rufe gefe tay tace gashi nan ta kaimata. Kasancewar Weekend ne gaba d'ayansu suna zaune a falo duk kaya ba masu nauyi bane a jikinsu Haisam da Fanan na kan 3 seater ya jingina a k'arshen kujerar Fanan kuma na kwance ta d'aura kanta kan kafafunshi Hajiya na akan 2 seater gaba d'aya idanunsu na akan tv suna kallon wani Indian film a Bollywood Fanan d'ince ke fassara masu abunda ake cewa don ta iya indiyanci sosae Musamman akwae lokacin da suka ware suna koyonshi acan, da yar sallama ta shigo Falon saidai ba wanda ya jita hakan yasa ta tsaya idonta akan Haisam wani abu take ji na bin jikinta ga zuciyarta dake bugawa da sauri da sauri ta kasa d'aga kafarta ta idasa shiga ciki kaman ji yay idanu na yawo a kansa hakan yasa ya d'an juyo suka had'a ido da ita shima kallon ya bita dashi from head to toe kafin ya tsaida idon cikin nata suna kallon juna can taji cikin cool voice dinshi yace "Zaraah ki shigo mana" Maganar da yay ce tasa duk suka juya suka kalli entrance d'in koda Fanan tayi arba da Fatuu tsaye da sauri ta yunk'ura ta mik'e ta nufeta ganin haka yasa Fatun nufo cikin falon suka had'e gaba d'aya ita da kwanon da take ruk'e dashi ta had'asu ta rungume tana Fad'in "am so so Happy Sis Zarah kin samu Lafiya sosae" d'agowa tay ta amshi abunda ke hannunta ta rungume a hannunta guda d'ayan kuma ta kama hannunta suka nufi ciki, a Sofa d'in da suke zaune ta zaunar da ita can d'ayan gefen ita kuma ta zauna tsakiya ta aje kwanon k'asa gabanta, "Hajiya Ina kwana" ta fad'a a sanyaye hajiya dake kallonsu tana Murmushi tace "Lafiya lou Fateema kin yi kyau sosae, ya k'arfin jikin?" da sauki ta amsa mata kafin ta juya ta gaida Haisam da shima kallonsu yake ya amsa fuska a sake yay mata ya jiki shima tace mashi da sauk'i,maido idon tay kan Fanan da ta d'aura hannunta guda kan k'afafunta tana ta sakar mata Murmushi, itama gaidata tayi ta amsa tace mata tayi kyau sosae godiya Fatun tayi mata ta kayan tace basai tayi wannan ba takai hannu ta zame gyalen kanta ganin yadda gashin yake ba gyara tace mata tasan saboda bata lafiya ne bata gyara ba yanzu tunda ta samu sauk'i yakamata a gyara zatafi jin dad'inshi ita dai jinjina mata kai kawae take, "To ke an kawo man abu kin tasa a gaba ki mik'o man in ga mi na samu haka" Hajiya dake kallon fanan ta fad'a aikuwa a hak'ik'ance tace "ba naki ne ba nawa ne" yar dariya hajiya tayi tace "hak'ilo, yanzu yaushe kika ji ance naki ne" kallon Fatuu tayi tace ita ta kawo mawa ko kallon hajiya Fatuu tay data kafeta da ido kaman zatayi murmushi ta sunkuyar da kanta ta d'aga ma Fanan d'in, yar k'ara tasa tace to gashi nan Sis Zarah tace nata ne, ruk'e ha6a Hajiya tayi tace "Wato dae Fateema an rabamu ko, ada Ya Handsome ya shiga tsakaninmu yanzu kuma ga wannan acicin ai shikenan zasu barni dake ne" yammm taji jikinta yayi jin Maganar Hajiya ta zasu barta da ita dama k'arfin hali kawae take zama a gurin, d'aukar kwanon Fanan tayi ta bud'e kamshin wainar ya daki hancinta har saida ta d'an lumshe ido sai dai bata gane minene ba hakan yasa ta juya ta tambayi Fatuu sunanta tace mata wainar fulawa, "Wasu kuma suna ce mata kalalla6a wasu suce waina gira ko alallagira wasu ma yar cana suke cewa" suka ji Hajiya ta fad'a, bud'a ido Fanan tayi jin wasu sunaye ta fara k'okarin maimaitawa tace "K...kal...kallalla6iya..." tunkan ta rufe baki suka sa dariya gaba d'ayansu ita dae Fatuu d'an Murmushi kawai tay Hajiya tace "Da alama dai za'a maimaita na taliyan hausa" da sauri Fatuu ta juya ta kalli Haisam suka had'a ido ya saki Murmushin gefe tunowa da ranar data kawo mashi taliyan hausa mai daddawa sanin Murmushin kona miye yasa itama tayi kafin ta juyar da kan, "Idan baki ci ki mik'o man nan k'amshinta duk ya cika man hanci" hajiya ta Fad'a idonta kan Fanan, da sauri ta girgiza kai tace ai ko bata ci sai taci abunda Sis Zarah ta kawo mata, d'aukar kwanon tay ta nufi dining Hajiya tace bata ci anan tace zata d'aukko fork ne, "Shine sai kin tafi da ita wato kar ki barma kura ko" d'an d'aga murya tay tace eh cinye mata abunta zatayi, ta sake cewa to wayace mata da fork ake ci hannu ake sawa bazata ji dad'in cinta da fork ba jin hakan yasa ta wuce dining area ta wanko hannunta ta dawo, daga inda Hajiya take ta fara nuna mata yadda zata ci ta nade d'aya da kayan cin acikinta ta dangwala yajin kamar yadda hajiya tace ta tura baki ta fara taunawa, d'an bud'e ido tay lokacin da ta cinye ta yarfa yatsa tace "it's so yummy" dariya hajiya tayi ta juya ta kai sauran ta hannunta bakin Haisam ya kalli abunda take bashin kaman bazai bud'e bakin ba sai kuma ya bud'e ta saka mashi ya gatsa ta janye sauran ta tura baki hajiya dake kallonsu tace "Fateema dai duk ta koya maku kwad'ayi, shima kwanaki a waya naga wainar fulawar ta burgeni nasa Saude tayi mana ita da rana ina tunanin shi ayi mashi wani abun yaci sai ce man yayi wai zai cita nayi mamaki don nasan ba lalle in ya ta6a ganinta ba balle ma ya iya cin dana tambayeshi dama yasanta ne yake ce man ai da Salla da ban dawo bane ta kawo mashi ita nan ya fara cinta" dariya Fanan keyi tana taunar wainar ita kuwa fatuu a hankali ta d'ago ta kalli Haisam da d'an Murmushi suka sake had'a idon gaba d'ayansu Maganar Hajiya ta tuno masu da can baya sallar farko data fara yi dashi lokacin daya dawo ta rink'a kawo mashi abinci har ya rink'a yi mata lesson lokacin ya koyi cin wainar don farko data kawo mashi cewa yay bai iya cinshi ba saida yaga kaman bata ji dadi ba har zata tafi yace ta kawo yaci tace mashi ita ba fushi tayi ba tunda bai iya ci ba bari taje zata kawo mashi wani Abincin amman yace karta damu zai ci don ta gaya mashi musamman don shi ta soya dama kuma saida gwaggo tace mata ba lalle fa in ya iya cin ta ba wannan dalilin ne yasa ya daure yaci amman kuma sai yaji dadinta musamman data kasance ba abinci ce mai nauyi ba tun daga nan duk in ta kawo mashi yana ci, janye idonta tayi ta maida kan tv kaman tana kallo saidae a can k'asan zuciyarta wani iri take ji tunawa da rayuwarsu ta baya rayuwa mai cike da nishad'i daidai da rana d'aya bata ta6a tunanin komae zai sauya haka ba tsakaninta dashi, "To sarakan son kai sai ci kuke kun barni da shak'ar kamshi da alama cinyewa zakuyi ma ba tare da kun bani ba ko" Hajiya tayi Maganar idonta akan su Fanan dake dariyar Maganar Hajiyar tana niyyar ba Haisam wadda ta gutsira ya girgiza mata kai yace ta kai mata cike da tsokana ta mak'e kafad'a alamar bazata bata ba Fatuu data juyo ta kalleta tunda hajiya tayi masu magana ganin abunda tayi yasa ta mik'e idonta akan Hajiyar tace bari taje tayo mata wata, da sauri Fanan ta kamo hannunta tace wasa take zata bata ba sai ta k'ara wahalar da kanta ba ta mik'e ta tunkari Hajiyar ta aje kwanon gefenta itama ta zauna tace to gashi nan su ci yar harararta tayi tace ita da bata da masoyi ko to itama a bakin zata bata tasa dariya tace wannan ai ba matsala bane ta d'aukko ta fara bata itama tana cigaba da ci, daga inda take bayan ta cinye wainar bakinta tace ma Haisam "Babe we need to go 4 an outing sis Zarah zata k'ara jin dad'in jikinta" tana rufe baki Hajiya tace "ba dai Ajiwa Dam d'in zaku je ba?" yadda tayi Maganar har saida taba Fanan dariya ta girgiza mata kai alamar a'a, tace "ato ai naji kina ce mashi ne kina son zuwa wurin da kika ga hotunansu nayi zaton can kike nufin kuje ince to kuje ku kad'ai banda ita a samu ma ta idasa dawowa daidai" sunkuyar da kai Fatuu tayi cikin ranta ta ayyana koda ma ance za'a can d'in ba zuwa zatay ba don yanzu Ajiwa Dam na d'aya daga cikin Wuraren da bata fatan k'ara zuwa fit ya fice mata arai ya kuma shiga cikin tarihin rayuwarta ko hotunan datayi a wurin bata son gani, tana son ta tafi gida amman tasan sai gwaggo tayi Maganar dawowarta da wuri gashi bata son taga tana sa gwaggon damuwa, kiran sallar Azahar ta tadasu gaba d'aya suka tafi yin salla bayan sun gama ne kuma Saude ta sanar ta shirya Table lokacin da Haisam ya dawo gaba d'aya suka nufi Dining din harda Fatuu da suka matsa mawa duk da tace masu ta koshi taci waina amman Fanan tace taci ko kadanne ai suma sunci wainar ba yadda ta iya, ita ta fara tashi tace ta koshi don ba k'aramin karfin halin zama take tana kallon yadda suke ciyar da junansu ba Fanan tace ta jirata a parlor inta gama zata gyara mata gashinta ta amsa mata da to kawae, bayan sun gaman visitor room ta kai Fatun taje dakin Hajiya ta daukko wani dan babban kit ta dawo lokacin data bud'e ba komai ne aciki ba sai uban kayan gyaran gashi da mayuka, nuna ma Fatuu dake zaune gefen gado stool din gaban mirror tayi tace tazo ta zauna, bayan ta zauna ta fiddo stretcher ta fara mata stretching sosae take yaba kyaun gashin Fatuu da yake cike gashi baki wuluk duk da na Fanan d'in yafi shi tsawo saidae baida cika, sosae ta gyara mata shi sai shek'i yake ta d'aukko wayarta ta fara masu hotuna ta rink'a masu styles da gashin kansu iri iri, dole Fatuu ta saki ta rink'a yin yadda duk tace mata tayi sosae hotunan su kai kyau ba kamar daya kasance ita gashinta brown na Fatuu bak'i bayan sun gama yin hotunan ta maida komae cikin kit ta maidashi Bedroom din Hajiya ta iske hajiyar kwance tana bacci hakan yasa data dawo tace ma Fatuu su kwanta suma su huta ba kowa a Parlor tace mata to kawae, zuciya nason mai kyautata mata duk da halin da Fatuu take ciki sam ta kasa jin tsanar Fanan din hakanne ma yasa wani lokacin bata iya yi mata gardama, har aka kira la'asar suna bacci ringing d'in wayar Fanan ne ya tasheta ta duba screen din taga Haisam ne ke kira bayan ta dauka ya tambayeta tana ina ne ya shigo har Bedroom bai ganta ba ta fadi mashi suna bacci ne a visitor room yace su tashi suyi salla ta shirya tace to don ta gane shirin zuwa gym yake nufi, tashi tay ta koma Bedroom d'in Hajiya within few minutes tayo wanka ta fito,shiryawa tayi cikin workout outfit riga da wandonta Ash colour rigar tight long sleeve ce irin mai dogon hannu ta kamata sannan iyakarta tsakiyar cikinta sai wandon shima skin tight ne dogone ya kai har kasan rigar sun matukar fiddo mata da dirinta kuma tayi kyau sosae hijjabai guda biyu ta d'auka ta koma d'akin da Fatuu take har lokacin bacci take dama tana fama da karancin baccin yan kwanakin nan, tashinta tay ta bud'e ido tana kallonta da Murmushi tace mata ta tashi lokacin salla yayi ta d'aga mata kai kawae ta saukko, lokacin data fito Fanan din ta kabbara salla don tayi Alwala a toilet hijab din data gani ajiye ta d'auka tasa itama ta kabbara sallar, bayan ta gama saida ta jira Fatuu ta gama sannan ta sanar da ita zasu tafi Gym ne ko zata k'ara kwanciya tace mata a'a gida zata tafi hakan yasa suka fito tare Fanan ta shiga d'akin Hajiya ta maida hijjaban tasa takalma sneakers farare ta d'aura farar jacket kanta kuma ta rufe shi da veil Ash kalan kayan tayi kyau har ta gaji, sallama tayi ma Hajiya tace adawo lafiya ta fito lokacin Fatuu na zaune kan kujera a Parlor tana ganin ta fito ta mik'e ta nufeta suka fita tare suna fitowa cikin harabar gidan Haisam ma ya fito cikin shirin gym hannunshi guda rataye da katuwar jakarshi abunda Fatuu ke ji duk ta ganshi shi taji gashi ta kasa barin kallonshi har ya k'araso inda suke Fuskarshi a sake yana kallonta Fanan ta kai hannu ta curo jakar ta rataya shi kuma ya nufi Parking Space don ya fiddo bike din lokacin Fatuu tace ma Fanan ta tafi gida ta dafa Shoulder d'inta tace in ta dawo zata zo kai kawae ta d'aga mata ta nufi hanyar gate, tana karya kwana bayan ta fito gate d'in gidan bike d'insu ya taho taja gefe don su wuce, dukkansu sun sa helmet a kawunansu Fanan na goye da katuwar jakar suna zuwa inda take Fanan ta d'ago mata hannu suka wuce fuuu,tsaye tayi a wurin tana bin su da kallo har suka yi nisa kafin suka 6ace ma ganinta, kasa d'aga kafafunta tay taci gaba da tafiya, da k'yar ta matsa ta jingina da fence a cikin zuciyarta ta ke ayyana Ya Handsome baisonta bai ta6a sonta ba yanzu ne ta k'ara gaskata hakan don ta gano dalilin dayasa bai ta6a goyata a bike d'inshi ba tunda suke, duk in ta nuna tana son su hau shi in zasu fita sai yace Mota zasu hau ko kuma in yaga kaman bata ji dad'i ba yace ba yanzu ba ashe duk don kar jikinsu ya had'u ne sai yanzu ta fahimci hakan ganin da suka wuce gaba d'aya Fanan na kwance a bayanshi ta sakala hannuwanta a cikinshi, wani 6angare ne na zuciyarta yace kawae ki cireshi a ranki tunda baison ki yayin da wata zuciyar kuma tace yanzu shikenan sai ki hakura dashi duk irin son da kike mashi ina kike tunanin zaki samu wani kamarshi, wasu kwalla ne masu zafi suka fara gangaro mata ta shiga yin kuka ba tare da sauti ba don ta rufe bakinta da tafin hannunta guda,can bayan wani lokaci tasa hannu ta fara gogewa kafin da k'yar ta d'aga k'afafunta da suka yi mata wani irin nauyi ta fara tafiya, tana karasowa kopar gidansu har zatai kwana sai kuma ta tsaya kaman mai yin tunani can ta mik'i hanya taci gaba da tafiya.............., Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2005* _Destiny may be delayed but cannot be changed......_ *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 5 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........gidansu Haulat ta nufa tana zuwa bakin lungun ta hangota ta taho jikinta sanye da Uniform d'in islamiyya hakan yasa taja ta tsaya suna kallon juna har ta k'araso gabanta tana kallonta ganin yanayin fuskar Fatun yasa da yar damuwa tace "kawata ya jikin har yanzu?" gyad'a mata kai tay idanunta sun cicciko da kwalla tace "kiyi hakuri don Allah in sha Allahu komae zai wuce ki dawo kaman da wllh Allah ne shaidata bana jin dad'in halin da kike ciki Fatuu, dake nike kwana nike tashi kullum Addu'ata Allah ubangiji ya yaye maki abunda yake damunki" ta k'arasa itama idanunta sun ciko, shiru Fatun tay kaman bazata ce komae ba sai kuma Haulat taji tace "Yanzu Haulat ki fad'i man ya zanyi in daina jin son Ya Handsome" a sanyaye tay Maganar, ajiyar zuciya Haulat ta sauke kafin ta dafa shoulder d'inta tace "shi so matsalarshi kaman ciwo ne farat d'aya yake shiga amman sauki sai a hankali ba kaman yadda yay maki mugun kamu,amman ba ina nufin bazai barki ba saidae a halin da kike ciki yanzu son Ya Haisam bazai iya barinki farat d'aya ba ba kaman da yake kina ganinshi, dole sai kinyi yak'i da zuciyarki sosae duk yadda zata rink'a azalzalarki kan sonshi ki daure ki cije kar ki biye mata in akwae abunda Ya Haisam d'in ya ta6a maki wanda ya 6ata maki rai ki rinka tunano shi duk in ta ayyana maki wani abu game da sonshi........" katseta Fatun tayi tace "ni bai ta6a man komae ba na 6acin rai, kawae dai abu d'aya ne banji dadinshi ba shine yadda ya 6oye man tsakaninshi da Aunty Fanan ni nayi zaton soyayyar yan'uwantaka ce kawae tsakaninsu kinga dana sani koda ke baki sani ba lokacin da mukayi Maganar yana sona da zan fad'i maki yana da wadda yake so" shiru Haulat tayi yayin da cikin zuciyarta take ayyana cewa koda ma ya ta6a yi maki abunda ya 6ata maki rai a halin da kike ciki bazaki ji haushin shi ba, a fili tace "to ki daure kiyi kaman yadda nace maki da farko sannan ki dage da Addu'a don ba abunda yafi karfinta in sha Allahu zaki ga komae ya wuce kaman ba ayi ba" jinjina mata kai kawae Fatun tayi, da d'an Murmushi Haulat tace "kinyi kyau sosae" godiya tayi mata tana son tayi mata Murmushin itama amman ta kasa ta kama hannunta tace suje kada ta makara, akan hanyarsu ne Haulat ke tambayarta sai yaushe zata dawo islamiyyar tace mata ta kusa, a daidai kopar gidansu suka rabu Fatun ta wuce ita kuma Haulat tay tsaye har saida taga shigewarta sannan ta girgiza kai,ba k'aramin tausayi take bata ba duk tayi sanyi sai kace ba Fatuu ba daka kalli fuskarta zaka fahimci she's in serious grief, juyawa tay saida ta gaishe da kawu Amadu kafin ta wuce. Lokacin data shiga gidan bata ga gwaggo ba har Parlor da d'akinta ta duba bata ganta ba hakan yasa ta wuce d'akinta ta haye gado ta fad'a duniyar tunani,tana son ta daina jin son Ya Handsome saidae son nashi ya rinjayi hakan acikin zuciyarta, dama don ta tabbatar ma kanta da baisonta ne yasa take jin gara ta daina son nashi ta huta amman a yanzu bata da burin daya wuce taga ta aureshi wani irin son shi zuciyarta ke azabta mata dashi, a hankali ta kai hannu ta goge kwallan dake zubo mata, mik'ewa tay ta zauna tsakiyan gadon ta d'aga hannu idonta na kallon sama a fili tace "Ya Ubangijina Allah ka yaye man damuwata ka cire man abunda nake ji acikin zuciyata na son Ya Handsome tunda bai sona...." fashewa tay da kuka ta shafa kafin ta koma ta kwanta tana sheshsheka a haka bacci ya kwasheta, sai gab da sallar Magrib gwaggo ta shigo gidan dama makwabta ta shiga dubiya ganin takalman Fatuu a bakin kopa yasa ta gane ta dawo ta nufi d'akin ta d'age labule, ganinta kwance tana bacci yasa ta shiga ta tasheta tayi salla,bayan Sallar isha saiga Fanan lokacin sun dawo daga Gym yau ma Abubuwan ci ta kawo mata kamar rannan ta sanar da ita gobe around 12 ta shirya zasu fita gari kaman tace bata zuwa amman kuma a gaban gwaggo ne hakan yasa ta amsa da to kawae, tare da gwaggo suka ci abubuwan da ta kawo masu ba don tana jin dad'insu ba sai don gwaggon ta matsa mata, bayan sun gama ta bata wanda aka d'ibar ma Amadu ta fita ta kai mashi bayan ta dawo saida ta watsa ruwa ta canja kaya zuwa na bacci sannan ta kwanta sai faman sak'e sak'e take aranta kaman ko yaushe don sam bata jin bacci saboda tayi na yamma koda gwaggo ta shigo yi mata Addu'a isketa tay idonta biyu tace to in ta tashi yin baccin ta tabbatar tayi ta amsa mata da toh. Washe gari tun bayan data yi breakfast ta tattara kayan wanke wanke tayi tana niyyar yin shara gwaggo tace ta barshi zatayi hakan yasa ta koma tay kwanciyarta, wuraren karfe sha d'aya da wasu mintuna gwaggo ta lek'a dakinta ganinta kwance yasa tace mata ba zasu fita bane tay kwance ta daure ta tashi ta shirya ta amsa mata da to, bayan ta tafi ta yunkura ta mik'e zaune ta zuro kafafunta k'asa har cikin ranta bata son fitan don tasan dole taga Ya Handsome kuma duk inta ganshi ita kad'ai tasan mi take ji, wani dan Murmushin takaici tay wai yau itace ke gudun ganin Ya Handsome, da k'yar ta mik'e ta nufi wardrobe d'inta ta cire kayan jikinta d'aura towel tay ta wuce Toilet, bayan ta fito mai kawae ta shafa tasa undies ta zumbula doguwar riga ta koma gado tay kwance, K'arfe sha biyu saura mintuna kad'an Fanan ta rafka sallama har saida Fatuu ta runtse idanunta jin muryartata, Ma sha Allah abunda na fad'a kenan ganin shigar da tayi ta kwankwatsetsen leshi Coffee brown yana da touches din light brown an mata wasu matsiyatan riga da skirt da suka bi shape d'inta skirt d'in daga k'asa ya bud'e sosae haka hannun rigar ma ya d'an kumburo k'afafunta sanye da takalma masu tsini sosae brown haka hannunta tana rike da yar madaidaiciyar jaka louis vuitton brown colour, tun daga kunnuwanta da wuyanta da hannayenta duk zinari ne harda zobban yatsun hannunta ta kifa daurin kallabi zarah buhari da alama tana son irin d'aurin gashin kanta ta lankwasashi ya tsaya k'asan shoulder d'inta ta d'aura d'an veil brown color a kafadarta d'aya da bata ma sa gyalen ba saida Haisam yay mata Magana sannan ta d'aukko tasa, tsayawa tay bakin Kitchen suna gaisawa da gwaggo data lek'o tana washe baki ta shiga kod'a kwalliyarta tana Fad'in "Tubarkallah ma sha Allahu d'iyata kin matuk'ar yin kyau, d'ana ya barki kikai kwalliya haka karfa a kwace mashi ke" dariya sosae Fanan ke yi jin Maganar gwaggon tace "ni tashi ne ai ba wanda zai iya mashi snatching" gwaggo tace "tabbas wannan haka yake" tambayarta tay Fatuu tace "tana d'aki tun da tay wanka ta shige nasan zuwa yanzu ta shirya bari in kirata" tana niyyar fitowa Fanan tace ta barshi bari tay mata Magana ta nufi d'akin, tana d'aga labule suka had'a ido da Fatuu data tashi zaune jin ta zata shigo, nufar ta tay ta zauna gefen gadon ta kamo hannunta tace "Zarah are u ok?" kai ta d'aga mata alamar eh, kallon jikinta ta d'anyi tace " ya baki shirya ba?" a hankali tace mata ta shirya, "But u doesn't look gud in dis" tay Maganar ta d'an kamo rigar jikinta ita dae shiru tay mata hakan yasa ta tambayeta a ina kayanta suke ta nuna mata bangaren da kayanta suke a wardrobe da hannu ta mik'e ta nufi wardrobe d'in idon Fatuu a kanta ita kanta tayi mata kyau sosae, dudduba kayan ta shiga yi can ta fiddo wasu riga da skirt na Red lace a sallar data wuce Haisam ya yi mata su, lokacin data juyo da kayan har saida gabanta ya buga, aje mata su tayi gabanta tace ta sasu zasu fi yi mata kyau akan wannan rigar, ba yadda ta iya dole ta saukko daga gadon ta d'auki kayan ta fita, bayan wani lokaci ta dawo ta saka su Fanan na ganinta ta saki Murmushi ta hau yaba kyaun da kayan suka yi mata don itama sun kamata sun fito mata da k'irarta saboda yanzu sun saba da Kb mai d'inki yasan irin d'inkin da take so duk da gwaggo bata son ana mata matsattsun kaya saidae bata ma sanin an kai d'inkin saidae ta gansu an kawo taita fad'a, kama hannunta tay ta kaita gaban Dressing Mirror yar light makeup tay mata ta tambayi inda jewellery d'inta suke ta nuna mata drawer chest tana jawowa tay arba da sark'a mahad'in kayan silver ce mai adon red stones harda d'an hannu da zobe ta d'aukko su ta saka mata ta sake d'aukko agogo zata saka mata Fatun tace ta barshi d'an hannun ya isa ta amsa mata Ok, d'aurin kallabi mai kyau tayi mata bayan ta gyara mata gashinta ta d'aure tun kafin ta tambayi takalma Fatun ta curo daga kan shoe rag dake gefen mirror d'in ta saka, d'agowa tay tana kallon kanta a madubi yaushe rabon data yi gayu haka,had'a ido sukai da Fanan ta cikin mirror d'in ta sakar mata Murmushi itama ta d'anyi mata suna cikin haka gwaggo ta d'aga labule ganinsu tsaye yasa tace "kar dai 6ata maki lokaci tay bata shirya ba tun d'azun" tana Murmushi tace "No ta shirya granny na sa ta canja kaya ne" kai gwaggon ta jinjina kafin ta saki labule, bayan ta yafa gyalen kayan da takalma bata d'auki jaka ba suka fito, gwaggo ta fito daga cikin kitchen sukai mata sallama kafin suka wuce idanunta akan Fatuu sosae taji dad'in ganinta tayi gayu haka, Wata rantsattsiyar Mota ce brown fake a kopar gidan bata ma ta6a ganinta ba suka nufeta Fanan ta bud'e mata baya ta shiga ta rufe itama ta bud'e gaba ta shige,wani masifaffen kamshine ke tashi cikin motar hadi da ni'imtaccen kamshin ac, yana zaune jikinshi sanye da jugunannar brown shadda da akai ma fav dinkinshi wato Sen style kanshi ba hula sumar nan tasha gyara sai salk'i take, tana shigowa ta kai hannu ta kama hannunshi guda tace "Sorry babe we kept u waiting" jinjina mata kai yay lokacin suka had'a ido da Fatuu ta cikin Mirror ta gaidashi a sanyaye ya amsa daga haka yaja Motar suka tafi, tunda suka hau hanya bata ce uffan ba sai Fanan ce keta mashi hira hannunta guda ruk'e da nashi hannun yana driving da d'aya wani lokacin kuma ya kan janye hannun kaman in zai sha round, sai Fanan d'in ta sakota sannan take bud'e baki tay Magana, kopar Marusa lowcost ya nufa dasu gidansu Nana suna tsayawa bakin gate d'in gidan Nanar ta fito dama tana ta dakon zuwan nasu don Haisam ya sanar da ita game da zuwan nasu, rungume juna sukai ita da Fanan cike da farinciki take mata sannu da zuwa bayan sun saki juna ta kai idonta kan Fatuu dake tsaye gefe da Murmushi ta kamo hannunta tana mata sannu da zuwa, nufar Motar tay Haisam ya bud'e kopar suka gaisa tace "lallai zakee wannan too match haka kaida Amarya kaman dae an d'aura" yana Murmushi yace mata miya rage ne, ce mashi tay yini zasuyi ko yace zaije dae ya dawo After zuhr akwae wuraren da zasu je, lokacin data shiga dasu gidan gaba d'aya yan gidan na a Falo don a k'agare suke da suga wadda Zakee zai aura don ba k'aramin zuzuta ta Nana tay a wurinsu ba,suna shiga duk suka mik'e suka tarbesu da fara'a suna masu sannu da zuwa kowa idonshi na akan Fanan dake ta masu dariya, bayan sun zauna duk suka shiga gaishe da ita tana amsa masu Fatuu ma ta gaidasu duk suka kira sunanta suka ce tana lafiya da yake sun santa yanzu sosae don duk salla gidan Haisam ke kawota kunshi harda kitso in tana so, wani lokacin ma hakanan in ya fito da ita kaman da yamma in ba islamiyya sai ya kawota gidan idan ya dawo sai yaje ya dauketa yanzu Nana ta san tsakaninta da haisam d'in don akwae lokacin data je gaida Hajiya lokacin taje gidansu Fatun suka gaisa da gwaggo, abubuwan ci da sha aka shiga jera masu kafin a gama Abinci,Fanan ce ta fara ci ita Fatuu cewa tay ta koshi Nana tace wai ko bata lafiya ne ita fa ta lura duk tayi sukuku ba kaman yadda ta santa ba tana rufe baki sauranma sukace duk sun lura da hakan harda mommy d'insu, Fanan ce ta gaya masu bata lafiya ne bata dad'e ma data fara samun sauki ba duk suka hau yi mata ya jiki tana amsa masu suka ce Allah ya sawake,saida Nana ta matsa mata sannan ta d'an ci wani abu, fira sosae suka shiga yi da Fanan dama ita bata da bak'unta ita dae Fatuu baka jin bakinta saida aka kira sallar Azahar Nana ta jasu d'akinta suka yi salla Fatuu na gamawa ta kwanta kan abun sallar su kuma suka ci gaba da yin fira a tsakaninsu har Fanan nace mata za dai tazo bikinsu ko Nanar tace ai ko a India akeyi sai taje balle Lagos Fanan d'in tace ai a Abuja ma take tunanin za'ayi just bai wuce ay wasu programmes a Lagos sannan a dawo Abuja a nan za'a daura aure, duk hirar da suke Fatuu na jinsu jin Maganar aurensu da Fanan ke yi yasa ta runtse idonta sosae kirjinta yay mata wani irin nauyi, suna cikin firar kanwar Nana tazo tace ga abinci can an shirya Fanan tace a kawo masu shi nan kawae tace to ta juya, bayan an kawo kayan Abincin Nana tay serving nasu Fanan tace ta zuba masu gaba d'aya su ci tare tana dariya tace "an gama Amaryarmu" kiran Fatuu ta fara yi ta tashi su ci abincin tana ji tay mata shiru har saida ta d'an bubbuga kafafunta sannan ta amsa mata koda tace mata ta tashi suci Abinci cewa tay ta koshi zuciyarta tashi take zata iya yin amai jin hakan yasa ta kyaleta suka fara ci su biyu har Nana na cewa gaskiya tana jin jiki Zarah mai Magana ka ganta haka Fanan tace ai da sauk'i ma yanzu, Bayan sallar Azahar Haisam yazo ya d'aukesu Nana da kannenta sukae masu rakiya har Mota don basu gaji da kallon Fanan d'in ba gaba d'aya ta tafi da hankalinsu, lokacin da suka isa bakin Motar bayan sun gaida Haisam har ce mata sukae amman dai Aunty zaki dawo ki mana wuni ko Nana tace ma Haisam ai gaskia wannan ba zuwa bane dole ya maido masu ita wuni shi dae murmushi kawae yake Fanan d'ince tace masu zata dawo kafin ta tafi in sha Allah Fatuu dai na tsaye gefe ta jingina da Motar duk ta k'agara su tafi ita in son samu nema su maidata gida kawae, sallama sukai masu harda Fatun suka shige mota suna d'aga masu hannu suka tafi sannan suka koma cikin gidan suka hau yabon Fanan. Daga nan Gra suka wuce gidansu khairat wanda tangamemen gidane had'addan gaske don babanta dan Majalisa ne a Abuja basu cika ma zama anan Katsina ba sunfi zama a Abuja yanzu ma don ana hutu ne,tayi murna sosae da zuwan Fanan haka Fatuu ma hannu biyu ta kar6eta tare da sauran yan gidan har tana tambayar Fanan sis d'insu ce tace mata eh don ranar da ta kai Fanan gidan Hajiya itama bata lura da sadda Fatun ta fito daga Mota ba ta shige gida lokacin idonta na akan Fanan da Masoyinta, lafiyayyan Abinci da abubuwan ci da sha aka jere masu akan c-table da khairat tace a shirya table Fanan tace ba wani ci zasuyi sosae ba don sun ci Abinci ita Fatuu ma cewa tay ta koshi saida khairat tace ya za'ai tazo gidansu first time tace kuma bazata ci komae ba, dole ta d'an tsakuri wasu abubuwan itama Fanan ba wani mai yawa taci ba suna cikin fira Haisam ya kirata su fito su tafi khairat d'in tace ita gaskiya bata yarda ba cewa tay zatai spending whole day shine daga zuwa zasu tafi saida tace mata ai zata dawo kafin ta tafi sannan ta yarda ta rakosu har waje bayan sunyi sallama da yan gidan harda kyautar undies da turare guda ukku masu kyau da tsada taba Fatuu tay mata godiya, suna baro gidansu khairat zagayawa yay dasu gari sai gabda la'asar suka wuce gidan Abbas suna yin parking Abbas da dama jiransu yake ya nufi Haisam yana dariya suka gaisa ya kalli Fanan data fito yace "Our bride u'r highly welcome" amsa mashi tayi da "thank u Abbas" tana dariya ya kai idanunshi kan Fatuu ta d'an yi mashi Murmushi yace "Mom Zarah kwana biyu" ita dae murmushin yak'e kawae take mashi kafin suka nufi ciki suna shiga entry din Falon Feenah ta tar6esu da fara'a tana sanye da doguwar rigar lace hannunta ruk'e da babynta data sake haifa kusan shekara d'aya data wuce, hannu Fanan ta mik'a mata ta amshi babyn da fara'a tace "What's her name?" tace "Nasreen" Abbas ne yace su shiga ciki mana, jin an fara kiran salla yace bari suje suyi salla su dawo suka juya da Haisam, cikin falon suka nufa bayan sun zauna suka gaisa da juna Fatuu ma ta gaishe da ita ta amsa tana ce mata kwana biyu itama Murmushin tay mata kawae ta mik'e taje ta kawo masu ruwa da lemu da d'an abun ta6awa ta koma ta zauna bayan ta zuba masu lemun a cups, hira sosae suka shiga yi da Fanan dama sun san juna ta waya badai su ta6a ganin juna ba a zahiri ita Feenah ta ta6a ganin pic d'in Fanan wanda suka yi tare da Haisam a wayan Abbas, bada jimawa ba su Abbas suka dawo akan 3 seater suka zauna Feenah ta gaida Haisam ya amsa mata fuskarshi a sake Abbas yana Murmushi yace ma Fanan "Amaryarmu zuwa ba sanarwa mu shirya maki sosae" tana dariya tace "it was a suprise" jinjina kai yay yace mata anzo lafiya ya karatu ta amsa mashi da Alhamdulillah, kallon Fatuu yay da tay shiru gefen Fanan da yake kan sofa 2 seater suka zauna yace "Mom Zarah ya karatu?" a sanyaye tace mashi lpy lou yace "an kusa graduation ko?" kai ta d'aga mashi alamar eh yace to Allah ya bada sa'a ta amsa da Amin ta tambayeshi ina Abdul yace yana tahfiz daga haka ya juya kan Fanan suka cigaba da hirar india ita kuma ta d'an kwantar da kanta tay shiru sai kace bata a falon can Abbas yace "Wai Mom Zarah kodae baki Lafiya ne?" d'ago kanta tay ta kalleshi kafin ta bashi amsa Feenah ta rigata cewa"Wllh Dear nima am about to ask her shirun nata yay yawa" shiru tay tana binsu da ido ta rasa mi zata ce Fanan tace masu ai bata lafiya ne almost a week yanzu ne ta d'an samu sauk'i har suka fito tare, jinjina kai sukae gaba d'aya sukai mata Allah ya sawake ta amsa masu da Amin suka cigaba da firarsu ita kuma ta koma ta jingina da kujera tana binsu da ido, tun bayan da Abbas yay Maganar jefi jefi yake juyawa ya kalleta duk in ya kalleta kuma sai su had'a ido hakan yasa tasha jinin jikinta sai yan kame kame take, wani d'an guntun Murmushi yay bayan sun k'ara had'a ido da ita yace "Mom Zarah ko ki shiga ciki ki kwanta" kafin ta bashi amsa Feenah tace "amman dear yamma yayi fa kuma ba'ason bacci irin wannan time en ba kaman ita da bata lafiya, "ai dama ba ina nufin tay bacci ba ta d'an hutu looks like she isn't comfortable here" kai Feenah ta d'aga tace "amman fa bata ci komae ba just drink tasha, kallon Fatuu yay still da Murmushi a fuskarshi yace " Mom Zarah ana ciwo ba cin abinci ai baza'a warke da wuri ba kuwa, ki daure kici Abinci" shiru tay tana kallonshi kafin ta kai kallon kan Haisam da tunda Abbas ya fara mata Magana yake kallonta, a hankali ta sunkuyar da kanta jin bugun da kirjinta ya fara ga kwalla dake neman zubo mata Abbas yace in bata son ci taje kawae aikuwa da sauri ta mik'e ba tare data yadda sun had'a ido da kowa ba ta nufi Bedroom d'in Abdul ta shige, Abbas da ya bita da ido ya juyo ya kalli Haisam yace "miyake damunta ne?" yana daga kishingid'en da yake ya fad'i mashi matsalar Aljanu ne da mamaki Abbas yace "Aljanu kuma, dama Mom Zarah nada Aljanu?" kai ya d'aga mashi kafin yace mashi shima bai san tana dasu ba sai yanzu, shiru Abbas yay kaman mai nazarin wani abu cikin ranshi ya ayyana dis is more like a heartbreak ba Aljanu ba,can ya tambayi Haisam waye yace tana da Aljanun, farko shiru ya d'an yi mashi sai kuma yace mashi a wurin Hajiya yaji daga haka bai k'ara cewa komai ba shima Abbas d'in bai k'ara tambayarshi wani abun ba, misalin karfe shidda mai d'aukko Abdul ya kawo shi cike da farinciki ya ruga ya haye Haisam yana fad'in "Baba Zakee ashe kazo" kai Haisam ya d'aga mashi yace "My Boy ka girma fa yanzu kana haye babanka haka zaka karya shi" kyalkyacewa yay da dariya Fanan ta bisu da kallo tana murmushi don tana son yara ba kamar yadda ta gansu haka yanzu sun burgeta shiyasa burinta suyi aure itama ta haihu, Abbas ne yace mashi ga Momy d'inshi nan tazo yaje ya gaishe da ita da sauri yace "Aunty Zarah?" girgiza mashi kai yay ya nuna mashi Fanan dake mashi dariya ya k'ura mata ido yana kallonta can ya juya ya kalli Abbas yace "ba Aunty Zarah ce Mommy na ba?" Abbas dake Murmushi yace "yeah ita Mom d'in Zakee ce ita kuma wannan Mom d'inka ce kai kadae kaman yadda Zakee yake babanka" da mamaki yace "to Matarshi ce?" Abbas yace "eh itace zai aura" bin ta yay da kallo ganin haka yasa Abbas yace yaje ya gaidata ya saukko daga jikin Haisam ya nufi wurinta yana zuwa ta rungume shi tana tambayarshi ya Makaranta yace mata lpy lou tace yana dai kokari ko yace mata eh duk bai wani saki jiki ba, can ya janye jikinshi ya koma wurin Abbas yace "Dad ina Mom Zarah ba'a zo da ita ba?" Yace "Tana d'akin ka bata jin dad'i ne" zaro ido yay yace "bata lafiya" kai Abbas ya d'aga mashi aikuwa da gudu ya nufi d'akin nashi suka bishi da ido da d'an Murmushi kan fuskokinsu, tun a bakin kopa ya fara kiran sunanta yana shiga ya ganta ta dukunkune saman gado baiwar Allah da k'yar ta samu bacci ya dauketa,hayewa yay saman gadon gefenta ya fara bubbuga jikinta yana kiran sunanta, a hankali ta bud'e idonta da sukai ja ta kalleshi tana ganin shine ta yunk'ura ta tashi zaune da d'an Murmushin da iyakarshi lips d'inta tace mashi ya dawo bai bata amsa ba ya kama hannuwanta da yar damuwa yace "Aunty Zarah wai baki Lafiya" shiru ta d'anyi tana kallonshi shima kallonta yake ba komae take tunawa ba sai farkon kawota gidan lokacin da sukai game dashi cike da nishadi da kuma sauran lokutta, ita yanzu shikenan haka zatai ta zama da damuwa ta ayyana a ranta kawae sai ta fashe da kuka, waro ido Abdul yay a rud'e yace "Aunty Zarah kuka kike" shiru bata ce mashi komae ba ta rufe bakinta da tafin hannunta, kokarin sauka daga kan gadon ya fara yi yana fad'in "bari inje in gayo ma su Dad baki lafiya kina kuka azo akai ki Hospital" da sauri ta kamo hannunshi tana girgiza mashi kai yace "kar naje na fad'i masu?" d'aga mashi kai tay alamar eh yace "to ki daina kukan don Allah" yadda yay Maganar kaman shima zai sa kukan, a hankali tace to ta daina ya kai hannu yana goge mata hawayen, da k'yar ta samu hawayen suka tsaya cikin muryar wanda yay kuka tace mashi ya Makarantar yace lafiya lou tace yana dae kokari ko yace eh sosae,shiru sukai na d'an lokaci can yace "Aunty Zarah yau bazamuyi game ba tunda baki lafiya ko?" kai ta daga mashi alamar eh yace "Allah ya baki lafiya sai mu yi" a hankali tace Amin suna cikin haka sai ga Abbas ya shigo d'akin Abdul na jin sallamarshi ya sauka daga gadon da sauri ya nufe shi yana fad'in "Daddy Aunty Zarah tayi kuka a kaita Asibiti" jinjina mashi kai yay ya nufi cikin d'akin ya tsaya gabanta yana kallonta kanta na kasa tunda taji Abdul yace tayi kuka, slowly Abbas ya kira sunanta ta amsa ba tare data d'ago ba hakan yasa yace ta kalleshi kaman bazata d'ago ba can ta d'ago da jajayen idanunta ta kalleshi duk ta kame kanta, "In akwae abunda ke damunki banda ciwon da akace kar kiji komae ki fad'a man" da sauri ta girgiza mashi kai tama kasa yi mashi Magana, d'an Murmushi yay yace "to miyasa kike kuka?" murya na rawa tace "d...da dama jikin nawane bana jin dad'inshi..." shiru ya d'anyi kafin yace "an kai ki Asibiti ne?" "A'a, amman Aunty Fanan tayi man Allurar zazza6i ta kwana ukku nama samu sauki sosae yanzu" "Ko mu kaiki Asibiti to tunda kince jikin naki har yanzu bai maki dad'i" taji ya fad'a, da sauri ta girgiza mashi kai tace "a...ai gwaggo tace ciwon bana Asibiti bane tasa anyo man Addu'a a ruwan zam zam ina sha" shiru yay yana cigaba da kallonta hakan yasa ta sunkuyar da kanta don gabanta wani irin bugu yake mata ita tsoronta wai kar ya gano mike damunta ya fita ya fad'i masu, sigh yay yace mata Allah ya bata lafiya ta amsa da Amin ya kalli Abdul yace ya cire Uniform d'in jikinshi yasa kaya yazo zasu je Masallaci ya amsa da to, wani sanyi taji bayan Abbas d'in ya fita Abdul ya nufi wardrobe d'in kayanshi don ya canja kaya bayan ya d'aukko wanda zai sa ya juya yace ma Fatuu wai ta juya zaisa kaya bata san lokacin data saki dariyar da rabon da tayi irinta ta manta, kifa fuskarta tay jikin pillow tace bata ganinshi yasa ya amsa da to, bayan ya fita saiga Feenah ta shigo da Murmushi ta nufi Fatun tana tambayarta ya karfin jikin tace mata da sauk'i tace to ta tashi tayi salla ta amsa da to ta mik'e ta nufi toilet itama ta fice dama Fanan ta kai d'akinta tayi salla shine tazo wurin Fatun, suna dawowa daga sallar Haisam yace ma Abdul yaje ya kira Zarah zasu tafi, tare suka fito dashi ya ruk'o hannunta idonsu akanta hakan yasa duk ta dabarbarce ta sadda kanta k'asa har ta k'arasa cikin Falon ta zauna kusa da Fanan, Abbas ne yace ko zasu tafi sai taci Abinci sannan, ba yadda ta iya dole ta d'an ci Abincin da Feenah ta zuba mata, har bakin Mota suka yo masu rakiya Feenah tace ma Fanan in sha Allahu kafin ta tafi tana nan zuwa dan da suna hira tace mata upper Monday zata tafi tace to tana jiranta, sallama suka yi masu suka k'ara yi ma Fatuu Allah ya sawak'e Abdul ya d'aga mata hannu yana mata bye bye itama ta d'an mashi kafin ta bud'e Mota ta shige suma duk suka shiga yaja suka bar gidan........... Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2006* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 6 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .......bayan sun baro gidan Abbas a wani Shopping complex ya tsaya dasu yace ma Fanan suje suyi shopping ta amsa mashi da owk ta bud'e Motar ta fita shima bud'e kopar side d'inshi yay har zai fita ya dakata ya juya ya kalli Fatuu dake zaune suka had'a ido, "Ki fito zamuyi shopping" ya fad'a da cool voice d'inshi, girgiza mashi kai tay a hankali tace "ni bani buk'atar komae" wani kallo ya bita dashi da sauri ta sunkuyar da kanta kirjinta na bugawa da sauri da sauri, "Let's go Zaraah" wani yamm taji a jikinta duk cikin masu kiranta da Zarah ba wanda ya kai shi iya Fad'a gashi da wani irin sauti mai dad'i sunan ke fita, d'agowa tay suka had'a ido kawae sai ta Fara yamutsa fuska tana ta6e baki alamar zatayi kuka dama har yanzu bata bar ta6e baki ba in zatayi kuka tun yarinta, still yay yana bin ta da ido sai far far take da ido don kada kwallan su zubo mata kawae sai yay wani murmushin gefen baki ya d'an girgiza kai ya fice daga Motar, zagayawa yay side d'in da Fanan take tsaye tana amsa waya tana ganinshi tace ma wanda suke wayan zata kira daga baya tay rejecting call d'in, ganin ba Fatuu tace mashi Zarah fa yace zuje kawae zasu d'aukar mata abunda ya dace ta amsa da Ok, sosae sukai shopping bayan sun gama aka zuba masu a shopping bags aka biyo su dasu, jakar da suka siya ma Fatuu kaya Fanan ta bud'e baya gefenta ta aje sauran kuma aka saka masu a boot daga haka suka shige Motan suka tafi,suna kan hanya jin shirun Fatun yay yawa yasa Fanan ta kira sunanta tana jinta tay mata shiru hakan yasa ta juya baya ta kalleta ganin ta langa6ar da kai gefe yasa tay tunanin bacci take, suna k'arasowa kopar gidansu ta bud'e Motar ta fita Fanan ma ta fito ganin bata d'auki kayan ba yasa ta tsaidata ta bud'e bayan ta d'aukko mata don tayi tunanin ko bata san nata bane har da ledan kayan da khairat ta bata, tana tsayen kafin Fanan ta d'aukko mata glass d'in gaban ya sauka Slowly, da sauri ta kai idonta wurin suka had'a ido dashi da yake akwae wuta globe din gaban shagon kawu Amadu ya haske wurin, ya d'an kwantar da kanshi jikin headrest kasa jure ma kallonshi tay ta sadda kanta k'asa lokacin Fanan ta mik'o mata jaka guda ita ta ruke mata guda tace suje, har lokacin idonshi na akanta ta juya kawae sai taji kaman bata kyauta ba don bai ta6a yi mata abu ba ba tare data gode mashi ba kuma hakan hud'ubar gwaggo ce, tsayawa tay Fanan ta juyo kafin tayi mata Magana tace mata zatai mashi godiya ne ta amsa da Ok tay gaba abunta, a hankali ta nufi Motar kamar wadda kwae ya fashe mawa a ciki ta tsaya gaban kopar tana kallonshi ba tare data ce mashi komae ba shima kuma baida niyyar tanka mata can ta bud'e baki da k'yar tace "Nagode Allah ya saka da Alkhairi" shiru kaman bazai tanka ba sai kuma taji yace "Ameen" k'okarin juyawa ta tafi ta fara yi taji yace "Zaraah?" wani mugun bugu k'irjinta yai dammn ta juyo a d'arare ta kalleshi gently yace "kina da wani problem ne?" a hankali ta girgiza mashi kai alamar a'a, "Then why d change?" wani irin harbawa zuciyarta take ita tsoronta ma kar Fanan ta fito su tutsiyeta tare har su gano abunda ke damunta don a yadda take ji komae zai iya faruwa, "am talking to u zaraah why u look different?" baki na rawa kaman zatai kuka tace "b..ba..banjin dad'in jikina ne ba kasan ban Lafiya ba" shiru yay yana nazarin Maganar calmly yace "Ok i understand, ki fad'a ma grandma d'inki zamuje hospital tomorrow" da sauri ta d'ago ta kalleshi tace "ai ba ciwon Asibiti bane Addu'a ake man kuma anyo man ina sha" ta kai Maganar tana sussuna kai k'asa don wani irin kuka ne ke taho mata, Sigh yay yace mata zata iya tafiya Allah ya bata Lafiya da sauri ta amsa da Amin ta juya a harhard'e ta nufi gidan tana shiga zaure ta lafe a jikin bango ta tura gyalenta a baki ta fashe da kuka,can zuciyarta ta raya mata kar Fanan ta fito ta ganta haka da sauri ta goge kwallan ta d'auki ledan ta shiga cikin gidan, a bakin kopar Parlor ta hangi takalman Fanan ta jiyo muryarta ita da gwaggo hakan yasa ta aje ledar a gefe ta nufi hanyar toilet, jin motsi yasa daga cikin falon gwaggo ta tambayi waye tace itace zata shiga toilet ne, koda ta shiga kukan taci gaba da yi, ita kanta yanzu tsoron fad'i ma Haisam d'in take game da son nashi don ta yarda da Maganar Haulat ta zata jefa kanta a wata Matsalar ne,har saida taji gwaggo ta rako Fanan suna sallama sannan bayan ta tafi ta wanke fuskarta sosae ta d'auro Alwala ta fito cikin sa'a tana fitowa taga gwaggo ta kabbara sallar isha hakan yayi mata dad'i don bata son ta gano kukan da tay, itama sallar taje d'aki tayi bayan ta gama sosae tayi Addu'a kan halin da take ciki daga baya ta kwanta kan abun sallan, tana kwancen gwaggo ta d'aga labulen ta kira sunanta tace ko har ta kwanta, d'an d'ago da kanta tay tace mata eh ta gaji ne sosae bacci take son yi tace "to bazaki ci Abinci bane?" d'aga mata kai tay tace "eh banjin yunwa munci Abinci" jinjina kai tay tace to ta tashi ta hau gado kuma ta tabbatar tayi Addu'a ta amsa mata da to ta juya ta tafi, mik'ewa tay ta cire kayan jikinta har zata nufi gado taji kuma ruwa take son ta watsa ta nufi toilet bayan ta yafa mayafi a kanta, tun bayan data fito ta saka kayan bacci ta haye gado ta dasa sana'ar tunane tunanenta, tabbas tana son ya Handsome sosae to amman ta gane ba samunshi fa zatayi ba matuk'ar yana tare da Fanan yanzu ya zatayi, nan take ta gano bata da wata mafita da ya wuce tay hakuri dashi tayi yak'i da zuciyarta kaman yadda Haulat tace mata, yin wannan tunanin yasa ta saukko daga kan gado ta d'aukko Al'qurani ta fara karantawa acikin zuciyarta bayan wani lokaci ta rufe ta d'aga hannuwa harda kwallanta ta rok'i Allah daya cire mata son Ya Handsome, bayan ta gama ta mayar dashi cikin jakarta ta koma kan gado tay lamo tana cigaba da zubar da kwalla a haka bacci yay awon gaba da ita. Washe gari data tashi ba laifi ta d'an ji k'arfin jikinta bayan tayi breakfast ta fara ayyukanta gwaggo nata jin dad'i duk in suka had'a ido sai tay mata d'an mumushi,da yake aikin safe take Fatun ta tambayeta mi zata dafa kafin ta dawo tace ayyukan bazasu yi mata yawa ba kuwa ko ta samu wani abun taci in ta dawo sai tayi Fatun tace ba komae zata iya, ta fad'i mata abunda zata dafa kafin ta tafi, tana ta ayyukanta tana tunane tunane har ta gama komae tayi wanka tay kwanciyarta, rashin zuwan Fanan ba k'aramin dad'i yay mata ba don ta fahimci duk in ta gansu su biyun k'ara mata ciwon suke,k'arfe biyu da wani abu gwaggo ta dawo lokacin Fatuu nata bacci abunta ba laifi yau ta samu bacci sosae bata tasheta ba ta wuce d'aki ta kimtsa kafin ta fito ta nufi Kitchen sosae taji dad'in ganin Fatun tayi Abincin lafiya lou ga Kitchen din tsaf a cikin ranta take godiya ga Allah da ya amsa addu'arta da take ma Fatun, sai wurin karfe ukku ta farka tayi mamakin irin baccin da tayi da har bata san gwaggo ta dawo ba, ana kiran sallar la'asar ta watsa ruwa tay salla ta fara shirin zuwa islamiyya, bayan ta gama ta lek'a d'akin gwaggo tace mata ta tafi islamiyya tana washe baki ta hau yi mata Addu'oi har da fitowa wai bari tayi ma yar autarta rakiya waje ta rungumo kafad'unta Fatun tasa dariyar da yaushe rabon da gwaggon taga tayi ta, Lokacin data je Haulat bata kai ga zuwa ba nan yan ajin suka hau yi mata ya jiki don Haulat ta sanar da rashin lafiyan nata, lokacin da Haulat ta shigo ajin suna had'a ido da Fatun ta nufeta da yar sassarfa ta duk'a ta dafata tana washe baki tace ta samu sauk'i kenan ta jinjina mata kai kawae, zama tay sosae taci gaba da k'arfafa mata guiwar tayi hakuri ta cire shi daga ranta ba tare da wani ya ji maganar da suke ba a haka har Malam ya shigo, bayan an tashi ma akan hanyarsu ta dawowa shawarwari taci gaba da bata ita dae saidae ta d'aga mata kai kawae duk da tana son amfani da shawarwarin saidae har lokacin ba abunda ya canja na daga son ya Handsome a cikin zuciyarta, bayan ta koma gidane gwaggo ke fad'i mata Fanan tazo tace da daddare zata dawo tace to kawae. Gaba d'aya satin guje ma duk wani abu da zai kaita gidan Hajiya take in gwaggo tace taje da ta fito sai ta wuce gidansu Haulat, Fanan har Maganar rashin zuwan nata tayi don a tunaninta ta samu sauk'i tace mata islamiyya take zuwa da yamma da safe kuma ita ke aikin gidan, sosae ta fahimceta bata sa komae a ranta ba ita taci gaba da zuwa, ba laifi kuma Fatun ta d'an k'ara sakar mata jiki, a cikin satin Haisam ya kaita gidansu Khairat ta wuni bata samu kara zuwa gidansu Nana ba amman ita tazo harda k'annenta yan mata guda biyu suka kawo mata kaya harda atampopi don ranar Monday zata tafi, Feenah ma tazo itama ta kawo mata abubuwa d'inkakkun Material masu kyau da tsada kala biyu sai kayan kamshi su humra da kullacca har gidansu Fatuu taje ta k'ara yi mata ya jiki suka gaisa da gwaggo Abdul yaji dad'in ganinta tana ta mashi dariya har yana cewa da yasan ta samu sauk'i da yazo da tab d'inshi sun yi game, Feenah tace shi damuwarshi kenan game ko duk suka yi dariya gwaggo tace ina ruwan yaro, daga baya suka yi masu sallama suka tafi Fatuu ta rako su kopar gida, Ranar Friday da safe gaba d'aya Haisam da Fanan da Hajiya suka tafi Daura suka zaga dangi Fanan ta gaisa da su sai washe gari da yamma suka baro daurar suka biya Ajiwa Dam sosae wurin ya burge Fanan Hajiya ma taji dad'in zuwa wurin Fanan tay masu hotuna ba kamar ita da Haisam sai bayan Magrib suka dawo ta gaji sosae shiyasa bata je gidansu Fatuu ba sai Washe gari lahadi bayan sun gama breakfast ta shirya ta nufi gidan Harda tsarabar Daura, lokacin data je Fatuu bata nan tana islamiyya hira suka d'anyi da gwaggo tay mata godiyar tsaraba, Fanan d'in tace in ta dawo ace mata tana nemanta gwaggo tace zata fad'i mata da ta dawo, bayan Fatun ta dawo ta canja kaya gwaggo ta kirata ta sanar da ita sak'on Fanan na tana son ganinta har saida ta d'anyi jimm don rabonta da gidan Hajiya tun wanccan satin haka haisam ma rabon data sanya shi a idanunta tunda suka je gidan Abbas sosae take guje ma ganinshi ba kuma don bata son ganinshin ba, bayan taci Abinci tayi sallar Azahar Gwaggo tace mata taje kar Fanan d'in taita jiranta ba yadda ta iya dole tace to bayan ta fito zata tafi ne ta kirata ta bata wata leda dake k'ulle tace ta kai mata, tunda ta tunkari gidan kirjinta ke bugawa hakanan ta daure ta k'arasa har Officer nace mata kwana biyu dama tana gari ta amsa mashi da eh kawae ta shige, da zata wuce har saida ta kalli Corridor d'in shiga part d'in Haisam ta d'an girgiza kai tunowa da baya yanzu shi kanshi mai part d'in ma gudunshi take rayuwa kenan, lokacin data shiga Falon Hajiya gaba d'aya suna zaune harda shi Haisam d'in kamar ko yaushe dai Fanan na manne dashi jikinta sanye da rigar shan iska wadda iyakarta guiwa santala santalan k'afafunta dake jajur a waje kanta a bud'e tayi parking gashinta a tsakiya yayinda daga k'asa wani ke zube, shima Haisam riga armless ce ajikinshi da wando 3 quarter, tana yin sallama duk suka juya suka kalleta Fanan ta mik'e zaune tana mik'a mata hannu tana mata murmushi nufarta tay tana zuwa ta kama hannunta ta zaunar da ita gefenta, gaida Hajiya dake kallonta tay tace "Oh Fateema k'iri k'iri dae kinyi mana yaji ko?" d'an guntun Murmushi tay a sanyaye tace "a'a Hajiya na koma islamiyya ne da safe kuma dana yi ayyuka na gama sai lokaci ya k'ure" da k'yar ta k'arasa Maganar saboda fargaba, Hajiyar tace "ai lokaci kam na gudu wllh Allah ubangiji yasa mudace" ita da Fanan suka amsa da Amin, d'an juyawa tay ta kalli Haisam da idonshi na akan tv ta gaidashi shiru bai amsa ba saida Fanan tace mashi Zarah na gaidashi sannan ya d'an kalleta ya amsa kafin ya mayar da idon ta lura da yadda ya amsa mata duk sai taji dama bata zo ba kaman ma ta mik'e ta tafi hakanan dae ta daure dama ita yarinya ce mai tsananin k'arfin hali ba k'aramin abu ne kesata raunin zuciya ba, mik'a ma Fanan sak'on gwaggo tay ta amsa da farinciki tun kafin ma taga miye aciki lokacin data bud'e kayan Fulani ne Navy blue riga da zani da kallabi harda mayafi sai abubuwan ado su sark'a yan hannu harda na sawa a kai,kayan sun yi kyau sosae da ganinsu masu ingaci ne ba tagajan tagajan ba, su kansu kayan sun sak'u sosae musamman gwaggo ta kira kawu shi6ado ta fad'a mashi tana son kayan shi kuma yaba wani abokinshi sautu ya aiko mashi dasu jiya kawun ya bada sak'on Mota aka kawo ma gwaggon, wata k'arar farinciki Fanan tay ta mik'e tana nuna masu abunda aka aiko matan hajiya na dariya ta shiga yabawa cike da zumud'i ta sungumi ledar kayan tace bari taje ta gwado Hajiya ma ta mik'e tana Fad'in bari ta biyota tana son shiga toilet, ya rage daga ita sai shi a falon kowa yayi tsit gashi duk ta sha jinin jikinta kasancewar akan kujera d'aya suke, a hankali ta d'an juyo zata saci kallonshi karaf suka had'a ido dashi da alama dama kallonta yake, idasa d'agowa tay tana kallonshi tana motsa baki kaman zata ce wani abu sai kyakkyafta ido take still idonshi na akanta yana mata wani kallo ko kyaftawa baiyi hakan yasa duk ta dabarbarce ta fara yamutsa fuska kaman zata yi kuka kawae sai gani tay yay dariya har fararen hakoransa suka bayyana ya dan ta6e baki ya maida idonshi kan tv ita kuma ta sadda kanta k'asa ji take kaman ta rusa ihu, fitowa Fanan tay cikin kayan Tubarkallah ma sha Allah fad'in kyaun da tay 6ata lokaci ne Hajiya ta taimaka mata tasa komae tay kyau Over harda takalma masu tsini ta sawo ta tunkari Haisam tana cat walk idonshi akanta yana Murmushi Fatuu ma idonta na akanta tana kallonta da d'an Murmushi, tana isowa gaban Haisam ta wani jujjuya tana fari da ido tace "how do i look babe?" dage gira yay slowly yace "like a bride" dariya tasa tace "yeah it's true am ur bride" tana yin Maganar ta fad'a jikinshi tana dariya shima dariyar yake ta d'auki wayarshi ta fara yi masu selfie duk wannan abun idon Fatuu na akan tv tun sadda ta fad'a mashi ji tay bazata iya cigaba da zama ba tana niyyar mik'ewa Fanan ta nufota da wayar ta zauna gefenta ta d'aga alamar itama hoton zatayi da ita, ba yadda Fatuu ta iya dole ta tsaya ganin bata murmushi fanan tace "Smile Zarah" dole haka ta daure ta rink'a yin murmushin yak'e ta rink'a d'aukarsu, can Fatun tace mata tafiya zatayi lokacin islamiyya ya kusa dama gwaggo ce tace tana nemanta tace eh ta mik'e hannunta cikin na Fatun ta jata d'akin Hajiya bayan taba Haisam wayarshi, lokacin da suka shiga Hajiya na kwance akan gado Fanan ta nuna mata stool tace ta zauna, kit d'in kayan gyaran gashinta ta d'aukko ta aje a gaban Fatun ta d'aukko wata babbar leda itama ta aje a gabanta tace gasu nan tana tunanin kayan ciki zasu yi mata tayi amfani dasu ta janyo k'aton trolley d'inta ta bud'e tace ta k'ara dubawa in akwae abunda take so karta ji komae ta d'aukka, gaba d'aya Fatuu ji tay ta rasa mik'e mata dad'i kawae sai ta fashe mata da kuka, (Allah sarki Fanan baki san Fatuu ba wannan take bukata a wurinki ba), Sosae Fanan ta rud'e ta hau lallashinta tana cewa tayi shiru ai ba abun kuka bane Hajiya dake kwance ma tace mata tayi shiru ai ba wani abu bane tunda ita ta bata, da kyar ta daina kukan fatun tace mata ba abunda take so suma wanda ta d'aukkar matan ta barsu Fanan d'in tace a'a ai ita ta bata, ba yadda ta iya dole ta d'auki kayan harda kit d'in tay mata godiya harda Hajiya, tare suka fito ta rik'e mata kit d'in har lokacin Haisam na zaune Fanan tace mashi zata je ta dawo ya d'aga mata kai kawae, akan hanyarsu Fanan d'in ke ce mata zatai missing d'inta sosae amman dae ai zata zo bikinsu ko fatun ta d'aga mata kai kawae,lokacin da suka isa gidan gwaggo ta ga abubuwan data ba Fatun sosae tay mata godiya had'i da Addu'oi tay fatan Allah ya nuna masu Aurensu lafiya, bayan wani lokaci tay mata sallama gwaggon tace zata shigo su k'ara yin sallama da daddare, bayan sallan isha gwaggo taja Fatuu ba don taso ba suka je gidan, Washe gari da Safe misalin karfe takwas da wasu mintuna Fanan ta rafka sallama tana sanye da skinny jeans da riga long sleeve ta d'an saukko mata kanta ta yafa mayafi ta fito a Baturiyarta, fitowa gwaggo tay daga cikin Kitchen tana ganinta ta nufeta tana fadin "y'ata har an fito" tace mata eh zasu tafi, gwaggo tace "to Allah ubangiji ya tsare, mungode, mungode Allah ya k'arawa rayuwa Albarka yasa ki gama da iyayenki lafiya, ki gaida mana da yan gidan sai munzo biki in sha Allah" d'an side hug tay ma gwaggon tana Murmushi tace "nima nagode da kulawa granny" suna cikin haka Fatuu ta fito jikinta sanye da doguwar riga kanta ba kallabi duk maganganun da suke tana ji kasa jurewa tay ta fito Fanan na ganinta ta saki gwaggo ta bud'a mata hannuwa, nufarsu tay tana zuwa ta fad'a jikinta idanuwanta sun cicciko da kwalla har sun fara zubowa, d'agota fanan tay ta shiga share mata tana Fad'in ta daina kuka ai zasu ci gaba da communicating kaman da, horn d'in da akai a waje yasa ta saki Fatun tace babe na jiranta tare zasu tafi ta juya suka rakota bakin kopa anan suka tsaya don ita Fatuu bata da kallabi ita kuma gwaggo ba mayafi, bud'e kopar Motar Haisam yay shima yayi gayun k'ananan kaya ya gaida gwaggo tay mashi Allah ya tsare ita kuwa Fatuu kasa ce mashi komae tay ta bishi da ido har ya koma Fanan na d'aga masu hannu suma suna d'aga mata ta bud'e gaban Motar ta shige yaja suka tafi, wani irin sanyi jikin Fatuu yay gwaggo ma har ta fara jin kewarta, juyawa sukai suka koma cikin gidan....... Wacece Fanan? Ya akai suka fara Soyayya da Haisam? Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2007* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 7 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .....Fanan jikar Hajiyace wato d'iyar Hajiya Maryam ta lagos kuma itace babbar diyarta, acan baya lokacin da mijin Hajiya wato General Adamu zakee yay ritaya a Lagos suka fara zama acan ne kuma ita Hajiya Maryam ta had'u da mijinta Wato Dr Mohammed Abraham wanda babban likita ne da ya kware a aikinshi lokacin tana karatu a Jami'ar Lagos, shi kuma Senator Alee yana Katsina yana kula da harkokin kasuwancinsu, tun lokacin da aka haifi Haisam Hajiya ta kwallafa rai akanshi k'arshe dae har tay nasarar rabasu dashi duk da suma suna matuk'ar kaunarshi don yaro ne mai tsananin farin jini ga kyau da Allah ya yi mashi duk wanda ya kalleshi sai ya tanka hakan yasa kullum cikin yi mashi Addu'oi suke, sosae Senator Alee ya rarrashi matarshi Fateema ya nuna mata Mahaifiyarshi ce bazata ta6a cuta mashi ba kuma tunda Allah yasa tana haihuwar ko shekara mai zuwa sai ta k'ara haiho wani d'an ba matsala bane, da k'yar ya shawo kanta ta hak'ura yana shekara hud'u aka ba Hajiya shi ta saka shi a Makaranta, gatan duniya Hajiya tayi ma Haisam saidae bata bashi gatan da zai sangarce ba duk da dama shi ba mai suffar sangartattun bane a tsayenshi yake tun yana yaro gashi ko dariya bai cika yi ba in kaga dariyarshi to wanda ya sani ne sosae, yana shekara bakwae lokacin yana primary 1 don saida yay nurserys Hajiya Maryam ta haifi d'iyarta ta fari wato Fanan itama dae Tubarkallah badae kyau ba don jinin Mahaifinta ta biyo harma ta fi shi kyau sosae, Fanan irin rigimammun yaran nan ne ga kukan banza da wofi abu kad'an ta 6are baki gashi kuma bata son bak'in mutum hakan yasa bata cika sakin jiki da mahaifiyarta ba ko yaushe tana manne da Mahaifinta shi kuma gashi ba mazaunin gida bane sosae saboda yanayin aikinsa yana aiki a asibitin gwamnati kuma yana da babban private Hospital hakan yasa kullum cikin yi mashi rigima take gashi tayi k'ank'anta bare yace ya tafi da ita koma ya tafi da ita baida lokacin kulawa da ita saidae in barin aikin zaiyi, hakan yasa in ya barta gida tay ta yi ma Hajiya Maryam rigima data yi mata fad'a kuma ta idasa rikice mata, duk wannan abun Mutum d'aya ne ke controlling d'inta wato Haisam duk da shima lokacin yaro ne,duk rigimar da take da sunzo gidan tay arba dashi baka k'ara jin kukanta tana sonshi taita shishshige mashi gashi shi ba son yara yake ba wani lokacin sai Hajiya tay mashi Magana yake d'an sakar mata fuska har ya d'auketa kowa yasan tana shakkar Haisam hakan yasa Hajiya Maryam watarana taje gidan Hajiya ta rok'eta ta bari Haisam ya dawo gidansu, fir ta k'i amincewa tace itama ai don tana son zama dashi ta rabo shi da iyayenshi, wai ance tsakanin d'a da Mahaifi sai Allah K'arshe dae saida Hajiya Maryam tay nasarar raba Hajiya da Haisam da sharad'in duk Weekend nan wurinta zaiyi shi tace su duka ma zasu rink'a zuwa,sosae suka samu sauk'in rikicin Fanan bayan dawowar Haisam gidan duk in zaije Makaranta sai yabar sak'on in tayi rigima daya dawo a fad'a mashi aikuwa har ya dawo bata yin rigimar data yi niyyar farawa Hajiya Maryam zata ce daya dawo sai ta fad'a mashi sai tace ta bari, a lokacin komae na Fanan ya dawo kan Haisam shine yi mata wanka bata Abinci data ga yayi fushi duk sai ta rud'e ta fara bashi hakuri har sai yace mata yayi sannan zata warware da yake lokacin girmanta yafi shekarunta tana da wayo sosae ga baki, Haisam na primary 3 lokacin shekararshi tara da wani abu ita kuma Fanan ta kusa shekara ukku aka ba mijin Hajiya wato Adamu zakee Ministan tsaro bayan wani lokaci suka shirya komawa Abuja dama ba wani son zama Lagos d'in yake ba yafi son ya koma gida Arewa, Hajiya Maryam ta nuna abar Haisam nan ya k'arasa karatunshi Hajiya kuwa tace bai yuwuwa ai iyayenshi ma sai suce wani abu don haka k'afarta k'afarshi aikuwa Fanan ta sa rikicin sai ta bi bro haka take kiranshi sam Hajiya Maryam bata son d'iyarta tai mata nisa saida Dr Mohammed ya nuna mata ta barta su tafi da ita kawae in ba haka ba wani sabon rikicin ne tunda ta saba dashi in ta k'ara wayo sai ta dawo kuma in d'a take so zata iya daina planning d'in da take sai ta haihu dama so take sai Fanan d'in tayi wayo sannan ta k'ara haihuwa, ba yarda ta iya dole ta hak'ura aka tafi da ita Abuja aka saka su Makaranta tare da Haisam sam bata son zama class d'insu kullum tana zarya class d'insu Haisam sai ya kamata ya maidata, da yan class d'insu sun ganta tazo sai suce Zakee ga d'iyarka nan aita dariya shidae sai dae yay d'an Murmushi kawae, har lokacin shi ke mata wanka da sun koma gida ya bata Abinci kullum tana lik'e dashi tun yana jin ya takura harma ya saba, bayan tafiyarta da shekara d'aya Hajiya Maryam ta haifi Farha shima Haisam lokacin Mahaifiyarshi ta k'ara haihuwar yara biyu Laila da Nameer, Haisam na Junior Secondary Mijin Hajiya wato Gen Adamu zakee yay Accident ya rasu lokacin ba k'aramin tashin hankali iyalin suka shiga ba lokacin Fanan na primary 4, rasuwar mijin Hajiya yasa ta kasa cigaba da zama a Abuja ta yanke dawowa Katsina lokacin kuma Hajiya Maryam ta buk'aci Fanan ta dawo gida da taso ta turje aikuwa ta bude mata wuta dole ta koma Lagos shi kuma suka dawo Katsina yaci gaba da yin Senior Secondary lokacin kuma Mahaifinshi ya zama Senator, bayan ya gama secondary ya tafi kasar waje yin degree d'inshi na farko,akwae wani zuwa da yay Lagos lokacin yazo k'asar Fanan na Secondary skul tana ganinshi ta rungumeshi cike da farinciki suka ci Abinci tare da daddare bayan sun gama fira zai je ya kwanta tace mashi wai yayi mata wanka kaman yadda yake mata da d'an murmushi yay mata yace mata ai ta girma yanzu bai kamata yay mata wanka ba tace amman ai shi yayanta ne ba wani abu bane ganin ta turje kan hakan yasa ya zaunar da ita ya fahimtar da ita game da tsakaninsu na shi yayanta ne amman ba muharraminta bane kuma koda ma shi muharraminta ne yanzu takai wani mataki da bazai mata wanka ba tunda shi Namiji ne ganin ta zuba mashi ido yasa ya tambayeta ko bata san miye muharrami ba tace ta sani wanda bazai iya auren Mutum ba yace mata hakane, da bud'ar bakinta sai cewa tay yanzu shi zai iya aurenta kenan yana d'an Murmushi yace mata eh ai shi cousin d'inta ne ba ta sani ba tace eh ta sani,Washe gari bayan sun gama breakfast da yake Weekend ne taje part d'in da ya sauka ta iske shi yana kallo ta zauna kusa dashi itama tana kallon American film d'in da yake kallo, can aka nuno jarumin film din ya duk'a kan knee d'inshi yana rok'on jarumar zata aure shi ya mik'a mata zobe can ta amsa mashi da Yes ta mik'a mashi yatsanta yasa mata zoben ya mik'e suka rungume juna, juyawa Fanan tay ta kalli Haisam da idonshi ke kan tv ba zato ba tsammani kawae ta duk'a a gabanshi ya maido idonshi kanta yana kallon abunda tay murya kaman zatai kuka tace "Ya Haisam will u marry me pls?" dan bud'a mata ido yay alamar mamaki sai kuma yay Murmushi kawae ganin haka yasa ta fara yamutsa fuska kaman zatayi kuka tace mashi"plss answer me,will u marry me?" d'an lumshe ido yay ya jinjina kanshi, wata k'arar murna tasa ta fita daga falon da gudu ya bita da ido kafin ya maido kan tv yaci gaba da kallonshi, wurin Mommynta ta nufa lokacin tana d'akin Dad d'insu saida tay masu sallama sannan tasa kai tana ta dariya ganin haka yasa Hajiya Maryam tambayarta lafiya cike da farinciki tace Ya Haisam ne yace zai aureta yanzun nan, gaba d'aya suka bud'a idanu kafin sukai dariya suka ce suna tayata murna ta dace miji ta juya da gudu tana dariya, bayan fitarta Hajiya Maryam ta kira Hajiya ta sanar mata sosae tay farinciki tace ita dama tasan wannan shak'uwar inda zata kaisu kenan, tun daga wannan ranar Fanan ta koma yima Haisam kallon wanda zata aura, Bayan ya gama degree ya dawo Abuja ya fara aiki ita kuma Fanan ta gama Secondary tace ma Mommynta taji ana Maganar tafiyarta karatu ita dae aure take so tunda tana da wanda zata aura in sunyi auren tayi karatun, jin wannan Maganar yasa Hajiya Maryam ta kira Hajiya ta sanar mata game da zancen Fanan d'in ita kuma ta kira Mahaifinshi Senator Alee, Lokacin da ya kira Haisam d'in yay mashi Maganar auren da mamaki yace ai shi wannan lokacin wasa ne yake mata don baiyi tunanin da gaske take ba ganin ita yarinya ce kuma ya za'ai ai mata aure ma yanzu tayi k'arama, Senator yace yanzu dae bazai aureta ba kenan yace shidae yana mata son yan'uwantaka ne amman bana aure ba,sosae ya fahimceshi ya kira Hajiya ya gaya mata duk da bata ji dad'i ba amman tasan bazasu yi mashi dole ba lokacin ta kira Hajiya Maryam don ta sanar mata duk suna zaune a parlor bayan sun gaisa ne ta fara mata bayanin abunda Haisam yace sam Hajiya Maryam ta manta ma tana tare dasu Fanan d'in take wayar saida taji su Farha sun saka k'ara suna fad'in Sis Fanan ta fad'i sannan ta kai idonta kan Fanan dake baje k'asa kan carpet ashe tana jin abunda suke magana ta mik'e shine ta yanke jiki ta sume wata zabura Hajiya Maryam tay ta cillar da wayar tay kan Fanan, Hajiya nata hello hello sai Abraham ne mai sunan kakansu ya d'auka ta tambayeshi miya faru yace sis Fanan ce ta sume data ji suna waya da Mommy d'insu, rushing dinta sukai Hospital din Dad d'insu anan yasan abunda ke faruwa suka shiga bata agajin gaggawa koda ta farfad'o ta ganta a Asibiti ga iyayenta akanta sai ta fashe masu da matsanancin kuka tana Fad'in"Ya Haisam will not marry me why, why mom, Dad why? Am i ugly?....." haka ta dingi sambatu Hajiya Maryam harda kuka sai lokacin ta amshi wayarta ta kira Hajiya dama tana ta kira ba'a d'agawa cikin muryar kuka take sanar da ita halin da Fanan take ciki tace tana tunanin ta samu heartbreak ne gashi dama raunannar zuciya gareta, Hajiya na jin hakan washe gari sai Abuja ta zauna da Haisam da iyayenshi tace mashi miye aibun Fanan da bazai aureta ba ko yana da wadda yake so ne yace mata a'a shidae kawae bai mata son aure, tace to yayi hak'uri tunda ita tana sonshi ya daure ya aureta ko don a ceci rayuwarta kar a rasata saboda abunda bai fi k'arfin suyi mata ba yace shikenan zai aureta amman ba yanzu ba sai ya gama Masters degree d'inshi da zai tafi bada jimawa ba Hajiya tace wannan ai ba matsala bane tunda dae ya amince itama sai ta fara karatunta duk in suka gama sai ayi bikin in Allah ya kaimu,Washe gari Hajiya da Haisam harda Senator suka tafi Lagos duba Fanan d'in har lokacin tana cikin mawuyacin hali a Asibiti sai faman koke koke take, koda suka ganta gaba d'aya ta basu tausayi ba kaman Haisam da shi Mutum ne mai tsananin tausayi hakanne ma yasa ya amince da auren nata ba tare da an kai ruwa rana ba, gaishe da ita sukae sukai ma iyayenta ya mai jiki cike da zolaya Hajiya tace "ashe mu Laila muka haifa ba Fanan ba to ai sai ki share hawayenki ga Majnun d'in nan na kawo maki" duk aka d'anyi Murmushi daga baya d'akin ya rage daga ita sai Haisam dake tsaye ya goya hannuwanshi a chest d'inshi ita kuma sai kallonshi take tana sheshsheka, can ya nufi gadon da take kwance ya zauna kan kujera tana ta6e baki tace mashi "Ya Haisam u don't luv me, u will not marry me why?" fuskarshi a sake yakai hannu ya kamo hannunta ya d'an matse shi Calmly yace "How can i reject a precious gift of a beautiful young lady like u" waro ido tay da sauri tace "u accepted me to be ur wife?" lumshe mata ido yay nan take ta gane mi yake nufi ta tashi da sauri sai kace ba mai jinya ba tanata mashi dariya tana rufe bakinta shima Murmushi yake mata, can kuma sai yaga ta daina dariyar ta kwa6e fuska idanunta sun ciko da kwalla da sauri ya tambayi miya faru kaman zatai kuka tace mashi tasan tausayinta ne yasa yay accepting aurenta ba don yana sonta ba tunda da yace bazai aureta ba, mik'ewa yay ya koma gefen gadon ya k'ara kama hannunta yace mata yana sonta sosae shiyasa ma ya yarda zai aureta kawai lokacin da sukai Maganar da farko ya d'auka tana wasa ne amman yanzu tunda ya tabbatar tana sonshi da aure shima yaji yana sonta sosae, jin haka yasa ta fad'a jikinshi tana dariyar farinciki, a takaice dae tun daga Wannan ranar yasa zuciyarshi ta amince da ita matsayin wadda zai aura dama shi ba Soyayya yake ba duk da akwae mata da yawa dake mashi tayin Soyayya anan gida Nigeria har ma da k'asar waje inda yay karatu, saida Haisam yay da gaske sannan Fanan ta rage had'a jikinta da nashi don ta riga ta saba wata irin zazzafar soyayya take mashi, lokacin da akai Maganar tafiyarta karatu k'asar india cewa tay Haisam zata bi inda zaije yin Masters degree tay karatun acan Dad d'inta ya nuna yafi son taje k'asar India don shima acan yay karatunshi kuma akwae dan'uwanshi shima likita ne acan zai taimaka mata sosae,Lokacin data kira Haisam ta gaya mashi ce mata yay karta damu taje can d'in tace ai ita tsoro take ji yaje can shi kadae wata ta k'wace mata shi har saida yay yar dariya dama yasan kishi ne yasa take son binshi hakan yasa ya tabbatar mata da they're meant for each other karta damu wannan dalilin ne yasa ta tafi k'asar India karatu, da anso ay auransu bayan ya gama karatun Dad d'inta ya nuna a bari ta gama karatun tunda Haisam d'in zai koma aiki Us ne sai su tafi tare akwae Asibitin da zai sama mata aiki acan itama tayi, lokacin ne kuma Senator ya nuna sai ya fara aiki anan kafin ya koma US d'in shine ya dawo wurin Sweetheart d'inshi K Hajiya, Wannan kenan game da Soyayyar Haisam da Fanan............. Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2008* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 8 *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........Satin da Fanan ta tafi su Fatuu suka koma Makaranta sun cigaba da zuwa ita da Haulat har lokacin tana cikin yanayin damuwa ga zuciyarta tay ta raya mata Ya Handsome na can suna shan soyayyarsu da Fanan, Haulat na lura da yanayinta hakan yasa bata gajiya da bata hakuri da kuma k'arfafa mata guiwar ta cireshi daga ranta, zubar da hawaye ya zamar mata jiki Fatuu mai zafi ta dawo Fatuu mai sanyi kowa ya lura da canjawar da tayi yan Class d'insu da Malamai suna ta tambayarta game da hakan saidae tace masu kawae bata lafiya ne, haka Haulat ma duk wanda ya tambayeta sai tace bata lafiya matsalar Aljanunta ne da yake dama ansan tana dasu ba kamar wadanda sukai junior tare, ko sauran juniors ma na section d'insu sun san SP d'insu tayi sanyi, a satin sau d'aya taje gidan Hajiya ranar Juma'a ta gaishe da ita sanin Haisam bai nan, suna d'an yin fira a Falon Hajiya ke cewa "wai ni kam Fateema ko har yanzu jikinne duk kinyi sanyi ba kaman da ba" saida gabanta ya fad'i jin haka cikin rawar murya tace mata jikinne bai mata dad'i kaman ba nata ba, hajiya tace "Allah ya baki lpy ya rabaki da ciwon gaba d'aya ki huta in sha Allahu zaki samu lpy ki dawo kaman yadda kike amman kasancewarki haka ba dad'i mutum mai kazar kazar duk kin dawo sukuku" d'an Murmushi tay batace komae ba dai, bayan wani lokaci tay mata sallama ta tafi, sam Hajiya bata kawo komae game da halin da Fatuu take ciki ba sanin tana da Aljanun da gaske sannan lokacin da suka dawo daga Ajiwa ba wanda yay tunanin Fatun taga Fanan kafin ta shiga gida don koda Hajiya ta tambayi Fanan sun ga juna ce mata tay a'a ta shiga gida kuma bayan sunje sun dawo suka ce sun iske bata lafiya. Ranar Monday lokacin Satin Fanan d'aya da tafiya misalin karfe bakwae da rabi Fatuu ta fito jikinta sanye da Uniform d'in boko sun sha guga bayanta goye da k'atuwar School bag d'inta tsaf tsaf da ita tana shirin hawa hanya ta tafi galleliyar Mota dark ash ta tsaya a gabanta har saida ta dawo baya da sauri, bin Motar tay da kallo lokaci guda k'irjinta ya fara bugu da k'arfi da k'arfi don ko ba'a fad'a ba tasan waye a ciki, Slowly glass d'in kopar ya fara sauka k'asa nan take tay arba da haisam cikin shirin zuwa aiki idonshi na a gaban Motar bai kalleta ba shiru tay tana bin gefen fuskarshi da gashi ke kwance luff da kallo can ya juyo a hankali ya kalleta suka had'a ido, bin shi tay da ido kawae shima kuma haka ganin kallon da yake mata ne yasa a sanyaye tace "Ina kwana" jinjina mata kai yay ta sake cewa "an dawo lpy?" fuska a sake yace mata lafiya, kallon juna suka ci gaba da yi ganin bata iya jure ma kallon nashi yasa ta sunkuyar da idonta k'asa can taji yace "in rok'e kine ki shigo?" d'an d'agowa tay tai mashi wani kallon k'asan ido acikin zuciyarta ta ayyana sai kace ni na kirashi ni dama ka tafi....." "Baki kirani ba ko" bata k'arasa ba taji ya fad'i haka, a firgice ta idasa d'agowa ta zaro ido cike da Al'ajabi jin abunda yace sai kace mai jin zancen zuci duk tay kalar rashin gaskia ta girgiza mashi kai alamar a'a kafin ta maida kan k'asa, "Zaraah" yarrr taji wani abu ya tsarga mata tun daga kan babban yatsanta har zuwa cikin kanta, kasa d'agowa tay ta kalleshi don komae zai iya faruwa a wannan lokacin inta had'a ido dashi, "Ki shiga Mota kina sani ina late in kuma baki son shiga ne let me know sai in tafi" a hankali ta daure ta d'ago ta d'an kalleshi kafin ta kawar da idon da sauri ta nufi other side d'in Motar ta bud'e ta shiga,tana shiga ta juyar da kanta tana kallon gefe duk yana kallonta ta Mirror bai dai tanka ta ba yaja Motar suka tafi, daidai lungun gidansu Haulat ya tsaya ta bud'e Motar ta fita ya bita da kallo,lokacin data shiga d'akinsu Haulatun tana kallon fuskarta ta tambayeta lafiya kaman zatai kuka tace "Ya Handsome ne..." sai kuma tay shiru, a d'an rud'e Haulat tace "miya faru dashi?" hannu tasa tana share kwallan da suka gangaro mata kafin tace "ya dawo yanzun nan ya ganni a kopar gida ya d'aukko ni yana waje" a k'agare tace "to wani abu ya faru ne" girgiza mata kai tay tace "ni banson ganinshi ne haulatu zafi kirjinta ke yi inji kaman in fad'a mashi halin da nike ciki" dafata Haulat tay ta shiga bata hakuri tana karfafa mata guiwa, koda suka fito kafin su isa wurin Motar cigaba da lallashinta haulat tay akan ta daure karta fad'i mashi don ba abunda zai mata saidai ya bata hakuri gwara tay hakuri komae zai wuce ita dai kai kawae ta daga mata, bayan sun shiga Motar gaidashi Haulat tay ya amsa mata yana k'ok'arin jan Motar bayan yaja sun fara tafiya tace "Ya haisam ya Aunty Fanan?" fuska a sake cikin cool voice d'inshi yace "ta koma skul tace a gaidaku" da yar fara'a tace "muna amsawa" a hankali ya d'an juya side d'in Fatuu suka had'a ido duk ta kame kanta da sauri ta juyar da kanta gefe ita kanta tasan bata kyauta ba da bata tambayi Fanan ba, yana aje su a Makarantar ta d'an juya tace mashi an gode ba tare data jira amsawarshi ba ta bud'e kopar tay ficewarta lokacin Haulat bata k'arasa fita ba Haisam ya kira sunanta ta tsaya kud'i ya mik'a mata tasa hannu biyu ta amsa tay mashi godiya ya jinjina mata kai, bayan ta idasa fita yaja Motar ya tafi, akan hanyarsu ta zuwa Class ne Haulat ke k'ara lallashinta akan ta daure ta cije taci gaba da yi ma Ya Haisam kaman da duk da tasan abu ne mai wuya amman dai ta rink'a d'an kamantawa gudun kada shi kuma yaga kaman ta rainashi tana wulak'antaci tunda ba haka suka saba ba, idanunta cike tabb da kwalla tace ma Haulat "baki san ya nike ji bane Haulat wllh shiga Motar ma ba k'aramin daurewa nay ba ji nake kaman in rusa ihu saboda takaici inna tuna na rasa shi, auranshi zay da wata...." bata k'arasa ba tasa kuka haulat ta shiga lallashinta tana Fad'in ta Fahimceta, haka Haisam ya cigaba da kaisu Makarantar duk da Fatuu taso ta rink'a zillewa Haulat ta nuna mata bai dace ba tunda shi ya saba kai su tsawon shekaru ba tare daya nuna gajiyawa ba bai kamata suyi mashi haka ba,dole ta Hakuri ita kanta wani abun ba don tana so ba take mashi don Haisam yafi karfin wulak'antawa a wurinta ita ba butulu bace tasan Haisam shi ya mayar da ita cikakkar Mutum, akwae watarana bayan ya aje su a Makarantar har Fatuu zata bud'e Motar ta fita yace ta tsaya jin hakan yasa Haulat ta bud'e kopar ta fita bayan tay mashi godiya kaman ko yaushe, shiru sukae shi yana kallonta ita kuma ta sunnar da kai can taji yace "Zaraah" amsa mashi tay ba tare data kalleshi ba yaci gaba "har yanzu baki lpy ne?" shiru tay tana d'an mommotsa baki har saida yace ba magana yake mata bane sannan tace mashi ta samu sauki yace "then why are u acting strangely?" shiru ta d'an yi sai kuma tace "kawae jikina ne banjin dad'inshi har yanzu" jin baice komae yasa ta kalleshi suka had'a Ido kasa janye idon tay can yace "kina bukatar zuwa hospital?" da sauri ta girgiza kai tace tana shan magani, gyad'a kai yay yace taje da sauri ta bud'e Motar ta fita yaja ya tafi, bayan taje wurin Haulat sun nufi ajine jin tayi shiru yasa Haulat tambayarta lpy dae ko kaman bazata ce komae ba sai kuma ta fad'i mata abunda ya tambayeta tace ta kyauta da bata fad'i mashi ba amman ta daure ta d'an rink'a sakewa kar watarana a samu matsala tace mata to kawae, tun daga wannan ranar Haisam bai k'ara tambayarta ba game da canzawar da tayi sannan shi bai canza mata ba daga abubuwan daya saba yi mata. Bayan Wata Biyu, Lanar lahadi da rana Fatuu ta dawo daga islamiyya lokacin gwaggo bata nan aikin rana take amman da wuri ta tafi saboda zata biya wata unguwa, d'akinta ta shiga ta aje jakarta wurin da take ajewa ta nufi gado ta cire hijab d'inta ta aje tana niyyar juyawa ta nufi Kitchen don ta zubo abinci idonta ya sauka kan wani abu dake sakin k'yalk'yali a gefen hijab d'inta da ta d'aura saman gadon, tsayawa tay idonta akan abun ta koma gaban gadon sai lokacin ta lura da envelope ce, a hankali ta kai hannu ta d'aukko tana k'are mata kallo ba k'aramin had'uwa tay ba sai walwali ke tashi gwanin burgewa kaman zata bud'e sai kuma ta juya bayanta idonta ya sauka akan wani rubutu dake daga can gefe guda shima yana ta sakin kyalli anyi shi da italic style, k'ura ido tay tana karantawa kamar haka _HAIFAN 2023_ kasa gane abunda yake nufi tay tanata k'ara maimaitawa can dae ta bud'e cikin envelope d'in ta fiddo da wata takardar mai kyau da salk'i dake linke ta warwareta ta fara karanta abunda ke jiki wanda katin gayyatar daurin Aure ne na Families d'in Sen. Alee Adamu Zakee da kuma Dr. Mohammad Abraham da za'a yi ma y'ay'ansu wato _ENGR. HAISAM ALEE ADAMU ZAKEE & DR.FANAN MOHAMMED ABRAHAM_ wanda za'ayi a karshen watan da ake ciki wato nan da sati ukku masu zuwa kenan don satin farko ake za'a shiga na biyu, a Central Mosque dake Abuja,mutuwar tsaye tay bayan ta gama karantawa ta sake maimaitawa har saida ta tabbatar ma kanta lalle Ya Handsome ne nan da nan hannunta ya fara rawa cike da Al'ajabi tasa tafin hannunta guda ta rufe bakinta, yanzu da gaske dae Ya Handsome aure zaiyi ya barta, wani irin kuka cikinta ya fara yi da sauri ta wurga IV d'in kan gado ta nufi hanyar waje a dudduk'e take tafiyar saboda k'ullewar da cikinta yay Allah dae ya taimaka ta k'arasa toilet d'in ba tare da abunda take ji ya zubo mata ba,tsawon lokaci ta d'auka a ciki kafin ta fito a galabaice duk tayi sharkaf da ruwa data sakarwa kanta ta nufi d'aki hannunta d'aya dafe da cikinta,tana shiga ta isa kan gado ta fad'a tana nishi da karfi da karfi, wai ance in tashin hankali yay tsanani kuka kasa yinshi ake to hakan ce ta faru da Fatuu sam ta kasa yin kuka sai zare idanu kawae take ga wata kerma da jikinta ke yi kaman wadda sanyi ya kama,duk da uwar yunwar dake cinta ta kasa tashi taje ta zubo abincin don a halin da take ciki bata wani Abinci take bama ko ta zubo ma ba iya ci zatai ba tana kwancen akai Azahar amman ta kasa mik'ewa taje tayi sallar sai bin envelope d'in dake gabanta take da ido zuciyarta na wani irin bugu mara dad'i. Bayan sallar La'asar Haisam na Masallaci Abbas ya kirashi yace gashi a part d'inshi yace mashi yana zuwa,bada jimawa ba ya dawo ya zauna kan L-shape Abbas kuma ya zaune kan armchair, gaba d'ayansu suka d'an kishingida kan kujerun da suke suka shiga tattaunawa kan bikin Haisam din Abbas yace "dazun munyi Magana da Amaryar taka kan program d'in da tace ta fad'a maka zasu yi a can saboda friends d'inta da bazasu samu zuwa Abuja d'in ba, wai Indian Night zasu yi, kenan kaga dole zamu je Lagos ni harma na tanadi kayan indian da zansa irin masu burgujejen wandon nan ko kuma in d'aura dan zani yadda suke" ya k'arasa yanata 6a66aka dariya haisam ma yar dariyar yay bai ce komae ba,Abbas yaci gaba "Maganar Dinner party dinma mun gama Magana da Saleem dress code da komae sai jiran lokaci kawae, ya kamata ma a k'ara program Dinner yayi kad'an gaskia bikin H,Zakee guda" d'age gira Haisam yay yana mashi wani kallo can k'asa yace "for me is enough, ba zakuyi wani a Lagos ba" Abbas na dariya yace "zamuyi dae ai kasan dae dole kaje,ko zamu je ba ango ne wannan kuma ai daban a Abuja nike nufin Dinner kawae yay kad'an amman ko ka k'i ma su Laila suma sun shirya wasu programs d'in don munyi Magana tace za'ai Arabian da wani can dae naku na Al'adan Ethiopia" dan ta6e baki yay kawae bai ce mashi komae ba, gyara zama Abbas yay kafin yace "Wai nikam ina Mom Zarah ne, da ita ya kamata ace muna preparation da tsare tsare don itama matsayin babbar k'awar Ango take" shiru haisam yaya idonshi akan Tv kaman bai ji abunda Abbas d'in yace ba, "Am asking u Zakee" sai lokacin ya kalleshi kaman bazaice komae sai kuma yace "nima ina nemanta" da d'an mamaki Abbas yace "kaman ya kana nemanta bata nan ne?" "No tana nan but ta daina zuwa nan kwata kwata" tashi Abbas yay zaune yace "to why ko kai mata wani abu ne?" d'an guntun Murmushin gefen bakin yay kafin yace "in mata mi, she just changed completely" ya k'arasa Maganar yanayin fuskarshi ya canja da gani ba jin dad'in hakan yake ba, Abbas yace "to amman ka ta6a tambayarta dalilin canjawar ne?" shiru ya d'anyi kafin ya gyara zamanshi sosae yana kallon Abbas din yace "Yea,nayi hakan i think 2 to 3 times but abu d'aya take bani shine bata jin dad'in jikinta as a result of wannan ciwon Aljanu ne komi da tayi" wani guntun Murmushi Abbas yay kafin ya sake tambayarshi tun yaushe ta fara ciwon Aljanun ne yay mashi bayani tun lokacin da suka dawo Outing Fanan tazo da yadda suka je da daddare suka iske bata lpy har tay amai sosae aka tabbatar Malaria ke damunta bayan sun dawo gida Fanan ta sanar ma Hajiya bata lpy anan suka ji tana da Aljanun, yana gama Maganar ya maida idonshi kan tv shi kuma Abbas ya sauke nannauyar ajiyar zuciya idonshi akan Haisam sam baiyi mamakin rashin fahimtar Haisam d'in kan abunda ke damun Fatuu ba don yasan shi ba wani sanin so yay ba sosae iya soyayyar Fanan kadae ya sani bai tunanin daga kanta ya ta6a yin soyayya da wata, sigh yay on a serious note yace "H,zakee Zarah has fell in love with u" Maganar Abbas ta daki dodon kunnan Haisam ba shiri ya maido idonshi akan Abbas yana mashi wani kallo with suprise written boldly all over his face, ganin kallon da yake mashi ne yasa Abbas d'in jinjina mashi kai cike da tabbatarwa yace "Yea am sure tana son ka ne shiyasa ta canja maka haka don ta gane kana da wadda kake so" ido kawae Haisam ke binshi da shi can kuma yay wani guntun Murmushi ya d'an girgiza kai kafin yace "pls Abbas don't start it,kai koda yaushe Magananka d'aya ne soyayya mata,Zarah ne zaka ce wai sona take how possible,yarinyar da bata da buri sai na tayi karatu ta zamo Doctor yaushe ta san wannan d'in" Abbas dake Murmushi yace "shine kuma bazata iya canjawa ba, sanin da kai mata yanzu ta girma zata iya having feelings for man saboda she's quite mature for her age" wani kallo haisam ke binshi dashi ya d'an ta6e baki jin Abbas yayi shiru yasa yace "Zaraah is still immatured" da mamaki Abbas yace "amman miyasa zaka ce hakan ga abu a fili kowa ya kalli Zarah yasan ta mallaki hankalinta ta zama cikakkiyar mace yanzu" shiru haisam yay yana d'an Murmushi kafin yace "da sauranta don har yanzu bata fara menstruation ba" da wani kallan expression mai nuna tsantsar mamaki Abbas yace "Zarah ce bata fara menses ba at her age? Kai ya akai kasan hakan??" nan take Haisam ya fad'i mashi yadda suka ta6a yi da Fatun da Azumi yace "so in da ta fara na tabbatar zata sanar dani" wani kallan Murmushi Abbas yay yace "H,Zakee Zarah zatai ta zama ne bazata yi hankali ba,kar ka manta kana man Maganar abunda ya faru kusan 3 years back ai dole zata k'ara hankali besides a shekarunta yanzu sun kai ace tana menstruating in kau har bata yi kaman yadda kace to tabbas bata lafiya tana bukatar akaita asibiti ko kuma tana daga cikin matan da basu yi kwata kwata wanda bana tunanin hakan ma gaskiya" shiru Haisam yay yanata kallonshi yayin da acikin zuciyarshi yake nazarin Maganar tashi ta k'arshe yasan Abbas ba likita bane amman abunda yake koyawa ya kunshi hakan wato biology, "Kayi Nazari sosae H,zakee tsawon lokaci kana tare da Zaraah ace baka ta6a sanin tana da Aljanu ba sai yanzu kuma basu tashi zuwa su sakar mata ciwo ba sai da Fanan tazo...." katseshi Haisam yay "amman Hajiya ta tabbatar da haka", "Eh dama ba ina nufin k'arya bane bata dasu sai dae koda tana dasu d'in to sun barta tun kafin kasanta ko kuma sune ke sakata rashin ji a can baya amman basu sakata ciwo kaman yadda take yanzu kayi tunani da kyau a gani na Zarah ta fara sonka kwatsam sai ga Fanan ranar da kuka dawo, tambayata anan da ka ga Fanan wane reaction kay? Zai iya yuwuwa ta haka ta gane akwae wani abu tsakaninka da Fanan saboda rikicewa ta shige gida tace bata lafiya sannan da kuka je da Fanan da daddare wane irin hira kukai? Shin wai ma da kuka dawo da ita akan hanya tace maka bata lafiya ne dama??" shiru bakin Haisam ya mutu yama rasa mi zaice mashi abun gaba d'aya ya gama d'aure mashi kai wai Zarah na sonshi.......... Tana ta kwance ba um ba umum kamar wanda tay Mutuwar kwance sai ido kawae ita kanta bata san mike faruwa da ita ba gaba d'aya jijiyoyin jikinta sun daina aiki a haka har akai la'asar ga bak'ar yunwa da ke cinta cikinta sai kuka yake amman ta kasa tashi, tana a cikin wannan halin Haulat ta d'aga labulan d'akin ta shiga da sallama jikinta sanye da Uniform d'in islamiyya, tunkarar gadon tay idonta akan fatuu ta tsaya gaban gadon tace "kawata lafiya ina sallama baki amsa ni ba" k'uri tay mata da ido ko kyafta su bata yi hakan yasa haulat kiran sunanta amman shiru da sauri tasa hannu a shoulder dinta ta jijjigata tace "Fatuu lafiya wai? Mi ke faruwa ne?" da k'yar ta iya mik'ar da yatsanta ta nuna ma Haulat Iv d'in dake gabanta ta kai hannu da sauri ta bud'e tana karantawa,a kid'ime ta d'ago ta kalli Fatun sai kuma ta zauna gefen gadon a hankali ta aje iv d'in a gefe ta fara Magana "nasan dole ne ki k'ara shiga matsananciyar damuwa yanzu amman don Allah kiyi hakuri Fatuu kaman yadda nike ta fad'i maki, ki d'auka Allah bai kaddara Ya Haisam mijin ki bane" sai lokacin ta yunk'ura da k'yar ta tashi zaune idonta akan Haulat da wata irin murya ta wanda ya karaya tace "amman Haulat wllh ina son ya Handsome Allah ne shaidata...." sai lokacin kwalla suka fara zubo mata da ganin yadda take kukan zaka san ba k'aramin ciwo take ji a cikin zuciyarta ba" dafata Haulat tay taci gaba da bata hakuri tana nuna mata kowa da irin k'addararsa a rayuwa ta d'auka wannan ce tata ita dae kai kawae take d'aga mata can Haulat tace "da zuwa nayi mu tafi islamiyya bazaki ma iya zuwa ba ko?" girgiza mata kai tay tace zata je, "Da alama ma tun da kika dawo da safe kike cikin wannan halin naga ko Uniform baki cire ba, kin ci ma Abinci kuwa?" girgiza mata kai tay alamar a'a tace "to in zubo maki zaki ki ci ko?" shiru ta d'anyi sai kuma ta d'aga mata kai don tana jin yunwa sosae, mik'ewa Haulat tay taje Kitchen bada jimawa ba ta dawo ruke da plate din dafa dukan taliya da wake ta mik'a mata ta sake fita taje falo ta d'aukko mata ruwa, bayan ta dawo komawa tay ta zauna gefen gadon tana rarrashinta akan tayi hakuri ta daure taci, ba wani mai yawa taci ba don sam bakinta bai mata dad'i tace ta k'oshi ruwan ne dae ta shanye shi duka,bayan ta gama saukkowa tay ta nufi hanyar fita walking Slowly Haulat ta tambayeta ina zata tace alwala zatayo, saida tay Azahar sannan tayi la'asar kafin ta mik'e ta daukko jakarta Haulat tace ta kawo ta rike mata tace ta bashshi daga haka suka fita, Kawu Amadu na shago bai dad'e da bud'ewa ba don baccin rana ya sha sai bayan la'asar ya bud'e Haulat ta gaidashi kafin suka wuce, tunda suka fito idonta akan gidan Hajiya suna zuwa daidai kwanar dake jikin gidan Fatuu ta ja ta tsaya haulat ta juyo ta kalleta ganin tayi tsaye yasa ta tambayeta lafiya ko bata iya zuwa, "Haulat kije kawae ni zan je in fad'i ma Ya Handsome halin da nike ciki gaskiya nasan yana nan tunda yau Lahadi" waro ido haulat tay a rud'e tace "Fatuu kar kiyi haka don Allah ki daure, wllh ko kin gaya mashi ba abunda zai maki saidae ya baki hakuri to kinga gara ma kar ki fad'i mashi d'in don k'imarki na iya ragewa a idonshi" kaman zatai kuka tace "naji koma mi zai faru ni ban damu ba in dai ya sani, kuma tunda shi mai tausayi ne nasan yana iya tausaya man ya aure ni har rokonshi ma zan iya yi ko matsayin mai aikinsu ce ya Aure ni" bud'a baki Haulat tay tasa tafin hannunta ta rufe cike da al'ajabin jin kalaman Fatuu, ganin tana niyyar juyawa yasa ta kamo hijab d'inta a rud'e take fad'in "Fatuu kar kiyi haka don Allah, wllh ni nasan ba zai aureki ya had'a ki da Aunty Fanan ba danginsu bazasu ta6a yarda ba....." bata k'arasa Maganar ba sakamakon buge mata hannu da Fatun tay ta nufi gidan Hajiyar kai da gani bata cikin hayyacinta idanunta sun rufe,tsaye Haulat tay ta rasa mi zatayi ta tsaida Fatuu, zuciyarta ta raya mata ko taje ta fad'i ma kawu Amadu sai kuma wata zuciyar tace ko kafin ki fad'i mashi ma ai aikin gama ya riga ya gama, sharr kwalla suka fara zubo mata ta fara fad'in "duk ni naja maki wannan halin Fatuu dana sani ban maki Maganar nan ba" k'arshe dae data rasa mafita kawae sai ta juya ta nufi hanyar islamiyyar tana share hawayen dake zubo mata, Fatuu na zuwa tabi ta k'aramar kopa dake bud'e tana zuwa bakin fence door ta kutsa kai part din Haisam............... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013n804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2009* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 9 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........Kallon Abbas haisam yay yace "let's say abunda ka fad'a gaskiya ne amman miyasa Zaraah zatai hakan, ban tunanin na ta6a yi mata wani abu da zai sa tay tunanin am in love wit her, so i don't believe all what you ave said" ya k'arasa Maganar yana d'an shaking kanshi alamar rashin yarda, Abbas yace "ai shi so ba ruwanshi da wannan H,zakee wani kallonshi kawae zakai kaji kana sonshi,kuma kai har kace ba kai mata wani abu da zata ji son ka ba duk irin kyautatawar da kake ma yarinyar......." katseshi Haisam yay da fad'in "ita kadae nike ma haka ne?", girgiza kai Abbas yay "nasan ba ita kadae kake kyautata mawa ba sai dae Maganar gaskia tata is special kana kulawa da yarinyar over ta yadda wani ma zai iya yin tunanin sonta kake, nasan ba wani abu bane hakan a wurinka duk wanda yake tare da kai yasan kai Mutum ne mai kyautata ma mutane wanda a zamanin nan da muke ciki da wuya asamu Wanda Allah ya bud'a mawa yake irin Alkhairin da kake, ba kuma don ganin idonka ba kamawa tay nake fad'a nasan ba so kake ba, sai dae kasani ka sake ma Zarah da yawa ta yadda ko siblings naka ban tunanin suna samun hakan daga gare ka hakan kuma zai iya juya komae" shiru haisam yay yana binshi da ido har ya gama sannan cikin cool voice d'inshi yace "komae nake ma Zaraah inada dalili Abbas, yarinyar is an Orphan marainiyane ita da Uncle d'inta and farkon dana fara Magana da ita na fahimci tana da ambition mai kyau wanda in aka tallafa mata zatai achieving don tana da kokari sosae, saidae kuma i found her behaviours so strange because i never came across wani da yake behaving yadda take shiyasa na fara tabbatar da lafiyanta ta hanyar tambayarta daga baya na fahimci haka take kuma tana buk'atar ta canja behaviours nata ta maida hankali kan karatunta shiyasa nai amfani da daman glass da ta fasa man" jinjina kai Abbas yay sosae ya gamsu da Maganar Haisam d'in sai yanzu ya fahimci komae dama kuma suna tallafa ma marayu sosae ta Foundation d'in Hajiya, "Wato ka gane H,Zakee, ita zuciya abu kad'an ke canja ta ba kamar kyautatawa don ingantaccen hadisi na Manzo (S.A.W) yay magana akan ita zuciya an halicce tane akan son mai kyautata mata da kuma k'in mai munana mata, nasan kasan da hakan to anan son zai iya kasancewa na soyayya ko akasin hakan to kwata kwata ba abun mamaki bane wllh don Zaraah taji tana sonka,zata iya tunanin kuma kaima son nata kake shiyasa kake mata hidima sosae kamar yadda nima can baya na fara zargin hakan bani kadae bama har Najeeb yay tunanin hakan har ina cewa wannan overtaking zai man kenan ya fara da biyu" ya k'arasa yana dariya shima Haisam dariyar yake kafin yace "da dae ba waccan sarkin kishin zan aure ba, just don nace bazan aureta ba fa ta kwanta Medical bed yanzu taji kuma zan hadata da wata in Aurensu i can't even imagine abunda zai faru kuma kaima kasan bani da ra'ayin mata biyu wannan sai kai da Najeeb, nayi mamakin ma yadda akai kakai yanzu da mace d'aya i thought by now kana da 4 wives" wata yar iskar dariya Abbas yasa shima Haisam d'in dariyar yake yace "saurin mi kake ka jira ka gani tunda Addini ya bamu dama ni bazan cuci kaina ba kai dai kaje ka k'arata da guda d'aya kaida gwauro baku da maraba ba kamar in ta fara aiki" d'an ta6e baki yay ya maida idonshi kan tv, duk wannan Maganganun da suke akan kunnan Fatuu dake lafe a gefen kopar parlon Haisam sakamakon lokacin da Abbas yay mashi waya yace yana parlonshi da ya dawo daga Masallacin shigewa kawai yay ba tare da ya rufe kopar ba ita da kanta ta rufe saidae bata idasa datsewa ba, Lokacin data shigo part d'in nashi sai kuma ta tsaya tana wasi wasin zuwa wurinshin can dae ta shiga cike da tsoron abunda zai biyo baya hakan yasa ta rink'a tafiya cikin sand'a har ta haye balcony d'in ba tare data yi wani kwakkwaran motsi ba tana zuwa bakin kopar ta jiyo muryar Abbas da yake shi yana d'aga murya in yana Magana ba kamar Haisam ba, duk da shima Haisam d'in ya d'an d'aga murya don ba wuri d'aya suke zaune da Abbas d'in ba yana can bangaren armchairs wannan dalilin ne yasa ta lafe ta kasa kunne tana sauraransu cike da tashin hankalin jin akanta suke Maganar,kenan Abbas ya gano tana son Ya Handsome ta fad'a a ranta, ba komae yafi tada mata hankali ba sai Maganar Haisam ta k'arshe da yace baida ra'ayin mata biyu da kuma zance kwanciyar Fanan gadon Asibiti, hannu tasa ta rufe bakinta sosae gudun kada tay abunda zasu gane tana a wurin, a hankali jiki a sa6ule ta juya har wani duhu take gani ba tare data ankare ba wurin sauka daga stairs d'in balcony d'in kafarta ta zame ta tafi gaba d'aya ta fad'a kasa tumm k'arar faduwar har cikin falon hakan yaja hankalinsu duk suka kalli kopar parlon Abbas ya mik'e yana fad'in bari ya duba yaga miye, tana fad'uwar cike da k'arfin hali duk da buguwar da tay ta yunk'ura ta mik'e da sauri ta nufi hanyar fita tana kaiwa bakin fence p door Abbas na fitowa ta fice da sauri saidae yaga bayanta kawae lokaci guda kuma ya shaida wacece, d'an cije baki yay had'i da girgiza kanshi cike da tausayawa ya ayyana a ranshi kenan ma tana zuwa Haisam d'inne bai sani ba,juyawa yay ya koma cikin falon ganin Haisam na kallonshi yasa yace mashi baiga komae ba k'ilan yara ne ya d'aga mashi kai kawae, komawa yay ya zauna idonshi akan Haisam dake kallon tv ya rasa mima zai ce mashi ya yarda abunda ya fad'i mashi game da Zarah gaskiya ne, can dae yace "H,Zakee yanzu in da gaske Zaraah son ka take ya za'ai?" juyowa yay ya kalleshi ya d'age gira yace "kai zan tambaya wannan ai tunda kai ka kawo issue d'in" shiru Abbas yay shi kanshi baisan mi zai ce ba, ta ko ina abun ba mai sauk'i bane ganin Haisam ya kafe shi da ido yasa yace "kawae na tambayane amman in ma hakanne bai wuce ka bata hak'uri ba in ace ta fad'a maka, yanzu kuma da bata fad'i maka ba rashin sanin is the Best ka rabu da ita kawae, amman fa kasani kayi breaking heart d'in yar Mutane wllh" d'an Murmushin gefe yay kawae ya maida idonshi kan tv don shi jin Abbas d'in kawae yake ba don ya yarda ba. Tafiya take saidae bata san inda take wurga k'afarta ba don wani duhu take gani Allah dae ya taimaka ta k'arasa gida lafiya hannunta guda dafe da gaban kanta, tana shiga d'akinta ta aje jakar hannunta a tsakar dakin tasa hannu ta cire hijab d'in jikinta ta cillar da ita can gefe ta haye can tsakiyar gadon ta zauna ta d'age k'afafunta sama tasa hannuwanta ta k'ank'amesu tana ta zare ido yayin da zuciyarta ke tariyo mata maganganun Haisam can ta saki k'afafun ta kama kanta da duka hannuwanta ta fashe da wani irin matsanancin kuka cikin kukan take fad'in "Ni in baka aure ni ba Ya Handsome ba gadon Asibiti zan kwanta ba mutuwa zanyi......" haka ta dingi maimaitawa can ta sark'e ta fara tari kan kace mi sai amai ta saddo kanta k'asa don ta kasa saukkowa daga gadon dama kitson kalaba ne akanta gaba d'aya sun saukko har k'asan d'akin kan carpet,tun tana aman d'an Abincin da ta ci har takai ba komae da yake fitowa sai kumallo gaba d'aya ta gama galabaita, tana cikin wannan halin Amadu ya shigo ya shiga toilet bayan ya fito yana niyyar fita ya jiyo kakarin aman da take yi da mamaki ya juya ya nufi d'akinta don shidae yasan ta tafi islamiyya don data dawo baiga wucewarta ba, lokacin da ya d'aga labulen d'akin cike da al'ajabi yake kallonta yama kasa shiga saboda tsoro, ganin halin da take ciki yasa ya kira sunanta shiru bata amsa ba har saida ya k'ara kiran nata sannan cikin mawuyacin hali ta d'ago mashi hannu tace "Kawu Amadu....." yana jin hakan ya kutsa kai da sauri ya nufi inda take yasa hannu ya d'agota ya maidata saman gadon sosae kafin ya zauna yana kallonta a razane ganin yadda ta koma sai faman nishi take yace "miya sameki ne haka, ba kin tafi makaranta ba?" fashe mashi tay da wani kukan tace "Son Ya Handsome nike amman shi baya sona" waro ido Amadu yay baki bud'e yake kallonta jin abunda ta fada wanda bai ta6a zaton ji daga bakinta ba, mamaki shimfid'e a kan fuskarshi yace "dama saboda shine kike ta ciwo?" jinjina mashi kai tay alamar eh, wani d'an guntun Murmushin mamaki mai d'an sauti yay yana kallonta cike da Al'ajabi can yace "to ke ya akai kika fara sonshi haka ina ma kika san wani soyayya da har zaki jefa kanki cikin wannan halin?" yunk'urawa tay da k'yar ta ja jiki ta jingina da bango tana nishi cikin jin jiki ta fara bashi labari tun farkon yadda akai ta fara sonshi dalilin Maganar da suka yi da Haulat har zuwa yanzu data je ta iske suna fira da Abbas, murus bakin Amadu ya mutu sai faman bin ta da ido yake sosae kuma yaji ta bashi tausayi don yasan wacece ita sam soyayya bata gabanta don wani lokacin shida kanshi yake ce mata in bata da saurayi taya zatai aure ta tafi ta basu wuri sai tace ai in tazama likita miji sai ta za6a, "Na fahimci komae, kiyi hakuri kinji, naji dad'i da baki sanar dashi ba don ko kin gaya mashi ba abunda zai maki saidae ya baki hakuri tunda kinga saura kwanaki ma bikinshi kuma dama bai kamata ma kice mashi kina son shi ba duk yadda kike ganin kuna mutunci dashi sai wani abu ya ragu na daga mutuncin da yake kallonki dashi don mace da kunya aka santa balle ke da kike cikakkar bafullatana wad'anda aka sani da tantsar kunya, ba wani abu bane don mace tace tana son Namiji tunda ga misali nan akan Manzo (S.A.W) da Nana Khadija Allah ya kara mata yarda ta furta tana sonshi saidae ita a lokacin ta girmeshi kuma bazawara ce,shiyasa in budurwa ta furta tana son namiji sai ad'auketa mara kunya mara kamun kai duk da ba haramun bane" "To Kawu Amadu ya zanyi da sonshi yana damuna baka ji yadda nike ji a kirjina ba, ba irin k'ok'arin da banyi in fitar da son nashi ko na huta amman kullum k'ara yawa yake wllh" ta k'arasa Maganar fuskarta sha6e sha6e da hawaye harda majina, Amadu dai sai kallonta yake abun gwanin ban Al'ajabi wai Fatuu ce so ya maida haka acikin ranshi yake fad'in nifa shiyasa ba ruwana da wata soyayya nafi gane ma in nemi kudi tunda naga sa Mutane hauka yake ga misali nan a gabana, a fili kuma sai ya mik'a mata hannu ta matso kusa dashi cikin sigar lallashi yace "na fahimci yadda kike ji amman ki daure ki cije ki fitar dashi zaki iya nasan ke ba raguwa bace kar ki bari sonshi yay galaba a kanki ya rusa maki mafarkinki na zamowa kwararriyar likita da muke burin yin Alfahari da ita bama mu kadae ba gaba d'aya k'asa zatai alfahari dake in kika dage, lokacin sai kiga Allah ya kawo maki wanda ma yafi shi" da sauri tay mashi wani kallo wanda ya fahimci kona miye yace "nasan Ya Haisam na dabanne samun irinshi zai matuk'ar wuya amman fa bawai baza'a iya ba shima ai cikin Mutane aka sameshi ko to tabbas akwae wasu irinshi wanda ma suka fishi komae, kyau, nasaba da sauransu ke dai kawae ki dage ki cimma burinki zaki ce nina fad'a maki zaki ga yadda maza da suka amsa sunansu zasu yi rububin samunki don kema d'in sarauniyace cikin mata Allah ya baki komae sai abunda ba'a rasa ba tunda mutum tara yake bai cika goma ba amman dae dole sai kinyi yak'i sosae da zuciyarki, sannan in kuma kika bari tay galaba akanki to kuwa zata kaiki ta baro ki ne, ki dage da Addu'a dare da rana nima yanzu tunda na sani zan tayaki da Addu'ar kar ma ki bari gwaggo taji wannan Maganar don ba lalle ta fahimce ki ba tana iya yi maki fad'a ma, kuma kar kiji haushin Haulat abunda ta fad'a maki nima kwanaki sai da nayi tunanin hakan har ina Addu'ar Allah ya tabbatar amman daga baya tun kafin in san da akwae wadda zai Aura na fahimci kawae kyautatawa ce, don haka mu bar ma Allah komae ki d'auka shi d'in ba rabonki bane don wata bata taba Auran mijin wata haka wani ma bai taba Auran matar wani kowa da wanda Allah ya kaddaro mashi matsayin abokin rayuwarshi in kuma shi d'in rabonki ne kina zaune ba tare da wata wahala ba zaki ga yazo ya aure ki har kita mamakin yadda akai hakan, kad'an daga cikin ikon Allah ne Abunda baka taba tunanin zai yuwu yasa ya yuwu, kiyi hak'uri kinji d'iyata kuma yar k'anwata" ya k'arasa Maganar had'i da jawota jikinshi ya rungumeta ta gefe tay lamo tana nazarin maganganunshi acikin ranta, yayin da shima a cikin ran nashi yake fad'in dole ya k'ara kiyayar so, "Amman kawu Amadu inason in daina ganin Ya Handsome yanzu, don duk in na ganshi ciwon k'aruwa yake" yaji ta fad'a cikin sanyin murya,d'agota yay yana kallonta yace "Amman baki ganin zaiyi tunanin wani abun ace ya daina ganinki kwata kwata?" "Eh nidae nafi son hakan kawae ai dama ya kusa tafiya ko" jinjina kai yay yace "shikenan daga yanzu zan rink'a taimaka maki har Allah yasa ki daina jin son nashi idan yazo d'aukarki da safe zan sanar dashi cewa Haulat tazo kun tafi nasan in akai haka sau biyu ko sau ukku zai yi tunanin ko kuna wani abunne a Makarantar yasa kike tafiya da wuri tunda yasan kun kusa fara jarabawa k'ilan ya daina zuwa, to amman bikin nashi fa bazaki ba?" da sauri ta d'aga mashi kai alamar eh, d'an Murmushi yay ya girgiza kai a ranshi yace rayuwa kenan wazai yi tunanin hakan zata kasance a tsakaninsu, komawa tay ta kwantar da kanta a kafad'arshi duk jinta take wani iri,shiru sukai na d'an wani lokacin kafin yace "nasan kina jin yunwa ko?" kai ta d'aga a sanyaye tace "amman ban iya cin komae bakina ba dad'i" yace "daurewa zaki fa karki illata kanki da yunwa su basu san ma kina yi ba kuma ba Abunda zasu fasa koda wani abu ya sameki, bari in kawo maki abu ki ci" ta d'ago daga kafad'ar tashi ya mik'e ya fita, bada jimawa sosae ba ya dawo dama saida ya kulle shagon ya shigo gidan har ya isketa a halin, k'aton biscuit da cup cake guda biyu ya d'aukko mata da lemu ya tasata gaba bayan yasa ta wanko bakinta saida taci sosae ta rage biscuit d'in bada yawa ba yace zaije yayo salla ta daure itama tayi tace to, saida ya gyara inda tay amai sannan ya tafi, ana idar da sallar ya dawo lokacin tana kwance akan sallayar yace taje tayi wanka zata ji dad'in jikinta ya rakata kar bakin toilet d'in bayan ta shiga ya shige d'akinshi, saida ya tabbatar ta gama shiryawa ya koma d'akin ya isketa akan gado tayi lamo ya shiga ya tambayeta akwae abunda take so tace mashi bacci take son yi amman yak'i zuwa, shiru ya d'anyi sai kuma yace mata yana zuwa ya fita, mashin d'inshi ya hau ya nufi bakin hanya can wani babban chemist yayi ma mai shagon bayanin kanwarshi ce ke cikin damuwa tana son yin bacci amman yaki zuwa in akwae Maganin da zata iya sha mara illa ya bashi yace mashi akwae ya d'aukko mashi,bayan ya dawo yadda ya barta haka ya isketa sai wurga ido take ya bata Maganin yace ta bari sai tayi sallar isha tasha tace mashi to tay mashi godiya yace ba komae shidae fatan shi ta cire damuwar a ranta tace in sha Allahu zata cire daga haka ya juya ya nufi Masallaci don yin sallar isha da aka fara itama ta mik'e ta fita tayo Alwala tazo ta kabbara sallar tana gamawa ta d'aukko maganin ta sha kafin ta haye gado, lokacin da Amadu ya k'ara dawowa wurinta har tayi bacci d'an Murmushi yay a fili ya furta "ciwon so ya kama manya,wato dae ashe ciwon nan da gaske ne, nifa na d'auka duk iskanci ne mutum yay shame shame wai shi ciwon so yake, to Allah ka k'ara kare mu da sharrin ciwon so Amin" daga haka ya kashe mata hasken d'akin ya tafi. Bada jimawa ba gwaggo ta dawo tana shigowa gidan d'akin Fatuu ta nufa bayan ta kunna globe ta hangota kudundune saman gado tana ta bacci a ranta ta ayyana yau da wuri akai bacci kenan ta juya bayan ta kashe hasken, tana fitowa tay kacibus da Amadu da ya shigo yana k'ara mata sannu da zuwa don yayi mata a waje,tace "Fatuu Lpy dae ko naga tayi bacci da wuri" da d'an Murmushi kan fuskarshi yace "Eh to da sauk'i tace man wai kanta na mata ciwo shine na bata Magani ta sha" "Bata ma je islamiyya ba kenan" yace "a'a taje" jinjina mashi kai tay tana shirin nufar d'aki shima ya juya yaji ta tambayeshi Fatun taci Abinci kuwa yace mata eh taci daga haka ya fice itama taci Abinci tayo wanka ta kwanta don a gajiye take. Tun bayan da ya gama komae ya kwanta Maganar Abbas ke ta mashi kai kawo acikin ranshi, duk da bai gasgata ba amman kuma wani sashi na Zuciyarshi yana neman takura mashi da zancen, kwance yake jikinshi sanye da sleeping dress riga da wando farare masu laushi yana facing saman d'akin sai faman tunane tunane yake, ba Maganar data fi damunshi sai ta Abbas da yace ya sani yay breaking heart d'in yar Mutane, hannu ya kai ya shafi forehead d'inshi ya bar hannun ba tare da ya cire ba idanunshi a runtse ya fara tariyo rayuwarsu da Fatuu tun farko har zuwa yanzu,wani lokacin yay d'an Murmushi wani lokacinma yar dariya yake har hakoransa su bayyana a haka har ya gangaro zuwa girmanta gaba d'aya rayuwarta cike take da nishadi da wuya kaga tana k'unci, ko ta d'aure fuska na d'an lokaci ne zata washe kaga tana dariya, in bai manta ba zai iya cewa rabon da ya ga farinciki akan fuskarta tunda suka baro Ajiwa Dam ne, a hankali ya cire hannun dake dafe da goshinshi ya bud'e idanuwanshi, yunk'urawa yay ya tashi zaune ya jingina bayanshi da headboard ya kai hannu ya d'auki wayarshi dake kan side drawer, bayan ya bud'eta direct images dake a gallery d'in wayar ya shiga yay scrolling har zuwa inda pictures d'in da sukai a Ajiwa suke ya fara kallonsu da Murmushi akan fuskarshi, kai da kaganta a hotunan zaka fahimci tana cikin tsantsar farinciki ba kamar yanzu ba duk ta canja kamar ba ita ba, a hankali ya maida wayar inda ya d'aukko ya ajiye ya d'age kanshi sama yana jin wani iri a zuciyarshi lokaci guda ya ayyana in dae da gaske shine silar shigar Zaraah halin data ke yanzu bai ji dad'in hakan ba........... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013n804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2010* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 10 _Destiny may be delayed but cannot be changed....._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........Washe gari da Asuba Amadu da kanshi ya je ya tasheta tay salla yace ta tabbatar tayi Karatun Alqur'ani kuma tayi Addu'a sosae tace mashi to sannan ya wuce Masallaci shima, ba laifi taji dad'in jikinta hakan yasa ta fara yin shirin zuwa Makaranta tana gama sallar, lokacin data fita gwaggo na kitchen ta nufi can ta tsaya bakin kopa ta gaisheta don lokacin da take karatu taga gwaggon ta lek'a dakinta da fara'a ta nufota tana amsa gaisuwar tace "ya ciwon kan jiya dana dawo kina bacci Amadu yace man kina ciwon kai" d'an Murmushin yak'e tay tace mata ta samu sauk'i gwaggon tace "Oh ciwo dae ya taso ki gaba kwanakin nan daga wannan sai wannan Allah ya baki lpy mai d'orewa" sadda kanta tay ta amsa da Amin kafin ta d'ago tace mata zata tafi Makaranta da d'an mamaki gwaggon tace "Makaranta da wuri haka, ban tunanin bakwae fa ta k'arasa in ma tayi to yanzu ne" d'an sosa gefen kanta tay tana kallon gwaggon tace "ai zamu fara practical ne yau wanda zai fito mana a Jarabawa shiyasa nike son zuwa da wuri mu samu gaba yadda zamu ga yanda ake yi sosae" jinjina kai gwaggo tay cike da gamsuwa ta juya tana Fad'in bari to ta mik'o mata abun karin kumallo taci sai ta tafi,bayan ta amshi Breakfast d'in ta koma d'aki ta fara ci, ba wani da yawa taci ba ta maida kayan Kitchen lokacin gwaggon bata ciki ta bita d'aki tace mata zata tafi ta bata kud'i, dama koda Haisam ke kaisu tana bata isassun kudin tara da zata iya hawa ma Bus har tay break, saida ta lek'a d'akin kawu Amadu tace mashi ta tafi ya rakota har kopar gida yana k'ara tausarta akan ta d'age ta cire damuwa ta maida hankali kan karatunta, saida yaga tayi nisa ya koma cikin gidan, duk da bata jin k'arfin jikinta sosae haka tay ta sauri don kar Haisam ya isketa a kan hanya har ta k'araso lungun gidansu Haulat, lokacin da ta shiga d'akinsu bin ta da ido Haulat d'in tay ta kasa mata Magana saboda zullumin jin yadda sukae da Haisam jiya itama Fatun kallonta kawae take Haulat din tace mata ta zauna mana, bayan ta zauna gefen katifar itama ta zauna a kusa da ita can dae ta daure tace "kin fad'a mashin ne?" girgiza mata kai tay alamar a'a, wani sanyi haulat taji har saida tay d'an Murmushi kafin ta tambayeta ya akai bata fad'a mashi ba, farko shiru Fatun tay hakanan taji bata son fad'a mata hirar da ta iske suna yi hakanne yasa tace mata kawae ta d'auki shawararta ne shiyasa ta fasa Haulat d'in tace mata ta kyauta, "Amman ya naga kin shiryo da wuri ko Ya Haisam dinne ya kawo ki?" girgiza mata kai tay tace" bashi ya kawo ni ba ni na taho,ban son ina ganinshi" cikin karyayyar murya tay Maganar idonta har sun ciko da kwalla Haulat ta dafata tace "na fahimta Allah yasa hakan yasa ki samu sassaucin abunda kike ji" a hankali ta amsa mata da Amin, tambayarta tay ko ta kawo mata abun kalaci tace mata taci a gida haulat d'in ta tashi ta fara shiryawa saida lokacin da suka saba tafiya yayi sannan suka tafi. Misalin k'arfe 7:30 Haisam ya parker a kopar gidan yay horn kamar yadda ya saba yi in ba kowa a waje, saida yayi sau wurin ukku sannan Amadu ya fito ya nufi Motar Haisam d'in ya sauke glass da Murmushi Amadu ya gaidashi ya amsa tun kafin ya tambayi Fatun Amadun yace mashi sun tafi tun d'azu, shiru Haisam d'in ya d'an yi sai kuma yace mashi Ok, Amadu yay mashi sai ya dawo ya amsa daga haka glass d'in ya d'aga sama ya rufe yaja Motar Amadu yabi bayan Motar da ido kafin ya d'an girgiza kai ya shige gida, Koda suka je Makarantar Haulat na lura da ita sam bata wani saki jiki ba har gara ma lokacin da bata kaiga ganin Iv d'in ba ta d'an fara saki amman yanzu an koma yar gidan jiya, saidae tay shiru ko ta d'aga ma Mutum kai in yayi mata magana sai ta kama take bud'e baki tay Magana, ita kanta halin da take ciki na matuk'ar damunta ba kuma kamar hukuncin da ta yanke na daina ganin Haisam duk sai take jin wani irin kad'aici gashi zuciyarta sai tay ta ayyana mata fuskarshi bata da aiki sai tunane tunane,Haulat dae bata gajiya da k'arfafa mata guiwa, A ranar da daddare bayan tayi sallar isha ta fita waje wurin kawu Amadu yana ganinta yace "Juliet ya akai" yay Maganar yana yar dariya ita kuma ta d'an tura mashi baki ganin tay mashi tsaye yasa yace mata ya akai ne tace "dama bacci nike son yi na kasa shine nazo ka bani wannan Maganin na jiya" bud'a mata ido yay yace "ke kina son zama yar k'waya ne?" a sanyaye tace "a'a ba magani bane?" "Eh magani ne amman in kika saba bazaki iya bacci ba sai da shi don haka ki je ki kwanta kawae baccin zai zo in sha Allah kiyi Addu'a" tana shirin k'ara yin Magana ta jiyo k'arar bike d'in Haisam ya dawo daga Gym aikuwa da sauri ta juya gudu gudu ta shige gida ta la6e cikin zaure tana lek'enshi har yazo ya wuce, sauke ajiyar zuciya tay ta d'an cije baki kafin ta nufi cikin gidan tana shiga d'aki ta haye gado ta kwanta tana ta tuna rayuwarsu da Haisam kwalla na gangaro mata duk ranta bai mata dad'i sai can dare ya nisa bacci yay awon gaba da ita. Washe gari ma sai ga Haisam yazo d'aukarta lokacin ta tafi Amadu ne ya lek'a ya k'ara ce mashi ai basu dad'e da tafiya ba ya amsa da Owk ya tafi, abu kaman wasa Amadu na cewa k'ilan in yazo sau biyu ko ukku ya daina zuwa sai gashi har ranar Juma'a saida yazo a wannan lokacin kunya ta gama rufe kawu Amadu hakanan yake daurewa yana ce mashi ta tafi shi kanshi ba don yana son hakan ba don sai yaga kaman ana wulakanta Haisam dinne wanda yafi karfin ai mashi haka, Zaune take a aji duk ranta a jagule yake kukan zuci kawae take wanda akace yafi na fili rad'ad'i sanin yau saura sati d'aya Haisam ya tafi kaman yadda taji a bakin gwaggo don sam bata san Fatun ma bata zuwa gidan Hajiya ba a tunaninta in bata nan tana zuwa wani lokacin kuma tana fita da sunan zata can d'in gudun kar gwaggo ta gano bata zuwan amman data fita sai tay tafiyarta gidansu Haulat haka in Fanan ta kira waya tana amsa su gaisa don sosae take kiran layin gwaggo ta gaishe da ita wani lokacin ma in Fatun na d'aki data ji suna waya sai tay baccin k'arya, Haulat har ta gaji da bata hakuri sai dae tay ta bin ta da ido don tasan in dai Haisam ba tafiya yay ba ta tabbatar ta rasashi bazata rage damuwar da take ciki ba a yanzu, suna zaunen Malaminsu na Chemistry ya shigo bayan yan ajin sun tashi sun gaidashi yace su same shi a Lab ya juya ya fita duk yan ajin suka mik'e suka fara fita hannuwansu ruk'e da littattafansu da biro, mik'ewa Haulat tay idonta akan Fatuu da ta d'aura Fuskarta kan desk, tasan ba bacci take ba don in dae ba malami a ajin haka take yi tace "Fatuu ki tashi mu tafi Lab za'ai Practical" shiru bata tanka mata ba har saida ta maimaita mata sannan ta d'aga mata hannu alamar taje kawae, jiki a sa6ule Haulat ta koma ta zauna kaman zatai kuka tace "Don Allah Fatuu kiyi hakuri nasan kina yi wllh, amman karki bari damuwar da kike ciki ta shafi karatunki wannan Practical d'in fa kinsan shine zai fito mana a ssce kaman yadda Malam yace kuma dole ba yadda za'ai mutum yaci paper d'in Chemistry da physics ba tare daya ci Practical ba ki yi hak'uri ki taso muje" jimm ta d'anyi kafin can ta d'ago idanunta sun yi ja cikin disashewar murya tace "kije Haulat ko naje bazan gane komae ba damuwa tay man yawa wllh amman daga baya sai ki koya man" tana niyyar maida kan Haulat ta kama hannunta tace "ki daure pls, sai kinfi ganewa in a gabanki akai ni kinsan ba lalle in gane ba sosae tunda wani lokacin kece ma ke k'ara man bayani in ban gane abu ba" zare hannunta tay ba tare data ce mata komae ba ta maida kanta kan desk, ba yadda Haulat ta iya dole ta mik'e don kar ai biyu babu ta d'auki littafinta da biro ta fita. Sai lokacin da aka tashi suka fito daga Laboratory d'in kasantuwar ranar Juma'a ne d'aya saura ake tashi gaba daya, lokacin da Haulat ta shigo ajin Fatun na a yadda ta barta, d'an girgiza kai tay cike da tausayawa ta nufi seat d'in ta maida littafinta a jaka kafin ta d'an bubbuga kafad'ar Fatun tana Fad'in ta tashi su tafi gida an tashi, shiru kaman bazata d'ago ba can kuma ta d'ago idanunta sunyi jawur da alama kuka tasha tana son karatunta amman damuwa ta hana ta maida hankali ji take gaba d'aya karatun ya fita a ranta abunda zuciyarta keso ne kawae a ranta,tasan ko taje gidan ba wani samun sauk'i zatayi ba gashi bata son kawu Amadu yaga bata d'auki shawararshi ba yaji haushi dama ba k'aramin kokari take ba a gidan tana 6oye damuwarta sai tazo makarantane duk sai abun ya kacame mata gashi yanzu tasan gwaggo na nan don aikin rana take sai karfe biyu zata tafi a halin da take ciki kuma tasan da taje gidan zata gano akwae abunda ke damunta don yan kwanakin nan tana yawan tambayarta kodai wani abun ke damunta ciwoce ciwocen sun yi yawa, tunawa da wannan yasa tace ma Haulat taje kawae ita ba yanzu zata taho ba, cike da damuwa Haulat tace "haba Fatuu ya za'ai ki zauna a Makaranta ke kad'ai bayan an tashi ba kowa don Allah ki taho mu tafi" da Haulat d'in ta takura mata akan ta tashi su tafi sai tace mata akwae inda zata je ne amman sai ta d'an k'ara hutawa zata koma gidan anjima, sarai haulat tasan k'arya take ba wani wuri da zata je amman sai tace to bari ta zauna in ta hutan sai su tafi tare, cike da tsiwa tace "to in banson zuwa dake fa, nace ki tafi ai ba 6acewa zanyi ba ko zan dawo anjima" d'an girgiza kai Haulat tay ta mik'e ta d'auki jakarta ta had'a data Fatun tace bari ta tafin mata da ita ba don ranta yaso ba ta tafi tana yi tana waiwayen Fatun har ta fita ita kuma tay kwanciyarta saman seat. Cikin sa'a Haulat ta samu Bus tana fita ta hau, daidai kwanar da aka saba aje su suka sauka da sauran yan Unguwar, bayan ta fita lungun tana shirin hawa hanya sai ga Motar Haisam ta taho shima ya dawo daga aiki dama duk juma'a a gida yake salla, tsayawa tay tana kallon Motar don ta gane shine yana zuwa saitin ta ya taka burki ya tsaya a hankali kuma glass d'in Motar ya sauka fuskarshi ta bayyana, da d'an Murmushi Haulat ta gaishe shi fuska a sake ya amsa mata yace mata an dawo tace mashi eh ya jinjina mata kai tana ta d'ar d'ar a cikin zuciyarta kar ya tambayeta Fatuu don tasan muddin ta fad'i mashi halin data baro ta to tabbas zai bita ne in kuma yaje ba makawa tasan Fatuu na iya fad'i mashi halin da take ciki ita kuma bata son hakan ya faru, kawae sai taga glass d'in ya fara d'agawa sama daga haka yaja Motar Haulat ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta juya ta tafi, a daidai gaban shagon kawu Amadu ya tsaya lokacin Amadun na shago yayi wankan juma'a yana jiran lokacin sallar ya idasa yi, yana ganin Motar ta tsaya ya fito da sauri glass d'in d'ayan side d'in ya sauka Amadun ya lek'a ta nan yana gaidashi ya amsa mashi kafin ya tambayeshi Zaraah ta dawo ne, shiru Amadu ya d'anyi alamar tunani sai kuma yace "gaskiya dae banga wucewarta ba amman bansan koda ina cikin d'aki ba don ban dad'e da fitowa ba bari in ga kota dawo" d'aga mashi kai yay ya juya ya nufi gidan bada jimawa ba ya dawo yace mashi bata dawo ba ya d'anyi shiru kaman mai tunanin wani abu sai kuma yaja Motar bayan ya amsa mashi da Ok, Yana isa gidan toilet ya shiga bayan ya rage kayan jikinshi a laundary, bada jimawa sosae ba ya fito ya fara shirin zuwa Masallaci,sanye cikin galleliyar shadda light blue ya d'aura hula data hau da kayan sai daukan ido take don yasan da ya je ba hular Hajiya sai tay Magana, haka ma takalman kafarshi kalar kayan ne agogon diamond d'in hannunshi nata kyalli sai sakin fitinannan kamshi yake ya nufi part d'in Hajiya, atare kaman ko yaushe suka tafi Masallacin bayan sun dawo suka nufi dining Area Saude tay serving nasu suka fara cin Abinci can bayan sunyi nisa da farawa Hajiya ta dakata idonta akanshi tace "wai nikam Fateema na zuwa wurinka,shirun yay yawa yaushe rabon da in ganta gidan nan, rannan da muna waya da Dijen nike tambayarta kwana biyu banga Fateema ba sai take ce man ai tana ce mata tana zuwa kilan bata iske ni ne nace to kilan dae wurin yayanta take zuwa ko kuma lokacin da take zuwa bani nan d'in amman dae gaskiya da tana zuwan zan ganta ne tunda ai ba ko yaushe nike fita ba, gaba d'aya tunda tay ciwon nan ta canja kwata kwata duk da dae dama mai irin ciwon nan komi yay ba abun mamaki bane" idon Haisam a kanta bayan ta gama Maganar yace "kinsan they're about to start their final exams k'ilan shiyasa bata da time en zuwan" jinjina kai tay sai kuma tace "amman kai d'in tana zuwa wurinkan?" shiru ya d'anyi sai kuma yace mata eh tana zuwa ta gaidashi kuma yana kaisu skul, shi kanshi baisan miyasa yay mata k'aryar ba abunda ba halinshi ba, gyad'a kai tay cike da gamsuwa taci gaba da cin Abincinta, kasa cigaba da cin Abincin yay ya mik'e ganin hajiya na kallonshi yace mata zaiyi abu a part d'inshi ne daga haka ya nufi cikin parlon ya fice, part d'in nashi ya koma yana shiga ya zauna kan kujera yasa hannu ya dafa gaban kanshi, tun bayan da sukai Magana da Abbas abun keta damunshi a rai yana son ya kauda tunanin amman abun ya faskara zuciyarshi na damunshi da son sanin da gaske ne abunda Abbas ya fad'a saidae kuma wani bangare na zuciyar na gargadinshi kan rashin sanin shi yafi kaman yadda Abbas din ya fad'a amman tabbas ya fara zargin akwae abunda ke damunta ba ciwon da yake tunani bane kad'ai ba kamar Maganar da Hajiya tayi, yanzu ya gane tana yi ma Grandma d'inta k'aryar tana zuwa gidan alhali kuma bata zuwa,mi zaisa tay haka? ya jefa ma kanshi tambaya, to ko dae anyi mata wani abune don har yanzu yana shakkun Maganar Abbas saboda yasan wacece Zaraah tun bata kai hakan ba, haka ya dingi sak'e sak'e a ranshi gashi shi sam baison damuwa duk sai yaji ya takura shiyasa ba k'aramin abu ke tsaya mashi a rai ba, cire hannun yay ya d'auki wayarshi dake ajiye a gefe ya shiga Contacts d'inshi bayan ya bud'e, lambar kawu Amadu ya kira bugu biyu yay picking yana gaidashi ya amsa mashi kafin ya tambayeshi Zaraah d'in ta dawo yace mashi a'a gaskiya ba kowa ma a gidan don gwaggo ma ta tafi aiki amman dae yana tunanin ko sun tsaya lesson ne don yanzu wasu ranakun suna kaiwa har yamma, amsa mashi yay da Ok ya kashe wayar, tunani ya shiga yi mi zaisa ya ga Haulat ta dawo in har lesson suka tsaya tunda tare suke class d'insu d'aya, yin wannan tunanin yasa shi mik'ewa ya kai hannu kan c-table ya dau car key ya juya ya fice daga parlon, yana fita ya nufi Parking Space ya hau Mota ya fice direct gidansu Haulat ya nufa bayan ya parker a kopar gidan ya sauke glass ya kira wani yaro dake can gefe guda yace ya shiga yace Haulat tazo, bada jimawa ba sai gasu sun fito tare tay wanka tana sanye da hijab kalan kayan jikinta, da mamaki kan fuskarta take bin Motar da kallo dama tun a ciki tayi mamakin jin wai mai Mota yana kiranta kamar yadda yaron yace da ya shiga, zagayawa tay bangaren da driver mota d'in yake har saida gabanta ya fad'i ganin Haisam, d'an Murmushin yak'e tay mashi ta gaidashi ya amsa kafin yace "Zaraah fa?" wurga ido ta fara tana motsa baki a dabarbarce tace "bata koma gida bane?" maimakon ya bata amsa sai ce mata yay "kun dawo tare ne?" hannu ta d'aga tana d'an juya shi tace "a'a bamu dawo tare ba" "Then where is she?" ya kafeta da kaifafan idanunsa duk tay kalar rashin gaskiya ta rasa yadda zatai mashi bayani can tace "da..dama zamu shiga Practical ne to sai nace ta taso mu tafi lab d'in sai tace man bata lafiya in je kawae,t..to lokacin da aka gama aka tashi da na koma class d'in sai ban ganta ba nayi tunanin taje wani wuri ne sai na d'an jirata amman shiru bata dawo ba sai na d'an dudduba sauran classes d'in amman bata nan sai nai tunanin ko ta taho gidane" still yay yana sauraranta har ta gama sannan yace "amman d'azun na ganki da bag d'inta right?" damm k'irjinta ya buga da karfi tace "e...eh ai dana koma ne naga jakar shine na d'aukko dama yanzu nike niyyar zuwa gidan in ga ko tana nan" sigh yay ya maida idonshi gaban Motar kaman mai nazarin wani abu can ya juya yace shikenan zata iya tafiya ta amsa da to ta juya da sauri ta shige gida shi kuma yay reverse ya fita daga lungun,tana shiga zaure ta tsaya ta dafe kirjinta cike da fargaba,abunda yasa bata fad'a mashi gaskiya ba tasan zai iya tambayarta miyasa Fatun tak'i biyota kuma zai iya ganin tayi rashin hankali na baro ta da tayi duk da ita tasan wacece Fatuu in ta kafe kan abu to fa sai tayi sai wani ikon Allah ne zaisa ta fasa don ma yanzu ta d'an yi sanyi saboda halin da take ciki, lokacin da ta lek'o wajen bata ga Motar tashi ba alamar ya tafi, tunani ta shiga yi na Fatun bata dawo bane har yanzu yasa yazo nemanta, can dae ta juya ta koma cikin gida, yana fita lungun ya mik'i hanyar da zata fitar dashi daga Unguwar yana hawa titi kai tsaye Makarantar tasu ya nufa, yana shiga main gate d'in ya nufi Senior Section a bakin gate ya tsaya yay horn mai gadi ya lek'o yana yin arba da Motar ya koma da sauri ya bud'e mashi gate d'in ya kutsa ciki a can gefe ya parker Motar mai maigadin ya nufo shi yana washe baki don ya sanshi sosae sakamakon yawan Alkhairin da yake masu, bud'e Motar yay ya fito bayan sun gaisa cikin cool voice d'inshi yace "Don Allah ko akwae sauran Students a ciki?" d'an jimm maigadin yayi kafin yace "gaskiya bana tunanin da sauran dalibai don gaba d'aya aka tashe su saboda yau juma'a har da yan aji shidda yau basu tsaya lessin d'in da ake masu ba, Allah yasa dae lafiya" yay Maganar idonshi akan Haisam d'in, "Akwae Sister na da nike kawo wa so bata koma gida ba har yanzu" da sauri maigadi ya ruk'e ha6a alamar Al'ajabi yace "Hajiya dae da kake kawowa itace bata koma gida ba?" kai kawae ya d'aga mashi maigadin yace "to kuma ba'a aiketa wani wuri ba ko tace zata biya wani wuri?" jin tambayar tashi yasa haisam d'in yi mashi bayanin da Haulat tay mashi, da sauri yace "to ina ganin mu duba ajin nasu ko tana can, ai ajin kimiyya take ko?" nan ma kai Haisam ya d'aga mashi alamar eh maigadin ya wuce gaba Haisam yabi bayanshi suka nufi Science classes d'in ya tambayi haisam ajin su Fatun ya nuna mashi, koda ya shiga wayam ya tadda ajin ba kowa sai tarkacen takardu da ledojin da aka yayyadda, juyowa yay ya kalli Haisam dake tsaye gaban class d'in yace "Wllh Yalla6ai kaga dae ba kowa a cikin ajin" shiru haisam yay yama rasa tunanin da zai yi, maigadin yace bari ya duba sauran ajujuwan kai kawae ya d'aga mashi, gaba d'aya saida maigadin ya zagaye classes d'in dake wurin amman ba Fatuu ba alamarta ya dawo wurin Haisam d'in yace mashi wllh baiga kowa ba, suna cikin hakan saiga Discipline Master na section d'in ya shigo zai nufi Admin Block yana ganinsu ya nufesu yana tambayar maigadin lafiya kuwa ya mik'a ma Haisam hannu suka gaisa maigadin yay mashi bayanin da Haisam d'in yayi mashi, shima da mamaki yace "to ina taje haka, yakamata ace by now tana gida ba Sp Fateema Muhammad Ardo bace?" cikin cool voice d'inshi yace mashi ita, "Malam nace ko a duba clilic (clinic) ko tana can tunda ance bata lafiya" maigadi ya fad'a yana kallon discipline d'in yace mashi "ai Baba bana tunanin tana can gaskiya don ko d'azun nabi ta wurin a rufe yake bamma tunanin an bud'e clinic d'in yau" gaba d'aya sukai shiru kowa da abunda yake tunani a ranshi Haisam dai yay shiru, can discipline ya kalleshi yace "Yalla6ai abunda nike tunanin za'ai shine a d'an tattambaya inda ake tunanin zata iya zuwa ko cikin unguwa haka don zai iya yuwuwa tabi wata ne tunda bata lafiya ni kaina kwanakin nan na fahimci ba daidai take ba mun kwana biyu ma bamu yi aiki tare da ita ba saidae mataimakiyarta tunda duk munsan tana da lalurar jinnu" jinjina mashi kai Haisam yay yaci gaba da cewa "nima yanzu zan fita cikin staff quarters in dan bibbincika muga, bari in baka lambar wayata in Allah yasa ka koma ka taras ta koma sai ka sanar dani nima nan in mun ganta sai a kira a sanar da kai in Allah ya yarda ma za'a ganta don ban tunanin tayi nisa" gaba d'aya suka amsa da Allah yasa Haisam yace mashi wayan na Mota ya bashi tashi sai ya saka mashi lamba d'in nashi yay mashi flashing, bayan ya saka mashi sukae sallama ya wuce suma suka dawo bakin gate saida yay ma maigadin Alheri yana ta mashi godiya da Addu'oi da fatan Allah yasa a ga Fatuu ya bud'e mashi kopar Motar ya shiga bayan ya juya ya fice daga cikin Makarantar Baba maigadin nata d'aga mashi hannu......... Jama'a ina Fatuu tayi????🤔🥹 _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2011* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 11 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ......Tunda ya fito daga Section d'in na su ya rasa tunanin da zaiyi game da inda Zaraah ta tafi a cikin halin ciwo,Wayarshi dake ajiye gefe ya kai hannu ya d'auka ya fara tunanin k'ara kiran Kawu Amadu ya tambayeshi ko ta dawo daidai lokacin ya fito daga Main Gate d'in Makarantar, yana k'okarin kara wayar a kunne kaman ance ya waiga gefe ya hango kaman wata a cikin Bus Stop dake a 6angaren hagu, cire wayar yayi ya katse kiran kafin ya taka burki a hankali ya fara yin reverse har yazo daidai Bus Stop d'in ya sauke glass d'in kopar, k'ura ido yay yana kallon cikin bus stop d'in, wata ce zaune ta d'age k'afafunta sama ta kifa kanta saidae ba lalle a gane ko d'aliba bace don hijabinta ya sauka ta lullube jikinta gaba d'aya kuma kalan hijab d'in ba irin ta sauran d'alibai bace, sanin Fatun irin hijab d'in take sawa don ita prefect ce yasa ya bud'e Motar ya fita ba tare da ya rufe kopar ba ya nufi Bus Stop d'in saidae tun kafin ya k'arasa ya shaida itace sakamakon takalmanta dake ajiye a gefe wanda shine ya k'ara siyo mata su wani zuwa da yay Lagos, tsaye yay bakin wurin yana k'are mata kallo fuskarshi a yamutse sam baiji dad'in ganinta a wurin ba don ba komae a ciki sai uban dirty, "ZARAAH" ya kirata da wata irin murya shiru bata d'ago ba har saida ya d'an k'ara d'aga Murya ya sake kiranta sannan ta fara kokarin fiddo kanta daga cikin hijab d'in, koda tay arba dashi a firgice ta mik'e tsaye tana kallonshi shima kallonta yake sam fuskarshi ba walwala ganin yadda duk ta canja ga idanunta sun yi ja sun d'an k'ank'ance, kasa jure ma kallon nashi tay ta sadda kai idanunta cike tab da kwalla k'irjinta na bugawa da sauri da sauri, "Follow me" ya fad'a had'i da juyawa, har ya tafi sai kuma ya tsaya ya juyo yana mata wani kallo ganin bata motsa ba,a sanyaye ta duk'a tasa takalmanta kafin ta nufe shi da kanshi ya zagaya ya bud'e mata kopar ta shiga ya rufe shima ya zagaya ya shige, jin bai ja Motar ba kuma taji ya shigo yasa ta d'aga kai a hankali ta kalleshi suka had'a ido da sauri ta mayar da kanta k'asa dama tunda ta shigo haka yake, tsit kake ji cikin Motar sai Ac dake ta aiki, "Zaraah" bayan wani lokaci taji ya kira sunanta, a hankali ta amsa mashi, "Look at me!" d'an cije baki tay da k'yar ta d'aga ido ta kalleshi sai kuma tasa hannu guda tana d'an murza idanun don bata iya jure ma kallon nashi, Gently yace "Zaraah what's ur problem??" cikin disasshiyar murya tace "ba komae" d'an ta6e baki yay kafin yace "in ba komae mi zaisa ki zauna a skul ke kadae after closing hours and kince ma Haulat baki lafiya bazaki attending Practical class ba ta dawo bata iske ki ba ina kika je da baki tsaya kun tafi gida tare ba?" d'an runtse ido tay jin yadda sautin muryarshi ke fita yaushe rabon data ji Maganarshi haka,to miyasa ma yake nemanta da har yaje wurin haulat ta ayyana a ranta, tana cikin haka taji yace ba Magana yake mata ba, d'aga kai tay ta kalleshi kaman zata sa kuka tace "naje Clinic ne ina can aka tashi lokacin dana dawo class kuma banga kowa ba shine na kwanta daga baya kuma na fito na zauna anan" duk da ta d'ago bata kallon idanunshi take Maganar, sigh yay idonshi akanta ya tambayeta mi yake damunta ne saida tay d'an jim kafin tace cikinta ke ciwo,shiru yay yana nazarinta sai faman sussune kai take, "Why kika daina zuwa gidan Hajiya??" har saida gabanta ya fad'i jin tambayar da yay mata d'an d'agowa tay tana yamutsa fuska tace "ai yanzu wani lokacin har yamma muke kai wa saboda lesson da ake to wani lokacin dana koma nike tafiya islamiyya Weekend ma ina islamiyya" yace "ranar da ba islamiyyan fa ba zaki iya zuwa ba?" "Ai wani lokacin in na koman na gaji ne amman ko ranar nan naje Hajiyan bata nan sai Aunty Saude kadae na iske kai kuma lokacin baka nan" tana k'arasa Maganar ta dukar da kanta don tasan k'arya ta shirga mashi bata son ya gane kuma tasan bazai ta6a zuwa wurin Saude da sunan ya tambayeta game da abunda ta fad'a ba shiyasa tace mashi haka,shiru yay na d'an lokaci still kallonta yake, "About coming to skul in d morning miyasa kike tahowa, in baki so ina kawo ki ne u should tell me sai in bari ba kisa inata zuwa kullum ba" d'an runtse ido tay ashe bai jin dad'in hakan, dama kawu Amadu kullum sai ya gaya mata yazo ran Alhamis har yana ce mata kodae ta daure yaci gaba da kai su tunda yak'i daina zuwa kar yaga kaman ana wulakanta shi tace ita dae a'a bata so, jin tunda yay Maganar bai kuma cewa komae ba yasa ta d'aga idanu ta kalleshi ashe kallonta yake nan take idanunsu suka had'u kasa saukesu tay a hankali tace "da..dama an fara yi mana lesson da wuri ne shiyasa muke tahowa amman kayi hakuri" kawae sai taga yay d'an guntun Murmushin gefe ya jingina kanshi jikin headrest, yana daga cikin abunda ke burgeshi da ita wato bada hakuri da ta yi mashi ba daidai ba, a da yayi tunanin harda tsoron yarjejeniyar dake tsakaninsu yasa take saurin bashi hakurin amman daga baya ya fahimci bashi yasa ba kawae haka take, ganin bai ce komae ba yasa tay tunanin baiyi hak'urin ba a hankali ta k'ara cewa "kayi hakuri Ya Handsome" daga yadda yake ya k'ura mata ido itama kallon nashi take tana d'an motsa baki, "Ya Handsome yayi hak'urin" yay Maganar had'i da lumshe ido da sauri ta kauda fuskarta gefe ita kanta bata ma san Ya Handsome d'in ta ambata ba tuni take son ta daina kiranshi da hakan amman ta kasa saboda ta saba bata ta6a kiranshi da sunanshi ba tunda suke, shiru ya biyo baya kowa da abunda yake sak'awa a ranshi haisam ya d'an d'age kanshi sama gaba d'aya ya yarda da abunda ta fad'a don yasan bata mashi k'arya hakan yasa ya d'an ji sauk'in damuwar da yake ji game da halin da take ciki wani sashe na zuciyarshi kuma na izashi akan ya tambayeta dangane da Maganar da Abbas yay saidae bai san ta ina zai fara ba sai kawae yace mata ance kina sona? ya tambayi kanshi the question sound so silly, juyawa yay ya kalleta ta juyar da kanta gefe tana kallon waje, hannu ya kai ya fara kokarin jan Motar ta juya ta kalleshi sai kuma ta sake kauda kan gefe ta d'an ja hijab d'inta ta rufe Fuskarta, tunda suka hau hanya ba wanda ya k'ara tanka ma wani shi idonshi na akan hanya ita kuma ta rufe fuskar, jin ya tsaya da Motar yasa ta d'an cire hijab d'in tana kallon inda suke don taji sunyi saurin isowa in dai gida suka zo, idasa cire hijab d'in tay tana k'are ma harabar da suke kallo lokaci guda ta fahimci inda ya kawota wato Wani babban private Hospital ne har saida kirjinta ya buga ta juya da sauri ta kalleshi suka had'a ido yace mata ta fito ya bud'e kopar Motar ya fita, ba yadda ta iya jiki a mace ta bud'e itama ta fita ya tunkari main entrance na Asibitin ta bi bayanshi walking slowly, yana shiga reception inda Medical records suke ya nufa dama suna da Family card a Asibitin nan Hajiya ke ganin likita bayan ya masu bayani an shigar da sunan Fatun suka ce ya kaita Nurses room za'a d'auki BP nata sai a tura su wurin likita ya amsa da Ok, juyowa yay yayi mata alamar ta biyo shi da hannu suka nufi window d'in da a samanta aka rubuta Nurses room d'in yana tsayawa kafin yay Magana yaji daga gefenshi an ce "H,Zakee d latest ango to be" juyawa yay ya kalli mai Magana da fara'a ya furta "Dr habeeb" yana k'araso ya mik'a mashi hannu suka gaisa da fara'a yace "to ya shirye shirye, ai Abbas ya tura mana iv in sha Allahu damu za'a d'aura Auren" da Murmushi kan fuskarshi ya amsa da Allah ya yarda, "Amman miya kawo ka Asibiti ko kana fever d'in angwancewa ne" yar dariya yayi ya nuna mashi Fatuu yace sis d'inshi ya kawo,ya kai idonshi kanta kafin ya juya kan haisam yace "an tura ta wurin Dr ne?" yace "No yanzu za'a tura" jinjina kai yay ya lek'a ta windown yace ma Sister d'in dake zaune tay taking BP nata ta tura mashi ita yanzu ta amsa da "Ok Dr", kallon Fatuu ya sake yi yace ta zagaya ta shiga ciki ta amsa da to bayan ta gaidashi ta tafi sukuku da ita ta shiga shi kuma suka cigaba da Magana da Haisam yana mashi complaining kan rashin Network mai kyau da suke fuskanta sai ana cikin aiki ya yanke Haisam d'in ya fara suggesting abunda yakamata suyi suna cikin haka Fatuu ta fito yace ma Haisam su tafi consultation room yace Ok, bayan sun shiga Dr d'in ya nuna ma Haisam kujeran dake gaban desk ita kuma Fatuu ta gefenshi yace ta zauna ya fara lallatsa Computer d'in dake sama kafin ya d'ago da d'an Murmushi yace " yauwa sis mike damunki ne?" shiru ta d'anyi sai taji dama bata ce ma Haisam ciwon ciki take ba yanzu ba daman ta canja ciwo, a hankali tace, "Ciwon ciki ne" "Ok ciwon ciki wane iri, kina period ne?" damm gabanta ya d'an fad'i duk sai taji nauyin tambayar shima Haisam dake latsa waya cak ya tsaya hakanan yaji yana son jin amsar da zata ba likitan, "Ok yaushe kika fara ne?" saidae kawae haisam yaji wannan tambayar ta likita don da kai Fatuu ta bashi amsar tana yi d'in, "Shekara biyu" ta fad'a k'asa k'asa, "To dama duk in zaki kina ciwon ciki ne?" kai ta d'aga mashi alamar eh ya sake cewa "Yanzu shine ya saki ciwon cikin ko kuwa wani ciwon cikinne daban?" a hankali tace mashi shine duk da k'arya take ba period d'in take ba yanzu, tambayarta yanayin yadda take jin ciwon yay ta bashi amsa ya jinjina kai kafin yaci gaba da rubutu a Computer d'in can ya sake kallonta yace bayan wannan ba abunda ke damunta tace eh, Jama'a ina Haisam? da alama ya k'ame a inda yake saboda tsabar mamakin jin wai Zaraah na period for good 2 years now abunda bai ta6a zato ba duk da yasan ya ta6a yi mata fad'a kan sakin baki tana fad'in abu irin haka amman bai yi zaton zata iya rikewa ba tsawon shekara biyu ba tare da ya sani ba, kallonta likita yay bayan ya gama rubutun yace ta jirasu a waje don ya lura duk bata sake ba ta mik'e sumimi sumimi ta fice, Doctor ya kalli haisam yace mashi ba wata matsala bace menstrual pain ne ai yaji ma ya d'aga mashi kai kawae yace yanzu ya tura Magani zasu je pharmacy a amsar mata ya amsa da Ok yana kokarin mik'ewa Doctor ya dakatar dashi ta hanyar cewa"amm H,Zakee, sis d'in nan naka ba wani abu dake damunta banda wannan ciwon?" komawa yay ya zauna yana kallon doc d'in yace akwae matsala ne, "No,ba wata matsala bace babba just bp d'inta ya d'anyi high gaskiya so bansan ko wani abun na damunta bane amman zai iya yuwuwa ciwon da take yasa shi hawan is possible" ya k'arasa yana jinjina kai, shiru Haisam ya d'anyi doc Habib yace kar ya damu zai iya yuwuwa ciwonne amman zai iya tambayarta yaji in wata damuwarce kar abun yay yawa ya amsa mashi da to suka mik'e tare suka fita lokacin tana zaune kan dogon bencin dake kallon d'akin ganin likitan suna fitowa ta had'a ido da Haisam da sauri ta juyar da kanta gefe don yanzu sai taji tana kunyar had'a ido dashi ganin yasan abunda tasan bai sani ba, shima d'auke kan yay ya bi Doctor suka je pharmacy d'in aka bata magungunan, lokacin da suka fito bata sani ba saida suka zo saitin inda take zaune ta d'ago yay mata alamar su je da kanshi ta mik'e da sauri tay gaba, suna fitowa harabar Asibitin Haisam yace ma doc ya koma shi dake cikin aiki suka yi sallama yay mashi godiya kafin kowa ya juya ai tana ganin ya nufo Motar ta bud'e da sauri ta shige, lokacin da ya bud'e Motan ya shiga ta juyar da kanta ta rufe face d'inta da hijab kaman yadda tay da zasu zo, idonshi akan hanya bayan sun fito yana ta driving bai tanka mata ba saidae can k'asan zuciyarsa he was totally surprise,sai yan tunane tunane yake lokaci bayan lokaci yake d'aga ido ya kalleta ta cikin Mirror, a daidai gaban wata babbar Super Market ya parker Motar gefen hanya tana jin sun tsaya ta cire hijab d'in tana kallon inda suke jin ya bud'e Motar yasa ta waiga ta kalleshi lokacin ya fita daga cikin Motar ya zagayo ta side d'in da take ya nufi cikin wurin tana ta kallon bayanshi har ya shige ciki taci gaba da kallon wurin, bada jimawa sosae ba ya fito hannunshi ruk'e da babbar shopping bag mai d'auke da tambarin wurin tana ganin ya taho da sauri ta k'ara rufe fuskar, back door ya bud'e ya ajiye ledan kafin ya zagaya ya shiga ya ja suka tafi, yana driving yana cigaba da kallonta ta mirror ba komae yafi tsaya mashi ba face hirar su da Abbas ga kuma Abunda Doctor Habeeb yace game da BP d'inta,suna shiga layin gidansu ta bud'e fuskar tana kallon gefenta har suka k'araso kopar gidansu a hankali ta juya ta kalleshi tace mashi ta gode yay nodding kanshi tana niyyar bud'e Motar taji yace "da yaushe kuke zuwa skul din?" d'an kyakkyafta idanu tay ta d'an d'age baki tace "da wuri dae muke tafiya wani lokacin k'arfe bakwae ko da yan mintuna" calmly ya furta "Ok" ta bud'e Motar ta fita ganin tana niyyar nufar gida ya sauke glass d'in ya kirata ta juya tana kallonshi yace ta d'auki kayan baya nata ne kai kawae ta d'aga mashi ta bud'e ta d'aukko ledar ta lek'a ta gaban tace mashi ta gode, bin ta da ido kawae yay ta janye kan sai kuma ta kasa tafiya tana ta kallonshi ya ja Motar ba tare da ya rufe glass d'in ba tabi bayan Motar da kallo, sai lokacin hankalinta ya kai kan wak'ar dake tashi daga cikin shagon kawu Amadu ta Hamisu breaker wato so dangin Mutuwa,natsuwa tay tana saurarar baitinkan wak'ar kamar haka, _🎼🎼🎻So dangin Mutuwa ne shi don baya duba rarrashi so guba ne kama da Madara yake, shi Masoyi yana da gaggawa buri nay ya yi wa so k'awa shi kuma so kama da kura yake🎼_ _So bai san wata kara ba,bazai ragawa kowa ba,kullum tanadin kushewa yake_🎼 _........So baza ya kyale tsoffi ba, kuma bai tsallake MAKWABCI BA nagane shi illatarwa yake🎼_ Tana jin wannan baitin ta juya da gudu ta shige gida sam shi kawu Amadu bai ma san da ita a wurin ba yana can yana sauraren wakarshi, tana shiga d'akinta ta nufa ta haye gado tana ta6e baki kwalla suka fara gangarowa kan cheeks d'inta don sai taji kamar don ita akai wakar can ta jawo jakar da ta shiga da ita ta zazzago abunda ke ciki, k'amewa tay baki bud'e tana kallon uwar Pads d'in da ya siyo mata dasu turarurruka kawae sai ta idasa fashewa da kuka, dole ma tay kuka wllh rasa Haisam matsayin Miji ba k'aramar Asara bace yanzu da bata had'a komae dashi ba ji uwar hidimar da yake da ita ina ga kuma ace shi Mijinta ne, Mutum ne shi da yasan yakamata wanda ba tantama zai kare hakkokin Matarshi sosae, haka ta d'ingi riskar kuka har ta gaji don kanta ta tashi duk da kanta na mata wani irin ciwo ta cire Uniform d'in jikinta ta d'aura towel ta nufi toilet don yin wanka, bayan ta gama shiryawa ta kabbara sallar Azahar da bata yi ba tana gamawa tabi da La'asar da aka yi bada jimawa ba, bayan ta gama sosae tayi Addu'oi tana zubar da kwalla ta rok'i Allah in Haisam rabonta ne Allah ya batashi matsayin miji in ba rabonta bane kuma yasa ta hak'ura dashi,bayan ta shafa ta mik'e jin kanta nayi mata ciwo ta fita taje d'akin gwaggo ta d'aukko Magani bayan ta sha ta koma kan gado ta kwanta ta fad'a duniyar tunane tunane ita kanta ta san mawuyacin abu ne ta Auri Haisam ba kamar da ta ji da bakinshi yace baida ra'ayin mata biyu kawae zuciyarta ce ke takura mata da soyayyarshi, yunk'urawa tay ta tashi zaune a fusace ta fara buga katifa tana Fad'in "Ki daina takura man don Allah, bai sona, bai sona miyasa kike azabtar dani da son shi ne!!!" ta k'arasa tana ta huci ta kumbura baki, a hankali kuma ta koma ta kwanta tana cigaba da hucin da alama zuciyarta ta kaita mak'ura a haka bacci 6arawo yay awon gaba da ita......... _Dandano Daga Next Page_ .......Da sauri ta runtse idanuwanta tana jin wani abu nayi mata yawo a duk ilahirin jikinta kafin a hankali kuma ta ware su kan santala santalan hannuwanshi farare tas masu d'auke da zara zaran yatsu ga gashi liya liya kwance luff,tunda take dashi tsawon lokaci bai ta6a sa hannu ya ta6a jikinta ba sai yau itace dae ada kan ta girma sosae take ta6a shi shima bazai wuce a kirga ba kaman lokacin da su goga suka so yin raping d'inta da ya zo ta kankameshi sai lokacin da zai masu hoto a park da kuma ranar salla shima da zai masu hoto....tana cikin tunanin taji ya kira sunanta a sanyaye, slowly ta d'aga idanuwanta da suka kankance ta kalleshi cikin ido kaman yadda shima yake kallonta lokaci guda kirjinta ya hau bugawa da mugun k'arfi shi kanshi k'irjin nashi bugawar yake amman ya daure Calmly yace "tell me what's it??" k'uri tay mashi ko kyaftawa batayi ya lumshe mata ido alamar ta fad'i mashin, A hankali ta fara motsa baki alamar zata yi Magana tace"...........TILL MONDAY IN ALLAH YA KAI MAMU RAI. Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524. Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2012* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* 2 Years Back........ Ranar wata Asabar Fatuu ta farka da Safe don yin shirin zuwa islamiyya, tana zuwa toilet don yin fitsari kawae sai taga jini jage jage a k'asanta, a razane ta fara k'wala ma Gwaggo kira tun acikin toilet d'in amman shiru gwaggon bata amsa ba sakamakon bacci da take, hannunta ruk'e da k'asan skirt d'inta ta fito ta nufi dakin gwaggon tana cigaba da k'wala mata kiran, bayan ta shiga d'akin gadon da take kwance ta nufa tana kiranta a firgice lokacin gwaggon ta farka idonta akanta cikin harshen fulatanci ta tambayeta lafiya, da d'ayan hannunta tay mata nuni da tsakankanin cinyoyinta gwaggon ta kai idanunta wurin ta k'ura ido tana kallo, can ta d'ago da alamun damuwa ta kalli Fatun, ganin yanayin fuskarta yasa Fatun cewa Gwaggo ko jinin hailan ne yazo....."tsit tayi sakamakon kallon data ga gwaggon nayi mata, can ta mik'e tace mata su je tace to tay gaba tana tafiya a gwaggwale sai kace yar shayi, toilet d'in suka koma tace mata ta cire kayanta ta wanke wurin da kyau amman banda sabulu sai tayi wanka tace to, komawa tayi d'akinta ta d'aukko mata towel ta kai mata kewayen tay tsaye a gefe tana jiranta har ta gama sannan suka nufi ciki tare tace ta shiga d'akinta tana zuwa, d'akinta ta koma ta samo mata wani yankin kallabinta mai tsabta da taushi ta koma d'akinta, lokacin da ta shiga Fatun na zaune gefen gado sai wuwwurga ido take ta mik'a mata tace "ki amfani da wannan ki tare kafin in fita....." tun kan ta k'arasa Fatun ta turo baki tace "kam gwaggo pad fa ake sawa ba tsumma ba", a harzuke tace "to banda shi, baki ji nace kafin na fita ba in siyo maki tunda Amadu bai sayar da ita" tana tura baki tace " to ko cikin taki ne ba sai ki ban ba...." tun kafin ta k'arasa gwaggon takai hannu zata make mata baki tana Fad'in bari ta buge bakin maras kunya tunda tayi da ita tana amfani dashi, da sauri ta goce lokacin kuma taji wani abu ya zubo mata ta d'an d'aga towel d'in ta lek'a gwaggo tay tsaye tana kallon ikon Allah, a firgice ta d'ago tace "gwaggo gashi nan ya zubo da yawa!" tsoki ta ja ta juya ta nufi wardrobe d'inta ta d'aukko mata pant ta dawo ta bata tace ta tashi tasaka in ta gama tasa kaya tace to gwaggon ta juya ta fice, bayan ta gama shiryawa cikin doguwar riga ta d'auki towel d'in da hannu d'aya cike da kyankyami ta nufi d'akin gwaggon lokacin tana zaune gefen gado da alama Al'amarin ya jefata a damuwa, "Gwaggo wannan yadda shi zanyi ne jinin ya 6ata shi" ta Fad'a tana d'age baki,wani kallo mai kaman harara gwaggo ta bita dashi kaman bazata tanka mata ba sai kuma tace "tunda baki da hankali ai sai kije ki yadda d'in", "To ya zanyi dashi"? Ta tambaya kaman zatayi kuka,gwaggon tace " kije ki kama wurin ki wanke shi tass ki shanya" Tura baki tay tace "Kai gwaggo bafa jinin yankewa bane baki ga daga inda yake fitowa ba kuma sai kice in wanke" banza tayi mata tana harararta hakan yasa ta juya tana d'an k'unk'uni taje ta wanke gwaggo na jinta zata shiga d'aki ta kwala mata kira tazo d'akin, nuna mata k'asa tay tace ta zauna tayi zaman cin tuwo tay mata k'uri da ido,saida ta d'an dauki lokaci suna kallon juna kafin ta fara Magana "ina son in gargad'e ki game da wannan abun da kika fara saura kije ki bud'e baki kina shelar kin fara Al'ada don kina yin hakan zai d'auke ya daina zuwa kwata kwata kuma mace bata haihuwa in bata yin shi don haka in dae baki son ya d'auke to kija bakinki kiyi shiru" tana dakatawa Fatun tasa hannu ta kama lips d'inta alamar bazata fad'i ma kowa ba sai kuma ta cire hannun da d'an murmushi tace "ashe dae shine kenan yanzu na balaga ko?" kai kawae gwaggon ta d'aga mata, "Wayyo, yanzu dole in rink'a yin Azumi duka kenan, amman dae ai in ana yin shi ba'a azumin da salla ko?" ta wurga ma gwaggon tambaya nan ma kai ta d'aga mata, kafin taci gaba da cewa "sannan zan kara gargadinki, Fatuu ba ruwanki da maza, nasan halinki sarae amman ki k'ara kiyayewa kar ki yarda wani yay maki wayo yay maki abunda bai dace ba don yanzu tunda kin fara Al'ada to ko hannunki Namiji ya kama zaki samu juna biyu ne"? Zaro idanu tayi a tsorace tace "cikin shege irin na d'iyar yar wajen aikin ku?" kai nan ma ta d'aga mata a tsorace ta fara girgiza kan tace "to bazan bari ba gwaggo ai kinga dae koda Bello na gidansu Umar ya kama man hannu can da dad'ewa har na falle shi da mari ai na gaya maki ko?" kai ta d'aga tace "eh kin gaya man amman yanzu kar ma ta kaiga kin bari an kama hannun" da sauri tace "toh", "Sannan sai kin dage da yin tsafta don in Mutum bai kula da ya je kusa da Mutane za'a ji yana wari, ki rink'a yin wanka akai akai, kina saka turare amman ba wai in zaki fita ba don ba kyau a jikinki zaki d'an rinka fesawa ki shafa na shafawa....." katseta Fatuu tay da fad'in "harda can wurin da yake zubowar?" girgiza kai tay a'a sai bayan kin kimtsa kin rufe sai ki shafa, kuma ba ta6a Al'qurani har sai kin samu tsarki...." "To harda Hadisai ba'a ta6awa?" kai ta girgiza mata alamar a'a, haka taci gaba da fad'i mata Abubuwan da ya kamata tayi da wanda bai kamata ba, koda Haulat taje islamiyyar bata ga Fatun ba hakan yasa da yamma ta biyo mata lokacin gwaggo bata nan tace mata ita bata lafiya bazata ba taje kawae koda ta tambayeta miya sameta bata fad'i mata ba tace ita dae bata lafiya kawae taje haulat d'in tay tunanin ko bata son zuwa ne kawae tay tafiyarta sai bayan Magrib gwaggon ta dawo tayo mata siyayyar su pads da panties duk da tana da su harda turare, Washe gari kuma da ciwon ciki ta farka ta d'ingi bullayi duk da ba wani ciwo bane na tashin hankali amman ta dingi raki har tana ce ma gwaggon ita dae in haka zata ci gaba to gwara ya d'auke kawae ta huta gwaggon dae tay banza da ita iyakar sannu kawae take mata da kyar bacci ya d'auketa bayan gwaggon ta bata Magani, Washe gari kuma data tashi ba ciwon har ta tafi Makaranta, sai ga Fatuu ta zama kamar kwad'o bunu bunu sai ta tafi tayo wanka ita don kar aji tana wari haka ta dingi 6arnar pads sai da gwaggo ta ankare ta tambayeta yadda akai tace ai sau biyar take wanka har saida taba gwaggon dariya tace wannan ai sai sanyi ya kamata tace mata sau ukku zata rink'a yi Safe da Rana da Dare tace to, sati d'aya tayi tana yi kafin tayi wankan tsarki don an koya masu a islamiyya ta iya kuma gaba d'aya da tana jinin bata je islamiyyar ba, sai da ya k'ara dawo mata ne wani watan lokacin suna Makarantar boko ta fara ciwon Haulat ta kaita Clinic anan tasan Fatun ta fara period d'in bayan sun fito ta fara mata tsiya tana ashe su Fatuu girma yazo shiyasa aka k'ara hankali ita dae banza ta mata tana ta kanta, ko su Hajiya sai da Azumi ya zo ne suka san ta fara Period d'in sosae ta ja bakinta tay shiru saboda Abunda gwaggo tace mata.Wannan kenan game da yadda Fatuu ta fara Menstruation. *** **** ***** Ranar Monday da wuri ya fara shirin zuwa aiki before k'arfe bakawae na Safe ya shirya tsaf ya fito ko part d'in Hajiya bai je ba don yasan ba lalle in ta tashi ba, Parking Space ya nufa ya hau Mota ya fice daga gidan su Officer na mashi a dawo lpy, daidai gaban gidansu Fatuu ya parker motar lokacin k'arfe bakwae tay daidai ya danna horn sai da yay kusan sau hud'u sannan saiga Amadu ya fito da alama ma daga bacci ya taso yana isowa bakin Motar ya sauke glass da Murmushi Amadu ya gaishe dashi ya amsa yace ya kira mashi Zaraah yace to ya juya don yasan bata tafi ba tunda bata yi mashi sallama ba, lokacin daya je d'akinta ta gama shirinta tsaf zata tafi yace "ke kije ga Romeo d'inki can yazo" wani kallo tay mashi cikin rashin fahimta tace waye romeo yace mata Ya Haisam yana jiranta a waje daga haka ya juya, sototo tay ita sam bata yi tunanin daya tambayeta time d'in da suke tafiya zuwa zai yi ba, tura baki tay ta d'auki jakarta taje tay ma Gwaggo sallama kafin ta nufi hanyar wajen kaman an mata dole, lokacin data fita ya rufe glass d'in side d'inshi hakan yasa ta zagaya ta bud'e gaban ta shiga kafin ta rufe,d'an juyawa tay ba yabo ba fallasa ta gaishe dashi ya amsa fuskarshi a d'an sake kafin yace mata ya jiki tace mashi da sauk'i daga haka ya ja Motar suka tafi, lokacin da taje gidansu Haulat bayan ya tsaya fuskarta kaman zata yi kuka Haulat ta tambayeta lafiya tace ba Ya Handsome ne bal yazo zai kaisu, "To shine na d'aure Fuska haka keda Ya Handsome d'inki" wani kallo ta jefa mata kaman zata kai mata bugu Haulat d'in tay yar dariya tace "yi hakuri wasa nike maki amman yakamata ki saki ranki don Allah" "To nifa nace banson ganinshi sai ciwon yay ta k'aruwa kuma ni so nike in daina jin abunda nike ji" tay Maganar kaman zata saka kuka, "Kar ki damu zaki daina ji ki dawo kamar da bada jimawa ba, da kin daina ganinshi in ya tafi" shiru kawae tay sam bata son kuma jin zancen tafiyar nashi, bayan sun koma wurinshi suna shiga Motar Haulat ta gaidashi ya amsa kafin yaja suka tafi kaman dae kullum Fatun bata Magana sai ma juyar da kanta da tay gefe,bayan sun isa tana shirin fita ya tambayeta lokacin da zasu tashi tace sai da la'asar ya bata kud'i tay kaman bazata amsa ba sai kuma ta amsa tay mashi godiya ta fita lokacin Haulat ta fita tana jiranta suka wuce aji. Da la'asar kuwa sai gashi ya dawo d'aukarsu har saida Haulat taji hakanan ya bata tausayi, Washe gari talata ma da wuri ya shirya yaje d'aukarta yana yin horn biyu sai ga Amadu ya fito bayan ya gaishe shi yace "aikuwa wai ta tafi" shiru yay yana kallonshi kafin yace "U mean ta tafi skul en?" Amadu yace mashi eh yanzu da yaji horn yaje d'akinta don yayi mata Magana ya iske bata nan shine ya tambayi gwaggo tace ta tafi,jinjina mashi kai yay yace mashi "thanks" Amadun yay mashi a dawo lpy ya juyo ya koma gida, zaune yay baija Motar ba yasa hannu guda ya ruk'e ha6arshi yana d'an bugun bakinshi da index finger dinshi wondering why Zaraah ta canja ne lokaci guda, nan take zuciyarshi ta bashi amsa da she loves u dat's why,d'age kanshi yay sama ya runtse idanunshi tunanin Maganganun Abbas ya shiga yi ga kuma Maganar Dr Habeeb na bp d'inta da ya d'anyi high hakan na nufin he's responsible for everything, sigh yay ya bud'e idanun a hankali ya kai hannu ya ja Motar ya tafi abun nata mashi yawo a Zuciya, lokaci guda yaji yana son ya tambayeta game da hakan saidae tunaninshi in da gaske Zaraah son shi take ya zaiyi?? A haka har ya isa wurin aiki ba tare da ya samu solution akan hakan ba. Da La'asar Fatuu ta dawo saida taci Abinci sannan ta shiga wanka bayan ta fito ta fara shirin islamiya hakan yasa ta d'an Makara, sanye cikin Uniform ta fito lokacin shagon kawu Amadu a rufe yake don shima yana Makaranta bai dawo ba, saura kad'an ta isa bakin lungun gidan Hajiya da zata karya kwana sai ga Haisam ya taho a kan bike d'inshi zaije gym hakan yasa ta ja ta tsaya shima tsayawar yay lokacin har ya d'an wuce ta don ma ba gudu yake sosae ba, baya yayo da bike d'in ya dawo gabanta suka fara kallon kallo duk da fuskarshi na acikin Helmet amman tana ganin idanunshi lokaci guda taji ta tsargu da kallon da yake mata a hankali ta kai hannu d'aya ta d'an kama gefen hijab d'inta tana d'an matsawa yadda zata hau kan kwanar sosae nan take ya gane abunda take shirin yi wato guduwa har saida ya d'anyi guntun Murmushin mamaki ta ciki ba tare data gani ba wato dae ita bata da ranar girma, hannu ya kai ya cire Helmet d'in daga kanshi hakan yasa ta tsaya tana kallon fuskarshi ba ko k'yaftawa shima kallonta yake a kausashe yace "kina ruguwa zan biki in take ki!!" zaro idanu tay da alama ba k'aramar razana tay da jin abunda ya fad'an ba don bata ta6a tunanin zaice zai mata hakan ba, still idanunsu na kallon juna k'irjinta na bugawa da sauri da sauri yayin da shi kuma yake nazarinta, can ta kasa jurewa ta duk'ar da kanta ba zato kawae sai ganin kwalla yay na d'iga kan hijab d'inta hakan kuma ya k'ara tabbatar mashi da abunda yake son ganewa hakanan ba yadda za'ai don yana kallonta ta kama yin kuka gashi sam a can baya bata jin nauyin had'a ido dashi yarinyar dake mashi k'uri da ido, "U can go" taji cool voice d'inshi ta fad'a,aikuwa ko kallonshi bata yi ba ta juya da sauri ta tafi saida ta d'anyi nisa ta waigo yana nan bai tafi ba juyawa tay taci gaba da tafiya ba tare da ta sake juyowa ba har sai da ta kai k'arshen lungun ta sake waiwayowa still he's there da sauri tasha kwana ta shige sai lokacin ya maida Helmet d'in ya ja bike d'in ya tafi,koda taje islamiyyar tunaninshi kawae take duk in ta ganshi sai zuciyarta ta k'ara rikice mata komae ya dawo mata sabo Haulat na lura da ita don ta rigata zuwa saidae yanzu har ma ta saba da ganin Fatun cikin irin halin don tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta k'ok'i. Bayan sallar isha lokacin da Haisam ya dawo ya tsaya bakin shagon Amadu yana ganinshi ya fito yaje wurinshi ya gaishe dashi bayan ya amsa yace yaje yace ma Zarah yana nemanta yanzu a part d'inshi ya amsa mashi da toh ya juya da sauri, lokacin da ya shiga tana parlor ita da gwaggo ta tasa Abinci a gaba tana d'an tsakurarshi, a bakin kopar parlon ya tsaya yace "Ke kije Ya haisam na kiranki ya wuce yace ki iske shi a part d'inshi yanzu" daga haka ya juya ya koma, lokaci guda gabanta yay wani irin bugu ta fara tunanin miyasa zai kirata a cikin ranta,ganin bata da niyyar tashi yasa gwaggo cewa "to ki tashi ko kyaje ki dawo dare nayi in kin dawo kya ci Abincin ki sauri" ido tabi gwaggon dashi lokacin ta mayar da idonta kan TV dama kallo take, a sanyaye ta mik'e ta fita hannunta ruk'e da plate d'in Abincin ta mayar kicin kafin ta koma d'akinta ta daukko mayafi ta d'aura akanta ta tafi, tunda ta tunkari gidan zuciyarta ke harbawa ji take kaman ta rusa ihu, lokacin data k'arasa part d'in nashi a hankali tasa hannu kan handle din ta d'an turo kopar ta leka ganin bai ciki yasa ta idasa shiga ta tsaya bakin kopar tana kallon cikin falon yaushe rabon da ta shigo,rasa yadda zatayi ta sanar dashi tazo tay hakan yasa tayi tsaye ta kasa k'arasawa ciki balle taje bakin Corridor kaman yadda take mashi a da,tanata tsaye ba tare data zauna ba can taji fitowarshi da sauri ta kai idanunta kanshi da alama wanka yayo yana sanye da jallabiya Maroon mai gajeran hannu ganin ya nufo cikin falon yasa ta sunna kanta kasa,kan L-shape yaje ya zauna idonshi a kanta ganin tak'i kallonshi yasa yace taje ta Zauna yana nuna mata bangaren da armchairs suke kaman bazata ba sai kuma ta nufi ciki kaman wadda kwai ya fashe mawa a ciki, kujera ta biyu taje ta zauna ta yadda suna da d'an nisa dashi shiru ya biyo baya kanta na k'asa tana wasa da yatsunta shi kuma ya zuba mata ido yana kallonta ya ma rasa ta ina zai fara mata Magana don yasan ba lalle ma ta fad'i mashi gaskiya ba kaman sauran lokutta,can ya tuna da bata ta6a yi mashi Maganar auren da zaiyi ba nan take ya samu ta inda zai fara, "Zaraah" taji muryarshi ta sauka a kunnanta a hankali ta amsa ba tare da ta d'ago ba, ya k'ara cewa "Zaraah look at me" jimm ta d'anyi kafin slowly ta d'ago idanun ta sauke su akan fuskarshi, "Dama ina son tambayanki ne baki san zanyi Aure ba?" motsa baki ta fara yanayin fuskarta ya canja amman ta kasa cewa komae har saida yace bata ji mi yace bane sannan kaman zata yi kuka tace ta sani, "Ok, ain't u happy for me shiyasa baki nuna man kina taya ni murna ba?" kaman zata saka kuka tace a'a tana taya shi murna, "k'arya kike Zaraah baki tayani farinciki zan yi Aure!" taji ya fad'a da d'an d'aga murya, girgiza kai ta fara idanunta har sun ciko da kwalla ta fara rantsuwar tana tayashi farinciki sai kuma tasa mashi Kuka, d'an guntun Murmushin gefe yay still kallonta yake Wannan yawan kukan kawae ya isa ya bayyana akwae abunda take 6oyewa, gently yace "Zaraah tell me what's ur problem mike damunki ne"? Cikin sigar lallashi yay mata Maganar, kallonshi tay fuskarta shabe shabe da hawaye tace " ba komai Ya Ha...." bata samu damar k'arasawa ba sakamakon buga hannun kujerar da yake zaune yace "U'r not telling me d truth Zaraah! Enough of all these lies kinsan bana son k'arya just tell me why u been acting strange! Ba haka nasanki ba, u are not d Zaraah i ave known!" zare ido tay tana kallonshi yana Maganar a harzuke sak kaman ranar da yayi ma Farha fad'a da tayi mata gori yanzu ma da gani ranshi a 6ace yake yay mata Maganar, "Am all ears Zaraah, mike damunki?" ya sake tambaya bayan ya d'an sassauta muryarshi ta rasa yadda zatayi sai kokonto take a cikin zuciyarta na ta gaya mashi ko karta gaya mashi, ganin ya kafeta da ido yasa ta fara motsa baki a hankali cikin Muryar kuka tace" Ba abunda ke damuna" yaraf ya maida bayanshi ya jingina da kujerar yana cigaba da kallonta ya kankance idanu ita kuma tana ta faman sussuna kai da gani yasan ba gaskiya ta fad'i mashi ba sigh yay calmly ya furta "u can go" aikuwa da sauri ta mik'e ta nufi hanyar fita saidae tana kaiwa bakin kopar sai ta kasa bud'ewa ta fice sakamakon ganin 6acin rai k'arara da tayi akan fuskarshi, kamar an zare mata laka ta juya ta kalleshi ya d'age kanshi sama idanunshi a rufe, slowly ta juyo ta dawo ta durkusa a gabanshi cikin muryar kuka tace "Don Allah YA HAISAM kayi hakurii....." kawae sai ta fashe da matsanancin kuka ta duk'ar da kanta k'asa,yana daga yadda yake yay wani guntun murmushi jin sunan data kirashi dashi wato HAISAM wanda tunda suke bai ta6a jin ta kirashi da hakan ba,shiru bai dago ba still idanunshi a rufe suke yana sauraran sautin kukan da take yi , sosae take kuka harda sheshsheka her tears trickling down, a hankali ya d'ago da kanshi yana kallon kanta da rabinshi ke a bud'e sakamakon zamewa da gyalen yay cikin wata kalan murya da bata sanshi da ita ba ya kira sunanta ba tare data kalleshi ba cikin kuka ta amsa yace "Look into my eyes Zaraah" a hankali ta d'ago idanunta sunyi jawur ta kalleshi still kukan take saidae ta d'an rage sautinshi, tunda yake bai ta6a jin zullumin a fad'a mashi wata Magana ba kamar yanzu saidae ya za6i yaji koma miye da ganinta cikin halin damuwa haka, shi Mutum ne mai damuwa da damuwar wani ba kuma kamar ita da yake ganin shine silar damuwartata in hasashen da suke ya tabbata, "Ki fad'a man abunda ke damunki Zaraah, why the sudden change?" bin shi da ido kawae take tana d'an motsa baki had'i da had'iyar yawu, yaci gaba da cewa "am not Happy seeing u like dis, am not at all" yay Maganar yana d'an girgiza kai alamar tabbatar mata da bai jin dad'in ganinta cikin wannan halin,tsam ya mik'e ya bi ta gefenta ya wuce, tissue box ya d'aukko ya dawo inda ya tashi tana ta dai kallonshi ya yago mai d'an yawa ya mik'a mata ta amsa ta fara goge fuskarta ya aje box d'in a hannun kujerar kafin ya juyo fuskarshi a sake cikin muryar lallashi yace "now tell me, kina da damuwa ko??" tsayawa tay da goge fuskar ta d'an bud'a baki a hankali ta jinjina mashi kai alamar eh, sauke boyayyar ajiyar zuciya yay ya d'an gyara zamanshi ya nuna mata close to him yace tazo ta zauna har saida ta kalleshi da sauri ganin wurin da ya nuna matan ya d'an lumshe mata ido ganin hakan yasa ta mik'e ta nufi Kujerar saidae bata zauna gab da shi d'in ba ta d'an matsa kad'an,juyowa yay ta yadda zai facing d'inta sosae ya fara bin ta da wani kalan kallo da sauri ta sadda kanta k'asa ba zato ba tsammani kawae taga ya kawo hannuwanshi ya kama nata hannuwan, da sauri ta runtse idanuwanta tana jin wani abu nayi mata yawo a duk ilahirin jikinta kafin a hankali kuma ta ware su kan santala santalan hannuwanshi farare tas masu d'auke da zara zaran yatsu ga gashi liya liya kwance luff,tunda take dashi tsawon lokaci bai ta6a sa hannu ya ta6a jikinta ba sai yau itace dae ada kan ta girma sosae take ta6a shi shima bazai wuce a kirga ba kaman lokacin da su goga suka so yin raping d'inta da ya zo ta kankameshi sai lokacin da zai masu hoto a park da kuma ranar salla shima da zai masu hoto....tana cikin tunanin taji ya kira sunanta a sanyaye, slowly ta d'aga idanuwanta da suka kankance ta kalleshi cikin ido kaman yadda shima yake kallonta lokaci guda kirjinta ya hau bugawa da mugun k'arfi shi kanshi k'irjin nashi bugawar yake amman ya daure Calmly yace "tell me what's it??" k'uri tay mashi ko kyaftawa batayi ya lumshe mata ido alamar ta fad'i mashin, A hankali ta fara motsa baki alamar zata yi Magana amman ta rasa ta ina zata fara, jinjina mata kai yay idanunsu cikin na juna ta sake bud'e baki _"Ya Haisam I luv u, I want u to Marry me pls......................._ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2013* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 13 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........Ganin ta zuba mashi Ido tak'i cewa komae gashi kuma tana son tay Magana yasa ya d'an matsa hannuwanta da har lokacin yake ruk'e dasu, firgit tay ta dawo daga zancen zucin da take ta d'aura idanunta kanshi lokaci guda Maganganun su Haulat da Kawu Amadu suka fara mata yawo a kai, gaba d'ayansu Maganganunsu iri d'aya ne kowa cewa yake Kota gaya mashi Hakuri zai bata kuma zai daina ganin k'imarta ga kuma Maganar da ita kanta taji ya Fad'a da Bakinshi na baya ra'ayin mata biyu ga kuma zancen kwanciyar Fanan Asibiti don yace bazai Aureta ba to ita ma kenan da take yar uwarshi yace bazai Aureta ba inaga ita da bata had'a komae dashi ba, lokaci guda tsoron fad'i mashi gaskiya ya kamata murya na rawa tace "da..dama banji dad'i ba zaka tafi don baka ta6a fad'a man zakai Aure ba shiyasa duk na damu" shiru tay ta sunkuyar da kanta don kar ya gane k'arya take, sigh yay ya saki hannuwanta ta jingina gefen jikinshi da kujera,tabbas bata yi k'arya ba bai ta6a Maganar Aurenshi da ita ba a tunaninshi baiga Amfanin yin wannan zancen da ita ba, nisawa yay Calmly ya fara Magana "am really sorry about dat Zaraah,u know Fanan is my sis so a hakan naci gaba da d'aukanta though we were engaged,ina ganin bashi da wani muhimmanci in ta Maganar aure tunda lokacin bai yi ba not knowing hakan zai iya zama matsala......" da sauri ta katseshi tace "a'a Ya Haisam ba wani abu bane kawae nayi zaton Maganar da muka ta6a yi da kai na zamu rayu tare gaskiya ne banyi zaton zakai aure ka tafi ba kwata kwata shiyasa banjin dad'i" zuba mata ido yay yana kallon yadda take Maganar fuskarshi a sake, nisawa yay cikin cool voice d'inshi yace "am so sorry Zaraah i caused u worries, amman don nayi aure ai ba yana nufin zamu rabu ba, mun zama family now ko bananan zamu kasance a tare hakan is so simple ko kin manta miye aikin Yayanki ne?" shiru tayi tana bin shi da ido hakanan sai taji ta samu wata irin Natsuwa, "We're leaving On Friday so ki shirya zamu tafi tare" taji ya fad'a, d'an far far tayi da idanu yanayin fuskarta ya canja ita dae bata son zuwa bikin hakan yasa ta fara tunanin mafita ganin haka yasa yace mata taji abunda yace ta bud'e baki cikin disasshiyar Murya tace "ai bazan samu zuwa bikin ba" wani iri yaji Maganar har saida ya taso ya zauna daidai ya tambayeta dalili, tace "Saboda Next week zamu fara papers d'in Practical kuma ran Friday d'in da ake Auren ranar zamu fara jarabawar gaba d'aya" da k'yar ta samu ta gama Maganar saboda faduwar da k'irjinta yake don tasan k'arya ce take shirga mashi sai Upper Week zasu fara jarabawar ma,shiru yay fuskarshi da experassion dake nuna baiji dad'in Maganar tata ba don ya yarda da duk abunda ta fad'a nan take ya k'ara yin tunanin harda hakan yasa ta damu sosae, cikin muryar lallashi yace "Ok, but banji dad'in hakan ba best friend d'in Groom bazatay attending ba" d'an tura baki tay jin ya kirata da best friend hakan yasa ya d'anyi Murmushi kafin yace "u shouldn't worry about dat ki maida hankali kan karatu sosae don ki passing exams and Maganar biki da komae in kinaso zaki ga komae live koda baki je ba i can arrange dat for u" d'an bud'a ido tay alamar mamaki da d'an Murmushi yace "ko baki so?" a sanyaye tace "amman ai hakan sai an kashe kud'i ko, ace komae na bikin zan rink'a gani" yar dariya yay ya koma ya jingina yace "to dama ba don a kashe su ake nema ba?", tace "to ai kaida kake da hidima" "Wannan ai angama komae kinga sauran kud'in sai akashe kawae" d'an yamutsa fuska tay tace "to amman ai ba iya hidiman bikinne ba kawae in aka yi Amarya ma kud'i ake kashewa sosae in kuma suka k'are ya zaka yi" sosae yake jin dad'in yadda take mashi Magana, d'an bud'a ido yay yace "still bayan uban kud'in dana kashe kuma in akayi auren ma sai na kashe wasu to mi kuma za'ai dasu kenan?" tura mashi baki tay tace "Kayan dad'i ake siya su kaza....." cak ta dakata don ita kanta sai taji she sounds foolish, ganin kallon da yake mata yasa ta yamutsa fuska kaman zata sa kuka kawae sai taga yasa dariya har fararen hakoransa sun bayyana da sauri tasa bayan hannunta ta rufe fuskarta tana yamutsa baki alamar zatayi kuka, a cikin ranshi ya ayyana wannan itace zaraah da ya sani a fili kuma sai cewa yay "Zaraah ko kina son cin kaza ne?" da sauri ta bud'e fuskar kaman zata yi kuka tace "nifa bason ci nike ba, ai haka ake yi ko in akayi aure aita cin kayan dad'i" dariyar ya k'ara yi ya d'age kanshi yana kallon sama da alama dai ba k'aramin dadin firar yake ji ba ita kuma sai kallon fuskarshi take abubuwa na mata kai kawo a cikin zuciya, juyowa yay suka had'a ido da Murmushi yace "kar ki damu da wannan ai itama Amaryar tana da kud'i sai ta d'auki nauyin wannan ni kuma zanyi ma beloved sis d'ina what would make her happy da nawa" d'an Murmushi tayi tace ba sai yayi hakan ba in su gwaggo suka dawo ta ga komae a wayan a Kawu Amadu dan ta6e baki yay yace "Ok in hakan yayi maki, but kema yakamata by now kina da Waya", tace "ai gwaggo bata son in ruke wayan tace sai zan cigaba da karatu sannan" shiru ya d'anyi sai kuma yace mata to taya zasu rink'a communicating in ya tafi tace ko ta kawu Amadu ko ta gwaggo, "No, suma suna da uzurinsu bai kamata a takura su ba, ba kaman Uncle d'inki shima yanzu yana karatu dole yana using phone d'in sosae so i will talk to her ta bari ki rike" jinjina mashi kai tay don tana son dama itama ta fara ruk'e wayar, can kuma sai tace "Nagode Allah ya saka da Alkhairi ya baku zaman lafiya da zuria nagari" d'an bud'a ido yay da Murmushi ya amsa da Ameen idonshi akanta yace "kinma tuna man kince inna yi aure matana ta haihu zaki rinka goya baby d'in ki mashi wasa right??" hannu tasa ta rufe baki tunawa da lokacin da tayi Maganar sai kuma ta cire ta yarfa hannuwa tace "to ai ba anan zaku zauna ba dana yi hakan?" "To ko in tafi dake??" waro ido tay baki bud'e tace "kasar wajen?" lumshe ido yay ya jinjina mata kai yace "sai kiyi karatun likitan acan" da sauri ta girgiza mashi kai tace "a'a so kake Aunty Fanan tace na lik'e ma mijinta ta koro ni a wurgo ni Nigeria gwara in zauna nan in yi karatuna kuma ma ni banson in rabu dasu gwaggo" sigh yay still da Murmushi kan fuskar tashi yace mata Fanan bazatayi mata hakan ba ta d'an ta6e baki tace "uhmm ya haisam baka san kishin mata bane idon mutum rufewa yake kuma ita nasan zata yi kishinka sosae" ita kanta bata san ya akai ma tayi Maganar ba ganin ya zuba mata ido yasa ta sha jinin jikinta kamar daga sama taji yace ya akai tasan zata yi kishi sosae a dabarbarce tace "kawae naga tana sonka ne sosae" tana kai Maganar ta sunnar da kai, jin bai k'ara cewa komae ba yasa ta saci kallonshi kawae sai taga ita yake ta kallo hakan yasa itama ta taci gaba da kallon nashi sun d'an d'auki lokaci haka kafin ya janye idonshi ya kai hannu ya shafi forehead d'inshi Calmly yace "last Sunday i need help to park my stuff nace da Zaraah bata gujeni ba nasan zata man wannan" taji fada a tausashe d'an murmushi tay tana tura baki tace "ni fa ba gudun ka nai ba" ya d'an ta6e baki taci gaba da cewa "to in kana so sai in tattara maka ko gobe ko kuma yanzu inje in fad'i ma gwaggo sai in dawo in had'a maka" shiru yay yana kallon yadda take Maganar har saida tace mashi "kaji" sannan yace "TK have done dat" gyad'a kai tay still da d'an Murmushi akan fuskarta yace "sarkin kuka kawae" dariya tayi wannan karon ta kai gefen jikinta itama jikin kujerar kaman yadda yayi, "Pls Zaraah bana son irin damuwar nan, when u have problem just feel free to tell me" yay Maganar yana tabbatar mata da abunda yace da kanshi ta d'aga mashi kai alamar to, kawae sai taga ya mik'o mata dogon yatsanshi manuni bin shi tay da kallo tun kafin tace wani abu yace "Promise zamu k'ulla bazaki k'ara shiga damuwa haka ba" nan take ta gane dalilin da yasa yayi hakan wato abunda ta ta6a yi mashi a Mota akan rashin cin abinci data ce su kulla Alkawari in yaje wurin aiki zai ci tunawa da hakan yasa tasa dariya sosae har gyalenta ya idasa zamewa shima dariyar yake yak'i janye hannun alamar sai sun k'ulla cikin dariyar tace mashi ba sai sunyi hakan ba wato amsar daya bata a lokacin itama ta bashi, sosae yaji dad'in ganin ta warware dama da biyu yayi hakan, wayarshi ya d'auka ya duba time lokaci guda ya mik'e yace mata yana zuwa ta d'aga mashi kai ya nufi hanyar beedroom ta bishi da kallo, yana shiga Corridor ya d'ago mata hannu ba tare daya juyo ba alamar yasan kallonshi take Murmushi kawae tay ta maida kanta ta kwantar jikin kujerar cikin ranta take ayyana shikenan ta dae rasa Ya Handsome saidae kuma ta wani bangaren taji dad'i sosae yadda ya damu da ita,bata yi tunanin yana ganiyar angwancewa ba zai wani damu da damuwarta haka dan Murmushi tayi kawae, bada jimawa ba ya fito hannuwanshi duka biyun ruk'e da manyan Akwatuna Maroon color da ratsin baki sun matuk'ar yin kyau da gani kuma ba sai an fad'a ba masu kudi ne sosae ya nufo cikin parlon ya aje a gabanta kafin ya sake komawa ya d'aukko wani madaidaici kaman trolley mahad'insu yana zuwa yace tayi amfani dasu tana kallonshi tayi mashi godiya yace mata ta tashi suje ya rakata ta mik'e, manyan da ya fara kawowa ya d'auka yace ta d'aukko k'aramin tace shi ya d'auka ya bata babba d'aya ganin abun zai zamar masu gardama yasa ya bata na biyun ya d'auki k'aramin suka tafi. Lokacin da suka je gidan atare suka shiga tana gaba yana biye da ita da sallama ya shiga saidae ba'a amsa ba Fatuu tace ya shigo suka shiga Falo kowa ya aje akwatin hannunshi kafin suka zauna sai kuma ta mik'e tace bari tayi ma gwaggon Magana ya d'aga mata kai,a daki ta isketa ta bud'e wardrobe tana shirya kaya tace mata ga Ya Haisam yazo tace to ta dakata da abunda take tabi bayanta suka nufi falon, da fara'a ta shiga ta zauna kan kujera ya gaishe da ita ta amsa tace mashi ya shirye shirye shima ya amsa mata da Alhamdulillah, bayan sun gama gaisawan Fatuu ta nuna mata akwatinan dake aje gefe tace gashi nan ya bata, hannu gwaggo tasa ganin dandatsa dandatsan akwatinan kafin ta kalleshi tace "d'ana Haisam baka gajiya ne, haka aka cika Amadu da kaya ran lahadi Tukur ya kawo mashi" da d'an Murmushi yace mata "ba wani abu" Addu'oi ta shiga yi mashi yana amsawa a hankali can ta mik'e tace bari ta zubo mashi Abinci ba tare data jira cewarshi ba ta fice, bada jimawa ba ta shigo ruk'e da babban tray ta d'auro plate d'in abincin rufe da wani ta aje Fatuu ta mik'e ta nufi Fridge ta d'aukko mashi ruwa da lemu ta aje mashi a gefe ta koma ta zauna, ganin yak'i saukkowa yasa tayi mashi Magana ya kalleta kafin ya saukko k'asa kan Carpet ya mik'ar da k'afafunshi ta yadda tray d'in ke gefenshi, hannu Fatuu ta kai ta bud'e mashi Abincin wanda farar taliya da macaroni ne sai miyan alaiyahu abincin gwanin kyau a ido sai kamshi ke tashi, hannu ya kai ya d'auki fork d'in ciki a nutse ya fara ci ita kuma tana zaune gefenshi ganin ya fara ci yasa ta maida idonta kan Tv can ta juyo suka had'a ido tayi mashi Murmushi hakan yasa ya dakata yace mata ita taci Abincinne tace ta fara ci ya aiko kiranta shine ta aje yace taje ta d'aukko ba musu ta mik'e ta fita,hannunta ruk'e da plate d'in Abincin nata ta dawo ta koma inda ta tashi ta zauna kawae sai gani tai ya mik'a hannu ya d'auki abincin nata ya k'ara mata cikin nashi ya maida mata tana dae ta kallonshi bayan ya aje ya kalleta yace yar rigen cinyewa zasuyi tana jin haka ta waro ido alamar mamaki tana guntse Murmushi wato abunda ta ta6a yi da Hajiya a gabanshi shine yace suyi da alama dae duk rayuwarsu da ita bai manta ba, alama yay mata na su fara ta kai hannu ta d'auki Fork d'in ta fara ci, tun tana ci a hankali har ta fara sauri sai gashi ta wuce shi ganin hakan yasa ya fara d'iba da yawa saidae rashin sabo da yin lomar yasa da ya kai Abincin wurin bakinshi duk sai ya zubo Allah ma yasa riga mai duhu ce a jikinshi daba k'aramin 6aci kayanshi zasu yi ba, Fatuu ko mi zatayi in ba Dariya ba sosae take kyalkyata mashi dariya ba 6ata lokaci sai gashi ta cinye nata lokacin nashi da saura da d'an yawa, aje fork d'in yay yana kallonta sai faman Dariya take mashi harda d'an kwantawa bata ta6a tunanin zaice suyi hakan ba, baisan ko shi kadae ke ganin hakan ba amman ba k'aramin kyau dariya ke mata ba hakan yasa sai yay ta kallonta wani lokacin in tana yi,hannu ya kai kan kujera ya d'aukko wayarsa yana dubawa can ya d'ago yay mata alamar ta matso da hannu ta d'an matsa kusa dashi kawae sai gani tay ya d'aga wayar ashe Camera ya shiga da d'an mamaki ta juya ta kalleshi don tasan ba ma'abocin son yan d'auke d'auken hotuna bane, alamar ta kalli Camera d'in yay mata da ido ta juya har zai d'auka kawae tasa dariya ganin taliya a gaban rigarshi a haka ya d'auki hoton kuma yay kyau sosae bayan ya aje wayan yace ko zata idasa sauran Abincin nashi tay mashi wani kallo tace Allah bata yarda ba bashi yace ai yar rigen ba dole shima ya cinye ya jinjina mata kai yaci gaba da ci har ya cinye, bayan ya sha tace lemun fa yace ya bar mata daga haka ya mik'e alamar zai tafi itama ta mik'e suka fito daga falon tare saida taje ta sanar ma gwaggo ta fito sukae sallama sannan suka fita tare, A daidai shagon Amadu ya tsaya yace mata ta koma dare yayi tace to ya juya ya tafi tay tsaye tana kallonshi yayin da sautin busar sarewa na wak'ar india ke tashi bada k'ara ba sosae daga cikin shagon Amadu lokaci guda idanunta suka d'an ciko da kwalla da sauri ta maidasu ta juya ta shige gida. Yana isa part d'inshi wayarshi tay k'ara ya duba mai kiran yaga Hajiya ce bayan yay picking take tambayarshi k'ara fita yay bai shigo yaci Abinci ba yace mata yaje gidansu Zarah ne kuma yaci Abinci acan daga haka sukae ma juna saida safe ya wuce Bedroom bayan ya rage hasken parlon, yana shiga ya aje wayar kan side drawer ya wuce cikin laundry duk da bai jima da yayi wanka ba bayan ya dawo gym saida ya k'ara yin wani saboda Abincin daya zubar mashi a jiki, sanye da bathrobe ya fito yana tsane gashinshi da wani farin short towel ya nufi cikin Bedroom din, shiryawa yay cikin Sleeping dress yasa turare ba mai k'arfi ba don su kansu kayan da ya sa sakin k'amshi suke ya goga roll-on kafin ya nufi wurin switch ya kashe hasken d'akin ya kunna bedside lamp guda daya ya haye gadon yana kallon ceiling lokaci guda zuciyarshi ta fara tariyo mashi abunda ya faru tsakanin shi da Fatuu, Murmushi kawae yake saki yana jin zuciyarshi Fresh can ya kai hannu ya d'aukko wayarshi,hoton da suka yi da ita ya bud'o ya k'ura mata ido yana kallon yadda ta washe baki tayi Dariya dimples d'inta sun lotsa sosae, murmushi kawae yake saki kafin ya maida wayan ya aje ya lumshe ido..................... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2014* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 14 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .......Tana komawa cikin gidan Falo ta nufa anan ta iske gwaggo zaune ta bud'e Akwatunan duka ta rafka uban tagumi tana ta kallon kayan sai kace lefe koda Akwatunan basu da yawa amma kud'in su dana kayan ciki zasuyi na wasu akwatinan lefen da suka fisu yawa itama Fatun tsaye tayi cike da Al'ajabin ganin uban kayan don ba abunda babu na buk'atar mace da ake sakawa a lefe kama daga d'inkakkun kaya da wanda ba'a d'inka ba,Cosmetics Undies takalma da dae sauransu, da alama dae bakin gwaggo ya mutu ta kasa cewa komae sai jinjina kai kawae take can ta kalli Fatun tace ta kama sukai d'akinta tace to ta matsa gwaggon ta tashi suka maida su d'akin nata, sai lokacin bayan gwaggo ta fita ta zauna ta fara dubawa nan take ta fara ayyana ina ma ace lefen aurensu ne a hankali siraran kwalla suka fara gangaro mata k'arshe ma sai ta kife kanta kan kayan ta shiga raira kuka ba mai sauti ba, Washe gari da safe yazo d'aukarta don kaita Makaranta yana yin horn biyu ta fito cikin shiri ta zagaya ta bud'e kopar ta shiga bayan ta rufe kopar ta juya suka had'a ido ya jingina kanshi da headrest, da d'an Murmushi ta gaishe shi ya amsa fuska sake yace "How was ur nyt?" ta bashi amsa da "Alhamdulillah" ya jinjina kai daga haka yaja Motar suka tafi saida suka biya aka d'auki Haulat kaman kullum kafin suka wuce, ba laifi ta d'an saki jiki yau jefi jefi yake mata Magana tana bashi amsa Haulat dae nata bin su da ido acan k'asan ranta tana ayyana Fatuu ta warware ne ko ya akai ta saki jiki haka, bayan ya aje su ya basu kudin break tana Murmushi ta amsa tayi mashi godiya har zai ja Motar ya tsaya ya kirata bayan taje side d'in da yake ya tambayeta karfe nawa zasu tashi ne tace sai yamma yace to zaizo ya daukesu, akan hanyarsu ta zuwa Class ne Haulat ke tambayar Fatun game da warwarewar da taga tayi tace zata fadi mata in sunje aji, saida akai break ne ta bata labarin yadda sukae dashi sosae taji dadi da bata fad'i mashin ba ta kuma yaba da kirkin haisam d'in daya damu da damuwarta har haka ta tayata farincikin kayan data ce ya siya mata saidae bata ji dad'in jin Fatun bazata bikin ba tace mata "amman Fatuu miyasa zaki k'i zuwa bikin Ya Haisam ne fa ni kaina da za'a barni wllh ina son zuwa saidae nasan babanmu bazai barni ba amman ke tunda nasan su gwaggo ma zasu ai da kinje kawae tunda dae kin hakura dashi" "Don na hakura ce maki akae na daina sonshi ne Haulat, har yanzu ba abunda ya canja kawae ba yadda zanyi ne shiyasa gwara ma kar naje naga abunda zai k'ara tarwatsa man Zuciya" ta k'arasa Maganar da damuwa kan fuskarta haulat tace ta fahimceta daga haka bata k'ara ce mata komae ba game da hakan bayan La'asar Haisam ya dawo ya d'aukesu, lokacin daya ajesu ya wuce gida yana zuwa bakin Gate Officer ya tsaidashi bayan ya tsaya ya nufo Motar lokacin ya sauke glass d'in, "Barka da dawowa Yalla6ai" kai ya jinjina mashi yaci gaba "dama kana da bak'o ne" tambayarshi yay ina bakon yake ya nuna mashi can gefe da hannu ya d'an lek'o kanshi ya kalli direction d'in da Officer ke nunawa, wani dattijo ne ya manyanta sosae cikin shiga ta kamala yana tsugunne gaban mashin d'in shi Jincheng yana ganin fuskar Haisam ya mik'e yana kallonshi da d'an Murmushi, maida kan Haisam yay yace ace ya shigo daga haka yaja Motar ya shige, lokacin da Haisam ya fito daga cikin Motar dattijon ya shigo yay mashi alamar ya aje mashin d'in cikin wurin, da sauri ya nufo shi bayan ya parker mashi d'in nashi ya d'an rankwafa yana kokarin gaishe dashi ya mik'a masa hannu suka gaisa kafin yace su shiga ciki yace to saida ya koma ya d'aukko wata leda gari yayi zafi a jikin mashin d'in kafin ya bi bayanshi suka nufi part d'in Haisam, suna shiga ya bi parlon da kallo baki bud'e tunda yake bai ta6a shiga irin falon ba shi ko ganin irinshi ma a tv bai ta6a ba ga ni'imtaccen sanyi had'i da daddadan kamshi da ke kaima hancinshi da sauran sassan jikinshi ziyara, nuna mashi bangaren Armchairs yay alamar ya zauna ya nufi wurin ya zauna a takure, shiru suka yi Haisam bai mashi Magana ba shima haka sai dae faman murmushi yake can ya fara Magana yace "Yalla6ai baka gane ni ba ko?" Kai Haisam ya d'aga mashi alamar eh, "Allah sarki ay dayake lokacin da tsawo sosae, Sunana Malam Garba kuma nine mutumin daka ta6a taimako ka biya masa kud'i a caji Office shekaru kusan ukku da suka shud'e tun lokacin naso nayi maka godiya sosae saidae ban samu halin hakan ba don baka d'aga waya dana rok'i Officer ya kiraka dama saida ya fad'a man bazaka d'aga ba karshe ya nuna man don Allah kai man in gode ma Allah kawae" d'an dakatawa yay Haisam dae nata kallonshi fuskarshi a sake don yanzu ya gane shi, Malam Garban ya d'aura da fad'in "Wato Yalla6ai sanadiyyar taimakon da kayi man na samu bud'i sosae, da yar trader na bud'e ma yarona habu Allah yasa ma abun Albarka yanzu ta Zama k'aton shago Alhamdulillah yanzu ba matsalar Abinci a gidana sannan karatun yara ma ana kamantawa yadda ya dace shi kanshi wanda yay silar zuwana caji Office d'in Allah ya shiryar dashi ya daina d'aukar kayan Mutane yanzu ya natsu sosae suke Kula da shagon ni kuma naci gaba da sana'ata ta faci wadda dama injin d'inne ya lalace na daina sakamakon taimakon kudi da kayi man na canja wani wannan dalilin ne yasa na kasa hakuri don ban manta da abunda kayi man ba saboda ba abune da zan iya manta ba dama Officer ya fad'a man a wurin kakarka kake da zama tun wanccan lokacin hakan yasa ban sha wata wahala ba wurin nemo ka don ita d'in sanannace, a tak'aice dae Yalla6ai Nagode, Nagode Allah Ubangiji ya saka maka da mafificin Alkhairinsa ya dawwamar dakai cikin Farinciki kaman yadda kake saka bayinsa Farinciki, Allah ya jik'an Magabata ya raya maka zuria......" kasa karasawa yay sakamakon muryarshi da ta karye idanunshi suka cicciko da kwalla", Sigh Haisam yay Calmly yace "ai ba wani abu bane ka d'auka rabonka ne a hannuna ba sai ka damu ba" yar dariya yayi yana kokarin mayar da k'wallan yace "duk da hakan ai ance yaba kyauta tukuici, ko don dakon rabon da kayi ai na gode maka" d'an murmushi Haisam yay baidae cemashi komae ba can ya mik'e ya nufi Fridge ya d'aukko lemu da glass cup ya dawo saida ya d'aukko c-table bayan ya tsiyaya ya aje mashi yace bismilla ya sha yay godiya kafin ya daukka ya fara kur6a, bayan yasha kaman rabi ya ajiye ya kai hannu gefenshi ya d'ago da ledar daya zo da ita yace "yalla6ai wannan daga cikin kayan shagonne su Omo, Sabulu Tolen paper (toilet paper) da dae sauransu na kawo a ba iyali" still da murmushi kan face d'inshi yace "Ok angode sai dae a kaima Hajiya" "Af,af d'ana ba dae ba iyalin ba?" ya tambaya da d'an mamaki shiru kaman bazai yi Magana ba sai kuma yace "Yea but Next week ne zanyi auren" ruke ha6a yay yace "iko sai Allah kace da sati mai zuwan nazu dana taras ana tsaka da hidima kenan", "Ba anan ne za'ai ba Abuja ne" idon Malam Garba a kanshi yace "Allah sarki Allah ubangiji ya kaimu ya nuna mana, aikuwa yakamata nima inje d'aurin auren nan" "No, ba sai kayi hakan ba" ya bashi amsa a takaice yace "d'ana ba dae baka son naje d'aurin auren naka ba" da sauri yace mashi a'a kawae basai ya takura kanshi ba in yayi mashi Addu'a ya isa yay yar dariya yace" shikenan tunda kace hakan amma wllh ba wata takura ai Alhamdulillah Allah ya bud'a, Addu'a kuma kullum cikin yi ake wllh ba zancen ganin idonka ba aduk sallar da zanyi ta Farilla kota Nafila kana cikin Addu'oi na ko bama a salla ba" sosae Haisam yaji dad'in Maganar yace mashi ya gode, Shiru suka d'anyi can Malam Garban yace "Yalla6ai bari in barka ka huta ka dawo aiki kuma na rik'e ka, saidae in ba damuwa ina son in gaisa da hajiyar taka,amsa mashi yay da Owk ya kai hannu gefenshi ya d'auki wayar shi yay Sending call, Tk ya kira saida ya tambayeshi yana gida yace mashi eh yace yazo part d'in nashi, bada jimawa ba sai gashi ya shigo da sallama ya gaida Haisam kafin ya juya ya gaida bak'on umarnin kaishi wurin Hajiya ya bashi yace to Malam Garban ya mik'e bayan ya dau ledan yace bari akai ma Hajiyan Haisam ya d'aga mashi kai, saida ya tsaya bakin kopa ya k'ara mashi godiya da Addu'oi sannan ya fita,suna fita Haisam din ya kira Hajiya tunkan tay mashi Maganar ya baizo yaci Abinci ba as usual ya rigata fad'in ga bak'o nan Tk zai kawo daga haka ya katse kiran ya mik'e ya nufi hanyar Bedroom. Lokacin da suka shiga parlon Hajiyar na zaune kan 2 seater idanunta sanye cikin glasses ta juyo tana amsa masu sallamar da suka yi Tk ya nufeta yace ga bak'o nan inji Ya Haisam ta jinjina mashi kai ya juya ya fita ta maida idonta kan Malam Garba da yay tsaye tace "ka zauna mana kayi tsaye" fuskarshi d'auke da faffad'an murmushi ya amsa mata ya nufi one seater ya zauna Matar da yake gani a talabijin ko yajita a Radio yau gashi gata ba k'aramin dad'i ya ji ba,bayan ya zaunan ya d'an sunkuya yana gaishe da ita ta amsa fuskarta a sake shiru ya biyo baya can yaji tace "to bak'o daga ina don ban wayeka ba" tay Maganar tayi mashi k'uri ta cikin gilashin, gyara zama yay ya fara mata bayanin kanshi da abunda ya had'a shi da Haisam, "Allah sarki da yake bamu ta6a ma yin Maganar dashi ba tunda ba fad'in abu yake ba in yayi" jinjina kai yay yace "Allah Akbar kaji mai yi don Allah, Allah ya saka da mafificin Alkhairinsa ya k'ara sutura" Hajiya ta amsa da Amin tana murmushi tace "ai Malam Garba da baka wahalar da kanka ba ma" da sauri yace "wllh Hajiya taimakon da yay man ne ya tsaya man a raina har mafarkinshi nike in ban zo nayi mashi godiyar ba bazan samu natsuwa ba" yar dariya hajiyar tayi ya fara bata labarin irin bud'in d'aya samu sanadiyyar taimakon da Haisam d'in yayi mashi tana ta fad'in Allah sarki an gode ma Allah, can ya mik'e ya kai ledar kayan gabanta yace ga irin kayan shagonne ayi amfani dasu ta kai idonta kan ledar tana fad'in harda hidima haka to an gode, komawa yay ya zauna yayi mata zancen bikin Haisam daya fad'i mashi tace eh in Allah ya kaimu juma'a mai zuwa ne da tun satin daya wuce ma zasu tafi to wai akwae uzurorin da bai kammala dasu bane saboda ba zai dawo nan ba to yanzu sai in Allah ya kaimu jibi zasu tafi yace ashe da rabon zai iskesu tace aikuwa, kokarin mik'ewa ya fara zai tafi da sauri Hajiyar tace "Malam Garba ya zaka tafi ko ruwa baka sha ba mun tsaya munata Magana bansa an kawo maka ba ka zauna sai ka sha ruwan zumunci tukunna, komawar yayi don bai iya yi mata gardama a ranshi kuwa yanata jinjina kirkinta yadda ta sake mashi sai kace dama sun san juna, Saude ta kwala ma kira tun kafin tazo cikin falon ta bata Umarnin kawo mashi ruwa da Abinci ta juya kitchen, bada jimawa ba ta kawo kayan Abincin cikin babban tray saida ta kinkimo sofa table ta kawo gabanshi sannan ta d'aura tray d'in tay Serving nashi bayan ta gaishe shi tace aci Lafiya yay mata godiya Hajiya ma ta mik'e tana fad'in bari ta bashi wuri ya samu sakewa ya tabbatar ya ci ya koshi ya amsa mata da to yana dariya, sosae yaji dad'in Abincin don Saude badae iya Abinci ba Musamman farfesunta in Mutum nasha kamar ya cinye da hannunshi don dad'i da wannan ta siye hajiya, bayan ya gama Saude taje ta sanar ma Hajiya ta fito don suyi sallama ta bashi kud'i tace ya sha mai yay mata godiya gami da Addu'oi ya tafi, Malam Garba bai tashi shan mamaki ba saida ya je parking space don d'aukar Mashin d'inshi nan ya iske Tk ya kawo mashi kwalin taliya da Macaroni harda yar galan d'in mai baki bud'e ya bi kayan da kallo kafin ya sauke idanun kan Tk dake ta washe mashi baki tun kafin yace wani abu ya riga shi fad'in Hajiya ce tace a kawo mashi kawae sai yasa ma Tk kuka yana fad'in wad'annan wane irin Mutane ne haka dama har yanzu ana samun Mutane masu tsananin kirki haka Tk yace "Wllh haka suke ni kaina nan daga Almajiri aka mayar dani d'an gida ba abunda ba'ai man wanda ake ma d'a Abinci,Sutura,Karatu da dai sauransu har iyayena ma ba'a barsu ba" waro ido Malam Garba yay jin wai shi Almajiri ne wanda ba kama ba alama ba don shi ya fad'a ba ma ba lalle ya yarda ba, cewa yay bari yaje ya k'ara yi mata godiya Tk yace ba sai yayi hakan ba ya tafi kawae su bama su cika son yawan godiya ba nan take ya tuna zancen SP acan baya hakan yasa ya hau mashin d'in Tk ya taimaka mashi ya d'aura komae har zai tafi ya dakata yace ma Tk don Allah in ba damuwa ya bashi lambar wayar Haisam yaji aurenshi ya kusa yana son in an dauran ya kira yay mashi fatan Alkhairi ya kasa tambayarshi ne d'azun yace Ok ya amshi yar wayarshi yay mashi saving lambar kafin ya mik'a mashi yanata shi mashi Albarka yaja mashin d'inshi ya tafi Farinciki fal cikin ranshi.(Allah ka had'a mu da Mutane irinsu Hajiyar Sanata ka bamu ikon sanya Farinciki a zukatan junanmu Amin) Sanye cikin gym outfit ya fito daga cikin d'ayan d'akin hannunshi guda rataye da k'atuwar Sport Bag d'inshi yana fitowa daga cikin Corridor ya d'an bud'a idanu alamar mamaki idonshi akan bakin kopar shigowa, Fatuu ce a tsaye jikinta sanye da Uniform d'in islamiyya ya nufi wurin da murmushi don yaji dad'in ganinta hakan ya tabbatar mashi da ta warware itama d'an Murmushin take mashi yace islamiyya zata ta d'aga mashi kai ya nuna mata kujera taje ta zauna, mikewa yay ya aje jakar a gefe kafin ya nufi Fridge ta bi shi da kallo babbar robar lemu Fanta ya d'aukko ya dawo ya zauna kan hannun Sofa inda ya tashi ya mik'a mata ta kalleshi ya d'an d'age gira ya furta "u'r my guest now" tana murmushi ta amsa tace ta gode shiru ta d'an biyo baya ta sunkuyar da kanta tana wasa da hannun jakarta can ta d'ago taga ita yake kallo motsa baki ta fara a sanyaye tace "dama nazo in yi maka godiyar kaya tunda safe naso yi maka,Nagode sosae Allah ya saka maka da Alkhairi ya k'ara Arziki mai Amfani" d'an bud'a ido yay with a broad smile on his face da kaji yadda take Maganar cikin hankali zaka fahimci ta girma ba kaman da ba, cikin cool voice nashi yace "Ameen don kin cinye ma Amarya kud'in cin kayan dad'inta su kaza da kika ce ana ci" waro ido tay tana mashi wani kallo yasa dariya tana ganin hakan ta tura mashi baki sai kuma itama tayi yar dariyar, mik'ewa yay yace suje yayi dropping nata kar tay late tace to bayan ta saka lemun daya bata cikin jaka tabi bayan shi, lokacin da suka isa Parking space d'in duk a tunaninta Mota zasu hau amman sai taga ya fiddo bike bayan ya hau ya d'aura jakar a gabanshi yace mata ta hau amman sai tayi tsaye hakanan taji yanzu bata son hawan don tasan dole jikinsu ya hadu shi kanshi tasan ba so yake ba kawae don ya faranta mata ne, juyowa yay ya kalleta yace ta hau mana ta d'an yamutsa fuska tace ita tsoro take ji yace kada ta damu ba abunda zai faru ba gudu zai yi ba, ba yadda ta iya haka ta daddage ta hau tabi ta daddafe jikin mashin d'in yaja suka tafi, gaba d'aya a tsorace take don sai taga tayi sama sosae shi kanshi yaji a takure take hakan yasa yace ta rike shi da sauri ta kai hannu ta kama gefe da gefen rigarshi gadagam har saida ya d'anyi dariya don ya gama fahimtarta abunda bai kai ya kawo ba shike bata tsoro bata tsoron babban abu, a gefen gate d'in islamiyyar ya parker duk ba dalibai da alama duk an gama zuwa, kokarin sauka ta fara yi kwatsam ta tafi gaba d'aya zata kifa cikin zafin nama ya damkota ta dawo sama ta matuk'ar tsorata sai numfashi take fitarwa da sauri da sauri lips d'inta na d'an motsi haka idanunta ta rufe su gam ga dogayen eyelashes d'inta sai rawa suke sakamakon idonta dake kyerma still yay yana k'are mata kallo tunda yake da ita bai ta6a samun closeness da ita ba haka da har zai kalleta tsaf ba, ba komae yafi d'auke mashi hankali ba irin gashin idonta dake rawa sai kace irin d'iyar roba da ake saka ma batir, jin ta d'an samu natsuwa yasa ta fara bud'e idanun a hankali kafin ta ware su sosae har saida ta d'an tsorata da ganin fuskarshi kusa ganin ya k'ura mata ido yasa duk taji wani iri a hankali tace zata sauka don har lokacin yana ruke da damtsenta sigh yay kafin yace "am so sorry for dat" kai kawae ta d'aga mashi ya taimaka mata ta sauka ta nufi cikin Makarantar, yana kokarin tashin bike d'in ya tafi kawae sai ganinta yay ta lek'o karaf suka had'a ido tasa dariya ta juya da sauri ta koma shima dariyar yake a fili ya furta "U'r too much Zaraah" daga haka yaja ya tafi. Washe gari Alhamis bayan ya aje su Makaranta tana kokarin fita ya tsaidata ya tambayeta yau ma sai yamma zasu koma tace eh, ganin ya d'an yi Jim yasa ta tambayi ko akwae wani abu yace da yana son zasu fita ne da rana,itama shirun tayi sai kuma tace to sai ta koma da an tashi ba sai ta tsaya lesson ba yace ba matsala tace eh ai dama past question papers ne ake fidda masu kuma duk ta iya yace Ok zai dawo lokacin tashin ya dauketa tace to, gaba d'aya sukuku take koda taje aji sam hankalinta bai a tare da ita sanin gobe ne Haisam d'in zai tafi ji take kaman ta bishi amman tasan tabbas hakan matsala zai k'ara zame mata gwara ta hak'ura kawae, ana tashi k'arfe biyu saura sai gashi ya zo d'aukartata Haulat ma tace binsu zatai ta tafi gida aka tafi da ita, bayan ya sauke Fatun tana shirin fita taji yace kada taci Abinci sosae yasan ita acici ce zasu ci in sun fita tayi yar dariya kawae ta fice shima murmushi yake ya nufi gida, tana shiga d'akin gwaggo ta nufa lokacin gwaggon na kwance tana bacci bata dad'e da ta kwanta ba bayan tayi sallar Azahar hakan yasa Fatun na shiga ta bud'e ido tace mata har sun dawo da wuri haka saida ta gaidata sannan ta sanar mata da zancen fitar da zasu yi tace to tay sauri taje ta shirya ta amsa da to ta fita, ko Abincin ma bata ci ba ta hau shiri ba tare da 6ata lokaci ba ta gama shiryawa cikin k'ananan kaya riga da skirt kayan roba ne hakan yasa suka kamata sosae shape d'inta ya fita sai ta d'aura After dress tay rolling veil d'in ta fiddo takalma masu tudu ta sa ba k'aramin kyau tay ba don ma kumatunta sun d'an fad'a, tana gamawa bada jimawa ba ta jiyo horn d'in shi saida ta lek'a don yima gwaggo sallama ta iske tay nisa a baccinta hakan yasa ta tafi kawae, zagayawa tay d'ayan side d'in Motar ta bud'e kopar ta shiga wani fitinannan kamshi mai tsuma zuciya ne ya bugi hancinta har saida ta d'an lumshe ido tana kokarin rufe kopar, juyawa tay suka had'a ido ta gaishe shi yay nodding kai tana shirin juya fuskarta ta kalli gaban Motar kaman daga sama taji ya furta "Kinyi kyau sosae" da sauri ta kalleshi with surprise ol over her face don bata tsammaci jin hakan ba saboda tunda suke da ita bai ta6a ce mata hakan ba ko a da saidae in ita ta tambayeshi tayi kyau in tayi gayu sannan yace eh ko in tasa kayan daya siya mata ta nuna mashi sai yace sun mata kyau, ganin ta k'ura mashi ido yasashi d'age mata gira yace "What?" da sauri ta girgiza mashi kai ta juyar da kanta yaja Motar suka tafi acikin ranta ta fara tunanin yadda yake mata abubuwa wanda bai saba yi mata ba can zuciyarta ta ayyana mata don ya sakata Farinciki ne kawae, ta juyar da fuskarta gefe tana kyakkyafta idanu don ta mayar da kwallan dake kokarin taruwa.......... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2015* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 15 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........Wani babban Eatery mai kyau da tsari ya nufa dasu bayan ya parker Motar a wurin da aka tanada don haka a tare suka fito suka nufi ciki Masha Allah ya dae tsaru Fatuu sai d'an bin wurin take da kallo ta yadda baza'a ga k'auyancinta ba, wuri ya nuna mata suka zauna suna facing juna suna zama sai ga waitress tazo tana sanye da Uniform d'in wurin bak'in skirt sai riga milk tasa yar himar bak'a dama ma'akaitan wurin Mata da Maza ne, Haisam ta nufa cike da salo tace "Barka da zuwa Yalla6ai" ba tare da ya kalleta ba ya d'aga mata kai Fatuu ta zuba mata ido tana kallon ikon Allah don sai faman rausaye rausaye take, Menu ta mik'a mashi mai d'auke da lists d'in dishes dake garesu bai amsa ba yace ta kawo mashi Fried rice d'an d'aga gira tay jin yadda yake Magana tace "with Beef or chicken yalla6ai" chicken ya bata amsa a tak'aice sai kuma ta k'ara kanne murya tace "to yalla6ai itafa mi za'a kawo mata?" Shiru yay mata jin wata tambaya mara kan gado gata ba sai ta tambayeta ba Fatuu kam har saida tay kaman zatai murmushi cikin ranta take ayyana kyama yi ki gama, har saida ta k'ara tambayarshi sannan idonshi akan waya yay mata nuni da Fatun yace "ask her" d'an ta6e baki tay ta nufi Fatun suka had'a ido tana kokarin bata menu d'in itama tace ta kawo mata babban robar ice cream da shawarma tace Ok ta juya Haisam yay ma Fatun kallon k'asan ido ya furta "Wannan ne zai isheki?" Yar dariya kawae tay bata ce mashi komae ba, bada jimawa ba waitress d'in ta dawo d'auke da k'aton tray wurin Haisam ta fara zuwa ta aje mashi nashi kafin ta nufi fatuu, tana niyyar tafiya Haisam ya tsaidata ta kalleshi sai lokacin suka had'a ido dashi yace ta kawo mashi pepper chicken da soft drink sai ruwa cikin kashe murya ta tambayeshi kaman ya complete chicken ko half yace complete ta d'an juya ido ta furta Ok kafin ta tafi, har ta kawo mashi bai fara cin fried rice d'in ba bayan ta aje mashi tace aci lafiya ta juya Fatuu ta d'an ta6e baki tabita da ido, tana juyowa taga ya turo pepper chicken d'in gabanta ta kalli kazar sai kuma ta kalleshi taga yana sakin wani Murmushin gefe nan take ta gane mi hakan ke nufi dama tasan tunda tay Maganar kaza yace ko tana son ci ne tabbas sai ya siya mata, tura mashi baki tay yay mata alamar ta fara ci shima ya fara cin nashi a nutse, ita kuwa Waitress d'in wuri ta samu can gaba ta zauna ta fiddo wayarta tana lallatsawa can wata ma'aikaciyar ta shigo d'auke da tray ta kai ma wasu bayan ta aje masu ta juya da tray d'in anan ta hango d'ayar zaune ta nufi inda take tana zuwa ta dafa shoulder d'inta tace "Su Billy manya shine kika bar aiki kika zo nan kikai zaune ko" wani d'an iskan kallo tay mata tana d'an Murmushi tace "zaman dole nike zuciya ce taga abunda take so" bud'a ido tay jin abunda billyn tace sai kuma ta juya tana k'are ma wurin kallo nan take idanunta suka sauka kan su Fatuu, "Kice bak'in Farar fata mukae,to ke burgeki sukae kenan shiyasa kikai zaune kina k'are masu kallo"? d'an juya ido Billy tayi tace "ya dae burgeni" da sauri d'ayar tace "yau naga ikon Allah daga ganin Mutum kuma kika sani ma wadda yazo da ita ko matarshi ce ko kuma budurwarshi" d'an ta6e baki Billy tai tace "I don't care ni dae yayi man ne baki ji dad'in voice d'inshi ba wllh, kuma ma ni ban tunanin wai ko matarshi ce ko budurwarshi nafi tunanin kanwarshi ce ma" d'ayar tace "kanwarshi kuma,haka kawae sai ya d'aukko kanwarshi ya zo da ita nan cin Abinci ko ba wani abu bane hakan ai nasan dae ba ita kadae ce kanwarshi ba", "Ke baki san in kud'i sukae ma Mutum yawa ba komae yi yake, ba kamar su daga gani ba cikakkun hausawa bane nafi tunanin half caste ne kuma ai zai iya yuwuwa yafi ji da ita ne acikin k'annan nashi" ta6e baki d'ayar tayi tace "lallai aiki ya sameki to, ki tashi kici gaba da aiki ko inje in kai k'ararki" ta k'arasa Maganar tana kokarin tafiya billyn tay dariya tace "ai na gama da kowa ba abunda zanyi" gyad'a kai tay tayi gaba abunta ita kuma billyn taci gaba da lallatsa wayan tana satar kallon yadda Haisam yake cin Abincinshi a nutse bai ma san tana yi ba, Fatuu na cikin shan ice cream idonta akan tv tana kallon maimaicin shirin dadin kowa da aka fara yi a tashar Arewa 24 hankalinta ya tafi har bata san sadda robar ice cream d'in ta kubce mata ba gaba d'aya ya zube akan after dress d'inta duk ta 6aci dashi da sauri ta mik'e tana d'an yarfa hannu idon Haisam a kanta suka had'a ido dashi ta d'an yamutsa fuska d'an ta6e baki yay tace mashi yanzu ya zatayi ya d'age gira yace "ni nasa ki sake shi" d'an tura baki tay kaman zatai kuka ya bita da ido yana d'an murmushi, duk abunda ke faruwa akan idon billy hakan yasa ta taso ta nufo su tana zuwa cikin kashe murya tace "Subhanallahi 6are maki yay ne?" Kai Fatuu ta d'aga mata tace bari ta taimaka mata ta ciro rigar Fatun tace to, ta kai hannu ta cire Billyn ta kar6a ta juya, duk sai kuma Fatun tajita wani iri da ba rigar don kayan ba k'aramin tighting nata sukae ba hakan yasa tay tunanin tabi bayan billyn in an wanke sai tasa, fita tay daga cikin seat d'in ta nufi hanyar data ga billyn tayi Haisam yabi bayanta da kallo, tunda suke bai ta6a kafeta da ido ya k'are mata kallo irin haka ba bare har ya fahimci yadda jikinta yake ya dae san ba ramamma bace kuma yana jin ana Magana kan structure d'inta kaman can baya lokacin da Najeeb yay Magana kan hakan, dressing d'in ba karamin fiddo mata da shape yay ba don har shatin undies nata ana gani kasantuwar kayan roba ne, a hankali ya d'an juya lokaci guda yay noticing gaba d'aya hankalin mutanen dake wurin ya koma kanta maida idon yay a kanta har takai tsakiyar wurin don kayan basu barinta sauri a hankali take tafiya d'an d'aga murya yay yace "ZARAAH" dakatawa tay lokacin da kiran ya sauka cikin kunnanta Slowly ta juyo ta kalleshi don tasan shine ya kirata da kai yay mata alamar tazo ta juyo ta nufo shi idanunshi a kanta har ta k'arasa kafin tace wani abu yace "Sit and wait for her zata kawo maki ne" d'aga mashi kai tay don dama da tana tafiyar ta lura da yadda ake kallonta alama yay mata taci kazar a shagwa6e tace ai tayi mata yawa yace taci wanda zata iya, "To kai bazaka ci ba" ta tambayeshi, shiru ya d'anyi sai kuma taji yace taci in ta rage zaici bud'a ido tay tace "ba baka cin saura ba?" Yar harara ya wurga mata tasa dariya ta kai hannu ta fara ci, can saiga billy ta dawo maimakon ta nufi Fatuu sai ta nufi Haisam cikin salo tace "amm Yalla6ai na wanke rigan tana can na shanya under fan don ta bushe da wuri in zaku tafi sai ayi man Magana in d'aukko mata" Slowly ya d'ago da fararen idanunshi tar masu d'auke da bakar kwaya mai baki sosae ya d'aura a kanta har saida taji fad'uwar gaba fuska a sake ya furta mata "thanks" wani far tay da ido ta washe baki tace "u'r welcome" daga haka ya maida idon yana cigaba da cin Abincinshi tay tsaye tak'i tafiya tana kallon sumar kanshi dake ta kyalli tasha gyara duk abun nan idon Fatuu na kanta ta gama kasheta da mamaki kasa jurewa tay tace "kar ki sa ya kware fa" kaman daga sama billy taji Maganar hakan yasa ta juya da sauri ta kalli Fatuu dake kallonta fuskarta ba yabo ba fallasa cikin dabarbarcewa billyn tace "a....am ina jira ya gama ne in d'auke kayan kar nayi tafiya biyu ba wani abu ba" wani kallo Fatun tayi mata cike da rainin Wayo tace "ba zaki kawo rigan ba ai sai ki d'auka lokacin ko" da sauri tace hakane ta manta ne ta juya cike da jin kunya ta tafi, kallon k'asan ido yay mata ta tura mashi baki yay d'an murmushi kawae bai ce mata komae ba, bai cinye fried rice d'in ba Fatuu ta mik'o mashi pepper chicken d'in ya d'an ci kadan daga haka ya yagi tissue ya fara goge hannu da baki tana ganin haka itama ta yaga ta goge tana kokarin mik'ewa taje ta amso rigar yace ta zauna ya mik'e ya nufi cikin wurin don kunya tasa billy ta bar wurin a can daga ciki ya ganta yace ta d'aukko rigar ta amsa da Ok ya juya ya koma bada jimawa ba sai gata tana wani shan k'amshi ta mik'a ma Fatuu rigar da d'an murmushi tace mata ta gode ba tare data kalleta ba tace ba damuwa ta juya taba Haisam bill d'in abunda suka ci ya fiddo Wallet ya biya yay mata kyautar dubu biyar tana Murmushi tace ta gode ya d'aga mata kai kawae ya tashi Fatuu ma ta fito bayan ta saka rigar tana zuwa saitin billy dake tattara kayan da suka yi amfani dasu ta tsaya tace "kiyi Hakuri in kinji haushi na sati mai zuwa ne d'aurin Aurenshi ban so ki wahalar da kanki ne" daga haka tay gaba abunta Billyn ta bita da ido baki bud'e acikin ranta ta fara ayyana to ko Fatun ce zai aura. Suna barin wurin Zoo and park ya wuce da ita bayan ya yankan Masu ticket suka shiga, wurin namun daji su zaki, giwa da dai sauranau suka fara zuwa suna kallo cike da nishadi daga baya suka koma wurin liluna ganin tayi tsaye tana murmushi yasa yace taje ta hau wanda take so amman sai cewa tay ita kunya take ji har saida ya d'an bud'a ido alamar mamakin yau Zaraah ce da kunyar hawa lilo, ganin ta toge yasa yace suje su hau tare cike da mamaki ta bishi ya biya masu irin mai juyawa suka hau suna facing juna sai faman dariya take shidae murmushi kawae yake yayinda Mutane keta bin su dana mujiya don a zaton mafi akasari ba hausawa bane, daga baya suka sauka ta hau swing ya d'an rinka turata can kuma ya k'yaleta taci gaba da yin abunta yaja gefe yana kallon yadda take yin sama tana dawowa, sosae Fatuu ta samu nishad'i anan yay sallar la'asar a Masallacin wurin sai wuraren k'arfe biyar saura sannan yace mata su tafi gidan Abbas bayan sun fito yace suyi ma Abdul shopping a Supermarket d'in wurin, leda biyu sukae yace d'aya tata ce tay mashi godiya kafin suka wuce, suna kan hanya ya kira Abbas d'in ya tambayi yana gida yace mashi a'a yana kan hanyarshi dae ta komawa daga Jami'a yace Ok su had'e yana kan hanya shi da Zaraah, suna dab da shiga gate d'in Estate d'in shima Abbas ya iso suka shiga tare a bakin gate duk suka tsaya Abbas ya fito ya bud'e masu gate d'in suka shiga shima ya koma Mota ya shiga, bayan duk sun parker Motocin suna fitowa Abbas ya nufeshi yana fad'in "the latest Ango" shidae murmushi kawae yake ya bashi hannu sukai shaking kafin ya maida idon kan Fatuu yace "Mom Zarah barka da zuwa" da d'an murmushi tace mashi yauwa yace "kin rako ango zaga garin bankwana kenan" shiru tay still da murmushi akan fuskar Abbas yace su shiga suna shirin juyawa sai ga Abdul ya fito da gudu ya nufi Fatuu ta rungumeshi yana ta dariyar Farinciki itama dariyar take mashi ta d'agoshi Haisam yace ta d'aukko abunshi tace to ta bud'e back door ta fiddo ledan kayan kwalama da suka siyo mashi ta mik'a mashi ya amsa yace nashi ne tace eh cike da murna yace "thank u so much Aunty Zarah I love u" gaba d'aya suka sa dariya Abbas na fad'in ba dole kasota ba tunda ta kawo maka abu da sauri yace "No Daddy wllh ba saboda su bane ina sonta tana da kirki kuma tana da kyau" murmushi duk suka yi Abbas yace "yau da alama Mom Zarah ta tafi da hankalinka shiyasa ko ta baban naka bakayi ba balle ka gaidashi ko" da sauri ya nufi Haisam yana fad'in "Good Evening Baba Zakee Ango" gaba d'aya suka sa dariya daga haka suka nufi ciki hannun Abdul cikin na Haisam, cike da Farinciki Feenah ta tarbi Fatuu don sun kwana biyu basu had'u ba bayan sun gaisa tace bari ta shirya table dama Abbas d'in bai ci Abincin rana ba shima tana shirin mik'ewa Haisam yace mata a koshe yake tace ma Fatuu ai ita zata ci ko tace mata a'a itama a koshe take ganin yamma ne tasan dole sunci Abinci yasa ta k'yalesu Abbas ma yace ba yanzu zai ci ba, d'aki Abdul yaja Fatuu wai suje suyi game su ci kayan dad'in data kawo mashi Feenah ma tace baza'a barta ba da ita za'a ci tabi su Abbas na dariya yana fadin da girmanta zata cinye ma yaro abu, bayan barinsu parlon hirar tafiyarsu Haisam d'in gobe suka shiga yi can ya tambayeshi yadda akai suka koma Normal da Mom Zarah anan ya bashi labari yace ba abunda yake tunani bane kawae ta damu da tafiyar da zaiyi ne don basu ta6a hirar Aurenshi da ita ba so abunne yazo mata unexpected kuma gashi bazata je bikin ba, da mamaki Abbas ya tambayi dalili yace mashi zasu fara final Exams ne Next week d'in, shiru Abbas yay kaman mai tunanin wani abu lokaci guda ya tuna da ba Next week ake fara Waec ba sai Upper week wato sati na sama nan take ya fahimci Fatun k'arya tay ma Haisam hakan kuma ya tabbatar mashi da zarginshi akanta duk da ba zargi bane duk alamu sun tabbatar da son Haisam take kawae shima don bai da experience kan hakan yasa yak'i fahimta shiru yay kawae bai ce komai game da hakan ba sai da sukayi Magrib sannan sukae masu sallama suka rako su gaba d'aya har bakin Mota anan Feenah ke ce ma Fatuu "Mom Zaraah sai mun had'e Abuja ko" Abbas yay saurin cewa "Mom Zaraah bazata samu zuwa ba don lokacin sun fara Waec" kallonshi fatuu tay suka had'a ido ya saki wani murmushi da yake akwae haske sosae sam Feenah bata ji dad'in hakan ba haka ma Abdul daga haka suka shige Mota Abbas nace ma Haisam sai sun had'e goben suka tafi bayan ya bud'e masu gate, akan hanyarsu ne yake ce mata zadae ta raka shi Airport gobe ko tunda da yamma zai tafi har saida gabanta yay wata kalan bugawa kafin da k'yar tace mashi eh ai bazata ma je Makarantar ba ta fad'i mashi hakan ne don kar yama zo daukarta, tambayarta yay dalili tace mashi ba komae kawae shiru yay bai ce komae ba har suka iso gidan ba wanda ya k'ara tankawa, jiki a mace tace mashi ta gode ya jinjina mata kai kafin yace ta d'auki ledan baya tace to, bayan ta d'auka ta nufi gida ko juyowa batayi ba ya bita da ido har ta shige ya lura da canjawar da tayi nan take zuciyarshi ta ayyana mashi saboda zancen tafiya da yayi mata ne d'age kanshi yay a fili ya furta "I too gonna miss u Zaraah" iska ya d'an fesar ya d'ago ya kai hannu ya ja Motar. Next Day........ Bayan sallar juma'a misalin k'arfe 3:30 sun gama shirin tafiya tsab Hajiya tasha adon lifaya haka ma Saude tana sanye da doguwar rigar Atamfa da babban gyale don da ita za'a tafi Tk kuma zai tafi garinsu ne gobe daga can zai tafi tare da iyayenshi, gaba d'aya Tk ya gama fita da kayayyakinsu yasa acikin Mota, lokacin da suka k'araso parking space Gwaggo ta shigo cikin gidan tana ta sauri ta nufesu tana fad'in ayi Hakuri ta taushe hannu don ta sanar da Hajiyar zata raka su dama suna haka sai ga Haisam da Abbas sun fito daga part d'inshi sun nufo parking space din Haisam na sanye da wani d'anyen bak'in voile haka hular kanshi da takalman kafafunshi da agogon hannunshi suma duk bak'ak'e ne wato shigar complete black yay just Ma sha Allah, suna isa Abbas ya gaishe da Hajiya don bai shiga wurinta ba sannan ya gaishe da gwaggo tanata fara'a ta amsa Haisam ma ya gaishe da ita har zai bud'e Mota sai kuma ya dakata ya kalli gwaggo yace "Zaraah fa?" shiru ta d'anyi Hajiya tace "wllh nima inata son in tambayeta nasan dae yau ba islamiyya ai", ganin duk ita suke jira tayi Magana yasa tace "d'ana Haisam kar ka damu mu tafi kawae" jimm yay haka Abbas ma Hajiya tace "wani abu Dije, ina Fateemar take?" Da yar damuwa tace "tana can tun jiya da daddare take abu guda yau ko Makaranta bata je ba sai aikin kuka ba irin lallashinta da ban yi ba amman a banza tunda ba jin Magana take ba" yar dariya Hajiya tayi sai kuma ta d'an girgiza kai tace "Allah sarki kinsan yadda sabo yake dole ta shiga damuwa Yayanta Handsome zai tafi gashi ba samun zuwa bikin zatai ba ko ni banji dad'in hakan ba itace ya kamata ace k'irjin bikin" gwaggo tace "to amman ai saitai hak'uri tunda kukan ba canja komae zaiyi ba kuma don an tafi ai ba shikenan an rabu ba ko" gyad'a kai Hajiya tayi tace suje kawae duk suka shiga Jeep d'inta Tk na niyyar shiga wurin driver don ya jasu Haisam ya tsaidashi yace ma Abbas ya kaisu shi zai taho tare da Tk d'in ya d'aga mashi kai da murmushi kan fuskarshi ya shiga mazaunin driver ya tashi Motar suka tafi, kallon Tk yay yace ya shiga shi kuma ya zagaya ya bud'e mazaunin driver d'in ya shiga daga haka yaja Motar Suka tunkari gate Officer na mashi Allah ya tsare sai ya zo suka wuce, A daidai gidan su Fatuu ya taka burki yace ma Tk yana zuwa,bud'e motar yay ya fita ya maida kopar ta rufe ya nufi cikin gidan................ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** *ASM Bk2016* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 16 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *This page is dedicated to Hajiya Kubra (Mommy) Allah ya k'ara girma da daukaka da nisan kwana Amin🤲🥰* *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........Yana shiga gidan Parlor ya nufa ganin ba kowa yasa ya wuce direct d'akinta tun kafin ma ya shiga ya jiyo shesshekar kukanta ya kai hannu ya d'aga labulen,tana zaune a k'arshen gado ta had'e kai da gwuiwa ga gashinta duk ya tarwatse, har ya shigo ya tsaya a tsakiyar d'akin yana kallonta bata sani ba goya hannuwan shi yay a k'irji idonshi akanta yama rasa mi zaice mata, a hankali k'amshin turaren shi ya fara kurd'ad'awa yana kai ma hancinta ziyara tun tana jinshi sama sama har ya cika mata hancin ta tabbatar k'amshin Ya Haisam ne hakan yasa ta d'ago a zabure idanunta suka sauka akanshi, zare ido tay tana kallonshi da idanuwanta da suka canja kala sunyi jawur gashi sun kankance sosae tsabar kuka duk a tunaninta sun ma tafi, lokaci guda ta kama kanta ganin kallon da yake mata ta fara jan jiki tana matsowa ta zo bakin gadon cikin hard'ewar murya tace "Y..ya ha.i..sam" shiru bai amsa ba yana cigaba da kallonta sai yan kame kame take tana kallonshi can yay sigh da wata irin murya yace "is this the Promise u ave made to me Zaraah" girgiza mashi kai tay tana yamutsa fuska kaman zata sa kuka, "Why, why all dis Zaraah kina son in tafi da damuwa ne?" tun kafin ya rufe baki tafara girgiza mashi kai ganin yadda yake Maganar da damuwa kwance akan fuskarshi shiru yay yana kallonta cikin muryar kuka ta fara fad'in "Don Allah kayi hakuri Ya Haisam wllh kukan ne yake zuwa da kanshi nayi nayi ya daina yak'i" ta k'arasa tana had'iye kukan wani irin tausayinta ne ya kamashi slowly yay moving zuwa gaban gadon ya samu wuri can gefenta ya zauna da sauri ta sunkuyar da kanta don duk kamshin turaren shi ya cika hancinta shiru ya d'anyi yana kallonta can yafara Magana Slowly "am so sorry Zaraah I caused u pain am sorry" ya k'arasa da breaking voice ya d'an cije baki d'agowa tay ta kalleshi hawaye na sauka daga idonta da sauri ya kai hannu cikin pocket d'in rigar shi ya fiddo farin hanky ya mik'a mata ta amsa ta fara goge kwallan yana ta kallonta yama rasa tunanin da zaiyi ji yake kaman kar ya tafi ko don ta daina damuwa but he knows isn't possible ita kuma ga exams d'inta kuma yasan ko taje ma in ta dawo still sai ta damu na wani lokaci saboda rashin shi sai faman dirzar ido take bata da niyyar tsayawa a hankali ya kai hannuwanshi ya kamo duka hannayenta ya sauke su k'asa suka kalli juna cikin ido picifically yace "kiyi Hakuri Zaraah am feeling almost d same thing am not happy zamu yi nisa da juna after being together for gud 3 years but we can still be together though we're in distance right?" Jinjina mashi kai tay alamar eh, yace "ok ki daina damuwa pls" nan ma kai ta jinjina mashi shiru ya d'anyi sai kuma yace "tunda baki son rakani ba wani abu lokaci na tafiya zamuyi Magana" daga haka ya saki hannuwan nata ya mik'e har ya juya yaji ta kira sunanshi da disasshiyar murya ya juya ya kalleta ta saukko daga kan gadon ta mik'e a hankali tace "zan raka ka" fuska a d'an sake ya d'an bud'a ido yace "really?" Kai ta d'aga alamar eh d'an murmushi yay ya nufeta yace ina ribbom d'inta ta juya kan gado ta d'aukko tana kokarin sawa ya mik'a hannu ya amsa yay mata alamar ta duk'o da kan kallonshi tay cikin ido sai kuma a hankali ta duk'ar da kan ya matsa dab da ita ta yadda har kan nata ya d'an gogi broad chest d'inshi a nutse ya fara tattara gashin don ba kaman na Fanan bane nata yafi cika hannu sosae bayan ya gama ya d'ago da ita yana mata murmushi ita kuma tana mashi wani kallo a hankali ta furta "I will miss u Ya Handsome" kawae sai ya janyota yay hugging nata very tight ya d'aura ha6arshi saman gashinta, sosae itama ta k'ank'ameshi idonta a rufe wata kalan natsuwa taji tazo mata yayin da scent d'inshi ke k'ara narkar mata da zuciya tana cikin hakan taji cool voice d'inshi yana fadin "I will miss u too Zaraah, I will miss ur everything ur smile,jokes and d whole moment we spend together......" Yadda Maganar ke sauka acikin kunnanta yasa ta k'ara kankameshi yana jin yadda kirjinta ke sama da kasa saboda numfashin da take da sauri da sauri hakan kuma yasa Haisam d'in jin wani bak'on yanayi a tattara dashi wanda sam bai ta6a jin irin hakan ba a tare da Fanan, ita da bai ma jin komae in ya had'a jiki da ita don koda Maganar Aure ta shiga tsakaninsu tana nan a matsayin da ya d'auketa cikin ranshi sai daga baya ne data k'ara girma ya fara jin canji game da hakan shiyasa yake kokarin kiyayewa bai cika son suna had'a jiki da ita ba sai ta kama ita ce dae in zai biye mata to kullum suna manne, jin abun na k'aruwa sosae yasa da sauri ya d'agota don shi kanshi yasan bai kamata ya had'a jiki da ita ba har saida ya nemi tsari yay istigfari cikin ranshi, sam ta kasa kallonshi don da k'yar take ma bud'e idonta wani bak'on yanayi take ji a jikinta, shima juyar da kanshi yay gefe trying to get ease kafin ya kai hannu ya kamo hannunta ya kaita gaban mirror bai iya tanka mata ba da hannu yay Mata alamar ta gyara fuskarta ta kai hannu ta d'auki puff d'in powder tana goge fuskar idonta akan shi suna kallon juna ta cikin mirror d'in suna haka wayarshi ta fara ringing ya kai hannu cikin pocket d'in rigarsa ya fiddo yaga Hajiya ce ke kiran nasa yay picking yana d'auka tace mashi yana inane yasan dai jirgi bai jiran Mutum ko yace mata he's on his way heading there d'aga haka yay cutting ya maida wayar Fatuu na kallonshi yace mata ina veil d'inta ta matsa wurin wardrobe ta ciro hijab tasa ya kama hannunta suka fita, back door ya bud'e mata da kanshi bayan sun fita ta shiga ta zauna ya rufe shi kuma ya bud'e gaban ya shiga ya ja Motar, a kai kai yake kai ido kan mirror ya kalleta wani lokacin su had'a ido wani lokacin kuma ta duk'e tana goge kwalla can ta d'ago kawae taga yana mik'o mata hanky kallonshi tay kafin ta mik'a hannu ta amsa, a hankali take kai hanky d'in fuskarta ta d'an goge kwallan in suka had'a ido dashi sai ta sadda kan kasa, basu d'au tsawon lokaci ba suka k'araso Airport bayan sun yi parking sun fito ya nufi inda su Hajiya suke Fatuu da Tk na bayanshi, Hajiya na ganinshi ta sha mur ganin Fatuu yasa bata dae ce mashi komae ba gwaggo ma tunda suka had'a ido da ita sau d'aya bata yarda sun k'ara ba don taga kallon da tay mata mai kaman harara Abbas kuwa sai murmushi yake mata a sanyaye ta gaishe dashi kafin ta nufi wurin Hajiya ta gaidata tana kallon fuskarta ta amsa kafin ta dafa shoulder d'inta tace "kiyi hakuri kinji Fateema ai ba an rabu ba kenan da zaki damu kanki har haka, dubi idanunki yadda suka kumbura kukan ya isa haka kinji" kai ta d'aga mata lokacin kuma aka fara sanarwa nan da mintuna biyar jirgi zai k'araso don haka matafiya su shirya Hajiya ta juya tana k'ara yin sallama dasu gwaggo da Abbas suka ce sai sun zo daga haka suka nufi cikin departure Haisam ya mik'a ma Abbas hannu suka yi sallama shima yace mashi sai yazo haka Tk da gwaggo duk suka yi mashi fatan a sauka lpy, juyawa yay side d'in Fatuu ya d'an kalleta for few seconds sai kuma ya tafi ba tare da ya ce mata komae ba har yayi kaman taku ukku zuwa hud'u yaji ta kira shi hakan yasa ya dakata ya juya nufo shi tay tana zuwa gaban shi ta mik'a mashi hanky d'inshi da ya bata a cikin Mota kaman bazai amsa ba sai kuma ya amsa ya juya yana niyyar cigaba da tafiya yaji Muryata tana fad'in "Thank u Sweetheart Ya Handsome, thank u for all dat u have done to me May Almighty Allah reward u Abundantly, ina rokon Allah ya dawwamar da kai cikin farinciki har abada kamar yadda kake sa bayinsa farinciki, Allah ya jibanci lamuranka ya baka y'ay'a wanda zasu ji k'an ka, Allah ya....." Kasa k'arasawa tay ta duk'e a wurin tana wani irin kuka mai cin rai duk abun nan yana tsaye cak ba tare da ya juyo ba yana jin yadda take Maganar cikin breaking voice dake bayyana she's in serious pain runtse idonshi yay can kuma ya bud'e yaci gaba da tafiyar saida zai shige wurin sannan ya dakata ya d'an juya suka had'a ido tana a durk'ushen sai kuka take can ya juya ya shige, kowa ta bashi tausayi har gwaggo saida jikinta yay sanyi ta sani sabo ba abunda bai sawa ba kamar su sabonsu na Musamman ne, Abbas ne ya nufeta ya duk'a ya kamo hannunta ta d'aga kai ta kalleshi tana gunjin kuka ya jinjina mata kai alamar ta mik'e, Mota ya nufa da ita ya bud'e baya yace ta shiga gwaggo ma ta bud'e d'ayar kopar ta shiga yace ma Tk ya taho da Jeep d'in yace to, tunda suka taho hanya take aikin kuka kanta na kan kafafunta ta rufe fuska Abbas sai bata hakuri yake har dae ta k'ule gwaggo ta fara surfa mata fad'a cikin harshen fulatanci Abbas na bata hak'uri duk da baisan mi take cewa ba amman daga ji yasan fad'a take mata, suna akan hanyar jirginsu Haisam d'in ya wuce, Allah sarki Ya Haisam d'in mu shikenan ya tafi wayyo Fatuu I feel ur pain ko baki son Haisam dole ne ki ji zafin tafiyarshi🥹, suna k'arasowa kopar gida gwaggo ta bud'e Motar bayan tayi ma Abbas godiya ta wuce gida abunta da k'yar ta iya bud'e Motar ta fita sakamakon k'afafunta da sukae mata nauyi sai faman shessheka take tana niyyar tafiya bayan ta rufe Motar Abbas ya bud'e ya fito har ta juya ya kira sunanta ta juyo da runannun idanunta ta kalleshi ba tare da ta amsa ba cikin muryar lallashi ya fara Magana, "Am so sorry Zaraah, i know how are feeling but I want u to know Allah yana jarabtar bawa ba don baya son shi ba and if u'r destined for sadness there is always a reason all u need is to put ur trust in Allah, shine kadae mai maida abunda ake tunanin bai ta6a yuwuwa ya yuwu cikin tsananin sauki, so all I can say to u is kiyi HAKURI kiyi HAKURI" kai ta jinjina mashi tasa hannu tana goge kwallan ya kuma cewa "Da gaske baki son zuwa Abujan?" Da sauri ta d'aga mashi kai alamar eh, shiru ya d'an yi, ya gama fahimtar ta sosae yasan what she's going through abune mai tsananin rad'ad'i a zuciya, sigh yay yace "ko in kawo maki Abdul ya taya ki zama kafin mu dawo tunda itama Grandma d'in naki zasu je tare ma zamu H,Zakeen yayi mun Magana" murya na rawa tace "a'a ka barshi shima ai yana son zuwa" shiru yay yana kallonta tabbas Abdul na son zuwa kullum sai yayi Maganar bikin Baba Zakee ya fiddo da sabbin kayan da aka d'inka mashi saboda bikin, can yace "is Ok zaki iya tafiya amman don Allah ki daina damuwa haka kinji nasan ba zai yuwu cikin sauki ba dole sai a hankali amman try ur possible best kiga kin cireta a ranki ki focusing kan karatunki ba kamar da final Exams dinku is approaching kar ki bari hakan yaja maki Matsala don O level is very important shine tushen kowane karatu Mutum ke son yi without O level u'r going no where" kai ta jinjina mashi yaci gaba "in kina da wani matsala kar kiji komae ki sanar dani H,zakee yace ya siya maki waya right?" Shiru ta d'anyi alamar tunani sai kuma ta girgiza mashi kai don ita dae tasan bai bata waya ba, "Ok amman tabbas yace ya siya maki waya nasan zata zo hannunki so zan amshi phone no dinki sai mu rink'a communicating" kai ta d'aga mashi yace zata iya tafiya har ta juya taji muryarshi na fad'in " _Destiny may be delayed but cannot be changed Mom Zaraah_" da sauri ta juya ta kalleshi taga yana sakin murmushi ya jinjina mata kai alamar tabbatar mata da abunda yace kafin yace "kar ki wasa da ADDU'A" daga haka ya koma cikin Motar yay mata alamar ta shiga gida kafin yaja kopar ya rufe ya tafi tana tsaye tana kallon bayan Motar har yay nisa sannan ta juya da gudu ta shige gida d'akinta ta nufa tana zuwa ta fad'a saman gado ta dasa sabon kuka abunda yafi damunta shine yadda Abbas ya fahimci abunda ke damunta amman Haisam bai fahimta ba, tun dae gwaggo na jan tsoki tana sambatun abu yak'i ci yak'i cinyewa sai kace an rabu kenan har dae ta saduda ta nufi d'akinta ta fara bata hakuri gudun kada kukan yaja mata wata matsalar, a jikinta ta rungumeta tana ta bata baki har ta fara sauka can ta d'agata tace suje tay wanka kota ji karfin jikinta ta d'aga mata kai, saida ta rakata har bakin toilet d'in sannan ta juyo tana girgiza kai da d'an murmushi kan fuskarta, sosae taji dad'in jikinta bayan tayi wankan ta zura doguwar riga tana gama shiryawa sai ga Haulat suka zauna kan gado tana kwalla take sanar da ita Ya Haisam ya tafi ya barta ita kanta Haulat saida taji ba dad'i hakuri taci gaba da bata ganin tana zubda kwalla. ABUJA NIGERIA (Wata School mate dina ta ce dai Abuja kiran Allah sai kace Macca🤣) Tuni jirginsu yay landing har anje an daukkosu gaba d'aya sun hallara a tamfatsetsen Parlon gidan mai d'auke da sets d'in Sofas sun kai ukku kama daga Royal sofas, Leathers da sauransu gaba d'aya sun jigunu komae na falon mai k'ayatarwa ne a tsare yake akwae dining area mai d'auke da dining table mai seats sha biyu haka duk inda set d'in kujeru suke akwae kayan kallo wato duk inda Mutum ya zauna zaiyi kallonshi ba tare da wani ya takura ma wani ba akwae manya manyan windows da zaka ga harabar gidan sosae kana daga cikin falon haka akwae manyan kofofi da zaisu kai ka wasu k'ananun parlos d'in masu d'auke da bedrooms, daga gefe da gefen dining area wasu had'addun tagwayen bene ne da zasu kai ka sama ma'ana sun sa dining area d'in tsakiya su Kansu abun kallo ne gaba d'aya yanayi da tsaruwar falon kai kace ba a Nigeria bane, in nace zanyi bayanin komae na gidan to tabbas har ranar d'aurin auren Haisam d'in sai tazo ban gama ba don haka na barma mai karatu ya idasa fasalta gidan da kanshi, zaka yi mamakin irin kirkin mutanen dake rayuwa a gidan don sai ka d'auka zasu yi girman kai amman sam ba haka suke ba bala'in kirki ne dasu sam daular da suke ciki bata saka su girman kai ba Haisam ma dae misali ne ai, gaba d'aya sun baje sai hirar biki ake dama sun k'agara Haisam d'in yazo kullum sai sun kira Hajiya game da hakan sai tace shine ya tsaidasu da tuni sun taho, sai tsare tsarensu suke yayin da hankalin Haisam gabadaya ya tafi kan tunanin halin da Fatuu take ci don ba k'aramin karyar mashi da zuciya tay ba a Airport d'in nan hotonta yak'i barin zuciyarshi jefi jefi yake saka masu baki suna hakan har aka yi Magrib duk suka tashi don yin salla Haisam da sauran mazan harda Mahaifinsu suka nufi Masallaci dake gefen gidan kaman dae na gidan Hajiya shima kalan fentin gidan ne sai dae su sai sun hau Mota suke fita su je don ba hanya ta cikin gidan kuma tafiyace in ace suje a k'asa don kafin ma a fita daga harabar gidan har a shanye jikin gidan a isa Masallacin aikine, sai da suka yi har Isha sannan suka dawo lokacin kuma an gama shirya table duk suka hallara harda Saude tana gefen Hajiya saida Senator Alee yasa Haisam yay masu Addu'a kaman yadda suka saba duk in za'a ci Abinci sai yasa wani yayi Addu'a, a nutse suka fara ci bayan ya gama Addu'ar still tunanin Fatuu yake bai wani ci da yawa ba ya mik'e duk suka ce badae har ya k'oshi ba yace ehh Senator ya ta6e baki yace "Wato Son har yanzu baka cin Abinci sosae ko?" Hajiya tay karaf tace "bai kuwa ci ba don d'aga k'arfe ba da tuni shida muciya basu da maraba" duk aka sa dariya Senator Alee yace "to Ango ne dae kai u need to be eating more Food" nan ma dariyar akai su Jidderh na sussuna kai shidae d'an murmushin gefen baki yay ya juya ya fara hawa staircases da d'an gudu gudu cike da k'warewa Senator na fad'in ya dawo ya k'ara Abincin ya d'ago mashi hannu kawae, wai saman benen ma ma sha Allah, ko ina walwali ke tashi saboda hasken da k'ayatattun fitilun wurin ke saki su kansu sai Mutum yay kauyanci akansu, yana kaiwa k'arshe dakakkar kopar dake kallonshi ya tura ya shige, to jama'a gamu a wata Aljannar duniyar, had'addan Falo ne mai d'auke da leather chairs ruwan Madara fess dasu suma L-shape ne Carpet da Curtains suma duk ruwan Madara ne sai tarkacen kayan kallo dasu surround sound systems akwae frames masu kyau da hotuna, yana shiga bai tsaya falon ba bedroom ya wuce shima dae ya k'awatu da tsadaddun furniture kai kace d'akin wata yar gayun Amarya ne sam tsarin d'akin baida hayaniya ga Ac nata aiki, a bakin gado ya zauna ya fara k'ok'arin kiran Amadu kwatsam kafin yay sending kiran sai ga kiran Fanan ya shigo still yay yana kallon screen d'in har kiran ya katse yana tsinkewa wani ya sake shigowa he ave no option dole yay picking kiran don in ya k'i d'agawa ta kira taji yana waya bazata ji dad'i ba kuma tunda suka iso ta kira yace mata suyi waya anjima ko ba haka bama shi d'in ba mai wulakanci bane, waya suka shiga yi cike da shauki tun suna yi a zaune har ya gaji ya kwanta yana facing ceiling sosae suka 6ata lokaci suna wayar wanda yawanci kan dae Maganar bikinsu ne sai da ya nuna mata yana jin bacci sannan ta k'yaleshi saidae koda ya duba Agogo dare yayi sosae don sha d'aya ta kusa, kifa wayar yay saman cikinshi can kuma sai ya mik'e ya nufi toilet after some minutes ya fito sanye da bathrobe ya nufi press bayan ya gama shiryawa cikin sleeping dress ya nufi gado saida ya latsa switch hasken d'akin ya d'auke kafin ya kwanta kanshi saman pillow nan take zuciyarshi taci gaba da tariyo mashi yanayin Fatuu a Airport a hankali ya fara reminiscing old times tun ranar farkon had'uwarsu har zuwa yau wani wurin yay murmushi wani lokacin dariya wani sa'in ya girgiza kai can ya kai hannu ya d'aukko wayarshi ya shiga gallery duk wani hotonta dake a wayan saida ya kalla wani ma ko ita Fatun bata san dashi ba a haka bacci yay awon gaba dashi ba tare da ya fita daga images d'in ba wayar a saman cikinshi........... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 18 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........A ranar Fatuu na dawowa daga Makaranta da yamma bayan taci Abinci gwaggo ta k'wala mata kira ta isketa a cikin d'aki ta zauna kan kujera tace ma gwaggo dake zaune a bakin gado ga ta, "Dama Maganar tafiyarmu ce Habuja, d'azun nan Abbas ya kira Amadu yake sanar dashi gobe da Asuba zai zo mu wuce duk nayi tunanin sai jibi to amman wai a goben in munje zasu wuce Lagos ne akwae shagalin da zasu yi acan to kinga ba yadda za'ai ba zai fasa tafiyarshi ba saboda mu tunda dae hidimar ta su ce, tuni ma na gama kintsawa Amadu bai dad'e daya dawo ba bayan na kirashi a waya gwara yazo ya shirya don bansan a 6atawa Abbas d'in lokaci daga abun Arziki" shiru Fatuu tay lokaci guda jikinta yay wani irin weak gwaggo taci gaba "ni gaskiya bazan barki ke kadae a cikin gidannan ba kaman yadda kika ce rannan sai kace ana hauka dae, da tunanin da nike ko in kai ki gidan Zaliha to amman can d'in zai maki nisa da Makaranta gaskia to amman dae k'arshe dole hakan za'ai tunda nasan ai ba'a rasa masu zuwa Makarantar taku daga can ba" sadda kanta tay k'asa batare data ce komae ba gaba d'aya ba abunda ke mata dad'i tafi buk'atar taji ta ita kadae, "Kinyi shiru kin d'ukar da kai" taji gwaggon ta fad'a, a hankali ta d'ago idonta har sun canja don ma ta cije ta hana kwalla su zubo mata cikin rawar murya tace "to ko inje gidansu Haulat kafin ku dawo" d'an jimm gwaggon tay sai kuma tace "ba wai na k'i bane ni kaina zanso ki zauna can zaifi maki sauki to amman nayi duba ne da halin da ake ciki na babu kar kaje ka k'ara ma Mutum nauyi kan wanda yake fama dashi", Fatun tace "ai ma har munyi Magana da Haulat din dana ji kince ba zaki barni in zauna anan d'in ba kuma tace tana komawa zata fad'i ma innarsu" gyad'a kai gwaggon tay tace "shikenan to zan ga abunda za'ai yanzu zaki islamiyya ne?" girgiza mata kai tay tace "ina son in yi wanka ne kuma naga lokacin ya k'ure" gwaggo tace "to je kiyi wankan sai ki had'a kayan da zaki amfani dasu anjima sai munje in kai ki" mik'ewa tay kawae har ta nufi kopa sai kuma ta juyo tace "ko ba sai na d'auki kaya ba sai in rink'a zuwa ina yin wanka anan" shiru gwaggon tay tana nazari hakan yasa Fatun cewa "sai mu rink'a zuwa da haulat" gyad'a kai gwaggon tayi alamar amincewa Fatun ta juya ta fice tana kukan zuci wanda yafi na fili ciwo, tana fita gwaggo ma ta fita ta nufi kitchen ta fara tunanin yi ma Fatun cin cin dama suna da lemuka a fridge tasan zata ji dad'in shi, Bayan sallar Isha suka nufi gidansu Haulat din lokacin duk suna a tsakar gida suna cin Abinci innarsu na jin sallamar gwaggo ta mik'e tana mata maraba fuskarta d'auke da fara'a haka ma gwaggon, innar tace su shiga daga ciki gwaggo tace ba komae su tsaya a wajen tunda duk anan ake innar ta nufi daki da sauri ta d'aukko mata darduma bayan ta shimfida tace mata Bismillah ta zauna, gaisawa suka shiga yi a mutunce tayi mata ya aiki gwaggon ta amsa da Alhamdulillah bayan sun gama gaisawar tace "dama zuwa nai rokon Alfarma, gobe in Allah ya kaimu zamu tafi bikin su Hajiya shine nake son in ba damuwa Fatuu ta zauna anan kafin mu dawo tunda bazata samu zuwa ba Saboda jarabawa da zasu fara" yar dariya innarsu haulatun tay tace "Haba gwaggo wannan ai ba wani abu bane da har sai kin taso kin zo, nan ai gidansu Fatima ne ko kina nan taji tana ra'ayin tazo ta kwana ai hakan ba matsala bane wllh, ba wani abu Allah ubangiji ya tsare ya kiyaye hanya shima babansu zasu je da sauran limaman su Malam Tanimu amman sai ana gobe d'aurin auren ni kaina naso zuwa to amman yace basai naje ba sai dae in yi Addu'a kawae Allah ubangiji yasa Alkhairi ya basu zaman lpy da zuria dayyiba, amman yaron yana da kirki wllh da ya barni koda iya kud'ina kenan sai naje har bashi ma zan iya ci wllh don inje bikin nashi" gwaggo na yar dariya ta amsa da Amin tay mata godiya kafin ta dasa yabon Haisam har tay mata tayin Abinci tace Alhamdulillah a k'oshe take, duk abun nan Fatuu na cikin dakinsu haulatu tun bayan da suka shigo ta gaida innarsu haulatun ta jata d'aki, zaune sukae a gefen yar katifar Haulat sukae jugum a hankali kwalla ke gangaro ma Fatuu haulat na kai hannu tana goge mata tana bata hak'uri suna cikin hakan taji muryar gwaggo tana cewa tafito su tafi ta mik'e bayan ta gyara fuskarta haulat ta bi bayanta suka fita, sosae gwaggo ta k'ara yima innar tasu godiya kafin ta fiddo kud'i ta bata amman tak'i amsa tace Allah ya kyauta don Fatima zata zauna gidan ta amshi kud'i gwaggo tace wllh ba don haka ta bata ba, da k'yar dae ta kar6a sanin dama tana yi mata Alheri, a tare suka rakosu innar na fad'in ai tayi zaton Fatun tazo kenan gwaggo na murmushi tace sai gobe in zasu tafi innar tace Allah ya kaimu goben lafiya daga haka suka k'ara sallama ta koma haulat kuwa saida ta rakosu har bakin lungu sannan gwaggo tace ta koma tay masu saida safe tace ma Fatuu sai sun had'u gobe ta d'aga mata kai kawae suka tafi. Zaune suke gaba d'ayansu kan Dining table suna cin dinner har saida aka k'ara wani table d'in shima mai kujeru sha biyu a haka ma wasu saidae zama sukae kan kujeru a falo, a Table d'in farko anan Senator da matanshi da kakanninsu Haisam sai Her Excellency Hajiya Zainab, Hajiya da Sameer da Haisam duk suke, lafiyayyun Abincine aka jere don musamman dama anyo hayar kwararrun chefs Saboda bikin to wasu tun yau sun fara aikinsu, yau dae dole kowa Serving nashi ake Saboda Hajiya Zainab ko ba don ita bama ba yadda za'ai Sameer yay serving kanshi Abinci Never yanzu ma a hakimce yake umarnin ma sai ya mula yasha iska yake iya badawa shima da kai ko hannu, tsit kake ji sai karar cokulla can sun yi nisa kakansu ya dakata idonshi akan Sameer da turanci yace "shi wannan sai yaushe zai yi auren ne?" Kakar mace tace "ya kamata ace shima yay Aure gaskiya" yar dariya Hajiya Zainab tay tace "wannan ina tunanin har yanzu ba'a haifi Matar da zai aura ba" waro ido duk sukae Senator yace "kar dae kice man baida wadda ya tsayar zai aura har yanzu?" Girgiza kai tay tace "I don't think so" tay Maganar idonta akan Sameer d'in da ko kallonsu ma bai yi ba tunda suka fara Maganar, jinjina kai Senator yay kafin yace "duk laifin Son ne ya zaka tsaida mata shi ka barshi ko baiso sai ka tursasa mashi ai" d'an guntun murmushin gefe Haisam yay yasan kawae dad d'in nashi ya fad'a ne amman ba wanda bai san halin Sameer ba ba yadda za'ai ayi masa dole don kuwa rai zai 6aci ne, "Ai kuwa ba zuba mashi ido za'ai ba k'ato dashi yay ta zama ba mata yakamata a nema mashi tunda shi baida Niyya, Akwae k'anwar wadda D'an uwan nashi zai Aura ita yakamata a nema mashi" duk suka yi murmushi sai lokacin Sameer d'in ya d'aga ido ya kalli Senator da yay Maganar bakin shi ya d'an d'aga kad'an wai a hakan murmushi yay shima na mamakin jin shi za'a had'a da mata, can sai ma ya mik'e don baison kallonshi da ake d'agowa anayi ya nufi upstairs yana taka staircases d'in cike da isa suma sunga ta kansu, duk bin shi sukai da ido Haisam dae d'an murmushi yay cikin ranshi yana imagining yadda zaman Aure zai yiwu tsakanin Sameer da Farha, kuma abunda basu sani ba shine yana da yan mata kawae ra'ayin Auren ne baida shi, bayan sun gama shima Haisam upstairs din ya haye part d'inshi nan ya iske Sameer d'in kan gado yana latsa waya dama duk in yazo a part d'in Haisam yake sauka yana shiga wayarshi ta fara ringing Amarya tay kira bayan ya d'aga tace tana son suyi Video call ya amsa da Ok kafin yay connecting da laptop d'inshi dake kan bedside suka fara magana akan program d'in gobe da za'ayi a Lagos duk abun nan ko kallonsu Sameer bai yi ba tamkar bai ma jin abunda suke can Fanan tace waye a bayanshi yace mata Sameer ne tace bari su gaisa, d'an janye jikinshi yay ya juya yace zasu gaisa ko tanka shi bai ba har saida Fanan d'in tace"Hi Sameer!" sannan ya d'an juya ba yabo ba fallasa ya bita da ido saidae yanayin fuskarshi ya d'an canja a hakan wai murmushi ne yay mata tana murmushi tace "hope u'r coming to Lagos 2morrow" D'an jinjina mata kai yay kawae daga haka ya maida kanshi kan wayar Haisam ya juya suka cigaba da Magana kafin daga baya sukae sallama ya juya ya kalli Sameer ya kai hannu ya kwace wayar yana fad'in bari yaga abunda yake da ya janye attention d'inshi ya kasa sakin jiki ya gaisa da bride d'inshi sosae, d'an d'age bakin dae yay Haisam ya kai idonshi kan screen d'in wayar da sauri ya d'aga kai yay mashi wani kallo Sameer d'in ya d'age mashi gira sigh Haisam yay yace "Bro stop decieving people and ur self Just get married" wani guntun murmushin gefe yay ma sha Allah ashe k'ilan yasan kyaun da yake in yay murmushi shiyasa bai cika yi ba shima dae yana da dimples kaman Haisam d'in saidae nashi biyu ne mik'ewa yay ba tare da ya ce mashi komae ba walking majestically ya nufi hanyar toilet, aje mashi wayar yay ya d'aura kanshi akan pillow yana son ya kira Fatuu yaji halin da take ciki amman yana ganin kaman dare yayi can dae ya kai hannu ya d'auki wayarshi yay sending mata kira baiwar Allah lokacin tana kwance kan gado tayi lamo don ta kasa bacci sai tsumayen kiranshi take don kwana biyu kullum da wayarshi take bacci tana haka taji ringing alamar kira da sauri ta kai hannu tana ganin shine tay murmushi kafin tay picking ta kifa wayar a Kunnenta, "Zaraah" a hankali tace "na'am ina wuni" amsawa yay yace ya akai batayi bacci ba tana murmushi tace hakanan baccin ne bai zo ba, d'an murmushi yay kawae ya tambayi ya take tace mashi lpy lou daga haka suka ci gaba da wayar yana cikin yi Sameer ya fito k'ugunshi d'aure da towel ya nufi press sai lokacin ya juya ya kalli Haisam lokaci guda ya gane da mace yake Magana jin ya ambaci Zaraah cikin husky voice d'inshi don ba irin muryarsu d'aya ba yace "U what do you think u'r doing, ain't u deceiving??? Wani kallo Haisam d'in yay mashi shi kuma ya ta6e baki ya juya yana kokarin sa short da sauri Haisam ya juyar da kai don yasan ba kunya ta ishe shi ba kimono yasa iya gwuiwa ya d'auki laptop d'inshi ya fice daga bedroom d'in ya nufi Parlor, sosae suke fira har yake ce mata gobe su Abbas zasu zo he isn't happy da batare da ita za'a zo ba saidae tay murmushi kawae daga baya yace ta kwanta gobe akwae skul sukae sallama sai gashi kuwa tayi bacci bada jimawa ba. Ana kiran sallan Asubar farko wayarta tay ringing har saida gabanta ya fad'i ganin lokacin da aka kiratan gashi bata san lambar ba, can dae ta d'aga tay shiru tana son jin waye ya kira on the Other hand taji an kirata da Zarah lokaci guda ta gane Abbas ne cikin muryar bacci ta amsa ta gaidashi yace gasu nan kopar gida a bud'e ma Feenah da sauri tace to ta saukko daga gadon, d'akin gwaggo ta nufa ta fad'i mata suka fito tare gwaggo ta nufi wajen taje ta bud'e Abbas ya fito yazo wurinta suka gaisa yace zai wuce Masallaci gasu Feenah nan zasuyi salla in ya dawo sai su wuce tace to ya juya Feenah ta shigo tana ruke da hannun Abdul ta rungume Nasreen gwaggo ta kar6eta Fatuu kuma taje ta kama hannun Abdul suka nufi d'akin gwaggo gaba d'aya bayan sun zauna suka shiga gaisawa Fatuu ma ta gaishe da ita tace "Allah sarki Zarah banji dad'i ba dake za'a ba wllh" Abdul ma yace "nima haka momy" ita dae d'an murmushi tay haka gwaggo ma Feenah ta sake cewa "Amman dae ba gida zaki zauna ke kadae ba ko" gwaggo tay saurin cewa "eh zata zauna a makwabta ne gidan kawarta da suke Makaranta d'aya" Feenah tace yauwa hakan yayi daga baya suka tashi jin an kira salla, bayan sun gama gwaggo tace kota dafa masu wani abu Feenah tace a'a bata iya cin abu yanzu amman akwae Abinci a Mota a hanya sai su ci, su Abbas da Amadu na dawowa daga Masallaci Amadun ya shigo ya fara fita da kayayyakinsu ba 6ata lokaci suka fito don tafiya gwaggo tace ma Fatuu ta d'aukko jakarta da uniform sai a ajeta gidansu Haulat, da tace zata zauna in safiya tayi saita shirya ta tafi Makaranta in ta dawo sai ta wuce can amman gwaggon ta k'i amincewa don gaba d'aya ma don ba yarda zatayi ne yasa zasu tafi su bartan, bayan ta daukko komae suka fita Amadu ya kulle gidan gwaggo tace ya ciri makullin guda yaba Fatun yace to, Amadu ne ya shiga gaba sai su kuma suka shiga baya Abbas na ganinta yace da ita za'a kenan gwaggo tace a'a za'a ajeta can gaba gidan da zata zauna yace Ok yayinda a ranshi yake jin wani irin tausayinta in ba so da rashin Adalci ba ya za'ai ace Mom Zarah bata je bikin Haisam ba da ranta da lafiyar ta, a daidai bakin lungunsu Haulat aka ajeta duk jikinta yay wani iri gwaggo tace taje ganin tayi tsaye rungume da jaka cikin breaking voice tace " Allah ya kiyaye hanya ya kaiku lafiya...." Da sauri ta juya jin tana niyyar fashewa da kuka Abdul ya kwala mata kira ta juya ya fito da hannunshi yana mata bye bye itama ta d'an d'aga mashi sai kuma Feenah da gwaggo har da Amadu suma suka d'ago suna yi mata kawae sai ta juya ta fashe da kuka saida suka ga shigarta gidan sannan suka tafi, kopar Marusa low-cost suka wuce aka d'auki Nana kaman yadda Haisam ya ba Abbas sak'o sai fatan a sauka lafiya. Tana shiga d'akinsu Haulat ta aje jakar gefe ta kwanta kan katifa ta rufe fuskarta da bakinta tana ta kuka, haulat dake gefenta tana ta bata hak'uri itama kaman zatayi kukan har saida wata k'anwar haulat taje ta gayo ma innarsu ta shigo tana fad'in "Fatima ya da kuka kuma da girmanki don an tafi unguwa an barki ai kaman gobe ne zata dawo ko haba daina kuka k'annenki nata kallonki sai suyi maki dariya ma" jin hakan yasa ta sassauta kukan, da gari ya idasa wayewa da k'yar haulat ta samu tasa ta tashi suka fara shirin tafiya Makaranta bayan sun gama aka kawo mata abun kalaci biredi da kosai da tea don Haulat ta fad'i ma innarsu Fatun bata shan koko, bata wani ci da yawa ba tace ta k'oshi haulat taitai da ita ta k'ara ta kafe akan ta k'oshi amai take ji dole ta kyaleta da aka kai ma innar tasu tace suje su ci, k'arfe bakwai da rabi suka fito suka iske innar a yar barandar da take sana'ar koko haulat tace zasu tafi har ta k'irgo kud'i zata basu cikin disasshiyar murya Fatuu tace ta barshi gwaggo ta bata kud'in da zasu rink'a yin break innarsu haulatun tace kuma dae banda wanda ta bata, godiya tay tayi masu a dawo lafiya kafin ta k'ara ba Fatuu hakuri suka tafi, jikinta sukuku suka nufi bakin hanya wai kuma sai take jin dama ta bisu don kwata kwata ta rasa mike mata dad'i a haka suka k'araso bakin titi bada jimawa ba sai ga School bus suka tafi. Tafiya yankin Azaba,Amadu sai dae ya d'anyi bacci ya farka ya kalli hanya yayin da cikin ranshi yake ta Murna yau dae Allah yayi zaije Abuja, akan hanya suka samu wuri acikin wani gidan mai da bai aiki suka yi breakfast don Abdul nata kukan yunwa harda Nana don bata wasa da cikinta shiyasa gata nan tubarkallah, bayan sun gama suka sake d'aukar hanya aka dasa baka jin komae sai muryar Nana da Abbas dake ta hira abunsu don ita Feenah tafiya galabaitar da ita take sai jefi jefi take saka masu baki, Alhamdulillah Allah yayi an iso a Abuja wuraren Azahar, sakin baki Amadu yay yana kallon ikon Allah da kafin su shigo Abujar a garuruwan bakin hanya har yana ce ma Abbas dama haka Abujar take Abbas na dariya yace ya jira tukun kafin ya yanke hukunci, sakin baki yay sai faman kalle kalle yake kaman d'an kauye yazo birni Abbas na ta faman yi mashi dariya gwaggo ma dae bata ta6a zuwa ba amman bata nuna k'auyanci kaman Amadu ba don shi fa tsakaninshi da Allah a k'asar waje yake ganinshi ba kaman shimfidaddun tituna masu girma da bai saba ganin irinsu ba, ko ina titi haka yake ta fad'i can kuma yace wai ba Keke Napep ne da babura sai motoci kawae yake gani Abbas dae dariya kawae yake yace mashi akwae bangaren da keda akwae su nan dae inda suke babu, saida suka sake 6ata kusan awa Saboda go slow na Motocin ma'aikata kafin suka iso gidansu Haisam d'in, "Ya ilahi ya rabbil alamen" haka Amadu ya fad'a acikin zuciyarshi saidae baisan ya fito fili ba Nana ma cewa tay "kan uban nan!,wai anan Zakee ke rayuwa shine don cutar kai ya koma Katsina ya tsugunna" gaba d'aya ta basu dariya, gwaggo ma dai ta yaba ba abunda take fad'i sai "Ma sha Allah" da alama fa Amadu yay mutuwar tsaye don mamaki ya gama cikashi tunda uwar data haifeshi bai ta6a ganin gida irin wannan ba nan take ya fara jinjinawa hali irin na Haisam harma da yan uwanshi yadda basu d'auki Duniya da zafi ba, bayan Abbas ya parker Motar a wagegen parking spot d'in gidan mai d'auke da jerin jigunannun motoci duk suka fito Abbas ne ya hangi Nameer yana nufar Mota dake can gefe ya k'wala mashi kira ya juyo yana yin arba dasu ya washe baki ya nufesu, yana zuwa ya shiga gaishe dasu yana yi masu sannu da zuwa duk suka amsa Nana tace "yauwa mai kama da Zakee" still dariya yake ya kai hannu ya dafa shoulder d'in Amadu yace "Mutumina barka da zuwa" murmushi yay mashi wanda yafi kama dana yak'e yace mashi yauwa, Nameer d'in ya kuma cewa "Ya banga yar gidan ya Haisam ba mai kumatu?" Dariya duk suka yi gwaggo ta sanar dashi bazata samu zuwa ba Saboda jarabawa da zasu fara yace baiji dadi ba, Abbas yace "zaka wani wuri ne?" Yace "No bakin gate zanje akwae wadanda zan shigo dasu wai security sun hanasu shigowa" Abbas na dariya yace "Ok muma saida aka tantance mu, amman ya naga ansa security sosae lafiya dae ko?" "Eh lafiya lou akwae na Momyn Nasarawa ne" D'an bud'a ido Abbas yay "kace her Excellency na nan ashe" kai ya d'aga alamar eh yace yaje bari ya shiga dasu Nameer d'in yace bari ya kai Amadu d'akinshi sai ya dawo ya d'aukar mashi jakar goyonshi Amadun na cewa ya bari ya d'auka yace ya bashshi ai shi bak'on shi ne suka nufi part d'inshi dake saman bene, ta baya suka bi don akwae benen da zai kaika saman Amadu dai na biye dashi zarare zarare tamkar rakumi da akala, Suna akan hanyarsu ta shiga mai Entrance na gidan Nana ke tambayar Abbas wacece Her Excellency d'in data ji suna Magana don Mutum yay taka tsantsan, sosae Abbas yasa dariya kafin yay mata bayaninta harda alak'arsu da Haisam ita gwaggo dama tasan labarinta, suna shiga parlon sukae kacibus da Jidderh cike da Farinciki ta nufosu tana masu sannu da zuwa ta gaishe su duk suka amsa suna mata Murmushi Abbas yace ta kaisu wurin Hajiya tace to tay gaba suka bi bayanta har part d'in da Hajiya take, lokacin da ta gansu sosae tay murna sai sannu da zuwa take masu harda rungume gwaggo bayan sun gaggaisa da Mutanen dake a parlon nata ta jasu cikin bedroom tace su huta duk suka ce salla zasu yi, kafin su gama sallar an jere masu Abinci da abun sha suna gamawa suka hau cin Abincin don suna buk'atar shi, saida suka samu natsuwa sannan Hajiya tay masu jagora part d'in Mahaifiyar Haisam d'in lokacin duk suna zaune a k'ayataccen parlonta harda Hajiya Zainab da Auntynsu Haisam nan su Nana suka ga ikon Allah sun rasa gane wacece ma Mahaifiyar Haisam d'in har saida Hajiya tay masu bayani suma Matan gidan ta gabatar masu dasu gwaggon duk da sun santa Feenah ma ta ta6a zuwa sau d'aya wani zuwa da sukai da Abbas ya kawota suka gaisa Nana ce dae ba'a sani ba duk ta wani natsu sai kace ba ita ba, faram faram suka amshe su sunata godiya da Addu'ar Allah ya bar zumunci ita dae First Lady d'an murmushi kawae tay masu daga baya Hajiya ta koma part d'inta dasu, Abbas na fita part d'in Haisam ya wuce anan ya iske shi da Sameer da Saleem dama shi yana a gidansu na Abuja, duk sunyi mamakin ganinshi don bai gaya masu sun iso ba last wayar da sukai da Haisam basu kaiga isowa ba hannu ya ba kowannen su suka gaisa harda Sameer don sun san juna ta dalilin Haisam daga baya yay joining nasu cin Abincin, Nameer na shiga da Amadu part d'inshi duk ya k'ara shan jinin jikinshi ganin kyawawan yan gayun samarin dake ciki harda yan Ethiopia bedroom ya wuce dashi nan ma dae ya iske wasu kyawawan guda biyu kan gado suna game a laptop cikinsu d'aya d'an Hajiya Zainab ne, Nameer ya kallesu da murmushi yace "Guys meet my Friend from Kt" d'aya ne ya d'ago yace mashi an zo lpy shikam d'an uwan Sameer d'in ko ci kanka bai ce ba da alama duk haka suke, Nameer ya lura da yanayin Amadu hakan yasa ya dafa shi yace "just feel at home" d'an murmushin yak'e dai kawae yay ya kai jakarshi cikin press kafin ya nuna mashi toilet yace ko zaiyi amfani dashi bari yaje ya shigo da mutanen yanzu zai dawo yace to Nameer d'in na fita ya shige toilet, farko jigum yay saman seat dake rufe hakanan duk sai yaji ya raina kanshi can kuma ya mik'e yay abunda zaiyi ya d'auro Alwala ya fito, yana fita cikin sa'a yaga basu saman gadon ashe yana shiga toilet Ashraf k'anin Sameer yace su koma d'akinsu nan ana interrupting nasu dama ba anan suke da zama ba shine suka fita, wani sanyi Amadu yaji ya fara kokarin gane inda gabas take saidae ya kasa dole ya zauna gefen gado har Nameer ya dawo d'auke da tray d'in kayan Abinci bawan Allah shi yaje ya amso mashi, tambayarshi gabas yay ya nuna mashi ya zauna ya jirashi har ya gama sannan yace ga Abinci nan yaci ya k'oshi bari yaje ya dawo aikuwa wa Allah ya had'a da Abinci ba Amadu ba sosae ya saki jiki ya kwashi gara ganin shi kadae ne a d'akin yana gamawa cike da karfin hali ya d'auki tray d'in ya fita bayan ya sauka k'asa ta baya cikin sa'a yaga d'aya daga cikin ma'aikatan dake aiki a babban Kitchen d'in dake bayan ta amsa tray d'in shi kuma ya juya ya koma upstairs yana shiga bedroom ya haye gado nan da nan kuwa bacci yay awon gaba dashi. Ana gama sallar la'asar masu tafiya Lagos suka fara shiri duk Abokan Haisam ne banda iyaye ko su Jidderh baza'a dasu ba sai dae Laila da Amal k'anwar Sameer itama kusan sa'ar Lailan ce da wasu daga cikin yan Ethiopia, haka Nameer ma banda shi da alama sha'anin na manya ne Jidderh harda kukanta taje ta fad'i ma Mom dinsu tana son zuwa don Allah tasa aje da ita tace tay hak'uri tunda ance baza'a da ita ba Hajiya Zainab tasa baki tace yakamata aje da ita itama ai yan mata ce da kanta ta kira Haisam tay mashi Magana akan a sama mata ticket itama sannan akace za'a tafi da ita, kusan su goma sha biyar harda Nana aka kaisu Airport wasu dama already suna can Najeeb ma acan ya sauka don bai k'asar, ba 6ata lokaci jirginsu ya tashi. THIS IS LAGOS........ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2019* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 19 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........Tuni jirginsu yay landing har an daukesu Matan na gidansu Fanan angwayen kuma na a Guest house d'in Dad dinsu Fanan nan da nan aka fara shirye shiryen event d'in da za'ai wato Indian Night, Misalin k'arfe Goma na dare aka fara d'aukar Mutane zuwa inda za'ayi wanda katafaren Hall ne acikin wani tsadaddan Hotel wanda na Mahaifin Fanan ne had'in gwuiwa da wasu Abokansa turawa, Wow! Wow!! Wow!!! Just Speechless abun ba'a cewa komae sai wanda ya gani Hall d'in ya k'awatu matuk'a kai kace a India ne koda yake indiyawan ne sukai decorating Hall d'in da taimakon Mommyn wata Friend d'in Fanan da suka yi karatu tare suma indiyawa ne amman a Lagos suke zaune duk ita ta tsara komae furanni kota ina, zuwa k'arfe 11 na dare duk an hallara Matan sun sha sari kala kala wasu masu wando wasu dogayen riguna wasu na nad'awa yayinda mazan ma ke sanye da nasu wanda yawanci fakistan ne na Maza, Farar fata kawae kake gani a wurin bak'ak'en yan k'alilan ne irinsu Abbas suma sai sukai kaman bak'ak'en indiyawa gashi dama Lagos badae fararan fata ba sun taru wurin sosae dama suna da wannan had'in kan sai dae basu ji ba har turawan duk shigan kayan indiyawan sukae can Ango da Amarya suka shigo Tubarakallahu ma sha Allah har saida Alk'alami na ya su6uce ba tare dana ankare ba saida zan ci gaba da rubutun na fahimci hakan, gaba d'ayansu shigan Red sukae Haisam na sanye da Pakistan riga red sai wandon golden brown haka takalmanshi ma red ne anyi masu adon golden brown tamkar na sarauta sumar nan tasha gyara sai salki take wuyanshi rataye da scarf irin wanda indiyawa ke sawa shima golden brown wohoho ba ka ta6a cewa ba ba'indiye bane tabbas da Fatuu tazo wurin nan zuciyarta na iya bugawa ganin ta rasa zuk'ek'en miji kamar Haisam yayin da Amarya Fanan aka sha rantsattsan Sari ja tun daga kafarta har wuyanta gwala gwalai ne ta fito sak ba'indiyyar Amarya masu Arziki don kuwa ba kananun kud'i bane a jikinta to d'iyar Hajiya Maryam face yar kasuwa ta kirki data san kaya masu daraja, su kansu kayan Haisam d'in da wad'anda Abokansa su Abbas suka sa duk daga India aka kawo su aka rarraba masu different colours and designs, a bayansu Haisam d'in su Hajiya Maryam ne dasu Laila harda kakarsu Fanan ta wurin uba baturiya da wasu daga cikin danginsu, su Farha ansha sari riga da wando yellow da fari sai faman yauk'i take, fuskar Haisam a sake suka shigo Fanan kuwa sai fara'a take fuskarta cike da tsantsan farinciki komae yayi mata yadda take so suna shigowa Friends d'inta suka hau watsa masu furanni, bayan duk an zauna an natsu MC wanda yake ba'indiye ne amman yana jin turanci sosae ya fara gabatar da abunda aka zo yi in yayi da indiyanci sai ya fassara da turanci, babbar kawar Amarya wadda mamanta ta tsara wurin ita ta fito tay ma kowa sannu da zuwa ta bada tarihin Amarya da indiyanci bayan ta gama sai khairat data sha sari maroon ta fito tayi da turanci bayansu sai aka bukaci babban Abokin ango Abbas ya fito cike da shak'iyanci ya bada da turanci yana yi yana kwa6awa da indiyanci gaba d'aya yaba Mutane dariya bayan ya gama aka kira k'awayen Amarya indiyawa harda khairat don da ita akai rehearsal d'in rawar da za'ayi aka sakar masu wak'ar indiya suka fara cashewa cikin gwanancewa ba tare da suna missing steps ba abun ba k'aramin nishadantar da mutane yay ba bayan sun gama aka bukaci Amarya da Ango su fito su taka Fanan ta mik'e dama ta shirya ma hakan amman sai Haisam d'in yak'i tashi don shi baya rawa balle kuma rawar indiya shi gaba d'aya program din ma baiso ba kawae don yaga tana so ne ya biye mata amman kuma shima abun ya k'ayatar dashi, ita kadae aka kunna ma wak'ar ta fara rawa a nutse tana yi tana zagaye haisam wani lokacin ta duk'a gabanshi ko ta sak'o kanta ta gefen kanshi kota d'aura fuskarta saman gashinshi yadda take bin wak'ar kai kace ita ta rairata sai k'arar sarkokinta ke tashi kowa sai murmushi yake saki hardae sarkin jin kai saida ya d'an murmusa wato Sameer, wak'ar na zuwa k'arshe ta kama hannuwan Haisam alamar ya mik'e ta rungume shi gaba d'aya aka sa tafi da sowa, haka aka ci gaba da gabatar da abubuwan nishad'i ana raba ma Mutane lemuna, har Abbas da Najeeb saida sukae rawa da yan Matan da sukae, oh su Abbas an yada mata a Abuja anata fantamawa🙄, can bayan wani lokaci aka bada damar cin Abinci kowa abunda yake so za'a zuba mashi yawanci duk Abincin indiyawa ne 6angare 6angare, Bangaren shinkafa akwae su chicken Briyani,Veg Briyani,Briesd beef rice,Butter chicken rice, bangaren kaji kuwa akwae su, Chicken Masala,finger chicken,chicken grilled,chicken prame, haka bangaren Salad akwae su Antipasto salad,chicken salad,crispy salad,ponir mix salad da sauransu dae haka lemun ma akwae su Orange juice,Apple,grape,pine apple juice da sauransu kowa saida yaci yay hani'an nima dae ba'a barni a baya ba naci na sha Alhamdulillah😋,wadanda suka ce bazasu zo ba kun ma kanku ai ☹️ Sai wurin biyun dare aka tashi kowa ya koma masaukinsa masu bacci sukayi masu hirar abunda akayi suka dasa, Washe gari kuma aka hau shirin komawa Abuja, kai Jama'a masu kud'i na abunda suka gadama dama iya abunda yasa aka zo Lagos d'in fa kenan🤔, Wuraren sha biyu wasu suka tafi yawanci Haisam ne da Abokansa dasu Nana da wasu daga cikin k'awayen Fanan d'in su kuma sai da akayi La'asar dasu Hajiya Maryam da dangin mahaifinsu lokacin sun gama duk wani shiri suka tafi don a Abuja hidiman take. Suna komawa ranar aka hau shirin yin Ethiopian Night wanda Laila ta matsa sai anyi har Mahaifiyar Haisam d'in ma tana so ayi dole Haisam ya bada had'in kai ba yadda ya iya, bayan sallar Isha duk an gama shiri danginsu na Ethiopia dasu Laila su Jidderh harda su Amal Amarya Fanan da wasu daga cikin kawayenta duk sunyi shigar kayan gargajiya na Ethiopia wato habesha khamis kala kala duk dogayen riguna Matan suka sa farare masu adon golden mazan ma riga da wando ne farare sai gaban rigunan anyi adon golden, wasu adon maroon, green da sauransu har iyaye su Mahaifiyar Haisam d'in da Hajiya Zainab da sauransu ba'a barsu a baya ba abun ya matuk'ar bada citta su Fanan dasu Jidderh har iyayen duk anyi masu irin gyaran gashinsu ya bud'e d'innan kaman fanka, ba wani wuri aka je ba a cikin gidan akai program d'in anata d'aukar hotuna a wurare daban daban har a saman staircases suka jere abun gwanin k'ayatarwa daga baya aka ci aka sha, Washe gari Alhamis Arabian night akayi a tsadaddan Event center nan ma da taimakon danginsu Laraba aka tsara komae ya tafi daidai su Ango da Amarya dasu Abbas an sha shigan larabawa anci dabino ansha tea an kuma sha Fruit dasu Alkubzu can na hango wasu daga cikin yan Comment section su Bahillot,husnarh,Ma'ulee,munah bature,Boss bature,Bajatu,sis Asma,Maman Amir,habibty, shafa adili,Angel love,Aisha da sauransu dae anata kwasan saura ana ci ana zubawa a jaka wasu harda dabinon k'asa suke tsinta an fake da ba'a murna da bikin kuma anzo ana k'walama lol🤣, FRIDAY..... Juma'at babban rana Allah ya kawo mu Abuja ta kar6i bak'uncin Manyan Mutane na gida da kasashen k'etare don halartar d'aurin auren jarumin mu, hidima ta kacame acan cikin gidan bak'i ta ko ina sai zuwa suke banda wad'anda dama sunzo tuni, tun safiyar ranar aka fara sanya anko, Abokan Haisam gaba d'aya na a wani apartment na Senator dake a cikin layin nan aka sauke su har shima Haisam can ya koma yayin da Senatorn kuma da bak'inshi na a katafaren Guest hause d'inshi, Ana gama sallar juma'a a Central Mosque dubban Mutane suka shaida d'aurin auren ENGR. HAISAM ALEE ADAMU ZAKEE DA DR. FANAN MOHAMMED ABRAHAM akan sadaki Naira 500k, Haisam yaga kara Al'umma ko ta ina ba K'aramin dad'i yaji ba, su babansu Haulat duk sun zo haka yan wurin aikinsu babbar Mota suka yo mata da maza har yan gym dinsu ma ba'a barsu a baya ba mata da maza harda Anah duk sun zo kai wasu ma shi kanshi Haisam d'in bazai tuna inda ya sansu ba sai zuwa ake ana gaisawa dashi ana mashi fatan Alkhairi fuskarshi cike da annuri yasha babbar rigar Farar shadda haka sauran Angwayen ma duk Farar shadda suka sa, to a can gida ma dae duk farinciki ake kar ma Fanan taji sam bakinta ya kasa rufuwa kamar ta zuba ruwa a k'asa tasha ba wata kunya da take ji sai faman godiya take ga Allah daya nuna mata wannan rana cike da murna ta kira Haisam lokacin sun nufi Hotel da za'a yi reception yana d'auka ta fashe mashi da kuka tana fad'in at long last ta zama matarshi Murmushi kawae yake saki kafin yace mata shima yana farincikin hakan su Abbas dake gefenshi suka fara mashi tsiya yace zai kira later, daga cikin manyan bak'in dake zuwa yin Allah yasa Alkhairi harda Hajiya Kubra ta Comment section dama Abuja tasu ce can na hangota cikin shiga ta Alfarma ta zo harda iyalinta aka kar6esu hannu bibbiyu ba kamar data gabatar da kanta a matsayin Fan d'in Haisam, bayan wani lokaci tace zata tafi Hajiyar Sanata tace ya kamata ta tsaya aje dinner dasu anjima tace to zasu je anjima zasu sake dawowa ta bukaci sanin time d'in da za'a yi dinner d'in aka fad'i mata, Jama'a wai ya Fatuu???? Gaba d'aya ranar ta k'ara harmutsewa sanin yau ne d'aurin auren Haisam k'arfin hali kawae take a Makarantar amman ko daga yanayin fuskarta zaka fahimci ba daidai take ba, ba abunda haulat ke gani kan fuskar tata face tsantsar tashin hankali, bayan an tashi suna zuwa bakin lungun gidansu Haulat tace mata gida zata anjima zata zo kasa dakatar da ita haulat d'in tay ta bita da ido har tay nisa, tana zuwa ta bud'e gidan ta maidashi ta datse tun a bakin kopar daki ta saki jakar ta fizge hijab dinta ta nufi gado da gudu sai lokacin ta samu damar sakin kukan dake ta cinta, sosae ta shiga rizgar kuka tana cikin kukan ta mik'e taje ta jawo drawer chest ta mirror d'inta ta curo IV d'in bikin ta koma kan gado tana kallo tana cigaba da rizgar kuka har time d'in da akasa za'a d'aura Auran yay tana a hakan sai ma abunda ya k'aru ma daga kukan duk ta fita hayyacinta fuskarta tay jajir can kuma a fusace ta fara Magana tana fad'in "nasan na rasa ka yanzu bazan ta6a samunka ba Ya Haisam kayi Aurenka ka barni cikin mawuyacin hali ko kirana ma ka daina yi to nima na daina sonka,na daina na daina na daina.......". Haulat na komawa gida ganinta ita kadae yasa innarta tambayarta Fatuu tace mata ta wuce gida ta d'aukko abu, bayan tayi wanka tay salla taje wurin innarta a d'aki tace a bata Abincin Fatuu zata kai mata tana kallonta tace "to ba zata dawo ba?" Yan kame kame ta fara yi tace "eh amman tace sai anjima" shiru innar tayi sai kuma tace "wai kodae wani abu na damunta ne naga duk ta canza kamar tana cikin damuwa ko?" Yan kyafcen kyafcen idanu haulat ta hau yi murya na d'an rawa tace "a'a... ba wani abu kawae dae har yanzu tun ciwon data yi kwanaki bata ida warwarewa ba ta koma kaman da" gyad'a kai innar tay tace Allah ya bata lpy da sauri ta amsa mata da Amin, bayan ta zuba Abincin haulat tasa Hijab ta nufi gidansu, tana isa kopar gidan ta iskeshi a rufe ta fara buga kopar shiru shiru ba'a bud'e ba kuma tana da tabbacin Fatun na ciki, can ta aje yar warmer d'in a gefe taci gaba da bugawa amman shiru har gabanta ya fara faduwa ta fara tunanin kar dae wani abu ya samu Fatun wata zuciyar kuma tace ko dae ba gidan ta dawo ba, ta kuma raya mata to ina zata tabbas tafi tunanin tana ciki, cigaba da bugawa tayi da k'arfi can ta tuna da Fatun nada waya ai da sauri ta fara kokarin kiranta har saida ta kira sau biyu tana niyyar tura kira na ukku taji ana bud'e kopar har saida taji wani sanyi a ranta a hankali ta d'an bud'e kopar ta lek'o da kanta suka had'a ido da Haulat ganin itace yasa ta idasa bud'e kopar haulat din ta d'an waro ido tana kallonta da Al'ajabin ganin yadda fuskarta ta koma idanuwanta sun kumbura gaba d'aya ma fuskar ta kumbure da gani ba d'an k'aramin kuka ta sha ba, a sanyaye haulat ta shiga bayan ta d'aukko Abincin ta tsaya tana kallonta tace "Fatuu ya zaki lahanta kanki akan..." Bata k'arasa ba Fatun ta fad'a jikinta tana fad'in "Haulat na daina son Ya Haisam daga yau, yayi Aurenshi ya manta dani inata wahala" nan da nan idanun haulat suka kawo kwalla cike da k'arfin hali ta d'ago ta tace shikenan su shiga ciki hannunta cikin nata bayan ta rufe gidan suka nufi d'akin Fatun, a gefen gado duk suka zauna Haulat ta aje Abincin k'asa kafin ta d'ago ta kama hannuwan Fatuu tace "Haka yakamata, ki daure ki daina sonshi tunda kinga yanzu yayi Aurenshi yana can yana farinciki shida matarshi ke kuma kina nan zaki ma kanki illa kuma ki sani duk abunda ya sameki kece a wahala iyaka kawae nasan bai wuce su kira ki a waya suyi maki sannu an k'ure ya turo kud'in magani, ki daure ki cije Fatuu ki raya mafarkin ki na son zama Doctor kinga jarabawa ke tunkaro mu bada jimawa ba kuma tattare da ita ne zaki raya burinki ko ki kashe shi ki duba irin d'awainiyar da gwaggo ke maki Fatuu kan karatunki Saboda rayuwarki ta inganta ta baro ki da garinku ta kawo ki nan ya kike tunanin zata ji in kika kashe mata kwarin gwiwar da take da a kanki? ki yi hakuri ki bar ma Allah komae kinji?" Kai ta d'aga mata duk tayi sanyi sai kace ba Fatuu ba, hannu Haulat ta kai ta d'aukko kulan Abincin tace "ga Abinci na kawo maki zaki ci ko?" Kai ta d'aga mata alamar eh, tace "to kin ma yi salla kuwa?" girgiza mata kai tayi cikin disasshiyar murya tace "banyi ba amman yunwa nike ji sosae" yadda tay Maganar gwanin ban tausayi, bud'e mata kulan haulat tay tace to taci in ta gama sai tayi Salla tace to haulat na kokarin zuwa ta d'aukko mata spoon a Kitchen taga ta sa hannu ta fara ci ta koma ta zauna tana kallon yadda take tura Abincin da gani ba k'aramar yunwa take ji ba dama ko da akayi break a makaranta bata ci komae ba wani irin tausayinta ne ya kama haulat ta mik'e taje ta daukko mata ruwa ta kawo mata saigashi ta cinye Abincin tass cikin d'an lokaci Haulat na d'an murmushi don taji dad'in yadda ta ci Abincin ta mik'a mata ruwan shima ta shanye shi tass haulat tace to taje tayo Alwala suka mike tare tana kokarin daukan kulan Haulat tace ta barshi ita ta d'auka suka fita, bayan ta gama sallan da kanta tace bari tayo wanka har saida haulat ta rakota bakin toilet kafin ta koma d'aki tana ta juya abun a ranta tana kuma Addu'ar Allah ubangiji yasa ta daina jin son nashi ko kuma ta rage tunda tasan ba abune da zai yuwu lokaci guda ba sai a hankali, bayan ta fito ta shirya cikin riga da skirt na atampa ta d'an fad'a daka kalli wuyanta amman dirin ta na nan yadda yake, falo suka koma suka kunna kallo saidae ita Fatun idonta ne akan tv d'in amman zuciyarta na duniyar tunane tunane sai faman imagination take akai akai Haulat ke juyowa ta kalleta su had'a ido ta sakar mata murmushi itama sai ta d'an yi mata na yak'e. Bayan isha aka shiga shirin tafiya Dinner zuwa k'arfe tara aka fara kwasan Mutane, wohoho Jama'a kuzo Kuga tsaruwar wurin dinner d'in Naira tasha kashi a wurin iya decoration d'in wurin abun tsayawa kallone, Ango yasha tsadaddun suit bak'ak'e yayin da Amarya Fanan ke sanye da wedding gown fara tun daga kunnanta wuyanta hannunta da yatsunta duk Diamond ne mai d'an karan tsada haka takalmanta da yar jakar hannunta masu d'auke hankalin Mutum ne, Angwayen ma duk shigan suit sukae haka k'awaye da yan'uwan Amarya ansha ankon rantsattsan leshi jama'a ina masu sana'ar lalle da d'inki ku zo ku dau style iri iri wani d'inkin sai kace na Aljanu gaba d'aya an watse karamar leshin, ina ganin Farha na hau tunanin yadda akai tasa fitted gown d'in jikinta k'arshe dai na yanke a raina k'ilan a Jikinta aka d'inka ta, Ma sha Allah an ci an sha an kuma nishadantu can na hango Hajiyar Sanata da Hajiya kubra suma duk sun sha leshi ashe dae ta dawo da gaske to Momy muna godiya Allah ya bar zumunci, su Fanan a banza an kadaddabe Haisam balle yanzu da igiyan Aure ya shiga tsakani sam bata barshi ya wataya ba tabi ta k'ank'ame abunta amman banga laifinta ba mijinta ne halak malak, sai wurin d'aya aka tashi Haisam duk ya gaji da hidindimun don shi ba mai son hayaniya bane, Washe gari Asabar akai Mother's eve wanda yazama tamkar Walima don a cikin gidan akayi shi ranar ankon shadda aka sha abun dae sai dae ace ma sha Allah, sai bayan isha taro ya watse masu tafiya suka tafi Misalin k'arfe goma da wasu mintuna Haisam na tare da Abbas a gaban parking lot basu dad'e da shigowa ba daga wurin sauran bak'in su da basu kaiga tafiya ba don wasu duk sun tafi tun jiya Sameer ma sun tafi yau da safe, zaune suke a saman boot duk suna sanye da shadda dinkin sen style duk basu da huluna akan suna cikin fira wayar Haisam dake ajiye gefe ta fara ringing ya kai idonshi kanta Amarya ce tay kira hannu ya kai ya dauka kafin yay picking call d'in ya kara a kunne tun kafin yace wani abu ta riga shi da tambayar inda yake taje part d'inshi bai nan ya bata amsa da inda yake daga haka tay cutting call d'in ya maida wayan inda take Abbas na murmushi ya tambayi Amarya ce ya d'aga mashi kai kawae, bada jimawa ba sai gata ta 6ullo ta baya jikinta sanye da wata matsiyaciyar fitted gown ta atampa super daga k'asa ta bud'e sai tay kaman kifi mermaid kanta tayi fav d'aurin kallabinta wato Zaraah buhari tana sanye da fashion d'an kunne da yan hannu hannunta ruk'e da wayarta yayinda kafarta ke sanye cikin flat shoes sumarta ta linkata ta yadda ta dawo daidai tsakiyar bayanta, wani kalan fitinannan kamshi mai narkar da zuciyar wanda ya shaka take saki ba a kayanta ba ba kuma a Jikinta ba don ba k'aramin gyara tasha ba tun daga cikin jikinta zuwa kan fatarta ita kanta tana jin canji a jikinta sosae ta tsumu da yawa, tunda ta tunkaro su idon Haisam na kanta haka Abbas ma sai sakin murmushi yake tun kan ta k'araso kamshin ta ya rigata isowa tana zuwa gabadaya ta fad'a jikin Haisam ta d'aura kanta a saman shoulder d'inshi don a zaune yake, wani kalan lumshe ido yay ya d'an juyar da kai yana kallonta daga yadda take ta gaishe da Abbas dake zabga murmushi ya amsa yace "Amarya ya gajiyar hidima?" K'asa k'asa tace "akwae shi don am completely exhausted" d'ago kan tayi idonta akan Haisam sukae ma juna kallon cikin ido seductively ta furta "I ave been looking for u since nayi trying no d'inka bai shiga ba sai yanzu" kallonta kawae yake yadda take Maganar underneath his breath ya furta"What's it, do u have any problem?" K'ara kwantar da kan tayi ba tare data ce komae ba, Abbas yace "baka ji tace she's exhausted ba I think she needs some fresh air ko ta rage gajiya ya kamata ta d'an ga gari ai ansha hidima da yawa?" daga yadda take tace "u'r right Abbas" wani kallo Haisam yay ma Abbas d'in ganin dariyar da yake yasa ya fahimci da biyu yay Maganar da yayi sigh yay yace "aiki ya sameka sai ka shiga kai driving muje" wata yar iskar dariya Abbas yay yace "aiki ya same ni ko ya same ka ko kana nufin mun gama ma hidiman bikin Matan ma mu zamu yi maka dawainiyar ta in zaka tashi kai aikin matarka ka tashi ni wllh ba in da zani zuwa ma zanyi in kwanta don nima a gajiyen nike" daga haka ya diro ya aje mashi car key d'in yay gaba yana dariya yana fad'in sai sun dawo, Abbas na tafiya ya kai hannu ya d'ago da face d'inta suka k'ura ma juna ido Fanan sai faman lumshe ido take shima nashi a d'an lumshen suke duk sun cika juna da k'amshi, dirowa shima yay ya kama hannunta ya zagaya other side d'in Motar ya bud'e mata ta shiga ya kai bakinshi ya manna mata kiss a cheek d'inta ta wani kalan lumshe ido bayan ya rufe Motar ya zagaya driver side ya bud'e ya shige bayan ya tashi Motar ta kai hannu ta kama hannunshi guda daga haka yaja suka nufi hanyar gate suna isa aka bud'e masu suka fice.............. _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2020* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 20 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ........Suna hawa hanya wayar Haisam tay kara alamar shigowar message a hankali ya janye hannunshi daga rik'on da ta yi mashi ya d'auki wayar yana k'ok'arin dubawa, _Take it easy on her sabon shiga._ Abunda aka turo kenan kuma ba kowa bane ya turo fa ce Abbas, d'an guntun murmushin gefe yay ya fita daga wurin ya maida wayan ya ajiye suka cigaba da tafiya, Abbas na komawa part d'in Haisam bedroom ya nufa ya fad'a saman gado nan take yaji kewar matarshi ta rufe shi wanda in ba don hidima ba ba yadda za'ai suna wuri d'aya har yaji kewarta can ya yunk'ura ya tashi zaune ya kai hannu ya d'auki wayarsa dake gefenshi ya shiga call log, lambar Feenah ya kira saida ta kusa katsewa tay picking yadda tay Magana daga jin muryarta ta fara bacci, bayan sun gaisa ya tambayeta yara tace duk sunyi bacci yace Ok yana son ganinta ta tambayi inda yake yace ta biyo ta kopar baya yana nan ta amsa da ok, saida ta d'aura hijab a kayan baccin dake jikinta sannan ta fita, tana zuwa bayan ta hango shi a tsaye d'an can nesa ta nufeshi tana zuwa gabanshi da murmushi tace mashi "Dear bakai bacci ba" d'an ta6e baki yay yace "yea na kasa shiyasa na kira ki ki taya ni fira" a d'an shagwa6e tace "kai dear wani irin fira yanzu bacin k'asan inda muke hakanan ka tado ni ina bacci na..." bata k'arasa ba ya janyota jikinshi ta waro ido kafin tace wani abu ya rigata fad'in "Wato kin manta dani ko har kina iya yin bacci hankalin ki kwance" tana ganin yadda yay Maganar ta fara k'ok'arin raba jikinta da nashi tana fad'in kada wani ya gansu, K'in sakinta yay ya riketa gam yace "to a gammu mana zunubi muka aikata ko me" d'an yamutsa fuska tay ya fara kokarin janta yace suje tay mashi massage k'ilan yay baccin turjewa tay a marairaice tace "amman Dear kasan fa a inda muke yanzu fisabilillahi a ina zan maka wani massage" ya bata amsa da part d'in Haisam idanu waje tace "ya hakan zai yuwu cikin Abokanka!" d'an murmushi yay yace mata ai ba kowa shi kadae ne Haisam d'in ma ya fita da Amaryarshi tana jin haka ta d'an bud'a ido Abbas d'in yay dariya yace su je mana, to dae itama tana kewan mijin nata hakan yasa ta bishi suka nufi kopan baya mai stairs da zasu kai ka parts d'in sama ta baya, suna shiga kopan ya sungumeta yana taka staircases d'in sai yan nok'e nok'e take don gaba d'aya a d'arare take Allah yaso har suka haye ba wanda ya gansu ya tura kopar ya shige da ita, to dae Allah ya kyauta jin kunya ko tashin yara, Suna hawa hanya sosae ya tambayi Fanan ko tana jin yunwa tace a'a just abu mai sanyi take buk'ata ya jinjina kai still hannunsu na cikin na juna a gaban wani cold store ya parker motan yace mata yana zuwa ya fita, after some few minutes ya fito hannunshi ruke da Leda mai d'auke da tambarin wurin ya zagaya ya shiga Motan bayan ya mik'a mata ya rufe kopan kafin yaja suka tafi, bud'e ledan tay Manyan robobin ice cream ne guda biyu ta curo d'aya ta bud'e ta fara sha cike da salon jan hankali ta rink'a d'e6owa tana kaiwa bakinshi ba tare daya ce komae ba ya rink'a d'an bud'e bakin yana sha, zagayawa yay da ita gari bayan wani lokaci ya tambayeta is she calm su koma gida sai ta wani langa6ar da kai cike da marairaicewa tace "I know su khairat aren't sleeping yet suna can suna shouting and it caused me headache" nodding kai yay idonshi akan hanya can ya tambayeta yanzu ina take so suje ba tare da ya kalleta ba, tace "somewhere very quiet and calm" d'an juyawa yay ya kalleta idonta akanshi ta d'an d'age mashi gira, d'an murmushi yay ya maida idon kan hanya can kuma sai ya taka burki a gefen hanya tana kallonshi yace ta fito tay driving d'in zai yi wani abu ta amsa da Ok ta bud'e kopan lokacin shima ya fito saida ta d'an shafi gefen fuskarshi yay mata Murmushi kafin ta zagaya ta zauna a driver seat shi kuma ya shiga inda ta tashi ya zauna bayan duk sun rufe kopopin kafin ta ja Motar ya kai hannu ya d'auki wayarta dake ajiye a gaba lokacin ta tambayeshi ina zasu yace mata yana zuwa hakan yasa ta dakata bata ja Motar ba, Google map d'in wayarta ya shiga ya rubuta inda zasu sannan ya aje mata inda zata rink'a gani ta kai idonta kan wayan tana ganin wurin daya sa ta d'an juyar da kanta gefe ta saki wani kayataccen murmushi kafin taja Motar tana bin Map d'in suka tafi shi kuma yanata latsa wayarshi da alama yana wani abu ne, kusan 30 minutes sannan suka iso harabar katafaren Hotel d'in ta nufi inda aka tanada don ajiye Motoci ta sama ma tasu wuri a cikin jerin rantsattsun Motocin dake wurin, juyawa tay ta kalleshi tace sun iso ya d'aga mata kai sai kuma ya d'ago daga kallon wayar yay mata alamar suje da kai tana k'ok'arin bud'e Motar taji cool voice d'inshi yace "Are u going like this?" Dakatawa tay ta langa6ar da kai shi kuma ya d'age mata gira alamar jiran amsarta sam ta manta ta d'aukko mayafi can ta tuna da kallabinta babba ne ta curo shi ta bud'e ta rufa saman kan ba laifi ya saukko har kusan k'ugunta sannan ya bud'e Motar itama ta bud'e ta fita, suna zuwa reception ba 6ata lokaci aka basu key d'in d'akin da tuni ya kama masu online suka nufi VIP inda d'akin yake ya bud'e yay mata alamar ta shiga kafin shima ya shiga kopan ta rufe, babban single room ne mai d'auke da had'addun Furniture d'akin ya k'awatu ga ni'imtaccen sanyin Ac had'i da sanyayyan kamshi na tashi, gefen gadon Fanan ta tsaya idonta akan shi har ya k'araso ciki ya aje wayoyinsu da keys kan bedside drawer ya d'ago shima ya tsaya a gabanta suka cigaba da kallon juna, wani kalan kallo da basu saba yi ma juna irinshi ba suke bin juna dashi kasa jurewa Fanan tay ta d'an sadda kanta don wani irin kwarjini yay mata, d'an murmushi ya saki ya kai hannuwanshi ya dafa shoulders d'inta da sauri ta d'ago ta kalleshi ya jata jikinshi yay hugging nata ta wani kankameshi sosae kawai sai jin sobbing d'inta yay alamar kuka take slowly ya d'ago da ita ya ga da gasken kukan take tak'i had'a ido dashi, da wata irin murya ya kirata"FANAN" yarrr taji tsigar jikinta ta tashi don rabon da ya kira sunanta har ta manta ganin tak'i dagowa yasashi sa hannuwanshi ya d'ago da face d'inta ta kalli cikin idanunshi da idonta jage jage da hawaye underneath his breath yace "what for??" Motsa baki ta fara a hankali tace "ba komae Ya Haisam am just feeling dat am d happiers person on earth now, nagode ma Allah burina ya cika mun zama married couple" murmushi kawae yake saki yana kallon yadda take Maganar, ya sani tana matuk'ar kaunarshi shima kuma yana jin sonta a ranshi, Cupping face d'insu yay suka cigaba da shakar kamshin juna gaba daya she's irresistible ga lafiyayyan Namiji at dat moment a hankali ya d'ago da face d'inta ta yadda har tsinin hancinsu ya had'u slowly ya had'e lips dinsu wuri guda without wasting time suka shiga ba juna deep French kiss kasa daukarsu kafafunsu sukae suka kai gadon suna cigaba da bawa juna very hot romances na wani lokaci ba k'aramin kokari Haisam yay ba ya iya controlling urge d'insa a lokacin ganin suna niyyar kaiwa wani mataki da bai shirya ma hakan ba, da k'yar ya d'an ja jikinshi breathing rapidly Fanan na ganin hakan ta kalleshi da idanunta da tuni sun canja daga sufar su ta ainihi shima kallonta yake ganin yanayinta yasashi d'an jawota ya kai bak'inshi saitin kunnanta cikin trembling voice ya furta "am sorry isn't proper in a Hotel room" da sauri ta runtse idanunta all she needs at dat Moment was for him to do it with her don ba k'aramin tsumuwa tay ba shi kanshi dauriya ce kawae don kuwa bacin kasancewarshi lafiyayye Abbas da Najeeb sai da shima suka gyare shi tsabb, kasa cewa komae tay ta kife kanta a chest d'inshi tana ci gaba da breathing quickly a hankali kuma wasu siraran hawaye suka fara zubo mata amman bata bari ya gani ba, jin yadda take numfashin yasashi kai hannu yana rubbing soft skin d'in bayanta dat's opened alamar rarrashi ta lumshe ido a hankali numfashinta ya fara daidaituwa bayan wasu mintuna ya d'an d'agota jin tayi tsit ya ga tayi bacci ashe bin face dinta yay da kallo kafin ya kai hannu ya goge yan guntun kwallan dake mak'ale a idanunta wanda bazai tantance na miye ba kafin ya gyara kwanciyarshi ya daurata kan chest d'inshi sosae, shiru yay duk jinshi yake wani iri don abunda ya faru tsakaninshi da ita abune da bai ta6a aikatawa ba shi ko had'a jiki da mace ma in ba ita ba da yan'uwanshi ko Farha bai ta6a had'a jiki da ita ba sai dai ya dafata ko ya kama hannunta in ta kama SAI KUMA ZARAAH zuciyarshi ta raya mashi hakan lumshe ido yay ya fara tunaninta kwana nawa bai ji ya take ba Saboda hidima lokaci guda yaji yana son ya kirata yaji ya take a hankali ya mik'a hannu kan side drawer ya d'aukko wayarshi saidae yana duba time yaga dare yayi sosae shi kanshi baisan dare yayi haka ba kusan d'aya saura na dare, shiru yay yana kallon wayar sai kuma ya shiga messaging ya rubuta mata sak'o kamar haka, _Hope u'r doing gud Zaraah._ Daga haka ya maida wayar ya ajiye,shiru yay yana tunanin yakamata su koma gida gashi duk baijin dad'in jikinshi yana son yay taking shower amman kuma baison maida kayan jikinshi kawae sai yay deciding in yaje gida yayi tunda ba wani abu ya same shi ba, kallon Fanan yay da alama in ba ya tasheta ba ba tashi zatai ba, a nutse ya fara tashin ta whispering her name a hankali ta fara motsa idanunta suka fara bud'ewa tana yi tana lumshe su har ta idasa ware su a kanshi ta k'ura mashi ido kaman bata ta6a ganinshi ba d'age mata gira yay ya furta "My Lazy wife..." tura mashi baki tay ta maida kan jikinshi tay lamo yaci gaba da fad'in "it's already late yakamata mu tafi u can rest more there" jinjina mashi kai tay ya d'an duk'a a hankali yace "do u need to take bath?" shiru tay har saida ya k'ara maimaita mata sannan ta d'aga kai alamar eh ya d'aga ta yace suje ya taimaka mata ba tare da ya jira cewarta ba bayan ya mik'e ya sunkuceta gaba d'aya yay toilet da ita. Tunda su ka hau hanya ta juyar da kanta tana kallon gefe akai akai yake kai ido ya kalleta can ya kamo hannunta ya d'an matsa ta juya ta kalleshi ya d'age gira yace "Why are u sulking?" a hankali ta girgiza mashi kai alamar ba komae suka ci gaba da tafiya ita kanta ta rasa mike mata dad'i ma jinta take wani iri, koda suka isa bai nufi Parking space ba a gefen Entrance d'in gidan ya parker Motar suka fito a tare ya zagaya wurinta ya kama hannunta suka shiga main parlon ba kowa tsit kake ji da alama kowa yayi bacci don kusan k'arfe 1:30 na dare, har bakin part d'in da aka saukesu ya kaita ya manna mata kiss a goshi had'i da fad'in "Good Night" ta d'an yi mashi murmushi kafin ta juya ta shige shima ya nufi hayar fita, tana shiga parlon ta iske khairat kwance kan doguwar Sofa tana waya koda ta ganta ta shigo da sauri ta tashi zaune Fanan d'in ta nufeta ta fad'a gefenta ta zauna ta d'age kai sama ganin haka yasa khairat ce ma wanda suke wayan "Honey excuse me I will call back" daga haka tay cutting call d'in idonta kan Fanan tace "bestie where u from at dis time nata nemanki ban ganki ba I even call ur phone yana ringing baki d'aga ba" daga yadda take ta juyo da kanta tana kallonta ba tare data ce mata komae ba itama khairat d'in bin ta take tayi da kallo can idonta ya sauka a kan Fanan d'in da rabinshi ke bud'e k'ura ma gashinta ido tay sai kuma ta kai hannu ta ta6a da sauri ta sauke hannun ido waje ta ke kallon Fanan da itama kallon nata take far far da ido khairat tay tace "what am i seeing kar dae kice man he has taken ur pride tun baku bar Kasar ba?" Sigh Fanan tay ta furta "dat's what i wished.." gwalo ido khairat tay ta maimaita abunda Fanan d'in tace cikin d'aurewar kai ta nuna kanta tace "but d wet hair..." tura baki Fanan tay kawae, cikin k'aguwa Khairat tace "pls tell me d truth abunda nike tunani ya faru ko?" D'an guntun tsoki Fanan tay kafin tace "uwar gulma to ba abunda ya faru khairat it nearly happened but he said it's improper to do it in a hotel room yanzu kin ji ko sai ki kyale ni pls" bud'a baki khairat tay sai kuma ta kyalkyace da dariya can tace "ai da kun fad'a man na baku keys d'in guest house d'in Dad sai kuyi shagalin ku a can ni ina nan ina aikin nemanki ashe kina can kina enjoying" harara Fanan ta galla mata ba tare data ce mata komae ba khairat d'in ta sake cewa "U know what gara da ba abunda ya faru asirinku a rufe don yadda mijin nan naki yake k'akk'arfa I am very sure if to say it has happened definitely u would come back with bow legs" tana rufe baki Fanan d'in ta kai hannu ta fara bugunta sosae ta mik'e da sauri tana fad'in bafa ita ta kashe zomon ba. Yana fita ya shiga Motan ya kai ta Parking space bayan ya parker ya d'auki d'ayar robar ice cream d'in da bata sha ba ya bud'e still akwae sanyi don lokacin da ya siyo shi a kankare yake a nutse ya fara sha don yunwa yake ji tun a Hotel d'in ma yaso su ci Abinci amman ganin dare yayi sosae yasa bai sa su tsayan ba, saida ya shanye shi duka sannan ya bud'e Motar ya fita ya nufi part d'inshi ta baya, yana shiga bedroom d'in ya had'a ido da Abbas dake kishingide jikinshi sanye da sleeping dress da alama bai dad'e daya kwanta bama yana ganin shi ya fara sakin wani shu'umin murmushi Haisam ya nufi edge d'in gadon ya zauna fuskarshi a sake Abbas yace "I thought can zaku kwana ai" d'age mashi gira yay ba tare daya ce komae ba, dagowa Abbas yay ya kai hannu gefen kafadar rigarshi inda jan bakin Fanan ya d'an goga ya bud'a ido yace "zargi na ya tabbata dae hope baka dae illata masu yarinya ba a Hotel H,zakee" hannu ya kai ya buge mashi hannu ya mik'e yana fad'in "We're Adult so we know what's right" daga haka ya nufi Toilet Abbas nata mashi dariyar shak'iyanci. Washe gari lahadi Abbas yaso su tafi to amman yana son ganin tashin su Haisam d'in hakan yasa yace ma su gwaggo sai washe gari in suka wace suma sai su d'au hanya tace Allah ya kaimu, Ranar Litinin Misalin k'arfe goma saura na safe su Haisam sun gama shirinsu tsab dam ba wani shiri bane sosae don daga su sai kayansu ita dama Fanan acan aka siya mata komae duk da gidan da zasu zauna Companyn da Haisam zaiyi aiki ne suka basu akwae komae a ciki amman duk da haka saida aka k'ara siya mata wasu abubuwan, Misalin k'arfe goma duk aka fito don rakasu Airport harda kakar Fanan da wasu daga cikin yan'uwansu da suka zo za'a tafi Farha ma taso ta bisu amman Hajiya Maryam tace ba yanzu ba sai in zata je sai su tafi tare gaba d'aya yan gidan dasu Abbas da gwaggo,kawu Amadu harda Saleem da Najeeb shima daga nan zai koma Lagos acan jirginsu zai tashi gobe dama bikin kawae ya kawo shi, Amarya Fanan na sanye da hadaddar jallabiya dark green ta fito mata da gasken ta sosae yayinda Haisam ke sanye da fararen suit bayan sun isa Airport d'in suka tsaya suna sake yin bankwana Farha sai kuka take yar uwa zata tafi suka rungume juna itama Fanan d'in hawaye take bayan ta saketa ta nufi Mommynta ta rungumeta sai lokacin tasa kuka sosae itama Hajiya Maryam d'in k'arfin Hali kawae take amman kad'an ya rage tasa kukan tana rungume da ita take k'ara jaddada mata fad'an da tayi mata game da rayuwar gidan Aure da biyayyar miji,haka dae sukae bankwana da kowa Senator ma ya k'ara yi ma Haisam nasiha kan Amanar Fanan da aka damka mashi ya tabbatar mashi da zai ruk'e Amanarta, saida ya rungume duk yan uwanshi su Laila Jidderh nata kuka haka su twins ya duk'a a gabansu yana rarrashinsu ya tabbatar masu in akae Hutu zai sa akawo su Jidderh na jin haka cikin muryar kuka tace "Big bro nima" ya d'aga kai ya kalleta da d'an murmushi ya jinjina mata kan, bayan ya mik'e ya nufi su gwaggo da Kawu Amadu yayi masu sallama duk sukai mashi fatan Alkhairi da godiya sosae ya kai idonshi kan Nameer dake ta sakin murmushi yace "Sarkin murmushi sai yaushe?" Yar dariya yay yace "ai ni nan zan zo in cigaba da karatu ba mun gama magana ba" jinjina mashi kai yay daga haka ya nufi Mahaifiyarshi ya kama hannunta duk ta shiga damuwa sai kace yau zai fara mata nisa, cikin breaking voice tayi mashi Addu'oi da fatan Alkhairi kafin suka rungume juna daga nan kuma Hajiya ya nufa ya tsaya gabanta suna ma juna murmushi ya kamo hannuwanta slowly yace "Thank u for everything Sweetheart, am gonna miss u....." bai ida ba ta fashe mashi da kuka ya jawota ya rungumeta sosae, yana matuk'ar k'aunarta kamar yadda take kaunarshi yadda yake jinta ko Mahaifiyar shi bai ji haka lokaci guda idanunshi suka canja yaso ta bishi amman ta k'iya ko jiya saida yayi mata Maganar to tama k'i zaman Abuja balle kasar waje, haka Fanan ma ta zagaya tay sallama da kowa shi Dad d'inta ya koma Lagos amman shima ya mata Nasiha kafin ya wuce kuma shi ganinshi a wurinta ba matsala bane don US gidane a wurinshi, bayan Haisam yayi sallama da kowa yan'uwanshi sannan ya nufi Abokanshi na Amana sukae mashi fatan Alkhairi kafin ya juya ya tafi sai kuma ya dakata ya kira Abbas ya nufeshi ya tsaya gabanshi idonshi akanshi shima Abbas d'in kallonshi yake yana jiran yaji mi zaice can yace mashi "Abbas pls ka kula da ZARAAH, i entrusted her to u yarinyar ta damu da nisan da zanyi pls make sure bata yi maraicin YA HANDSOME ba" yana kai k'arshen Maganar yaji wani abu mai kaman kwalla na son taruwa a idonshi tunowa da yadda suka rabu da sauri ya d'an d'aga masu hannu ya juya Fanan da sauran masu tafiyan suka rufa masu baya anata d'aga masu hannu masu kwalla nayi, nima dae nayi kwallan Ya Handsome d'in mu ya tafi😭Muna maka fatan Alkhairi. Uhmmmm, an gama Takun Farko da Sabon salo yanzu saura kuma An yanka ta tashi, amman fa ba wani abu nike nufi ba face Kaza aka yanka ta tashin🤣 _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2021* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 21 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .....Suna komawa gida su Abbas suka fara shirin tafiya dama tun jiya kowa ya kimtsa kayanshi ba 6ata lokaci sukae sallama da kowa aka rakosu parking space bacin an had'a masu sha tara ta Arziki Senator har 50k yaba kowanne na shan ruwa a hanya Nameer ma uban kaya yaba Kawu Amadu harda sababbi dasu takalma a cikin madaidaicin trolley sosae yayi mashi godiya d'an zaman nan da suka yi sun shaku sosae ji yake kaman karsu rabu gwaggo ma saida tayi mashi godiyar dama tun jiya ya bashi kayan, su Hajiya,Mommyn Haisam Hajiya Maryam,Laila,Jidderh,twins duk suka rakosu ana ta sake yin bankwana Farha dae na ciki tana aikin kuka dama kuma ko ba kukan take ba ba lalle ma ta rako sun ba, Hajiya ji take kamar ta bisu to amman Senator ya hana yace ba yanzu zata koma ba sai ta huta gajiyar biki Saude tun ran Asabar ta wuce ita da wasu yan'uwansu Hajiya na Daura Hajiyar ta hadasu sanin bazata koma yanzu ba Nana tabi wasu yan wurin aikinsu yanzu daga gwaggo sai Amadu Feenah da Abbas sai su Abdul. Tunda gari ya waye Fatuu keta faman farincikin su gwaggo zasu dawo har fuskarta ta kasa 6oye hakan dama duk kad'aicin su ya isheta kullum sai taje gidan tayi zaune, bata je Makaranta ba don kuwa jibi Laraba zasu fara Waec suna tashi bayan sunyi Karin kumallo Fatun tace ma Haulat tazo ta rakata taje ta gyara gida ta tambayi innarta tace suje, bayan sun koma gidansu Fatun zagewa sukae ba 6ata lokaci suka fara gyara ko'ina na gidan yay fes dashi bayan sun gama Fatuu tace su d'aura girki amman haulat tace mata ta bari sai d'an Anjima Abuja fa ba nan kusa bace in sukae da wuri zai iya dankarewa a cikin kula tace to su je bakin hanya su siyo Nama da zasu sa a Abincin haulat tace to, basu wani dad'e ba suka dawo suka zauna a Parlor suna kallo can Fatuu ta tuna da sauran cin cin d'in da gwaggo tay mata taje ta de6o masu suka had'a da lemu suna sha, bayan wai lokaci Fatun ta kira gwaggo ta tambayeta ko sun taho tace mata eh gasu a hanya ta shiga yi masu Addu'oi gwaggon na amsawa tana yar dariya don daga yadda taji muryar Fatun akwae tsantsar farinciki a cikin ta, tana gama wayar tace ma Haulat su d'aura girkin yanzu don suna hanya tace to ta mik'e suka nufi kitchen suka fara shirye shiryen abunda zasu dafa, zuwa Bayan Azahar sun gama dafa Abincin wanda Farar shinkafa ce da miya dama suna da cefane a cikin d'an fridge d'in gwaggo na kitchen harda Coleslaw suka had'a da suka je bakin hanya suka siyo harda kayan had'in shi saidae yanka su cabbage d'in kawae sukae basu ida hadashi ba gudun lalacewa ko mayonnaise din ta saki sun bari sai sun iso sai su had'a, bayan sun gama Fatuu ta tafi kai markaden Aya da dama sun gyarata don tasan gwaggo na son kunun Aya bata dad'e ba ta dawo suka hau had'awa sai kamshi ke tashi dama Fatuu ba dae iya Abinci ba komae ta koya a wurin gwaggo haka 6angaren na yan gayun ma duk ta koya a wurin Saude, zuwa k'arfe ukku duk sun gama komae haulat taci Abinci ta koshi ita kuwa Fatuu wai sai sun dawo ba yadda bata yi da ita ba amman tak'i ci k'arshe ta kyaleta tay kwanciyarta ta hau yin bacci ita kuwa Fatuu zaune tay duk bayan lokaci take kiran layin gwaggo taji sun kawo ina wani lokaci ta samu layin wani lokaci ace out of reach can dae da yunwa ta isheta taje ta zubo Abincin kad'an ta ci kafin ta wuce toilet tayo wanka lokacin data fito an fara kiran sallar la'asar ta yi Alwala ta wuce d'aki, ubansun leshi tasa riga da skirt sabbi dal farko kamar karta sa kayan don acikin kayan da Haisam ya yi mata ne sai kuma wata zuciyar ta raya mata in bata sa ba zubar dasu za'ai kuma shi ai ba sanin bata sa ba zai yi hakan yasa ta sanya kayan, tayi kyau sosae bayan tayi Salla harda yar light make up tayi yaushe rabo ita kanta taga kyaun da tayi tay tsaye a gaban mirror tana ta sakin murmushi kafin ta koma Parlor ta tashi haulat koda ta tashi bin Fatuu tay da kallon mamaki tace "k'awata kinga kyaun da kikae kuwa wllh sai kace Amarya" wani kallo tay mata mai kaman harara tace "ke kika d'aura man auren ko" haulat na dariya tace "Eh mana keda Ya Haisam" nan da nan fuskar Fatun ta canza ta daureta sosae Haulat na ganin haka ta hau bata Hakuri tana fad'in wasa take mata amman dae tana fata daga haka ta mik'e ta fita itama sallar taje tayi tana gamawa tayi wanka dama ta taho da kayan da zata canja, koda Haulat ta fita daga parlon lamo fatuu tay tana juya Maganar haulat d'in ta tana fatan ta zamo Matar Ya Haisam to ta ya ya? Fatun ta jefi kanta da tambayar ita yanzu ta riga ta fidda ran ma samunshi matsayin miji lokaci guda ta tuna da sakonshi data gani jiya da safe a ranta ta ayyana yanzu bai ma da lokacin kirana kada matarshi taji haushi haka ta dingi tunane tunane can da ta ga abun na neman yay yawa sai ta mik'e ta hau k'ara gyara gidan tasa turaren wuta, har Magrib ta gabato basu iso ba Fatuu na zaune jigum a falo har ta fara damuwa haulat na toilet bayan ta fito ta nufi Parlon k'arar tsayawar Mota da taji a kopar gidan yasa ta fasa shiga Falon ta nufi hanyar waje tana lekawa taga sune da sauri ta koma cikin gidan tana fad'in "Fatuu gasu sun iso...." tun kafin ta rufe baki Fatun ta fito da gudu kallabinta a hannu ko ta kan Haulat bata bi ba tay kopar gida daidai lokacin duk sun fito daga cikin Motar da gudu ta nufi gwaggo ta k'ank'ameta tana fad'in "ga gwaggota ga gwaggota" dariya sosae gwaggon keyi itama tana fad'in "ga Autata ga Autata" duk suka ba su Abbas dariya Haulat ma dariyar take tayi a gefe guda, Boot Amadu ya bud'e ya fara shigar da kayayyakinsu dama su kadae suka rage don an sauke Feenah Saboda tafi kusa da shigowa gari, bayan Amadu ya fito ne yace ma su gwaggon to su shiga ciki mana sai ta maida ita ciki ma kawae gwaggon na dariya tace ai sai ta maida tan daga haka ta juya ta kalli Abbas dake tsaye ya dafa kopar Mota ta shiga yi mashi godiya da Addu'oi da fatan Allah ya huce gajiya tace sai tazo k'ara yin godiya har gida a gaishe mata dasu Abdul yana dariya yace ai ba komae suka juya yana ta kallon Fatuu itama murmushi kawae take mashi ba tare data ce mashi komae ba Amadu ma yay mashi godiya sosae ya nufi gida har sun kusa shiga gida Fatuu ta juyo ta dawo ta tsaya gefen Motar tana kallon Abbas da har lokacin yake defe da kopar Motar yana mata Murmushi, shiru tay ta kasa mashi Magana don Haisam kawae take gani sai yan kyafcen kyafcen idanu take tana d'an motsa baki, "Mom Zarah kina lafiya?" Jinjina mashi kai tay kafin a Hankali tace "lafiya lou kun dawo lpy?" Kai ya d'aga mata kafin yace "ya shirye shiryen Waec yaushe zaku fara ne?" Tace "jibi zamuyi paper d'in physics practical sai Islamic da yamma" jinjina kai yay ya d'an yi shiru tana bin shi da ido can taji yace "Ya damuwar ta rage ko?" d'an tura baki tay kaman bazata ce komae ba ganin ya kafeta da ido yana murmushi yasa tana tura baki tace "eh na daina damuwa ai shima ya yi Aurenshi ya manta dani da yana kira na amman yanzu ya daina" da alama abun na mata ciwo shi kuwa Abbas fad'ad'a murmushin shi yai cikin ranshi ya ayyana kishi kumallon mata ganin murmushin da yake yasa ta sadda kanta k'asa ita kanta bata san ya akai tayi Maganar ba ji tay ya kira sunanta ta d'aga kai ta kalleshi yace "kiyi hakuri amman ba haka H,zakee yake ba shi mutum ne mai damuwa da wanda ya damu da shi in dae yasan kuna gaisawa ya jika shiru yana tuntubar mutum yaji ko lpy ke kanki ba hakanan ya daina kiranki ba hidima ne yayi yawa amman nasan da ya zama well settled zaki ji daga gareshi ke ai yar gatan shi ce kina d'aya daga cikin mutanen da ya damu dasu sosae hakan ma ne yasa ko yau kafin ya bar Kasar saida yay Maganar ki" d'an bud'a ido tay ya jinjina mata kai alamar tabbatar mata da abunda yace kasa jurewa tay tace "to miya ce game da ni?" Yana murmushi yace "ya bani Amanarki ne yace kar na bari kiyi maraicin shi" zaro ido tay sai kuma tay yar dariya tace "to sai ka dawo gidan Hajiya kenan" dariya kawae yay itama tay shiru tana maimaita Maganar da Abbas d'in yay cikin ranta har taji sanyi don da tayi tunanin ya manta da ita ne, "Akwae Account da yace man a bud'e maki so ki fad'a a gida zuwa gobe da safe sai muje kafin ku fara exams d'in" taji Abbas d'in ya fad'a idonta akanshi ta d'an tura baki tace "Account d'in me kuma?" Da murmushi yace "Bank Account mana yana bukata ne nasan Saboda ya samu sauk'in turo maki kud'i ne" yamutsa fuska tay kaman zatai kuka tace "to ai ya bani kud'i masu yawa da zai tafi ni bani buk'atar wasu kud'i" Abbas yace "ke da zaki cigaba da karatu aikuwa kina buk'atar kud'i sosae Mom Zaraah our future Doctor, ai dama kin bishi can kin yi karatun cikin sauk'i" wani kallo tay mashi tace "kam Matarshi taga na lik'ewa mijinta ta koro ni, nima bazan ma je ba" dariya yasa ganin yadda tay Maganar kafin yace bari ya wuce Magrib ya kusa ya tambayeta tana da passport guda biyu tace eh ganin yana k'ok'arin shiga Mota tace "Ya Abbas ka tsaya kaci Abinci sannan ka tafi" dakatawa yay ya kalleta yace mata kar ta damu sun ci Abinci a hanya kuma gida zai koma zai ci acan" tura baki tay a shagwa6e ta langa6ar da kai tace "ni dae don Allah ka tsaya kaci nifa na dafa shi" k'ura mata ido yay yana murmushi acikin ranshi yake ayyana yanzu ya gane dalilin da yasa suka shak'u da Haisam sosae sam in kana magana da ita baka jin ka k'osa komae nata nada burgewa katse mashi tunani tay da fad'in "Ya Abbas zaka ci ko don Allah?" Sigh yay yace "Ok ki zubo man in tafi dashi sai in ci a gida yanzu Magrib ya kusa amman fa bada yawa ba" washe baki tay alamar taji dad'i tace to ta juya da sauri ta d'aura kallabin saman kai ya bi bayanta da kallo har ta shige hakanan shima yana son ta da Haisam don ba k'aramar fahimtar juna za'a samu ba tsakaninsu ba ita kanta yanzu yadda akanshi ta fara sanin so to ba lalle ta so wani Namiji har ta samu natsuwa da shi kaman haisam d'in ba to amman yasan kasancewarsu tare matsayin ma'aurata ba k'aramin abu bane gashi yasan Haisam baida ra'ayin mata biyu saidae hakan ba matsala bane don yasan Mutane masu irin ra'ayin nashi wanda yanzu suna da mata fiye da d'ayan amman kuma ita kanta Fanan zata iya zama shamaki kan hakan don Ya fahimci ba k'aramin kishi zatayi ba a k'arshe ya yanke duk hakan k'aramin abu ne a wurin Ubangiji in dai ya kaddaro masu zama ma'auratan, rungume da Warmers babba da k'arama ta fito sai Leda yar babba ruk'e a hannun ta sak'o robobin kunun Aya da Coleslaw tana ta washe mashi baki ta nufeshi bud'a ido yay lokacin data k'araso yace "Mom Zarah wannan ai kin kwaso man Abincin yayi yawa" bata ce komae ba ta bud'e kopar baya ta saka Warmers d'in da ledan bayan ta rufe tana dariya tace "ai ba naka bane kai kadae harda Abdul da Aunty Feenah na zubo mawa in kuka ci ina jira ka fad'i man yayi dad'i ko bai yi ba" yana dariya ya jinjina mata kai kawae ta juya tana ce mashi sai Allah ya kaimu yace Ok zai kirata ya fad'i mata time da zasu fita daga haka ya shige Motar ya tafi. Tana shiga d'akin gwaggo ta nufa lokacin tana cikin cin Abincin da Haulat ta zubo mata ta nufeta ta zauna ta jingina da jikinta a Shagwa6e take fad'in "shine kuka je kukai zaman ku bacin tun ran Juma'a aka d'aura Auren baku damu da kun bar ni ni kadae ba ko" dakatawa gwaggo tay tana dariya tace "to ayi hakuri auta kamawa tay nima duk na damu da rashin ki kusa amman kuma dae ai nasan ba ke kadae na bari ba ko" tura baki tay haulat dae nata dariyar yadda Fatun keta shagwa6a, yabon Abincin gwaggo ta shiga yi da yadda suka gyara gidan tace sunyi kokari sosae hakan yasa ta warware ta fara dariya cike da tsokana gwaggo tace "shiyasa bani da wani shakku akan ku in ku kai aure" turo baki Fatun tay tace "in dae tay aure" gwaggo tace "kema ai zaki yi ne ko an dingi karatun ne ba ranar gamawa?" Tace "ai kona gama ni bazan yi aure ba" da sauri gwaggo tace "ba Amin ba ban fata in ma kina cikin karatun Allah ya kawo Nagari ai aurar dake zanyi kawae Kya idasa a d'akin mijinki" shiru tay kawae cikin ranta tana ayyana da nasamu wanda nike so ma kafin in fara karatun zanyi aure na kallon haulat tay suka had'a ido tay mata Murmushi ita kuma ta tura mata baki, Bayan Magrib duk sunyi salla gwaggo ta kwala masu kira suka shigo d'akin suka zauna ta janyo wata katuwar jaka cikin kayan da suka zo dasu ta tura ma Fatun tace "ga sak'on Yayanki nan tunda bazaki tambayeshi ba da Auntyn taki Amarya, d'an kallon juna sukai ita da Haulat cikin kama kai tace "ai na tambayi ya Abbas ne fa shiyasa banyi maki Maganar ba" gyad'a kai tay Haulat ta kai hannu ta bud'e jakar wadda ta bikin ce mai d'auke da sunayensu a cikinta ma duk tarkacen souvenirs ne da aka rarraba a bikin kaya jibgi guda sai kace d'an gidansu ne yay auren ai ko d'an gidansu ne bazata samu rabin su ba ma, wata k'atuwar Calendar Haulat ta fiddo ta bud'e har bata san lokacin data furta "Wow! Gaskia sunyi matuk'ar kyau wllh" gwaggo ta amshe da fad'in "ah ai ba'a cewa komae Haulat sai Mutum ma yaje hidimar abun sai san barka wllh amman an yi matuk'ar kokari kowa yabo da fatan Alkhairi yake masu" Haulat dake murmushi tace "Allah ubangiji yasa Alkhairi ya basu zaman lafiya" gwaggo ta amsa da Amin Fatuu ma ta amsa a hankali duk jikinta yay sanyi lakwas, mik'a mata Calendar d'in Haulat tay kaman bazata amsa ba sai kuma ta amsa ta zuba mata ido Haisam kawae take kallo sun yi kyau iya kyau hoto ukku ne a jiki babba na sama sai biyu a k'asa gefe da gefe sunyi shiga daban daban ta Alfarma dake nuna mawadatan Mutane ne ko ina Fanan tayi dariya shi kuma d'an Murmushi yayi wuri d'aya ne yay yar dariyar da har dimple d'inshi ya lotsa da sauri ta mik'a mata Calendar din jin kwalla na niyyar taruwar mata a idanu, Haulat taci gaba da fiddo abubuwa harda jakunkunan kwali suma masu d'auke da pic dinsu gwaggo ta sake janyo wata jakar ta fiddo yan buckets masu kyau guda ukku suma dai na bikin ne tace ma Fatuu ga kuma sak'on Hajiya suma haulat ce ta bud'e marfinsu d'aya dublan ne d'aya cincin da doughnuts d'ayan kuma Alkaki ne da cake gwanin sha'awa d'an murmushi tayi ta tambayi gwaggo ita sai yaushe zata dawo tace bata sani ba amman zata d'an kwana biyu, suna haka Amadu ya shigo ya zauna hiran bikin ya shiga yi masu harda pictures da Vedios ita dae Fatuu zugudum tayi Haulat nata washe baki tana tsuma had'i da yabawa sai faman zuzuta bikin yake da gidansu ya Haisam d'in da gaba d'aya garin Abujar don sun fita da Nameer ya zaga gari dashi bama sau d'aya ba gaba d'aya jikin Fatuu yayi weak lokaci guda ta yanke tun farko sunyi kuskuren da har sukae tunanin Haisam zai so ta don kwata kwata ba ajinta bane ma, sai da akayi isha Haulat tace zata tafi gida gwaggo ta d'ibar mata abubuwan bikin tace ta kai ma Innarta ta kuma bata kud'i farko K'in amsa tay saida gwaggon tace yaushe suka fara wasa irin haka sannan ta amsa tayi godiya itama Fatuu ta d'ibar mata komae cikin nata ta rakata har gida koda innarsu taga abubuwan da aka bata sosae tay godiya har tana zolayar Fatuu tana cewa da yake fa gwaggo ta dawo gashi nan tana ta fara'a yanzu ita dae yar dariya kawae tay daga baya tay masu sallama haulat ta rakota bakin lungu ta tafi, da wuri gwaggo tay bacci ita kuma sam baccin ya k'aurace ma idanunta tay zaune saman gado ta tasa Calendar d'in tana sake kallo bata yi kuka ba saidae wata irin kewar Haisam d'in take ji k'arshe ta kwanta hannunta kan fuskarshi tana shafawa tana d'an murmushi mai ciwo tunowa da abubuwa da dama a haka dae har bacci yay awon gaba da ita.Washe gari tana cikin yin Breakfast Abbas ya kirata yace wurin 11 zai zo ya d'auketa ya d'an shiga Jami'a ne tace to sai lokacin ta tuna bata ma fad'i ma gwaggo ba dama suna tare a falon ta sanar mata godiya ta shiga yi da yima Haisam d'in Fatan Alkhairi tace tay sauri ta shirya kar lokaci ya k'ure yazo ta 6ata mashi lokaci ta amsa to ta mik'e, kafin lokacin ta gama shiryawa cikin doguwar rigar Atamfa ta d'an yi yar light make up k'arfe 11 saura yan mintuna yazo ta yafa gyalen da suka hau da kayan da takalma ta d'auki yar jakarta ta fita saida ta lek'a tace ma gwaggo sun tafi sannan ta nufi wajen, lokacin data isa bakin Motar kwankwasa glass tay ya bud'e yana sanye da jeans da t-shirt ta d'an lek'a tana murmushi tace gaba zata shiga ko baya sosae ta bashi dariya jin tambayar da tayi shima ya tambayeta a Motar ya Handsome ina take zama ta nuna mashi gaba yace to nan zata zauna sannan ta bud'e Motar ta shiga tana yar dariya ta gaidashi tay mashi ya gajiyar hanya ya amsa sannan yaja suka tafi, basu wani 6ata lokaci mai tsawo ba a Bank d'in aka gama mata komae bayan sun fito gari ya d'an zagaya da ita saida ya tabbatar ta warware sosae dama Abbas d'an barkwanci ne sosae yake ta saka ta dariya har tambayarshi tay game da Abincinta yace yayi dad'i sosae Feenah ma da Abdul sun yaba har santi sukae sosae ta washe baki can tace to in mark zai bata nawa zai bata, d'an jimm yay sai kuma yace "zan baki 95%" d'an jujjuya kai tay tace "Gaskia Ya Abbas ban yarda ba ka cike man 5 marks d'in kawae mana ba kace har santi su Aunty Feenah sukai ba" yana dariya yace "No bazan baki 100 ba da dai a gidan mijinki kika yi shi confirm kin cancanci 100%" d'an murmushi kawae tay bata ce komae ba, a wani Eatery ya tsaya yace suje suci Abinci batare data musa ba tace to suka nufi ciki ya tambayi abunda zata ci bayan sun zauna tace "Burger and ice cream" yar harara ya wurga mata kafin yace "I mean Abinci ba kayan kwad'ayi ba" tace "to ai suma Abincin ne tunda ana koshi" girgiza kai yay yace ta dai fad'i Abinci a shagwa6e tace "ni dai su nike so inna koma gida naci Abincin...." Tun kafin ta rufe baki ya fara girgiza mata kai kaman zatai kuka tace "Wayyo bafa haka Ya Haisam ke man ba dana fad'i abunda nike so yake man kuma kace Amanata aka baka fa" dariya sosae yasa yace shikenan yaja ma kanshi dama bai fad'i mata ba dariya itama take yasa akawo mata abunda take so d'in shima ya fad'i abunda za'a kawo masa, bayan duk an kawo masu suna cikin ci wayar Abbas dake gefenshi ta fara ringing ya kai idonshi kan screen d'in yana ganin mai kiran ya dakata yana murmushi ya kai hannu yay picking kafin ya karata a kunnanshi yace "Latest Ango Mutanen US....." Jin hakan yasa Fatuu ta kalleshi da sauri............ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2022* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 22 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .......wayar Abbas dake gefenshi ta fara ringing ya kai idonshi kan screen d'in yana ganin mai kiran ya dakata yana murmushi ya kai hannu yay picking kafin ya karata a kunnanshi yace "Latest Ango Mutanen US....." Jin hakan yasa Fatuu ta kalleshi da sauri yaci gaba da fad'in "Mutanen Waje ya gajiyan hidima da tafiya" Haisam d'in ya amsa mashi da Alhamdulillah cigaba da fira su kae har Abbas d'in na tambayar shi lokacin da zai ci gaba da aiki yace sai Next week Abbas yace "Allah ya kaimu" amsa mashi yay da Amin ya d'an yi shiru Abbas d'in yace "gani tare da Mom Zaraah mun dawo daga bank an bud'e Account d'in amman mun tsaya Eatery muna cin Abinci" yar dariya Abbas d'in yay jin amsar da Haisam d'in ya bashi yace to, daga haka ya cire wayar Fatuu dake kallonshi lokaci guda ta yanke a ranta koma yace a batan ko bai ce ba, ita dama tasan ya daina damuwa da ita ne kawae don yayi Amarya tana cikin zancen zucin taga Abbas ya mik'o mata wayarshi yace gata, bin shi da ido tay yace "Vedio call ne zaku yi da Ya Handsome d'in ki" yay Maganar yana yar dariya jiki mace ta mik'a hannu ta amshi wayar kafin ta kalli screen d'in har saida gabanta ya d'an fad'i da suka had'a ido dashi, yana zaune kan leather sofa ya d'an kishingid'a jikinshi sanye da armless data bayyanar da suffarshi abunka da zuciya tuni Fatuu taga ya canja mata yayi mata wani irin Fresh, bin shi da ido tay ta kasa ce mashi komae Abbas dae ya ci gaba da cin Abincin shi, "Zaraah ina wuni" ta ji cool voice d'inshi ta fad'a, d'an tura baki tay ta d'auke idonta don tasan da biyu yace haka can ta sake kallonshi taga still kallonta yake cikin shaky voice tace "..ina wuni, an je lpy" shiru yay mata ta fara yamutsa fuska ta k'ara gaidashi ya k'ara yin shiru d'an tura baki tay kaman zata sa kuka tace "to kayi hakuri" wani d'an guntun murmushi yay dama da biyu yak'i amsawa just yana son ganin reaction d'in da face d'inta zatai displaying, bin shi da ido kawae tay can yasa hannu ya shafi beard d'insa yace "ina fushi dake" da sauri tace "to mi nayi maka?" "An d'aura man Aure but u couldn't call and rejoice wit me" d'an motsa baki tay ta sadda kai tabbas bata kirashi ta taya shi murna ba kuma har Haulat saida tace mata ta kira shi amman ta k'iya, d'agowa tay a hankali still kallonta yake duk ta kame kanta cikin rawar murya tace "to don Allah ka yi hak'uri Ya Haisam dama inata so in kira" d'an ta6e baki yay baice komae ba ta tura mashi baki fuskarta a yamutse alamar ya tanka amman yak'i cewa komae sai kallonta yake kawae sai da ya ga dama sannan ya tambaye ta ya Exams tace mashi Alhamdulillah yay mata fatan Alkhairi ta amsa sai lokacin ta tambayeshi ya Aunty Fanan yace tana lafiya daga haka yace zasu yi magana ta d'aga mashi kai ta mik'a ma Abbas wayan yana amsa yace "wai ina Amaryar ne ta barka kai kadae zaune"? Ya bashi amsa da tana Bedroom cike da jan Magana Abbas yace "d'anyen aure amman kai kana Parlor ita tana Bedroom ko har kun fara fad'a ne" yar dariya Haisam d'in yay jin wata magana ta Abbas d'in sai kace wasu k'ananun yara wai har sun fara fad'a sigh yay yace mashi tana hutawa ne bata jin dad'i, d'an buda ido Abbas yay kafin yace "Subhanallahi mi ya same ta ne naga lafiya lou ku ka tafi" bin shi da ido yay kawae Abbas d'in ya k'ara tambayar shi abunda ya same ta yasan in ba fad'i mashi yay ba bazai k'yaleshi ba hakan yasa shi ce Masha is Nausea daga tafiyan da sukai amman duk da haka saida Abbas d'in yace "amman dama tana hakan naga ta saba hawa jirgi sosae fa" ya k'are Maganar yana guntse dariya Haisam d'in yace zasu yi magana da sauri Abbas yace "No yakamata mu gaisa ai muyi mata ya jiki ga ma Mom Zarah itama zata gaidata" ya d'aga ido ya kalli Fatuu yace "Auntyn ki ce bata lafiya zaki gaidata ko?" Tura mashi baki tay yay yar dariya ya maida idon kan screen d'in yace ma Haisam Zarah zata mata sannu ya kai mata laptop d'in ya amsa da Ok kafin ya yunk'ura ya mik'e, had'add'an Bedroom ne mara hayaniya sosae komae na cikinsa fari ne tass sai d'an ratsin baki kadan a wasu wuraren, tana kwance ta kudundune cikin lallausan farin bargo ya tunkareta saida ya aje laptop d'in ta kalli can gefe kafin ya fara tada Fanan d'in a hankali ta fara motsi kafin ta yaye bargon daga fuskarta suka had'a ido, yar harara ta wurga mashi tana kokarin rufe fuskar k'asa k'asa yace Abbas ne zasu mata sannu shi da Zarah wani kallo ta wurga mashi tun kafin tace wani abu ya riga ta fad'in it's connected yay mata nuni da laptop d'in da ido, shiru tay ta fasa yin Magana ganin bata da niyyar tashi yace mata "sit up" d'an yamutsa fuska tay dama fuskar duk a harmutse take tay jajir abunka da fara ga idanunta ma sun d'an kumbura da gani dai tasha kuka gashin kanta ma duk ya harmutse haka lips d'inta ma sun d'an kumbura suma, cikin disasshiyar murya tace "but u know I can't am feeling pain al over my body" kallonta kawae yake yana tuna gumurzon da suka sha da ita wanda gaba d'aya ita taja har yay losing control yasa ta jigata sosae sam baiji dad'in hakan ba don da bakinta ta rink'a gaya mashi she hates him tunda shi mugu ne baida tausayi duk da yasan Azaba ce tasa ta fad'in hakan abun ne ma ya isheshi yay zaune a Falo har ya kira Abbas d'in a waya don su gaisa ko ya rage damuwa, matsawa yay ya kai hannu ya taimaka mata ta zauna ta jingina da heardboard sai faman fad'in ahhh take bayan ya zaunar da ita ya kai hannu can gefe ya d'aukko mata hula yasa mata duk abun nan Abbas na jin su duk da bada sauti sosae suke Maganar ba shi dama yasan ba wani ciwon tafiya dake damunta sai kace yau ta fara tafiya ai koda ma tana yin hakan to badae har abun ya kaita ga kwanciya ba ashe mazan gaske taji ya ayyana a mind d'inshi, juyo da laptop d'in yay ta kalli screen d'in suka had'a ido da Abbas dake mata murmushi itama da k'yar ta d'an yi mashi na yak'e yace "sannu Amaryarmu ashe baki ji dad'i ba yanzu yake fad'a man wai Nausea na damunki" d'aga ido tayi tay ma Haisam dake tsaye ya goya hannuwanshi a broad chest d'inshi wani kallo kafin ta kalli Abbas tay murmushi kawae bata ce komae ba yace ga Zaraah zata gaidata ta d'aga mashi kai ya mik'a ma Fatuu wayar kaman bazata amsa ba amman ba yadda ta iya ta kar6i wayar ta kalli Screen d'in suka had'a ido da Fanan kafin tace wani abu Fanan d'in tace "Zaraah how are u?" A hankali tace mata lafiya lou kafin tace ya jiki ta amsa mata da da sauki, shiru Fatun tay tana ta kallonta ita kuma sai d'an yatsine yatsine take tana sa hannu tana dafa forehead d'inta can ta kalli Fatun tace "naga baki zo biki ba gwaggo ta fad'a man kina Exams" jinjina mata kai Fatun tay tace Allah ya bada sa'a ta amsa da Amin daga haka ta mik'a ma Abbas wayar shima ya k'ara yi mata Allah ya sawake Haisam na d'auka yace mashi zasu yi magana kawae yay disconnecting don yasan halinshi yana iya mashi wata Maganar da bata kamata ba a gaban Zaraah, tun da su ka gama wayar taji komae ya fita mata a rai zuciyarta harta yanke mata Fanan d'in ciki ne da ita don tana jin k'awayenta in suna ma wad'anda zasu yi aure cikinsu da sun gama Makaranta Addu'ar Allah yasa suna zuwa first night su samu ciki wata tara su zo suna, Abbas ya lura da yanayinta da ya canza yace mata ta ida cinyewa su tafi ta d'aga mashi kai kawae haka ta rink'a turawa ba don tana jin dad'in su ba, bayan sun gama ya biya suka tafi ya maida ta gida kafin ta tafi yay mata fatan Alkhairi a jarabawarta tay mashi godiya sannan ta tambaye shi yaushe zai kawo mata Abdul wuni yace karta damu in ta gama exams in dae suka samu Hutu zai kawo shi yay mata hutun yanzu dae ta dage tayi karatu sosae Allah ya bada sa'a ta amsa da Amin daga haka suka rabu, koda ta shiga gida sosae tay yak'i da zuciyarta wurin kauda damuwa ta d'aukko littattafan da zata karanta ta fara karatu. Washe gari Laraba Misalin k'arfe tara na safe suka shiga paper d'in practical physics sam bata yi mata wuya ba duk da lokacin da aka rink'a koya masu tana cikin damuwa sosae amman kuma ta fahimta tunda tana da brain mai kyau, kafin lokacin da za'a gama ma ita har ta gama ta taimaka ma Haulat wurin da ta kakare ko da Malaminsu ya zo Lab d'in yay going around yana ganin yadda suke yi yana zuwa kanta ya duba da murmushi yace "Weldone Sp kinyi komae daidai" d'an murmushi tay yace ta d'an taimaka ma na kusa da ita wanda basu gane ba tace to amman tana tsoron supervisors dake cikin lab d'in kar tay laifi yace ba wani abu sun yi magana dasu, aikuwa sosae ta shiga taimaka ma sauran students tana nuna masu yadda zasu yi, bayan sun fito ne kuma ta rarraba ma wasu daga cikin k'awayenta abubuwan bikin Haisam da ta kwaso, zo ka ga yadda Students suka rud'e suna yaba kyaun da sukae wasu na cewa sun ji sanarwar bikin a Radio wasu a Tv, wasu harda Addu'ar suma Allah ya basu mijin Novel yayin da wasu ke tambayarsu su d'in Matan Novel ne da zasu samu mijin Novel haka sukae ta shak'iyanci sosae suke ta Fatuu dariya wata har tana ce ma Fatun itama tasan mijin Novel zata aura tunda tana da suffar Matar Novel ita dae dariya kawae tayi yayin da cikin ranta ta ayyana na samu kuma na rasa, har Malamai duk wanda yazo wucewa yaga Calendar d'in ko wani abu mai hotonsu sai ya tsaya ya tanka har discipline master d'insu da ya gani yace yana so shima aka bashi Calendar dasu jotter, basu koma gida ba a Cikin Makarantar suka ci Abinci har Abbas ya kirata yay mata ya Exams haka gwaggo ma da Kawu Amadu, k'arfe 3:00 suka shiga next paper ta IRS wannan ai ko awa ba'ayi ba ta gama ana fara amsa duk suka bada don itama Haulat d'in ta gama cike da farinciki suka koma gida. After 2 Months, A kwana a tashi ba wuya a wurin ubangiji, a yau su Fatuu na cikin tsananin farincikin da Allah ya nuna masu gama jarabawar su lafiya sai murna suke suna celebration don har anko sukae dogon skirt da yar top sai coat mai d'auke da year d'in da sukae graduation da department d'in da Mutum yay wasu sun sa himar wasu hula facing cap wasu kuma gyale sukae rolling sai d'aukar hotuna suke harda Malamai sukae d'an party, Fatuu ba tayi komae ba ta raba kaman da Jsce, gwaggo ta so yi mata abubuwa don har kud'i Haisam ma ya turo mata yace tay hidiman graduation d'in amman tace ma gwaggo duk asara ne ayi wani abun dasu kawae, tun wurin Azahar suka gama amman basu fita daga Makarantar ba sai wuraren La'asar a k'asa suka taho suna ta nishad'i ganin suna ta tafiya haulat tace mata ita dae gaskiya ta gaji amman Fatun tace aikuwa yau k'asa zasu je gida, suka ci gaba da tafiya har suka fara yin nisa sosae, suna cikin tafiya wata galleliyar Mota ta tsaya a gefensu da yake a gefen titin suke tafiya juyawa sukae a tare suka kalli Motar kafin suka juya don cigaba da tafiya kawae sai gani sukae glass d'in Motar ya fara sauka nan take sukae arba da mai tuk'a Motar wanda matashi ne zai iya kaiwa shekaru 28 haka wankan tarwad'a ne yana sanye da kananan kaya kuma da gani Hutu ya zauna mashi sosae, lek'o da fuskar shi yay da d'an murmushi yace "Barka dae yan graduation" Haulat ce ta tsaya ita kuwa Fatuu gaba tay abunta itama d'an murmushin tay tace mashi yauwa yace "I just passed sai na gan ku shine nace bari mu gaisa" tana murmushi tace sun gode d'an juya kanshi yay ya kalli Fatuu da tay gaba yace "ita friend en naki bata gaisawa da wanda bata sani bane" juyawa tay itama ta kalli Fatuu dake ta tafiyarta kafin ta maido idon kanshi tace "kusan hakane kasan ba kowa ake yadda dashi ba yanzu" yar dariya yay yace "hakane nima bai kamata in tare ku a bakin titi ba, in ba damuwa ki bani no d'in ita friend d'in taki sai in zo gida mu gaisa da ita" d'an jimm Haulat tay sai kuma ta juya ta k'ara kallon Fatun tunani ta shiga yi tasan ko ta bashi no d'in Fatuu aikin banza ne don ko ya kira ma ba saurararshi zatai ba don sam ta haramtawa kanta yin saurayi, dubara ce ta fad'o mata ta juya tace mashi "kayi hakuri ko na baka no d'in ba zatai maka wani amfani ba don ita d'in akwae sa rana a kanta dama da mun gama Makaranta za'ai bakin ta kuma gashi mun gama d'in to ba lalle ta saurare ka ba" d'an buda ido yay sai kuma yayi murmushi yace "Ok bansani ba ne amman ba wani abu Nagode sosae" tana murmushi tace to har zata juya yace su zo ya kai su subar tafiya cikin rana, juyawa tay da niyyar yi ma Fatun Magana kawai sai ta ga har ta tsaida masu Keke Napep kallon shi tay tace yayi hakuri ta riga ta tsaida masu abun hawa yace to ba matsala tace mata yana mata fatan Alkhairi Haulat d'in ta amsa da to daga haka glass din ya d'aga ita kuma ta tafi, lokacin da ta k'arasa Fatun har ta shige cikin Napep d'in itama sai ta shiga dama ita suke jira mai Napep d'in ya tambayi inda zai kaisu Haulat tace mashi Barhim sabuwar Abuja ya ja suka tafi, kallon Fatuu tay da yake mai Napep d'in ya kunna Wak'a tasan ba jin su zai ba tace "Wannan Mutumin fa don ke ya tsaya har cewa yay na bashi no d'in wayar ki sai ya kira tunda baki tsaya ba amman nasan ba lalle ki saurare shi ba shiyasa nay mashi k'aryar an kusa bikin ki" d'an ta6e baki Fatun tay tace "gwara da kika ce mashi hakan ya kama gabanshi don kuwa ba sauraran nashi zan yi ba" idon Haulat a kanta ta d'an girgiza kai tace "Wai Fatuu miyasa kike korar samari ne, da wuya mu fito ba'a samu wanda ya nuna yana son ki ba Amman sam kin k'i ki fara saurarar kowa komi kice karatu to karatu yana hana ayi saurayi ne ko kuwa zaki ta karatun ne ba ranar da zaki aure??" wani kallon gefe tay ma Haulat d'in ba tare da ta ce mata komae ba Haulat taci gaba "nasan duk Saboda Ya Haisam ne baki saurarar kowa ba wani abu ba, zuwa yanzu yakamata ki cire son shi kwata kwata a ranki kema ki tsaya ki samu wanda zaki rayu tare dashi kada kita korar Mutanen kirki ba tare da kin sani ba, ki yi hakuri in na 6ata maki rai amman gaskiya nike fad'i maki kaman yadda ya samu abokiyar rayuwa wadda yanzu na tabbatar bata rasa juna biyu kema ki fara tunanin sama ma kan ki wanda zaku rayu tare ki hak'ura da ya Haisam don matuk'ar yana ranki to fa bazaki ma kanki abunda ya dace ba shawara ce nake baki a matsayina na mai son cigaban rayuwarki" a hankali tace mata ta gode kawae don kuwa son Ya Haisam na nan a cikin ranta ta rasa ta yadda zata cire shi, suna haka wak'ar da mai Keke Napep d'in ya kunna ta k'are wata ta shiga ta Labarina baitikan wak'ar suka fara kaman haka 🎶🎶Dawo bamu gama zama ba, dama ba mu raba jini ba, wai nikam mai naiwa kauna bata mi ni wuri ba labari da kai ne dawo bamu gama zama_🎶🎶 _🎶🎶Ban gani duhu haka na kwana, yanzu ma hakan na ishi rana, damuwa ta damu da gani na gashi ta raba ni da wani na, mi nai wa kauna ne guna bata iya zama ba, yafe man in na mutu so ne bai gama salo ba...🎶🎶_ Natsuwa sukae suna sauraran wak'ar dama Fatun kusan kullum sai ta saurareta ji take tamkar ita a kai ma wak'ar lokaci guda kwalla suka fara zubo mata sharrr da sauri Haulat tace ma mai Napep d'in "Malam don Allah in ba damuwa ka canja wata wak'ar" yace "yanzu kuwa Hajiya ai dama don jin dad'in ku muke sawa bari a canja maku" ya kai hannu yana yana k'ok'arin canzawa ana fara taken wak'ar Fatun ta saki d'an murmushin takaici don kuwa itama wak'ar kamar dae waccan ita wannan ma jinta take kaman ita ta raira ma kanta ita ta hamisu breaker ce mai taken ' _so gaskiya ne yadda yay min ni na gane, in dai amo ne kanshi ban daina shi zancen gaskiya_🎶🎶 da sauri Haulat tace "Don Allah malam ka kashe wak'ar duka ta cika mana kunne" wannan karon juyowa yay yana niyyar yi mata Magana idonshi ya sauka kan fuskar Fatuu yana ganin kwalla yay d'an murmushi had'i da girgiza kai ya juya ba tare da ya ce komae ba a cikin ranshi ya ayyana ta Kamu da mugun ciwo ya kai hannu ya kashe gaba d'aya kaman yadda Haulat d'in ta buk'ata, suna gab da isa gwaggo ta kira Fatuu bayan ta d'aga ta tambayeta har yanzu basu taho bane don d'azun sun yi waya lokacin da suka gama Exams, ce mata tay gasu nan sun kusa isowa tace to ta taho harda Haulat ta amsa da to, dai dai gefen shagon Amadu dake a rufe mai Napep d'in ya tsaya suka fito bayan sun biya shi suka nufi cikin gidan mai Napep d'in ya bisu da ido a ranshi yake ayyana "Gata dae tubarkallah ko wani ya yaudareta ko kuwa wani take so ta rasa shi Allah kadae ya sani" daga haka yaja ya tafi, suna shiga cikin gidan suka jiyo Wak'a na tashi ta happy graduation Fateema Zarah a cikin falo da sauri suka nufi falon suna shiga sukae turus a bakin kopar da tsananin mamaki akan fuskokinsu gaba d'aya an k'awata falon da flowers da balloons cards da sauransu kaman dae irin decoration d'in birthday a bangon dake kallon Mutum in ya shiga an had'a rubutun Happy Graduation Fateema Muhammad Ardo and Haulat is'haq a tsakiyar d'akin kuma k'aton cake ne saman table da sauran abubuwan ci, da gudu Fatuu ta nufi gwaggo dake tsaye tana masu dariya ta kankameta cike da farincikin surprise da suka mata sakin ta tay ta nufi Kawu Amadu dake gefe shima ta rungume shi sai kuma ta fashe da kuka duk suka sa dariya Amadu ya hau goge mata kwallan yana fad'in yau ranar Murna ce don daga yau ne ta hau matakin cikar burinta ta jinjina mashi kai yace yana mata fatan nasara cikin muryar kuka tace ta gode haka Haulat ma saida gwaggon ta rungumeta duk suka yi mata fatan sa'a tana ta dariya tay masu godiya, ci gaba da celebration d'insu sukai su hud'u gwanin burgewa Fatuu sai rawa take da wak'arta da aka yi mata ba tare da ta sani ba hakan aikin Amadu ne yaba wani abokin shi yay mata kuma tayi dad'i sosae daga baya Fatuu da haulat suka yanka cake Amadu na masu Videos da iPhone d'in wani abokin shi da ya aro Saboda hakan, sosae su kae hotuna kuma sunyi matuk'ar yin kyau sai bayan Magrib sannan Fatuu ta raka Haulat bayan an d'ibar mata komae cake d'in ma mai yawa aka bata tanata godiya, Fatuu na dawowa tasa Kawu Amadu ya tura mata pics d'in da videos ta shige d'aki ta fara aikin d'aura su a Status kan kace mi aka fara mata comments na taya murna wasu ma duk suka d'auka suma suka d'aura sai farinciki Fatuu ke yi jin yadda ake ta yabawa har wasu Friends d'insu na cewa shine ko a gayyace su, tana cikin duba wad'anda suka d'aurata kwatsam taci karo da na Haisam da mamaki ta bud'e hoton farko wanda akai mata ita kadae a gaban rubutun cikin falon tayi dariya duk dimples d'inta sun lotsa sosae a k'asan shi ya rubuta 'Wishing u success in ur Exams beloved sis Zarah' na gaba kuma wani d'an short video ne tana ta dariya had'i da yin Magana sam bata ma san anyi mata shi ba can kuma ta tura yankin cake a baki duk ya 6ata mata gefen baki kai da ganinta a Videon zaka fahimci tana cikin tsantsar farinciki sosae tasa Dariya da ta ga Videon wato tun kafin Amadu ya turo mata ya tura ma Haisam, tana cikin hakan kuma sai ga kiranshi ta d'auka ta gaishe dashi bayan ya amsa yace mata congratulations tace mashi thanks waya suka cigaba da yi wadda rabon da su jima suna yin waya har ta manta har ta tambaye shi Fanan yace tana wurin aiki da yake su can rana ce tace shi yana ina yace shima yana wurin aiki k'arshe ma cewa yay bari ya maida Video call tace to dama akwae haske d'akin koda ya maida tana ta sakin murmushi shima haka suka ci gaba da yin firan har yana nuna mata Office d'inshi na can ta yaba sosae da had'uwar shi don irin manya Office d'in da take gani ne a Fina finan turawa. Bayan sati d'aya da yin candy d'in su Haulat tazo gidan ta sanar da ita zata tafi Nijar kuma bazata dawo ba har lokacin bakin ta dama a can za'ayi, Fatuu bata ji dad'i ba har tana ce mata ba sai bikin ya kusa ba sannan zata tafi tace itama tayi tunanin hakan to amman innarsu tace taje ta zaga dangi kafin bikin don ta dad'e bata je ba, Ranar Juma'a da zata tafi har tasha Fatuu da Kawu Amadu suka rakasu da yake da yayanta Usman zata tafi suna ta kuka suka rabu Fatuu tace mata sai sun zo biki, Allah sarki Haulat k'awar Arziki. Satin Haulat d'aya da tafiya lokacin ya kama satinsu biyu da gama Makaranta ran Asabar Fatuu ta dawo daga islamiyyar safe tana tafe tana ta tunane tunanenta da suka zame mata jiki don yanzu wani irin kad'aici ne ke damunta, ba Haisam ba Haulat gashi Hajiya har yanzu bata dawo ba balle ta d'an rink'a zuwa can a haka har ta k'araso gida tana shiga tun a zaure ta jiyo Muryar gwaggo cikin harshen fulatanci tana ta fad'a, lokacin da ta k'arasa a tsaye ta ganta gaban kitchen sai kai da kawowa take ga wayar Amadu kange a kunnanta tana yin waya, tsayawa tay tana bin ta da ido hakan ya bata damar jin Maganar da take a lokacin kamar haka "Sam bazan yarda ba wllh! Lokacin da aka bani ita ai ba ace man za'a rabani da ita ba hasali ma kowa ba son ta yake ba anata muzguna mata sai yanzu da aka ga ta zama Mutum shine za'a nuna man iko da ita, to bari kaji bazan ta6a yarda ta dawo ba sai dai komae zai faru ya faru na shirya ma hakan!!!" daga haka ta katse kiran ta juyo a fusace ta mik'a ma Amadu wayar kafin ta wuce d'akinta fuu tana ta kwafa, juyawa Amadu yay ya shige d'akinshi yayin da Fatun tay tsaye jikinta duk yayi sanyi yaushe rabon data ga gwaggo na fad'a haka sam ta kasa fahimtar inda zancen da ta ji tana yi ya dosa, har zata nufi d'akinta sai kuma ta juya ta nufi d'akin Amadu lokacin data shiga yana zaune a gefen katifa yayi jigum da alama shima abun ya dameshi sosae, d'aga kai yay ya kalleta ganin hakan yasa ta duk'a tana kallonshi itama, a sanyaye ta tambayeshi abunda ke faruwa, farko shiru yay mata yana dai ta kallonta saida ta marairaice mashi kaman zata sa kuka tana had'ashi da Allah sannan ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi yama rasa ta ina zai fara ganin dae ta zuba mashi ido ne yasa yay k'arfin halin cewa "Dama Baffan ki ne ya kira yace zai zo ya tafi dake wai Ard'o ya bada auren ki" wani bugu k'irjinta yay ta zaro ido tana kallonshi kafin cikin sark'ewar murya tace "y...ya bada au..aurena, ni...d'in???" Kai ya d'aga mata alamar eh, a razane tace "Waye ya ba aurena??" Shiru ya d'anyi shima duk damuwa ta bayyana akan fuskarshi can yace "Chairman Alhaji Lawal ya nema ma d'an shi wai Dr Khalid Auren ki tun lokacin da muka je shekara ukku da ta wuce shine ma yace a barki sai kin gama Secondary don da tun lokacin Ard'on yace ya bashi................ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wannan no 09013804524._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2023* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 23 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........bin Kawu Amadu kawai take da ido da alama tayi mutuwar zaune abun kaman a mafarki take jin shi wai ita za'a ma Aure kuma ma a garinsu, shima Kawu Amadun zugudum yay yana kallonta can ta yunk'ura da k'yar ta mik'e hannunta ruk'e da jakarta ta fita daga d'akin ta nufi d'akinta har wani Jiri Jiri take ji a haka ta isa tana shiga ta aje jakarta a gefe ta nufi bakin gado ta zauna sai zare ido take sam tama rasa tunanin da zata yi can zuciyarta ta fara tunano mata da Mutumin wato wanda ta iske a fadar Ard'o har ya rink'a mata tambayoyi da turanci ashe da biyu yayi mata hakan kenan,wai d'anshi Dr Khalid za'a aura mata! haka ta dingi maimaita sunan a cikin ranta tana haka wayarta dake cikin jakar islamiyya ta fara ringing da k'yar ta yunk'ura ta nufi jakar ta fiddo wayar kafin ta koma bakin gadon sai lokacin ta kalli screen d'in taga mai kiran nata, My Lovely Dad shine sunan da ta gani wato Baffan ta ne kenan, d'an jimm tayi cike da fargaba kafin hannu na rawa ta d'aga kiran ta kara a kunne kafin tayi Magana daga can yace "Inna wuro" har saida gabanta ya d'an fad'i kafin a hankali tace "ah Baffa", "Kin dawo daga Makarantar kenan Amadu ya fad'a man kina can" wani abu ta had'iya jin muryar shi ta canza sosae a hankali tace mashi eh ta dawo ta gaida shi ya amsa, shiru ya biyo baya daga ji yana son mata magana ne amman ya kasa, can tay k'arfin halin cewa "Baffa wai da gaske an bada ni za'a man Aure?" D'an jimm yay kafin ya fara Magana "Wallahi tallahi inna wuro wannan duk aikin Ard'o ne ni sam bansan da Maganar wai ya bada ki ba sai wata guda da ya wuce lokacin kuna cikin yin jarabawa shine ya kira ni yake sanar dani wai in fad'a maku ya bada ke ga yaron chairman kuma ya sanar mashi kun kusa k'are karatun naki don haka kuna gamawa in zo in d'aukko ki, Wllh inna wuro ranar banyi bacci ba Saboda tashin hankali ban k'ara shiga damuwa ba sai bayan da kuka gaman ya kira ni yace ai Chairman ya fad'a mashi kun k'are don haka in zo in d'aukko ki ranar gwuiwa na a k'asa na rokeshi da a kyale ki karatu kike son yi in kika yi za'a amfana sosae amman da bud'ar bakin shi sai cewa yay ina kokarin nuna mashi iko da ke abunda wani bai ta6a yi mashi ba, duk yadda na so in fahimtar dashi abun ya gagara don ce man yay ba don Alhaji Lawal d'in ya ce a barki ki k'are karatun ba ai da tun lokacin da ya nuna yana son a bawa yaron nashi za'ai maku auren yanzu kuma ba abunda zai fasu don har sadaki ya amsa yana wurin shi, tun ranar inna wuro banda cikakkar lpy wllh nasan kina son karatu sosae kuma muma duk muna so hakan yasa na kasa ma kira in sanar daku don wannan Auren dole ne....." D'an dakatawa yay yana maida numfashi dama tunda suka fara Magana ta fahimci canji a muryarshi, ci gaba da magana yay "bayan sati guda da yay man Magana ya ga ban zo na taho dake d'in ba shine ya tara yan gidan yana masu kukan na nuna mashi iko da d'iyata ina son bashi kunya to kowa ya shaida in dae na hana Auren bashi ba ni, nan abun ya zama abun Magana gaba d'aya aka tsangwame mu ni da iyali na ana ta maganganu dama suna jin haushi yadda Ardon ke d'aura ni akan komae nashi nan aka samu wasu suka zugeshi yace bai son in k'ara sa mashi hannu a harkokin shi, jiya naga tashin hankali inna wuro cewa yay in tattara in bar masa gida ya yafe ni kuma in har ban bari anyi auren ba Allah ya isan shi bai yafe man ba......" Karyewa muryarshi tay ya fashe da kuka, wani irin zaro ido Fatuu tay jin Mahaifin nata na kuka abunda bata ta6a gani ba ko ji da Hankalinta da sauri cikin rawar murya tace "Baffana kuka kake!!" Had'iye kukan yay yace "inna wuro har ga Allah ban son abun nan ban so wllh na fi so kiyi karatun ki zai amfanemu gaba d'aya in kika gama ko kuma kina cikin yi Allah yasa kina da wanda kike so ku ka daidaita sai ki yi auren ki amman ba ai maki dole ba, yanzu bansan ya zanyi ba" sosae jikin Fatuu yay wani irin mugun sanyi wani irin tausayin Mahaifin nata ne ya kamata lokaci guda taji ranta ya 6aci da abunda ake masa wani irin kwarin gwiwa ta ji ta samu tace "Baffana ka daina damuwa na yarda ayi man auren kazo ka d'auke ni!" murya na rawa yace "Inna wuro kin yarda kenan kin hak'ura da karatun?"d'an murmushin takaici tay kafin tace "Eh Baffa in dae hakan zai fitar da kai cikin halin da kake ciki to na hak'ura in Allah ya sa ina da rabo ko ba yanzu ba zanyi in kuma bani da rabon yi ko ba ai man auren ba bazan yi ba" sosae ya shiga yi mata godiya yana fad'in "Nagode, Nagode inna wuro yadda kika sadaukar da farin cikin ki Saboda nawa farincikin in sha Allahu ko ba yanzu ba kema zaki dawwama cikin farin ciki har k'arshen rayuwarki, Nagode Allah ya jik'an Mahaifiyar ki dama Aysha Alkhairi ce a gurina gashi nan har bayan ranta ina ganin Alkhairin ta..." Shesshekar kukan shi kawae take ji hakan yasa itama kwalla suka zubo mata sharrr saidae bata bari kukan yayi sauti ba don kar ya ji cikin breaking voice tace mashi don Allah ya daina kuka bata jin dad'in hakan da sauri yace to ya bari, can taji yace "yanzu ita gwaggon ki fa naga ta d'auki zafi da Maganar sosae" damm gaban Fatuu ya fad'i tunowa da yanayin da ta riski gwaggo tabbas ba k'aramin 6aci ran ta yay ba sai kuma ta ayyana k'ilan in ta nuna ta amince zata saukko hakan yasa tace mashi kar ya damu zata fad'i mata ta amince tasan zata saukko, sosae ya shiga yi mata godiya yana saka mata Albarka da harshen fulatanci tana Amsawa kafin ta tambaye shi yaushe zai zo d'aukan ta d'in yace zai sanar da ita ta fara shiri dae sannan zai tura na Amadu kud'i in akwae abunda zata siya na amfanin kitchen tunda yaga a birni jere ake mashi ta amsa mashi da to kafin suka yi sallama, k'ura ma wayar ido tay bayan ta cire ta daga kunnanta sai lokacin kuma ta fara tunanin anya bata yi gangancin saurin Amincewa ba kuwa, tasan waye za'a aura mata? tsuru tay tana ta faman zare idanu can kuma ta yanke koma waye zata aureshi ko don ta fitar da Mahaifinta daga halin da yake ciki don tasan dama can ana bak'in cikin yadda Ardo yafi ji dashi yanzu in ta k'iya sun samu abun da suke so, shiru tay tana tunanin yadda zata tunkaro gwaggo don wata irin shakkarta ce ta kamata can ta yanke bari ta bari sai Anjima lokacin tasan ta d'an huce, tana haka aka fara kiran sallar Azahar ta mik'e don yin salla lokacin data fito suka yi kacibus da gwaggon ta yo Alwala zata koma d'aki fuskarta sam ba walwala ko kallon Fatun bata yi ba ta wuce d'aki hakan ba k'aramin k'ara ma jikin Fatuu sanyi Yay ba, bayan ta gama sallar zaune tay a d'aki tana ta sak'e sak'e a ranta gaba d'aya gidan yayi tsit kai kace sakon Mutuwa aka fad'a masu kowa yana d'aki ko Abinci ba wanda ya nema kuma tuni gwaggon ta gama don lokacin data gama tana kitchen ne Amadu ya kai mata wayar, mik'ewa Fatuu tay ta fito ta nufi kicin ta zubo ma Kawu Amadu da shima tunda ya dawo daga Masallaci yana d'aki, lokacin da ta shiga ya d'an kishingida kan Katifar shi da alama tunani yake jin sallamar Fatun yasa shi kai idanunshi kopar shigowar, a bakin katifar ta aje plate d'in Abincin da d'an murmushi tace "Kawu Amadu ga Abincin ka" tashi yay zaune yana mata kallon mamaki ganin ta ba wata damuwa sosae a tattare da ita don ya d'auka zuwa yanzu tana can tasha uban kuka koma tana cikin yi, ganin kallon da yake Matan ne yasa tace "Baffa na ya kira ni yayi man bayanin komae kuma nace mashi na amince da auren" bud'a ido Amadu yay yana kallonta wit surprise written boldly all over his face don bai ta6a tunanin hakan ba ta cikin sauki surprisingly yace "yanzu kenan kin yadda ayi maki auren kin hak'ura da karatun?" D'an guntun murmushin takaici tay kafin cikin karewar murya tace "to Kawu Amadu ya zanyi Baffana na cikin matsala kuma zai k'ara shiga wata in har ban Amince ba don Ard'o yace ya bar mashi gida in dae bai zo ya d'aukko ni an Mani auren ba kuma wai bai yafe mashi ba...." Sai lokacin tasa kuka ba k'aramin sanyi jikin Amadu yay ba dama yasan ba yadda za'ai Baffanta ya goyi bayan hakan cikin sauk'i don kuwa duk Abunda Fatun ke so shima shi yake so, rarrashinta ya shiga yi yace ta daina kukan, sam bai son Al'amarin don bai dace ayi mata hakan ba ba kamar da Kamalu yayi mashi bayanin wanda za'a aura Matan d'azun da ya kira shi don jin Karin bayani, sauke nannauyar ajiyar zuciya yay kafin yace mata Allah ya za6a abunda yafi zama Alkhairi tace Amin, tambayarta yay ita ta ci Abincin tace a'a yace to suci tare, bayan sun gama yace ta k'aro masu farko tace ta k'oshi yace bai yarda ba dole ta k'aro suka ci bayan sun gama ta d'auke plate d'in ta maida kitchen har zata shiga d'akinta ta dakata tana kallon kopar d'akin gwaggo a ranta tana tunanin anya ma gwaggon ta ci Abincin don bata ga alamun ta d'iba ba can ta juya ta koma kicin d'in ta zubo mata ta nufi d'akinta lokacin data shiga tana zaune kan dardumar salla da alamu tunda ta gama sallar bata mik'e ba, amsa sallamar da Fatun tay ba tare data kalleta ba ta nufi gefenta ta duk'a ta aje plate d'in Abincin a sanyaye tace "Gwaggo ga Abinci ki ci" jimm tay kafin ta juyo ta kalleta har saida gaban Fatun ya d'an fad'i ganin yadda idanunta suka sauya kaman itama kuka tayi, ganin yadda fatun ke kallonta yasa ta d'an k'ak'alo murmushin yak'e tace mata ta gode Fatun ta mik'e ta bita da kallo har ta fita wani irin tausayin yarinyar ne ya kamata don duk a tunanninta Fatun bata san abunda ke faruwa ba, k'ara dawowa tayi ta kawo mata ruwa ganin bata ko ta6a Abincin ba yasa a marairaice tace "Don Allah gwaggo ki ci" fuskarta a sake ta d'aga mata kai alamar to, har ta juya taji tana tambayarta ita taci Abincin ne tace mata eh sun ci da Kawu Amadu kai ta k'ara d'aga mata Fatun ta fita ta koma d'aki ta zauna a bakin gado tana wasi wasin ko in ta gama taje tayi mata Maganar tana ta sak'e sak'enta ta d'an kwanta har bata san bacci ya kwashe ta ba saida akayi la'asar gwaggo tazo ta tada ita tace bazata islamiyya bane, ba 6ata lokaci ta shirya ta canja wasu Uniform d'in ta tafi, Bayan sallan isha lokacin Fatuu ta gama cin Abinci ta maida plate d'in kitchen bayan ta fito tay tsaye bakin kopar d'akin gwaggo tana sak'e sak'e can dae tay shahada ta shiga da sallama lokacin gwaggon na zaune kan sallaya hannunta ruk'e da cazbaha ta jingina bayanta da jikin gado tana lazimi, daga can gefe Fatun ta duk'a idon gwaggo a kanta ita kuma sai sussuna kai take ganin haka yasa gwaggo d'aga hannuwa ta shafa Addu'a kafin tace mata da wani abu ne, farko Fatun shiru tay ganin yadda gwaggon ta zuba mata ido yasa cikin rawar murya ta fara Magana "d..dama d'azun Baffana ya kira ni ya sanar dani abunda ke faruwa wai Ard'o ya bada ni za'a man Aure...." Wani murmushin takaici mai d'an sauti gwaggon tayi kafin a harzuk'e tace "ki k'yale ni da shi zan nuna masa nima ina da iko dake ba Ard'o ba ko lamid'o ne shi sai inda k'arfi na ya k'are wllh don ina ji ina gani bazan k'yale a lalata maki rayuwa ba har wani ne d'an chairman can" ta k'arasa tana huci ba k'aramin tashi hankalin Fatuu yay ba murya na rawa kaman zata sa kuka tace "A'a gwaggo don Allah ki yi hak'uri ki k'yale shi ni na Amince ayi man Auren....." Bata k'arasa sakamakon wata gigitacciyar tsawa da gwaggon ta daka mata tace "dum hetsi!!!" ba k'aramin firgita Fatuu tay ba har saida ta dan goce daga zaune jikinta ya hau kerma tana zare ido, a fusace gwaggon tace "a wodi hakkilo! tashi ki fita ki ban wuri!!" Fashewa Fatuu tay da matsanancin kuka ta hau bata Hakuri tana mata magiya akan ta Amince in ba haka ba Baffanta na cikin matsala Ardo tsine mashi zai yi, haka ta shiga fad'i mata halin da baffanta ya fad'i mata yana ciki gwaggon tay banza da ita kanta a k'asa can ta d'ago idanunta cike da tsantsar 6acin rai a kausashe tace "iyakata zaki nuna man Fatuu??? Da sauri ta girgiza mata kai tace "a'a don Allah gwaggo kar kice haka kawae ina son na fitar da Mahaifina daga halin da yake ciki idan aka hana Ard'o yin yadda yake so zai tsine masa ne kuma yace ya bar masa gida ma don Allah ki bari ayi man Auren kawae ni na hak'ura da karatun kuma dama kwanaki ba kince in ina cikin karatun ma na samu miji ba aurar dani zaki na idasa karatun acan gidanshi to ki barni don Allah gwaggo in da rabo sai in yi acan d'in" duk abun nan idanun gwaggo na akanta ta d'an kya6e baki can tay wani guntun murmushin takaici irin mai nuni da yaro yaro ne kafin cikin raunatacciyar murya tace "ki je kiyi duk yadda ranki ke so!" Tana niyyar sake cewa wani abun gwaggon ta mik'e a fusace tayi kanta tana fad'in "ki fita ki ban wuri shashasha...." Kasa k'arasawa tay sakamakon muryarta da ta karye kawae sai tasa kuka tana fad'in "ni ai da yake bani na haife ki ba shiyasa baki damu da damuwata ba" da gudu Fatuu ta nufi d'akinta ta fad'a kan gado tana wani irin kuka mai cin rae to itama dae gwaggo kukan tasa tay zaune a gefen gado ana cikin haka Amadu ya shigo gidan yana jiyo kukan Fatuu ya nufi d'akinta ko sallama bai yi ba ya kutsa kai jin yadda take kuka hankali a tashe ya shiga tambayarta abunda ke faruwa amman abu d'aya take fad'i shine "Gwaggo ce...." Cikin rashin fahimta yake tambayarta mi gwaggon tayi mata ganin bata da niyyar bashi amsa yasa shi fita ya nufi d'akin gwaggon sai dae ba shiri yay turus bayan ya shiga d'akin ganinta zaune tana ta matsar k'walla jiki a mace ya k'arasa gabanta ya duk'a bisa gwiwowinshi idanunshi har sun kawo kwalla, dafa knees d'inta yay cikin rawar murya yace "gwaggota Mike faruwa kike kuka" shiru bata bashi amsa ba bata kuma kalleshi ba, hawayen idonshi ne suka fara sauka ya fara mata magiyar ta fad'i mashi abunda ke damunta can ta kalleshi cikin muryar kuka tace "ni Fatuu zata watsa ma k'asa a ido ina k'ok'arin kwatar mata yancinta amman ta nuna man iyakata duk irin kokarin da nike akanta amman ta kasa bani goyon baya Saboda ni bata damu da farin ciki na ba..." Sosae tasa mashi kuka ya mik'e da sauri ya janyota jikinshi ya shiga lallashinta yana bata baki had'i da yi mata Nasiha da k'yar ya samu ta d'an saukko tace "Shikenan taje Allah ya taimaka na cire hannuna daga kan ta tayi duk Abunda yafi mata" da sauri Amadu ya girgiza kai yace "a'a Don Allah gwaggo kar kice hakan..." Katse shi tay da fad'in "To mi kake so in ce, zan ci gaba da damuwa da ita ne bacin ta nuna man iyakata, ko da yake dama nima ce da katsaladan da nike kokarin shiga tsakanin uba da yar sa" "Gwaggo kema ai kaman matsayin uwa kike a wurinta iya Abunda Mahaifiya zata ma d'iyarta kike mata" girgiza mashi kai tay cike da 6acin rai tace "a'a Amadu ni ba matsayin uwa nike ba a wurinta tunda gashi ta nuna" duk Maganganun da suke Fatun na la6e tana sauraran su ta rufe bakinta da tafin hannunta jin Maganar Gwaggon ta k'arshe yasa ta watsa da gudu d'aki tana cigaba da rizgar kuka, sosae Amadu ya shiga kwatanta ma gwaggo dalilin Fatun na amincewa da Auren yana rok'on ta akan tayi hak'uri kar tai fushi da ita in sha Allahu komae zai daidaita, to a Daren ranar dai tsakanin gwaggo da Fatuu ba wanda ya runtsa shi kan shi Amadun baccin shi Sama sama ne ya ma rasa tunanin da zai yi don samun mafita shin zai ce ma Fatuu kar ta yi ma Mahaifinta biyayya tayi ma Mahaifiyarshi ko ya ya? Itama Fatun sak'e sak'e kawae take in wata zuciyar ta nuna ta yi ma gwaggo biyayya sai wata zuciyar kuma ta ce kenan ta Amince mahaifinta ya shiga mawuyacin hali akanta duk da zata iya taimaka mashi??? _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2024* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 24 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ............A kan kunnanta aka fara kiran farko na sallar Asuba ta yunk'ura ta saukko idanunta sun yi luhu luhu ta fita, Alwala ta d'auro tazo ta kabbara Nafila bayan ta gama tana kuka tana Addu'oi, lokacin da gari ya waye sosae ta fito don ta share gidan tayi wanke wanke kafin ta wuce islamiyya duk jinta take wani iri kaman wadda ta tashi daga ciwo jikinta sam ba k'arfi, d'akin gwaggo ta fara zuwa ta gaisheta amman ko kallon Arzik'i bata samu ba haka ta fito tana goge kwalla da gefen hannunta, tsintsiya ta d'aukko tana fara sharar gwaggon ta fito daga d'akinta fuskar ta a daure tamau da hannu tay mata alama ta aje tsintsiyar cikin muryar kuka tace "don Allah gwaggo ki yi hakuri ki bari in share" a fusace tace "to ban so ko gidanki ne, kuma daga yau ban amince ki k'ara ta6a komae da sunan aiki ba ki bar man kayana zan yi na riga na yaye ki wanda kikai kuma nagode" daga haka ta juya ta koma d'aki, kallon Amadu dake tsaye bakin kopar d'aki Fatun tay da fuskar kuka ya d'an girgiza mata kai alamar ta barin da sauri ta aje tsintsiyar ta shige d'aki sai gashi ya biyo ta ya zauna a gefen gado ya fara rarrashinta cikin kuka tace "Kawu Amadu ya zanyi gwaggo ta kasa fahimta ta ni wllh ba wai ban damu da damuwarta bane ko ban son abunda take so, nasan Saboda in yi karatu ne yasa bata son ayi man Auren to amman Baffana na cikin matsala in ban taimaka mashi ba kana iya ganin Allah ya ki bani sa'a ma a karatun amman inna taimaka mashi in da rabo sai kaga Allah nima ya taimaka man ya cika man buri na" ajiyar zuciya ya sauke kafin yace "na fahimce ki sosae ki yi hak'uri Kinji ki bi komae a hankali dole dama zata shiga damuwa kuma ranta ne ya 6aci sosae shiyasa take ta maganganu kar ki damu ki daina yawan kuka kar wani ciwon kuma ya kama ki" kai ta d'aga mashi alamar to yace taje ta de6o breakfast ta ci ta tafi islamiyyar cikin karyayyar murya tace "amman tace fa kar in k'ara ta6a mata komae" d'an murmushi yay yace "kar ki damu da hakan kije ki de6o bazata hana ki ba kuma aikin ma in bata nan sai ki yi in kuma ta nuna maki bata son abu a yanzu ki daina jayayya da ita tunda ranta a 6ace yake" tare suka fito ya tsaya a bakin kitchen d'in har ta zubo ta koma d'aki sannan shima ya nufi d'akinshi, sam tama kasa cin wani na kirki karshe d'auka tay ta mayar kicin d'in ta dawo ta shirya, koda ta fito saida taje bakin kopar d'akin gwaggon tace mata ta tafi islamiyya sanin ba amsa mata zatai ba ya sa ta tafi, lokacin da ta fito Kawu Amadu ya bud'e shago saida ya k'ara mata magana kan ta daina damuwa tace to kafin ta wuce, Koda taje islamiyyar duk takurewa tay wuri guda da ka kalleta zaka fahimci tana cikin damuwa har wasu na tambayarta sai dae tace ba komae sam hankalinta bai kan abunda ake koyawa a haka har Malaminsu na hadda ya shigo wato discipline d'in su Malam Nazifi, d'aya bayan d'aya ya rink'a bi yana amsar hadda da ya basu har aka zo kan Fatuu ya kira sunanta saidae kwata kwata bata ji shi ba har saida wata ta kusa da ita tay tapping nata sannan ta dawo cikin hankalinta k'awar ta nuna mata saitin Malam tace yana magana da sauri ta kai idonta kan shi ganin kallon da yake mata yasa tasha jinin jikinta ta kusa da itan tace mata haddar ki zaki bada, shiru tay sai zare ido take to inama ta ga kwanciyar hankali jiya da har zata yi hadda, ce mata Malam Nazifin yay ta mik'e tsaye bayan ta mik'e yace ta bashi haddar tay wuri wuri da ido sai faman mommotsa baki take ta rasa yadda zata yi kawae sai tasa mashi kuka dama so yake yay Nazarinta sosae shiyasa yay mata hakan alamu yay mata na ta zauna ta koma da sauri ta zauna duk jikin sauran daliban yay sanyi, cigaba da amsar haddar yayi har aka kammala ya basu wata bayan ya gama ya mik'e zai fita lokacin Fatuu ta d'ukar da kanta ya kira sunanta ta d'ago da jajayen idanu yace ta biyo shi daga haka ya fita ta mik'e ta bi bayan na shi tana fita yan ajin suka fara chapter kan ta. Can k'ark'ashin wata k'atuwar bishiyar dalbejiya dake a cikin Makarantar ya nuna mata yace ta jira shi ya nufi Staffroom bada jimawa ba ya fito ruke da plastic chairs ya nufeta bayan ya aje su ya nuna mata d'aya yace ta zauna shima ya zauna kan d'aya ya zuba mata ido hakan yasa ta sunnar da kan ta can ya kira sunanta ta amsa ba tare da ta kalleshi ba yaci gaba "Fateema Muhammad Ardo na fahimci kina cikin damuwa ba tun yanzu ba tun wasu watanni can baya kin canja sosae akan yadda na san ki in ba damuwa ina son jin miye damuwarki ko da taimakon da zan iya yi maki kan hakan" Shiru tay tana sheshsheka har saida ya k'ara tambayarta sannan ta d'ago fuskarta duk hawaye ta fara Magana "Malam ba komae, ba abunda ke damuna" d'an murmushi yay kafin yace "sai dae in baki son in sani ne amman ai duk wanda ya sanki yasan kin canja Fateema yaushe rabon da ki yi laifin da na d'aga bulala na bugeki wanda inda da ne ba yadda za'ai a kwana biyu baki laifin da ban buge kin ba" shiru tay tana ta matse ido ya nisa yace " in baki son in sani ne bazan takura maki ba zaki iya tafiya dama ina tunanin ko da shawara haka in kina buk'ata sai in baki watak'il ta taimaka maki", shiru tayi can ta d'ago cikin muryar kuka tace "Malam abubuwa ne duk basu man daidai farko na rasa wani abu da nike tunanin nawa ne yanzu kuma wata matsala ce a gida na rasa yadda zan yi" sosae take kuka tana goge fuskarta da gefen hijab d'in ta, hanky ya fiddo daga cikin Aljihun shi ya mik'a mata yace ta goge kuma ta daina kukan zasu yi magana tace to, saida ya ga ta natsu sannan yay gyaran murya ya fara Magana, "Wato Fateema ita rayuwa da kike gani dama cike take da k'alubale kala kala, dole kana musulmi mai cikakken imani ka rink'a fuskarta jarabawa kala kala ba kuma don Allah bai son bawan sa bane yake jarabashi sai don ya gwada imanin bawa ya ga zai yi hakuri ya cinye jarabawa ko kuwa zai butulce, wanda in bawa yay hakuri silar hakan Allah ubangiji zai daukaka shi, hakan na nufin duk abubuwan da suke faruwa da bawa marasa dad'i Alkhairi ne atare da shi matuk'ar yay hakuri, akwae ayoyi a cikin surorin Al'qur'ani da yawa da sukae Magana kan hakuri misali: Suratul Ali Imran Aya ta 200 fad'inshi Allah SWT, Bismillahir Rahmanir Rahim "ya ku wad'anda suka yi imani ku yi hakuri,kuma ku jure kuma ku zama acikin shiri, kuma kuji tsoron Allah zaku rabauta". Suratul zumar Aya ta 10 fad'in SWT "hak'ika masu hak'uri ne kawae ake cikawa ladansu ba da lissafi ba". Haka suratul Anfal Aya ta 46 fadinshi SWT "kuyi hakuri hak'ika Allah yana tare da masu hak'uri". Suratul Ali Imran karshen Aya ta 146 ".....Allah yana son masu hak'uri". Sannan akwae jerin ayoyi a Cikin Suratul baqara daga k'arshen Aya ta 155 zuwa Aya ta 157, fad'in shi SWT ".....kuma kuyi Albashir ga masu hak'uri(155) "sune wadanda idan wata musiba ta same su sai su ce, mu na Allah ne kuma mu wurinsa zamu koma" (156) "wad'ancan gafarar Allah ta tabbata a gare su da rahamarsa, kuma wadancan su ne shiryayyu". Haka a cikin Suratul Ma'arij Aya ta 5 fad'inshi Allah SWT "ku yi hakuri, hakuri mai yawa", da sauran dai Ayoyi da sukae Magana kan hakan, "Sannan Magana ta farko da kika yi ta kin rasa wani abu akwae Aya ta 216 a cikin Suratul baqara da Allah SWT yay Magana akan hakan, "An wajabta maku yak'i a kan ku alhali kuwa shi abin k'i ne a gare ku, akwae fatar cewa ku k'i wani abu alhali shi ne mafi Alkhairi a gare ku, kuma akwae fatar cewa kuna son wani abu alhali kuwa shi ne mafi sharri a gare ku, kuma Allah ne yake sani kuma ku ba ku sani ba" "Anan Fateema ina mai baki shawarar ki yi hakuri akan duk wani abu dake damunki ki fawwala ma Allah ki kuma d'age da yin Addu'a dare da rana in sha Allah zai yaye maki dukkan damuwar ki, sannan Jinkirin samun biyan buk'atar ki tare da naciyarki wajan Addu'a kada ya zama sanadiyyar debe kaunar ki. Allah ya laminta ne zai amsa Addu'ar bawa akan abun da ya za6a mashi ba akan abun da shi ya za6awa kan shi ba, a lokacin dashi ya ga dama ba a lokacin da kai ka ke so ba, jinkirin samun biyan bukata kan abunda mutum ke tsananin buri da fatan mallaka na daga jarabawa amman idan akayi hakuri sai Allah ya ba mutum wannan abun ko ma wanda ya fi shi " Sosae Malam Nazifi yay mata Nasiha kuma ta ji sanyi a ranta harda Nafilolin da zata rink'a yi ya rubuta mata tay mashi godiya sosae. (Abunda na fad'a daidai Allah ya bamu Ladan in da nayi kuskure Allah ka yafe man). Tafe take bayan an tashi tana ta juya Maganganun Malam Nazifi tana fatan Allah ubangiji ya kawo mata k'arshen matsalolinta, tana gab da isa bakin lungun da zata bi wata budurwa da zata yi sa'an Fatun ko kuma ta d'an girme mata kad'an don ta fi Fatun tsawo ta 6ullo ta mik'o hanya tana sanye da pink Hijab Fatuu na ganin ta ta ayyana wani abu a ranta da sauri ta k'wala mata kira tace "Jamila" juyowa budurwar tayi sai lokacin ma ta lura da Fatun ta nufo ta tana mata murmushi a gabanta ta tsaya tace "Fatuu wllh bamma lura dake ba daga islamiyya kike" kai Fatun ta d'aga mata alamar eh ita kuma ta gyad'a kai har zata juya Fatun tace "Jamila don Allah ina son rok'on ki wani abu" tsayawa tayi da alamun mamaki kan fuskarta tace to, Fatuu taci gaba "dama so nike in rok'e ki abubuwan da nayi maki a can baya ki yafe man lokacin harda yarinta" dariya Jamila tayi tace "kai Fatuu abunda ya wuce ai ba wani abu kuma ma ni ai rigima dake Alkhairi ta zamar man wllh, zaki iya tuna wani lokaci can da kika 6arar man da awara har kafin ki zubar wani mutum ya raba mu?" Da sauri Fatuu ta jinjina mata kai, taci gaba "to ai d'an gidan Hajiyar Sanata ne nasan k'ilan baki rasa sanin shi to ta silar hakan wata rana ya ganni ina tallan k'osai da safe da yake ranar da kika zubar man da awaran shi ya bani kud'i anan na fara sanin shi to shine ya tambayeni miyasa bana zuwa makaranta na fad'i mashi baban mu ne bai lpy...." Nan ta kwashe komae da Haisam yayi masu ta fad'i mata tace "kinga yanzu bamu da matsalan komae na bar tallan Saboda shi innata ke yin sana'ar a cikin gida babana kuma ya samu lafiya sosae Shima Yana yin sana'ar su hatsi da cefane anan k'opar gida kuma har yanzu suna gaisawa da babanmu da zai yi aure ma babanmu yaso zuwa shi yace ya barshi" Fatuu dake ta bin ta da idanu jin tayi shiru yasa ta gyad'a mata kai kawae Jamila tace "ko baki lpy ne na gan ki sukuku" a sanyaye tace "kai na ne ke ciwo" tayi mata Allah ya sawak'e daga haka tace bari ta wuce dama innarsu ce ta aikota cikin unguwa, ba k'aramin sanyi jikin Fatun yay ba jin abunda Haisam yayi ma su Jamilar a ranta ta rink'a ayyana "dama haka halin shi yake mu kuma Mu kai tunanin so na yake" wani irin k'una zuciyarta ta fara mata a fili ta ke fad'in "ina son ka Ya Haisam duk da nasan na rasa ka har Abada" cigaba da tafiya tay sukuku da ita abubuwa sun mata yawa gashi ba Haulat balle ta tausheta ko ta waya wuyar samu take mata don k'aramar waya ce a hannunta tun kafin ta tafi tata ta lalace aka ce bazata gyaru ba sai ta sayar ta amshi k'arama, farko da suka je Nijar da wayar Yayanta Usman suke chat yanzu kuma shi ya dawo dama rakata yay d'an sauk'inta shine Kawu Amadu sosae ya damu da halin da take ciki yake yawan bata baki gwaggo kuwa abun ba'a Magana, Washe gari da safe wurin karfe 11 na safe lokacin gwaggo ta tafi aiki Amadu ya isketa a d'aki ya bata kud'i Naira dubu d'ari yace Baffanta ne ya turo yace a bata daga haka ya fita, bin kud'in da Kallo Fatuu tay ganin abun take kamar almara wai kud'in da zata Siya kayan kicin d'in gidan auren ta ne ta rasa tunanin da zata yi kan kud'in ta san ko ta kai ma gwaggo ma ba amsa zata yi ba ita gashi ba iya zuwa kasuwa zatayi ba da sunan siyo wani abu kawae sai ta mik'e taje ta saka su cikin wardrobe, haka suka ci gaba da yin zaman doya da manja ita da gwaggo sam in tana ma gidan Fatun k'umshe wa take a d'aki bata samun sukuni sai in ta tafi aiki gashi ta kasa bin yadda gwaggon ke so na bijirewa Maganar auren Don har Baffanta ya sanar da ita sati mai zuwa zai zo ya d'auketa har tayi rama Saboda damuwa amman duk da hakan bata wasa da yin Addu'a, Ranar Laraba tana fitowa don tafiya islamiyya sai ga Tk ya taho kan mashin d'in shi zai nufi gida yana ganinta ya tsaya yana murmushi itama d'an Murmushin ta ke mashi yace "Manyan gari kwana biyu ina kika 6oye?" itama tambayarshi tay a sanyaye tace "Tk ashe ka dawo?" Yace "eh tunda uwar d'akina ta dawo ai kinga dole in dawo" d'an bud'a ido tay tace "Hajiya ta dawo ne?" Yace "eh tun ranar Monday ma ashe baki sani ba" girgiza kai tay tace bata sani ba yace to ta dawo, har zai ja mashin d'in sai kuma ya dakata yace "Amman dae baki lpy ko" d'an cije lip d'inta na k'asa tay kafin ta d'aga mashi kai alamar eh yace ai ga alama nan Allah ya sawak'e daga haka ya ja ya tafi, tsaye tayi tana tunanin zuwa gun Hajiyar yanzu ko sai ta dawo can ta yanke bari ta koma gida ta aje jakar ta canja kaya sai ta je kawae, doguwar rigar material da mayafinta ta sa bayan ta koma gidan ta fito ta nufi gidan Hajiya, lokacin da ta shige gate bin part d'in Haisam da kallo tay rabon da ta shigo gidan tun kafin yay aure d'an girgiza kai kawae tay ta wuce, Hajiya na zaune a Falo idanunta sanye da glasses tana kallon tv Fatun tay sallama ta shiga har saida gabanta ya fad'i don tana shiga tay arba da wasu manyan hotuna wanda a da babu su, d'aya Haisam ne da Fanan da ganin yanayin shigar da suka yi da bikin su ne sunyi matuk'ar kyau shine a tsakiya sai gefe d'aya kuma Hajiya da su ne sun sakata a tsakiya duk sunyi dariya sai d'ayan gefen kuma hoton Fatun ne ita da Haisam wanda aka yi masu da kayan Fulani a cikin falon Hajiyan yayi kyau sosae, juyowa Hajiya tayi tana kallonta ta cikin gilashin har ta k'arasa ciki ta zauna kujerar kusa da ita da d'an murmushi tace "Hajiya ina wuni an dawo lpy" d'an kya6e baki Hajiyar tay kafin tace "idon ki kenan Fateema, ai nayi zaton sai na nemo ki da kaina ace kwana biyu na dawo amman baki zo kikai man sannu da zuwa ba har Dije dae ta shigo, ko don yayan ki ya bar gidan shiyasa za'ai man tawaye ko da yake tun ma kafin ya tafi ai kika d'auke man k'afa" ita dae d'an murmushi kawae tayi Hajiyan tayi mata murnar gama Makaranta da fatan sa'a a hankali ta amsa mata, shiru ya biyo baya can taji Hajiyar tace "Wai Fateema ko dae har yanzu ba ki jin dad'i ne naga duk kin yi wani iri gashi har rama ma naga kin yi sosae" sadda kanta tay ba tare da tace mata komae ba hakan yasa Hajiya k'ara tambayar tata aikuwa kawae sai tasa mata kuka, bin ta da ido hajiyar kawae tayi with mouth agape ganin bata da niyyar dainawa yasa ta kai hannu kan shoulder d'inta tace "shikenan ya isa hakanan kuka ai bai magani in baki lafiyan ne ko wani abu na damun ki ai sai ki fad'a man ba kita kuka ba, fad'a man miye?" Shanye kukan tay ta d'ago fuskarta duk hawaye cikin shaky voice tace "Gwaggo ce...." Sai kuma tayi shiru tana motsa baki Hajiyar tace tana saurarenta mi dijen tayi mata Fatun taci gaba "f...fushi take da ni, bata man magana, bata kula ni ta hana ko aikin gida in rink'a yi...." Cigaba da kukan tayi da tsananin mamaki Hajiya tace "Dijen ce ke maki haka harda gaba da girmanta to mi ki kai mata Fateema da har yay zafi haka?" Cikin muryar kuka Fatun ta bata labarin duk abun da ke faruwa, jinjina kai Hajiya ta shiga yi ita kanta ta girgiza da jin batun auren har ta kasa magana Fatuu nata sheshsheka can tace mata ya isa haka tayi shiru kafin tace "Amman Dije bata kyauta ba gaskiya to da mi zaki ji ne, ni Sam koda ta shigo bata man Maganar ba kuma komae ai a hankali ake bin shi ko ba ta dau zafi haka ba hakan zai samar da mafita ne, ki k'yale ni da ita" ta k'arasa ta sigar lallashi kai kawae Fatun ta d'aga mata tace ta daina kukan ta share hawayenta, bayan ta goge Hajiyar tace bari a zuba mata Abinci ta ci farko cewa tay ta k'oshi amman hajiyar tace a'a sai ta ci, bayan ta k'wala ma Saude kira ta bata umarnin ta kawo ma Fatun Abinci a nan cikin Falon bayan ta kawo mata har saida Saude ta tambayi Fatun bata lpy ne lokacin da ta gaisheta tay shiru sai Hajiya ce cikin 6acin rai tace mata ita da Dije ne, sai da Hajiya tasa ta taci sosae bayan ta gama tace taje d'akinta ta watsa ruwa ta kwanta tace to ta mik'e ta d'auki plate d'in Abincin walking slowly ta kai Kitchen kafin ta wuce d'akin Hajiya, bayan tayo wankan ta kwanta a k'asa kan carpet tana ta tunani bada jimawa ba bacci ya kwashe ta, sosae Fatuu tasha bacci don har Hajiya ta shigo don yin sallar Magrib da ake kira bacci take ta yi saida ta tasheta kafin ta tashi tayi salla bayan ta idar saida ta jira Hajiya ta gama don tana dad'ewa in tana yin salla sannan tace mata zata tafi amman Hajiyar tace tay zamanta a nan bayan sallar Isha zata je ta samu Dijen a hankali Fatun tace to, ganin kaman ta k'i sakin jiki yasa Hajiya ce mata taje d'akin Saude tace to ta mik'e ta nufi hanyar fita idon hajiya a kanta tana kallonta cike da tausayi yarinyar da koda yaushe take cikin nishad'i ce ta koma sukuku da ita, bayan sallar Isha hajiya ko cire hijab bata yi ba ta nufi gidansu Fatun baiwar Allah bata ma jin dad'in k'afafunta ciwo suke mata dama tana da ciwon shiyasa ma Senator ya hana ta dawo don sai da suka je US checkup daga can suka biya gurin su Haisam tare da Mahaifiyarshi harda Aunty da Hajiya maryam da mahaifin Fanan d'in duk aka je ganin d'aki, lokacin data isa da sallama ta shiga gwaggo ta fito daga d'akinta tana ganin hajiyar ta fara mata fara'a ta nufo ta tana yi mata sannu da zuwa....... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2025* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 25 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .......Parlor Gwaggo tace su shiga, a saman 2 seater Hajiya ta zauna gwaggo ta zauna kan one seater tana fuskantar ta ta shiga gaida ta rai a 6ace Hajiya tace "bazan amsa gaisawar ki ba Dije don kin ban mamaki wllh" waro ido gwaggon tayi a d'an rude tace "Hajiya mi kuma ya faru?" a d'an harzuk'e tace "haba Dije ace da girman ki ki tasa yarinya gaba kina gaba da ita sai kace wata kishiyarki to da me kike so ta ji ne? Baki tunanin hakan na iya jefata cikin wata matsalar kuma sakamakon damuwa da tayi mata yawa! Haba Dije in ran ki ya 6aci ai ba Kya bari hankalin ki ya gushe ba komae a hankali ya kamata a bi shi, nasani abun Sam ba dad'i to amman wannan abun da kike ba shine zai samar da mafita ba sai ma ya jaza wata matsalar" tana yin shiru cikin karewar murya gwaggo tace "amman hajiya mafitar nike son samo wa amman Fatuu ta watsa man k'asa a ido ta nuna man iyakata ta goyi bayan Mahaifinta...." Katseta Hajiya tayi a fad'ace tace "ta k'i bin bayan mahaifinta Dije duk D'iya ta gari kina tunanin zata ga mahaifinta a cikin matsala ne alhali tana da hanyar da zata taimaka mashi kuma ta k'i, ko kece Fateema na tabbatar hakan za ki yi kada ki zama mai son kan ki mana, sannan Maganar nuna iyaka ba wata iyaka da Fateema ta nuna maki kema kina da naki muhimmancin kamar yadda mahaifinta keda nashi" dakatawa tay tana maida numfashi yayin da gwaggo ta sadda kanta tana matsar k'walla Hajiya ta koma lallashinta tana bata baki akan a bi komae a hankali itama Fateemar ta san ba son Al'amarin take ba kawae bata da yadda zatayi ne don haka sai ayi Addu'a Allah ya za6a abunda yafi zama Alkhairi kawae amman ta daina abunda take Matan don zai iya jawo wata matsalar, sosae ta lallasheta har saida ta ga gwaggon ta saukko sosae sannan ta mik'e don tafiya bayan sun fito tsakar gida tace ma gwaggo taje ta d'aukko mata kayan baccin Fateema bama zata dawo gidan ba tunda dama kora da hali ake mata, d'an guntun murmushin yak'e gwaggon tayi kafin taje ta d'aukko mata saida ta sawo hijab ta rakata har wurin gidanta tana ta ta koma kafin suka yi sallama hajiyar na jaddada mata kan aci gaba da Addu'ar Allah ya za6a abunda yafi zama Alkhairi, lokacin da ta koma gidan a d'akin Saude ta iske Fatun kwance ta bata kayan baccin tace mata ta sa tay kwanciyarta har zata fita kuma sai ta dakata ta tambayi Saude Fatun ta ci Abinci tace mata a'a wai ta k'oshi hajiyar tace ta tashi taci ba yadda ta iya dole ta tashi Saude taje ta zubo mata Abincin, bayan ta gama komae tasa kayan baccin ta kwanta tunanin yadda Hajiya tayi da gwaggo ta shiga yi, Hajiya na komawa bedroom d'in ta toilet ta shiga tayo wanka bayan ta fito tayi shirin kwanciya ta kwanta, tunanin Maganar auren Fatun ta shiga yi ita kanta bata farinciki da Al'amarin sai dae tana fatan Allah ya za6a mata abunda yafi zama Alkhairi. Washe gari bayan sun yi breakfast Fatuu na zaune a d'akin Saude tunanin gwaggo ya dameta hakanan take jin son ganinta lokacin Hajiya ta koma bacci Saude ta shigo bayan ta gama gyara gidan da murmushi ganin Fatun ba bacci take ba tace mata ko ta tashi tay wanka tafi jin dad'in jikinta tace to, bayan ta fito ne ta maida kayan jiya data zo da su gidan tace ma Saude zata je gida ta canza kaya tace to, lokacin da ta isa a zaure ta tsaya tana ta wasi wasi can dae ta shiga ciki ba kowa a tsakar gidan hakan yasa bata yi sallama ba daga yanayin kopar d'akin gwaggon ta gane tana nan a ciki d'an jimm tayi kafin tay shahada cike da fargaba tay yar sallama ba tare da ta shiga ba shiru ba'a amsa mata ba hakan yasa ta k'ara yi sai lokacin ta jiyo muryar gwaggon ciki ciki ta amsa mata a hankali ta d'aga labulan ta shiga gwaggon na kwance saman gado tana huta gajiyar aiki da ta gama, ta ji shigowarta saidae bata bud'e idanunta dake a rufe ba balle ta kalleta, saman kujera ta kai ta zauna a d'arare idonta akan gwaggon, har bayan wani lokaci bata kalleta ba hakan yasa Fatuu shan jinin jikinta ta ji kamar ta tashi ta fita don ta lura kaman gwaggo bata huce ba can dae tayi k'arfin halin kiran sunan gwaggon murya na rawa shiru bata amsa ba bata kuma bud'e ido ta kalletan ba don sama fuskarta ke facing ta tada kai da Pillow, murya na rawa Fatuu ta ci gaba da cewa "Gwaggo don Allah ki yi hakuri ki yafe man ki daina fushi da ni wllh ban jin dad'i don ke matsayin Mahaifiya ta ce bazan so in ga kina fushi da ni ba, kuma ba iyakar ki nike son nuna maki ba kawae ina tausayin Baffa na ne don ban son Ard'o ya tsine mashi hakan matsala ne a gareshi kuma kinsan Ard'on zai iya kema nasan bazaki so hakan ta faru ba" ta k'arasa cikin karewar murya tana share hawayenta duk Maganganun da take gwaggon na jinta har can k'asan ranta wani iri take ji, mik'ewa Fatuu tay ta nufi gaban gadon ta duk'a akan gwuiwowinta ta dafa bakin gadon da hannu cikin muryar kuka tace "gwaggo don girman Allah ki yi hakuri ban son ganin ki a cikin damuwa..." sai lokacin ta bud'e idanun jin Maganar a kusa a hankali ta sauke su kan fuskar Fatun dake share share da hawaye sai kuma ta yunk'ura ta tashi zaune ta jingina bayanta da kan gadon shiru kaman bazata yi magana ba fatuu nata kallonta can ta sauke ajiyar zuciya murya ciki tace "Shikenan Allah ya za6a abunda yafi zama Alkhairi" a hankali Fatuu ta amsa da Amin kafin ta sadda kai tana kallon saman gadon can taji gwaggon tace ta tashi taje tay abunda zatayi ta d'ago suka had'a ido tana son ta k'ara bata Hak'uri amman ta kasa ganin yanayin fuskar tata, mik'ewa tay jiki a mace ta nufi hanyar fita gwaggon ta bita da ido har ta fice, d'akinta ta nufa tana shiga ta zauna a gefen gado tay zugudum hakanan hankalinta ya k'i kwanciya da yanayin gwaggon tana ta zaune can ta mik'e ta nufi wardrobe don ta canja kaya tana k'ok'arin fiddo kayan kud'in da baffanta ya aiko mata suka fad'o k'asa d'aukko su tay har zata maida su ciki sai kuma tay wani d'an tunani ta fasa maidawar ta aje su a gefen gado, bayan ta gama shiryawa d'aukar kud'in tayi ta fita ta sake komawa d'akin gwaggon k'irjinta na bugawa, lokacin da ta shiga har sannan gwaggon na zaune yadda ta barta, a bakin gadon ta tsaya da kermar murya tace "gwaggo gashi" kallon kud'in da take mik'a Matan tay kafin ta d'aga ido ta kalleta without saying anything ganin haka yasa Fatun cewa "d..da...dama Baffa ne ya turo ma Kawu Amadu wai ya bani in Siya k... kayan kitchen" da k'yar ta kai Maganar gwaggo na jin hakan nan da nan yanayinta ya canza sosae ta juyar da fuskarta gefe kaman bazata ce komae ba ita kanta Fatuu k'irjinta bugawa yake sosae bayan d'an wani lokaci ta ji gwaggon tace "sai ki je ki siyan ko" da sauri tace "ai ni bansan ma ina ake saida su ba kuma bansan mi zan siya ba" nan ma shiru gwaggo tay sai daga baya tace "sai kije in Saude bata komae ta raka ki tunda ita tasan inda ake saidawar zata taimaka maki da abunda ya dace" shiru Fatun tay ganin tak'i tafiya yasa gwaggon juyowa ta kalleta sai lokacin ta juya jikinta sukuku ta nufi hanyar fita gwaggon na bin ta da kallon takaici, d'akinta ta koma ta zauna a gefen gado tana tunanin ko ta kai ma Saude ko kuwa kar ta kai can ta mik'e ta yafa gyalen ta ta fita saida ta tsaya bakin kopar d'akin gwaggo tace mata ta tafi gidan Hajiyar shiru tay mata da farko saida ta k'ara maimaitawa sannan ta jiyo muryar ta ba yabo ba fallasa tana fad'in a dawo lafiya, Lokacin da ta isa Hajiya na zaune a parlon saman 2 seater tayi wanka ta shirya tana kallo bayan tayi sallama hajiyar ta amsa mata da d'an murmushi ta nufeta, gefenta ta nuna mata taje ta zauna tun kafin tayi Magana Hajiyar tace "ai d'azun nike tambayar Saude ke tace man kin je canza kaya nace ko dae kin kasa jurewa kinje ganin masoyiyar taki" ta k'arasa tana yar dariya itama Fatun murmushi take yi Hajiya tace "in ce dae ta sake maki yanzu?" Kai Fatuu ta d'aga kafin tace "eh" jinjina kai Hajiyar tayi tace "komae d'an hakuri ne kuma duk abunda Allah ya kaddara sai ya faru to kuwa ba makawa sai ya farun shiyasa ake son komae a rink'a bin shi a hankali ba a dau zafi ba" shiru Fatun tay kan ta a k'asa can Hajiyar tace mata ko taje d'akin Saude ta k'ara hutawa sai lokacin ta d'ago ta kalleta a hankali ta mik'a mata kud'in hannunta hajiyar ta kalli kud'in kafin ta kalleta kafin tayi Magana Fatun tace "dama Baffana ne ya turo man su wai in sayi kayan kitchen to lokacin gwaggo tana fushi ban bata ba sai yanzu shine tace in je in sayi kayan nace mata ban san inda ake saidawar ba sai tace in zo in Aunty Saude bata komae ta raka ni" ta kai Maganar kamar zata sa kuka, yar ajiyar zuciya hajiyar ta sauke kafin ta amshi kud'in tace taje d'akin Sauden ta amsa da to ta mik'e jiki a sa6ule ta wuce, shiru Hajiya tay tana bin kud'in da kallo cikin ran ta tana ayyana da gaske dae Auren zasu yi mata Sam itama bata son hakan saidae ta san in Allah ya kaddaro hakan to fa ba makawa sai ya faru, ajiye kud'in tay a saman hannun sofa taci gaba da kallon can kuma Haisam ya fad'o mata a rai ta san ba lalle in yasan da Maganar ba hakan yasa ta kai hannu gefenta ta d'auki wayarta ta fara kokarin kiran shi, Lokacin da kiran ya shiga Haisam d'in na zaune kan kujera 3 seater a Parlor yana operating laptop dake ajiye a saman table d'in gaban shi Fanan kuma na kwance kan ta na a saman cinyoyin shi tana bacci daga ita sai wasu matsiyatan lingerie da suka bayyana kaf surar ta sunan dae tasa ne kawae, hannu ya kai ya d'auko wayar da ke ajiye a gefen laptop d'in yana ganin sunan da yay appearing saman screen d'in yay d'an guntun murmushi had'i da maida bayanshi jikin kujera ya jingina sosae kafin yay picking tun kafin tay magana cikin cool voice d'inshi yace "Sweetheart how a'r u" daga can d'ayan bangaren ta amsa mashi da tana lafiya kafin ta tambayi ya suke yace mata lpy, "Ina rigimammar matarka?" Ta tambaya da yar dariya still da murmushi akan fuskarshi ya d'an kai idon shi ya kalli Fanan d'in, kamar kuwa tasan rigimar ta gama yi mashi kafin tay bacci ita ala dole suje a duba lafiyar su ganin har yanzu bata samu juna biyu ba dama tun suna wata guda da auren take Maganar samun cikin shi kuma yace is too early a fara wannan kuma yasan lafiyar su lau kawae time ne bai yi ba, amsa mata yay da tana bacci tace su fa dare ne ko ya amsa mata da yea, "Yar gidanka dae Aure za'ai mata nace bari in sanar maka nasan ba lalle in ka sani ba" Hajiya ta fad'a bayan sun gama gaisawar, shiru ya d'an yi lokaci guda yanayin fuskar shi ya d'an canja don ya fahimci wadda take Magana akai slowly ya yace "waye zai mata aure?" Hajiya tace "wllh can garin su wai kakan ne ya bayar da ita sai dae kawae Mahaifinta ya kira ya sanar zai zo d'aukar ta......" Nan ta kwashe komae ta fad'i mashi har da halin da Fatun ke ciki ita da Dijen, sosae ya 6ata fuska ya ma kasa cewa komae har saida Hajiyar tace "Haisam are u there?" Sigh yay yace "yea" taci gaba "abun ba dad'i wllh yarinyar na son yin karatu to kuma ga Maganar aure" Haisam d'in yace "but this's a forced marriage I think zaki iya yin wani abu bai kamata ayi mata aure ba" sauke ajiyar zuciya Hajiya tay tace "kagane su a wurinsu hakan daidai ne don haka suka saba za6a ma yara miji ...." Katseta yay "amman ita ba a wurin su take ba ai why za'a mata haka? U ave to do something sweetheart I think is part of ur work right?" D'an guntun murmushi mai sauti Hajiya tay tace "abunda nike son ka gane wannan family issue ne kaman yadda na fad'i maka haka suke ma yaran su yanzu inna ce in shiga Maganar ba lalle in yi nasarar hana yi mata auren ba in kuma aka yi nasarar to kuwa mahaifin nata ne a matsala kamar yadda na fad'i maka d'azun hakan ne ma yasa ita Fateema ta nuna ta Amince don fitar da mahaifinta daga halin da yake ciki" fuska a kwa6e yake saurararta bayan ta gama yace "so now u mean there's no way out dole ayi mata auren?" Hajiya tace "to ya za'ai in haka Allah ya kaddaro dole sai anyi mata auren sai dae ai fatan Allah ya zaba abunda yafi zama Alkhairi, ita kanta Fateemar ta ban mamaki wllh ban yi tunanin zata yi k'arfin hali har haka ba to amman nasan ba yadda zata yi ne bata son mahaifinta ya shiga matsala ne Saboda ita, yanzu tace sati mai zuwa mahaifin nata zai zo d'aukar ta yanzun nan ma ta kawo man kud'i da ya turo mata don ta sayi kayan kitchen" shiru bai ce komae ba har saida hajiyar tace ko shima ya fara baccin ne sannan ya yi magana yace Allah yasa hakan yafi zama Alkhairi ta amsa da Amin daga haka su kae sallama tace ya gaishe da Fanan, tun bayan da suka gama wayar still yay hannunshi dake ruk'e da wayar ya d'an dafa ha6arshi da shi kwata kwata bai ji dad'in Maganar auren ba sosae ran shi ya 6aci don har fuskar shi ta bayyana hakan, ya dau lokaci a hakan mutsu mutsun da Fanan ta fara yi ne yasa shi kai idanun shi kanta slowly ta fara bud'e nata idanun kafin ta ware su a kan fuskar shi tana ganin yanayin fuskar tashi ta yunk'ura ta tashi zaune shi kuma ya d'age kan nashi yana facing sama duk a tunanin ta Saboda rigimar zuwa Asibitin da ta gama yi mashi ne hakan yasa ta kai hannu ta kamo hannun shi guda a sanyaye tace "babe are u angry with me?" Shiru bai ce komae ba bai kuma d'ago ba cikin breaking voice ta kuma cewa "am sorry for dat son da nike maka ne yasa am eager to ave child wit u..." Kwalla ne suka taru a idonta tay shiru sai lokacin ya d'ago ya bita da ido kawae, shi kan shi bai san miya sa Maganar auren Fatun ta dame shi ba, sosae yake jin ba dad'i a ran shi da k'yar ya d'an yi mata guntun murmushi yace kar ta damu ba wannan ke damun shi ba, cike da kulawa ta tambayi abunda ke damun shi kawae sai ce mata yay bai jin dad'in jikin shi ne da sauri ta matsa ta fara tatta6a jikin nashi wai ko fever ce shi dae bai ce mata komae ba can ya fara k'ok'arin tashi yace zai je ya kwanta itama mik'ewa tay ya kai hannu zai d'auki laptop d'in ta rigashi d'auka bayan ta rufeta suka nufi bedroom d'in shi yana shiga ya kwanta dama shima sleeping dress ne a jikinshi, Fanan duk ta damu don tunda suka yi aure bata ta6a ganinshi a cikin irin yanayi haka ba yawanci in taga canji tattare da shi ta tambaye shi zai ce ya gaji ne ko kan shi na mashi ciwo yanzu kuma ta fahimci kamar yana cikin damuwa ne, cike da kulawa ta zauna a gefenshi ya kalleta tace mashi ko ta had'o mashi coffee ko tea ya d'an girgiza mata kai alamar a'a tace to miya ke damun shi ta d'aukko mashi magani tun da taji ba fever a jikin shi d'an murmushi yay mata ya kai hannu ya jawo ta ta hawo gadon sosae a hankali ya furta "am Ok" da yar damuwa tace "are u sure?" Lumshe mata ido kawae yay ta kwantar da kan ta a chest d'in shi tana shafa lallausar sumar dake kwance a wurin da hannunta guda akai akai take d'aga ido ta kalli fuskar shi ya rufe idonun shi hakan yasa tay tunanin yay bacci a wani bangare na zuciyarta kuma she's thinking what makes him so worried sanin shi ba abu kadan ke sa a ga damuwar shi ba, jin saukar numfashin ta a saman chest d'in shi yasa shi gane tayi bacci slowly ya ware idanunshi dama yayi hakan ne don bai son taci gaba da tambayan shi abun da ke damun shi gashi ya kasa sanar da ita zancen Auren da za'a yi ma Fatun don baison ma yin maganar, a nutse ya kai hannu ya janyeta daga jikinshi ya tashi zaune ya had'e hannuwan shi ya d'aura habar shi sam ya rasa ma tunanin da zai yi ba kamar da Hajiya ta nuna ba abunda za'a iya yi a hana su yi mata auren can ya sauke hannuwan ya kai hannu kan side drawer ya d'auki wayar shi saida ya gyara ma Fanan kwanciya ya lullu6e mata rabin jikinta da duvet ya rage hasken d'akin sannan ya juya ya fita, Parlor ya nufa ya zauna kan kujerar da ya tashi ya fara kokarin kiran layin Fatuu........ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2026* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 26 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........Tana zaune kan darduma ta gama salla tana lazimi a d'akin Saude wayarta dake aje a gefen katifa ta fara ringing, a hankali taja jiki ta matsa ta kai hannu ta d'auki wayar ta duba mai kiran nata, Jim tay ganin sunan Ya Haisam ya bayyana kafin tayi picking ta kai kunne, shiru sukae gaba d'aya kaman bazasu yi Magana ba can Haisam d'in ya kira sunanta "Zaraah" har saida gabanta ya d'an fad'i jin yanayin da ya kira sunan nata cikin shaky voice tace "N..na'am Ya Haisam ina wuni" bai amsa mata ba ta sake cewa "Ya Aunty Fanan" sai lokacin yace "she's fine" shiru suka d'an k'ara yi kafin yace "I heard u'r going to get married right?" Har saida ta had'iye abu cikin karewar murya tace mashi eh, "Kin hak'ura da zama Doctor kenan?" d'an runtse ido tay lokaci guda kuka yazo mata tace "Ehhh.. " yana jiyo sheshshekar da ta fara yi a hankali, d'an yamutsa baki yay kafin yace "Why are u crying, ba kina so ba shiyasa kika amince" cikin kuka tace "a'a Ya Haisam wllh bani so ba ni da yadda zan yi ne in ban amince ba Baffana zai shiga matsala ne Baban shi Ard'o zai tsine mashi yanzu haka ma duk yan gidan sun juya masu baya Saboda ya nuna bai so ayi man Auren shiyasa kawae na Amince don in taimake shi" sosae yake jiyo sheshshekar kukan nata yanzu slowly ya runtse idonshi ya d'age kan shi sama boiling from inside, ba k'aramin abu ke k'ona mashi rai ba amman wannan Al'amarin sosae ya ta6a mashi zuciya ba kamar yanzu da yake jiyo kukan ta ya fahimci itama abun ya ta6a mata zuciya sosae, sun dau d'an lokaci haka kafin ya sauke nannauyar ajiyar zuciya ya kira sunanta ta amsa yace "is Ok, I get u so stop crying and pray for d best" jinjina kai tay kaman yana ganinta sai kuma tace to daga haka yace mata zai kwanta su dare ne yanzu tace mashi sai da safe, koda suka gama wayar zaune yay a wurin bai tashi ba still kan shi a d'age yake saidae ya bud'e idanunshi ya k'ura ma ceiling ido da alama tunani yake, suna gama wayar taci gaba da kukan da take yi wanda ba na komae bane face tabo da Haisam ya fama mata, a cikin ran ta take ayyana da ta aure shi duk da yanzu bata shiga wannan halin ba tunda ba wanda zai ce ai zai mata aure tana cikin haka Saude ta shigo don tace mata ta fito ta ci Abinci ta iske ta haka da sauri ta zauna gefen Katifar ta janyo kan Fatun saman cinyarta ta shiga tambayarta lafiya cikin kuka take fad'in ita bata son auren nan, sosae ta ba Saude tausayi don Hajiya ta fad'i mata zancen Auren da za'ai ma Fatun, lallashinta ta shiga yi tana mata Nasiha har sai da tayi shiru sannan ta kama ta ta kaita toilet don ta wanke face d'in ta bayan ta gama ne suka nufi Parlor. Kullum gidan Hajiya take wuni ba laifi gwaggo na d'an sake mata amman ba wani sosae ba, ranar Friday da safe Baffanta ya kirata ya sanar da ita game da zuwan shi ranar lahadi in Allah ya kaimu yace mata akwae wani Abokin shi da zai kawo shanaye kasuwar charanchi ranar lahadin in zai koma sai su tafi tare koda akwae kayan da za'a d'auka tunda Motar tashi babba ce, wata irin kyerma jikinta ya fara yi a dabarbarce take amsa mashi bayan sun gama wayar zaune tay tana ta zare ido ya dae tabbata auren za'ai mata ji take tamkar ana zare mata lakar jikinta ta d'au lokaci a haka kafin da k'yar ta mik'e taje ta sanar ma gwaggo to itama dae ta girgiza da jin zancen amman bata nuna ba kawae sai ce mata tay Allah ya kaimu bata ji komae ba da yanayin yadda gwaggon ta bata amsa don tama saba da yadda take mata Magana yanzu, bayan ta fito ta koma d'aki gyale ta yafa ta nufi gidan Hajiya lokacin da ta je hajiyar na bedroom d'inta da sallama ta shiga ta amsa mata da murmushi gefenta ta baza wasu takardu da alama tana duba wani abun ne, gaida ta Fatuu tayi ta nuna mata gefenta tace ta zo ta zauna bayan ta zauna ne hajiyar ta tambayeta lafiya ta ganta sukuku nan da nan idanunta suka kawo ruwa tana kyakkyafta idanu don kada su zubo murya na rawa ta fad'i mata game da zuwan baffan nata itama hajiyar Maganar ta dake ta tay shiru can kuma sai tace Allah ya kawo shi lafiya Fatuu ta amsa da Amin yayin da kwallan da take ruk'ewa suka fara zubowa Hajiya ta fara lallashinta had'i da yi mata Nasiha mai tsuma jiki sosae taji ta samu natsuwa. Washe gari Asabar Fatuu da ta je islamiyya ta yi ma k'awayenta bankwana had'i da neman yafiyar su duk sunyi mamakin jin zancen Auren don ba wanda ya san da Maganar har Malaman su ma sun yi mamaki sun kuma yi mata Addu'oi har Malam Nazifi na cewa bata fad'i da wuri ba da an yi mata sauka amman ko bayan ta tafin in sha Allahu zai sa ayi mata bai amshi hadda ba a lokacin sai kawae yayi masu Wa'azi game da rayuwar gidan Aure da yin biyayya ga miji sun sha kuka ita da k'awayenta yan ajin su da aka tashi har saida suka rakota har gida, tunda ta dawo take k'umshe a cikin d'aki ko Abinci ta kasa ci Alwala kawae ke fiddo ta haka ma gwaggo kowa dae yana cikin matsananciyar damuwa, bayan sallar la'asar ne tana zaune kan abun salla wayarta tay ringing ta mik'e taje bakin gado inda take ajiye ganin hajiya ce yasa ta d'auka da sauri bayan ta gaishe ta ta tambayeta tana gida ko ta tafi islamiyya tace mata tana gida tace to ta zo yanzu ta amsa da to, dama akwae hijab a jikinta wucewa kawae tay bayan ta lek'a ta sanar ma gwaggo hajiya na kiranta ta d'aga mata kai kawae, a Parlor ta iskesu ita da Saude da Tk ga wasu manya manyan kwalaye guda biyu dake a bud'e shak"e da kayan amfanin kitchen gaida su tayi su duka suka amsa mata fuska a sake hajiya ta nuna mata kayan tace "Fateema ga kaya nan ki duba in akwae abunda kike so wanda babu sai ki yi Magana, can waje a bayan Mota akwae freezer da gas cooker ba'a shigo dasu ba kar ai wahalar sake fitar dasu kuma" mutuwar tsaye Fatuu tay tana ta zare ido ganin uban kayan dake gabanta wai kuma nata ne, ganin bata da niyyar dubawar yasa Hajiya ce ma Saude ta firfito mata da kayan ta gani ta amsa da to ta duk'a ta fara fiddo kayan, ba abunda babu da zaka samu a kitchen d'in yan gayu tun daga kan kaya masu amfani da wuta da sauran kayan amfani a cikin d'ayan kwalin harda rantsattsun zannuwan gado da labulaye sai daga baya ne ma Fatun ta lura da k'aton kwalin plasma TV dake can gefe itama Hajiyar tace tata ce she was completely speechless sai bin komae take da ido Hajiyar ta tambayeta akwae sauran abunda take so wanda babu girgiza mata kai kawae tay don ta kasa Magana ganin abun take tamkar a mafarki tana cikin hakan Hajiya ta mik'o mata kud'i tace "ga wannan kud'in da kika kawo man ne Yayan ki ne ya turo da kud'i aka siya maki komae sai ayi wani amfanin da su" idanu raurau ta kalli hajiyar tace ta kar6a mana sai kawae ta saka mata kuka Hajiya tace "Fateema wannan koke koken yayi yawa zai iya ja maki wata matsalar ina mun gama Magana dake?" Kai ta d'aga mata tace to tayi shiru sai lokacin ta yi mata godiya Hajiya tace ma Tk ya tashi su maida su cikin Mota a had'a da sauran akai can gidan ya amsa da to ya mik'e Saude ma ta tashi ta kama mashi suka fara fita da su, gaba d'aya da Sauden da Fatuu aka tafi lokacin Amadu na shago Tk ya parker hilux d'in Hajiyar duk suka fito Amadu na ganin su shima ya fito suka fara kai kayan ciki, jin anata kacaniyar shigo da kaya yasa gwaggo fitowa tana yin arba da kayan tay turus tana bin su da ido Fatuu ce ta nufe ta ta tsaya a kusa da ita a sanyaye tace "wai Hajiya ce tace a kawo Ya Haisam ne ya turo da kud'i aka siya ga wanda na kai mata tace a yi wani abun da su" ta kai Maganar tana mik'a ma gwaggo kud'in hannunta a hankali tace ta ruk'e a hannunta, lokacin Saude ta k'araso ta gaishe da gwaggon da d'an murmushi ta amsa mata tayi mata godiya, bayan an gama shigo da komae su Tk d'in sun tafi Amadu ya fara firfito da komae cike da mamaki yana dubawa itama gwaggo idonta na akai lokacin da ya gama ya d'ago ya kalli Gwaggo yace "Naira dae tasha kashi a wurin nan wannan ai an kashe million koma fi, ji wannan k'atuwar freezer da gas cooker don Allah ga plasma ma babbar" ajiyar zuciya kawae gwaggo ta sauke kafin a hankali tace an gode Allah ya saka da Alkhairi Amadu ya amsa da Amin ganin tana niyyar juyawa ta koma d'aki yace ba za'a shiga dasu bane ta dakata tace tunda tafiya za ai dasu su kauda su gefe daga haka ta shige d'aki bada jimawa ba kuma sai gata ta fito sanye da hijab ta nufi gidan Hajiya don yin godiya, da daddare lokacin Fatuu ta gama komae ta kwanta tay tunanin yakamata tayi ma Ya Haisam godiya duk da bata son Auren taji dad'in kayan don ko d'iyar wasu masu kud'in ce iyakar abunda za'a mata kenan, lokacin da ta kira dawowar shi kenan daga Masallaci sallar Asuba a edge d'in gado ya zauna yay picking call d'in bayan ta gaida shi ya amsa ta shiga yi mashi godiya yace ba wani abu shiru suka d'an yi jin kaman tana kuka yasa shi fara lallashinta suna cikin hakan Fanan ta shigo jikinta sanye da jalbab da alama itama sallar tayi zama tayi kusa da shi tana sauraran yadda yake Magana cikin kwantar da murya har saida ta d'an yi mamakin da wa yake Magana haka, sosae ya kwantar mata da hankali kafin sukae sallama yay mata Allah ya tsare hanya yace sai ya sake kira, yana cire wayar Fanan ta tambaye shi wacece yake lallashi haka bin ta da ido yay ganin ta kafe shi da idanu alamar amsa take jira yasa shi d'age mata gira yace "kishiyar da zan maki ce" wani kalan kallo ta jefa mashi ta d'aure fuska tamau can kuma sai ta ce "Babe I hate dis kind of jokes" murmushin gefen baki yay ya ja jiki ya jingina bayanshi da heardboard yana cigaba da kallonta ta wani sha murr ita ala dole bata son zancen kishiya ganin baida niyyar yi mata bayani yasa ta k'ara tambayarshi da wa yake wayan sannan yace mata Zaraah ce with surprise tace to mi ya faru taji yana lallashinta haka sai lokacin ya sanar mata zancen Auren da za'ai mata itama ta nuna bata ji dad'in hakan ba k'arshe tace Allah yasa hakan yafi zama Alkhairi. Washe gari da safe lokacin da ta je gaida gwaggo tace mata ta shiga makwabta tay masu sallama tace to, duk inda taje da an ji zancen Auren sai anyi mamaki jin abun kwatsam akai tayi mata fatan Alkhairi harda masu bata kud'i amman ta k'i amsa daga baya ta wuce gidan su Haulat lokacin da ta sanar ma innarsu haulat batun Auren sosae ta girgiza don abu ne da ba wanda ya ta6a tunani Fatun harda kwallarta innar ta shiga bata Hak'uri anan ta tambayeta Haulat kuwa ta sani tace mata a'a bata samun ta a waya innar tace in sha Allahu zata kirata ta sanar mata, da zata tafi ta d'aukko wani glass jug da kwalin set d'in Warmers da unbreakable plates cikin kayan Auren haulat ta bata Fatun na ta bassu tace sai ta amsa in ba haka ba zata aika mata dasu gida dole ta amsa tay mata godiya ta tafi innar nata jajanta abun a ran ta, Sai wuraren La'asar Baffan Fatun ya iso sosae taji dad'in ganin shi sai dae tana kallon shi ta fahimci ya rame sosae har duhu ma yayi hakan ya tabbatar mata da duk abunda ya fad'a na halin da yake ciki dama kuma ta gasgata shi tun da ya fad'i mata, a d'akin Kawu Amadu ya sauka bayan sun gaisa Amadun ya fita ya rage daga shi sai Fatuu dake gefenshi tana mashi murmushi yace "inna wuro an saka ki cikin damuwa ko?" d'an girgiza mashi kai tayi yace "ah kar ki man k'arya da ganin ki kina cikin damuwa fuskar ki ya nuna" tana murmushi tace "Baffana kai ma ai ka rame sosae" d'an murmushi shima yay yace "Ya za'ai sai Addu'a kawae, ki yi hakuri don Allah" da sauri tace "ba komae Baffa na rungumi hakan a matsayin kaddara ta" jinjina kai yay lokacin gwaggo ta shigo da sauri ya tsugunna itama ta duk'a daga can wurin bakin kopa ya shiga gaidata cikin harshen fulatanci tana amsawa fuskarta ba yabo ba fallasa tay mashi an zo lpy ya amsa da lafiya lou suka d'an yi shiru sai kuma ta mik'e tace Allah huta gajiya ta fita, a sanyaye ya kalli Fatuu suka had'a ido ya tambayeta har yanzu bata hak'ura ba ne tace mashi kar ya damu ta hak'ura ya dae yi shiru kawae amman daga yanayin da yaga gwaggon yasan tana cikin fushi don yadda suka saba gaisawa ma ba haka tay mashi ba duk da yasan dama dole tay fushi sosae don ba'a kyauta mata ba ita tasan wahalar inna wuro gashi an nuna mata fin k'arfi, da k'yar Fatuu ta sa ya d'an ci Abincin da aka kawo mashi ba sosae ba bayan ya gama tace yazo yaga kayan da Ya Haisam ya siya mata farko cewa yay ba sai ya gani ba tunda dasu zasu tafi amman ta matsa mashi saida ya fita duk da ya hana ta bud'a amman shima yayi mamakin uwayen kayan, bayan sallar Isha tare da Fatun yaje gidan Hajiya yin godiya lokacin tana Bedroom Fatuu taje ta kirata da fara'a ta fito tana mashi maraba lale shima ya mik'e yana mata dariya bayan ta iso ta zauna har k'asa ya duk'a ya gaishe da ita tana ya mik'e haba ya zauna, sosae suka shiga tattaunawa game da batun Auren da za'a ma Fatun bawan Allah harda kukan shi ya nuna bai ji dad'in hakan ba Hajiyar ce ta nuna mashi ya daina damuwa ya bita da Addu'a Allah yasa haka yafi zama Alkhairi daga baya suka hau yabon Fatun irin sadaukarwar da tayi ta hak'ura da karatun ta ita dai d'an murmushi kawae take, da zasu tafi sosae yayi mata godiyar kaya da abun Arziki da ake masu ta nuna mashi ai an zama d'aya su kai sallama Hajiyar ta tambaye shi lokacin da zasu tafi yace gobe bayan an gama sallar Asuba har hajiyar na cewa bazai bari ya k'ara hutawa ba yace ai da Abokin shi ne zasu tafi Saboda kaya kuma Abokin nashi gobe zai tafi tace ta fahimta sai Allah ya kaimu zata lek'o in zasu tafi, suna komawa gida Baffan nata yace taje ta kwanta tunda da wuri zasu tafi ta amsa da to tayi mashi sai da safe, tana komawa d'akin ta wayarta ta fara ringing taga Abbas ne bayan ta d'aga ta gaishe dashi yace ashe abunda ke faruwa kenan shi bai sani ba tunda bai nan sai yanzu Haisam ke fad'i mashi tace eh ga ma Baffanta har ya zo gobe da Asuba zasu tafi, sosae ya jinjina Al'amarin ya nuna baiji dad'in hakan ba daga baya yay fatan Allah ya za6a abunda yafi zama Alkhairi tace Amin yace in sha Allahu zai zo d'aurin Auren ta fad'a mashi Date d'in tace yanzu dae bata sani ba amman in ta tambayi Baffanta zata turo mashi yace Ok, suna gama yin wayar saiga Alert na 50k daga Abbas d'in ya turo mata text message cewa tayi amfani da su ba yawa har saida tay yar kwalla, a wannan Daren dai tsakanin Fatuu da gwaggo ba wanda ya runtsa har gwara Fatun tana d'an yin baccin sai kuma ta farka ta fara tunane tunane, yanzu abunda yafi damunta shine waye zata aura??? Wace irin rayuwar Aure zasu yi ita bata son shi kuma shima ta san ba son ta yake ba tunda dae Auren had'i ne ko ganin juna basu ta6a yi ba. Washe gari kiran sallar farko Abokin baffan nata ya iso ba 6ata lokaci suka fitar da kayan aka shirya su a bayan babbar Motar suna gamawa suka nufi Masallaci don yin sallar Asuba lokacin itama Fatuu taje tayo wanka tazo ta kabbara sallar dama tuni ta gama shirya kayanta da zata tafi dasu don ba komae zata d'auka ba k'aton Akwatin da Haisam ya bata ne sai trolley d'inshi anan ta shirya kayanta na sawa ta bar ma gwaggo na tsakiyan sai wata jaka da ta zuba littattafanta da sauran abubuwan ta da take so, tana zaune Kawu Amadu ya shigo yace ta gama shiryawa tace eh ya fara fitar mata da kayanta lokacin da ya dawo zai d'auki na k'arshe ne Fatuu dake tsaye ta kira sunan shi ya kalleta kaman zata sa kuka ta mik'a mashi wayarta tace " gata kaci gaba da amfani da ita sai ka bani taka" waro ido yay baki bud'e alamar mamaki kafin yace "a'a ki bar abun ki can ma ai zaki iya amfani da ita" da sauri tace "ai shiyasa nace ka bani taka kaga can bama wani Network ke da akwae ba mai kyau ko naje da ita bazata yi man amfani ba sosae kaman yadda kai zata maka don Allah ka amsa" ta k'arasa hawaye na zubo mata hannu ya kai yana goge mata yana cewa tayi shiru zai amsa, dama ta goge abunda zata goge tace ya tura mata abubuwan da ta bari kafin su tafi yace to ya amshi wayar ya d'auki d'ayar jakar da yazo d'auka ya fita, gari na fara wayewa suka fito don tafiya har lokacin Fatuu bata ga fuskar gwaggo ba lokacin da ta shiga don yi mata sallama a zaune kan abun salla ta isketa ta d'ukar da kanta k'asa, duk'awa tay gefenta ta gaishe da ita ta d'aga mata kai kawae shiru Fatun tayi can kuma tay k'arfin halin cewa "G...gwaggo zamu tafi" farko shiru tay sai kuma murya a disashe taji tace "Allah ya tsare hanya yasa Alkhairi Amadu zai kawo maki sak'o" daga haka tay shiru sosae gaban Fatuu ya fad'i don daga jin muryarta kuka tayi cikin rawar murya Fatun tace "to gwaggo ke bazaki zo ba?"shiru tay mata ta k'ara tambayarta nan ma tay mata shiru kawae sai tasa mata kuka tana fad'in "Don Allah gwaggo ki yi hakuri ki yafe man kar ki ce bazaki zo ba, kowa in za'a mata aure Mahaifiyarta na mata fad'a da nasiha ni waye zai man in kika k'i zuwa??" sai lokacin ta d'ago idanunta sun yi jawur cike tabb da k'walla tay d'an guntun murmushin takaici kafin tace "ga yadikkon ki ga kuma wasu iyayen naki cike da gida Fatuu" sosae take kuka tana rok'onta ita dae don Allah ta zo suna cikin haka Hajiya ta shigo gidan da sallama jiyo kukan Fatun yasa ta nufi d'akin gwaggon tana fad'in "koke koken ne har yanzu ba'a gama ba an bar mutane nata jira a waje tafiya bata kusa ba" d'aga labulan kopar tayi ta shiga ganin yadda fatun ke kuka ta tambayeta abunda ya faru cikin kuka ta sanar mata, wani kallo tay ma gwaggon rai 6ace tace "haba Dije wai miyasa kike haka ne don Allah, yarinya zata tafi baza kuyi rabuwar Arziki ba ki faranta mata rai sai ki fad'a mata abunda zaki tada mata hankali haka" girgiza kai gwaggon tayi tace "nifa ban ce mata bazan je ba ita ta yanke hukunci" Hajiya ta kai hannu ta mik'ar da Fatun tsaye tana ce mata tayi shiru tama isa tace bazata je bikin ba suna nan zuwa harda ita sai lokacin taji sanyi a ranta suka nufi hanyar fita tana ta waiwayen gwaggo da tayi zaune bata da niyyar mik'ewa bare ta rakata, waje suka fito dama ita kawae ake jira Hajiya ta kaita har bakin Motar tace ma Baffanta gata nan su tafi kar suyi dare a hanya cike da girmamawa ya amsa mata da to ya bud'e ma Fatuu kopar Motar ta baya ta haye ta lek'o da kanta tana kallon su Tk da Amadu da Saude harda wasu daga cikin makwabta da suka fito sai kuka take Amadu ma ya kasa jurewa saida ya yi kwalla da k'yar ya matsa ya mik'a mata wayar tashi cikin kuka tace "Kawu Amadu zaka zo ko?" Da sauri ya jinjina mata kai ya kamo hannunta guda yace "in sha Allahu tun kafin bikin ina nan zuwa ki yi hakuri don Allah ki kwantar da hankalin ki kin ji" kai ta d'aga mashi lokacin Baffanta yace ma Amadu ya rufe mata kopar yace to ya saki hannunta ta maida kan ta ciki ya rufe sannan ta sake lek'o da kan ta windown kopar, zagayowa Baffanta yay ya yi masu sallama ya k'ara ma Hajiya godiya duk suka yi masu Allah ya tsare ya kai su lafiya ya amsa masu daga haka ya juya ya nufi gaban Motar ya shige shima Abokin nashi wanda shine driver d'in da zai tuk'a Motar ya lek'o yay masu sallama daga haka ya maida kan nashi ya tashi Motar wani bugu gaban Fatuu yay ta d'aga hannu tana masu bye bye tana ta kuka suma duk suka d'aga mata Tk da Saude ma duk kasa jurewa su kai sai da suka zubar da kwalla Motar na fara tafiya kawae sai ganin fuskar gwaggo tay ta lek'o sosae ta d'aga mata hannu ta kira sunanta da k'arfi "Gwaggo!!!" hakan yasa duk aka waiga ana kallon gwaggon don ba wanda ya lura da ta fito da k'yar ta d'aga ma Fatun hannu guda itama tay mata bye bye.......... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2027* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 27 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ...........Saida Motar ta bar layin sannan duk suka juya Hajiya ta kalli Gwaggo ganin hawaye a fuskarta ta shiga bata baki kafin suka wuce gida ita dasu Saude Amadu kuwa tsaye yay duk jin jikin shi yake ba dad'i yana ganin gwaggo ta koma ciki shima ya shige gidan ya nufi d'akin shi ya kwanta, akai akai yake kai hannu yana share kwallan dake gangaro ma shi, gwaggo na shiga d'aki ta haye gado tasa kuka mai cin rae taci guri in Allah ya nuna mata auren Fatuu sai gashi komae ya juye zata yi aure ba tare da tana farin ciki da hakan ba, sosae ta sha kuka daga baya ta lallashi kanta ta yi shiru. Tun da suka hau hanya take ta kuka Baffanta da Abokin nashi nata bata Hak'uri har dae ta yi shiru sai dae kwalla basu daina zubo mata ba tana kai gefen gyalen ta tana gogewa daga baya bacci ya kwashe ta, sosae Baffanta yaji dad'in hakan don ba k'aramin ta6a mashi zuciya kukan da take ke yi ba, sai da suka tsaya Kano sannan ta farka suka siya abunda zasu ci aka mik'a mata nata kamar bazata ci ba baffanta yace tayi hak'uri ta ci idanunta duk suyi luhu luhu ba yadda ta iya dole taci don tana jin yunwa Bayan sun d'an huta suka sake d'aukar hanya duk garin da suka tsaya sai Baffanta ya siya mata abu wani ta ci wani ta k'i ci, Alhamdulillah sai Bayan la'asar wuraren karfe biyar na yamma suka isa tunda suka iso jumeta Fatuu ke jin tamkar za'a kaita kurkuku sai ma da suka isa rugar kukan zuci kawae take, Motar na tsayawa gaban gidan Kamalu da su Mino dake ta dakon isowar su suka nufo Motar cike da farinciki Baffan Fatun ya zagaya ya bud'e mata kopar ta fito sai murnar ganinta ake ita kam ta kasa yin ko murmushi ganin yanayinta yasa Kamalu da Mino suma d'an shiga damuwa baffanta yace su shiga daga ciki Mino ta kama hannunta shi kuma kamalun yace ya tsaya su sauke kaya, bin Mutane da ido kawae ta rink'a yi ana mata sannu da zuwa kan kace mi labarin zuwanta ya isa ko ina a cikin gidan harda uban kayan da aka zo dasu yan gidan duk aka fito wasu suka lek'o ta Katanga ganin kwakwaf ita dae kallon su kawae take tamkar yau ta fara ganin su, kafin su isa sashen su sai ga yadikko ta fito cike da farinciki ta zo ta rungume Fatun tana mata sannu da zuwa lokacin da ta d'agota suka had'a ido kawae sai ganin kwalla tay ta zubo mata da sauri ta Sunna kai k'asa sosae jikin yadikko yay sanyi ta kama hannunta suka nufi ciki, an gyara sashen na su sosae har da su fenti haka d'akin yadikkon an maida shi ciki da falo har da bathroom a cikin uwar d'akan, zaunar da ita yadikko tay kan kujera ta zauna gefenta haka su Mino ma duk suka zazzauna suna kallon ta ta sadda kai k'asa, kan kace mi d'akin ya cika da yara harda wasu daga cikin Matan gidan suka shigo yi mata sannu da zuwa suna ce ma yadikko ashe Amarya ta iso ita kuma tana bin su da eh kawae don tasan yawanci duk gulma ce ta kawo su, sai Bayan wani lokaci mutanen suka lafa yadikko tace ma sauran yara suje su k'yaleta ta huta bayan duk sun fita ya rage saura yan'uwan Fatun kawae cike da nuna damuwa yadikkon tace "Fatuu ki yi hakuri kin ji, kowa yasan ba'a kyauta maki ba wllh duk bamu ji dad'in wannan abun ba ba yadda zamu yi ne da muka nuna bamu so baki ga halin da muka shiga ba akai ta mana wulak'anci da Maganganu duk aka tsangwame mu Baffan ki har ciwo yayi...." Dakatawa tay tana goge kwallan da suka taru haka ma su Mino duk kwalla suke zubar wa a hankali Fatun ta d'ago ta kalli yadikko cikin rawar murya tace "ba komae ki daina kuka ai gani na zo sai suyi man Auren" kamata tay ta rungume tana mata godiyar taimakon su da tayi ta amince da wuri wanda duk basu yi tunanin hakan ba ta tambayeta har yanzu gwaggo fushi take don baffanta ya sanar da ita ta d'au ki zafi sosae Fatun tace mata a'a ta hak'ura tana nan zuwa sosae yadikko taji dad'in hakan, d'agota tay tace bari ta zubo mata Abinci ta barta da yunwa ga gajiyar hanya Fatun ta mik'e tace band'aki zata shiga da sauri Mino ta mik'e tana nuna Mata cikin d'aki tace an yi sabo a ciki suka nufi cikin tare, harda Alwala tayo Bayan ta fito ta kabbara salla a cikin uwar d'akin lokacin Baffanta da Kamalu suka shigo d'akin a Falo suka tsaya baffan ya tambayi Mino inna wuron ta kwanta ne tace mashi tana salla ne ya nemi wuri ya zauna Kamalu ma ya zauna lokacin yadikko ta shigo ta jere ma Fatun kayan Abinci kafin ta zauna a gefe tana ma Baffan ya gajiyar hanya Kamalu ya shiga basu labarin uban kayan da Fatuu tazo da su yace yawanci ma shi duk bai san mi ake dasu ba wasu dae ya san su a cikin film harda wanda ake gasa kaji duk su kae yar dariya kafin kuma shiru ta biyo baya can kuma Baffan yace ma yadikkon kayan na a d'akin shi aka kai su da d'akin Kamalu za'a sa to kuma kar a lalata wani abun tunda bashi kadae bane a ciki tace hakan yayi suna haka Fatuu ta fito duk suka d'aga ido suna kallonta ta k'araso da d'an murmushi zata zauna a k'asa kan leda Baffan yace tazo ta zauna kusa dashi yadikko tace ai Abinci zata ci yace to, saida ta tambaye ta abunda zata ci tace duk wanda ta zuba mata tasa mata burabusko tace in ta cinye sai a k'ara mata wani Abincin ita dae shiru kawae tay, Sam ta kasa sakin jiki ta ci Abincin sai dae tai ta juya cokali baffanta ne da ya kula da hakan yace ta daure ta samu ta ci tace to ta d'an k'ara tsakura kafin ta ture tace ta k'oshi, yadikko tace ai bata ci komae ba tace bata jin dad'in bakinta ne, fura ta zuba mata tace ta daure ta sha zata ji k'arfin jikin tace to, ba laifi ta sha da d'an yawa suna son suyi fira da ita saidae kowa bai cikin yanayi mai dad'i ba kamar ganin yanayin Fatun duk sunyi jigum jigum sai jefi jefi suke Magana daga baya Baffanta da Kamalu suka tafi yin salla suma suka Mik'e don su yi, Bayan sun gama sallar ne su Aysha suka matsa ma yadikko kan tazo ta ga kayan da aka zo dasu har saida ta mik'e ta bisu, koda taga kayan kitchen d'in tsananin mamaki ne ya kamata don ta san ba kananun kud'i aka kashe ba don kuwa ta ta6a yin aikatau a gidan wasu yan gayu a Abuja duk ta san amfanin kayayyakin yan gidan ma duk suna ta zuwa suna gani tuni labarin irin kayan da aka zo da su ya kai ma su Yaya, Bayan yadikkon ta koma d'aki ne ta zauna a gefen gado da d'an murmushi tace ma Fatuu dake zaune kan sallaya "ko zaki je ki gaisa da su Yaya nasan sun san da kun iso tuni" tura baki Fatuu tay ta juyar da kanta wani irin haushin Yayar take ji don ta san harda ita aka had'a komae, ganin bata ce komae ba yasa yadikkon k'ara mata Magana a hankali ta juyo tace mata ta gaji ba yanzu ba sai ta huta, d'aga mata kai kawae tayi itama gudun Magana ne yasa tace taje su gaisan don tasan sai anyi tsegumin rashin zuwan nata ta gaishe dasu, shiru suka d'an yi kafin yadikkon tace "naga uban kayan kicin gaskia gwaggo ta kashe kud'i ba kad'an ba, ni baffan ki ce man yay dubu d'ari ya tura har ina cewa sun yi kad'an don jere ake ma kicin sosae a birni kuma kayan suna da kud'i to sai yace man bai gama biyan kud'in kayan gado da kujeru ba don shi kad'ai aka bari da hidimar Ard'o ne kawae ya bashi shanu guda d'aya ya siyar yayi maki kayan d'aki sai kuma kud'in sadakin ki dubu 100, shi kuma so yake yayi maki kaya irin na yan birni shiyasa duk ya tattara kud'in shi ya biya don kayan fin rabin miliyan ne za'a maki" shiru Fatun tay yayin da tausayin mahaifin nata ya k'ara kamata, "Wai nikam Fatuu ina Ya Handsome d'in ki??" Har saida kirjin Fatuu ya d'an buga damm jin tambayar da yadikkon tayi mata, shiru ta d'an yi sai kuma a hankali ta kalleta ganin tana kallon ta alamar jiran amsa yasa tace "Ya yi aure" dan bud'a ido yadikko tay kafin tace "Allah sarki yaushe?" tace "kusan wata ukku yanzu" rausayar da kai yadikko tay kafin ta sake cewa "a nan Katsina?" "A'a basu nan k'asar suna America" da k'yar ta bata amsar ta d'ukar da kanta k'asa jin kwalla na niyyar zubo mata girgiza kai yadikko tay tace "Allah bai k'addara mijin ki bane don ni da nayi tunanin son ki yake wllh koda kika ce man ba haka bane wancan lokacin kawae na jiki ne na zata yana son ki ne ya bari sai kin k'ara girma don hidimar da yake tayi yawa yawanci zaki ga irin hakan ba hakanan mutum ke yi ba da dalili ashe shi don Allah yake yi" a sanyaye Fatun ta d'ago tace "shine ma ai ya turo kud'i aka siya wancan kayan" hannu yadikko tasa ta ruk'e ha6a tace kai don Allah Fatun ta d'aga mata kai alamar eh, "Kai amman dae wannan mutumin d'an Arziki ne wllh ni bamma ta6a jin mutum mai Alkhairi irin nashi ba, ace daga makwabta ka ya dinga hidima haka ni fa wllh nayi mamakin kayan can don ko banza sai sun yi miliyan ko ma fi" dakatawa tay tana maida numfashi kafin da d'an murmushi ta dafa kafad'ar Fatun tace "amman da gaske bai son ki kuwa?" D'agowa Fatuu tay ta kalleta idanunta sun k'ara sauyawa a hankali tay shaking kanta tace "bai ta6a so na ba, dama yana tare da wadda ya auran yar uwarshi ce" cike da zolaya yadikko tace "to amman ke nasan ai kina son shi ko?" bin ta da ido Fatuu tay ta kasa ce mata komae kawae sai ganin kwalla yadikko tayi tana zubo mata zaro ido tay Fatun ta kifa kanta a jikin kafafun yadikkon ta sa kuka, wani irin sanyi jikin yadikkon yay ta kai hannu ta d'ago ta ta zaunar da ita gefenta ta rungumo ta ta gefe cikin kuka Fatun ke fad'in "ina son shi sosae yadikko nayi tunanin shima yana sona ne ashe ba haka bane bai ta6a so na ba ina ji ina gani yayi auren shi ya tafi ya barni" har idanun yadikko sun ciko da k'walla ita dama tayi mamakin saurin amincewa da Fatun tay ai mata auren ashe ashe ciwo ne da ita a zuciya sosae ta bata tausayi ta shiga rarrashinta tana bubbuga bayanta tace "kiyi hakuri Fatuu na fahimci yadda kike ji ki bar ma Allah komae in har shi rabon ki ne Allah ya k'addaro zaku rayu matsayin mata da miji ko ba dad'e ko ba jima hakan sai ta faru don in dae abu rabon ka ne kana zaune zai iske ka har inda kake har kai ta mamakin yadda hakan ya kasance wannan kad'an daga ikon Allah ne don ni kaina shaida ce na so Mahaifin ki kamar mi muna cikin soyayya aka ce an bayar dani ga wani abokin mahaifina ina ji ina gani aka man Auren dole kaman zan yi hauka naje gidan shi sam ba kwanciyar hankali ga wulak'anci dama shi bai d'auki mace a bakin komae ba tamkar riga haka yake canja mata shima Baffana harda kwad'ayi yasa ya bashi aure na k'arshe ya yi man sakin wulakanci lokacin yunwa duk ta k'arar dani abun bak'in cikin lokacin Mahaifin ku har yayi auren shi koda na tuntu6e shi Bayan na gama idda sai ya bani hak'uri ya nuna man bai da ra'ayin mata biyu, ya dae fad'a man haka ne kawae amman nasan kawae ya daina so na ne dama na samu labarin irin son da yake ma matarshi wato mahaifiyar ki gata yar birni mai ilimin boko a lokacin ne na samu aka man hanya na tafi aikatau Abuja nayi nisa da garin to ashe Allah bai kaddaro zasu rayu tare tsawon lokaci ba wllh lokacin na girgiza da jin labarin mutuwarta don lokacin ni nama fidda ran auren nashi na nemi number d'in shi ta hanyar wani Yayana na kira don yi mashi gaisuwa to anan muka samu lambar juna mu ka d'an rink'a gaisawa ina d'an kwantar mashi da hankali ana haka Bayan wani lokaci watarana sai kawae yayi man Maganar Aure yace in ba damuwa lokacin na k'ara gasgata girman ubangiji don kuwa in nace ban son shi to fa nayi k'arya Saboda son gaskiya nike mashi wanda bai k'arewa, ba 6ata lokaci na nuna mashi na amince sanin yana cikin hali ga marayun yara kuma duk da ina jin dad'i a in da nike aikatau haka na baro Abuja na dawo mu kai Aure" lamo Fatuu tay yayin da cikin ranta ta ke kokonton anya Ya Haisam zai zama mijinta ita tama fidda ran hakan, to yaushe ma ita da zata auri wani shima kuma yana can yana auren wata, Yadikko taci gaba da cewa "ina so ki sani Al'amarin mumini dukkan sa Alheri ne, in samu yay Alheri ne in ya rasa ma Alheri ne, acikin wani hadisi aka fad'i mana hakan lokacin ina zuwa islamiyya a Abuja don haka ki sa a ranki duk abunda ya faru dake mai kyau ne ki daina damuwa don duk abunda zai faru da bawa an riga da an rubuta ki ci gaba da Addu'a muma kuma muna yi maki" kai Fatun ta d'aga mata ta d'ago da fuskarta tana share mata hawayen da d'an murmushi akan fuskarta bayan ta gama goge mata tace ta tashi tayi sallar Isha sai ta ci Abinci ta amsa da to, bayan ta ci Abincin wanka tayo ta saka kayan bacci ta haye gado ta fara tunanin gwaggo tana son kiranta amman kuma tana zullumi don tasan in da Lafiya lau bata fushi ba yadda za'ai ace har yanzu bata kira taji ya suka iso ba tana cikin hakan wayarta ta fara ringing ta d'auka ta duba Kawu Amadu ne mik'ewa tay zaune ta kara wayar a kunne bayan ta d'auka, gaisawa sukae yay mata anje lafiya ta amsa kafin ta tambaye shi gwaggo yace tana d'aki shiru tay bata ce ya kaima ta ba shima bai ce zai kai Matan ba, yar hira suka yi yawanci dae lallashin ta ya k'ara yi kafin daga baya sukae sallama ta cire wayar, zaune tay bata koma ta kwanta ba gaba d'aya ta rasa ma tunanin da zata yi komae bai mata dad'i tana cikin hakan wayarta ta sake yin ringing ta kai idonta kan screen d'in sunan Ya Haisam ta gani lokaci guda ta saki murmushin da ita kanta bazata tuna when last da tayi irin shi ba don taji dad'in kiran nashi ko ba komae ta fahimci ya damu sosae da halin da take ciki, picking tay ta kara kunne kafin a hankali tay mashi sallama ya amsa mata a sake ya tambayeta ya suka isa tace mashi lpy Lou, shiru suka d'an yi sai kuma taji yace "kin daina kukan ko?" tana murmushi tace eh yace "dat's gud ki yi hakuri haka rayuwan yake we plan but God plans d best for us and all tests from Allah are Alkhair" jinjina kai tay ta d'an had'e lips d'inta sosae take jin dad'in yadda yake mata Magana bayan d'an shiru cike da zolaya yace "kin had'u da groom d'in naki ko?" Tura baki tay kaman yana ganinta, yace "ba tura man baki zaki ba ki ban amsa" waro ido tay jin ya gane abunda tay a hankali tace "a'a ni har yanzu ban san shi ba" d'an murmushi yay sai kuma yace "Ok in kun had'u sai mu gaisa in bashi amanar ki" d'an murmushi tay bata ce komae ba yace "ko baki so?" Da sauri tace "ina so" shiru suka d'an yi can tace mashi ya Aunty Fanan yace yana wurin aiki itama tana wurin aiki tace to, "baku da Network mai kyau da na maida vedio call in ga sore eyes d'in ki" zaro ido tay da yar dariya kawae yace "ko idanun basu kumbura ba?" Tura baki tay tace "sun kumbura" lallashinta ya shiga k'ara yi suna haka yadikko ta shigo dama tana falo ita da yaran ta hana su shigo don kar su takura mata har saida tay mamakin ganin Fatun zaune tana waya kuma harda murmushi akan fuskarta ganin kallon mamakin da take mata ne yasa tace ma Ya Haisam d'in ga yadikko zasu gaisa yace Ok ta cire wayar ta mik'a mata ta fad'i mata ko wanene da sauri ta amsa ta zauna a bakin gado tana ta washe baki suka gaisa kafin ta hau yi mashi godiyar abun Arziki yace ba wani abu sosae tay mashi Addu'oi kafin ta mik'a ma Fatuu wayar tana amsa yace bari ya kyaleta ta huta sukae sallama, bayan sun gama firar Haisam d'in ta shiga yi ma Yadikko ita kuwa ganin sakewar da tay yasa ta biye mata, Washe gari tana cikin yin karin kumallo don bata tashi da wuri ba Baffanta ya shigo duk suka gaishe dashi da fara'a yabi Fatun ya samu wuri kan kujera ya zauna yana amsa gaisuwarta yadikko ma ta gaishe dashi ganin ya shirya tace har zai fita ne yace "Eh ina son zan je can jumeta ne wurin masu kayan gadon" yadikko tace "za'a d'aukko ne?" Shiru ya d'an yi kafin yace "tukunna dae kinsan har yanzu akwae sauran kud'i da zan cikashe masu dubu 200, da nayi tunanin zan samu wasu kud'i ne to amman tunda lokaci k'urewa yake zan k'ara kai shanuwa guda kasuwa sai a basu kawae" da yar damuwa yadikko tace "amman shanayen ba biyu ne suka rage ba kuma kace zaka sayar da d'aya Saboda hidimar bikin yanzu in ka saida wannan shikenan fa sun k'are" yar dariya yay yace "to ai biyan buk'ata yafi dogon buri sai a gode ma Allah da ya sa akwae" shiru kawae tay acan k'asan ranta kuwa haushi ne ya turnuke ta na Ard'o duk shi ya tattago hidimar ba tare da an shirya ba, shi yakamata ace ai yay kusan duk hidimar amman ya k'ame hannu duk tulin Arzik'in da ke gare shi, shiru Fatuu tay tana bin su da ido can kuma sai ta mik'e ta nufi cikin uwar d'akin bada jimawa ba ta dawo ta nufi gefen baffanta ta zauna da d'an murmushi ta mik'a mashi abunda ta d'aukko, bin yan kunnan dake a tafin hannunta yay da kallo kafin ya maida idanun nashi kanta cikin alamun rashin fahimta tace "Baffa wannan zinari ne kuma 200k aka siye shi in kasan in da ake sayarwa sai ka saida kayi amfani da kud'in" ba shi ba har Yadikko waro ido sukae cike da Al'ajabi baffan ya tambayeta ina ta same su ta fad'i mashi da Ya Haisam makwabcin su zai yi aure ne ya bata kud'in shine Gwaggo ta siya mata yan kunnan, jinjina kai duk sukayi a tare suka shiga yabon Haisam d'in baffan yace "to inna wuro abu mai daraja haka ai bai kamata a sayar dashi ba" yar dariya tay tace ai don ajiyar kudin aka siya tunda yanzu ana buk'ata ba sai a sayar ba, duk yadda tayi K'in Amincewa baffan yayi da a saida yan kunnan yace ta bar abunta zai mata amfani ba abunda zai gagara in sha Allah, bata ji dad'i ba ta yamutsa fuska cike da wasa yace ko tayi kuka ba zai amsa ba gwara ta adana hawayenta, can ta tuna da kud'in da ya tura mata ta siya kayan kitchen ta mik'e da sauri tace to tana zuwa, bayan ta dawo ta d'aura mashi kud'in kan cinyarshi tace "to ga wad'annan su dae dama kai ka tura man kud'in kayan kitchen to kuma an siya komae sai kai amfani dasu sannan ga Atm d'ina akwae dubu 70 a accnt d'in sai ka cire su ka had'a" baki bud'e suke kallonta ganin haka yasa tay mashi bayanin inda ta samu kud'in cikin account d'in nata 50k da Abbas ya tura mata sai dama akwae 20k cikin sauran kud'in Graduation da Haisam ya tura mata, "Amman inna wuro ke ba amfanin da zaki da kud'in ki ne da kin bar su dama na ta6a sadakin ki" da sauri tace "a'a ba abunda zanyi da su Baffa kayi amfani dasu kawai" yace zai cire dubu 50 ta bar 20k d'in ta mata wani amfanin, sosae suka shiga yi mata godiya shida yadikko harda yar k'wallar shi yace in sha Allahu yadda ta za6i farin cikin shi fiye da nata ita ma Allah zai faranta mata haka ya shiga jera mata Addu'oi tana amsawa da Murmushi daga baya ya mik'e yay masu sallama ya tafi. JUMETA babban Parlor ne mai d'auke da set d'in dankara dankaran Sofas da kayan kallo irin dae falon da daka kalla zaka shaida na masu hannu da shuni ne, a kowanne 6angare na bangon d'akin akwae hotuna wanda yawanci duk na yan siyasa ne kama daga d'an majalisa, governor harda na shugaban k'asa, zaune a saman 3 seater Alhaji lawal ne yana sanye da farar jallabiya idanunshi sanye cikin glasses yana kallon labarun yamma a kai akai yake juyawa gefenshi ya kalli Matar shi Hajiya Rabi'atu dake gefenshi tana mashi hira, babbar mace ce saidae bata manyanta ba sosae kana kallonta zaka fahimci hutu ya zauna mata sosae, tana da kyau ba laifi gata jajir da ita sannan tana da k'iba ba irin mai muni ba jikinta sanye da had'addan lace ta kashe d'auri kana kallon ta kaga wayayyar bafullatana, da yar sallama ya shigo cikin parlon duk suka d'aga kai suka kalleshi, matashi ne wanda a k'alla zai iya yin shekaru 35, dogo ne sosae sai dai sam bai da jiki kuma ja ne irin kalar fatar Mahaifiyar shi har kama suke ga sumar kan shi da ta k'ara bayyana shi a matsayin bafullatani don a nad'e take amman bata da yawa, jikin shi na sanye da bak'in silk wando da blue riga mai dogon hannu da ma6allai ya yi zanzaro hakan ya bayyanar da had'addan bak'in belt d'in dake d'aure a k'ugunshi haka hannun shi na sanye da wrist watch silver, saman kujerar dake opposite da su ya zauna fuskar shi sam ba annuri ya gaishe da su duk suka amsa Alhaji lawal yace "Khalid ka dawo?" Amsa mashi yay da "Yes Dad" "To ya aikin?" yace "Alhamdulillah" ita dae Hajiya Rabi'atun kallonsu take tana murmushi, "Dama dalilin da ya sa na kira ka don in sanar da kai Amaryar taka ta iso tun jiya don haka sai ka samu kaje ku gana da juna, sannan duk abunda ya kamata kayi in kaje sai ka tabbatar kayi ma'ana ka sallame ta da abunda zata yi hidimarta don kasan 2 weeks ya rage so we need not to waste time" wani irin k'ara d'aure fuska Khalid d'in yay har saida Dad d'in yace bai ji bane sannan kaman an masa dole ya ce "Ok" kallon Hajiya Rabi'atu yay yace "Ke wurin ki ina fata kin kammala komae" tana murmushi tace "Eh an kammala had'a lefen dama abunda ya rage akwae kayan da za'a d'inka mata already na fitar dasu suna ma wurin d'inkin to amman ba'a d'inka ba Saboda rashin measurement nata tunda ba saninta mu kae ba amman tunda ta zo yanzu ko zuwa gobe sai Sadeeya taje da driver su taho tare aje a d'auki measurement d'in nasan ba 6ata lokaci zai d'inka" jinjina kai yay alamar gaisuwa sai kuma ya maida kallon kan Khalid yace "kai yaushe zaka je d'in?" shiru ya d'an yi sai kuma ya watsa hannu yace "ko Next tomorrow tunda naji zasu wurin d'inki goben" shiru Alhaji lawal d'in ya d'anyi yana d'an tunani can yace "kai yakamata kaje goben ku ga juna zuwa wurin d'inkin sai a bari sai Next tomorrow d'in" d'an yamutsa fuska yay yace Ok daga haka ya fara kokarin tashi ya tambayi shikenan Alhaji lawal d'in yace eh zai iya tafiya yay masu sallama ya nufi hanyar fita................ _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2028* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 28 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .........Bin Khalid da ido Mahaifiyar shi tay har ya fuce fuskarta d'auke da d'an murmushi a ranta take ayyana in ba don yarjejeniyar dake tsakanin shi da Mahaifin shi ba tasan ba yadda za'ai ya yarda da wannan Auren had'in saidae ta wani 6angaren taji dad'in hakan don rashin Auren nashi na damun su tana fatan kuma ya zama silar canzawar shi. Bayan Fatuu ta gama breakfast d'in gyara d'akin ta fara yi yadikko na ta bari tace zatayi, sosae ta gyara su Mino duk sun tafi Makaranta tun kafin ta farka da sun nuna basu zuwa yadikko ta ce in dae don Adda d'in tasu ne ta zo kenan Saboda a garin zata zauna a cikin gidan Gonar Chairman shi kan shi yana zuwa Hutu da iyalan shi wani lokacin amman Khalid d'in ya fi su zama a gidan, bayan sallar Azahar Fatuu tayi wanka ta shirya cikin riga da skirt na atampa da sukai mata cif a jiki dama duk haka kayanta suke sai yan k'alilan d'in dogayen riguna, ganin ta shirya yasa Yadikko matsa mata kan ta daure taje ta gaishe da su Ard'o da Yaya ba don ta so ba ta yafa mayafi mahad'in kayan ta tafi, a nutse take tafiya ta shiga shashen Yaya lokacin da ta shiga ba kowa a filin wurin sai su K'anwar Altine dake wanke wanke a gefe, kallonsu kawae tay ta wuce kaman daga sama taji sun sa Dariya k'anwar Altine tace ma d'ayar mai suna zakiyya "Yar uwata ki bar wani yanga da ji da kai wai ke zaki auri mai kud'i duk fa munsan kalan mijin da zaki Aura" Fatuu na jin hakan ta dakata don sai taji tana son jin wani irin miji ne zata auran dama kuma da biyu suke Maganar shiyasa ma suke yi da hausa, Zakiyyar tace "Bai kamata fa in rink'a yanga ba kuka yakamata in yi zan auri mashayi wanda har giya yake sha ya shigo gari yana niyyar taka mutane da Mota" sosae k'anwar Altine ke dariya kafin tace "dama iya hakan ya tsaya ai da sauki kin manta da d'ayan aika aikar da kowa yasan yana yi...." Da sauri zakiyya tasa hannu ta rufe mata baki tana fad'in kada aji mutuwar sarki a bakin su, wata irin mutuwar tsaye Fatuu tay mi take ji haka game da wanda zata aura, Mashayi kuma! Kuma miye d'ayan abunda yake aikatawar, a hankali ta juya ta kallesu sai tik'ar dariya suke suna kashe wa, wani irin nauyi k'afafunta sukae mata taji tamkar bata iya taka su ga jikinta tamkar ana zare mata laka take ji da k'yar ta daure taci gaba da tafiya, lokacin da ta je kopar d'akin Yaya ji tay kaman ta koma kawae ganin takalma tasan ba ita kadai bace da wasu mutanen kuma a halin da take ciki tsoron k'ara jin wani abun da zai iya tarwatsa mata zuciya take sanin sun iya ya6a bak'ar Magana, shahada kawai tay ta cire takalmanta ta shiga da yar sallama duk mutanen cikin d'akin suka d'ago suna kallonta hakan yasa ta sadda kanta duk suna zaune a k'asa su hud'u sai Yaya d'in na zaune a bakin k'aramin gadon k'arfe idon ta akan Fatuu har ta k'arasa gefenta ta tsaya, d'aya daga cikin Matan ta mik'e tana fad'in bari ta bata abun zama tasan yan birni basu zama a k'asa, darduma ta shimfid'a mata Fatun ta hau ta zauna tay shiru kaman bazata ce komae ba can ta d'aga ido a hankali ta gaishe da Yayar dake ta faman bin ta da ido, d'an ta6e baki tay tace "Amarya Sai yanzu aka ga damar zuwa gaishe dani kenan" shiru bata ce mata komae ba innar su Altine tay yar dariya tace "Yaya kin san Amaryar ta Manyan Mutane ce" d'an guntun murmushi yayar tay tace "haka fa ai na manta mune ma Yakamata muje mu mik'a gaisuwa, an zo lafiya Amarsu?" K'asa k'asa tace lafiya lou, innar su Altine tace "to muma bari mu mik'a gaisuwa ga Amaryar manya, ina wuni Amarya an zo lafiya?" Kafin Fatuu ta bata amsa wata tace "aikuwa saidae mu d'in mu gaishe da itan tunda Yaya ma da k'yar ta samu gaisuwar ballantane mu" ita dae Fatuu shiru tay masu can Yaya tace "sai kuka ji abun arzik'i kwatsam abun farinciki, ai dashi Baffan naki har zai maki bakin ciki Allah ya baki miji d'an Arziki muka dage kai da fata tunda da Arziki a garin wasu ai gara a naku a gidan ku ma, ko ba haka ba?" Banza Fatun tay mata ita dama tasan duk zugar Su ce tasa Ard'o ya tursasa ma Baffanta kan Maganar, tsam ta mik'e tace masu sai anjima Yayan na ba ta bari tasha ruwa ko don kar su je gidanta suma ta basu, bata tanka ta ba ta yi wucewarta tana jiyo yadda su innarsu Altine ke dariya suna fad'in ai kuwa dole a basu ruwa harda Naman kaji ma su da sukae ruwa sukae tsaki za'a auri mai Arziki, bayan fitar ta wata mai suna Hasiya ta kya6e baki tace "Sai wani d'aure fuska take don a ga bata so" a harzuk'e Yaya tace "aikuwa ko mutuwa zata yi sai an yi auren nan badae ita ga mara d'a'a ba bata ganin kowa da gashi an d'aure mata wutsiya ta raina kowa dama nace sai nayi maganin ta ai shiyasa Ard'o na yin Maganar Auren ta da d'an gidan chairman d'in na nace sai abun ya yuwu, inda lafiya lafiya ai wllh cikin yaran ku zan sa wata ta Aure shi a k'yaleta to amman gwara ita ta aure shin yadda zata kwashi kashin ta a hannu waye bai san rashin Mutuncin d'an gidan Chairman ba Mutumin dake taka kowa yadda ya ga dama kinga daidai da ita kenan sai taje tayi mashi rashin kunyar da ta saba ma Mutane" kyalkyacewa da dariya innar su Altine tay tace "ya kuwa sassa6a mata kaman ni wllh, wannan wa zai so yaron shi ya aure shi banda shaye shaye ga lalata yaran Mutane yanzu ji bi yarinyar nan Danejo yadda ya d'irka mata ciki hankalin shi kwance k'arshe kuma ya zubar mata tak'amar shi likita ne" Hasiya ta amshe "yo ai ba itace farko ba mata kala kala yake kawo wa a gidan Gonar nan aka ce harda arna" haka suka cigaba da tattauna mugun nufin su kan Auren Fatuu. Har wani duhu duhu take gani ta nufi sashen su lokacin da ta shiga falon su Mino ne zaune suna cin Abinci hakan yasa ta wuce cikin uwar d'aki ba tare data tanka ma kowa ba, Mino na kiranta ko jin ta bata yi ba, tana shiga ta haye saman gado can k'arshe tayi rubda ciki tana numfashi da k'arfi da karfi tana zare ido waye wanda za'a aura mata? Da gaske mai shaye shaye ne? Ita da a rayuwarta ta tsani mashayin mutum shine yanzu zai zama mijinta, shin miye d'ayar aika aikar da taji su zakiyya sun fad'a? Tana haka Mino ta shigo ta zauna a bakin gado tana kallon Fatuu ganin tak'i ce mata komae yasa a sanyaye tace "Adda Fatuu" shiru bata amsa mata ba bata kuma kalleta ba Mino ta sake cewa "Adda Fatuu miya faru kin yi shiru?" Sai lokacin ta kai idonta kanta amman still ta kasa tanka mata ganin hakan yasa ta mik'e ta fita bada jimawa ba sai gata sun dawo tare da Yadikko, a bakin gadon ta zauna ta kai hannu ta ta6a jikin Fatun da harshen fulatanci ta shiga tambayarta lafiya Mike damunta can ta yunk'ura ta tashi zaune idonta akan yadikko cikin karyayyar Murya tace "Don Allah waye za'a Aura man??" Da mamaki yadikkon tace "dama Baffan ki bai fad'i maki wanda zaki Auran ba?" da sauri tace "Ya fad'i man d'an Chairman ne amman ina son ki fad'a man wane irin Mutum ne?" Dam k'irjin yadikko ya buga ta hau had'iye miyau ganin ta kafe ta da ido alamar jiran amsa take yasa tace "Mutum ne kamar kowa kuma likita ne...." Katse ta Fatuu tay "ba wannan nike son sani ba wane irin hali gare shi?" Shiru yadikkon tay tana kallon Fatun ganin haka yasa tasa mata kuka ta kama hannuwanta tana fad'in "ki fad'a man yadikko don Allah da gaske Mashayi ne?" Zaro ido tay cikin rawar murya tace waye ya fad'a mata hakan nan take ta kwashe firan da ta ji su zakiyya nayi ta fad'a mata, shiru bakin yadikko ya mutu don bata san mi zata ce mata ba Fatun ta hau rok'onta kan ta fad'a mata, juyawa yadikko tay tace ma Mino da ke yin hawaye ta fita ta ce to, bayan ta fita yadikko ta juya kan Fatuu ta kama hannuwanta tace "haka ake cewa amman ni ban san ko gaske bane tunda ban ta6a gani da ido na ba na dae san shi tunda yana yawan zama nan gidan Gonar bayan ya gamo karatun likitancin da yayi a K'asar waje..." Tun kan ta rufe baki Fatuu ta tari numfashin ta "to bayan shi naji sun ce akwae wani abun da yake aikatawa miye?" Wani abu Yadikko ta had'iya a ranta take raya taya zata ce mata yana neman Mata ko shaye shayen ta san da gaske yana yi don kada ta tada mata hankali ne yasa ta nuna mata bata san ko gaske bane, ganin tayi shiru yasa Fatuu d'an girgiza hannunta tace "Yadikko ta don Allah kar ki 6oye man ki fad'a man" sauke ajiyar zuciya tay cikin rawar murya tace "k...kin gane w..wai ana zargin yana neman Mata ne a gidan gonar da yake zama....." Zaro ido Fatuu tay a kidi'me tace "Neman Mata kuma kenan Mazinaci za'a Aura man!!" ganin yadda ta rud'e yasa da sauri yadikkon tace "a'a fa kawae ana zargi ne wai ana ganin shi da mata amman kuma ai zai iya yuwuwa Abokan aikin sa ne tunda ba wanda ya ta6a shiga ya kama su suna aikata ba daidai ba kinsan irin Wannan baka saurin gasgata wa" girgiza kai Fatuu ta shiga yi cikin kuka take fad'in "ai yadikko in dae aka cika Maganar abu to tabbas akwae alamar gaskiya, mi zai sa ya rink'a zuwa da mata gidan gona in Abokan aikin nashi ne suyi aikin acan wurin aikin su mana, ni dae na bani na lalace k'arshe na ya zo za'a lalata man rayuwa taya zan yi rayuwar Aure da Mashayi kuma Mai neman mata, Ya akai Baffana ya amince a jefa man rayuwa cikin had'ari yadikko ya akai kuka amince bacin kun san halin shi haka yake so kuke ya lalata man rayuwa ne??" Itama Yadikkon kukan ta sa tana fad'in "a'a Fatuu kar ki ce haka Don Allah kin fi kowa sanin yadda muke son ki muka damu da rayuwar ki hakan ne ma yasa lokacin da Ard'o ya sanar da zancen Auren naki Baffan ki ya shiga mawuyacin hali har yay sanadin kwanciyar shi ciwo duk Saboda jin Mutumin da za'a aura maki k'arshe dae har zuwa yay wurin Chairman ya rok'e shi kan a hak'ura da had'a ku Aure koda ya tambaye shi dalili bai 6oye mashi komae ba game da halin yaron nashi da ake fad'a kuma ya nuna mashi ke karatun likita kike son yi anan ya nuna mashi ya kwantar da hankalin shi in dae wannan ne damuwar shi to saida ya tabbatar da d'an nashi ya shiryu ya daina komae sannan kuma har yarjejeniya sukae kan ko bayan auren ya kama shi yana aikata wani abu ba daidai ba sai ya sa6a mashi don dama a bisa sharad'i ya nema masa auren kuma ya tabbatar ma Baffan ki cewa da kunyi auren zaki cigaba da karatun ki don ya fahimci kina da kokari sosae tun lokacin da ya fara ganin ki tun sannan yaji kin burgeshi har yayi sha'awar D'an nashi ya aure ki, wannan ne dalilin da ya sa har Baffan ki ya gamsu sanin chairman d'in Mutumin Arzik'i ne ba zai ta6a had'a aurenku don son zuciya ba" shanye kukan Fatuu tay sai taji hankalin ta ya d'an kwanta ganin haka yasa Yadikko cigaba da lallashin ta tana k'ara kwantar mata da hankali had'i da nuna mata wani abun da biyu suka fad'a dama don su tada mata hankali su k'untata mata, ganin ta d'an samu natsuwa yasa ta d'agota ta tambayeta taje ta gaida Ard'o ta girgiza mata kai alamar a'a ta ce to ta daure taje in Baffanta ya dawo yaji bata je ba bazai ji dad'i ba a sanyaye tace to ta sauka daga saman gadon ta fita idon yadikko akan ta cike da tausayi take kallonta tana d'an girgiza kai. Koda taje iske shi tay da Mutane hakan yasa ba yabo ba fallasa ta gaishe su ta juyo ta dawo ta koma kan gado tay lamo. Sai bayan Magrib Baffanta ya shigo d'akin lokacin duk sun gama salla suka gaishe shi da fara'a ya amsa kafin ya zauna a nan yake sanar da yadikko game da zuwan wanda Fatun zata Aura gobe in Allah ya kaimu da yamma ta amsa da to ya nuna mata k'atuwar ledan da ya shigo da ita yace ga cefane nan sannan a yanka kaza ayi amfani da ita wurin shirya mashi Abinci ta amsa da to Fatuu dae tay tsit kanta a k'asa don wani irin bugu kirjinta ke mata jin wanda aka ce zai zo d'in, ganin yanayin ta yasa Baffan tambayar ta lafiya ta d'ago da d'an murmushi tace mashi lafiya lau daga baya ya fita, da daddare bayan ta kwanta duk kewar gwaggo ta dame ta don har yanzu basu yi waya ba can ta d'auki wayarta ta kirata tana jin ta fara ringing ta tashi zaune har kiran ya kusa katsewa bata yi picking ba har Fatun ta fidda ran zata d'auka sai gashi gab da zai tsinke ta d'aga tay yar sallama wani kalan lumshe ido Fatuu tay da d'an murmushi ta gaidata gwaggon ta amsa mata suka d'an yi shiru can gwaggon tace "anje lafiya, koda yake mun yi Magana da Kamalu yace kun isa lafiya" Fatun ta amsa mata da lafiya lau daga haka tace mata ta kwanta sai da safe bata jira cewarta ba tay cutting kiran, cire wayar tay daga kunnanta ta bita da ido kawae. Washe gari tun bayan da ta gama gyara d'akunan da suka gama karin kumallo wanda bata wani ci sosai ba ta yi wanka tasa doguwar riga ta haye gado, tana kwancen yadikko ta shigo ta zauna gefen gadon da d'an murmushi tayi mata sannu a hankali Fatuu ta amsa mata da yauwa yadikkon tace "Dama shawara nazo tambaya ku yan birni kun fi mu sanin kalolin Abinci masu dad'i wanne kike ganin ya kamata ay ma bak'on naki" shiru Fatuu ta d'an yi sai kuma cikin sanyin murya tace "Yadikko kema ai kin san Abincin masu dad'i ko" yar dariya tay tace "to ai duk na manta zuwa yanzu kuma ai nasan akwae wasu iri iri da ni ban sani ba" kaman bazata ce komae ba ganin yadikkon na kallonta yasa tace "ba naji Baffa yace a yanka kaza ba kawae ayi mashi pepper chicken ba sai anyi wahalar yi mashi wani Abinci na daban ba" shiru yadikkon ta d'an yi alamar tunanin sai kuma tace "amman kina ganin shi kawae ya isa, kamar da Abincin zai fi nike gani" d'an ta6e baki Fatuu tay tace "ai ba lalle fa yaci Abincin ba fa in aka yi wannan d'in sai a had'a mashi da fura sai in ga ya isa" cike da gamsuwa yadikkon tace hakan yayi ta mik'e Fatun ma ta yunk'ura zata tashi tace mata tay kwanciyar ta zasu yi komae dasu Mino daga haka ta fita, komawa tay ta kwanta don duk jikinta a sake yake ga fargaba had'i da zullumi da suka mata yawa, Bayan sallar Azahar Baffan ya dawo ya kawo Drinks masu sanyi yace ma yadikko tasa wanda za'a bashi cikin cooler sauran sai su sha tayi mashi godiya, koda Fatuu tay salla komawa tay ta kwanta da aka mata Maganar Abinci cewa tayi ba yanzu ba saida Yadikko ta matsa mata sannan ta d'an tsakura kad'an, ganin har k'arfe ukku tana kwance yasa Yadikko ta shiga tayi mata Magana kan ta tashi ta shirya kar yazo kuma bata kimtsa ba, zuru Fatuu tay mata har saida ta k'ara mamaita abunda tace Matan sannan tace ba sai ta shirya ba ai tayi wanka d'azun, "To ki tashi ki canza kaya ko" tsuke fuska tay idanunta har sun kawo ruwa ganin haka yasa yadikkon fara rarrashin ta ta shiga nuna mata in tayi shigar kirki hakan zai sa ya mutunta ta amman in taje mashi a yamutse zai iya raina ta, da k'yar ta tashi don ta shiryan, wanka tayo lokacin an fara kiran la'asar hakan yasa ta d'auro Alwala saida tay salla sannan ta fara kokarin shiryawa tama rasa wane kaya zata saka can dae ta fiddo wata straight gown ta Maroon lace da touch d'in golden ta saka ta sa yan kunnan zinarin ta da yan hannu tana cikin shiryawa ta jiyo Muryar Kamalu a Parlor yana fad'in "Yadikko ga bak'on nan ya iso" ta amsa mashi da to ta mik'e tana tambayar yana ina ne yace mata yana a Fadar Ard'o, shigowa tay cikin uwar d'akan ta iske Fatuu zaune a gefen gado ta rafka tagumi itama ta zauna gefenta ta dafa Shoulder d'inta tace "bak'on naki ya iso Fatuu" kallonta tay ta fara d'an ta6e baki alamar zata fara kuka yadikko ta girgiza mata kai tace "Don Allah Fatuu ki yi hakuri ki fawwala ma Allah komae, shi mai ji ne kuma mai gani yafi kowa sanin halin da kike ciki don haka ki dogara da shi na tabbatar zai baki mafita ya za6a maki abunda yafi Alkhairi gare ki" d'aga mata kai tay ta kama hannunta ta mik'ar da ita, gaban mirror ta kai ta tasa ta ta shafa powder har jan baki tace ta shafa amman ta k'i tasa lip glow kawae yadikkon ta gyara mata d'aurin kallabin ta ya zauna sosae gashin ta dama ta lankwasa shi ya fito yay tum a baya, golden brown gyale mahad'in kayan ta yafa haka takalma ma sosae tay kyau duk da ba wani make up tay ba, tun da ta fito ta nufi hanyar soron k'irjinta ke bugu tamkar ana mata luguden ta6are hakanan take jin tsananin fargaban zuwan ganin abun take kaman almara ba gaske ba wai wurin wanda zata Aura nan da sati biyu zata je, da yar sallama ta shiga lokacin da ta k'arasa ko cire takalman k'afafunta bata yi ba tun a bakin kopar kamshin turaren da ya baza a jikinshi ya d'aki hancinta, a d'arare ta idasa shiga idonta a kan shi yana zaune akan kujerar da Ard'o ke zama ya sadda kanshi yana latsa wayarshi yana sanye da shadda brown wanda ta hau da fatar jikin shi sosae anyi mashi irin fav d'inkin Haisam wato senator style saidae basu amshe shi kaman yadda suke amsar jikin Haisam ba don yanayin halittar jikin ba d'aya ba, bai sa hula ba hakan ya bayyanar da sumar shi dake a lallank'washe hannunshi sanye da brown wrist watch, ba laifi shigan tay kyau kana ganin shi kaga wayayyan d'an boko, tsaye tayi daga d'an can nesa bayan ta shigo tana kallon shi tana haka su Mino suka shigo da kayan Abinci suka nufi gaban shi suka aje had'i da gaishe dashi kaman bazai amsa ba sai kuma yace "lafiya" ba tare da ya d'ago ba balle su samu Arzik'in kallo suka juya suka fita, sun d'auki lokaci a haka sai da ya mula ya sha iska sannan slowly ya d'ago ya sauke mayatattun idanunshi tamkar na mai jin bacci akan Fatuu dake tsaye a gaban shi, kallo suka bi juna da shi tun bayan da ya d'ago Fatuu ke mashi kallon sani hakanan taji kaman ta ta6a ganin shi to amman a ina? Shine abun da take son ta gano, wani irin jarababben kallo yake bin ta dashi from head to toe tsam ya mik'e walking slowly toward her, a gabanta ya tsaya har saida Fatun tay stepping back Saboda yadda ya k'ure mata, a hankali ta kai idanunta kan fuskar shi lokaci guda k'irjinta yay wani irin bugu tuna inda ta ta6a sanin shi d'an buda ido tay sai kuma da sauri ta sadda kan ta kasa, "Why am I having d feeling dat I know u somewhere??" taji husky voice d'in shi ta fad'a wato shima ashe yaji ya santa wani wurin, K'in d'agowa tay gaban ta naci gaba da fad'uwa wani irin mugun tashi hankalinta yay ganin shi matsayin Mutumin da zata aura, "Hey!" taji ya fad'a da d'an d'aga Murya a hankali ta d'ago duk ta kame kanta sai zare ido take ya k'ara kankance idon shi yana kallon ta da alama so yake ya tuna inda ya santa can bayan d'an lokaci kawae sai gani tay yay wani kalan murmushin mamaki ya d'an kya6e baki kafin ya furta "Wonders Shall Never End, so u'r My Wife to be!!!" bin shi da ido kawae take sai faman sakin Shu'umin Murmushi yake......... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2029* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 29 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* .......Juyawa yay walking majestically ya koma inda ya ta so ya zauna idon shi a kanta, "zaki ta tsayuwa ne?" Ya tambaya had'i da d'age mata gira wani kuka cikinta ya fara yi, kaman k'wai ya fashe mata a ciki ta fara moving zuwa gefe inda wata kujerar take ta zauna tana cigaba da kallon shi, "From all indications kema kin gane husband to be en naki ko?" wani wahalallan miyau ta had'iya bata dae ce komae ba, "I ave been wondering wata kucakar Dad ya sama man matsayin Mata a Wannan tsukukun k'auyen ashe ba kucakar bace mara kunya ce mai zagin iyayen Mutane" still bata ce mashi komae ba yaci gaba "But duk da haka am so happy Dad has made a right Choice for me, it's nice meeting you my lovely wife" bakin Fatuu fa ya mutu murus ba kamar da ta ga irin murmushin da yake saki tasan ba har zuciya yake fad'ar abubuwan da yake fad'i ba, "Kin bi ni da ido ko baki farin ciki da ganin husband en naki bane shiyasa ko Welcoming dina bazaki ba balle in sa ran za'a gaida ni, koda yake I know who my wife to be is ba lalle in ta iya gaida Mutane ba" d'an motsa baki tay sai kuma ta sunnar da kai katsa yayin da a cikin ranta ta furta innalillahi Wa'inna ilaihir raji'un, sam ta kasa bud'e baki tace wani abu don ba k'aramin Al'ajabi ne ya kamata ba, a hankali ta saci kallon shi taga still kallon ta yake hakan yasa ta idasa dagowa cikin trembling voice tace "ina wuni an zo lpy" d'an tafa hannu yay yace "Wow what a sweet voice, lafiya lou wife hope na same ki lpy?" tabdijan ya gama kashe Fatuu da mamaki duk yadda tay zaton zai mata ba haka take gani ba ganin tayi kasak'e tana bin shi da ido yasa ya d'age mata gira yace "Wife Kaman ke baki farin cikin gani na a matsayin wanda aka za6a maki ba ko" murya a hard"e tace "a'a nayi" jinjina kai yay yace "To ya Katsina fatan kin zo lafiya" tana d'an kikkafta ido tace mashi lafiya lau yaci gaba "dama ina ji ana cewa Katsina akwae beautiful babes masu ilimi da wayewa yanzu na shaida haka even though ke d'in asalin yar nan ce amman su suka maida man ke yadda nike son wife ena ta kasance" ya k'arasa yana wani juya yaudararrun idanun sa, sunnar da kanta tay k'asa don Maganar tashi ba wanda ta tuno mata sai Haisam Saboda shi ne ya maida ta yadda take, "na fa san kina Magana so ki daina acting as if baki magana ko yana maki wuya, ki saki jiki ki kuma bud'a baki ki man magana kaman ranar da kika zage ni" da sauri ta d'ago ta kalle shi ya bud'a mata ido d'an yamutsa fuska tay cikin breaking voice tace "ni fa ba zagin ka nayi ba kuma Kaine ka fara zagi na ai" Shegen murmushin shi ya saki yace "kika rama kuma ko, anyway ai baki ji nace kin yi laifi ba ya wuce koma kin yi ai Amarya bata laifi if u wish yanzu ma zaki iya zagi na I won't feel offended" ya ilahi ya rabbil alamen mutumin nan nema yake ya tarwatsa ma Fatuu zuciya, shiru suka d'an yi sai faman k'are mata kallo yake can yace "Wife ina buk'atar ruwa or I should serve myself ?" a hankali ta juya ta kalleshi sai kuma ta mik'e ta nufi gaban shi ta duk'a ta fara kokarin zuba mashi lemu hannunta har d'an rawa yake, bayan ta zuba ta d'ago da niyyar bashi taga gaba d'aya hankalin shi na a wani wuri a jikinta hakan yasa ta d'an d'ukar da idonta don taga abunda yake kallo ashe saman boobs d'inta da sukae fam fatar wurin fari fat da ita ya kafe da ido yana kallo sakamakon wuyar rigar da yake a bud'e sosae, da sauri ta ja gyalen ta rufe wurin hakan ya sa shi dawo wa cikin hayyacin shi ya kalleta da murmushi kafin ya kai hannu ya amshi glass cup d'in had'i da furta "thanks my beautiful wife" mik'ewa tay ta koma ya bi bayanta da kallo har ta zauna sannan ya kai cup d'in baki ya fara sipping lemun saida yasha kaman rabi sannan ya ajiye ya kalleta ta d'ukar da kanta tana d'an wasa da yatsunta taji ya d'an yi gyaran murya hakan yasa ta kalle shi yace "Wife miye labari" d'an watsa hannu tay tace "babu" yace "What about preparations na bikin mu?" Kaman bazata ce komae ba sai kuma tace "ana yi" gyara zama ya d'an yi yace "Ok dame dame zaku yi ne?" tace "ba komae" d'an buda ido yay alamar mamaki yace "Haka zaku yi bikin ba wasu programs kaman zaki auri enermy en ki" ido kawae take bin shi da shi yaci gaba "koda yake baki da Friends anan ko?" Kai kawae ta d'aga mashi ya jinjina nashi, "To yanzu kaman nawa kike buk'ata na abunda kike ganin zaki yi like gyaran jiki and so on" ya tambaya, tace "zanyi ba sai ka bani ba" yar dariya yay ya d'an shafi sumar shi yace "Ashe wife en nawa Hajiya ce" shiru bata ce komae gaba d'aya sai taji ta k'agara ma ya tafi kota koma ciki don gaba d'aya kanta a d'aure yake bata da natsuwa, "Gobe sister d'ina zata zo zaku je wurin tailor zai taking measurement naki sai ki shirya" kallon cikin ido tay mashi yace "let me have ur digits so dat lokacin da zasu zo sai in sanar maki" karanto mashi phone number d'in ta tay bayan ta gama ya kira jin wayan na ringing ba anan ba yasashi tambayar inda wayan take tace tana cikin gida yace to in ta koma sai tay Saving harda fad'i mata sunan shi Khalid ya tambayi nata tace mashi Fateema yana murmushi ya furta "Fatima Zaraah" har saida kirjinta ya buga damm, ganin yana kokarin mik'ewa yasa tace bai ci Abincin ba yana wani kashe mata ido yace he's Ok bai jima da ya ci Abincin ba but next time in ya zo zai ci daga haka ya mik'e itama tana ganin hakan ta mik'e ya nufo in da take ya tsaya suna facing juna ya kafeta da mayaudaran idanunshi seductively ya furta "Hope ban yi laifi ba da ban ci ba kar next time a ki dafa man don nasan girkin ki must ba as hot as u'r" wani dam dam k'irjin ta ke yi ganin yadda yake mata Magana ba zato ba tsammani sai ji tay ya kawo hannu ya janyota ya had'e jikinsu a gigice ta shiga kiciniyar kwace jikinta saidae ta kasa a rud'e tace "Don Allah ka sake ni kar wani ya shigo fa ayi tunanin wani abu nike yi" gaba d'aya ya zuba ma lips d'inta ido yadda tay Maganar ba k'aramin tafiya tay da shi ba kokarin had'a face d'in su yake a kidi'me Fatuu ta tattara duk k'arfinta ta tura shi tay baya ta fad'a kan kujerar da ta tashi, wata yar iskar dariya ya saki yace "Wife zaki ji ma kan ki ciwo fa and miye abun rud'ewa haka kaman na aikata wani abu ba daidai ba, ko basu yi informing naki an biya sadakin ki bane?" Kasa cewa tay komae sai numfashi take fitarwa da sauri da sauri duk ya gama tsorata ta, still dariyar yake yace "I forgot wife en tawa Secondary graduate ce but at least be romantic Babe" daga haka yasa hannu a cikin Aljihun rigarshi ya fiddo rafar yan dubu dubu guda biyu ya d'aura mata akan cinyarta kafin ya sake sa hannu a aljihun ya fiddo farin glass ya sa a fuskar shi yana murmushi yace sai sun sake had'uwa daga haka ya fice, Mutuwar zaune Fatuu tay tama rasa tunanin da zata yi akan shi da k'yar ta iya yunk'ura wa ta mik'e jikinta har lokacin rawa yake ta nufi cikin gidan a kan hanya ta had'u da Mino tace mata taje ta kwaso kayan abincin da suka kai tace to, a Falo ta iske yadikko zaune tana ganinta tay mata Murmushi tace har ya tafi ta d'aga mata kai kafin ta wuce cikin d'aki tana shiga ta cillar da takalmanta ta cire gyalen shima ta wurgar ta haye gadon sai zare ido take tunani kala kala acikin ranta ba kamar akan had'a jikinsu da yay hakan yasa ta fara shakkun anya ba gaskiya bane yana neman mata in ba haka ba mi zai sa daga fara haduwar su yau ya had'a jikinsu bama wannan ba kadae har fa kusan had'a bakunan su yay ba don ta samu ta fizge ba, wata zuciyar kuma ta ayyana mata ai yace don an biya sadakin ta ne to amman ai ba'a d'aura masu aure ba ko, gashi sam ta kasa yadda da yanda ya sake mata sai take ganin kamar akwae dalilin hakan, tana ta zancen zuci har Yadikko ta shigo bata sani ba saida ta zauna ta kira sunanta sannan ta kai idanunta kan ta, tambayarta tay lafiya dai ko taga ta shigo ta kwanta ko wani abun ya faru ne ta k'ak'alo murmushin yak'e tace mata a'a lafiya lou, "To Allah yasa dae kun fahimci juna yayi maki kuma" d'an ta6e baki Fatuu tay a sanyaye tace "koma bai man ba yadikko ya zanyi dole ai in Aure shi ko" shiru tay tana kallonta gaba d'aya tausayinta take ji don daga yanayin ta sai taga kaman bai mata ba, tambayarta tay ya akai taga bai ci komae ba Fatun tace "Yace ya k'oshi sai ya sake dawowa zai ci" jinjina kai tay tace mata to ta taso suje ta ci farko taso ta k'i tace ta k'oshi saida Yadikkon ta matsa mata sannan ta saukko lokacin ta nuna mata kud'in da ya batan na abubuwan da zata yi tace to ta ruk'e a wurinta. Da daddare tana cikin yin shirin kwanciya sai ga kira ya shigo wayarta koda ta duba bata gane mai kiran ba hakan yasa tak'i d'agawa taci gaba da abunda take sai gashi an sake kiran, zama tay bakin gado ta d'aga ba tare da ta ce komae ba on the other hand taji ance "Wife ko kin yi bacci ne" rass gabanta ya buga jin muryarshi sai lokacin ta tuna da d'azun ta bashi no dinta har ya kira yace tay Saving, sake maimaita tambayar da yayi mata yay sai lokacin tace mashi a'a yanzu zata kwanta, "Gani na kasa bacci Saboda tunanin ki wannan shi ake kira da luv at first sight all I need in ji ki gefe na hope kema hakan?" shiru tay mashi har saida ya k'ara tambayar tata sannan ta tura baki tace "a'a" tana jiyo sautin dariyar shi yace "Don't worry Babe zan koya maki yadda kema zaki rink'a jin hakan game da ni" shirun dae ta k'ara ita duk ta fara tsorata ma da shi haka ya dingi yi mata kalaman soyayya harda tambayarta wace tarba zata mashi a first night d'in su ita dae a tak'aice take bashi amsa wani wurin kuma ta mashi shiru jin shiru shirun nata yay yawa yasa shi tambayar ko ta fara jin bacci ne tace mashi eh yace bari ya barta ta kwanta harda cewa tayi bacci mai dad'i kuma tayi mafarkin shi shima zai yi nata ita dae shiru tay mashi tana niyyar cire wayar taji sautin wani matsiyacin kiss da yay mata har cikin dodon kunnanta da sauri ta cire wayar ta k'ura ma screen d'in ido kirjinta na beating very fast can ta runtse idanunta sai ga kwalla sun fara zubowa ba kowa ne ya fad'o mata a rai ba face Ya Haisam ji take inama shine yake nuna mata so haka ba wannan ba da take tunanin duk k'arya ne da biyu yake mata hakan ba don yana sonta tsakani da Allah ba, tana ta tunane tunanenta har bacci yay awon gaba da ita, Washe gari bayan sun kammala yin breakfast ta gyara d'akin sai ga kiran shi wai ya kira ya ji ya ta tashi tace mashi lpy Lou anan yake sanar da ita ta shirya around 1:00 za'a zo atafi da ita ta amsa da to, lokacin ta sanar ma yadikko ita kuma ta kira Baffanta a waya ta gaya mashi yace to ta dawo lafiya ta so ace Mino ta dawo daga Makaranta ta rakata, wurin karfe d'aya saura tana cikin shiryawa yadikko ta shigo cikin d'akin ta sanar da ita game da zuwan wadda tazo tafiya da ita wato Sadeeya tace to, doguwar rigar shadda sabowa dal acikin irin kayan da Haisam yayi mata Navy blue tasha aiki blue da fari yayi kyau sosae ta sa yan kunne da sark'a sai Agogo duk silver sai farin mayafi haka takalma ma high heels ne farare ta d'auki yar clutch dark blue, a saman kujera Sadeeya ta zauna ita da wata yarinya da zata yi shekara bakwae da suka zo tare tana sanye da jeans da t-shirt kanta sanye da hula da bayanta ya d'an yi tudu alamar gashin ta a fake yake, itama Sadeeyar a shekaru zata yi shekara 25 zuwa 26 itace k'anwar Khalid ta biyu, ta farkon wato Yayar Sadeeyar tayi Aure, a ABU Zaria Sadeeya ke karatu itama fara ce saidae bata kai Khalid haske ba sannan ita da Chairman take kama duk da ta wani 6angaren ta d'an yi yanayi da Khalid d'in tana da d'an jiki ba kamar khalid ba, sanye take da doguwar rigar atampa d'inkin Abuja Boubou ta kashe daurin kallabi hakan ya bayyanar da wutsiyoyin kitson dake kanta da ta tubke, da fara'a lokacin da yadikko ta fito ta sanar mata Fatun na fitowa tana k'arasa shiryawa ne itama tana fara'ar tace Ok ba damuwa, ruwa da Abinci yadikko ta kawo masu Sadeeyar na cikin shan ruwan Fatuu ta fito ba shiri ta cire cup din daga bakinta ta bi ta da kallo wanda ke bayyanar da mamaki akan fuskarta, sam bata taba tsammani ganin ta hakan ba duk da ta samu labarin ba anan take ba batai tunanin ganinta a waye haka ba ba kuma kaman da taji Secondary graduate ce, kujerar dake gefen su Fatuu ta nufa ta zauna fuska a d'an sake ta gaishe da Sadeeyar da sauri tace "Ah Auntyn mu ni ai yakamata in yi wannan" tay Maganar tana ma Fatuu dariya ita dae d'an murmushi kawae tay kafin tace sun zo lafiya Sadeeya ta amsa mata da lafiya lau, shiru sukae Fatuu ta lura da kallon da take mata hakan yasa ta d'an juyar da kanta gefe, can Sadeeyar tace "Auntynah if u done we can go driver is waiting for us outside" juyowa Fatuu tay ta kalleta sai kuma ta kalli Abincin gaban su a nutse tace "But u aven't ate d Food" d'an lumshe ido Sadeeya tay kafin tace "bamu jin yunwa ne amman tunda kin yi Magana bari mu d'an ci" tana niyyar tashi don ta zuba masu Sadeeyar tace mata ta bashshi bari ta zuba masu yarinyar da suka zo tare sai kallon Fatun take can ta d'an duk'a saitin fuskar Sadeeya tace "Aunty Sady who is she?" d'agowa tay tana yar dariya tace "she's ur New Aunty Ya Khalid's bride" waro ido yarinyar tay Sadyn tace taje ta gaida ta ta nufi Fatun tana zuwa ta tsaya gabanta ta gaishe ta da turanci Fatun ta amsa mata ta tambayi sunanta tace mata Basma, ba wani mai yawa Sady ta ci ba ita basma ma bata ci ba suka tashi don tafiya Yadikko tace ma Fatuu ta biya dasu su gaisa da Yaya ba don ta so ba ta amsa mata da to kawae itama Yadikkon gudun tsegumi yasa tace su je don zai iya zama abun Magana, kaman ko yaushe tana zaune da yan taya ta gulma su ukku lokacin da suka shiga cikin d'akin Yaya na d'aura idonta kan Sadeeya ta gane yar gidan Chairman ce hakan yasa ta nuna mata gefen gado tace ta zo ta zauna ita dae Fatuu tsaye tay Sadeeya ta shiga gaishe dasu da fara'a suka amsa suna ma Basma wasa, Yaya ce ta tambayi Sadeeya daga gidan Chairman ko tace mata eh sun zo zasu tafi da Amarya ne za'ai mata awon d'inki ta jinjina kai alamar gamsuwa daga baya ta mik'e tay masu sallama suka fita ba tare da Fatuu tace ma kowa komai ba, bayan fitar su Yaya ta ta6e baki had'i da yamutsa fuska cikin harshen fulatanci tace "Yi ma yarinyar can aure ba k'aramin rufa mata Asiri akai ba don Allah kadae yasan abunda take aikatawa a can, kuji irin yadda take saka sutura kai kace itace d'iyar Chairman d'in ma a ina ita kakar ta ta taga kud'in da zata rinka d'inka mata suturun da da gani masu tsada ne" Hasiya ta kar6e "ai fa dama da gani idonta a bud'e yake wllh" Yayar tace "kin ga an za6a mata miji daidai da ita kenan" haka suka cigaba da yi ma Fatun kazafi, suna fita kopar gida Driver ya fito ya bud'e ma Fatuu kopa bayan ya gaidata ta amsa mashi a sake Sadeeya ta zagaya d'ayar kopar ta shiga Basma kuma ta shige gaba, Tafiyar kamar Minti 35 ta kawo su a bakin k'aton gate d'in gidan Driver yay horn mai gadi ya lek'o kafin ya koma ya bud'e masu ya shigar da Motar, bayan sun fito da murmushi Sadeeya tay ma Fatuu jagora zuwa cikin gidan lokacin da suka shiga Main Parlor d'in gidan ba kowa hakan yasa tace ma Fatuu su je cika ta nufi wata babbar kopa suna shiga wani madaidaicin Parlor ne da bai kai na farkon ba, zaune akan sofa 3 seater Hajiya Rabi'atu ce jikinta sanye da doguwar rigar Atamfa a gefenta kuma wata mata ce itama tana sanye da doguwar rigar shadda kafad'arta d'aya rataye da gyale da gani bak'uwa ce tayi, suna shigowa duk suka kalle su da sauri Sadeeya ta d'aga gyale ta rufe saitin Fatuu tana dariya tace "Mom sai kin biya zaki ga face en bride d'in mu" tana rufe baki Basma ta ruga ta fad'a saman jikin Mom d'in nasu tana dariya tace "Mom she's very beautiful" d'an buda ido Mom d'in nasu tayi sai kuma ta d'aga basmar ta mik'e tana dariya ta nufi Sadeeya tana zuwa tasa hannu ta d'an tureta gefe tana fad'in sai ta ja mata rai zata bari taga Daughter d'in ta gaba d'aya harda k'awar tata sukae dariya, had'a ido sukai da Fatuu bayan ta janye Sadeeyar ta bi ta da kallo hakan yasa Fatuu ta sadda kan ta k'asa, tana sakin kayataccen murmushi tace "U'r highly welcome My Beautiful Daughter nayi matuk'ar farin cikin ganin ki" a hankali Fatuu ta d'ago ta kalleta a sanyaye ta gaishe da ita tana ta fara'a tace su je ta zauna sai su gaisa sosae tay patting shoulder d'inta suka wuce, kan one seater ta Zaunar da ita kafin ta koma inda ta taso itama ta zauna k'awar tata tace "in ce Amaryar Khalid d'in ce" ta amsa mata da itace tace "Ma sha Allah kyakkyawa da ita Allah yasa Alkhairi ya kaimu Ranar" duk suka amsa da Amin idon Momy akanta tana ta mata murmushi ita dae Fatuu sai faman sussunar da kai k'asa take, "Daughter fatan an zo lafiya" ta tambayi Fatun a hankali tace mata lpy lau ta k'ara cewa "Ya Grandma d'in taki ance a wurinta kike zaune" wani iri Fatuu taji jin an ambaci gwaggo kafin ta d'an kalleta tace tana lafiya, "Ya karatun ki ai kin gama ko" kai Fatuu ta d'aga tace eh, "Mom ya kika ga Amaryar Ya Khalid?" Sadeeya ta tambaya Yar dariya tay ta furta "Tubarkallah Daughter d'in nawa, sai fatan Allah ya kaimu ya basu zaman lafiya da fahimtar juna" duk aka amsa da Amin, kallon Sady tay tace taje tasa a shirya table ta amsa da Owk ta mik'e ta fita suka cigaba da hira da bak'uwar tata sai dae akai akai take juyawa ta kalli Fatun da murmushi wani lokacin su had'a ido, bayan Sady ta dawo ta sanar da Momy an shirya tace to suje da ita taci Abinci Fatuu tace ta k'oshi amman tace dole ta ci ai nan gidan su ne yanzu ta mik'e suka fita da Sadeeya, bayan fitar su k'awar tata ta kalleta tace "a ina take ne?" Momy ta bata amsa da a Kt take zaune tace "University ta gama ne naji kina ta gama karatu?" d'an girgiza kai tay tace "No, I mean Secondary school" jinjina kai tay tace "yanzu nan Secondary graduate ce haka wayayya da ita kai kace yar Jami'a ce" Momy ta amshe "Wllh Hajiya Safeena nima cikin raina saida nayi mamakin ganin ta haka don I never thought zan ganta haka duk da nasan ba a k'auyen take ba har na fara tunanin akwae abubuwan da yakamata a k'ara zubawa acikin lefenta" Dariya Hajiya Safeena tasa tace "to da ba'a sa na kirki bane komi?" Itama Momy dariyar take tace"Ah ba laifi an sa kaya masu kyau to saidae ganin dressing d'in jikinta yanzu gaskiya we need to add wasu kayan taje tay ta d'aukar wanka tana kashe mijinta da gayu" gaba d'aya sukae dariya ta k'ara cewa "Yarinyar ta burge ni sosae wllh yanzu na fahimci dalilin da yasa Yalla6ai shima ta kwanta mashi a rai har yay sha'awar had'a auren na su gashi yace tana da kokari sosae" cigaba da yabon Fatun sukae daga baya Hajiya Safeena ta tafi, sai da akai la'asar sannan Driver ya sake d'aukar su ya tafi dasu shagon d'inkin bayan sun gama komae duk a tunanin Fatuu za'a wuce da ita gida ne amman sai suka koma gidansu Sadeeyar lokacin Magrib ta gabato, bayan sunyi salla gaba d'aya a Main Parlor suka zauna Sadeeya da Basma wadda itace auta sai Haidar wanda Basma ke bi mawa, Fatuu duk ta k'agara ta bar gidan suna zaune Momy ta fito da murmushi ta zauna tana facing Fatuu tace "Daughter kin k'i sakin jiki dae kuma nan d'in gidan ku ne so just feel at home" d'an murmushi kawae tay bata ce komae ba suna haka sai ga Khalid ya shigo da yar guntuwar sallama, damm kirjin Fatuu ya buga da suka had'a ido da sauri ta sunkuyar da kanta k'asa yana sanye da Jeans da T-shirt kujerar da Fatun ke zaune ya nufa ya zauna kan hannun kujerar yana bin ta da kallo a hankali ta d'ago ta kalle shi suka had'a ido ta gaida shi yana sakin murmushi ya amsa mata ta maida kan k'asa suma su Momyn duk murmushin suke sosae taji dad'in yadda Khalid d'in ya nuna ta yi mashi tun jiya da ya dawo shima Chairman yaji dad'in hakan don suna tare bayan ya dawon ya fad'a masu, kallon Momyn tashi yay yace "Mom how do you see My Wife?" Yar dariya tay tace "the Match was absolutely perfect" hannu ya kai ya shafi Beard d'insa yana cigaba da yin murmushi ya k'ara juyawa ya kalli Fatuu ganin kaman bata saki jiki ba ya kalli Mom d'in nashi yace sun ma yi fira kuwa tana murmushi tace "ai ta k'i sakin jiki tana ta bak'unta" d'an ta6e baki yay yace "kuma tana Magana Kaman parrot fa" da sauri Fatuu ta d'ago kai ta kalleshi ya d'age mata gira Momy tace "Ashe mu ne ba'a son yin firan da mu" Khalid yace "No nima bata saki jiki da ni ba jiyan ina Maganar can baya ne" da d'an alamun mamaki Momy tace "Kenan dama ka santa" yace "Yes we once met a rugan su" kallon shi kawae Fatuu ke yi tana zare ido gabanta na fad'uwa tsoron ta kar ya ce ta zage ta ya lura da yadda ta d'an razana hakan yasa Ya rink'a sakin wani shu'umin murmushi sai dae bai k'ara cewa komae ba can ya kalli Sady yace "Ya preparation na biki, ita tace bazata yi komae ba cos bata da Friends anan" da sauri Sady tace "dat's not a problem ai tunda akwae Family and Friends d'in mu" tambayarta yay mi zasu yi tace zasu yi Kamu da Bridal shower Momy ma zata yi Walima yace lafiya lou duk abunda ake buk'ata tay mashi Magana tana murmushi tace "Ok bro" kokarin tashi ya fara yi Momy ta tambayi inda zashi yace zai je sallar Isha ne tace to in ya gama yazo sai ya maida ta tana jira su gaisa da Daddyn su ne shiyasa bata sa an maidata ba yace ai yayi zaton zata kwana ne har saida Fatuu tay mashi wani kallo Momy na dariya tace so yake a biyo sawunta tunda ba'a ce zata kwana ba, Bayan gama sallar Isha d'in Chairman ya dawo Momy ta kai Fatun falon shi don su gaisa cike da farin ciki ya amsa gaisuwarta yay mata an zo lafiya, tana a falon Khalid ya dawo ya zauna nan Daddyn ya yi masu nasiha ya nuna yaji dad'in yadda suka kar6i juna had'i da yi masu Addu'oi ita dae Fatuu kanta na a k'asa ta rasa mi yake mata dad'i komai ganin shi take tamkar mafarki ba gaske ba, bayan ya gama Momy tace ma Khalid suje dare na k'ara yi yace Ok had'i da mik'ewa Dad d'in nace mashi ya kula sosae yana dariya ya d'aga mashi hannu alamar Ok, tare da Momy dasu Sadeeya aka rakota harda ledar turarurruka dasu Humra aka bata tay godiya, ji take kaman tace bata son ya kai ta saidae ba yadda ta iya haka ta bud'e front seat ta shiga Sady ta rufe mata kopar tana ce mata sai tazo kaita gyaran jiki suna daga mata hannu ya ja Motar suka tafi................... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2030* *💖A SANADIN MAKWABTAKA💖* _*(Love and Destiny)*_ _*BY ZAINAB LALUH📲*_ ~(Oumm Imam)~ Book 2 Bonus Page 30 _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ..........Tun da suka hau hanya ba wanda ya tanka ma wani Fatuu ta juyar da kanta tana kallon gefe yayin da Khalid ke driving sai dae a akai akai yake d'an juyowa ya kalli Fatun, hannu ya kai ya kunna music ya rage volume sosae kidan na tashi kad'an kad'an, har lokacin kuma bata kalleshi ba can ya juya ya kai hannu ya kamo hannunta da ta d'aura akan lap d'inta a firgice ta juyo ta kalleshi duk da dare ne tana d'an ganin fuskar shi sakamakon hasken fitilun wasu Motocin dake wucewa, ganin murmushin da yake saki yasa ta tamke fuska ta fizge hannun nata ta k'ara juyar da fuskarta, bai tanka mata ba ya kai hannu yana kokarin bud'e glove box jin k'arar bud'ewa yasa ta d'an juyo tana kallon abunda yake wani abu ya fiddo ya maida wurin ya rufe saidae bata gane mi ya d'aukko ba hakan yasa ta sake juyawa, wani d'an babban kwali ya fiddo sam nima na kasa gane na miye har saida ya bud'e yasa baki ya ciro cigarette guda, ashe kwalin sigari ne saidae ina tunanin ba irin tamu bace ta nan daga yanayin kwalin da kuma yanayin shi kan shi karan sigarin, amfani yay da lighter dake a cikin kwalin ya kunna kafin ya mayar da kwalin ya fara sha idon shi a kan hanya, a hankali warin ta ya fara kaima hancin Fatuu ziyara can ta juyo kaman an zabure ta lokacin da ta tabbatar daga cikin Motar warin yake, a razane take kallon Khalid dake smoking hankalin shi kwance idon shi akan hanya, wani irin bugu kirjin Fatuu ke yi gaba d'aya hankalin ta ya tashi nan take ta fara gasgata zancen su Zakiyya na yana shaye shaye, duk kallon da take mashi yana gani ta wutsiyar idon shi can ya d'an juya yana murmushi yace "kin k'i man hira as if am alone in d car dat's why na fiddo abunda zai taya ni hiran" sam ta kasa ce mashi komai bin shi da ido kawae take, cigaba da driving yay yana shan abun shi cike da k'warewa wasu kwalla masu zafi ne suka ciko a idanunta a rayuwarta ta tsani ta ga mutum na shan sigari ko warin ta ma bata so don ma wannan bata k'auri sosae amman duk da haka har zuciyarta ta fara tashi hakan yasa ta juya da sauri tasa gefen gyalenta ta toshe hancinta da bakinta lokacin kuma ta samu damar fara zubda kwallan da suka taran mata, Har suka k'araso bata sani ba jin ya tsaya yasa ta d'ago da sauri tana kallon wurin da k'yar ta gane inda ya parker wato a farkon gidan bai je kopar gidan ba daga inda suke tana hango inda teburin Kamalu na rake yake da sauran Mutane dake zaune a kofar gidan harda yara dake wasa, da sauri ta kai hannu zata bud'e ta fita hakanan taji bata yarda da inda yay parking d'in ba aikuwa kafin ta bud'en taji carabb ya kamo hannun ta a fusace ta juya ta kalleshi tace ya sakar mata hannu ta tafi, shiru kaman bazai tanka mata ba tana ta kiciniyar kwacewa ta kasa don ba k'aramin ruko yay ma hannun nata ba ganin bata iya fizge hannun yasa ta fara mashi magiya kan ya kyaleta cikin kararrar murya, d'an murmushi mai sauti yay kafin yace "Wife why ain't u romantic at all? ko ni driver d'in ki ne ya kamata ki fita kawae ba tare da kin man godiya ba..." Tun kafin ya k'arasa da sauri tace "To Nagode" yar dariya yay ganin duk ta rud'e yace "ni ai ba driver en bane I just give u an example ba wai godiyar nike so ba at least a single kiss da zai nuna u'r grateful" waro ido tay ya wani lumshe mata ido yana pointing lips d'in shi da sam basu yi kalan na masu shaye shaye ba da yake yana kula da hakan sosae, da sauri ta girgiza mashi kai alamar bazata yi ba sai kace ba yanzu a gabanta ya gama shan sigari ba ai koma bai sha ba bazata yi ba tunda tasan ba kyau, kokarin janyo ta ya fara yi ta toge hakan yasa ya d'an matso gab da ita kiciniyar kwace hannunta taci gaba da yi tana cikin hakan ba zato ba tsammani sai jin d'ayan hannunshi tay Saman boobs d'inta wata kalan gigicewa tay don abu ne da ba wanda ya ta6a mata hakan koda kuwa yar uwarta mace to mima zai kai hannun wata ko wani kan chest d'inta ita da ba yar iska ba, ganin gaba d'aya hankalin ta ya koma kan cire hannun na shi yasa ya shammace ta ya saki hannunta d'aya ruk'e ya kai hannun nashi ya tallabo kan ta ya had'e fuskokin su tana bud'e baki da niyyar yin Magana kuma ya had'e lips d'in su, iya k'ok'ari Fatuu tayi na ta janye bakinta abun ya gagara sai gunji take tana gurnani had'i da bugun shi saida yay sucking up duk wani saliva na bakinta sannan ya saki kan nata ya maida nashi jikin headrest breathing rapidly, a gigice ta bud'e Motar ta fice ta duk'e anan kan kace mi ta fara Kwara amai kaman yan cikinta zasu fito tana ji ya ja Motar ya tafi bayan ya tillo mata ledar turarurrukan ta, saida ta amayar da komae na cikinta a wurin kafin tasa wani irin kuka mai cin rai wannan wane irin bala'e ne a yanzu kam ta gasgata zancen su zakiyya gaba d'aya in ba d'an iska bane mi zai sa yayi mata hakan, da kanta ta rarrashi kanta ta mik'e kaman bazata d'auki ledan ba sai kuma ta d'auka kallabinta a kwance tana tafiya tana goge kwallan da suka k'i daina zubowa had'i da tofar da yawu sai sheshsheka take wani iri take jinta duk ba k'arfi a jikinta, har ta shige ba wanda ya lura da ita lokacin da ta shiga falo su Yadikko duk suna zaune dasu Mino da k'yar ta k'ak'alo d'an murmushin dole tayi masu sannu su Mino na mata sannu da zuwa cikin wasa Yadikko tace ai tayi zaton a can zata kwana bata ce komae ba ta wuce cikin d'akin tana shiga ta cire gyalen ta don duk kyankyamin shi take don sai take jin k'aurin sigarin da ya sha a jikin shi, aje ledar hannunta tay ta wuce band'aki don yin wanka, bayan ta fito ta shirya cikin doguwar rigar bacci da ta wuce gwuiwar ta ta haye gado zuciyarta nata tariyo mata abunda ya faru duk sai take ji ta tsangwami kanta ba kamar bakin ta ji take kaman ta cuzge shi duk kuwa da irin dirzar da ta yi mashi a bathroom, tana kwancen Yadikko ta shigo dama ta shigo d'azun ta taras tana wanka a bakin gadon ta zauna da d'an murmushi tace "an dawo lafiya?" a hankali tace mata lafiya lou, shiru ta d'an yi sai kuma ta k'ara cewa "Ya yan gidan nasu sun yi maraba da ke kuwa?" Kai ta d'aga mata kafin tace Momynsu na gaidata da fara'a tace tana amsawa Fatun ta lumshe idanunta jin kwalla na niyyar zubo mata yadikko ta bita da kallo can tace "Ya akai ne na gan ki duk wani iri ga idon ki kaman kin yi kuka ko dae kin 6oye man wani abu" bud'e idon tay ta d'an yamutsa fuska tace mata har ta fara bacci ne sannan aka maido ta cike da gamsuwa yadikkon ta jinjina kai tace to ta tashi ta ci Abinci kafin taci gaba da baccin, tana son ci don cikinta ba komae amman da ta tuna abunda Khalid yay mata sai taji bata iya ci tace mata a k'oshe take kawai, tana kwance bayan fitar Yadikko sai ga sak'o ya shigo wayarta ta d'auka tana dubawa bata gane wanda ya turo ba saida ta shiga ta fara karantawa ta gane Khalid ne Don bata yi saving number d'in tashi ba, sak'on ban hak'uri ne ya turo mata ya nuna son da yake mata ne yasa ya kasa resisting har hakan ta faru kuma kar ta damu hakan ba wani abu bane tunda ya biya sadakin ta ba yaudarar ta yake ba amman tun da bata so bazai k'ara mata ba har sai an d'aura masu aure yana fatan zata yafe mashi sosae yay mata kalaman da zasu kwantar mata da hankali, ta dad'e tana kallon sak'on kafin ta kife wayar, ba laifi ta d'an ji sanyi a ranta ba kamar da yace bazai sake mata hakan ba sai dae kuma abunda ya fi damunta da yace sai an d'aura masu aure don ita yanzu k'yamar shi ma take can sai gashi ya kira K'in picking tay sai bayan da ta yanke wani kiran ya sake shigowa sannan tay picking ta kara wayar a kunnanta ba tare da ta ce komae ba sanin tana sauraran shi yasa yaci gaba da bata hakuri yana kwantar mata da hankali har dae ta saukko ta fara tunanin k'ilan da gaske ne ya canza hali kamar yadda Mahaifin shi ya sanar da Baffanta dama kuma yadikko tace duk zargi ne abun da su zakiyya suka fad'a ba wanda ya tabbatar, da wannan tunanin ta d'an sake mashi suka d'an yi hira kafin daga baya yace ta kwanta saida Safe, Washe gari Juma'a sai gashi yazo da daddare bayan sallar Isha koda ta fita yana zaune a Mota yace ta shigo tace a'a ba sai ta shiga ba yana yar dariya yace to shi bai iya fitowa ya tsaya kaman wani d'an k'auyen su, k'arshe da yaga ta toge duk da yace ba abunda zai mata sai yace ta shigo sai tabar kopar bud'e sannan ta amince, Ranar Lahadi wurin sallar Azahar aka kawo lefen Fatuu dankara dankaran akwatuna guda takwas set biyu masu hud'u hudu shak'e da kaya na gani na fad'a masu kyau da tsada abun ka da aikin Naira gaba d'aya wad'anda za'a d'inka har an gama, a d'akin Yaya aka kai su nan kowa ke zuwa gani sai yabawa ake ana zuba k'auyanci, sam Fatuu bata yi farin cikin kayan ba da su Mino suka zo suna fad'a mata bin su da ido kawae take yanzu dae ta idasa tabbatarwa da gaske Aure za'ayi mata, wurin k'arfe ukku na rana Khalid ya kirata bayan ta d'aga ya sanar da ita zai zo bayan sallar la'asar zasu d'an je wani wuri, shiru ta d'an yi mashi a ranta ta shiga tunanin ina kuma zasu har saida yace bata ji bane sannan tana tura baki tace ina zasu yace bata ji yace wani wuri zasu bane, sam ran ta bai kwanta da fitar ba don ita yanzu tsoron shi take hakan yasa tace mashi ita bazata je ko ina ba, shu'umin murmushin shi yay yace Ok tunda shi bai isa da ita ba bari ya kira wanda ya isa dashi ya sata ta bi shi nan take ta gane Ard'o zai fad'a mawa k'arshen ta kuma ya sanar da Baffanta ta san kuma bazai ji dad'in hakan ba, ba yadda ta iya tace mashi zata shirya tamkar ta fasa ihu, bayan la'asar ta gama shiryawa tasa jallabiya bak'a tay rolling veil d'in tana gamawa bada dad'ewa ba sai gashi ya kirata ya sanar da ita yana a kopar gida, a Falo ta samu yadikko tace mata sai ta dawo da yake ta sanar da ita game da fitar tace a dawo lpy, Yana zaune a Mota ta fito ya k'ura mata ido har ta k'arasa ta bud'e gaban ta shiga fuskarta a d'aure ta gaishe dashi yana murmushi ya amsa yace ta rufe su tafi bin shi da kallo tay tace "Wai ina zamu ne?" d'age gira yay yace "zan saido ki ne" tura baki tay ba tare da ta ce komae ba ganin bata da niyyar rufe kopar yace mata zai kai ta ta gaisa da wasu ne sannan ta rufe yaja suka tafi, Yar tafiya sukae suka k'araso bakin garin daidai k'aton gidan Gonar su ya karya kan Motar ya shige gate d'in farko dake a bud'e mai gadi na d'aga mashi hannu yay mashi horn ba tare da ya tsaya ba, wata tafiyar suka k'ara yi kafin suka sake isowa wani gate d'in na fence ya tsaida Motar ya fita ya bud'e Fatuu nata bin wurin da ido bayan ya dawo yaja suka kutsa ciki, wurin parking ya nufa ya parker Motar ya kalleta da Murmushi yace ta fito, a hankali ta kai hannu ta bud'e Motar bayan ta fita tay tsaye tana k'are ma wurin kallo shi kuma ya koma yaje ya rufe gate d'in tana cikin kallon wurin zuciyarta ta ayyana mata nan ai kaman gidan Gonar su ne dammm kirjinta ya buga sam ita da farko bata gane ba sai yanzu bayan ya dawo in da take tsaye yace mata su shiga yay Maganar yana nuna mata k'aton Flat d'in dake gaban su togewa tay tana bin shi da ido yace "Let go in wife" tana tura baki tace "Amman ai gidan kaman ba kowa" yana murmushi yace waya gaya mata ba kowa bata ga gida bane lafiya lou, shiru tay tana nazari lokacin Maganar yadikko da ta ce har Chairman d'in da Matan shi suna zuwa Hutu nan ta fad'o mata hakan yasa tay tunanin k'ilan da gasken akwae Mutane ganin ta d'aga k'afa yasa yay gaba yace su je tabi bayan shi suka nufi entry d'in, Babban falo ne mai d'auke da duk wani abu da zaka samu a falon yan gayu akwae corridors a 6angaren dama da hagu bin falon da kallo Fatuu tay Khalid d'in ya nuna mata ciki wajen da Sofas suke yace suje, zaunawa yay kan 3 seater ya nuna mata gefen shi yace ta zauna tay tsaye tana kallon shi kafin tace mashi ina wad'anda zasu gaisa d'in yace ta zauna mana ko zai cinye ta ne kaman bazata zaunan ba sai kuma ta d'an d'osana ta zauna a d'arare tana ta kallon shi, yana ganin ta zauna ya fad'ad'a murmushin shi had'i da d'an kwantar da kan shi yace ko ita fa, shiru tay ganin kallon da yake mata yasa fuska a d'aure tace "Wai ina Mutanen?" Hannu ya kai ya shafi sumar shi still da murmushi akan fuskar shi ya fara Magana "Wife ba fa wasu da zaku gaisa I just want us to spend time together yadda zamu k'ara fahimtar juna don naga kin k'i sakin jiki da ni gashi nan da few days zamu zama Couples" wani kallo ta bi shi da shi baki bud'e shi kuma sai faman lumshe mata ido yake can ya fara matsawa wurinta tay zumbur ta mik'e ta kumbura baki a fad'ace tace "shine duk gidan mu bai isa ba sai ka kawo ni nan harda yi man k'arya to ni dae ka tashi ka maida ni ko in tafiya ta tunda nasan hanya!" d'an ta6e baki yay kawae bai ce mata komae ba aikuwa a fusace ta juya ta nufi hanyar fita daga falon saidae tana kaiwa kopar taji ta a rufe gam wani bugu kirjinta yay kenan kulle kopar yay bayan sun shigo, juyawa tay ta kalle shi ko kallon ta bai yi ba hakan yasa jikinta mutuwa ta nufi cikin Falon gefen kujerar da yake ta tsaya idon ta a kan shi kamar zatayi kuka tace "Don girman Allah kai hak'uri ka maida ni gida" bai kalleta ba sai ma cigaba da latsa wayar shi da yake yay kwalla ne suka fara zubo mata taci gaba da yi mashi magiya saida ya mula yasha iska sannan ya d'aga ido ya kalleta cikin kashe murya yace "Don kin ga na damu da ke shiyasa kike taking advantage d'in hakan kina neman wahalar dani ko? Kuma ni kike ce ma makaryaci don kawae na buk'aci mu kasance tare dama ashe har yanzu baki daina rashin kunya ba?" d'an girgiza kai tay tace "a'a kai kace zamu gaisa da wasu ne ai da ka fad'i man gaskiya" kya6e baki yay ya d'age gira yace "in na fad'i maki gaskiya zaki zo ne?" shiru tay tana ci gaba da yamutsa fuska yaci gaba da cewa "Zuwa yanzu yakamata ki d'auke ni kaman yadda na d'auke ki just 6 days ya rage a d'aura mana aure what's there don na bukaci mu kasance tare, da wasu ne ma yanzu tuni sun d'auki kan su matsayin ma'aurata, kodae ban yi maki bane?" Wani wahalallan yawu ta had'iya a halin yanzu dole ta bi shi gudun kada yay mata wani abun ganin daga ita sai shi gashi ya kulle kopa, sake tambayarta yay bai yi mata bane a dabarbarce tace a'a yayi mata yace to ta kwantar da hankalin ta ba wani abu zai mata ba kuma nan gidan da take gani nan za'a kawo ta don haka gidan tane ya nuna mata gefe inda ta tashi yace ta zauna suyi hira tace to sai yaushe zasu tafi yace bada jimawa ba, bata da yadda zatayi dole ta koma ta zauna ya kai hannu kan c-table ya d'auki remote ya kunna masu kallo, bayan ya koma ya zauna yana murmushi yace mata miye labari a hankali tace mashi babu ya tambayi taga kaya akwae abunda babu tace mashi kawae akwae komae duk kuwa da bata ma ga kayan ba, tambayarta yay abubuwan da take so da wanda bata so ta kasa bashi amsa yace shi bari ya fad'i mata ya shiga lissafo mata tana dae ta kallon shi can ya tambayeta wai tana da saurayi farko shiru tay mashi don tsoron bashi amsa take ganin hakan yasa shi cewa in fa tana son ya maida ta gida ta bud'e baki ta rink'a mashi Magana ta girgiza mashi kai a hankali tace bata da shi yana dariya yace ta dai fad'a ne ya za'ai mace kaman ta ace bata da saurayi yace "Ni kin ga inada yan mata saidae ba wadda ta yi man matsayin Matar aure na don duk basu da qualities irin naki" sototo tay tana kallon shi haka ya ci gaba da bata mamaki ta hanyar yi mata kalamai masu d'aure kai har dae ta d'an fara sakewa sai gashi har tana yin d'an murmushi in ya kama can ya mik'e yace bari ya d'aukko masu lemu kishi yake ji itama tana bak'uwa ya barta ba ko ruwa duk da nan d'in gidanta ne, bada jimawa ba ya dawo ruk'e da babbar robar Fanta da glass cups guda biyu ya d'aura su akan c-table ya bud'e ya fara tsiyayawa cike da tsokana yake fad'in "nasan Fulani da son jan lemu" kallon shi kawae take sai kace shi ba bafullatanin bane, bayan ya zuba ko ina ya mik'a mata cup d'aya ta amsa ta ruk'e shima ya d'auki d'ayan ya koma ya zauna ya kai baki ya fara sha, ganin ta ruk'e wanda ya batan yasa shi ce mata ta sha mana ko tsoron sha take bata ga shima ya sha ba jin hakan yasa ta kai cup d'in ta fara sha...... ***** ***** Bayan Wani Lokaci, A hankali ta fara motsa idanunta da sukae mata nauyi kafin da k'yar ta idasa waresu kan Pop ceiling d'in da take facing, k'ura ido tay tana kallo kaman mai nazarin wani abu can ta mik'e zaune zumbur da mamaki ta kai idonta saman gadon da take zaune kafin ta bi cikin d'akin da kallo with extreme surprise tunanin abunda ya kawo ta d'akin ta shiga yi da yadda akai har ta kwanta kan gadon, lokaci guda kwakwalwarta ta fara tariyo mata abubuwan da suka faru kafin yanzu, to miya faru da ita ne bayan ta sha lemun da ya bata? ta jefa ma kanta tambaya, wani irin bugu k'irjinta yay da sauri ta kai idonta jikinta ta fara bin kanta da kallo abun mamakin lafiya lou rigarta na a jikinta haka dogon skin tight d'in da ta sa a ciki shima yana nan hannu ta kai ta shafi kanta dake bud'e amman gashinta na a fake shima, kan ta ya gama d'aurewa tana cikin hakan taji an turo kopar da sauri ta kai idonta wurin Khalid ne ya shigo jikinshi sanye da singlet sai wandon jeans d'in da yazo da shi suna had'a ido ya sakar mata k'ayataccen murmushi ya tsaya a jikin kopar ya goya hannuwan shi a kirji yace mata ta tashi kenan, tabdijancan! ido waje take kallon shi murya na rawa tace "Ya akai nazo nan waya kawo ni??" d'an yamutsa baki yay yana lumshe ido yace "kin yi bacci ne and u'w not comfortable there har kina niyyar fad'owa shine na maido ki nan" k'ara zaro ido tay ta furta Kalmar ya maido tan nan da ya fad'i, a kidi'me tace "to ya akai nayi baccin ni bansani ba?" d'an watsa hannuwa yay alamar bai sani ba ta k'ura mashi ido alamar bata yadda ba can murya kaman zata yi kuka tace "Daga shan lemu sai bacci..." dakatawa tay tana tunani can ta tuno da maganin bacci da Kawu Amadu ya ta6a amso mata a rud'e tace "k...ko dae maganin bacci kasa man kai man wani abun???" d'an ta6e baki yay yace "u can check ur body" daga haka ya juya ya fita, da sauri ta saukko daga kan gadon ta nufi gaban dressing mirror tana kallon kanta ko zata ga wani canji amman bata ga komae ba da sauri ta d'aga rigarta sama ta k'ura ma k'irjinta ido boobs d'inta na acikin bra lafiya lau sakin rigar tay ta gwada yin tafiya don tasan in dae yayi mata wani abun a gurin zata gane amman bata ji komae ba lafiya lou take tafiya kasa yadda tay ta nufi wata k'opa da take tunanin toilet ne ta tura sai gashi toilet d'in ne ta shige, sosae ta duba under d'inta lafiya lau bata ga wani canji ba tsaye tay sam ta kasa yarda da bai mata wani abu ba don zuciyarta na raya mata wani abu yasa a cikin lemun nan, hakanan bazata yi nauyin baccin da har zai maido ta d'aki ba ba tare da ta farka ba tana haka taji wani abu na yawo cikin rigarta da sauri ta zura hannu ta jawo sai ganin hannun bra d'inta tay wani irin bugu kirjin ta ya fara yi ta zazzaro ido waje da sauri ta k'arasa gaban mirror d'in dake cikin wurin ta k'ara d'age rigar sama sai lokacin ta lura da bra d'in bata kamata sosae ba kamar yadda ta sata, hannu na rawa ta fiddo breast d'inta guda tana dubawa koda ta kalli nipple d'in da sauri tasa hannu ta rufe bakinta ganin yadda yay jajir da shi gashi ya fito sosae, wani irin kuka Fatuu ta saka tana fad'in ta shiga ukku ta bani ta lalace sakin rigar tay a fusace ta juya ta fita ta nufi falo, lokacin da ta shiga yana zaune ya kishingid'a jikin kujera ta tsaya gaban shi kaman an jefota cike da Masifa tace "Ashe abunda zaka aikata man kenan yasa ka kawo ni nan, dama an ce kai d'in manemin mata ne d'an shaye shaye kuma dama ban yarda da duk abubuwan da kake fad'a man ba, ba wani so na da kake yaudarata kawae kake kana son ka cutar dani don in kana sona da gaske bazaka man haka ba nima kuma ban son ka ban kaunar ka na tsaneka kuma bazan Aure ka ba wllh!!!" d'age gira yay yana kallonta da d'an murmushi hakan yasa ta k'ara k'ulewa taci gaba da zazzaga mashi Masifa har tana kiran shi da Mazinaci aikuwa tana fad'in hakan ya daka mata tsawa ya mik'e har saida ta d'an ja baya fuska tamke ya fara Magana "Kar ki k'ara kirana da wannan sunan! Ke in ni Mazinaci ne kina tunanin yadda na samu dama akan ki zan kyaleki ne iya hakan??" Duk da ta tsorata tay k'arfin halin cewa "ai duk d'aya ne miyasa zaka bud'e man jiki har ka ta6a man jikina!" tay Maganar kwalla na zubo mata, sassauta murya yay cikin sigar rarrashi yace "it's just a romance wife and ba don na biya sadaki ba ba abunda zai sa in ta6a ki kuma duk laifin ki ne kin k'i ki saki jiki da ni, I truly love u shiyasa nike maki hakan kuma bai kamata ki tada hankalin ki ba komi nai maki ai ni zaki aura ko......." A fusace tace "Allah ya kyauta! wllh bazan Aure ka ba na tsane ka kuma sai Allah ya saka man abunda kai man tunda dai ba d'aura mana aure akai ba" yar dariya yay ya girgiza kai yace "Do u think is as simple as u said?" banza tay mashi tana huci kwalla naci gaba da zubo mata yace "Look Wife ki bar wannan a tsakanin mu ba wani abu bane muje in maida ki" wani kallo take bin shi da shi cike da takaici ranta na mata wani irin suya ya wuce Bedroom d'in bada jimawa ba ya dawo ya maida rigar shi ya mik'a mata veil d'inta kaman bazata amsa ba yace ta amsa su tafi Magrib ta kusa in kuma zata kwana ne anan to, amsa tay ta yafa yay mata alamar suje tayi gaba yana bin ta a baya suka fita ba yadda ta iya ba don ta so ba ta shiga Motar don kuwa akwae tafiya ga Magrib tayi, tunda suka hau hanya take sheshsheka yana bata hak'uri had'i da nuna mata ba fa wani abu bane shi yanzu ma ji yay ya k'ara sonta don gaba d'aya yadda yake son Matar shi ta kasance haka take, suna isowa ta bud'e Motar ko rufewa ba tayi ba tay gaba, Lokacin da ta shiga falon iske Yadikko tay tana salla ta wuce uwar d'akan ta fad'a kan gado tasa kuka mai cin rae yadikko na sallame sallar ta shigo d'akin da sauri don tun tana sallar take jiyo sauti kukanta, hayewa tay Saman gadon ta d'ago Fatun tana tambayarta abunda ya faru cikin kuka ta kwashe komae ta fad'a mata tace "ban son shi yadikko don Allah ki fad'a ma Baffana kada a Aura man shi mutuwa zanyi in na aure shi, wllh da gaske d'an iska ne kuma yana shaye shaye" Ajiyar zuciya kawae yadikko ke saukewa tasan hakan ba mai yuwuwa bane ba kamar yanzu da ya rage saura yan kwanaki bikin, sosae ta shiga rarrashinta tana nuna mata lokaci ya k'ure kuma ita a tunaninta da gaske don ya biya sadakin yasa yay mata hakan tunda yana ganin saura yan kwanaki ta zama Matar shi ta daina damuwa tunda ma shi d'in da yay mata hakan zata Aura kuma da bai son ta abunda yafi hakan zai aikata mata ya dawo yace kuma bazai Aure ta ba, ita kanta yadikkon hankalinta ya tashi sosae da jin abunda ya faru hakanan ta danne don kar ta k'ara tada ma Fatun hankali da k'yar ta shawo kanta ta d'an saukko har taje tayo wanka ta dauro Alwala bayan ta gama sallar ta d'aga hannu tana kuka tana rokon Allah kan ya kawo mata Mafita, kasa cin Abinci tay duk da tana jin yunwa ta sha yar fura kawae, koda ta kwanta sak'e sak'e taci gaba da yi a ranta da ta tuna wani ya gane mata jiki har ya ta6ata sai wani kunci ya k'ara lullu6e ranta lokaci guda ta fara tunanin yadda zata guje ma Auran Khalid abunda bata ta6a tunanin yi ba tunda aka fara Maganar Auran sai yanzu........... _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 *ASM Bk2031* _Destiny may be delayed but cannot be changed...._ *DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI* ..........Tana cikin tunanin neman mafita wayarta ta fara ringing da k'yar ta kai hannu ta d'aukko ta duba screen d'in ganin Number yasa ta gane Khalid ne ta kife wayar kawai ba tare da tayi picking ba, sake kira yay sai kawae ta kashe wayar ma gaba d'aya ta cillar da ita taci gaba da tunaninta da k'yar bacci ya dauketa, Washe gari da zazza6i ta tashi da k'yar tayi sallar Asuba ta koma ta kwanta sai da yadikko ta zo tashin ta don tayi karin kumallo tasan bata lafiya da k'yar ta lalla6ata ta tashi ta yi breakfast d'in ta bata Magani ta sha kafin ta koma gado, sai wurin sallar Azahar ta farka ba laifi ta samu sauki sosae hakan yasa ta wuce bathroom tayo wanka ta d'auro alwala, bayan ta gama sallar ta zura doguwar riga ta fita falo anan ta iske Yadikko itama ta gama salla da murmushi tay mata ya jikin tace ta samu sauki ta samu wuri kan kujera ta zauna, ganin yanayin damuwa tattare da ita yasa yadikko ta shiga rarrashin ta kan ta kwantar da hankalin ta da k'yar ta lalla6a ta ta zubo mata Abinci tana cikin ci sai ga Sadeeya tazo tana sanye da jallabiya tay rolling veil da fara'a yadikko ta tarbeta ta nuna mata wurin zama kafin suka shiga gaisawa daga baya ta kalli Fatuu da fara'a ta gaishe da ita anan take sanar ma yadikko tazo ne zasu je wurin gyaran jiki lokaci guda yanayin fuskar Fatun ya canza yadikko ta lura da hakan ita kanta Sadeeyar ta ga canji a Fuskar ta nan yadikko ke sanar mata yau ta tashi bata jin dad'in jikinta ne amman ta samu sauki da ta sha Magani cike da nuna damuwa Sadeeya ta shiga yi mata sannu har tana cewa amman dae Ya Khalid bai sani ba ko tunda bai fad'a masu ba yadikko tace eh ai yau ne ta tashi da ciwon, kallon Fatuu tay da bata da niyyar tashi tace taje ta shirya su je tunda da sauk'i sosae kaman ta saka ihu haka taji ba yadda zatai dole ta mik'e ta wuce ciki, gyale kawae ta yafa akan doguwar rigar material din jikinta tasa takalma ta fito, lokacin da suka fita kopar gidan ja tay ta tsaya ganin Motar Khalid sam bata yi tunanin shi ya kawo Sadeeyar ba daba abunda zai sa ta fito tay zaton driver ne kaman rannan ganin ta toge yasa Sadeeya ce mata suje mana da K'yar ta ja k'afa suka nufi Motar don bata son ta gane da wani abu duk Khalid d'in na kallon ta duk da Motar a rufe take ruff kuma glass d'in black tinted ne, Front seat Sadeeya ta bud'e mata ta shiga bayan ta rufe itama ta bud'e baya ta shiga, wani kalan d'aure fuska tay ba tare data kalle shi ba shi kam sai kallonta yake with smile on his face yace tana lafiya kafin ta bashi amsa Sadeeya tace "Big bro Bride en ka fa bata lafiya" d'an bud'e ido yay idon shi akan Fatuu ya tambayi Mike damunta da kyar ciki ciki tace mashi zazza6i, shiru ya d'an yi still idon shi na akanta ita kuma ta juyar da fuskarta can taji yace ko su wuce Asibiti ya duba ta ne, ba shiri tay mashi wani kallo ya d'age mata gira baki kumbure tace ta samu sauk'i yace Ok daga haka yaja Motar suka tafi, sai firar bikin suke shida Sadeeya tay masu banza tamkar ma bata acikin Motar sam Sadeeya bata kawo komae ba ta d'auka don bata jin dad'in jikinta yasa tay shiru kuma dama ta san bata Magana sai ta kama, lokacin da suka isa shagon Fatuu na niyyar fita taji ya kamo hannunta akan idon Sadeeya tay d'an murmushi kawae ta fita Fatuu na jin ta rufe kopar ta fara k'ok'arin fuzge hannunta amman ta kasa a fad'ace tace "Ka sakar man hannu!" d'an lumshe ido yay yana mata wani irin kallo ganin bai da niyyar sakin yasa idanunta suka cicciko da kwalla murya kaman zata yi kuka ta k'ara cewa ya sakar mata hannu ita ba yar iska bace da zai rink'a ta6a ta sai lokacin yay d'an murmushi cikin kashe murya yace "nima ba d'an iska bane wife......" A fusace ta katse shi da fad'in "wllh kai d'an iska ne in ba haka ba mi yasa zaka bud'e man jikina ka ta6a ni!" Daga yadda tay Maganar zaka fahimci ba k'aramin ciwo abun yay mata ba, d'an ta6e baki yay still da murmushi akan fuskar shi yace "Ok mu barshi a hakan na yadda ni d'an iska ne but nan da next 5 days zan assuring naki hakan" damm k'irjin ta ya buga ta bi shi da ido ya wani d'age mata gira, d'ayan hannunta ta sa tana goge kwallan dake zubo mata ya kai hannu ya bud'e glove box ya fiddo hanky ya mik'a mata don ta goge kwallan k'in amsa tay tabi hanky d'in da kallo ba komae ya tuna mata ba sai ranar da Ya Haisam zai tafi, ganin ta k'i amsa ne yasa shi ce mata in fa bata amsa ta goge su ba bazai bari ta fita ba sai dae suyi ta zama har sai sanda ta gogen, ba yadda ta iya cike da takaici don ita k'yamar hanky d'in take Saboda rannan a cikin wurin ya fiddo kwalin cigarettes, saida ya ga ta goge su tass sannan ya kyaleta ta fita lokacin Sadeeya tuni ta shige cikin wurin gyaran jikin. Da yamma wurin k'arfe biyar ya dawo d'aukar su bayan da Sadeeya tay mashi waya ta sanar mashi sun gama, a gida ya fara sauke Sadeeya tana cewa Amarya bazata shiga su gaisa da Momy ba yace yamma yayi yana so yay dropping nata before Magrib tay ma Fatun sallama, tun da suka hau hanya jininta akan a kaifa yake har sukae nisa bai tanka mata ba yana ta sauraren music d'in da ya kunna yana bi a hankali, saida suka iso bakin gari wurin gidan Gonar su sannan ya kalleta ta juyar da fuskarta tana kallon gefe yace "Wife ko muje ki huta anjima sai in maida ki" tun kafin ya rufe baki ta juyo a harzuk'e tay mashi wani kallo, k'ok'arin juya kan Motar ya fara yi aikuwa a firgice har bata san ta kai hannu kan hannunshi dake ruk'e da steering murya na rawa ta fara mashi magiya ya kaita gida wani irin lumshe ido yay sakamakon shak'ar daddad'an k'amshin da jikinta ke fitarwa dama tunda ta shigo Motar yake d'an bugun hancinshi ba shiri ya taka burki, jin ya tsaida Motar yasa ta juya ta kalleshi tana ganin yadda idanuwan shi suka koma da sauri ta cire hannunta ta juya zata bud'e Motar da sauri ya kai hannu yay locking Kopar ido waje ta juya ta kalle shi yana ta bin ta da wani irin mayen kallo tana ganin haka ta fara yamutsa fuska nan da nan ta fara kuka tana had'a shi da Allah kan kada yay mata wani abu hakan bai da kyau ya bud'e mata ita zata tafi a k'asa ma, Still kallonta yake bai san miya sa ba komae yarinyar tay sha'awa yake bashi shi kad'ai yasan yadda yake ji ko jiya a gidan gona ba k'aramin yak'i yay da zuciyar shi ba har ya iya k'yaleta don ya fahimci bata san namiji ba daga yadda take tsoron ya ta6a ta shiyasa ma ko tunanin kaiwa can ma bai yi ba ko ba haka ba bai iya yin hakan tana a yanayin bacci don zai zama kaman yay raping nata ne shi kuma abunda ya tsana kenan shi yasa ko ada da yake kula mata wani abu bai shiga tsakanin shi da mace face da amincewar ta, Kuka sosae take mashi duk ta rud'e can ya sauke ajiyar zuciya cikin kasalalliyar murya yace mata tay shiru ba abunda zai mata in kuma bata yi shirun ba to zai wuce da ita gidan gonar ne ba Arziki tay tsit sai motsa baki take tana zare ido, idanu a lumshe yake kallonta sai kikkafta ido take taji yace tana so su tafi, da sauri ta d'aga mashi kai alamar eh jinjina kai yay yace "I want a single kiss pls" k'ara zaro ido tay baki bud'e take kallon shi ta kasa cewa komae yaci gaba "in kikai man hakan zamu tafi in kuma kika k'i saidae muyi ta zama anan har dare yayi sai mu wuce gidan gona mu kwana can" k'ara rud'ewa tay ganin on a serious note yay Maganar murya na rawa tace "amman fa kasan babu kyau tunda ba'a d'aura mana Auren ba" still bin ta yake da kallo yay d'an guntun murmushi yace "But ai zamu yi auren ne ko, kuma miya rage abunda yake dole saida shi ake d'aura auren already an bada so ba wani abu bane" kuka ta fara k'ok'arin ci gaba da yi yace ko na jini zatai in dae bata yi mashi ba ba tafiya zasu yi ba kuma da gaske gidan gona zasu wuce, wani irin bak'in ciki ne ya turnuk'eta taji ta k'ara tsanar Auren shi ganin da gaske bazasu tafin ba don yama jingina da seat ya d'age kan shi yasa tace zata yi mashi jin hakan yasa ya d'ago yana murmushi ita kuma ta d'aure fuska tamkar bata ta6a yin dariya ba nuna mata lips d'in shi yay alamar anan zata yi mashi ta ce ita bazata yi mashi anan ba yace Ok bata shirya su tafi ba kenan ganin yana niyyar maida kan yasa tace to zata yi mashi amman kar ya ta6a ta yace ya yarda tana kukan zuci da har ya bayyana kan fuskarta ta fara matsawa shi kuma sai sakar mata murmushi yake, kasa yi mashi tay tana ta yamutsa fuska can dae ta daure ta cije ta rufe ido ta kai bakin ta saitin fuskar shi amfani yay damar daya samu ta rufe idon da tay ya kai hannu ya kamo kan nata ya had'e bakin su, irin yadda yay mata ranar da ya maido ta daga gidan su yau ma yay mata, lokacin da ya saketa wani irin kukan bak'in ciki Fatuu ta saki tana yi mashi Allah ya isa kuma Allah sai ya saka mata in sha Allahu bazata Aure shi ba, bai ce mata uffan ba don shi kadae yasan abun da yake ji da k'yar ya tashi Motar suka tafi, suna isowa tun kafin ya idasa tsayawa ta kai hannu zata bud'e kopar Allah yasa a rufe take har saida ya tsaya sannan ya bud'e kopar a fusace ta fice ya bita da ido ta cikin glass har ta shige cikin gida, sai da ya d'au d'an lokaci kafin da k'yar ya ja Motar ya tafi, Tana shiga saida ta tsaya a soro ta goge fuskar ta sosae sannan ta shiga ciki lokacin da ta shiga falon su da yar sallama cak ta tsaya ta kasa k'arasa sallamar sakamakon wadda ta gani a zaune ta d'an kishingid'a kan kujera suna had'a ido ta fara sakar mata murmushi da tsananin mamaki Fatuu ta furta "HAULAT.....!" tashi zaune sosae Haulat tay tana dariya tace "Na'am k'awata Amarya" aikuwa da gudu Fatuu ta nufeta ta fad'a jikinta cike da farinciki haulat sai dariya take yi, d'agowa Fatuu tay fuskarta d'auke da tsantsar farin ciki tace "yaushe kuka zo ne?" Haulat tace "bamu dad'e ba salla kawae nayi ko Abinci kin ganshi ban ci ba nace sai na gan ki tukunna na dae sha fura, ance gyaran jiki kika je gaki nan ai sai annuri kike kin fito sak Amarya" ta k'arasa tana murmushi Fatuu ta tura mata baki kafin tace "keda wa kuka zo" tace "da kawu Amadu ne" da d'an mamaki tace "shine bai sanar da ni ba,to Gwaggo fa?" Haulat tace "gaskiya mu biyu muka zo sai kaya k'ilan ko ita sai daga baya ina jin" shiru Fatuu tay sai kuma ta mik'e da sauri tace mata tana zuwa tay hanyar fita Haulat ta bita da kallo tana ta murmushi, d'akin su Kamalu dake a soro ta nufa tana zuwa ko sallama bata yi ba ta kutsa kai tana shiga ta iske Kawu Amadu kwance yana latsa waya ta nufe shi tana kiran sunan shi ya d'ago ido yana ganinta ya saki murmushi yana kokarin tashi zaune, a gefen shi ta zauna tana kallon shi tace "Kawu Amadu ashe kun zo" yana murmushi yace "Eh Amaryarmu bamu dad'e da zuwa ba na tambaye ki aka ce kun fita" a sanyaye tace "Gwaggo fa, haulat tace ku biyu kuka zo" shiru ya d'an yi sai kuma yace "Eh amman tace zata zo ta bada kaya ma akawo" kafe shi da ido Fatuu tay kaman bata yarda ba tace "to yaushe zata zo?" Shiru yay baisan ranar da zai ce mata ba don in ma yayi mata k'arya yasan ranar zata zo kuma ba zuwa gwaggon zatai ba, ganin haka yasa fuskarta canzawa tamkar zata sa kuka tace mashi bazata zo ba ko, farko shiru yay ganin ta kafe shi da ido yasa ya d'aga mata kai alamar eh, kuka ta fashe mashi da shi tana fad'in ashe bata hak'ura ba har yanzu fushi take da ita, side hug Amadu yay mata ya shiga rarrashin ta yana tayi hakuri a hankali komae zai wuce yasan dole zata zo ne koda bayan anyi auren ne can ta d'ago tace mashi Hajiyar Sanata fa itama bazata zo ba, da yar damuwa yace mata Hajiya bata lafiya ciwon kafafu take yanzu ko wurin aiki ma ba zuwa take ba amman taso ta zo koda taji gwaggo bazata zo ba har fushi tay da ita, sosae ya rarrasheta ya nuna mata tayi hak'uri wannan jarabawa ce daga Allah, kiran sallar Magrib yasa shi tashi yace mata ta koma ciki zai je yay salla ya dawo, zaune tay a cikin d'akin tana cigaba da matsar k'walla sai daga baya ta tashi ta nufi cikin gidan lokacin da taje d'akin su a k'urya ta iske Haulat na yin salla itama taje tayo Alwala tazo gefenta ta kabbara salla, bayan sun gama Haulat ta kalleta da Murmushi tana ganin yanayin fuskar Fatun tace "K'awata lafiya dai ko, idanun ki naga sun canja kuma dama naga har rama kin yi" kaman zata sa kuka tace "Haulat baki ji Auren dole za'a man bane?" da yar damuwa Haulat tace "naji Fatuu lokacin da innata ta kira waya can Nijar ta sanar da ni na matuk'ar girgiza da jin zancen tun lokacin nike kokarin kiran ki amman bata shiga daga baya ne na kira kawu Amadu ya fad'i man komae, na matuk'ar tausaya maki Fatuu wllh Allah ne shaida har kuka nayi sosae nace Ashe ba rabon dae kiyi karatu kuma ki auri wanda kike so" kuka sosae Fatuu ta fashe dashi tasa hijab d'in jikinta ta rufe bakinta don kar sautin ya fita itama Haulat kwallan ta fara yi ta shiga rarrashinta tana cewa tayi hakuri kowa a rayuwa da kalar kaddarar shi ita kuma wannan ce tata, cikin kuka tace "Haulat za'a man Aure ba tare da gwaggo ta zo ba Saboda tana fushi dani don na amince aman auren, nima don banda yadda zan yi ne amman wllh ban son Auren nan....." sosae taci gaba da yin kuka suna haka yadikko ta shigo a rud'e ta shiga tambayar ko lafiya Haulat tace ba komae Saboda gwaggo bata zo bane nan itama tasa baki suka cigaba da rarrashin ta tare suna ce mata dole gwaggo zatai fushi yanzu amman zata saukko ko ba yanzu ba, sai da aka kira sallar isha suka tashi suka yi Bayan sun gama ne Yadikko ta nuna mata kayan da su Haulat suka zo dasu Manyan bokitan su cin cin da dublan ne dasu zannuwan gado da labulaye harda kayan gara su buhun shinkafa biyu katan d'in Taliya da Macaroni suma bibbiyu jarkar Mai su gishiri Man shanu da sauran su dae bin kayan da ido kawae tay ba tare da ta ce komae ba, tana gama nuna mata tace bari taje wurin Yaya ta d'aukko kayan lefenta da shiru har yanzu ba'a maido su nan ba, lokacin da Yadikkon taje bayan sun gaisa da wad'anda suke d'akin ta sanar ma Yaya ta zo d'aukar kaya ne, wani kallo ta jefa mata cikin harshen fulatanci tace to cinye kayan zasu yi da har sai an biyo sahu d'an murmushi had'i da d'an ta6e baki Yadikko tay tace dama daga gidan su Angon ne ake ta kira ana son aji ko akwae abunda baiyi ba kaman takalma da kuma d'inkakkun kaya anata ce masu bata gwada ba shiyasa tazo ta tafi dasu ta gwada amman bari taje sai a sanar masu har yanzu Amaryar bata ma ga kayan ba, tana fad'in hakan ta fara kokarin juyawa ta tafi Yayar ta tsaidata Fuska a murtuke tace ai sai su yi ta d'auka kuma dole za'a fitar ma da Mutanen gida nasu, ita dae Yadikko bata ce komae ba don tasan yanzu ace tayi rashin kunya kaman yadda aka saba cewa, guda biyu ta fara d'auka duk suna kallonta ba wanda yay yunkurin taimaka mata sai bayan da ta kai su daki ne ta dawo tare da Haulat da Mino suka kwashe sauran, bayan sun maida su can suka zauna don sake kallon kayan dama basu samu sun duba ba sosae da suna can, sosae Haulat ta shiga yaba kayan duk yadda akai da Fatuu tazo taga kayan ta gwada k'iyawa tay tace ai ba sai tasa ba tunda tailor ya gwadata, suna cikin kallo sai ga Kawu Amadu da Kamalu sun shigo yadikko tace yazo shima ya ga lefen sosae shima ya yaba saidae acan k'asan ranshi sam bai farin ciki da Auran ba kamar da Kamalu yay mashi bayani kan wanda za'a aura matan don shima ba so yake ba yafi son tay karatun ta kamar yadda shima yake da burin ya koma Katsina don yay karatu, bayan sun gama gani yadikko ta kawo ma Haulat Abinci da k'yar ta matsa ma Fatuu ta d'an ci suna gamawa Haulat ta shiga bathroom tayo wanka don a mugun gajiye take bayan ta fito tay shirin kwanciya itama Fatun ruwan ta watso bayan ta shirya ta hau gadon lokacin tuni bacci yay awon gaba da Haulat, Sam Fatuu ta kasa bacci sai faman sak'e sak'en mafita take rashin zuwan gwaggo ya dameta sosae ga Auran da shima bata son ayi can wata zuciyar ta ayyana mata ko ta kira Haisam ta fad'a mashi halin da take ciki game da wanda za'a aura matan sai kuma ta ayyana to in ta fad'i mashi shi mai zai iya yi mata tasan ba iya sa Ard'o ya fasa zai yi ba k'arshe ya bata hak'uri kawae dama a k'ule take dashi don kwata kwata ya daina kiran ta, haka taci gaba da yin tufka da warwara ta sak'a wannan ta kwance wannan har dare ya raba ba tare da ta ankare ba, can wuraren Asuba ta mik'e ta saukko daga kan gadon ta nufi inda akwatunan da tazo da su suke ta bisu da ido kaman mai nazarin wani abu kafin ta kai hannu ta d'aukko trolley d'in a hankali don kar ya saki sauti, k'asa ta aje shi ta bud'e ta sake d'aukko babban shima ta bud'e ta fiddo wasu kaya ta saka acikin trolley d'in ta d'aukko wasu takalma daga can gefe suma ta saka ciki duk wani abu da tasan zata buk'ata ta saka sannan ta rufe babban Akwatin ta maida shi inda yake ta d'aukko wata Handbag d'inta dake rataye ta bude kud'in da Khalid ya bata ne a ciki dama bata ta6a ko yar biyar ba ta curo su ta nufi akwatunan lefenta ta d'an bud'e d'aya daga ciki ta cusa kud'in kafin ta rufe ta dawo wurin trolley d'in ta rufe shi ta kai hannu ta d'aukko Hijab d'inta dake sagale jikin gadon ta saka har ta d'auki trolley d'in ta nufi hanyar fita sai kuma ta dakata ta juya tana kallon Haulat dake kwance tana bacci hakanan ta ji kamar bata kyauta mata ba in ta tafi ba tare da ta sanar mata ba, a hankali ta jingine trolley d'in ta nufi gadon ta hau a hankali tasa hannu ta fara tashin ta da yake haulat bata da nauyin bacci a nutse ta bud'e idanunta tana ganin Fatuu a gabanta ta yunk'ura da sauri da alamar mamaki akan fuskarta tace "wai har Asuba tayi kin ma yi salla kenan" a hankali Fatuu ta girgiza mata kai murya k'asa k'asa tace "Asuba bata yi ba Haulat" ganin yadda tay Maganar yasa itama Haulat yin k'asa da murya ta tambaye ta miya faru, shiru ta d'an yi tana kikkafta ido kafin tace "Gida zan koma" cikin rashin fahimta Haulat ta sake tambayar ta wane Gidan tace mata Katsina waro ido Haulat tay baki bud'e jin abunda tace Fatuu taci gaba da cewa "Haulat ban son Auren nan, ban so gwara in gudu kawae in dae aka ga bana nan ai dole a fasa" a razane Haulat tace "Amman Fatuu baki ganin lokaci ya k'ure saura fa yan kwanaki a d'aura auran ki miyasa tun farko baki nuna baki so ba sai yanzu" kuka ta fara yi k'asa k'asa tace "Saboda Baffana ne Haulat Kawu Amadu baya fad'i maki ba" kai ta d'aga mata tace eh ya fad'i mata taci gaba da fad'in "Yanzu ban son auran nan Haulat....." Katse ta tay tace "amman Fatuu kina ganin abu ne mai sauk'i fasa auran nan don kin gudu, ni a ganina kawae zaki jawo wata matsalar ne ki k'ara jefa su Baffa cikin wani tashin hankalin" Fatun tace "ai dama gwaggo bata so dalilin hakan ne yasa take fushi da ni don na k'i goyon bayanta nace na amince aman auren yanzu in naje nasan zata yi wani abun a fasa" shiru Haulat tay tana kallonta kawae ta lura ganin hakan take abu mai sauk'i can ta dafata tace "Fatuu ni a ganina ki hak'ura kawae tunda har an zo nan....." Cikin kuka tace "Allah bazan Aure shi ba in ba haka ba mutuwa zanyi don baki san wanene za'a aura man bane yasa kike cewa in hak'ura, Mashayi ne fa mai neman mata kuma..." Nan ta kwashe komai harda gidan gona da ya kaita da Maganin bacci da ya saka mata a lemu harda abunda yay mata jiya da yamma da ta dawo ta isketa ta zo, hannu Haulat tasa ta rufe bakinta cike da Al'ajabi kafin ta cire a sanyaye tace "Shikenan Fatuu in dai kina ganin gwaggon zata iya yin wani abu da zai sa a fasan kije" da sauri ta goge kwallan fuskarta ta juya zata sauka daga gadon Haulat tace "Amman Fatuu ni fa?" juyowa tay ta kalleta tace "ba sai ku dawo da kawu Amadun ba" gyad'a kai Haulat tay sai kuma ta sake cewa "amman lafiya lau zaki iya tafiya dare fa ne" jinjina mata kai Fatuu tay tace zata iya lafiya lou ba abunda zai sameta in sha Allahu daga haka ta idasa sauka ta nufi hanyar fita idon Haulat a kanta tana kallon ta cike da tausayi har ta kai hannu zata d'auki trolley d'in taji muryar Haulat ta kira sunanta juyawa tay ta kalleta ta saukko ta nufo inda take tana zuwa tace "bari mu tafi tare" da mamaki tace "amman haulat jiya fa kuka zo ko hutawa sosae baki yi ba ki kwanciyar ki daga baya sai ku dawo" girgiza mata kai tay tace su tafi ba komae har cikin ran Fatuu taji dad'in hakan, Hijab Haulat ta d'aukko ta saka ta maida kayan da ta cire jiya cikin jakarta dama ita kadae ta zo da ita ta d'auka Fatuu ma ta d'auki trolley a hankali tasa k'afa cikin Falon ba kowa sai k'annenta dake ta bacci kan shimfid'a dama cikin d'akin daga ita sai Haulat Yadikko na d'akin Baffa, cikin sa'a suka fito daga cikin d'akin gaban Haulat nata bugawa gaba d'aya a tsorace take suna fitowa Fatuu tay ma Haulat nuni da hanyar bayan gidan a hankali cikin rad'a tace ta can zasu fita bata kopar waje ba........... *Uhmmmm, shin su Fatuu zasu samu fita daga cikin gidan kuwa? In sun fita zasu samu komawa Katsina? Gwaggo zata saurari Fatuu in sun samu komawar? Za'a fasa auran ko baza'a fasa ba???* _Littafin A Sanadin Makwabtaka part 2 Naira 300 ne za'a tura ma Mutum har part 1 ga mai so zai turo kudin ta wannan Account din, 1509618776, Zainab Bature Access Bank, za'a turo shedar biya ta wad'annan nos din 09013804524 ko 08169856268._ Domin karanta cikakken Littafin sai ku danna bulun Rubutun dake kasa ko kuma hoton dake kass 👇👇👇👇 https://aihausanovels.com.ng/novel-document/a-sanadin-makwabtaka-book-2-complete-hausa-novel 👆👆👆👆👆 ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels WhatsApp Number: 08138873799 Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ **************************