asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) STEP TWO 1 and 2 ƘASAR JIDDER✈️🌎 Razhdeen shi da Roshan ne suke zaune a babban falon masarauta, sun jeru akan wani tsararren sopa mai uku, gwanin burgewa. Mai martaba ne ya zuba musu ido sai faman sakin murmushi yake yana daga kan kujerarsa, yayi matuƙar yin farin cikin ganin su Razhdeen, fuska ɗauke da murmushi yake faɗin "a gaskiya naji daɗin zuwanku tin a lokacin da Mahaifinku ya sanar mun cewa kuna hanya, amma nayi mamaki sosai da naji labarin dawowarku Nigeria tsawon wata biyu amma baku tako ƙafarku kun zo ba sai yanzu, yanzun ma saboda bikinku ne yasa....." Murmushi Roshan ya yi tareda faɗin "Uncle kayi haƙuri wallahi abubuwan ne suka cakuɗe mana..." Mai martaba yace "daman nasan abinda zaku ce kenam ai, toh gaskiya ku gyara domin zumunci yanada kyau...." Roshan kai a sunkuye yace "Insha ALLAHU Uncle, a mana afuwa..." Mai martaba yace "shikenam ba damuwa, ALLAH ya muku albarka" ya kuma cewa "yaushe ne bikin nakun?..." Ɗan ɗago da kansa Roshan ya yi daga bisani yace "am sauran kwana biyar yanzu, amma Ni kaɗai ne mai yin Auren banda twins..." Mai martaba kallon yanda Uncle Deen yake yayi tareda faɗin "why? Razhdeen!..." Ɗagowa Uncle Deen yayi shima idonsa akan mai martaba ya ce "Uncle!..." Mai martaba yace "baka magana ne?..." Daƙer yake motsin da lips ɗinsa yace "ina yi..." ataƙaice. Mai martaba yace "naga tinda na fara magana baka ce komai ba, kai meye zai hanaka yin Auren?..." Kafin mai martaba ya iddasa maganarsa sai ji sukayi Hajiya Maamie ta tari yawunsa da cewa "ya zaka tambaye shi alhalin ku kuka hanashi...." Duk ɗagowa sukayi suna kallon ta cike da mamaki ko sallama batayi musu ba, kuma da alamun laɓe tayi tana jin duk maganganunsu. Mai martaba yace "haba baiwar ALLAH ai ko sallama zakiyi Koh..." wani irin harara ta wurga masa cike da takaici take faɗin "ai ba buƙatar yin sallama tinda ana shirin watsa mun ƙasa a ido, fisabilillah mai martaba saboda rashin gaskiya irin taka mun gama tsaida magana akan cewa ku haɗa Razhdeen da Ramlat in yaso ayi bikin rana ɗaya duk gaba ɗaya, amma shine yanzu kake tambayarsa wai meye zai hanashi Aure? toh wa kuke tunanin zai Aura kenam?...." Mai martaba girgiza kai yayi sannan yace "Maamie kenam! shin kin tsaya Kinga ƙarshen wasan ne? ki tsaya kiga gudun ruwana mana, Nima abinda nake shirin yi kenam, nima so nake a haɗa bikinsu gaba ɗaya..." Hajiya Maamie ɗaga kafaɗa tayi tareda cewa "gwara kam in har anason ganin farin ciki na, zanje na turo Ramlat tazo su gana da juna..." tana kaiwa nan tayi ficewarta. Mai martaba sunkuyar da kai yayi ƙasa yana jinjina irin ƙarfin hali na Maamie. Razhdeen gaba ɗaya bai gama fahimtar abinda suke nufi ba, juyowa yayi ya kalli Roshan, cikin sa'a kuwa shima Roshan Uncle Deen ɗin yake kallo, haka suke kallon juna cikin rashin fahimta abinda ake nufi da haɗa Razhdeen da Ramlat, Ganin basu fahimci ina aka dosa ba yasa duk suka maida kallonsu kan Mai martaba wanda kansa har zuwa yanzu yake durƙushe, Roshan ne ya buɗi baki yace "Uncle me yake faruwa ne kam? naga kana cikin damuwa..." Mai martaba ya ɗago a hankali yana binsu da kallo yace "shin Razhdeen yanada wacce yake so?..." ya tambayi Roshan ne saboda yana ganin shi zaifi bashi amsa akan lokaci, Roshan yace "gaskiya Uncle banida masaniya akan haka amma ka tambaye shi mana gashi nan, nidai a sanina dashi bai taɓa yin budurwa ba kuma har zuwa yanzu babu wata..." Kafin ya ƙarasa mai martaba ya dakatar dashi da cewa "ya isa haka Roshan, kowa yasan halin Razhdeen ba kula mata yake ba, Razhdeen abinda nake so dakai shine za'a haɗa bikinku gaba ɗaya ayi kai da Roshan, tin ba yau ba na rigada na maka matar da zaka Aura tinda kai bazaka iya zaɓo ba...." ya ƙarasa maganar idonsa akan Razhdeen wanda shima mai martaba yake kallo fuska a murtuƙe ba bu Annuri.. "Who is her?.." yayi tambayar a taƙaice. Mai martaba yace "ƙanwar matata Maamie wato Ramlat, tana zaune anan gurin mu..." girgiza kai Razhdeen yayi zaiyi magana saiga Ramlat ta shugo da sallama a bakinta tana ɗauke da tray ɗin kulolin abinci, ta ajiye akan glass table dake tsakiyar falon, ba jumawa kuwa saiga kuyange su uku sun shugo ko wacce tana ɗauke da tray ɗin kayayyakin abinci aciki, suna ajiye wa suka fice, Ramlat ce ta zauna a ƙasin carpet tana gaishesu, Roshan ne kawai ya amsa shi kuwa Razhdeen ko kallon yanda take beyi ba, tasha ƙwalliya sosai sai fidda ƙamshin turare take tana satar kallon Roshan, ita har cikin zuciyarta tafi son Roshan saboda ya kasance mutum mai faram-faram babu ruwansa kuma ko wanne acikin su da kalar tsarin kyan da ALLAH yayi masa, babu wanda yafi wani kyau, sanin dai-dai sai ALLAH. Mai martaba idonsa akan Razhdeen wanda kansa akan wayar hannunsa yanata pressing ko ɗagowa baiyi ba, Mai martaba yayi ƙarfin halin cewa "Razhdeen ganan Ramlat wacce ake son haɗa ku, dan Allah ka dubeta da kyau kar ka watsa mana ƙasa a ido, Ni na zaɓa maka ita, ban taɓa neman alfarma a waranka ba sai yau...." Gira a haɗe Razhdeen ya ɗago cikin ɓacin rai yake kallon Mai martaba murya ciki-ciki yace "Uncle alfarmar mai kake so nayi maka?..." Mai martaba yace "akan Auran wannan yarinyar..." ya ƙarasa maganar yana nuna Ramlat da yatsa, sannan ya kuma cewa "Na rigada nayi magana da Abbanku kuma ya amince mun akan wannan batun, mun rigada mun tsayar da maganar rana yata yau Insha ALLAHU za'a ɗaura muku Aure gaba ɗaya, sannan itama Ramlat zata biku can Nigeria ta zauna har zuwa ranar bikin..." Gaba ɗaya ran Razhdeen ya gama ɓaci har eyes ɗinsa sun kaɗa sunyi jawur, cikin ɗaga murya yace "Umarni ake bani ko kuma Zaɓi?..." shi kansa Mai martaba sai da ya ɗan tsorita ganin yanda yanayin Razhdeen ya chanza lokaci ƙanƙani, Roshan ne yayi saurin dafa kafaɗarsa yana ɗan bubbuga shi kaɗan alamar rarrashi domin yasan halin ɗan uwan nashin muddin ransa yakai maƙura toh zai iya yin rashin kunya a kowa ma, kuma gashi suna matuƙar girmama mai martaba, Razhdeen jin anyi shuru ba'a bashi amsa ba ya kuma cewa "ina tambayarku Umarni kuke bani ko kuma zaɓi?..." Ramlat dake zaune itama ta gama tsurewa, ƙirjinta ne yake bugu da ƙarfi-ƙarfi domin tana matuƙar tsoron Razhdeen, shiyasa jininsu bai haɗu ba, Mai martaba shima daƙer ya iya buɗe baki yace "umarni muke baka Razhdeen..." A ɗan zabure yakai eyes ɗinsa kan Mai martaba tareda faɗin "whattt!? kuna nufin kuce Auren dole?..." cike da mamaki yake girgiza kai yana cewa "impossible...." ya ƙarasa maganar tareda miƙewa tsare ya nufi hanyar fita, shima Roshan da sauri ya miƙe yabi bayansa, shi kam mai martaba ido kawai yabi su dashi, shima har cikin zuciyarsa bason haɗin nan yake ba, zaiyi ne saboda matarsa Maamie amma yasan Razhdeen in har ya bijirewa abu baya taɓa jin ƙira. kallon Ramlat yayi sannan yace "toh Kinga a gaban ki abinda ya faru, da haka zaki zauna dashi?..." Ramlat tana kuka tace "Abul wallahi Aunty Maamie ce take son haɗin nan Ni Yaya Roshan nake so, daman nasan Uncle Deen bazai taɓa sona ba..." Jinjina kai Mai martaba yayi sannan yace "Roshan kuma kinga da matar da zai Aura..." "Dan ALLAH Abul wallahi inason Yaya Roshan mezai hana ku Aura masa mata biyu Ni da wacce yake son Aura, wallahi zan zauna dashi a haka..." Mai martaba yace "shikenam kije sai nayi shawara..." ta tashi jiki ba ƙwari tayi ficewarta, Shi kuwa Razhdeen niyarsa shine yabar ƙasar gaba ɗaya, daƙer Roshan yake rarrashinsa yana so ya shawo kansa amma fur Razhdeen yaƙi, sai cewa yake "Please inason komawa Nigeria daga nan zan wuce U.S, saboda an raina mun wayo Ni za'ayi wa Auren dole? hakan ma wannan kucakar yarinya marar class, a gabana Auntynta take wulaƙanta Uncle amma a haka zan Aure ta? Impossible..." Roshan riƙe hannayensa yayi yana bashi haƙuri game da cewa "My Man ka kwantar da hankalinka, Insha ALLAHU wannan haɗin bazaiyu ba, saboda Nima kaina yarinyar bata mun ba, sannan ga ɗabi'un Yayarta marasa kyau amma inaso komai ka bishi a hankali, ka dubi darajar Uncle shima kamar mahaifi yake a wurin mu, Uncle ba kamar Abbah bane yanada sauƙin kai, muje ka same shi muyi magana ta fahimta sannan ka nuna masa cewa kanada wacce kake so kaima..." Daƙer Razhdeen ya haƙura suka koma cikin masarautar, kai tsaye part ɗin da aka tanadar musu suka wuce domin a halin yanzu Razhdeen baya buƙatar yin wata magana ta fahimta... INDO tana zaune kan sallaya da carbinta a hannu tana lazumi ta fara jin kururuwar Maamie daga Falo sai balbala masifa take, Dasauri INDO ta tashi a tsorace ta fice domin ganowa abinda ke faruwa, tana fita Falo ta tarar da mai martaba zaune akan sofa ita kuma tana tsaye a kansa baki ya gagara rufuwa, ga kuma Ramlat itama zaune a one seater ta ɗora hannu akan goshi, gaba ɗaya ta tsani ganin Maamie tana masifa a mai martaba wannan abun kunya, INDO ce ta ƙaraso wurin tareda faɗin "lafiya kuwa?..." a fusace Maamie ta kallo yanda take tsaye da zureren hijab ɗinta, ta ɗago yatsa tana nuna ta dashi tace "ki maida hankalinki bada ke nake ba, ina ruwanki da shiga shirgina, tin ba yau ba na gaya miki idan ina magana da mijina ki daina shiga...." INDO tace "naji hayaniya ne shiyasa na fito naji meke faruwa..." Maamie cikin tsawa tace "toh babu ruwanki, idan kinji abinda ke faruwan akwai abinda zakiyi ne?..." INDO ta girgiza kai tareda cewa "a'ah kiyi haƙuri, naga bai dace ki tsaya a kansa kina ɗaga masa murya bane..." Kafin ta ƙarasa maganar Maamie ta malmalo wata ashar ta maka mata tareda faɗin "kije kiji da wannan tsohon uban nakin da yake gab da mutuwa akan kujerar mulki ya gagara sauƙa saboda kwaɗayin abun duniya..." INDO tace "kiyi haƙuri abun bai kai ga haka ba..." Mai martaba ne ya buɗi baki yana cewa "kibi duniya a sannu Maamie..." Harara ta watsa masa tareda faɗin "Duniya kam gani a cikinta ta ishi kowa ma bani kaɗai ba, Kuma wallahi kusan yanda zakuyi ku Aura wa Razhdeen Ramlat tin kafin ajiyo kan mu, kana maganar wai tace Roshan take so yooo banda na ga, mai Roshan yake da shi, wanda ko rabin kamo ƙafar Razhdeen baiyi ba a arziƙi..." Sai a yanzu Ramlat ta buɗi baki tace "nifah Maamie Yaya Roshan nake so...." Maamie a fusace ta miƙar da hannu tana danƙwalonta tareda faɗin "ke kin ci ubanki, ina samar miki waran da zakiji daɗin rayuwa ki ƙwanta a dukiya ki tashi a dukiya amma ke kina Kai kanki wurin wahala, mai za'ayi da kishiya banda dole, ALLAH ya tsinewa wanda ya ƙirƙiri sunan kishiya babu daɗin ji, Haka zamu ƙare rayuwar mu a zuwa kan kishiya? lokacin da mai martaba zaiyi Auran farko mu biyu ya haɗa ya Aura lokaci guda Ni da Maimuna wacce ba'a san duniyar da take ba yanzu, kafin daga baya ya ƙara Auran wannan matsiyaciyar, shine ke kikeso kema ayi miki irin nawa? kamar wasu marasa gata da farin jini, toh bazaiyu ba Razhdeen ɗin zaki Aura..." Mai martaba hannu yasa ya dafe saitin zuciyarsa jin an ambaci sunan da yake tada masa da hankali wato Maimunatu... Ana cikin wannan halin saiga Razhdeen da Roshan sun shugo falon, duk maganganun da Maamie tayi suna jinta, Roshan ne yazo har gaban Maamie ya tsaya yana mata kallon ƙurilla daga bisani ya cire glass ɗin kan dara-daran idanuwansa, ya soma magana cikin ɓacin rai yake faɗin "Alhamdulillah tinda ALLAH ya hore mun abinda zan rufawa kaina asiri, dukiya inada su dai-dain gwargwado kuma fiye da yanda kike tunani, domin da za'a haɗa kanki dana danginku gaba ɗaya bazaiyi kwatan yawan adadin dukiyarda nake da shi ba, naji ɗan uwana Razhdeen ya fini yawan dukiya amma inaso ki sani cewa ko a yanzu nace ya bani rabin dukiyarsa ba musu zai bani saboda mu ɗin gudan jini ne, nashi nawa ne haka kuma nawa nashi ne, Ƙanwarki kuma ki sanar mata cewa koni Roshan bazata samu shiga ba balle my twins da ko ƴar aiki bazai ɗauketa ba balle a matsayin mata..." Hajiya Maamie kama kunkumi tayi tana kallonsa cike da mamakin maganganun da yake jifarta dasu, Murmushi tayi tana yatsina fuska tace "Hmmm! Roshan kenam, Ni baka isheni kallo ba, bata kai nake ba ka matsa ka bawa ɗan uwanka wuri mu magantu..." Roshan ɗaga kafaɗarsa yayi tareda faɗin "okay fine! Idan kikayi dashi tamkar kinyi dani ne..." Ya ƙarasa maganar tareda komawa gefe, Razhdeen ne ya maye gurbin da Roshan ya tsaya shima yana fuskarta da hannayensa a goye kan ƙirjinsa, fuska a ɗaure ba Annuri. Maamie itama kallonsa take fuska a sake sai faman sakin murmushi take tace "Razhdeen inaso muyi magana ta fahimtar juna, kaga yanzu mun zama ɗaya Ramlat tamkar ƴar uwarka ce, kuma ka dubeta ita ɗin marainiya ce bamuda uwa babu uba, dan ALLAH ka temaka ka Aureta ko zata samu farin ciki, Ni zanyi iya ƙoƙarina naga ka Aureta tinda wannan matsolon Sarkin ya kasa aiwatar da komai...." Saida ta kammala zantuttukanta tass sannan tayi shuru tana son jin amsar da zai bata, itadai addu'arta shine yace ya amince..." Sakin nannauyar numfashi yayi sannan yace "kin gama?..." Tace "kai nake sauraro Razhdeen..." Kafin ta ƙibta ido har ya kai hannu ya zabga mata wani irin gigitaccen marin da bata san lokacin da ta dungura kan kujera tayi tsalle ta faɗa bayan kujerar ba, Kaf waran babu wanda bai tsorita da wannan marin ba, hatta shima mai martaba bai san lokacin daya miƙe tsaye ba, ita kuwa Ramlat bata san ta zamo daga kan kujerar da take ba, ta kafa gwiwowinta a ƙasan carpet, Itama INDO ja da baya tayi tana zazzaro ido waje hannayenta a toshe da bakinta, Shima Roshan bai taɓa tunanin Razhdeen zai iya marinta ba, abun yayi matuƙar bashi mamaki sosai kuma ya jinjina wa zafin ransan nan... Maamie tana kwance a bayan kujera shuru bata ɗago ba har zuwa wannan lokacin, Mai martaba murya na kakkarwa yace "Razhdeen meka aikata haka? shin bakada hankali ne? Matata ce fah? ka manta yanda nake a wurinka?..." Cikin ɓacin rai Razhdeen yake kallonsa tareda faɗin "bana juran ganin irin waɗannan dabbobin matan, saboda haka ne yasa bana zama inuwa ɗaya da matar Abbanah saboda nasan wata rana zan iya illata ta, duk da yanzu naji labarin basa tare, don haka itama wannan tabi a hankali kafin nabar ƙasar nan..." yana kammalawa ya juya zai fita shima Roshan bin bayansa yayi zasu fice a tare, Juyowa Roshan yayi yana kallon Mai martaba cikin tausayawa yace "Uncle akwai ɗauri a jikin ka Please ka nemi maganin karya asiri domin ba haka aka barka ba, Uncle wanda na sani a baya bakai bane yanzu, duk zafin ran Abbanah baiyi ka ba amma yau kaine nake gani haka mace tafi ƙarfinka? Amma zan tayaka da addu'a karka damu...." yana kammalawa shima ya fice, kai tsaye part ɗin su suka nufa... Mai martaba girgiza kai yayi domin al'amarin yana shirin fin ƙarfinsa, kallon yanda INDO take yayi sannan yace "ki kai musu abinci basu ci komai ba tinda suka zo, sannan ki lallamesu su ci karsu zauna da yunwa..." Amsa masa tayi cikin girmamawa ta wuce kitchen, yana tsaye yaji kukan Ramlat tana faɗin "Abul ta mutu kazo ka duba ta bata motsi wayyo Allah nahhhh..." tana kuka sai faman jijjigata take amma Maamie ko motsi babu, Saida mai martaba ya zagayo bayan kujerar ya tarar da ita kwance ga fuska har ya kumbura, a hankali ya furta cewa "kije ki ɗauko mun ruwan sanyi.." Da gudu Ramlat ta miƙe taje frig ta ɗauko jug mai ruwan sanyi ta kawo, ana watsa mata kuwa ta farfaɗo tana sauƙe numfashi sama-sama, tareda faɗin "aina nake? ina ne Nam? gida nake son zuwa.." Daƙer mai martaba ya ɗagota sannan ya wuce da ita bedroom ɗinta tana sumbatu cikin rashin hankali domin ji take kanta yana juyawa bata san a yanda hankalinta yake ba, da haka aka shige da ita ciki... *A TANTANCE MUN* *SHIN DA HAJIYA MAAMIE DA KUMA HAJIYA KILISHI WACCE TAFI WULAƘANCI????* asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) STEP TWO sorry for the mistake a farkon step two nasa 51 to 52 maɗorin ƙarshen step one neh, naga wasu suna mun complain akan anyi musu nisa sosai a step two, toh ba haka bane farkon ne, but yanzu zamu cigaba akan page 3 and 4 na step two *Chapter* 3 and 4 Mamie kamar wata zautacciya haka ta rikice bata san yanda kanta yake ba, lalume ta fara yi tareda faɗin "ina Ramlat? Ramlat kina ina bana gani dai..." Ramlat ce ta zauna gefenta a bakin gado ta riƙo hannayenta tana faɗin "Aunty gani nan dai..." Maamie tana kuka tana cewa "duba mun akwai fuska a jikina?.." Ramlat tace "akwai fuska mana" Maamie ta kuma cewa "ki duba da kyau shin ba'a rabe mun kaina da gangan jikina ba? yanzu haka kina kallon fuskata? naga duhu nake gani sannan banji alamun kai a jikina ba..." Ramlat tace "haba Maamie ai duk ke kika jawo haka, gashi kema Uncle Deen bai barki ba balle Ni, shin har yanzu kina kan bakarki ne? gashi kinyi mun biyu babu shima Yaya Roshan ɗin yana shirin kuɓuce mun..." Maamie tace "kina nufin kice ba Razhdeen zaki Aura ba? toh wallahi tallafi ko naman jikina yake yanke wa kullum saina sa ya Aureki dolensa..." "Hmmm! kece a wahalai nidai zanbi tawa hanya yanda bazan jawo a illatani ba...". a cewar Ramlat. Maamie cewa tayi "au ina nema miki gidan daɗi ke kuma kina mai watsa mun ƙasa a ido?..." cikin ɓacin rai Ramlah tace "shikenam Aunty Maamie kiyi duk yanda kika ga ya dace..." tana kaiwa nan tayi ficewarta, Maamie cikin ɗaga murya tace "Ai kuwa zanyi abinda ya dace idan naje wurin Boka matsagwal, wallahi sai Razhdeen yazo yana binki har da tsuguno..." ta ƙarasa tana jan numfashi sama-sama ga fuska yanda ya kumbura suntum har shatin photon hannunsa ake gani akan fuskar... 🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️ ƳAR AMANA tana zaune a yanda suka saba hallaruwa tana riƙe da jitar ta sai kaɗawa take, Dake duk mutanen wurin ba wanda baya jin daɗin sautin jitarta, tana cikin wannan halin sai ga wata danƙararriyar mota baƙa ƙatuwa wasu matasa ne su biyu suka fito suna rufe da fuskokinsu da baƙar hula suka yo kan Ƴar Amana dake zaune, duk waran babu wanda bai tsorita da ganinsu ba domin har da masu riƙe da bindiga, ɗagowa tayi tana binsu da kallo kafin ta ankara har sun finciko hannunta, sun ɗagata sama tana bubbugan bayansu haɗe da shure-shure amma ba bakin yin ihun, kafin kace mai tsofin wurin sun haɗe waran da kururuwan "wayyo ɓarayi mun shiga uku, akawo mana ɗauki ƴan fashi...." Nan danan suka ja motarsu a ɗari suka bar wurin, daman sun juma suna target ɗinta tin barinta a hannunsu ogansu ya hura musu wuta akan sai sun nemota sai yau Allah ya bada sa'ar kamata... Cikin Daji aka nufa da ita already sun rufe mata fuska da baƙin ƙyalle.. 🤏Baiwar ALLAH tin da Aunty Yolash tazo take faman gyarata irin gyaran Amare duk da bata son Auren ko kaɗa, har ila yau fuskar Razhdeen ne yake mata gizo, wani sa'in sai taji kamar ta fita taje ta nemo Razhdeen ta roƙe shi akan ya Aureta, kwata-kwata batada wani sukuni, ba wai bata son Roshan bane Ita dai zuciyarta Razhdeen ya zaɓa mata kuma shi yafi dacewa da ita amma babu yanda ta iya... Minal kuma tana can gidan Razhdeen ita da Mohandas ita take masa girki duk da bata iya sosai ba sai ya saka mata hannu, wani sa'in kuma shi yake yi da kansa, Soyayya iya soyayya suna shanta sun fahimci juna sosai domin har Mohandas ya amince akan cewa bayan bikin Roshan shima zai musulunta sannan a ɗaura musu Aure a ɓoye in har Abbah bai amince ba.... Misalin ƙarfe 2 na dare Roshan ya yi sujjada yana sallar lafula, shi kuwa Razhdeen yana saman gadonsu yana karanta karatun Alkur'ani mai girma. Hajiya Maamie kuwa ta rigada ta ziyarci Bokanta akan maganar Auren Razhdeen da Ramlat, ya amsa mata da cewa komai zai iya yuwa da zaran tabi duk dokokin da ya sharɗanta mata, ya bata wani ɗan ƙaramin turare wanda Ramlat zata shafa sannan ta nufin wurin Razhdeen, da zaran ya shaƙi wannan ƙamshin turaren shikenam aikin gama ya gama kuma da sunansa akayi amfani, Hajiya Maamie tayi matuƙar yin farin ciki sosai saboda wannan ƙaramin al'amari ne, tana murna tace "shikenam da zaran ya shaƙa zai rinƙa bin Ramlat kenam? kamar irin wanda ka bani nayi amfani dashi waran toshe bakin mai martaba Koh?.." Boka yace "dokar wannan turaren shine muddin ya shaƙi ƙamshi toh asiri yayi dai dai, in kuma wari ya shaƙa toh al'amari ya ɓaci domin babu wani tsafin da zai shafe shi, tashi kije.." ta tashi cikin zumuɗi ta tafi, Washe gari da sassafe Hajiya Maamie taje ɗakin Ramlat ta tashe ta daga bacci tareda faɗin "Ke dallah tashi mun samu abun ƙaruwa..." tayi maganar dai-dain lokacin da take shirin zama a bakin gado, Ramlat tashi tayi tana murtuƙe fuska domin ta tsani a tashe ta a bacci indai ba lokacin tashinta ne yayi ba, tana turo baki tace "wai meye ne Aunty Maamie?..." Maamie tace "naje wurin Boka ya bani turaren bita zaizai kuma ba makawa asirin nan saiya kamashi domin Boka bai taɓa yin rashin nasara ba..." Ramlat tsayawa tayi tana kallonta cike da mamaki take girgiza kai sannan tace "wai Aunty Maamie bazaki daina zuwa wurin bokan nan ba koh? meye amfanin haka? toh Ni gaskiya ki daina sakoni a lissafin waɗanda boka zaiyi musu aiki...." ta ƙarasa maganar tana murguɗa baki... Maamie ta ƙafeta da kallo tareda riƙe haɓarta tace "iyyeeee! Lallai yarinyar nan kema na kusa nayi aiki akanki indai zakina bijire mun wallahi, kuma dole sai kinyi aikinda Boka yace kiyi aikin banza kawai, wawiya arziƙi na biyoki kina guduwa masa tsabar shirme irin nakin, dallah malama tashi ki shashshafa turaren ki kai musu abincin breakfast tin kafin wancan matsiyaciyar ta kai musu uwar shishshigi..." "Toh naji..." A cewar Ramlat wacce take ƙoƙarin tashi, tayi duk abinda Maamie tasa ta wato turaren nan haka yake tashi yana bada zazzaƙar ƙamshi, haka suka fice a tare kai tsaye kitchen suka nufa, suka tarar an kammala girki an saka musu a kuloli na musamman, Ɗaukar kayan girki tayi ta nufi Falo tana shirin ficewa, saiga INDO daga upstairs tin kafin ta ƙarasa sauƙowa tace "Ramlat ina zaki da kulolin abinci?..." Maamie wacce take zaune a kujerar Falo ta ɗora ɗaya akan ɗaya sai wani irin kallo take watsawa INDO, baki a murguɗe tace "yanda kika aiketa uwar shishshigi, kina so a baki ki kaiwa dangi ne? don naga akwai tamowa a jikinsu..." Sauƙe numfashi INDO tayi domin ta fara gajiya da kalar wulaƙancin da Maamie take mata acikin gidan nan, baki ta buɗe cikin sassanyar murya tace "Aunty Maamie duk zuriya ta sun wuce ace musu mayunwata, domin kin san asalina da tushe na, daga gidan sarauta na fito sannan na ƙara shiga gidan sarauta Kinga kuwa gaba da baya Arziƙi ne ke bibiyata..." Maamie sake baki tayi tana mata kallon mamaki, tasa hannu a saitin haɓarta tana faɗin "iyyeeee! Lallai matar nan, yanzu har kina da bakin da zaki gaya mun magana? Ahh lallai wuyanki ya isa yanka, tabbas saina ƙara miƙewa tsaye a kanki ƴar banza..." INDO kallonta kawai take cikin rashin fahimtar abinda take nufi, Abinda Maamie take nufi shine akwai sihirinda tayi mata kuma yana shirin karyewa dole sai ta sake zuwa gurin bokan ta... Ramlat ganin bazata iya tsaya sauraronsu ba yasa tayi saurin ficewa zata nufi masauƙin su Razhdeen..... A ɓangaren su Razhdeen kuwa suna zaune akan dadduma a ƙasin gadonsu suna tsare-tsaren yanda bikin Roshan zai kasance, Jin sallama yasa Roshan ɗogowa tareda amsa sallamar shi kuwa Razhdeen daman ko ɗagowa baiyi ba yana rubuce-rubuce, Ramlat durƙusawa tayi tana gaishe su tareda ajiye musu kulolin abinci, kafin kace mai ƙamshin turaren jikinta har ya hargutsa ɗakin gaba ɗaya, Roshan idonsa yakai kan Ramlat yana yamutsa fuska tareda faɗin "wannan wani irin turare ne babu daɗin ji..." Itama ɗagowa tayi tana kallonsa ido a zazzare tsananin tsoro ne a bayyane kan fuskarta, dasauri takai idonta kan Razhdeen wanda tinda kansa yake ƙasi ko ɗagowa bai samu daman yi ba, Ganin har zuwa yanzu bai ko motsa ba yasa jikinta yin sanyi domin da sunansa akayi amfanin haɗa turaren, Razhdeen ganin shima turaren ya ishe shi da wari yasa ya ɗago a fusace yana wurga mata harara cikin tsawa yace "You'll get out inside our room or u want me to remove u by myself..." A tsorace tayi firgit ta miƙe tsaye ba shiri tayi waje da gudu, dogon tsuka yaja tareda faɗin "non sense girl..." hakan na nufin tsafin baiyi aiki ba tinda so ake yaji ƙamshi shi kuma wari yaji, an samu matsala kenam... Haka ta shige Falo tana kuka, kai tsaye bedroom ɗin Maamie ta wuce ganin bata tarar da ita a falon ba, Maamie tana ganinta a cikin wannan halin tayi saurin dafe ƙirjinta tareda faɗin "na shiga uku kar dai kice an samu matsala..." tana kuka tace "naga korata yayi cikin fushi, Ni Maamie nace miki mu rabu da Uncle Deen ɗin nan babu wani tsafin da zai kama shi...." kafin ta rufe baki Maamie tayi saurin katseta da cewa "yi mun shuru dallah! ai wannan tsoron nakin ne zai jawo mana matsala, zakiyi abu amma bazaki sake jiki kiyi ba ƴar Banza kawai..." Ramlat tace "toh Maamie ya zanyi, yanzun meye mafita? gashi gobe asubanci zasu yi su koma Nigeria..." Maamie tace "wa? ai ƙafarki ƙafarsu dake zasu tafi kuma dole Abbansa nasan saiya tilasta shi akan ya Aureki tinda yana jin maganar mahaifinsa..." Ramlat tace "toh shikenam yanzun naje na fara shiri kenam?..." Maamie tace "eh mana, kuma da daddare inaso kije ki kusance shi da waɗannan ƙananun kayanki nan masu bayyanar da surar jiki, amma ki tabbatar Roshan baya ɗakin..." Zaro ido Ramlat tayi tareda dafa ƙirjinta tace "nashiga uku Maamie wallahi kasheni zaiyi, ke baki san halin Uncle Deen ba koh?..." Maamie a fusace tace "Dan buro ubansa idan yafi ƙarfin kowa ai baifi ƙarfin makircin mace da surar jikinta ba..." Ramlat shuru tayi tana kallon Maamie cikin kalar tausayi... Maamie ta kuma cewa "kiyi duk abinda nace, kai inta kama kiyi tsindir a gabansa..." Haɗiyar yawu Ramlat tayi tareda cewa "tam! I'll try my best..." Misalin ƙarfe 9 na dare Roshan da Razhdeen sun kammala cin abincin dare kenam saiga Mai martaba ya shugo musu ɗakin da sallama a bakinsa, Da fara'a akan fuskar Roshan ya amsa sallamar tareda faɗin "Uncle kaine a room ɗin mu..." Mai martaba yace "ina Razhdeen?..." Roshan yace "ya shiga bathroom yanzu ina tunanin wanka yake yi..." Mai martaba yace "Roshan yanzu Abbanku yake cemun tareda Minal ku ka taho, ina kuka barta?..." Saida ƙirjin Roshan ya buga jin asirinsa ya tonu, baiyi tunanin Abbah zai sanar wa Uncle ba, Cikin ƙinƙina Roshan yake faɗin "Am daman Uncle..." hannunsa akan sumar kansa ta wurin ƙeya yana sosawa gaba ɗaya ya rasa mai zai ce. Mai martaba kallon ƙurilla yake masa yace "ina jinka banason rashin gaskiya fah..." Roshan yace "Uncle damun koma can falonka sai mu tattauna..." Mai martaba yace "tattaunawa akan meye?..." Roshan yace "Please Uncle maganar tanada muhimmanci sosai..." Mai martaba yace "okay ina jiranka yanzun nan..." yana ƙarasawa yayi ficewarsa, shima Roshan dasauri yabi bayan Mai martaba.... Suna fita Ramlat tayi saurin shugowa daman ta daɗe tana tsaye tana jiran fitarsu, tsayawa tayi tana kalle-kalle a ɗakin kamar wani baƙonta, tana sanye da Black net shirt wanda bai rufe mata cibiya ba, duk ana kallon surar jikinta ba tareda tasa ko breziyya ba, sai wani ɗan gajeren wando wanda ya tsaya a iya cinyarta, Ga daman tanada dirin jiki... Saida tayi kusan minti talatin tana tsaye kafin Uncle Deen ya fito daga cikin bathroom ɗaure da white towel a kunkuminsa, Ganinsa yasa ta zaro ido waje ta ƙame a wurin ganin yanda tsarin surar jikinsa yake, ga gargasa a kwance luf-luf kamar gashin jarirai, yanda kasan ba mutum ba domin Ni kaina bazan iya tsara muku yanda surar jikin Razhdeen yake ba, Ga farin fata mai ɗauke ido har wani shining yake, tsayi kuwa ba'a magana domin idan ya jeru da Ramlat zata zamana a iya kunkuminsa zata tsaya, bugu da ƙari ma ga ƙira mai kyau haɗi da murɗaɗɗen jiki, ƙirjinsa kuwa sai ya haɗe mata biyu zuwa uku aciki tsabar faɗi kamar tray.. Razhdeen bai ankara da mutum acikin ɗakin ba saida ya waiwaya ya ganta, domin yasan fitar Roshan shi da Mai martaba.... asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) STEP TWO 5 and 6 "Roshan ka daina mun ƙin-ƙinda ka fito fili ka sanar mun abinda ke faruwa, kunyi wa Abbanku ƙaryar cewa kun taho da Minal Ni kuma ban ganku da ita ba, shin ina kuka barota?...." Roshan yana sunkuye da kai ƙasi tinda Mai martaba ya fara magana bai ɗago ba, Saida mai martaba ya sake ƙiran sunansa ganin ya tafi dogon tunani... A firgice Roshan ya ɗago yana faɗin "na'am Uncle.." ya zuba masa ido alamun bai ji duk abinda ya ce ba. Mai martaba ya kuma cewa "shin ina ku ka baro Minal?..." Girgiza kai Roshan yayi tareda faɗin "Uncle ana bikin ƙawarta ne shine ta tsaya a wurin kuma itace babbar ƙawar Amarya..." Jinjina kai Mai martaba yayi yace "duk alamun rashin gaskiya sun bayyana akan fuskarka Roshan, babu gaskiya acikin lamarinka amma ban sanka da wannan halin ba, Roshan baka ƙarya meyasa yanzu?..." Gaba ɗaya gumi duk ya wanke masa fuska kamar wanda ya fito daga cikin rijiya, wani irin yawu ya haɗiya wanda ya tokare masa maƙogaro, tsoronsa idan har Abbah yasan cewa Minal tana tare da Marshall toh kashinsa ya bushe, motsi yake da lips ɗinsa a hankali ya furta cewa "Uncle ka sanar wa Abbah cewa bada Minal muka zo ba?..." Mai martaba yace "ehh tabbas saboda ban ganta ba.." Zaro ido waje Roshan yayi yana kallon Mai martaba, gaba ɗaya jikinsa yayi la'asar kamar ba jini, sai ji yayi mai martaba yace "Ni ban sanar masa komai ba, yadai gaya mun cewa tareda Minal kuka zo amma ban ce masa bakuzo da ita ba, rashin sanin abinda zan gaya masa ne yasa na katse wayar domin sai naji daga bakin ku tukun na yanke hukunci..." wani irin sauƙe nannauyar numfashi Roshan yayi yana faɗin "thank God, sannan yace Uncle zan sanar maka duk halin da ake ciki..." Mai martaba yace "TOH ina sauraronka..." Nan Roshan ya sanarwa mai martaba halin da ake ciki na Minal da kuma Mohandas.. Dogon numfashi mai martaba yaja sannan yace "TOH banda abinka Roshan meye zaka iya a wannan lamarin? kadai san halin Mahaifinku idan yace baya son abu TOH kuwa duk duniyan nan bamai sashi yayi, sannan kuma shi Mohandas so kake ya bijirewa iyayensa kenam akan mace?..." Roshan idonsa akan mai martaba yace "Uncle ina tausaya musu ne, wallahi suna son junansu kuma shima Mohandas ya amince akan zai musulunta, nasan idan ya karɓi musulunci Abbah bazai hanashi Auren Minal ba..." Murmushi Mai martaba yayi yace "yaro yaro ne, Roshan har yanzu da ƙuruciya akanka, kana nufin kace Abbah zai bawa Mohandas Auren Minal ba tareda iyayensa suna so ba? ko kuma Abbah zai ɗauki yarinya ya bashi ba tareda iyayensa sun sani ba? TOH bari kaji shi Aure ya wuce yanda kake tunani, ina mai sanar maka cewa Mahaifinku bazai taɓa yadda da wannan al'amarin ba sai dai idan har iyayen Yaron suma sun Aminta nan ne za'ayi abu cikin lumana..." Roshan Dafe goshinsa yayi yana hura iskar bakinsa tareda jinjina maganganun mai martaba, Ɗagowa yayi yana faɗin "yanzu ya zamuyi Uncle?..." Mai martaba yace "ku sake shawara dai..." Roshan yace "Uncle inason jin daga bakinka duk yanda kace hakan za'ayi..." Mai martaba yace "sai dai a samu iyayensa ayi magana cikin hankali idan su bazasu musulunta ba to subar yaronsu ya musulunta inyaso sai a Aura masa yarinyar..." Roshan jinjina kai yayi sannan yace "tabbb! Uncle ai gwara tawa shawarar zai iya yuwa, amma nasan iyayen Mohandas yanda suke riƙe da ƙarfin Addininsu bazasu taɓa yadda ba wallahi...." Mai martaba ne ya buɗe baki zaiyi magana yaji wayarsa tana ringing, Dubawa yayi yaga number Abbah ne, Saida ya kalli Roshan tukun yace "shine..." Zaro ido Roshan yayi ya haɗe hannayensa biyu alamar roƙo kar Mai martaba ya gayawa Abbah halinda ake ciki, Mai martaba ne yasa wayar a speaker yanda Roshan zaiji duk tattaunawar da zasuyi... Mai martaba ne yayi sallama tareda faɗin "na gaida mazan pama..." Abbah yace "yadai muna cikin waya ka katse ƙiran?..." Mai martaba yace "wallahi naɗanji hayaniya ne shine naje dubowa meke faruwa..." Abbah yace "okay! yakamata yaran nan su dawo gida yau saboda hidimar bikin da za'ayi yau sauran kwana huɗu..." Mai martaba yace "yau kuma? sai dai gobe su taso da sassafe, saboda har da matan gidan gaba ɗaya zasu tafo..." Abbah yace "TOH shikenam kaifah?..." Mai martaba yace "a'a Ni sai ana gobe ɗaurin Aure zan taho, Amma Roshan shi kaɗai za'a Aurar ne? mezai hana a haɗa da Razhdeen?..." Abbah yace "kabar zancen Razhdeen shi da bai tsayar da kowa ba, ai baza'a Aura masa babu ba..." Mai martaba yace "hakane amma maizai hana a haɗa shi da Ramlat ƙanwar Matata Maamie naga tana sonsa sosai..." Abbah ne yace "shi ɗin yana sonta ne? In har yana sonta sai a haɗa Auren gaba ɗaya, idan kuma Razhdeen baya ra'ayinta TOH gwara Abar maganar nan saboda banason damuwa, kasan halin Razhdeen nima haƙuri nake dashi, kuma ba kowace mace ce zata iya zama dashi ba in har ba sonta yake ba, domin ita zata sha wahala Ni kuma hakan ne banaso..." Mai martaba dogon numfashi yaja tareda faɗin "toh maganar gaskiya dai Hajiya Maamie ce take son haɗin nan amma shi Razhdeen baya so domin jiya ma Saida suka samu matsala har Saida Razhdeen ya mareta a take ta sume a wurin..." Abbah yace "whattt! Ita yarinyar ya mara ?..." Mai martaba yace "a'ah ita kanta Uwar yarinyar, kasan Razhdeen bashida haƙuri kuma baya son raini ita kuma Maamie rashin kunya da wulaƙanci..." Abbah yace "kana nufin kace matarka Razhdeen yasa hannu ya mara?..." Mai martaba yace "No bawai na gaya maka saboda ranka ya ɓaci bane i just tell you that haɗin Auren bazai yu bane tinda ba son yarinyar yake ba..." Abbah numfashi ya sauƙe yana faɗin "ba abun mamaki bane domin Razhdeen zai Aikata, shiyasa banason tura shi baƙunta wani wuri amma zanyi maganin shi, Please King kayi haƙuri Razhdeen Sam bai kyauta ba..." Mai martaba yace "wallahi ko a jikina Yaya, kadai san zaman haƙuri kawai nake da ita, ta zamo mun ƙarfen ƙafa..." Abbah yace "kayi haƙuri idan kuka zo gaba ɗaya za'a san yanda za'ayi..." Mai martaba yace "TOH shikenam ba damuwa, Amma Yaya ita kuma Minal fa ya za'ayi da ita yakamata a Aurar da ita tinda ta kammala karatunta..." Abbah yace "bata da manemi shiyasa..." mai martaba yace "naji tace tanada wanda take so ai..." Abbah yace "Arne take so kuma ko zata mutu bazata Auri jinin Christal ba..." Mai martaba yace "inda zai musulunta sai kawai a Aura mata shi..." Abbah ya kuma cewa "Da nayi tunanin nan amma yanzu na sauya ra'ayina koda ya musulunta ma ƴata bazata Auri jininsu ba, yanda ta fito a cikin Musulunci haka jininta zai cigaba da gudana a cikin Musulunci, banason jikokina su kasance sunada family christoci..." Mai martaba yace "Yaya wannan hukunci yayi......." bai ƙarasa maganar ba yaji Abbah ya katse shi da cewa "nafa gama maganata babu sauyi kuma, idan Roshan yana kusa ka bashi wayar...." Mai martaba babu yanda ya iya haka ya miƙawa Roshan wayar, Roshan hannu na kakkarwa ya karɓa tareda karawa a kunne da sallama a bakinsa, Abbah yace "ina Razhdeen?..." Roshan yace "na barshi a ɗakin kwanan mu..." Abbah yace "kaje ka same shi kace ya taho Nigeria yanzu yanzu inason ganinsa..." Roshan yace "TOH Abbah.." Kafin Abbah ya katse ya kuma cewa "inaso zanyi video call da Minal kaje ka same ta yanzun nan..." Saida ƙirjin Roshan ya buga jin abinda Abbah ya faɗa, A birkice ya tsaya yana kallon screen ɗin wayar, bai ankara ba yaga Abbah ya juyar da ƙiran zuwa video call, sai gwala-gwalan idon Roshan ne suka sauƙa akan Fuskar Abbah dake cikin wayar, nan suka fara kallon juna, Abbah ne ya katse shi da cewa "meye kake kallona haka, kaje ka bata wayar ina kallonka..." Shima mai martaba Saida ya jinjinawa Abbah Sarkin wayo... Roshan tashi yayi ya fara tafiya da haka yabar falon mai martaba ya fice kai tsaye ɗakinsu ya nufa yana zuwa ya buɗe ƙofa ya shige, samun Razhdeen yayi yana zaune a bakin gado ya shirya tsab cikin ƙananun kaya ga yanda ƙamshin turare yake tashi, Roshan yana zuwa ya juyar da wayar saitin fuskar Razhdeen, wani irin kallo ya watsawa Roshan ganin yanda ya saita masa fuskar waya a tunaninsa photo zaiyi masa ne, sai ji yayi daga cikin wayan ance "Minal nace ka haɗani da ita ba wannan mai kama da mutuwa ba fuska ba annuri...." Razhdeen idonsa akan wayar ta ciki yake kallon Abbansu, shima Abbah kallonsa yake, daga bisani Abbah yace "kai kuma Razhdeen inaso yanzu ka dawo gida banason dogon zance..." Kai kawai Razhdeen ya ɗaga masa, Roshan kuwa kasa ɗage wayar yayi daga saitin fuskar Razhdeen hannu sai kakkarwa yake, Abbah ne ya kuma cewa "ina Roshan ya haka ne, nagaji da kallon fuskar Razhdeen haka ka kawar mun da wayar kaje ka haɗani da Minal...." Roshan wayar ya kawo saitin fuskarsa yana kallon Abbah fuska a jagwalgwale kamar zaiyi kuka, Abbah yace "ha'a Roshan zan saɓa maka fa, ina wasa dakai..." A hankali yake jan ƙafa zai fice daga ɗakin kwatsam yaji Abbah yana faɗin "dakata! dakata mun!! Ɗaga mun wayar sama saitin fanka naga abu yana lilo kamar mutum..." Shima Roshan ɗaga kansa sama yayi domin tabbatar da abinda Abbah ke magana akai, Zaro ido yayi baki a sake ganin Ramlat a ɗaure saman fanka kanta na kallon ƙasi, sawaye kuma a ɗaure da fanka, Saida ya nannaɗeta da zanin gado kafin ya ɗaureta sannan ya janye ta sama, iya fuskarta ne a waje, bayan ya gama mata dakun sakwara, ba ƙaramin duka yayi mata ba ganan hancinta yanda yake ɗigo da jini, Dasauri Roshan ya sauƙar da kansa ƙasi yana maida kallonsa kan Razhdeen sai yanzu ya lura da dorinar da yayi kaca-kaca a ɗakin, Ji sukayi Abbah ya fara salati yana faɗin "Innalillahi wa inna'ilaihi raju'un, Razhdeen Koh? Razhdeen Koh? nasan shi yayi mata haka, wayyo Allah ya zanyi da Razhdeen ɗin nan, Kai Roshan miƙawa Razhdeen wayar nan..." Dasauri Roshan yaje ya miƙawa Razhdeen wayar domin yana so Abbah ya manta da batun Minal, Razhdeen karɓa yayi tareda kawar da fuska gefe domin bazai iya fuskantar Abbah a halin yanzu ba, yana jin yanda Abbah yake zaginsa game da cewa "anya kuwa Razhdeen kai mutum ne? Dan ALLAH ka dawo na kai ka bakin ruwa nafi tunanin kai ɗan ruwa ne, Amma Aljanun nan basu kyauta mun ba, kai kaɗai ne suka canza mun kai, ban saniba ko tin kana cikin uwarka suka ɗauke mun Razhdeen ko kuma tin kana jariri, Bakin ruwa dole saina kaika domin bazan barka kaita kashe ƴaƴan mutane ba...." Razhdeen kai a gefe kunne ne kawai yake jiyo maganganun Abbah, Shi kuwa Roshan ya kama kunkumi kansa a sama yanda yake ta kallon Ramlat yana tunanin ta yanda akayi Razhdeen ya ɗaureta haka, kuma alamun a sume take domin ko motsi bata yi kodai mutuwa, haka yake ta wannan tunanin, Abbah yace "Razhdeen na roƙe ka da sunayen Allah ka dawo Nigeria a yanzun nan dan ALLAH, Ina Roshan?..." Roshan ne ya karɓi wayar yana faɗin "gani Abbah..." Abbah yace "kasan yanda zakayi ka since yarinyar nan..." Roshan yace "TOH Abbah..." Daga nan ya katse wayar... Roshan sauƙe numfashi yayi yana faɗin "yanzu ta ina zan fara?..." Razhdeen kuwa ko kallonsa baiyi ba balle ya furta wani abu, suna cikin wannan halin sukaji bugun ƙofa, Roshan ne yayi ƙarfin halin cewa "waye?..." Hajia Maamie ce tace "Ni ce nazo duba Ramlat ne ko tazo nan..." Roshan yace "daman kinsan da zuwanta?..." Hajia Maamie tace "ehh! A'ah!! Eyy!!! A'ahh!!!!! Ehhh tohhh...." Razhdeen ne ya juyo suka haɗa ido da Roshan, fuska a haɗe Razhdeen yace "ki shugo ki ɗauke kayanki..." Saiga Maamie ta shugo baki a washe ta ɗauka cewa sun gama fahimtar juna ne data jita tayi shuru a ɗakin, ta shugo tana faɗin "tana inane? ha'a kodai itace a lulluɓe saman gado, ahhhh Masha Allah tinda bacci take bari na barku karna takura muku Koh....." Har zata fice Roshan yace "ɗaga kanki sama..." Maamie tana ɗagawa ta wani sau ƙara tana dafe da ƙirjinta, ƙafafunta har wani rawa suke, lokaci guda gumi har ya wanke mata fuska...." Sai ga mai martaba shima ya shugo jin ihun MAAMIE yana faɗin "lafiya kuwa meke faruwa?..." Saiga INDO itama domin ihun ya karaɗe ko ina na gidan, Ai kuwa duk suka ɗage kayiwansu sama suna kallon ikon ALLAH,. Mai martaba yace "meye wannan?..." Maamie tana kuka tace "wani irin tambaya ne wannan kana ganin sun kashe mun ƙanwaaaa...." nan ta fashe da matsanancin kuka harda majina, Mai martaba yace "meya kawo ta ɗakin nan TOH?..." Maamie tace "kafin ka gama tambayarka Ni a Ciro mun gawar ta tinda sun kasheta mungwaye kawai azzalumai macuta, Allah ya isana tsakanina daku wallahi...." ta nufi wurin Roshan tana kai masa duka, Shi kuwa sai faman kaucewa yake, ita kuwa sai duka ta ko ina... Mai martaba ne ya rirriƙeta yana faɗin "meye haka kike dukansa shi ba ƙaramin yaro ba, ko ce miki akayi shi yayi mata haka? TOH gashi can kije ki same shi ki dake shi..." ya nuna mata yanda Razhdeen yake, kallonsa tayi taga yanda yake wurga mata wani irin kallo kamar idanun zasu faɗo, tin daga lokacin da ta fara kaiwa Roshan duka yaji kamar ya shaƙota kawai yana ganin mutuncin Mai martaba ne, shi dai yasan in har ya miƙe daga zaune to saiya ɗage mata numfashi ne, kafin a ankara aka nemi Maamie aka rasa harta fice da gudu tana kuka... Girgiza kai mai martaba yayi yana faɗin "kaga Roshan kayi haƙuri dan ALLAH, yanzu ya za'ayi mu Ciro ta..." Roshan ya kalli Razhdeen sannan yace "my man ka temaka ka Ciro ta..." Miƙewa Razhdeen yayi ya nufi yanda Akwatinsa yake tareda faɗin "Impossible..." ya ɗauko Akwati yana ja zai fice mai martaba yace "ina kuma zaka je?..." Tsayawa yayi yace "Abbah yana son ganina right now sannan idan na ƙara kwana ɗaya a ƙasar nan wancan matar saina hallakata..." Mai martaba yace "a'a! ALLAH ya huci zuciyarka Major General Razhdeen Allah ya kiyaye hanya ya tsare rayuwarka..." Razhdeen amsa masa yayi da Amiin sannan ya fice... Shima Roshan bin bayansa yayi zai rakashi can airport da motar gidan... Mai martaba tsayawa yayi ya rasa yanda zai yi duk sun tafi sun barshi, Saida yasa aka ƙira ma'aikatan mazan gidan kafin suka zo suka Cirota daƙer.... Roshan bai tashi dawowa ba saida yaga jirgin Razhdeen ya tashi kafin shima ya dawo masarautar, Razhdeen an koma Nigeria..... *POSTING DAYS* *SUNDAY* *TUESDAY* *THURSDAY* *FRIDAY* *A SATI SAU HUƊU ZA'ANA POSTING* *GA RANAKUN YIN POSTING...* *ALLAH YA BANI IKON BIN TSARIN YANDA YA KAMATA* *SANNAN A DAGE DA COMMENTS DOMIN SHI ZAISA A RINƘA YAWAN MUKU POSTING....* asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) STEP TWO 7 to 8 Bayan Razhdeen ya sauƙa a airport already akwai sojojin da suka zo ɗaukarsa, Saida yasa suka miƙi hanyar mabarata yanda zai ga Ƴar Amana, cikin rashin Sa'a ya zuba ido yaga babu alamar ta sai tarin tsofin da suke zazzaune a wurin, Razhdeen yana zaune a back seat eyes ɗinsa kawai yake ta wurgawa, cije lips ɗinsa yayi sannan yayi magana ciki-ciki yace "let's go..." Jan motar driver yayi suka miƙi hanya, haka sauran motar ma suka bi bayan motar su Razhdeen, mabaratan ganin motocin sojoji ne yasa babu wacce tayi motsin tashi balle suzo yin Bara, sai gani sukayi wani soja ya dirƙo daga kan mota ya nufi yanda suke fuska ba annuri ga bindiga a rataye a kafaɗa, ko wacce jikinta ne ya fara kakkarwa ganin sojan yayo kansu, tsayawa yayi ya zuge jakar hannunsa sannan ya Ciro wasu maƙudan kuɗaɗe duk ya rarraba musu, lokaci guda suka fara washe hakwara sai faman zabga masa godiya suke tare da Addu'o'i, ko amsa musu baiyi ba ya juya yaje ya shiga cikin motar daya rage iya shi kaɗai ne a wurin, yana shiga kamar walƙiya suka bar wurin, daman Razhdeen ne yasa a raba musu ta hanyar tura musu saƙo ta waya.... Isar su keda wuya duk falon an hallaru ana jiran shugowar Uncle Deen, Ummy gaba ɗaya ta kasa zama tsabar farin ciki da zumuɗin ganin Uncle Deen, tayi matuƙar farin ciki sosai da Abbah ya dawo dashi cikin Ahali da temakon Aunty Yolash wacce take zaune itama a two seater sai faman pressing phone ɗinta take, Pinky da Rukky suma suna zaune a five seater Rukky ce take kwance kanta a saman cinyar Pinky tana ɗan lumshe ido kamar mai jin bacci, a yayinda Pinky take ta danna wayar hannunta alamar charting take, duk abubuwan da ke faruwa a gidan tana sanarwa mommy wato Hajia Kilishi, yanzu ma charting take da ita... Baiwar ALLAH kuma tana can cikin ɗakinta a kwance saman katafaren gadonta kamar mai yin Bacci, sai dai ba baccin take ba, amma idonta a lumshe suke, Ga wata ƙatuwar waya ƙiran iPhone 15S, ƙira ake tayi ba ƙaƙƙautawa daga wannan ƙiran ya yanke sai wani ƙiran ya sake shugowa anyi ƙiran yafi sau 15 a lokaci guda kuma duk mutum ɗaya ne mai wannan ƙiran, Baiwar ALLAH tana ji amma taƙi ɗaukar ƙiran domin ta rigada tasan cewar Roshan ne mai wannan damun, wani ƙiran ne ya sake shugowa Once takai ƙwayar eyes ɗinta kan screen ɗin wayar ganin ROSH a rubuce kan screen yasa taja dogon tsuka tareda tashi zaune tana hararar wayar cikin ɓacin rai ta soma magana tana faɗin "Mttssww! aikin banza wai dan saboda kai ka sayi wayar shine zaka takura Ni? I hate dis nonsense wallahi, banason mutum mai nacin tsiya, takurawarka ne yasa nake ƙara tsanarka wallahi Roshan....." a fizge tasa hannu ta ɗauki wayar ganin bazai daina ƙiran ba, ɗaukar ƙiran tayi ta kara a kunne tayi shuru tana hararar gefe, magana yake ta cikin wayar yana ambaton sunanta "Ammata! Hello Ammata!! Assalamu alaikum bakya jina ne? Ammata nah Dan ALLAH kiyi magana mana...." ɗan tsuka tayi acan ƙasin harshenta tace "wai dan ALLAH meyasa kake son takura mun ne? ko dan saboda kai ka ban wayar shine zaka rinƙa takura mun, Ni gaskiya bana son irin haka..." ta ƙarisa maganar tareda tura ɗan lips ɗinta kamar wacce take gabansa, daga ɓangarensa sauƙe nannauyar ajiyar zuciya yayi murya ciki-ciki yace "oh my God, Ammata banida burin daya wuce na rinƙa ganin farin cikin ki akoda yaushe, inasonki wallahi l, ina ƙaunarki har cikin zuciyata, tinda Allah yasa nabar Nigeria ban ji muryarki ba sai yau, ina kan ƙiranki amma bakya ɗauka mun ƙira why?..." buɗar baki tayi zatayi magana saiga ƴaR tinny ta kutso kai da gudu tare da faɗin "Aunty Dota Ankuy Deen ya dawo..." tana iddasa maganar ta juya ta fice, Ita kuwa Baiwar ALLAH ido ta zazzaro waje cike da mamaki take bin bakin ƙofar da kallo, lokaci guda wani irin farin ciki ne ya wanzu mata, Roshan yanata magana amma shuru ko jinsa bata yi, bata san lokacin da tayi wurgi da wayar ba ta miƙe tare da sauƙar da ƙafarta ƙasin carpet da gudu tayi hanyar bakin ƙofa itama, zata je taga abinda idanuwanta suka daɗe suna muradin gani, Da gudun gaske ta faɗa Falo, lokaci guda ta danna burki ganin kowa ya hallaru, duk juyowa sukayi suna kallonta ganin kamar wacce aka hankaɗota, itama tsayawa tayi tana binsu da kallo, idanunta ne suka sauƙa akan kayan lefen da aka bazasu a tsakiyar Falo, wasu irin tsararrun akwatina ne guda sha biyu pink colours, ga kayan cikin su kansu basu san adadin kayan lefen ba tsabar yawansu, ga takalma kala-kala kamar wanda za'a buɗe shagon kayayyaki, kayan bacci suma sunfi hamsin, kayan makeup ba'a magana, gyalulluka da hijabai abun ba'a cewa komai, komai da komai akwai su, ganin kayayyakin yasa gabanta yanke wa domin tasan duk nata ne, a hankali ta ɗago da shanyayyun idanuwanta ta sauƙe su akan Razhdeen wanda shima yana zaune a kujerar da yake facing ɗinta, idonsa akan wayarsa yanata pressing, jikinsa ne ya bashi cewa ana kallonsa, kamar bazai ɗago ba shima a hankali ya ɗago da kansa tare da wurga ƙwayar eyes ɗinsa kan Baiwar ALLAH wacce take tsaye ta ƙura masa ido ko ƙibtawa babu, shima kallonta ya shiga yi duk suka fara kallon juna, abinda ya fara tunawa shine wankan da yayi mata da kasancewar da sukayi a ɗaki ɗaya..." Itama dogon tunani ta faɗa abinda take tunowa shine lokacin da tayi ciwon ciki a ɗakinsa da kula da ita da yayi, har wankan da yayi mata, Kowa da abinda yake tunawa acikin ransa... Ƴar tinny ce tayo kan Razhdeen tare da faɗawa saman cinyarsa tana faɗin "Ankui Deen wai yauce Mommy nah jata dawo ne?..." hankalinsa ne ya karkato kan Ƴar tinny murya ciki-ciki yace "Mamana kiyi haƙuri zata dawo coming soon kinji Koh..." tace "Ni a dawo mun da ita, kullum idan nace Abbah ya dawo da ita sai yace zai dake Ni ...". kamar zata fashe da kuka ta ƙarasa maganar cikin lankwasa murya... Shima kansa ta bashi tausayi shafar sumar kanta kawai yayi, Abbah kallon Baiwar ALLAH yayi yace "Dota ya kike tsaye ne, ki ƙaraso mana..." haka take jan ƙafa ta ƙaraso cikin falon ta zauna itama a cikin ɗaya daga jerukan kujerun, Aunty Yolash murmushi tasau tana kallon Baiwar ALLAH tace "Ammatan Roshan an kusan zama Amarya, duk wannan kayayyakin kine, saboda haka ki kwantar da hankalinki Roshan shine mijin da yafi dacewa da rayuwarki, mutum ne mai kyakkyawar zuciya, kuma yana matuƙar ƙaunarki tinda kullum sai ya ƙirani ya bani labarinki, kinsan Roshan in har yana son abu toh haukacewa yake, don haka ki riƙe mana ɗan Amanar mu hannu bibbiyu, idan muka ganshi cikin ƙunci to kece sila, haka kuma idan muka ganshi cikin walwala da farin ciki nan ma kece sila, Ƴar Amana da Ɗan Amana ku kula mana da kan ku dan ALLAH, yanzu dai sauran mana kwana uku ɗaurin Aure, Insha ALLAHU daga gobe zamu fara ganin manya-manyan baƙi daga ƙasashen waje da garurruwa, sannan ƴan uwan mahaifiyarsu daga Saudiyya suma suna nan tafe...." Baiwar ALLAH hawaye ne kawai yake faman gangaro mata, abu biyu ne suka tada mata da hankali na farko bata son Auren nan sannan kuma taji an ambaci sunan Ƴar Amana, sai kawai taji zuciyarta na bugun uku-uku, maganar zuci ta shiga yi tana faɗin "yanzu a wani hali kike ciki Ƴar uwata, shin kin mutu ne ko kina raye? a cikin haske kike ko a cikin duhu? wayyo Allah Ƴar Amana ina kewarki...." bata san lokacin da kuka ya kuɓuto mata ba, kuka take na gaske kanta na kallon ƙasi... Aunty Yolash tana cikin jawabi taji ƙarar kukan Baiwar ALLAH nan ta dakata da maganar tana kallonta, Shima Abbah hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba, murya a harharɗe yake faɗin "lafiya kuwa Dota? meya sameki kike kukan? shin bakya son Auren ne? ki gaya mun dan ALLAH yanzu a dakatar..." kowa ya kasa kunne yana son jin abinda Baiwar ALLAH zata ce, Aunty Yolash ce itama ta tashi ta nufi wurin da take zaune ta zauna tare da rungimarta tace "Dota kiyi haƙuri ki sanar mana abinda yake ranki, Bama son muyi miki dole domin ke ɗin Amana ce a gare mu, shin bakya son Auren ne?..." Razhdeen idonsa a kanta ya rasa gane meye dalilin kukanta, Ummy tana zaune kai a ƙasi ƙirjinta na bugun uku-uku tana addu'ar kar Baiwar ALLAH tace bata son Auren, domin Roshan zai iya shiga mungun mawuyancin hali, tsoronta kar ciwon zuciyarsa ta tashi..." Rukky tana kwance kan cinyar Pinky domin ba lafiya ne gareta ba tana fama da zazzaɓi, murya na kakkarwa alamar jin sanyi tace "Aunty daman fah idan Amarya anayi mata nasiha kuka take, kowace Amarya ma hakane..." Aunty Yolash tace "a'ah muna son jin daga bakinta ne domin bamu san abinda ke ranta ba, kar mu toye mata hakki..." Pinky ɗan tsuka taja tare da kawar da fuska gefe daman ita sam bata ƙaunar Auren nan domin a duniyar nan babu mace data fi tsana kamar Baiwar ALLAH, a cewar ta ita tayi sanadiyar rabasu da mahaifiyarsu..." Aunty Yolash ce ta ƙara tambayarta cewar "Dota bakya son Auren ne?..." Girgiza kai Baiwar ALLAH tayi alamar a'ah... Aunty Yolash tace "to meyasa kike kuka?..." Baiwar ALLAH tace "babu komai kawai lokaci guda naji kukan ban san meyasa ba...." Aunty Yolash tace "Ayyah sorry Dota saboda zaki kasance cikin Amarci ne shiyasa, kuma son samu ace iyayenki suma suga ranar Auren ki...." kafin Aunty Yolash ta ƙarasa maganar taji Baiwar ALLAH ta ƙara fashewa da wani sabon kukan, rungumarta tayi tana rarrashinta daƙyar ta iya dakatar da kukan..." Saida Abbah yayi mata nasiha sosai mai ratsa jiki, ya rarrasheta kafin nan zuciyarta tayi sanyi, Saida suka kammala tattaunawarsu tsab akan batun Auren kafin nan Abbah ya dawo kan Razhdeen, ya kalle shi sannan yace Razhdeen!.." Uncle Deen kallon Abbah yayi jin ya ambaci sunansa, shi gaba ɗaya hankalinsa akan Ƴar Amana yake, tunaninta kawai yake sai fuskarta yana masa gizo... Abbah ya cigaba da cewa "Yakamata duk wannan shirmen da kake ka dena shi Razhdeen, faɗan da nake maka bawai bana sonka bane, bazan taɓa iya cire hannuna daga kanka ba Razhdeen, miskilancinka yayi yawa ka rage koda bazaka iya cire wa gaba ɗaya ba, girman kanka yayi yawa komai naka yayi yawa haba Razhdeen, wani irin zuciya ne Allah yayi maka, acikin sojojin duniya gaba ɗaya da wuya a samu mai kalar ɗabi'unka na rashin jin magana, amma duk da haka ina mai ƙara godewa Allah yasa kai ba manemin mata bane sannan kai bame shaye-shaye bane, kai ba ɓarawo bane, duk waɗannan Bad behavior zan shaidi ƴaƴana babu maiyinsu, sai rashin jin magana, Please Major General Razhdeen be careful about all the things that is make me unhappiness..." Razhdeen idonsa akan carpet ko ɗago da kai baiyi ba, motsi ya fara yi da lips ɗinsa a hankali yake furta "sorry Dad I'll try to make you happy but my behavior's can never change..." Aunty Yolash kawar da kai gefe tayi tana dariya ciki-ciki domin Razhdeen ba ƙaramin dariya ya bata ba, daɗinta dashi baya ɓoye maitarsa, koda mutum bazaiji daɗi ba to dole saiya gaya masa abinda ke ransa, baya tsoro kuma baya fargaban abinda zaije ya dawo..." Abbah cikin kalar tausayi yace "why Razhdeen?..." Yace "because I don't have a Bad character's, kawai raini ne bana so sannan banason wulaƙanci da rashin tarbiyya, har yanzu baku fahimci yanda tsarin rayuwata take ba, inada zuciyar da bazan iya ɗaukar duk wani shirme ba, lokaci guda zan ɗauki hukunci akan mutum shiyasa kuke ganin rashin haƙuri na..." Abbah yace "TOH shi Roshan daka ɗauki hukunci akansa fa? shi da ya gama fahimtar halinka kuma yake kiyaye ɓacin ranka..." Razhdeen kallon Abbah yayi sannan yace "why tin lokacin baku tambayeni laifin da yayi mun ba sai yanzu? Dad you known banason yawan magana sosai, my headache..." Abbah yace "it's okay nasan Kanada matsalar nan, abinda ya wuce ya rigada ya wuce sai dai bama fatan hakan ya sake faruwa, kayi haƙuri da wannan ciwon kan nakan magana nakeso nayi dakai, dole yau zaka ɗan motsa yin magana kafin kaje kaɗan huta Koh..." haɗe gira yayi tare da faɗin "okay let me go and sleep before..." ya ƙarasa maganar yana ƙoƙarin miƙewa. Abbah yayi saurin dakatar dashi yana faɗin "Noooo ka saurara kaji kalar tattaunawar da zamuyi mana..." zama yayi ya kasa kunne yana sauraron Abbah, Baiwar ALLAH haka kawai sai satar kallon Razhdeen take tayi... Abbah ya cigaba da cewa "naji mai martaba ya fara mun wata magana ne dangane da ƙanwar matarsa Maamie, akan cewa za'a haɗa Auren ka dana Roshan itace wacce zaka Aura..." Dasauri Razhdeen ya ɗago yana kallon Abbah fuska a murtuƙe babu alamun Annuri a fuskar, Aunty Yolash itama da sauri ta furta "whattttt!..." Yaran gidan kuwa gaba ɗaya haɗa baki sukayi wurin cewa "Ramlatttt!..." Baiwar ALLAH kuwa kanta ne yayi wani irin sarawa da ƙarfin gaske kamar wanda aka doka mata Gatari, dasauri ta sunkuyar da kanta ƙasi tana dafe dashi.... Aunty Yolash tace "wai Yaya kana nufin kace Ramlah ƙanwar MAAMIE? Impossible wallahi, kaima kasan cewa Hajia Maamie ta shure Hajia Kilishi matarka wulaƙanci da rashin mutunci Koh? shin baka san cewa Hajia Maamie ita take iko da mai martaba ba koh? toh idan baka saniba yau zan sanar maka, duk abinda hajia Maamie tace ayi a masarautar nan shi akeyi idan tace bata son abu TOH kuwa mai martaba bai iya yayi ba, itace hakima mai mulkar masarautar...." Abbah yace "ehh king ya sanar mun amma nace ya bari sai sunzo zamu tattauna akan batun tinda duk zasu zo Auren nan, amma ita yarinyar batada matsala ai koh?..." Aunty Yolash tace "hakane amma kuma tana ɗaukar zugar Yayarta Hajia Maamie, nipah gaskiya Yaya bazaiyu a rinƙa tara mana mata marasa tarbiyya a gida ba, Hajia Kilishi ma ya muka ƙare da ita kuma du a ƙara kawo mana wata, itama Hajia Maamie za'a ɗau hukunci akanta ai....." wani irin harara Pinky ta wurga wa Aunty Yolash dai-dain lokacin da suka haɗa ido da Aunty Yolash, Aunty Yolash ce ta ɗauki pillow ta wurga mata tare da faɗin "kin ci ubanki Balkisu! Ni sa'arki ce ko kuma ina wasa dake? aikin banza kawai shin ƙarya nayi ne Uwarki tayi abun arziƙine a gidan nan ? tin kafin a haife ku ake shan gwagwarmaya da ita, gaskiya kuma dole a faɗe ta..." murguɗa baki pinky tayi tana gunaguni tace "Uwata bata gidan ma amma baza'a barta tasha iska ba..." Aunty Yolash tace "ita data sha iska kuwa har abada domin ko mutuwa tayi dole a faɗi halayarta na Arziƙi ko akasin haka, ke nifa ba abokiyar yinki bane, Uwarki ce sa'ar yina domin ko Auntynki Minal bata isheni kallo ba tinda a gabana duk aka haife ku..." ƙara wurga mata harara Pinky tayi tare da murguɗa baki tace "to kiyi dani ɗin mana..." dasauri Rukky ta tashi daga cinyarta tana Binta da kallo cike da mamakin yanda Pinky ta tsaya tana yiwa Aunty Yolash ƙanwar Abbansu rashin kunya, Pinky bata ankara ba taji Abbah ya zabga mata mari tare da jefota ƙasin carpet yana cankinta, Abbah cikin zafin rai yake tattaka ta yana faɗin "ƴar uwar tawan kike wa rashin kunya dan ubanki, itama mahaifiya ce a wurinku, ashe rashin tarbiyar takun har takai haka?..." Abbah har numfashinsa ne yake shirin ɗagewa tsabar ɓacin rai dake yanada hawan jini, Aunty Yolash ce ta tashi tana rirriƙe shi tare da bashi haƙuri tana rarrashinsa, Pinky tana kwance ba abinda take sai kuka, ji nayi an ɗagota da hannu ɗaya ana janta suka nufi hanyar bakin ƙofa za'a fita da ita, idanuwanta ta buɗe tana ƙoƙarin ganin wanda yake shirin fita da ita, naga Razhdeen ne fuska ba annuri, daga nan ta saddaƙar cewa yau ranar mutuwarta ne, Ihu ta fara kurmawa tana ƙiran sunan Mommy, "wayyo Allah nah Mommy kizo ki temake Ni zasu kashe Ni, Mommy nah wayyo, Dan ALLAH Uncle Deen kayi haƙuri ka ƙyaleni, wallahi bazan ƙara baaa...." Abbah kuwa cewa yake "kaje ka hukuntata tinda itama halin uwarta gareta, ba'a gidan nan za'a mun wannan iskanci ba..." *ƳAR AMANA*🕊️🕊️🕊️ wani makeken ɗaki ne wanda yake zagaye da wantalelen carpet babu kujera ko ɗaya a ɗakin, fili ne kawai, ga wasu ƴan mata guda 50 duk suna zazzaune a filin ɗakin sun jeru hannayensu a ɗaure ta baya, ƙafafu ma a ɗaure, kana ganin kasan sato su akayi, aciki kuwa harda ƴar Amana itama anyi mata ɗaurin da akayi wa sauran... ɗakin duhu ƙirin baka iya ganin abinda ke ciki dake ƙofar a ƙarƙame yake, sai wani ɗan ƙaramin window wanda iska zai rinƙa shiga kaɗan-kaɗan, wannan lokacin kuwa window ma an rufe babu mashigar iska, duk matan nan babu wacce bata rigirta ba, numfashi sama-sama haka suke shaƙa, wata a ciki kuwa har ta mutu tana zaune kai a durƙushe wuya ya rigada ya karye, amma babu wanda yasan ta mutu... suna cikin wannan halin suka ji motsin mutum yana ƙoƙarin buɗe ƙofa, a hanzarce duk suka ɗaɗɗago suna bin bakin ƙofar da kallo duk da duhu ne wurin basa iya ganin ƙofar ma, wani irin farin ciki ne ya bayyano musu domin suna muradin shaƙar iskar waje... Buɗe ƙofa akayi sai ga haske ya haskaka wantalelen ɗakin, wani irin iska ne yake ratsa su, ko wacce sai buɗe kafar hanci take tana shaƙar iska mai daɗin gaske, Wani gabjejen mutumi ne ya shugo yana huci yayo kansu ya canko wasu ƴan mata biyu da hannu ɗaɗɗaya yayi waje dasu, duk na cikin kuwa kuka suka fara yi suna faɗin "wayyo mun shiga uku, yau ne ranar da za'a kashe mu..." sai ga wasu mazan suma sun shugo, haka aka rinƙa fita dasu waje, duk aka jejjera su a waje, ga wurin kurmin daji ne babu mutane a dajin sai su, anan suke aikata miyagun ayyukan su, kuma anan suke ƙirƙiran ƙwayoyin maye, anan ake sato ƴan mata a kawo su, wasu a fitar dasu ƙasar waje aje a sayar dasu, wasu kuma yankasu ake acire wasu abubuwa ajikin mace ta hanyar nan suke samun maƙudan kuɗaɗe, suna zazzaune ga wasu manya-manyan zabga-zabgan maza suna tsaye a kansu, saiga wata ƙatuwar motar baƙa ƙirin har wani sheƙi take, mai taya ta bayan mota, baka iya ganin wanda yake cikin motar, can ba jumawa sai ga wanda yake cikin motar ya buɗe murfin motar a hankali ya fara sauƙar da ƙafarsa ta hagun daga baya ya fito gaba ɗaya, wani mutumi ne ɗan dattijo dashi, yana sanye da baƙin glass ga gemu ya ɗan sauƙo, mutumin baƙi ne yana sanye da manyan kaya water fruit, zuwa yayi ya tsaya a gaban ƴan matan yana wani irin lanƙwasa yana binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, cikin dirarren murya yace "wayyo ga ƴan mata zuƙa-zuƙa amma dole na ganku na ƙyale ku saboda banida abun more rayuwa kashhhhhh!!!..." Yarinyar data rabani da dukiyata inda zan ganta a yau wallahi babu abinda zaisa na yankata a yau..." ya ƙarasa maganar yana bugar ƙafarsa da ƙasa tsabar takaici.... Duk tsaya kallonsa suka tsaya yi, wani daga cikin yaransa ne yace "Ogah ɗaya daga cikinsu ta sheƙa pah..." Yallaɓai yace "ina gawarta..." cikin ƙanƙanin lokaci suka ɗaukota, yace "okay kuje ku cire abinda ake buƙata ajikinta saiku bisineta...." hakan kuwa akayi... saiji sukayi yace "kai ina yarinyar dana ce ku nemo mun ita a duk inda take a doron ƙasa ?...." yayi maganar a ɗaya daga cikin yaransa, wani ne yazo yanda Ƴar Amana take zaune yasa hannu ya janyo ta har gaban Yallaɓai... Ƴar Amana tin lokacin data gashi taji gabanta yanata faman yankewa domin tasan mutumin asalin mungune bashida imani, Yallaɓai kallon ƴar Amana yayi tare da tintsirewa da wata mahaukaciyar dariya harda tafa hannayensa, yana faɗin "shegiyar yarinya ashe tana wurin tana jin ina cikiyarta tayi luƙusss,..." ya durƙusa a gabanta tareda kamo sumar gashinta ya kuma cewa "yau gaki a fadata, nine Sarkin wannan yankin, a wancan lokacin nasa an kamo ki a gidan marayu kin kuɓuce kin gudu, TOH yau kam babu ƙafar guduwa idan kuma kikace zaki ƙara tsere mun wallahi tallahi saina yanke miki ƙafafu Kinga kuwa ke kurmiya sannan gurguwa, shin ina ƴar Uwarki Baiwar ALLAH? tana ina? Hhhhh naji cewar tana gidan General koh? akwai tsaro sosai a gidan shiyasa banyi gigin zuwa yanda take ba, ke da ita kunyi bankwana har abada daga nan sai ƙiyamar da ba dawowa...." Ƴar Amana sunkuyar da kai tayi ƙasi ko ɗagowa tayi ta kalleshi bata yi ba... hannu yasa ya ƙara ɗago ta kanta suna kallon juna yace "munafuka ko irin hawayen nan bata yi, ke wai jaruma ko? to yau zan nuna miki tsoro a cikin idanuwanki..." ya miƙe tare da ja da baya yana faɗin "duk ku Aske musu sumar kansu domin waɗannan babu wacce za'a sayar da ita da ranta, idan aka musu yankan rago zasu fi Albarka, yau za'a yanka mutum biyu gobe ma mutum biyu da haka har su ƙare, kullum mutum bibbiyu, da zarar sun ƙare sai a ƙara sato wasu ƴan matan kuma du, bamason talauci ya wanzu mana, indai akan kuɗi ne zamuyi abinda yafi haka..." Duk matan wurin babu wacce bata tsorita ba, wata a ciki tana kuka tace "Allah sarki Babana da Mamana basu taɓa haihuwa ba sai a kaina kuma ni ɗaya ce tilo, bayan Ni Allah bai ƙara basu haihuwa ba, gashi yau Nima zasu rasani, a hanyar zuwa makaranta aka sace Niii...." ta face da matsanancin kuka mai cin rai.... Wata ma ta amsa da cewa "Ni ƴar talakawa ce Babana makaho ne Ni da Mamana muke buga-buga muciyar da kanmu, Ni a wurin tallah suka sato Ni..." itama ta fashe da kuka... Wata ma tana kuka tace "Ni marainiya ce a wurin Kakata nake zaune iyayena sunyi hatsarin mota duk sun rasu, ina kan hanyar dawowa da islamiyya saiga baƙar mota ta tsaya a gabana suka ɗauke Ni ....." Haka ko wacce take gabatar da kanta wa junansu da yanda akayi aka sato ta, aka zo kan Ƴar Amana bata ce komai ba ita, sai wata ce tace "wannan kamar kurmiya ce Allah sarki, ko wacce da kwanakin ranar da zata mutu..." Duk Yallaɓai yasa aka Aske musu gashin kansu anyi musu tanƙwal, kayuwa sai sheƙi suke, Sai a wannan lokacin Ƴar Amana ta fara tsiyayar da hawaye ganin yanda akasa Aska ana yanke mata zara-zaran sumar gashin kanta, ganin yanda sumar gashinta yake zubowa ƙasi yasa ta yanki jiki ta faɗi sumammiya, duk da haka ba'a dena ba saida aka yanke gashin gaba ɗaya kayin yayi tal kamar madubi... Ko wacce haka akayi mata domin daman in zasuyi yanka sai anyi wa mutum Aski, Sannan aka zo duk wacce take wurin Saida aka manna mata wani kalanda mai danko ajikin kalandar an rubuta ranar da za'a yanka ka da lokaci, Ita Ƴar Amana an manna mata ranar Jumma'at ranar 15 ga watan August next week kenam da misalin ƙarfe 7 na safe itada wacce tace ita kaɗai iyayenta suka haifa... Domin akowace rana za'a yanka mutum biyu ne, Idan aka yanka abubuwan da ake buƙata sune kamar Nonuwa, ƙwayar idanun, harshe, sai kuma farjin mace, Duk suna zaune aka kamo waɗanda aka manna musu cewa yau za'a yanka su, duk matan ihu suka fara yi suna kururuwa ganin an janye wasu ƴan uwansu guda biyu, shigar dasu akayi cikin wani ɗaki a ɗan gefe da dajin, shi kuwa Yallaɓai zama yayi domin shine ogansu shine maisa ayi, hango Ƴar Amana yayi tana kwance har zuwa yanzu bata farfaɗo ba, murmushin mugunta yayi tare da kawar da fuskarsa gefe, Can wasu ɗan lokuta sai ga masu yanka sun fito hannayensu riƙe da wuƙaƙe duk jini, ɗaya yana riƙe da ƙaton faranti yanda aka ɗoɗɗora kayan amfanin ƴa mace, har dana wacce ta mutu a ɗakin zuwa sukayi suka ajiye a gaban Yallaɓai wanda fuskar yake murtuƙe babu kyan gani, Ciro wayarsa yayi ya danna ƙiran wani daga ƙasar waje yana faɗin "Hello David akwai kayayyakin mata uku sun hallaru, zaku iya turo mun da kuɗin ta Acc, a yau zan tura yarana biyu su kai muku, kuma gobe ma haka daga yau har kullum, daman mata hamsin ne kafin a nemo wasu..." daga other side suka tambaya cewa "nawa ne zamu baka?..." Yallaɓai yace "mun gama magana ai! mace ɗaya a 20millions take kaga kuwa mata uku 60millions kenam..." other side "ok don't worry we'll send you right now, but we need the things Early morning..." Yallaɓai yace "ai cikin dare zasu tafi..." Da haka suka katse, Sannan ya bada umarnin gangan jikin mata biyun a bisine su tinda an ciri abinda ake buƙata already an bisine ɗayar, sannan ya kuma cewa a maida sauran matan cikin ɗakin duhu zuwa gobe kuma du... Hakan kuwa akayi....... Innalillahi wa inna'ilaihi raju'un Rayuwa kenam! Allah ka kawo wa waɗan nan matan ɗauki, ka cecesu🙏🙏 Waɗanda suka tafi kuma Allah ya jiƙansu ..... asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) STEP TWO 9 to 10 Washe gari ranar Thursday manya-manyan baƙi ne suke ta sauƙa a gidan General, dake ranar Friday ne ɗaurin Aure, Roshan da mai martaba tare da iyalansa gaba ɗaya duk sun iso, ƴan uwan mahaifiyarsu Razhdeen da Roshan kusan su Ashirin duk sun zo daga Saudiyya, ga family su Abbah wasu daga ƙasar Egyph wasu kuma London wasu daga Ethiopia banda waɗanda suka zo daga garuruwa Kano, Bauchi, Kaduna, pataskum jahar Yobe dadai sauran garuruwa, Gidan General baƙi ne tam a gidan, tsabar girman gidan an raina yawan mutanen da sukazo domin gidan duk ya cinye su dan ma wasu da yawa basu zo ba, Razhdeen ganin yanda ake ta baƙi yasa ya koma can gidansa yanda Mohandas yake, ita kuma Minal Roshan ne yabi ta gidan ya ɗauketa suka dawo gida, Baiwar ALLAH gaba ɗaya a takure take ganin yanda ake ta zuwa ganin Amarya, tin daga yau aketa faman shishshiryata dake yau da daddare akwai dinner hall da za'a taru ayi, Roshan tin dawowarsa yake ɗaukin ganin fuskar Baiwar ALLAH amma ya kasa ganinta, taƙi fitowa daga room ɗinta, ga kuma yanda mata suke shiga cikin ɗakin, babu halin ya shiga ciki, ya ƙirata a waya sau ba adadi amma taƙi yin picking balle ta ɗan fito ya ganta.. Daƙer ya samu ganin Ummy dake itama rawar kanta ya ƙaru sai gigiwa aketa yi anata shiri kamar wanda zasu fita ƙasar waje, a waya ya sanar mata cewa tazo swimming pool ta same shi, tayi mamakin jin haka sosai ganin yanda aketa shirin tafiya hall amma shi yana gida, amsa ɗaya ta bashi cewa gata nan zuwa... zuwa tayi ta same shi a swimming pool yana zaune akan kujerar wajen ya kifar da kansa akan table, Dafa kafaɗarsa tayi tare da faɗin "Yaya Roshan lafiya kuwa, meya faru dakai?..." Ɗagowa yayi yana kallonta da shanyayyun idanuwansa alamunsa sun nuna yana cikin damuwa sosai, murya a sanyaye yace "zauna.." zama tayi tana fuskantarsa, ba ƙaramin kyau tayi ba, tasha makeUp matuƙa tana sanye da Shadda-Less doguwar riga wanda har ƙasi yake ja, ga wani irin takalmi mai tudu sai ya ƙara mata tsayi sosai gata daman Ummy da ɗan tsayinta... riƙo hannunsa tayi sannan tace "Yaya Roshan Please tell me what's wrong with you? gaba ɗaya ka chanza kamar ba Ango ba, kasan akwai Dinner amma har yanzu baka shirya ba why? ga can abokanka sunata nemanka amma basu sameka ba, kasan kuma akwai abokananka waɗanda suka zo daga Egyph da U.K and U.S but kazo nan ka ɓuya..." Dogon numfashi yaja sannan yace "Ummy akwai matsala..." tace "wani irin matsala Yaya Roshan?.." ya kuma cewa "Ammata kamar bata sona, naga gaba ɗaya ta sauya mun, hatta kalamanta sun sauya, bansan meke damunta ba..." Ummy tace "Yaya Roshan haka zaka cigaba da haƙuri da ita har a ɗaura Auren domin yanzu kowa ma haƙuri yake da ita, bawai kai ɗaya ba, koda jiya ma Saida Abbah da Aunty Yolash suka tambayeta matsalarta kodai bata son Auren ne tace a'a, amma nafi tunanin ko tunanin iyayenta take shiyasa kasan baza taji daɗi ba ace ana Aurenta amma dangin mahaifinta ko mahaifiyarta babu wanda ya halarci wurin, babu ƴan uwanta ko ɗaya kaga dole zata shiga damuwa matuƙa, ina tunanin wannan ne matsalarta gaskiya...." Sai yanzu Roshan yasau ƙayataccen murmushi har saida kyawawan dimple ɗinsa suka lotse yace "tabbas na gamsu da jawabanki My love, wannan shine matsalar sai yanzu nayi tunanin nan..." Ummy tace "Hmmmmmmmmmm TOH yanzu zaka iya tashi kaje ka shirya?..." Yace "TOH yanzun ba yanda za'ayi na ganta ko sau ɗaya ne? kinsan tinda na iso ban ganta ba nayi missing ɗinta over..." yamutsa fuska Ummy tayi tare da faɗin "ku haɗu a wurin dinner, kasan dai yanzu Aunty Dota bazata iya ratsa mutane tazo nan ba koh?..." Yace "okay shikenam mu haɗu a can..." dariya tayi tareda barin wurin dasauri, Bayan isar ta cikin babban Falo ta tarar da wani babban tashin hankali, duk mutanen wurin sun taru a falo suna ganin ikon ALLAH, Hajiya Kilishi ce tazo itama wurin hidimar tana durƙushe da gwiwowinta akan carpet ɗin falon tana roƙon Abbah akan ya dawo da ita, shi kuwa Abbah ya dage akan saita tashi tabar masa gida tinda bai gayyato ta bikin ɗansa ba, Minal kuwa tsabar kunya ko fitowa falon batayi ba balle taga kayan takaicin nan acikin bainar jama'a, Rukky itama ɗakin su ta nufa domin bazata iya ganin wannan ƙasƙancin ba, Pinky kuwa tin jiya da Razhdeen ya rufe ta a ɗakin horo har zuwa yanzu bai fito da ita ba kuma key ɗin ɗakin yana hannunsa, ga baya zaman gida saboda taron mutane domin baya son hayaniya, shima Abbah ya manta da batun Pinky a ɗakin horo, su kuwa sauran yaran gidan kowa yana fargaban yin maganar Pinky, Aunty Yolash ma a tunaninta an fito da ita dake yau ranar hidima ce, Hajiya Kilishi fashewa tayi da matsanancin kuka tana roƙon Abbah tare da faɗin "Dan girman Allah Chief kayi haƙuri ka dawo dani kan ƴaƴana nayi kuskure sosai, sam bana jin daɗin zaman gidan mu ga kasa an dakatar dani a wurin Aiki bana zuwa ko ina, kayi haƙuri..." Abbah yana huci yace "duk wanda ya bani shawarar na dawo dake wallahi tallahi ba masoyina bane, babban maƙiyi nane kuma Ni da shi zumunci ya yanke har abada saboda haka ki tashi kibar mun gida yanzun nan, ƴaƴanki koda ke ko babu ke zasu rayu cikin aminci, kuma ki dube su dakyau babu abinda ya ragu a jikinsu da bakya nan, saima girman jiki da suka ƙara, ina mai miki albishir da cewa a gobe ranar Jumma'at za'a haɗa Auren Roshan da Aurena a ɗaura, an bani ƙanwar Matata marigayiya Fatima akan na Aura, kuma Alhamdulillah ɗabi'unsu ɗaya da tarbiyyar su da duk wasu nau'ikan zamantakewar Aure, sunanta Ummu Salamah Amintacciyar yarinya daga Saudi Arabia, Kilishi ki tashi kibar mun gida yanzun nan tin kafin nasa karnukana su korar mun ke...." Jiri ta fara ji jin chief zaiyi Aure, nan ta ƙara fashewa da kuka ta buɗi baki zatayi magana yayi saurin daka mata wani irin gigitaccen tsawa har saida sauran mutanen wurin suka firgita, a gigice ta miƙe tsaye ta nufi bakin ƙofa tana kuka, anan ta tarar da Ummy tana tsaye bata ƙarasa shugowa ba duk ta wanke kwalliyar fuskarta da hawaye, tsayawa tayi Hajiya Kilishi a gaban Ummy ta kamo hannayenta biyu tana ƙiran sunanta ciki-ciki tace "Ummy ki gafarce Ni..." Daga nan tayi wucewarta... Abbah shima juyawa yayi ya haura saman upstairs rai a ɓace, kab mutanen wurin babu wanda yaji daɗin abinda ya faru amma masu faɗin madalla su sukafi yawa domin da yawan su babu wanda yake jin daɗin zama da Hajiya Kilishi saboda ta kasance mace marar son mutane, Aunty Yolash ɗan tsaki taja tareda wurga ƙwayar idonta kan Hajiya Maamie wacce itama tana wurin tace "waɗanda za'a kora ai sunada yawa, ina mai martaba shima yazo yahau kan layi, domin baza'a mayar mana da ɗan uwa bita zai-zai ba...." Duk sauran mutanen suka tintsire da dariya tare da faɗin "wallahi kuwa..." Hajiya Maamie dogon tsuka taja tana hararar Aunty Yolash da sauran ƴan uwansu tace "Ni kuwa an mutu dani wallahi, babu yanda aka iya dani, mutu karaba takalmin kaza Ni da mai martaba, dole a ganni a barni domin na zamo ciwon ido..." Aunty Yolash tace "yooo wa kika ajiye balle ki zauna dashi har ƙarshen rayuwa? To dai kina gani wacce ta ajiye har ƴaƴa biyar ma ta fita balle ke ko ɓatan wata baki taɓa yi ba...." Hajiya Maamie tace "au gorin haihuwa ne ya tashi? ey gwara Ni a gidan mijina nake ba yawon tsinantaka ba, anyi shekara kusan arba'in amma babu mijin Aure..." Aunty Yolash ta gama ƙuluwa matuƙa tace "bari kiji Madam! Bawai rasa miji nayi ba, niyya ne banyi ba kuma ko a yanzu naso yin Aure zanyi kuma na haihu da yardar Allah..." Hajiya Maamie tace "to kiga dama mana yanzun ma, wa ya hanaki ƙirrr kutu kutu..." Aunty Yolash tace "Uhmmm! Kin yanda nayi Aure yanzu ke kuma ki samu ciki a wata ɗaya zuwa biyu?..." Hajiya Maamie Saida taji bugun zuciya domin a asibiti an tabbatar mata cewa mahaifarta yayi ƙarami a ɗaukar ciki sannan ta gama yawon bin bokaye da dama amma ba'a dace ba, Harara ta wurgawa Aunty Yolash sannan tace "shi haihuwa daga Allah ne Dan buro ubanki...." Aunty Yolash a ruɗe ta dafa ƙirji tare da faɗin "buro ubanaaa?! kika ce buro ubanaaa?!! buro ubanaaa kika ceee?!!!..." Nan danan idon Aunty Yolash ne ya kaɗa yayi jawur domin tin tana cikin mahaifiyarta ta rasa mahaifinta memakon a bishi da addu'a sai kuma zagi, ai bata san lokacin da tayi sufa ta cabko wuyan Hajiya Maamie ba, Hajiya Maamie ta tsorata sosai da ganin yanayin Aunty Yolash, mutanen wurin ne suka rirriƙe Aunty Yolash domin ba ƙaramin shaƙa tayi mata ba, duk yawan mutanen falon babu wanda ya iya ɓanɓaran Aunty Yolash daga jikin Hajiya Maamie, Abbah jin hayaniya yayi yawa ne yasa shi sauƙowa dasauri, shima daƙer ya iya fizgar Aunty Yolash ganin bazata saurari abinda zai faɗa ba, Cikin faɗa yake magana tare da faɗin "wannan wani irin hauka ne? babu dama a barku ku kaɗai sai an samu matsala?..." ya kalli Aunty Yolash yace "ke meyasa bakida haƙuri ne? to ku same Ni acan falo ɗina yanzun nan..." yana kaiwa nan yayi ficewarsa, Aunty Yolash harara ta wurgawa Hajiya Maamie itama tayi gaba, Hajiya Maamie itama bayanta tabi, a falo duk suka tarar da Chief yana zaune akan tsararren Soparsa kai a sunkuye yanata karkaɗa ƙafafu, duk zama sukayi a ƙasin carpet domin falon Chief indai ba manya-manyan baƙinsa bane ba'a zama masa akan sopa, Chief ɗaukar waya yayi ya ƙira wata dattijuwa a can falonsu wacce tana wajen akayi komai, can sai gata ta shugo da sallama a bakinta, amsa mata yayi tare da nuna mata saman kujera ta zauna, zama tayi tare da faɗin "to gani naga an ƙira Ni..." Chief yace "Uma shin kina nan suka fara faɗa?.." tace "tabbas kuwa " Chief yace "toh inaso ki gaya mun gaskiyar abinda ya haɗasu kar kiga cewa kinada alaƙa da Yolash kawai tsakanin ki da Allah zaki sanar mun...." Tsohuwa tace "tsakani da ALLAH kuwa zan gaya maka.." nan ta kwashe komai ta sanarwa Chief abinda ya haɗasu... Chief ya kalli Aunty Yolash yace "bakida gaskiya Auntyn Yara, meyasa bakida haƙuri ne? meyasa ZAKIYI mata gorin haihuwa? shin ba Allah ne yake badawa ba ne? ko kin isa ki bata haihuwar? ko kuma ita ta isa ta bawa kanta haihuwar? ko kuma mijinta ya isa ya bada haihuwar da Allah bai sauƙar ba? kuna abu da tunani mana, komai sai ku rinƙa nuna rashin ilimi akai, wannan ai zunzurutun jahilci ne gori akan abinda Allah ne mai bada shi bawai wani halitta ba, toh wallahi daga yau kar Na sake jin wannan kalmar daga bakin ki..." Aunty Yolash tana hawaye tace "Amma Yaya itama tamun gorin Aure fah..." Chief yace "Aure ai ke kika hana kanki, Allah ya baki damammaki da dama amma kin ƙi amfani dashi, nawa ne mazajen Aure suka zo nemanki amma duk kin ƙisu, kuma dan anyi miki gori sai kiji haushi? Ai gorin haihuwa yafi na Aure ciwo, har yanzu damarki bai wuce ba, akwai waɗanda suke zuwa neman Aurenki, aciki akwai Governor Kaduna da Governor Bauchi ga Alhaji Tafidan Bauchi ga manya-manyan shuwagabannin nan Abuja da dai sauransu idan kuma kince a'ah TOH saiki cigaba da toshe kunnuwanki da jin duk wasu ƙananun maganganu akan ki, Ku tashi ku ban wuri...." Dasauri Aunty Yolash ta miƙe ta fice tana kuka, Hajiya Maamie kuwa zaro idanuwa ta fara yi jin manya-manyan mutanen da suke neman Aunty Yolash da Aure, da hassada acikin zuciyarta tabar falon Chief, Ita kuwa Tsohuwa zama tayi ta cigaba da tattaunawa da Chief akan yanda bikin zai kasance gashi ɗaurin Auren har da nashi.... Aunty Yolash tana shiga babban falonsu kai tsaye room ɗinta ta wuce ta danna sakata, Mutanen da suke falo babu yawa duk sun kutsa kai ɗakin da Amarya take itama Baiwar ALLAH ta kulle kanta a cikin Bathroom taƙi buɗewa, sunyi da ita akan ta buɗe amma taƙi, gashi har lokacin dinner yayi, sauran yaran gidan ma ko wacce tana ɗakinta cikin damuwa ganin yanda Abbah ya wulakanta Mommynsu kuma sannan sunji labarin shima zaiyi Aure, Angwaye sun jira har sun gaji basu ga ko mutum ɗaya ba acikin matan gidan balle suga idon Amarya, Da haka har lokaci ya ƙure aka bantsar da hidimar Dinner, amma ba ƙaramin takaici suka shaƙa ba kaf Abokanan Ango da shi kanshi Angon, Daman Aunty Yolash ce kawai zata iya tsawatar wa Baiwar ALLAH akan ta buɗe TOH itama ga a halin da take ciki itama ta kulle kan natan, Ummy ma wacce itace Yakamata ta rarrasheta itama ta zama uwar ɗaki.... 🕊️🕊️🕊️🕊️🕊️ Razhdeen shi da Mohandas layin mabarata suka nufa da isar su tsayar da motar sukayi a dai-dain layin suna baza idanu ko zasu hango Ƴar Amana, a wannan lokacin ma sun yi rashin Sa'a basu ganta ba, ɗan tsuka Razhdeen yaja tare da jan mota zai bar wurin Mohandas yayi saurin dakatar dashi tare da faɗin "wait Major! Bayan barin ka Nigeria nasha zuwa nan duba yarinyar nan amma bata nan, banyi tunanin sauƙa daga motar zuwa tambayarsu ita ba amma a wannan lokacin dole zamu je mu tambayesu ita, ina tunanin rashin zamanta anan ba lafiya ba..." Dasauri Razhdeen ya juyo yana kallonsa cikin yanayin damuwa, ƙirjinsa ba ƙaramin bugawa yayi ba jin abinda Marshall ya faɗa..." Mohandas yace "let me go and check her, stay inside the car..." yana kaiwa nan ya fice kai tsaye wurin tsofin ya nufa, shi kuwa Razhdeen yana daga ciki yana kallon wurin da take yawan zama... Mohandas tsugunawa yayi a gaban tsohuwar da Ƴar Amana take suka gaisa sannan yake tambayarta labarin Ƴar Amana, Nan tsohuwa ta fashe da kuka tana faɗin "Allah sarki kurmiyar Allah, Amanar Allah sun ɗauke ta..." Mohandas cike da mamaki ya furta cewa "daman kurmiya ce?..." Tsohuwa tace "ey kurmiya ce, ɓarayi ne suka sace ta..." Dasauri Mohandas ya miƙe tsaye tare da faɗin "whattttt!!!!...." Juyawa yayi da gudu ya nufi motarsu, buɗewa yayi ya shiga yana jan numfashi ido a zazzare, Razhdeen ganinsa ba ƙaramin tsorita yayi ba ganin halinda ya kasance, tsoronsa kar wani mummunan abu ya faru da ita.. A ɗan ruɗe Razhdeen yace "what's wrong?..." shuru Mohandas bai bashi amsa ba, A tsawace Razhdeen yace "ina maka magana ka bani amsa mana ..." Razhdeen bai taɓa buɗe murya yayi magana kamar yanzu ba, cike da mamaki Mohandas ya juya yana kallonsa ganin yanda ya rikice lokaci guda, a ɗan tsorace Mohandas yace "someone kidnap her..." Razhdeen cikin go slow ya juyo yana ƙarewa Mohandas kallo ido a zazzare, Jin bai gamsu da maganar Mohandas ba yasa ya buɗe murfin motar ya fice, kai tsaye wurin tsofaffin ya nufa yana zuwa ya tsaya yana binsu da kallo, a tsawace ya fara magana yana faɗin "Who kidnap her?, tell me please who come and kidnap my sarah?..." Duk tsaya kallonsa suke domin babu wacce tasan mai yake faɗi domin da turanci yake maganar, tsohuwar ƴar Amana ce tace "kayi haƙuri yaro Bama jin Yaren nan..." Razhdeen hannu bibbiyu yasa a cikin sumar gashinsa yana cakurkuɗawa cikin zafin rai yace "nace waye ya sace mun Sarah? ..." Anan duk suka sanar masa duk yanda akayi da cewar suma basu ga fuskarsu ba domin baƙar hula ce akan su...." tsohuwar ta miƙa masa jitar Ƴar Amana... Razhdeen kamar zai dungura haka ya nufi motar yana shiga ya finciki motar a ɗari suka bar wurin, A wannan ranar Razhdeen da Mohandas ba yanda basu shiga ba neman Ƴar Amana amma babu ɗuriyarta, duk yanda suka san ƙungiyoyin Dabanci Saida suka je amma basu samu labarinta ba, Saida suka yiwa wasu ƴan Daba dukan tsiya ganin zasu raina musu wayo, yanzu misalin ƙarfe 2 na dare suna hanya, Mohandas gaba ɗaya ya gama gajiya daƙer ya lallami Razhdeen suka koma gida akan washe gari zasu ƙara fitowa nemanta...... asmeetah writer ✍️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *11_ TŌ _12* Misalin ƙarfe uku na dare, agogo ne yake harbawa a hankali ƙit-ƙitt-ƙittt a yayin da Razhdeen yake kwance saman katafaren gadonsa, yana rufe da mayafi sai iya fuskar sa ne a waje yana kallon ceilling, kashe hasken ɗakin yayi sai ɗan hasken lamp da ya bari mai launin green, A daren yau Razhdeen bai samu yin bacci ba sakamakon abin da yasa a ran sa, ɓatar Ƴar Amana ba ƙaramin girgiza shi yayi ba domin a halin yanzu bai san a wani hali take ciki ba, gashi an bayyanar masa cewa zuwa akayi har wurin da take aka ɗauke ta, duk yanda akayi sun haɗa mata tarko ne, Tunani ne barkatai acikin kwakwalwar sa, mafita yake nema yanda zai samu yarinyar nan domin a halin yanzu ita ce raunin sa!... Washe garin ranar ɗaurin Auren Roshan da Baiwar ALLAH, kowa ya hallaru baƙi ne a gidan Chief kamar basa mutuwa tsabar yawan family, misalin ƙarfe 12 na rana Ango da Abokan sa kowa yayi shirin zuwa ɗaurin Aure dake can babban masallaci, Abbah shima da abokansa waɗanda suka zo ɗaurin Aure sun sha manya-manyan kaya, kowa ya hallaru sai fita ake da wasu manya-manyan motoci ga motocin sojoji suma zasu yi rakiya, kowa ya tafi sai iya Ango ne kawai ya rage shima yasha farar gizner da babbar gariya sai shining giznar take, ga wani irin ƙamshin da yake fitarwa kai kace wanka yayi da zallar turare, Roshan ba ƙaramin kyau yayi ba, ga hular kalar kayan, sai wasu Abokansa guda uku motar su ce kawai ta rage basu tafi ba, ganin Roshan yaƙi tafiya yasa suma suka ƙi tafiya domin saboda Angon za'aje wurin ɗaurin Auren shi kuma bai tafi ba, Roshan ba kowa yake jira ba illa twins ɗinsa Razhdeen, duk taron mutanen da akayi babu Razhdeen a ciki, kowa sai tambayar sa yake, domin shine twins ɗinsa kuma babban Abokin Ango, an ƙira wayarsa switch up, anje gidansa baya nan babu wanda yasan yanda yake hatta Mohandas shima ya halarci wurin ɗaurin Auren Roshan, Ganin shuru babu labarinsa yasa Abokanan Roshan suka ja shi cikin motar nan da nan kamar walƙiya suka bar gidan domin iya su kawai ake jira a wurin taron ɗaurin Aure... Baiwar ALLAH tana bedroom ɗinta tare da masu kula da ita ba abinda take sai kuka, gaba ɗaya fuskar nan tayi jawur tsabar kuka kamar ba Amarya ba, ji take kamar ta sanar cewa bata son Auren Roshan amma sai dai idan tayi hakan tayi butulci sannan aikin gama ya gama tinda an tafi ɗauro Auren, har cikin ranta bata cire son Razhdeen acikin zuciyar ta ba kuma gani take bazata taɓa cire soyayyarsa ba, kulle kanta da tayi a bathroom tayi niyar tasha poison ta kashe kanta amma tayi tunanin kashe kai ba abu ne mai sauƙi ba, tana ciki Abbah ya shugo domin a lokacin har anje an gayo masa dake tana jin shakkar Abbah, tana zaune a bakin bed tunanin samawa kanta mafita take, amma zuciyarta na sanar mata cewa "kiyi haƙuri ki zauna da mijinki haka ƙaddarar ki tazo miki, a duk yanda kika tsinci kanki to ki gode wa ALLAH..." Sauƙe numfashi tayi domin tayi na'am da shawarar da zuciyarta ta bata, a hankali take ɗago da kanta tana bin mutanen ɗakin da kallo, ganin kowa yana cikin farin ciki yasa ta yin maganar zuci cewa "Allah sarki farin cikin ku kawai kuka sani amma baku san tawa farin cikin ba..." tana cikin saƙe-saƙe kwatsam taji an dafa kafaɗarta, da sauri Baiwar ALLAH ta juyo tana kallon wacce ta zauna gefenta tare da ɗora mata hannu akan kafaɗa, Ramlat ce tasau mata murmushin takaici da kuma kishi ta ce "Sannu Amarya bakya laifi, Amma fah kin ciri tuta gaskiya duk da baki da asali amma haka Yaya Roshan ya nace miki, kuma ba wani dace wa kuka yi da juna ba, kina nan kamar wata farar goɗiya..." Duk mutanen ɗakin ne suka juyo suna kallon su, wata daga ciki ne ta ce "toh ikon Allah duk meya kawo wannan maganar?..." Ramlat ta kalleta sama da ƙasa sannan ta ce "bakin da Allah ya tsaga baya rasa ta cewa, don haka abin da ke raina na faɗa..." wacce tayi maganar ce ta kuma cewa "Amma ai bai kamata kiyi irin wannan maganar a cikin mutane ba..." Ramlat ta ce "Oh ashe dai a cikin mutane nake, ai Ni kuwa na ɗauka dabbobi ne..." Duk shuru suka yi saboda ba mai iya tanka mata, tsoron Ramlat ake saboda Hajiya Maamie domin ba ƙaramar masifaffiyar mata ba ne, yanzu sai ta iya hargutsa taron bikin, Ummy uwar masu gida wacce jugowarta cikin ɗakin kenam, kalmar da Ramlat ta furta ne ya daki dodon kunnenta, ai kuwa nan itama ta buɗi baki ta ce "dabbobin suna da yawa ai amma sai dai wacce take agolanci tafi dabbobin dabbanci..." Ramlat miƙe wa tayi tsaye tana bin Ummy da kallo cike da mamaki ta ce "Ummy Ni kike ƙira da Agola?..." Ummy ta ce "to ƙarya akayi miki ne? ko gidan Uncle mai martaba da kike zaune a gidan Ubanki ne shi? kin samu matsayi ne albarkacin zaman da kike a gidan sarauta amma in ba haka ba kin isa ki buɗe baki kiyi wani maganar banza ne anan, duk mutanen da kike gani acikin gidan nan duk jini ɗaya ne babu bare sai ke, Yayarki ce matar mai martaba ita kuwa ba haihuwa take ba hakan yasa ta jawo ki gidan sarauta kizo ki ci arziƙi babu a house..." Ramlat ita kaɗai tasan takaicin da take shaƙa a yanzu buɗar baki tayi ta ce "au gorin haihuwa zakiyi wa Aunty nah? eh naji bata haihuwa amma ai ta kama kanta tana zaune a gidan mijinta, wata uwar kuma zubar da ƴaƴanta tayi take bin yawon hotel..." Ramlat tana kammala fitar da abinda ke ranta tayi saurin barin room ɗin domin tasan uwar Ummy ce take yawon hotel, wani abu mai kama da kibiya ne ya soki saitin zuciyar Ummy tsabar takaici da baƙin cikin har an fara mata gori akan mahaifiyarta, Da sauri ta juya zata bi bayan Ramlat taji an riƙo ta juyawa tayi taga Baiwar ALLAH ce take ta faman girgiza mata kai alamar karta biye mata, Ummy tsabar takaici bata san lokacin da ta rausa uban ihu ba tare da durƙusa gwiwowinta ƙasi, duk mutanen ɗakin ne suka rufu kanta suna bata haƙuri akan abinda ya faru, Ummy kuwa kuka take ko sauraron su bata yi domin abun da ciwo ta sanadiyar haka yasa Mahaifiyarta tabar gidan Mahaifinsu, Jin Ihun ya jawo hankulan wasu daga cikin mutanen gidan, Aunty Yolash ce first ɗin shugowa dake tana kusa da ɗakin sai ga Rukky da Pinky wacce ba'a daɗe da fito da ita daga ɗakin duhu ba, Ummy tambayarta ake meya faru da ita amma babu bakin magana sai waɗanda akayi a gabansu ne suka faɗi duk abin da ya faru, sam babu wanda yaji daɗin abinda ya faru a cikinsu, Baiwar ALLAH dake tsaye ta kama kai tayi shuru sakamakon wani irin Jiri da hajijiyar da take ji, kanta ne yake mata wani irin matsanancin ciwo, ko kaɗan bata son hayaniya a halin da take ciki yanzu domin ba isasshen lafiya gareta ba, a cikin tana jurewa har ƙarfinta ya ƙare ta yanki jiki ta faɗi a wurin, daga lokacin bata san ina hankalinta yake ba domin alamun suma tayi, sai kuma kallo ya koma kan Amarya, nan da nan magana ta bazu cewa "Amarya ta yanki jiki ta faɗi ga babu maza a gida duk taron mata ne... Ramlat kuwa ɗakin su ta shige ita da Auntyn ta Hajiya Maamie, tsaya wa tayi tana huci a yayin da Hajiya Maamie take zaune a bakin gado sai shan kwalliyarta take, ganin Ramlat a cikin wani hali yasa ta cewa "ke kuma lafiyar ki ƙalau kuwa?.." Ramlat ta ce "ina kuwa lafiya Aunty Maamie, wannan ƙaramar Yarinya tana shirin raina mun wayo..." Hajiya Maamie ta ce "koma wacece meyasa baki ci ubanta ba sai kuma kizo kina mun cika baki aikin banza kawai, ai indai bazaki buɗe baki kici mutuncin mutum ba to ke da raini kuwa yanzu kuka ƙulla, wai ma wacece yarinyar?..." Ramlat ta ce "Ummy mana kodan a gidan ubanta take ne shiyasa zata nemi ta ci mun mutunci, har wani ƙirana take da Agola ke kuma ta ce bakya haihuwa..." Hajiya Maamie data bugi ƙasa da ƙafarta ta wani narka uwar ashar ta ce "buuuuro uban nan, ke kuma me kike ce mata dan durun uwarki?..." Ramlat ta ce "ce mata nayi ai kinfi uwarta da take yawon bin hotel tinda ke kin kama kanki kina zaune da mijinki..." Hajiya Maamie washe baki tayi tare da faɗin "kin burge ni da kika gaya mata haka, kinga gaba bazata sake miki gori ba tinda abun gori yana gindin su, ai wallahi da baki tamka mata ba saina zabga miki mari sannan na kora ki garin Kaka can ƙauye..." Ramlat ta ce "cab ɗin ai wallahi bazan iya zaman ƙauye ba hakan ma a wurin Kaka, wai ma Aunty Maamie ya batun Aure na ne kam? an fasa ne?..." Hajiya Maamie taja dogon numfashi tana hura iskar baki ta ce "ai ki bar batun nan kawai, domin sai bokan nan yayi mun aiki tuƙuru akan Razhdeen, ko ba yanzu ba za'ayi Auren, a duniyan nan babu wanda tsafi baya kamashi don haka ki kwantar da hankalin ki, domin idan muka cika yin maganar tsab Razhdeen rabaki zaiyi da duniyan nan gwara mu bi komai a hankali ba'a gaggawa da rayuwa..." Ramlat ta ce "Ni dan Allah kibar batun Uncle Deen ɗin nan, mu koma kan Yaya Roshan ni nafi son sa wallahi, kuma kinga shi da wuri za'a iya shawo kan sa..." Hajiya Maamie ta ce "Dan ubanki Roshan ɗin da aka tafi ɗauro masa Aure shine zakiyi batun sa? ki bar komai a hannu na dole fa sai Razhdeen ya Aure ki..." Ramlat ta ce "wallahi ban gama warkewa da dukan da yayi mun ba, har yanzu gaɓoɓina ciwo suke mun hakan ma ki duba yanda ya ɗaure ni a saman fanka kamar wata lauje, Ni gaskiya bazan iya zama da Uncle Deen ba..." Hajiya Maamie har ta buɗe baki zatayi magana suka ji kururuwa a falo, hayaniya duk ta baza ko ina na gidan, da sauri suka fice domin gane wa idonsu, suna fita suka tarar an fito da Baiwar ALLAH a sume, wasu sun riƙe hannayen ta biyu wasu kuma sawaye da haka suka fito da ita, Aunty Yolash ce tayi gudun shiga room ɗinta ta ɗauko key ɗin motar ta zata kai ta hospital, A ruɗe take faɗin "dan Allah ku taya ni ɗaga ta mu kai ta wurin parking kunga ba maza a gidan sannan duk sojojin ma babu wanda aka bari..." wata tsohuwa ce ta ce "wai ma duk meya jawo haka ne..." Ummy tana kuka ta ce "duk ata sanadiyar waccan Agolar yarinyar ce..." ta ƙarisa maganar tare da nuna yanda Ramlat take tsaye. Ramlat kama kunkumi tayi ta tari yawun ta da cewa "Hmmm! Allah na gode maka a iya Agolanci na tsaya, ke bari kiji in banda tsautsayi da kuma tsananin soyayyar Yaya Roshan a cikin zuciyata ba mai zai sa na tsaya haɗa kishi da wannan yarinya mai kama da farar goɗiya..." Ummy ta ce "ai wallahi ko mata sun ƙare a duniya Yaya Roshan ba zai taɓa Auran ki ba domin bakya cikin lissafin tsarin matan da yake so..." Ramlat tayi dariya tare da tafa hannayenta biyu tana faɗin "ai kuwa you should see what am going to do yarinya, Yaya Roshan Auren ta kawai zai yi amma ainihin shi ɗin nawa ne..." Pinky dake wurin ta ce "wai duk akan wancan marar asalin ake wannan ce ce ku cen? Lallai kun haɗu da aiki..." Rukky itama buɗar baki tayi ta ce "ai daman tsautsayi da ƙaddara ne zai sa Yaya Roshan Auren marar asali..." Ramlat ta kalle su tare da sau wata ƙayatacciyar murmushi ganin an goya mata baya ta ce "yawwa ƴan gari shiyasa nake ƙara ji da ku twins saboda akwai faɗan gaskiya sannan bakwa goya wa ƙarya gindi..." Rukky ta ce "Ni fa dalilin da yasa bana ƙaunar Baiwar ALLAH saboda Abban mu ya fi nuna mata kulawa, bai damu da mu kamar yanda ya damu da ita ba, ni kuma inada kishi gaskiya..." Pinky ta tari yawun ta da cewa "ni kuma daman can bata raina, haka kawai nake jin tsanar ta wallahi, na rasa mai Yaya Roshan ya gani a jikin ta har ya nace akan Auren ta..." Ummy tana zaune akan kujera ta kifar da kanta akan gwiwowin ta tana jin duk tsegumin da suke amma ta kasa tanka musu, Aunty Yolash kuwa daman ko tsaya sauraron su bata yi ba tin tinin sun fice da Baiwar ALLAH, a can wurin parking suka tsaya ganin an tsayar da wata jibgegiyar baƙar mota, cikin nuna damuwa Aunty Yolash ta ce "yawwa ga Razhdeen ya zo..." Da gudu ta nufi wurin da yayi parking motarsa ko fito wa bai samu damar yi ba, zuwa tayi ta fara ƙonƙosa masa murfin motar domin tasan halin sa kafin ya fito sai ya ja musu aji, ganin tana shirin takura masa ne yasa shi fitowa fuska a turnuƙe ba alamun annuri, kafin ya buɗi baki ya yi magana har Aunty Yolash takai ƙarshen maganar ta tana faɗin "dan Allah Razhdeen ka taimaka ga can Amarya a kwance ta faɗi, kuma kaga ba wani namiji a gidan..." kallon gefen ido ya yi mata tare da faɗin "zanje ɗaurin Auren twins ne, tinda kun fito da ita ku kaita mana..." yana kaiwa ƙarshe ya juya zai shige motar sa Aunty Yolash tayi saurin riƙo hannun sa tana faɗin "wai kai wani irin murɗaɗɗen mutum ne kam, ga can yarinya rai a hannun Allah amma kai ko a jikin ka? na tabbata inda Mijin ta ne kafin na ƙarasa magana ta zai nufi yanda take..." Razhdeen haɗe gira ya yi tare da faɗin "Mijinta fa kika ce, ba Razhdeen ba don haka sai ku jira mijin natan ya dawo tinda muharramar sa ce..." Aunty Yolash fuska ɗauke da damuwa ta ce "Please Razhdeen ka taimaka dan Allah, ba dan ni ba..." Lumshe idanuwan sa yayi tare da buɗe su a hankali ya sauƙe su akan Baiwar ALLAH dake kwance ƙasin floor kanta na kan cinyar wata tsohuwa... ratsa gefen Aunty Yolash ya yi sannan ya nufi yanda Baiwar ALLAH take kwance, yana zuwa kuwa nan take yayi mata ɗaukar jaririya ya nufi motar sa da ita, iya Aunty Yolash kawai ya buƙaci su tafi tare, sauran kuwa komawa ciki suka yi... Nan da wasu ƴan mintuna har sun isa hospital, a harabar hospital ya yi parking da motar sa, lokaci guda wasu nurses sun kai biyar suka fito da gadon tura wa, Razhdeen da Aunty Yolash suma facility ɗin hospital suka shiga, a wasu kujeru suka zauna domin har an shiga da Baiwar Allah emergency room, Bayan wasu mintuna sai ga Doctor ya ce musu yana son ganin su a office ɗin shi, hakan kuwa suka yi a office suka tarar da shi zaune yana duba wasu files, suma zama suka yi suna fuskantar Doctor, numfashi Doctor ya sauƙe idon sa akan Razhdeen ya ce "Major meyasa zaku bar yarinya ciwo ya ci jikin ta har haka? ta juma tana fama da rashin lafiya domin zazzaɓi ne mai zafin gaske yake damun ta, rashin tarar abun da wuri ne yasa duk jinin jikin ta tsotse wa, zata iya rasa rayuwar ta a cikin ɗan kwanakin nan in har bata sha ledar jini biyu zuwa uku ba..." ya ƙarasa maganar tare da miƙa musu file ɗin ta, Razhdeen ne ya karɓa yana duba wa daga ƙarshe kuma ya ce "yanzun mai ake jira ne?..." Doctor ya ce "jinin da zai yi dai-dai da nata domin a yanzu ana wahalar samun jini sosai..." Jin jina kai Razhdeen ya yi sannan ya ce "okay kaja mata jini na indai zai yi mata..." Aunty Yolash murmushi tayi ganin yanda Razhdeen ya damu da rashin lafiyar Baiwar Allah lokaci guda, Doctor ya ce zamu duba mu gani in har zai yi mata, a take Razhdeen ya miƙa hannun sa aka ja jinin da za'a gwada da nata, Bayan wasu ɗan mintuna sai ga Doctor ya dawo fuska ɗauke da murmushi ya kalli Razhdeen sannan ya kai idon sa kan Aunty Yolash ya ce "Ma sha ALLAH! group ∅ negative zaka iya bawa kowa, amma ita ɗin matar ka ce ko wacce zaka Aura?..." haɗe gira Razhdeen ya yi tare da faɗin "daman ina ba da jini na a kowa duk wanda ya buƙaci jini, ba a kanta na fara ba kuma bazan dai na akan ta ba, taimako ne kuma nayi niyar yinsa..." Doctor ya ce "sorry Major yanzu za'a iya jan jinin..." lokaci ƙanƙani aka ja jini leda ɗaya daga ɓangaren sa, nan da nan Doctor ya je ya ɗaura mata har zuwa yanzu bata farfaɗo ba... After 4hours har zuwa wannan lokacin Razhdeen da Aunty Yolash suna nan babu mutum ɗaya da ya zo hospital sakamakon rashin sanin halin da Baiwar ALLAH ke ciki, already Aunty Yolash ta sanar wa mutanen gidan cewa kada wacce ta sanar wa su Abbah da Roshan cewa Baiwar ALLAH tana hospital har sai ta farfaɗo, saboda kar su shiga wani hali gashi a ranar biki, An ɗaura Aure lafiya Roshan da Baiwar ALLAH wacce ta amsa suna (AMATULLAH), Roshan Abokan sa sun ja shi sun tafi yawon shakatawa sai zuwa dare ya gana da Amaryar sa, shima Abbah an ɗaura Auren sa da ƙanwar Matar sa ta farko wato mahaifiyar Razhdeen da Roshan, Amaryar Abba mai suna Ummu Salamah, bazawara ce mijin ta shine Marigayi Alsheikh Mahmoud Shureim babban malamin ƙasar Saudiyya, Ummu Salamah yau shekara guda da gama takaban mijinta kuma a yau Abbah ya Aure ta, yaron su ɗaya tak mai suna ARASH! ya kammala master's ɗinsa a ƙasar Pakistan a ɓangaren lawyer, yanzu ya zama babban lawyer a ƙasar Saudiyya (according to Qur'an).. Gobe za'a ɗauko Amaryar Abba daga Saudiyya zuwa Nigeria... A ranar Baiwar ALLAH sai da ta sha jini laida biyu duk daga jikin Razhdeen aka ja, an basu dama sun shiga duba ta amma sai dai ta tafi dogon bacci bayan ta farfaɗo, laidar jini na biyun ma har ya kusan ƙare wa, Aunty Yolash tana zaune akan kujerar gefen gadon shi kuma Razhdeen yana tsaye ta saitin kanta yana ƙare ta da kallo, Doctor ne ya shigo yana faɗin "Insha ALLAHU a yau za'a sallame ku domin ba ƙaramin duba ta muka yi ba, yanzu haka bacci ta samu yi ne zuwa an juma kaɗan zata farka..." Aunty Yolash ta ce "Allah yasa ta farka da wuri domin bana so su Abba su san muna hospital balle shi Roshan, bana so hankalin kowa ya karkato kan Amarya saboda ba kowa ne yasan muna hospital ba a cikin matan gidan ƴan biki, amma gobe ko wacce zata koma yanda ta fito idan aka kawo Amaryar Yaya General..." Razhdeen yana tsaye gaba ɗaya ya gama gajiya da zaman hospital ɗin nan, ga tunanin kurmiyarsa wato SARAH (Ƴar Amana) Meaning of Sarah (princess) Razhdeen kallon Aunty Yolash ya yi sannan ya ce "zan tafi gida..." Aunty Yolash ta ce "gaskiya ya kamata kaje ka huta kayi ƙoƙari sosai Uncle Deen, cire laida biyu na jini a jikin mutum kuma a rana ɗaya ba wasa bane, mun gode sosai..." Razhdeen kawar da kai ya yi zai tafi yaji an damƙo hannun sa, a hankali ya juya bayan sa yaga hannun Baiwar ALLAH tana riƙe da na shi, Aunty Yolash itama tsaya kallon ta tayi cike da mamaki, Idon ta a lumshe ta fara motsi da lips ɗinta a hankali ta soma furta "Uncle Deen jinin jikin ka ne yake gudana a jiki na? daman ina jiran wannan ranar ta zo na haɗakar jini, shikenam ka zamo jinin jiki nah, ina muradin ganin jinin jikin ka a cikin jikina, ina matuƙar ƙaunar ka da son kasance tare da kai har kullum, dan Allah ka ce wa Yaya Roshan ya yi haƙuri ya bar maka ni ..." Jin haka yasa a zabure Aunty Yolash miƙe wa tsaye tare da faɗin "whattttt?..." shima Razhdeen fizgar hannun sa ya yi cike da mamaki babu bakin magana, Baiwar ALLAH duk wannan maganganun da tayi shi ba'a cikin hayyacinta ta faɗe su ba, domin har zuwa yanzu idonta a rufe suke, sambatu kawai take tana cigaba da ɓare-ɓaren maganar ta... Aunty Yolash zuwa saitin ta tayi tare da sa hannu tana ɗan bubbugan fuskar ta tare da ambatar sunan ta, "Dota! Dota!! ke Dota ki buɗe eyes ɗinki kin san abinda kike faɗi kuwa?..." Muryar Abbah suka jiyo tare da wasu mutanen sun nufo ɗakin da aka ƙwantar da Baiwar ALLAH, Razhdeen fargaba da tsoro ne suka bayyana akan fuskar sa jin abubuwan da Baiwar ALLAH ke faɗi kuma ga su Abba suna shirin shugo wa, domin sun ji labarin Amarya tana kwance a gadon hospital ba lafiya, Da sauri Razhdeen ya yi saurin fice wa kafin a tarar da shi ga kuma bakin ta ya gagara rufuwa..." Da ƙer Aunty Yolash ta samu ta farkar da ita, dai dai lokacin da su Abbah suka shugo da Roshan da wasu... Razhdeen ta wata hanya ya bi domin baya so a san shima yazo hospital kuma ita Aunty Yolash tayi alkawarin baza ta sanar cewa jinin Razhdeen ba ne, shima Doctor ya yi wannan alƙawarin, Doctor a iya Baiwar ALLAH ya sanar lokacin da zai ɗaura mata jini na biyu domin a lokacin ta farfaɗo daga bisani ta wuce da yin bacci sakamakon Allurar baccin da akayi mata..... *DAN ALLAH FAN'S KUYI HAƘURI 🙏 INA CIKIN BUSY NE SHIYASA BAN SAMU LOKACIN YI MUKU UPDATE BA...* *SANNAN INA MAI SANAR MUKU CEWA AN KUSAN KAWO ƘARSHEN FREE BOOK A CIKIN STEP TWO ƊIN NAN* *MY ENEMY BOOK YANZU NE WASAN FARKO DOMIN DUK WANI CHAKWAKIYAR YANA CIKIN PAID BAZAN GUDANAR A CIKIN FREE BOOK BA...* *MY ENEMY PAID 300₦* *MY ENEMY PAID 300₦* *MY ENEMY PAID 300₦* *BA ƘARI☝️BA KUMA RAGI✌️* *BAN TSAWWALA BA DUK WACCE ZATA BIYA ƘOFA A BUƊE TAKE ITA ZATA NISHAƊARTU SANNAN TA FAƊAKARTU TA KUMA ILMANTU DA SANIN HALIN RAYUWA DA KUMA SOYAYYA...* *FREE BOOK YA KUSAN ƘARE WA🙏* *WACCE TAKE JIN DAƊIN LITTAFIN TO BIYAN KUƊIN LITTAFIN BAZAI MATA WUYA BA, 300₦* *ALLAH YA BADA IKON BIYA🙏🙏🙏* asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *13_ TO_14* Roshan a firgice ya yo kan Baiwar ALLAH dake kwance, zama yayi gefen gadon tare da sa hannu yana shafar sumar kan ta, cikin sassanyar murya yake faɗin "Ammata meya faru da ke? har da laidar jini?..." Kallonsa tayi tare da tsiyayar da ruwan hawaye, ta kai idon ta kan Abbah wanda yake ta ambatar sunanta yana gaishe ta da jiki, ga Aunty Yolash itama a zaune gefe guda tana cike da mamakin kalaman Baiwar ALLAH akan Razhdeen.. A ranar aka sallame su kuma a ranar da daddare aka kai Baiwar ALLAH ɗakin mijinta, anyi niyar yin party amma sakamakon rashin lafiyar ta yasa aka dakatar. Gidan Roshan a cikin gidan Abbah yake, shima ɓangarensa daban, Roshan yaso ya koma gefe can da Amaryarsa amma Abbah sam yaƙi sakamakon baya son ya rinƙa barinta ita kaɗai saboda zai fara zuwa wurin aiki tin daga safe har yamma, kafin kaje part ɗin Roshan sai ka wuce na Abbah kafin ka iske ƙaton gate mai launin golden, part ɗin sa ba ƙaramin tsaruwa ya yi ba, sai dai ma sha ALLAH... Misalin ƙarfe 10 na dare kowa ya watse daga part ɗin Amarya sai iya ita kaɗai ce ta rage a tsakiyar fantamemen gadonta na alhurma, tana rufe da mayafi akan ta sai sharar kuka take gaba ɗaya eyes ɗinta ya yi jawur, Tana cikin wannan halin sai taji an turo ƙofar ɗakin tare da yin sallama, wasu irin ƙamshin turaruka ne yake dukan hancin ta kala-kala alamun ba mutum ɗaya bane, Abokanan Ango ne suka rako Ango ɗakin Amaryarsa a ciki har da Razhdeen, wani daga ciki ne ya fara ƙirarin "Amarya bakya laifi ko kin daki hancin twins ɗin Ango..." Suka kalli Razhdeen dake tsaye a wurin bakin ƙofa su kuwa duk suka kwashe da dariya, Roshan zama yayi a bakin gado yana bin Baiwar ALLAH da kallo dake lulluɓe da mayafi, Sai da Angwaye suka gama musu nasiha da shawarwari tare da musu fatan alkhairi, kallon Razhdeen suka yi tare da faɗin "Major kai ba abinda zaka ce ne?.." Baiwar ALLAH jin an ambaci sunan Major yasa ta ɗan ɗago da kanta ta cikin mayafi take binsu da kallo har eyes ɗinta suka sauƙa akan Razhdeen wanda yake takowa a hankali ya nufo wurin Roshan tare da ajiye masa wani ƙaton laida wanda yake ɗauke da naman chicken da su eggs har da su kayan fruit da laimuka kala-kala, ya ɗauki hannu ya ɗora akan kafaɗar Roshan yana jijjiga shi, Shima Roshan ɗago wa yayi yana sau masa ƙayataccen murmushi, shima Razhdeen sake masa nasa murmushin ya yi a haka suka yi sallama, Duk fice wa suka yi aka bar Ango da Amaryarsa, ita kuwa Baiwar ALLAH wani sabon kuka ne ya sake kuɓuto mata, Roshan ne ya kulle ɗaki tare da yo wa kan Amarya yana faɗin "Ammata na an zamo Amarya yanzu kuma sauran ki zamo maman Baby.." Ya ƙarasa maganar tare da ɗage mata mayafin kan fuskar ta, abinda ya tarar ne ya ji sam bai ji daɗi ba ganin yanda take ta sharar kuka, Murya ciki-ciki ya soma faɗin "Ammata what's wrong with you? please kiyi haƙuri ki sanar mun matsalar ki, kinsan yanzu a hannu na kike duk wani matsalarki da issues ɗinki duk suna rataye a wuya na ne, ki taimaka ki sanar mun..." Girgiza kai tayi tare da faɗin "babu komai..." Ya ce "Okay kina kukan Amarci ne? ki kwantar da hankalin ki ai kina tare da ƴan uwanki tinda duk a gida ɗaya kuke, kuma Uwar masu gida zata na zuwa taya ki hira kinji koh?..." Shuru tayi ba tare da ta bashi amsa ba domin ita abinda yake ranta daban yake, kuma kukan da take shima akwai dalilai daban, na farko anyi Auren ta ba tare da iyayenta ba sannan kuma wanda take so ba shi ta Aura ba..." Roshan riƙo hannun ta yayi yana shirin ɗago ta tare da faɗin "tashi muje muyi alwala muyi sallah ko ƴar lelen mijin ta..." Zamar da hannun ta tayi fuska a ɗaure ta ce "kaje ka fara yi mana..." Ya ce "Okay bari toh naje nayi tinda Allah ya haɗa ni da mata mai alkunya..." Baiwar Allah ko ɗagowa tayi ta kalle shi ma bata yi ba. Shi kuwa tashi yayi ya shiga bathroom bayan wasu mintuna sai ga shi ya fito, itama tashi tayi ta shiga ta ɗauro alwala sannan ta fito suka tsayar da sallah a tare, bayan sun idar suka ci suka sha cikin ƙoshin lafiya ba tare da ɓacin rai ba, Bayan kammalawa cikin kulawa da dabara Roshan yakai hannunsa kan hannunta yana wasa da hannun natan tare da jan ta da hirar soyayya, a hankali yake matsawa dab da ita cikin wayancewa yake faɗin "Ammata nah ke fa ba matar Alaramma bace ki cire wannan hijab ɗin mana..." ya ƙarasa maganar tare da sa hannu ya zamar da hijab ɗin, A zabure Baiwar ALLAH ta miƙe tsaye fuska a ɗaure tana kallon gefe, Shima tashi yayi tsaye tare da kamo hannun ta yana faɗin "lafiya kuwa Ammata? ya naga kamar bakya cikin farin ciki..." Ganin yana shirin takura mata yasa ta cewa "Please Yaya Roshan ka ƙyale ni nikam..." Cikin sassanyar murya ya ce "why?.." Cikin ɗaga murya ta ce "Ni dai kawai ka barni.." Ya ce "Okay muje to ki cire kayanki sai ki sanya sleeping dress ko.." Ba tare da ta yadda sun haɗa ido ba ta ce "nan ɗin ɗakin waye?..." Ya ce "Ɗakin ki ne mana, Ni baƙunta nazo miki..." Juyar da eyes ɗinta tayi tare da faɗin "Okay zaka iya fitar mu a ɗaki yanzu..." Roshan cike da mamaki ya ce "what kinsan me kike cewa kuwa ?..." Ta ce "Yes i known what am tooking about, please can you pack your self and get out inside my room?..." Dogon numfashi ya ja tare da faɗin "Ammata daman nasan bakya so na, amma meyasa kika gagara sanar mun dan ALLAH?..." Tsuka ta ɗan ja tare da ɗaukar pillow tana faɗin "zan je parlor na kwanta nake ga zai fi mun wannan dogon jawabin nakan..." Har ta juya zata fice yayi saurin riƙo hannun ta tare da girgiza mata kai ya ce "dan ALLAH Ammata kar ki mun haka, zaki cutar da ni ne domin ba ƙaramin tsumi aka mun ba, ki taimaki rayuwata da kuma halin da zan shiga a cikin daren nan..." Numfashi ta sake tare da faɗin "wannan damuwar ka ce, ka sake mun hannu nikam..." Roshan kamar zai yi kuka haka yake riƙe da hannunta ya kasa sake wa, Sai da tayi magana sau uku akan ya sakar mata hannu amma fur ya ƙi, Cikin zafin nama ta fizgar da hannunta tare da ɗaukar wani ɗan ƙaramin wuƙa na yankan fruit ta ɗora a saitin maƙogaron ta ido a lumshe take faɗin "Yaya Roshan wallahi tallahi idan ka cigaba da tsayuwa mun a ɗaki saina ja wuƙar nan ta yanke mun wuya in yaso kowa ma ya huta da ni...." Lokaci guda Roshan ya birkice eyes ɗin nan suka yi jawur yana kar kaɗa mata hannu murya ta ƙi fito wa a haka yabar ɗakin a gaggauce, Jin shuru yasa ta buɗe eyes ɗinta taga baya nan tukun ta ajiye wuƙar ta taho da sauri ta danna key a ƙofar ɗakin, Wani ruɗaɗɗen kuka ne ya zo mata ba shiri, haka ta doku saman gadon tana rera kukan ta... Roshan shima ɗakin sa ya nufa hankali a tashe, zuciyarsa ce take masa zafi, kai tsaye bathroom ya shige tare da kunna ruwa a kansa domin sam ba'a cikin hayyacinsa yake ba... Bayan kwana biyu An kawo Amaryar Abbah itama cikin ƙoshin lafiya, kowa ya watse daga matar gida sai yaran gida sai kuma Roshan dake can part ɗinsa shima da Amaryarsa, Pinky da Rukky sun shirya tsab zasu koma karatu ƙasar London, Aunty Yolash ma ta koma Bauchi wurin Aikin ta, daga Ummy sai Ƴar tiny da Babbar Auntyn su Minal, sai kuma Amaryar Abbah Ummu Salamah wacce suke ƙiranta da Ammy, Itama Ramlat tana nan bata tafi ba tana so ta ɗan ƙara hutawa kafin ta koma... *AFTER ONE WEEK...* Cikin Daren Juma'a da misalin karfe 2:00 AM, Wayar Razhdeen ne ya yi ƙara alamar shugowar message a yayin da shi kuma yake kan sallaya ya idar da sallar dare, eyes ɗinsa yakai kan wayar dake kan drower, a lokacin bai saurari wayar ba sai kawai ya cigaba da lazuminsa, daga baya ya tashi ya cire jallabiyarsa already ya yi wankan sa tsab, daga shi sai Three quarter da singlet mai kakin soja, feshe jikinsa yayi da turare mai shegen ƙamshi kafin ya faɗa saman katafaren gadonsa tare da jan mayafi, gaba ɗaya ya mance da saƙon da aka turo mishi, lokaci guda bacci ɓarawo yayi awun gaba da shi... Ta ɓangaren Ƴar Amana kuwa a cikin daren nan ko rimtsawa batayi ba, ga sauran yanda duk bacci ya ɗauke su gaba ɗaya an rarrage mutanen su waɗanda aka kamo ta hanyar kashe su, A washe garin Jumma'a ne za'a kashe Ƴar Amana da misalin ƙarfe 6:00 na asuba, sumar kanta kuwa har yanzu bai fara tofowa ba, A wannan lokacin har ta saddaƙar cewa babu wanda zai zo ya cecesu daga halin da suke ciki, tayi kukan har ta gaji, Dab da asuba ƙarfe 4 Yar Amana bata san lokacin da bacci ya ɗauke ta a zaune ba, Lokaci guda wani farin haske ya bayyano kan goshinta kafin ƙibtawar ido har hasken ya ɓace kamar walƙiya, hasken bai sauƙa a ko ina ba sai a kan goshin Razhdeen dake kwance yana ta shan baccin sa, a lokacin ne ya fara wani irin mafarki akan Ƴar Amana, A cikin mafarkin aka bayyana masa halin da Ƴar Amana take ciki, abu kamar video haka yake gani a cikin mafarkin tin daga farkon al'amarin har zuwa yanzu da kuma yanka ta da za'ayi a gobe juma'a, Ya juma yana wannan mafarkin mai birkitar wa kafin daga bisani aka farkar da shi, A ruɗe ya tashi yana fitar da numfashi sama-sama kamar wanda aka ɗage masa numfashi, gaba ɗaya ya yi jirib da gumi duk da sanyin A.C da ke cikin room ɗin, Idanuwansa ne suka sauƙa akan Ƴar Amana dake tsaye a gabansa da wannan kan natan da babu sumar gashi ko ɗaya yanda kasan madubi, ta zuba masa ido babu alamar annuri a fuskar, Zaro eyes ɗinsa shima yayi yana binta da kallo lips na motsi a hankali yake jera Addu'o'i, Ji yayi an dafa kafaɗarsa ana faɗin "what are you looking for? kayi mummunar mafarki Koh?...." Sai a lokacin idanuwansa suka fara ganin dai-dai ashe Marshall Mohandas ne ya shugo ɗakin shi kuma sai yake kallon Ƴar Amana a madadin sa..." Razhdeen lips na motsi a hankali yake furta "Sarah! Sarah!! Sarah!!!..." Mohandas ya ce "shin ka gano a yanda take ne?..." Girgiza kai Razhdeen ya yi tare da faɗin "Naga a yanda take but I can't find a way, wurin is too far forest..." Mohandas sauƙe numfashi yayi tare da goya hannayensa kan ƙirji. Da sauri Razhdeen yakai eyes ɗinsa kan wayarsa sai yanzu ya tuna da message ɗin da aka turo masa, a gaggauce yasa hannu ya ɗauki wayarsa ko message ɗin yana da alaƙa da ita, Ai kuwa cikin sa'a yana buɗe wa yaci karo da Address ɗin yanda Ƴar Amana take can cikin daji ne, ana ƙiran dajin da suna dajin dutse, da kuma lokacin da za'a aikata ƙiyama... Zaro ido waje Razhdeen ya yi yana kallon wayar, Mohandas karɓar wayar yayi shima yana dubawa ganin yanda Razhdeen ya ƙame a wurin, Da sauri Mohandas ya ɗaga kai sama yana kallon agogo yaga ƙarfe 5 ne yanzu na asuba, cikin ɗaga murya ya ce "Major bamu da isasshen lokaci remain 1 hour ...." Razhdeen a firgice ya ce "Okay.." Ya tashi ya nufi hanyar fita, Mohandas ya riƙo shi yana faɗin "wait Major ka tsaya kayi sallar asuba, bari na ƙira sojojin nan su tanadar mana da elekwabta da kuma sojojin da zamu tafi da su domin bamu san mai zamu tarar ba..." Yanda Mohandas yace haka Razhdeen ya yi, shiga toilet yayi tare da ɗauro alwala ya fito wannan lokacin kam a gida ya yi sallar asuban sa, bai tsaya wata-wata ba ya yi shirinsa cikin kakin soja irin na ƙasar U.S, ya fito a Major General Razhdeen ɗinsa, ya ɗaure sumar kansa da wani jan ƙyalle mai zanen gum a jiki, kayan sojojin nan ba ƙaramin masa kyau suka yi ba duk da a birkice yake, Shima Mohandas yayi shirinsa na kakin soja shima na ƙasar U.S duk suka ɗauki bindigun su already an kawo musu jirgin da zai kai su cikin dajin domin sun shigar da bayanai sosai duk da basu tabbatar ba tukun... Da sassafe an fito da kowa kamar yanda aka saba kullum sai an kashe mutum biyu to haka yau ma, yau kuma akan Ƴar Amana za'a fara sai wata daga ciki itama, A wannan ranar Guess shima yana wurin, ga kuma Yallaɓai a zaune akan kujera, Yallaɓai ya kalli Guess sannan ya ce "You Guess a wancan lokacin na baka ajiyar wannan yarinyar amma ka barta ta gudu, toh yau kuma kai da hannunka zaka yanke mata maƙogaro a filin nan kowa yana kallo..." Guess yana tsaye da baƙar hula a fuska daman shi koda yaushe fuskarsa a rufe take, babu wanda yasan kamannun sa, Yallaɓai tashi yayi ya nufi wurin da Ƴar Amana take a durƙushe, ya ɗagota sannan ya since mata igiyoyin da aka ɗaure ta da shi, yana faɗin "Allah sarki kurmiyar Allah yau za'a wuce ƙiyama, idan kinje kice ina gaida su mutanen mu da kuma sabuwar Shugabar ku mace da aka kawo wato Madam Aliya wacce nayi silar mutuwarta ta hanyar doke motar ta da trailer, da kaina nake tuƙin babbar mota trailer nayi fushhhh na doke motar ta, domin ta maye mun gurbin shugabanci nah a gidan marayu, Ni kuwa bazan juri ganin haka ba, ohhhh ashe dai ke baki santa ba lokacin nasa an sace ki sorry! sorry!! sorry!!!, ki dai gaishe ta kinji ko?..." Yana ƙarisawa ya hankaɗata gaban Guess sannan ya wulla masa wuƙa yana faɗin "yanzun nan ba tare da ɓata lokaci ba ka yanke mata maƙogaro..." Guess yanjo ta yayi tare da ɗora mata wuƙar akan wuya ya ɗaga mata haɓar ta sama, Yallaɓai wani irin murɗaɗɗen murmushi yayi ya ce "ehen gurza mata wuƙar..." Guess dai ya kasa ai watar wa wuƙar kawai ya ɗora mata amma ya kasa gurzawa, Yallaɓai ganin Guess bazai yanka ba yasa ya fitar da ƙaramin bindigar sa ya saita kan Guess yana faɗin "Guess kafin na ƙirga 1 zuwa 5 ka yanke mata maƙogaro in ba haka ba saina fasa maka kai sannan itama na kashe ta, ta tabbata kenam kai ka barta ta gudu ko?..." Shuru Guess ya kasa aiwatar wa, Yallaɓai ne ya fara ƙirge kamar haka "I, 2, 3..." Guess ganin Yallaɓai da gaske yake kuma yana matuƙar tsoron mutuwa a hankali ya fara danna wuƙar yana shiga a hankali, nan jini ya fara zubowa sakamakon shigarta da wuƙar ya fara yi... Yallaɓai ganin haka yasa ya dakatar da ƙirgen still bindigar tana hannun sa..... Ɓangaren su Roshan da Baiwar ALLAH sa har zuwa wannan lokacin bata bashi haɗin kai ba, ko kaɗan bata son haɗa ɗaki ɗaya da shi... Tana kitchen taji shugowar mutum da sauri ta waiwaya ganin Roshan ne yasa ta haɗe rai tare da juyawa ta cigaba da aikin ta, A hankali ya furta "good morning Ammata..." Bata kula shi ba ta cigaba da aikin ta, ya ce "dan ALLAH zan iya sanin laifi na? ki sanar mun a yanzu zan iya durƙusa miki na baki haƙuri, amma kina azabtar dani Ammata, shin yaushe zaki bani lokaci na ne a matsayina na mijinki?..." Juyowa tayi tana kallonsa fuska a haɗe ta ce "babu rana, bare wata bare kuma shekara, tunda har ka Aure Ni a haka sai kuma ka cigaba da zama dani a haka har sai ran da ka gaji da zama dani..." tana kaiwa nan tayi ficewar ta, ta bar shi a kitchen shi kaɗai.... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://chat.whatsapp.com/ERHR7h6oEY76fTvAQFZauw https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *15_ TO_16* Ƴar Amana har ta fara shiɗewa sakamakon wuƙar da ya ke shigar ta a hankali, ga jini har ya wanke gaban rigar ta. Yallaɓai yana riƙe da bindiga a saitin kan Guess kwatsam yaji bullet ya shigar masa hannun da yake riƙe da gum ɗin, a firgice ya jefar da bindigar hannunsa yana kallon yanda aka harbo bullet, gani yayi Elekwabtan Sojoji yana shirin sauƙa har guda biyu kuma duk a cike da Sojoji, Yallaɓai ganin haka yasa ya yi gudu ya shige cikin daji yana riƙe da hannunsa da aka harba, shima Guess jefar da wuƙar hannunsa ya yi tare da tserewa, haka duk yaran Yallaɓai suka fara guduwa suma Sojojin dirƙowa suka rinƙa yi suna bin bayan su, iya Razhdeen da Mohandas ne kawai suke tsaye a wurin. Razhdeen ido ya zaro sosai ganin halin da Ƴar Amana take ciki domin kallo ɗaya yayi mata ya gane ta dake ba kowa ne zai iya gane ta ba saboda Askin da aka mata babu alamun gashi.. Ƴar Amana itama a tsaye take idonta na kallon dishi-dishi amma da haka ta iya gane Razhdeen, kafa masa shanyayyun idanuwanta tayi waɗanda suke shirin rufe wa, ga kuma wuya yanda aka fara yanka wa, ganin idanuwanta ba ƙarya suke gane mata ba shi ɗin ne Razhdeen yasa ta fara takawa da gudu tana yowa kansa, duk da a halin da take ciki amma bai hanata gudu ba ga wani irin hajijiyar da take ji, har tayi kusan zuwa dab da shi aka harbo mata kibiya ta baya, ido ta zaro waje jin an soketa ta baya, tangal-tangal ta fara yi zata faɗi ƙasi Razhdeen ya yi saurin riƙo ta a ruɗe, rungumarta yayi sosai idonsa akan kibiyar dake soke a bayanta, gani yayi kamar an ƙara jefo da kibiyar a karo na biyu ya yi saurin juyar da ita ya kasance shine a gurbin ta, ai kuwa kibiyar bata sauƙa a ko ina ba sai a bayan Razhdeen yana rungume da ita, sake jefo da wata kibiyar akayi a karo na uku nan ma ya sake sokar Razhdeen ko motsa wa baiyi ba ya rungume Ƴar Amana sosai idanuwansa a lumshe domin kibiyoyin ba ƙaramin sokarsa suka yi ba, A wannan lokacin ne Mohandas ya saita yanda ake harbo da kibiyar da bindigarsa nan take ya harbe saitin goshin wanda yake harbowa, ba kowa bane illa Yallaɓai, daga nan Yallaɓai bai ƙara shurawa ba domin goshin sa aka samu da bullet, Mohandas ne ya ja Razhdeen tare da Ƴar Amana cikin Elekwabta tare da yara ƴan matan da suke wurin duk aka sassaka su da sauran Sojojin duk suka shiga jirgin ya tashi suka tafi, ɗayan Elekwabta kuma masu laifin da aka kamo duk ɗinsu ne aka sassaka su a ciki har da Guess suma suka tafi, bayan sun je sama sosai Sojojin suka jefo da bom gaba ɗaya wurin ya tashi duk abubuwan su suka tarwatse... Razhdeen da Ƴar Amana ba ƙaramin jikkata suka yi ba domin kibiyar yana da dafi sosai dafin har ya ratsa jikinsu, especially Ƴar Amana ita daman ga wuyan ta da aka fara yanka wa, Cikin lokaci ƙanƙani suka isa cikin gari, Razhdeen ne ya yi musu alama da hannu cewa kada su tsaya a ko ina sai gidansa baya buƙatar zuwa hospital, hakan kuwa akayi sauran ƴan mata kuwa da masu laifukan duk headquarters aka wuce da su. Mohandas ne ya shiga da Razhdeen wani soja kuma ya shigo da Ƴar Amana, kai tsaye part ɗin Razhdeen aka wuce da Ƴar Amana dake can cikin falo na biyu, shi kuma Razhdeen sai aka shigar da shi bedroom dake falo na farko, shi ya bada umarnin haka domin baza'a rasa masu zuwa duba shi ba kuma baya so asan Ƴar Amana tana nan, ya sanar wa Mohandas shima cewa baya son kowa yasa Ƴar Amana tana hannun sa... A lokacin yasa aka ƙira masa wani Abokin sa babban Doctor yazo shi kaɗai da kayan aiki domin an sanar masa cewa Razhdeen ne ya samu hatsari kuma ba'a buƙatar zuwa hospital, bayan wasu mintuna sai ga Doctor ya zo da akwatin kayan aiki a hannun sa, da sauri ya yo kan Razhdeen zai duba shi bayan ya isko shi a bedroom. Razhdeen yana kife akan gado babu riga a jikin sa ga kibiyoyi guda biyu da Mohandas ya cire masa akan drower, Razhdeen ido a lumshe murya ciki-ciki ya ce "kuje ku fara duba Yarinyar tana cikin mawuyancin hali..." Doctor da Mohandas ne suka fice da sauri kai tsaye ɗakin da aka ƙwantar da Ƴar Amana suka nufa domin tafi jikkata sosai wanda a halin yanzu ba'a sani ba ko tana raye ko kuma ta mutu.. Doctor yana samun ta a wannan yanayin shi kansa sai da ya tsorita ganin ana shirin yanka mata wuya ga kibiya yanda aka cire mata a baya, babu alamar numfashi a tattare da ita. Girgiza kai Doctor ya yi sannan ya ce "wannan aiki ai sai hospital bana aikin gida bane domin akwai abubuwan da ake buƙatar yi mata a hospital..." Mohandas ya ce "aikin ba zai yu a gida bane?..." Doctor ya ce "zai yu mana amma zai fi kyau a kaita hospital..." Mohandas ya ce "to in har zai yu kayi abinda Major ya ce kawai, jinyar ana so ayi shi cikin sirri ne ba tare da kowa ya sani ba, hakan yasa muka ƙira ka ai mun san da hospital muka ƙira ka, ka dai san halin mutumin nakan kawai kayi aikin da ya dace..." Doctor ya ce "okay ai sai ku mun bayani tin farko, insha Allahu zanyi iya ƙoƙari na..." Daga nan Doctor ya fara cire kayan aikin sa shi kuwa Mohandas fice wa yayi domin ba'a son a tsaya akan majinyaci idan ana masa aiki... Abinda Doctor ya fara yi shine ɗinke mata wuya sannan ya sanya mata bandeji ya ɗaure wuyan, sannan ya juyar da ita ya fara ɗinke mata wurin da aka soke ta da kibiya sai da ya gama treat ɗinta sosai sannan ya buƙaci a ɗaura mata laidar jini domin ta zubda jini sosai.. Bayan an sanar wa Razhdeen sai ya buƙaci a ja nashi jinin, Doctor bai yadda da hakan ba sakamakon shima ya zubda jini sosai kuma bai juma da bawa Baiwar Allah jini laida biyu ba, kuma son samu sai ya yi wata biyu kafin ya ƙara bada jininsa, duk da anyi masa wannan bayani amma fur Razhdeen yaƙi yadda wai shi sai an ja mata jininsa, babu yanda kowa ya iya a cikin su haka aka ja jininsa aka je aka ɗaura wa Ƴar Amana... Bayan an gama da ita shima aka zo akayi treat ɗinsa sosai, daga nan Doctor ya yi tafiyar sa... Bayan kwana biyu da faruwar haka sai a lokacin su Abbah suka ji labarin abinda ya faru da Razhdeen, hankalin Abbah ba ƙaramin tashi ya yi ba ko jinkiri baiyi ba haka ya kama hanya da sojojinsa masu raka shi zuwa gidan Razhdeen, a ruɗe Abbah ya shiga cikin wantalelen gidan bai tsaya a ko ina ba sai a babban falon gidan, anan ya tarar da Razhdeen yana zaune a kujerar falon ga jiki fari sol babu riga sai tilin bandaje, ga kuma Mohandas ata gefen sa shima dake shine mai masa duk ɗawainiyoyinsu shi da Ƴar Amana, Abbah zama yayi yana facing ɗin Razhdeen ya ce "Razhdeen ashe akwai abinda zaka iya ɓoye mu dan gane dakai? idan ka ɓoye mun komai ai bai kamata ka ɓoye mun rashin lafiyar ka ba kuma a wurin yaƙi haba Razhdeen? shin ka kyauta mun kenam? ban tashi jin maganar ba sai a television cewar kun ceci wasu yara da aka yi kidnaping ɗinsu har kaima kaji rauni sosai..." Razhdeen sunkuyar da kansa ya yi ƙasi yana sauraron Abbah, sai ji ya yi Abbah ya ƙira sunan sa cikin sassanyar murya, Razhdeen ɗagowa yayi yana kallon Abbah, Abbah ya ce "yanzu ya jikin nakan?..." Ya ce "naji sauƙi..." Abbah ya kuma cewa "Sosai?..." Kai Razhdeen ya ɗaga masa.. Mohandas already ya bar wurin tin shugowar Abbah, ya gaishe da Abbah amma sam yaƙi sauraronsa.. Abbah ya juma sosai a wurin Razhdeen kafin daga baya ya yi tafiyar sa ya sanar masa cewa zuwa dare zai ƙara zuwa ya duba shi... Bayan fitar Abbah ba jumawa sai ga Roshan da Baiwar ALLAH sun shugo, gaba ɗaya hankalin Baiwar ALLAH akan Razhdeen yake, zumuɗinta tazo taga a wani hali yake ciki domin tinda taji labarin hankalinta yaƙi kwanciya, Roshan shi kaɗai yayi niyar zuwa ya duba twins ɗinsa amma Baiwar ALLAH ta dage akan cewa zata zo duba shi itama, babu yanda ya iya haka ya taho da ita... Roshan ba ƙaramin tausayawa twins ɗinsa ya yi ba ganin a halin da yake ciki, bayan sun kammala gaisawa ya kalli Baiwar ALLAH sannan ya ce "Ammata ganan My Man ki gaishe shi da jiki mana, kinyi shuru bayan ke kika damu akan zaki zo ki gànshi..." Jin haka yasa Razhdeen ɗagowa ya kalle ta sannan ya kawar da kansa gefe tare da haɗe gira, saboda ya tuna maganganun da ta rinƙa yi a hospital wanda sam bai ji daɗin hakan ba. Itama kallon sa tayi gaba ɗaya kamar wanda aka ɗaure mata baki, ta kasa cewa komai lokaci guda taga yayi mata wani irin Mungun kwarjini da kuma shakkarsa, wani irin harara ya wurga mata ta wutsiryar ido ba tare da Roshan ya gani ba, da sauri ta sunkuyar da kanta ƙasi kamar zata fashe da kuka... Roshan ne ya ce "am ina Mohandas yake ne?..." Razhdeen murya ciki-ciki ya ce "yana ciki..." ya nuna yanda yake da hannu can part ɗin da aka ƙwantar da Ƴar Amana.. Shi sam ya manta da cewa a part ɗin Ƴar Amana take sai daga baya ya tuna, da sauri ya juya zai yi wa Roshan magana yaga har ya tashi ya nufi part ɗin, Razhdeen bai damu ba saboda yasan Roshan idan aka sanar masa cewa secret ne bazai sanar ba... Ɗagowar da zai yi kwatsam suka haɗa eyes da Baiwar ALLAH ta zuba masa ido ko ƙibgawa babu, cike da mamaki ya ce "what are you looking for?..." Ciki ƙwarin gwiwa ta ce "You..." haɗe fuska ya yi tare da faɗin "whatt?..." Roshan kai tsaye upstairs ya haura room ɗin farko ya fara buɗe wa yaga babu kowa still ya yi gaba ya buɗe room na biyu sai kawai ya tarar da Mohandas zaune kan kujerar ɗakin yayi tagumi kansa na kallon ƙasi, Roshan har zai yi sallama idonsa suka sauƙa akan Ƴar Amana dake kwance saman gado, sake baki yayi yana kallon wurin, daga bisani ya ce "Marshall aina ku ka samo yaro?..." A ruɗe Mohandas ya ɗago yana bin Roshan da kallo ganin ya yi masa shugowar bazata, Ƙarasa shugowa ya yi still yana faɗin "yaron nan fa meya same shi?..." Mohandas ya ce "samu wuri ka zauna tukun, wannan ba yaro bane yarinya ce..." Haɗe gira Roshan ya yi tare da faɗin "taya ya zai zamo mace bayan ga kansa a tanɗe kamar lale kobo..." Mohandas ya ce "bazaka fahimta bane in har ba bayani aka yi maka ba..." Roshan ya ce "okay ina jinka..." Mohandas ya ce "kai ma kasan kalar mafarkin da Razhdeen yake yi ko? kuma kasan me yake ƙunshe acikin mafarkin, yarinyar da yake gani koda yaushe a cikin mafarkin ba kowa bace illa wannan yarinyar, tin da Allah yasa Razhdeen yayi ido huɗu da yarinyar bai sake yin mafarkin nan ba sakamakon kasan itace maganin mafarkinsa..." Nan Mohandas ya sanar wa Roshan duk halin da ake ciki da irin ƙalubalen da yarinyar ta fuskanta a hannun mutanen nan, Roshan yana tsaye bai san lokacin da ya nemi wuri ya zauna ba, yayi matuƙar tausayawa yarinyar kuma yana mamakin meyasa take yawan fitowa a cikin mafarkin Twins ɗinsa, tambayoyi ne tarin-tarin a cikin zuciyarsa. Mohandas ne ya kuma cewa "mun ɓoye ta ne a cikin gidan nan ba tare da kowa ya sani ba, kuma bama buƙatar kowa ya sani daga Ni sai kai sai kuma uban gayyar wato Razhdeen da kuma likitan da yayi musu magani..." Roshan ya ce "to amma meyasa Twins ya damu da yarinyar har haka?..." Mohandas ya ce "meyasa bazai damu da ita ba? ita ce fa mafarkinsa..." Jinjina kai Roshan ya yi sannan ya ce "Okay ba damuwa zamu cigaba da tsare ta ba tare da kowa ya sani ba Insha Allahu..." Mohandas ya ce "gud! Amm daman Roshan inaso zanyi magana da kai Please..." Roshan ya ce "about Minal ko?..." Mohandas ya ce "of course, sannan Abbah yazo na gaishe shi amma he didn't answer me I don't know why..." Murmushi Roshan ya yi sannan ya ce "kafi sanin kowa dalilin da yasa ba zai kula ka ba, amma mun kusan kawo ƙarshen wasan..." Mohandas ya ce "tayaya kenam?..." Roshan ya ce "ta hanyar ɗaura muku Aure ba tare da kowa ya sani ba, tinda Allah yasa kai ka musulunta, idan Abbah yasan ka musulunta ma bazai taɓa Aura maka ɗiyarsa ba saboda iyayenka kuma na farko ba shiri suke yi ba..." Mohandas ya gamsu da bayanan Roshan yasau numfashi tare da faɗin "Nima iyaye na baza su taɓa sani ba sai lokacin da aka kawo ƙarshen wasan, don haka Roshan inaso a cikin satin nan a Aura mun Meenat ko hankali na zaifi kwanciya Please..." Roshan ya ce "a kwai wurin da zamu je a ɗaura gobe da safe Insha Allahu, domin har nayi magana da malaman wurin, za'a yi hakan ba tare da My Twins ya sani ba tinda ya nuna shima baya son harkar munafurci..." Jinjina kai Mohandas ya yi tare da faɗin "that's gud, but ita Meenat da ita zamu je?..." Roshan ya bashi amsa da "Eh". Sai da suka kammala tattaunawarsu tsab tukun suka baro ɗakin, Ƴar Amana har zuwa ɗan kwanakin nan bata samu farfaɗowa ba.. Razhdeen suna zaune zaman kurmanci babu wanda ya kula kowa a tsakanin sa da Baiwar ALLAH, sai dai su kalli juna su kawar da kai amma ko wannensu da saƙe-saƙen da yake a cikin zuciyarsa, Razhdeen ganin har yanzu su Roshan basu fito ba yasa shi miƙe wa zai bi bayansu, ai kuwa nan bayansa ya riƙe sosai haka ya yi baya zai faɗi da gudu Baiwar ALLAH tayo kansa ta rungume shi sosai tana ƙoƙarin tare shi, dai-dain lokacin da su Roshan suka fito, idonsu ne ya sauƙa akan Baiwar ALLAH yanda ta rungume shi, shi kuwa ya dafa saman kujera da hannunsa ɗaya, ba wai riƙe shi da tayi ne yasa bai faɗi ba domin bata da ƙarfin da zata tare shi idan yazo faɗuwa, already ya rigada ya dafe kujerar, ita dai kawai ta an ƙara ne domin a tsorace tayo kansa kamar wanda take jira ya goce... Ganin yanda ta rungume shi ne yasa shi fusata da ɗayan hannunsa ya hankaɗata baya har sai da ta doku akan kujerar da take before, Komawa yayi ya zauna yana binta da kallon takaici ya ce "You are ingratitude fool, Nonsense girl wannan wani irin hauka ne? shin idan aka barki zaki iya dakatar da ni ne idan nazo faɗuwa? bana son wannan gangancin kada ki sake mun irin haka na gaya miki idan kuma ba haka ba sai na miki abinda bakiyi zato ba, mtsws useless girl..." Ita kuwa baiwar ALLAH kanta a ƙasi ba abinda take sai kuka domin ba ƙaramin ci mata mutunci yayi ba... Roshan da Mohandas ne suka ƙarasa shigowa cikin falon bayan sun gama jin duk chakwakiyar da suke yi, Roshan ne ya zaune kusa da Razhdeen tare da dafa kafaɗarsa ya ce "haba My Man abun gwaninta fa tayi maka bai kamata kayi mata haka ba, Please am so sorry na amshi bakin ta..." Razhdeen kallonsa yayi fuska a haɗe ya kuma kawar da kansa gefe yana faɗin "ka tashi ka fice mun da ita daga gida, next time idan har kasan da ita zaka zo mun to kaima kayi zaman ka bana buƙatar ku..." Murmushi Roshan ya yi tare da faɗin "duk mai ya yi zafi haka My Man?..." Tsuka Razhdeen ya yi tare da ƙoƙarin tashi zai bar wurin, kasa tashi yayi sai da Mohandas ya tallafa masa tukun daman shine mai taimaka masa da wasu abubuwa, suna tafiya hankali sai da suka ɗan yi nisa kaɗan sannan Razhdeen ya waiwayo idonsa akan Roshan wanda shima miƙewa yayi zasu tafi ya ce "Please kana zuwa kana duba mun jikin Yarinyata..." Da murmushi kwance saman fuskar Roshan ya ce "Okay ana kan duba ta zata samu sauƙi Insha Allahu, naga jikin natan ya fara warware wa kawai farfaɗowa ne bata samu damar yi ba..." Razhdeen bai bashi amsa ba ya juya gaban sa, Mohandas ne ya kuma cewa "kar ka manta Yarinyar kasan a Kashmir take..." Roshan ya ce "Okay don't worry..." Duk sunyi wannan maganar ne saboda kar Baiwar ALLAH ta fahimci wani abu.. Da haka suka kammala Roshan ya ja matarsa suka tafi, Razhdeen kuma kai tsaye room ɗin da Ƴar Amana take ya nufa shi da Mohandas domin hawan upstairs zai bashi wahala indai ba riƙe shi akayi ba ... Baiwar ALLAH wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne ya daki saitin zuciyar ta jin Razhdeen ya ambaci sunan wata da Yarinyarsa, Da wannan tunanin a cikin zuciyarta suka isa gida.... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *17_ TO_18* WASHE GARI Baiwar ALLAH ne zaune akan sopar falon ta tana kallon plasman abin ta, Daga ganin yanda take ta zuba murmushi kasan Film ɗin yayi matuƙar burge ta, Minal ce ta shigo tana lanƙaye da handbag ɗin ta ko sallama bata samu damar yi ba, tazo ne saboda Roshan ya riga da ya sanar wa Abbah cewa zasu fita unguwa, Baiwar ALLAH a bazata taji Minal ta ce "ina Yaya Roshan?..." Baiwar ALLAH ɗago wa tayi tana binta da kallo ko amsa bata ba ta ba. Minal ta ce "Malama magana nake miki dai ko dai kin kurmance ne?..." Baiwar ALLAH cewa tayi "ai naga baki yi sallama ba ne..." A fusace Minal ta ce "saboda nan ɗin gidan Ubanki ne? ke ki dakata kiji saboda Abban mu ne yasa muke respecting ɗinki Albarkacin kina Auran Ɗan uwan mu amma wallahi baki isa ki gaya mun maganar banza ba, saboda ko ba komai nasan na girme ki sosai..." Baiwar ALLAH dai shuru tayi bata ce mata komai ba sai cigaba da kallonta da ta yi, Minal tsabar ƙololuwar baƙin ciki bata san lokacin da ta fincikota ƙasin carpet ba tare da faɗin "ba magana nake miki ba dan ubanki, aikin banza kawai idan baya nan ki sanar mun mana..." Baiwar ALLAH ɗagowa tayi tana kallon ta dai-dai lokacin da Roshan ya fito daga part ɗinsa dake cikin falon gaba ɗaya, Idonsa ne ya sauƙa akan Baiwar ALLAH wacce take baje a ƙasin, ƙaraso wa yayi dab da ita tare da miƙa mata hannu zai ɗago da ita, ba tare da ta miƙa masa ba ta tashi da gudu tana kuka ta wuce part ɗinta... Roshan kallon Minal yayi sannan ya ce "mai kika mata ne?..." Minal tana yamutsa fuska ta ce " Yarinyar ce tana da raini wallahi, na shugo ina mata magana tayi wani banza da ni..." Roshan ya ce "Minal kin dai san mata ta ce ko? kamar yanda kike respecting ɗina ya zama dole itama kiyi mata, idan kika raina ta toh kamar ni kika raina ne, so be careful..." Maganganun Roshan ba ƙaramin ƙona mata rai ya yi ba, kamar zata yi kuka ta ce "Sorry in ba dan uzuri ne ya kawo ni ba babu abinda zan zo yi ɓangaren ta tinda ita batada mutunci..." Roshan ya ce "okay zaki iya tafiya Minal..." Cike da mamaki take bin sa da kallo ta ce "wurin da zamu je fa?..." Juyawa ya yi zai koma ciki ya ce "babu ruwa na da lamuran ki, kije kiyi duk abinda kika ga dama..." bata san lokacin da ta fara kuka ba tana faɗin "Yaya Roshan dan ALLAH kayi haƙuri wallahi in har bada taimakon ka ba babu yanda zanyi na samu Marshall, Abbah yana shirin haɗani da wani Abokinsa kaima kasan da haka, ya hanani fita ko ina koda wurin aiki ne, sojojin gidan suna nan koda yaushe babu halin fita ba tare da kai ba, wallahi ina son Marshall inaji a jikina bazan iya rayuwa ba tare da shi ba, shekaru na sunata ja ina buƙatar yin Aure ga wanda nake so, ka taimaka..." Roshan tsayawa yayi yana sauraron ta daga bisani ya ce "Okay kije ki bata haƙuri tukun..." Tana kuka ta ce "bazan iya ba Yaya Roshan..." Tana share hawaye tayi ficewar ta.. Shi kuwa girgiza kai ya yi yana faɗin "girman kan ki Minal shi yake azabtar da ke..." Shima wuce wa yayi ya nufi room ɗin Baiwar ALLAH yana zuwa ya samu ƙofar a ƙarƙame yayi bugawar duniya amma taƙi buɗe wa haka ya haƙura ya wuce room ɗinsa... Minal tana fita daga part ɗin Roshan kai tsaye wurin swimming pool ta nufa tana kuka.. Tana zuwa ta jefar da handbag ɗinta a gefe tare da mayafin ta, tazo dab da bakin ruwan zata faɗa ciki taji anyi saurin dakatar da ita, Da sauri ta waiwaya tana bin Roshan da kallo wanda ya biyo bayanta bayan yayi tunanin halin da zata iya shiga, Ƙaraso wa wurin ta yayi tare da faɗin "meye kike shirin aikata wa? Minal daman zaki iya hallaka kan ki akan soyayyar ki?..." Tana kuka ta ce "Yaya Roshan babu wanda ya damu da damuwa ta, ina cikin wani halin da ba kowa ne zai fahimce ni ba, kai ma da kake son taimaka mun yau kana shirin juya mun baya saboda matar ka..." Nan ta fashe da kuka sosai, Riƙota yayi yana faɗin "lolz my bloody bai kamata ki yanke wannan hukunci a kanki ba, kiyi haƙuri ina tare da ke, yanzun muje mu tafi ko..." Rufe bakin ta tayi da hannaye biyu tana dariyar farin ciki, cikin nuna farin ciki ta ce "Nagode sosai Yayana..." Ya ce "don't worry let's go..." Anan ta ɗauki mayafinta da jakar ta suka tafi tare, Already sunyi sallama Ammy Amaryar Abbah da Abbah cewa zasu je shopping, sai bayan sun dawo zasu sanar da duk abinda ya faru... Iya su biyu suka shiga mota ba tare da security ba Roshan shi yake driving, sojojin bakin gate ganin Roshan ne yasa suka buɗe masa gate, Kai tsaye wurin da za'aje a ɗaura Auren suka nufa, Mohandas kuma Roshan ya tura masa da Address yanda suke saboda in har yaje gidan Razhdeen ɗaukar sa za'a samu matsala sakamako sojojin da suke gidan Razhdeen zasu iya sanar wa Abbah halin da ake ciki... Mohandas shima fita yayi da motarsa ba tare da Razhdeen ya sani ba.. Wasu manya-manyan malamai Roshan ya tara a wani office na ƴancin kai, ba ƙaramin manyan kuɗaɗe aka basu ba amma sai dai shaidun basu fi su goma ba, A ranar ne aka ɗaura Auren Minal da Mohandas ga Roshan wanda yake tsaye shima aka yi amma hankalinsa gaba ɗaya ba'a jikinsa yake ba, tunaninsa taya zai fara tunkarar Abbah da wannan maganar... A wannan ranar kwata-kwata Roshan bai rintsa ba, kuma bai sanar wa Abbah halin da ake ciki ba, a yayin da Minal take cikin farin ciki, tana kwance a ɗakinta da waya a hannu alamar video call take bada kowa ba sai da mijinta Mohandas, shima yana cikin farin ciki ta wani ɓangaren kuma yana tunanin kalar hukuncin da Abbah zai ɗauka idan yaji wannan batun, gaba ɗaya a tsorace yake, ita kuma Minal bata tunanin komai kuma bata jin komai a ranta, abu ɗaya ne yake damunta shine rashin kasancewar ta tare da mijinta... Roshan sai da yayi kwana uku yana inda-indar sanar wa Abbah, sai a yau ya cire fargaba ya gayyato Mohandas zuwa gidan su a yau za'a sanar wa Abbah dake yau ranar hutunsa ne babu fita aiki... Mohandas yana zuwa Sojojin suka buɗe masa gate ya shige already Roshan ya sanar musu cewa Mohandas zai zo ba tare da Abbah ya sani ba, Roshan ne tsaye a wurin parking yana jiran isowar Mohandas cikin lokaci ƙanƙani sai gashi ya iso, a tare suka nufi babban falon gidan suna shiga suka tarar da Ummy uwar masu gida ita da Ammy da kuma Baiwar ALLAH zaune suna karatun wani ɗan littafin hadisi, da dukkan alamun Ammy ce take koya musu wasu abubuwa a cikin littafin, jin sallama yasa duk suka ɗago tare da amsa sallamar. Ummy zaro ido waje tayi ganin Mohandas ɗan maƙiyin Abbah kuma shima maƙiyin ne tinda yana neman ɗiyarsa, Ammy kuma dake bata san Mohandas ba yasa ta fara sakin murmushi tana faɗin "babban baƙo mukayi ne? sannu da zuwa Roshan ga wuri ku zazzauna..." Hakan kuwa akayi duk zama suka yi, Ammy kuma tashi tayi ta shige kitchen zata haɗo musu abin taɓawa, Uwar masu gida kuma itama tashi tayi da haura saman upstairs da gudu zata je ta sanar wa Minal cewa ga Mohandas a gidan su, sai ya rage iya Baiwar ALLAH a falon, idonta akan Mohandas sau ɗaya ta taɓa ganinsa ran da suka je gidan Razhdeen nan ma bata ƙare shi da kallo ba sai yau, haka kawai take jin tsinkar jikinta yana tashi ga wani irin bugun zuciya, ta rasa meye dalilin faruwar wannan al'amarin, shima Mohandas ɗin kallon ta yake ya dai san itace Amaryar Roshan amma bai gaba saninta ba sai yau shima yana jin wani abu sosai a kanta, Idon Baiwar ALLAH ne suka sauƙa akan wani ɗan sarƙar dake ɗaure a hannunsa shigen irin nata, sai dai ita a wuyanta yake ɗaure kuma akwai mayafi a kan ta balle ta sake ganin kalar natan, ƙirjinta ne yake wani irin bugawa sosai, A lokacin ne Abbah ya fito daga part ɗinsa wayar sa a ɗore kan kunne sai muryarsa kake ji yana ta waya, da haka ya gama sauƙowa daga upstairs idonsa ne suka sauƙa akan Mohandas kamar wanda aka ɗauke masa wuta haka ya tsaya cakk. Itama Minal fitowa tayi da gudu ita da Ummy suka sauƙo falo, Ammy ce ta jejjera musu kayan abinci akan table ɗin falo saitin gaban Mohandas, Abbah ne ya sanar a wanda yake waya dashi cewa "Please I'll call you back, cut the phone..." Still idonsa akan Mohandas, shima Abbah zama yayi yana fuskantar su ba tare da ya ce komai ba.. Jikin Mohandas ne ya fara rawar sanyi ganin yanda Abbah ya chanza cikin lokaci ƙanƙani, A fusace Abbah ya ce "meya kawo ka gida na?..." Mohandas kasa magana yayi sai Roshan ne ya yi ƙarfin halin cewa "Am Abbah daman akwai maganar da muke so muyi ne..." Abbah ya ce "nasan akan maganar Amina ne ko? wai shin dole sai ɗiyata zai Aura ne? nace bazan taɓa haɗa jini da familyn su ba kuma babu mahalukin da ya isa yasa na haɗi, dan haka ya tashi ya bar mun gida tin kafin na fusata..." Roshan ya ce "dan ALLAH Abbah ka saurare ni..." Abbah ya kalli wurin da Mohandas yake a zaune ya ce "saboda kai na hana ƴata zuwa wurin aiki, na hanata fita ko ina, shin me kake yi a Nigeria da har yanzu bazaka koma ƙasar ku ba, na hanaka tarayya da ƴata ka ƙi, to ƴaƴana mazan ma zan hanaka tarayya dasu saboda haka daga yau zamanka a gidan Razhdeen ya ƙare, na datse Abotar ta kun, sannan Roshan ma kada ka sake shiga sabgarsa na gaya maka, in har ba haka ba zanje na samu mahaifinka na ja masa kunne ya dakatar tinda ni ban isa da kai ba, idan ba haka ba gavar da nake da mahaifinka zai ƙara ninkuwa ne kuma wallahi sai mun shiga kotu da ku..." Abbah tashi yayi zai koma ciki Roshan ya ce "Abbah Please ka bamu lokacin ka..." Abbah a fusace ya juyo yana faɗin "Roshan ka maida hankalinka na gaya maka, ka fitar mun da wannan ƙabilan a cikin gidan nan..." Ammy da ta kasance bata san komai ba amma a yanzu ta fahimta domin taji labarin Minal da Mohandas, Baiwar ALLAH itama tana wurin akayi komai gaba ɗaya hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba, ga bata san dalilin da yasa take jin tausayin Mohandas haka kawai ba, Uwar masu gida har da kukan ta. Abbah har zai motsa ya tafi yaji Minal ta buɗe baki tana kuka ta ce "Abbah wallahi inason Mohandas kuma bazan taɓa rabuwa da shi ba, sai dai kayi haƙuri amma aikin gama ya rigada ya afku tinda akwai Aure a tsakanin mu..." Ba Abbah ba hatta waɗanda suke wurin babu wanda bai girgiza da jin abinda Minal ta furta ba banda Roshan, A firgice Abbah ya ce "whattttt!!!???..." Murmushin takaici yayi ya kalli Roshan ya ce "kaine silar faruwar hakan ko? Minal bata fita ko ina sai da kai saboda na yadda dakai Roshan ashe kaima zaka iya cin Amana ta? Amma ka cuce ni Roshan saboda in ba dan kai ba babu yanda za'ayi Minal tabar gidan nan saboda tsaron da na sa mata, ban sa a raina cewa hakan zata faru ba saboda na yadda da kai, shiyasa duk abinda kace mun nake Amince maka..." Roshan gaba ɗaya jikinsa ne ya yi sanyi, bai san lokacin da ya fara zubda hawaye ba, sai yanzu ya yi nadamar aikata hakan..." Abbah kallon Minal yayi tare da faɗin "kin kyauta, amma ki sani cewa bazai bar gidan nan ba tare da ya baki takardar sakin ki ba..." Tana kuka ta ce "Abbah ya musulunta fa..." Wani irin gigitaccen tsawa ya daka mata tare da faɗin "ko Alqur'ani ne a jere a kansa bazaki shiga familyn su ba, babu jini na da zai zauna da familyn su nayi Alƙawarin haka..." Ya maida kallonsa kan Mohandas sannan ya ce "inaso a yanzun nan ka furta kalmar saki wa ƴata a yanzu..." Ammy ce ta buɗe baki ta ce "Chief indai ya musulunta ka barsu kawai dan ALLAH, kar a toye musu hakki..." Abbah ya ce "bana chanza magana idan nayi..." Sai a wannan lokacin Mohandas ya buɗe baki shima wurin cewa "kayi haƙuri Abbah bazan iya sakin ta ba..." A fusace Abbah ya ce "haka kace ko? to ku jira Ni ina zuwa, yau zan nuna muku zamani na ya ninka naku sau ba adadi..." ABBAH yana kaiwa nan da sauri ya haura upstairs domin akwai abinda yake son ɗauko wa (kodai gum ɗinsa zai ɗauko 🤣🤣) Ammy ce ta bi bayansa itama tana so naje tayi roƙo, Bayan su Abbah sun haura Roshan da gudu yabi bayansu, yana haurawa can part ɗin da suke, jawo ƙofar room ɗinsu yayi tare da murɗa key yabar key ɗin a jikin ƙofar sannan ya dawo yana ce musu "Marshall ka kama matarka ku tafi duk yanda ya kamata, kada ka bari kowa yasan yanda kuke domin Abbah zai iya sawa a nemo ku a duk yanda kuke, daga nan ka wuce airport ku bar ƙasar..." Girgiza kai Mohandas yayi alamun bazai iya ba, Minal ta ce "Dan ALLAH Mohandas kazo mu tafi kafin Sojojin gidan su ankara kaga yanzu basu san halin da ake ciki ba..." Jin haka yasa Mohandas riƙo hannun Minal suka fice, Roshan ne yabi bayansu saboda yana so ya fita dasu kar Sojoji su fahimci wani abu, Hakan kuwa akayi motar Mohandas suka shiga, Mohandas shine mai driving sai Roshan a gefen sa, Minal kuma tana ta back seat da haka suka fice a gidan gaba ɗaya kai tsaye airport suka wuce... Abbah da Ammy suna cikin bedroom ɗinsu sai ji sukayi an ƙarƙame su, ga bindiga a hannun Abbah yayi ƙolon duniya akan azo a buɗe mishi ƙofa amma babu wanda ya nufi wurin, ga wayar sa ya barta a falo balle ya ƙira sojojin gidan gaba ɗaya Abbah ya rasa mai yake masa ciwo, ita kuwa Ammy alwalarta tayo tazo ta tsaida sallah domin a halin yanzu Abbah ba sauraronta zai yi ba, Baiwar ALLAH tana so taje ta buɗe musu ƙofar jin yanda Abbah yake ta ƙiraye-ƙirayen sunayen su especially sunan Uwar masu gida yafi ƙiran ta akan taje ta buɗe amma Ummy fur taƙi zuwa sannan tana riƙe da hannun Baiwar ALLAH taƙi sakin ta, Ummy tana kuka ta ce "haba Aunty Dota har yaushe za'a kawo karshen wannan bala'in ƙiyayyar Abbah da su familyn Yaya Mohandas? Aunty Minal da Yaya Mohandas suna matuƙar ƙaunar junan su hakan yasa bazata iya Auran kowa ba kuma kinsan a halin da take ciki, ita fa ba ƙaramar yarinya ba ce, tanada matsalar matsinancin sha'awa amma Abbah ya kasa ganewa, Yaya Mohandas saboda soyayyar Aunty Minal ya musulunta fa, ai abun alfahari ne wallahi, don haka baza'a buɗe ƙofar nan ba sai har Yaya Roshan ya dawo tukun..." Baiwar ALLAH gaba ɗaya ta rasa mai zata ce a wannan al'amarin gashi bata san meya haɗa ƙiyayyar ba, amma itama tana mungun tausaya musu sosai... Ganin bazata iya juran ƙiraye-ƙirayen sunayen da Abbah yake yi ba yasa ta fice a falon gaba ɗaya, kai tsaye can part ɗinta ta nufa zuciyarta a jagulgule... Itama Ummy haurawa upstairs tayi can room ɗinta, Roshan bai tashi dawowa ba sai da ya tabbatar jirginsu ya tashi tukun, wuce wa part ɗinsa yayi cike da fargaba domin bai san wani irin hukunci Abbah zai ɗaukar masa ba... Dab da mangariba sai ga motar da ake kai Ƴar tinny school kuma a dawo da ita, a falo ta tsaya tare da jefar da jakar ta anan taci karo da wayar Abbah akan kujera, ɗauka tayi tana faɗin "Yaaa wayan Abbah..." Da gudu ta haura upstairs ta nufi room ɗin su Abbah, buga ƙofar ta soma yi tana ƙiran sunan Abbah tare da faɗin "Abbah ganan wayay ka..." Daga ciki Abbah ya ce "yawwa Auta duba mun akwai key a jikin ƙofar?.." Ƴar tinny ta ce "ehh akwai..." Abbah ya ce "kama key ɗin ki murɗa ƙofar zai buɗu..." Ƴar tinny ita ba tsayi ba haka ta rinƙa ɗigalgal daga bisani ta ce "Nifa woyyayi Abbah cayina baje je ba..." Abbah ya ce "kiyi iya ƙoƙarin ki Auta zaki iya kinji..." Ƴar tinny wani dabara ne ya faɗo mata nan ta koma falo da gudu taje ta ɗauko jakar ta tazo ta ajiye a ƙasi ta taka kansa tana ƙoƙarin murɗa key ɗin, da ƙer tayi nasarar buɗe ƙofar sai ga Abbah ya fito da hanzarinsa kai tsaye falo ya nufa, ganin falon wayam ba kowa ne yasa shi haurawa upstairs su Minal, buɗe room ɗinta yayi yaga bata nan, ya komo falo kai tsaye ficewa yayi ya nufi part ɗin Roshan da motar sa saboda da ɗan rata sosai, Abbah yana zuwa ya fara buga ƙofar falo, Baiwar ALLAH dake tana kusa ita tazo ta buɗe masa daga shi sai jallabiya har ƙasi, jikinta ne ya fara ɓari ganin yanayin Abbah duk ya canza ga eyes ɗinsa har sunyi jawur tsabar ɓacin rai. Tambayar ta ya soma yi cewa "ina Roshan?..." Bata ɓoye masa ba ta ce "yana ciki Abbah amma ban sani ba ko yayi bacci..." Abbah ya ce "Baccin sa na banza da wofi ina ruwana da baccin sa, ko yana baccin kije ki tayar mun da shi yanzun nan..." Da sauri ta nufi part ɗin Roshan wanda tunda aka kawo ta gidan nan bata taɓa zuwa part ɗinsa ba, duk da bata san ina ne room ɗinsa ba amma da haka ta lalumo ganin shima yana ƙoƙarin fitowa ne, Jin ƙira daga Abbah ne gasa zuciyarsa bugawa da ƙarfin gaske, babu yanda ya iya domin ya rigada ya san ya yi laifi sosai, Yana shiga falo ya tarar da Abbah tsaye ya kasa zaune, Abbah yana ganinsa yaje gaban Roshan ya zabga masa mari, kafin Roshan ya ɗago Abbah ya ƙara zabga masa mari.. . asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *19_ TO_20* A kwana a tashi yau wata uku kenam da guduwar su Minal, Abbah ba irin neman duniya da baiyi ba amma an rasa su, yayi bala'in sa har ya haƙura, tsabar baƙin cikin da Abbah yake ciki har ya yanke cewa koda Minal ta dawo bazai amsheta a matsayin ƴa ba, ya furta cewa ya haƙura da ita duniya da lahira har hawan jininsa ya tashi, domin sai da yayi wata guda a kan gadon hospital, amma yanzu Alhamdulillah ya cire Minal a ransa ƙarfi da yaji... A kwana a tashi sai hantsi, yau da Gobe sai ALLAH Ƴar Amana jiki yayi sauƙi sosai, babu wani ciwo a tattare da ita sakamakon kulawar da ake bata, Roshan shine likitan ta kullum sai ya je ya duba ta, yanzu Ma sha ALLAH!. Abu ɗaya ne yake damun ta yanzu kuma yake hanata wargi shine rashin sumar kanta, yanzu almost 3 weeks kenam tin lokacin da ta sanya hula a kanta bata taɓa buɗe wa ba koda wanka zata yi saboda ji take kamar ta hallaka kanta in ta ga ƙoƙon kanta ba gashi. Razhdeen yayi iya dabarar sa akan ta cire hular ya gani ko gashi ya fara tofowa amma furr taƙi yadda... Yau ranar Sunday Razh da Rosh ne suke zaune a babban falon cikin gidan Abbah a yayin da shima Abbah yake zaune a ɗaya daga cikin jerukan kujerun falon, iya su uku ne da duk kan alamun akwai tattaunawar da suke yi. Abbah ne ya kalli Razhdeen sannan ya ce "Deen wai yaushe zaka koma wurin aiki ne?..." Idonsa na kallon gefe ya fara motsi da lips ɗinsa murya ciki-ciki ya ce "Dadd sun turo mun da letter akan na koma zuwa end of this month..." Abbah ya ce "shine baka sanar mun ba sai da na tambaye ka, yanzun zuwa lokacin zaka tafi?..." Razhdeen ɗaga masa kai kawai yayi ba tare da ya furta komai ba.. Jinjina kai Abbah yayi sannan ya ce "Deen bana so ka bar ƙasar nan ba tare da ka tsayar da wacce zaka Aura ba, domin in har kasa ƙafa ka tafi ban san ranar dawowar ka ba, zaman ka a haka ba Aure kuma ba son haka nake ba..." Razhdeen kallon Abbah yayi tare da cizar laɓɓensa na ƙasi kamar mai nazarin wani abu.. Roshan ne ya katsar da su da cewa "Abbah wacce yake nema bata mallaki hankalin kanta ba tukun, a ɗan bashi dama zuwa shekara biyar..." "Whatt?..." Abbah ne ya furta haka yana maida kallonsa kan Roshan. Roshan ne ya kuma cewa "seriously Abbah..." ganin irin kallon da Abbah ke masa.. Abbah ya ce "wace ce yarinyar? kuma aina take? su waye iyayenta? sannan makaranta take yi ne ko kuma meye da dalilin da yasa sai nan da shekara biyar?..." Roshan da sauri ya sunkuyar da kansa ƙasi yana faman zazzaro da eyes jin irin tambayoyin da Abbah yake jairo masa ba ƙaƙautawa, kuma shi da za'a kashe shi bai san inane asalin yarinyar ba balle ya zayyano... Razhdeen wani irin kallo yake watsawa Roshan ganin bazai iya kame bakinsa ba, Da sauri Razhdeen ya rubuta text ta wayarsa ya tura wa Roshan. Shima Roshan jin saƙo ya shugo masa waya yasa yayi saurin dubawa yaga ashe twins ne, Abinda ya rubuta shine: "ka cika surutu twins, yaushe na sanar maka cewa ina son yarinyar? I just pity her because she need help, please twins kar kasa Dad ya bincika yanda yarinyar take banason kowa yasan ina tare da ita i beg.." Roshan yana gama karantawa shima ya tura masa saƙo da cewa "ok don't worry my Man..." Abbah kallon Razhdeen yayi sannan ya ce "Deen tell me wace ce yarinyar da kake nema? domin ba ƙaramin farin ciki nayi ba jin wannan albishir, burina shine na ganka da matar ka..." Razhdeen fuska a ɗaure ya ce "i don't have any lady Dad, kawai ya sanar maka ne batare da ya sani ba shima..." Abbah ya ce "Please Deen bana son maganar wasa fa..." Razhdeen ya ce "seriously Dad ban taɓa cewa ina son ko wace mace ba, ban sani ba ko sai zuwa gaba, but ina neman Alfarma a barni sai na dawo daga U.S kafin a fara mun wannan maganar..." Abbah ya kalli Roshan ya ce "kai meyasa ka koyi ƙarya ne?.." Roshan ya ce "Sorry Abbah..." Abbah ya juyar da ganinsa kan Razhdeen sannan ya ce "Deen meyasa bazaka yadda a Aura maka Ƙanwar matar mai martaba ne kam? banga laifin yarinyar ba naga tana da hankali da tarbiyya..." Razhdeen zuciyarsa ce ta fara ƙuna kamar wanda aka zabure shi ya miƙe yana faɗin "Dad zan tafi gidan da nake idan akwai wani damuwa a tuntuɓe ni..." yana kaiwa nan yayi ficewar sa daga falon, shima Roshan tashi yayi da sauri ya bi bayansa. Shi dai Abbah zuba musu ido kawai yayi sakamakon rashin abun cewa... Abbah yana zaune shi kaɗai a falo yana duba saƙonnin da aka turo masa ta waya, sai ga Ammy ta shugo falon da sallama a bakin ta, Abbah ya amsa mata cikin fara'a, durƙusa gwiwowinta ƙasin carpet tayi fuska ɗauke da murmushi ta ce "Barka da hutawa Abban yara..." Abbah ya ce "yawwa Mar'atussaliha barkan ki kema da aiki..." Ta ce "Nagode sosai, Allah ya yi albarka..." Cikin jin daɗi ya ce "Amiin ya ALLAH Mar'atussaliha..." Kai a sunkuye ta ce "daman na kammala girki ne shine nazo tambayarka shin a kawo maka nan ne ko kuma zaka zauna a dinning ne?..." Sai da ya sauƙe wata nannauyar numfashi na jin daɗi kafin nan ya ce "a'a zan biki muje dinning ɗin, kin san bana so kina wahalar mun da kan ki shiyasa naso a nemo miki ƴan aiki..." Murmushi tayi tana faman rufe fuska da hannu ta ce "ai ba'a gajiya da neman lada, idan ka kawo mun ƴan aiki ai shikenam nayi banƙwana da fin rabin ladan da nake samu..." Ya ce "hakane Allah ya miki albarka..." Ta amsa da Amiin cikin jin daɗin mijinta ya sanya mata albarka.. Abbah idonsa akan ta sai yake tunowa da marigayiya matarsa uwar su Razhdeen sak kalar ɗabi'un ta irin na wannan matarsa, ga kamannun ma iri ɗaya, haka kawai yake jin wani irin farin ciki sai yanzu yayi dacen samun mata ta gari bayan uwar su Razhdeen da Roshan.. Abbah miƙewa yayi akan zasu tafi yaga har yanzu Ammy tana nan a durƙushe bata motsa ba, murmushi yayi domin yasan halin ta indai ba shi ya bata umarnin ta tashi ba to sai dai ta kwana a wurin.. Gyaran murya yayi mata tare da faɗin "toh Mar'atussaliha zaki iya tashi ko..." Murmushi tayi sai a lokacin ta motsa itama ta miƙe tsaye suka bar falon... Motar Razhdeen ne ta parker a wurin parking dake gidan sa, fitowa yayi da ƙasaitarsa ga ya sha black glass ba ƙaramin kyau yayi ba, order part shima Roshan ne ya fito fuska ɗauke da murmushi shima yana sanye da white glass daman shi ya saba sakawa koda yaushe shima yayi matuƙar yin kyau sosai, ya biyo Razhdeen ne saboda yazo ya ga Ƴar Amana da comedy ta domin Ƴar Amana tanada abun ban dariya dan ma tana takaicin rashin sumar kanta... Tin shugowar su gidan suke jin ƙarar sound na kiɗa an ƙura volume sosai, Razhdeen kallon Roshan yayi jin ƙarar waƙa a gidan, Roshan da bakinsa ya gagara yin shuru ya ce "waye ya kunna waƙa kuma? na farko dai Sarah kurmiya ce bata jin sound balle....." ya gagara ƙarisa maganar ganin Razhdeen ya wuce ya bashi wuri domin shi ya rigada yasan ita ce... Roshan dai shuru yayi ya bi bayansa ba tare da ya ƙarasa maganar ba, Suna shiga falo ai kuwa sai suka tarar da Ƴar Amana sai ɗirkar rawa take tayi ita kaɗai, har suka shugo bata san sun dawo ba, shi dai Roshan zama yayi sai dariya yake ta mata, Razhdeen ne ya ɗauki remote ya kashe waƙar, da sauri ta juyo tana kallonsa gira a haɗe kamar zata fashe da kuka... Roshan ya ce "ai da ka bar mata waƙar tinda nata so, domin idan tana cikin nishaɗi zata rage wasu damuwar..." Razhdeen idonsa a kanta ya ce "bata da wani damuwa sai na rashin sumar kanta...". Ƴar Amana cikin fushi ta wuce da gudu ta nufi part ɗinta can falo na biyu saman upstairs ga hula tum a kai irin hular sanyin nan... Razhdeen idonsa akan hanyar da tabi fuskar sa a sake ya ce "nafi so ta rinƙa kaɗa jitar ta, hakan yasa na siyo mata..." Roshan ya ce "to banda abinka ai dole zata haɗa duk biyun tinda duk ta same su, amma na fahimci tana son kiɗe-kiɗe da rawa duk da kurmiya ce amma tana jin komai da komai mayar wa ne kawai bazata iya ba, shawara ɗaya tinda tana son hakan mai zai hana a shigar ta makarantar koyan rawa? kaɗa jita kuwa sai dai ta koyawa wasu..." Razhdeen shuru yayi na ɗan wasu lokuta daga bisani ya ce "idan na tafi wa zai rinƙa kula mun da ita? bazan bar ta ita kaɗai a gidan nan ba..." Roshan ya ce "to ka bayyanar da ita mana kaga saika ajiye ta a can gidan mu..." Girgiza kai Razhdeen yayi tare da faɗin "nop! saina dawo ko hakan zata faru, bana so ta takura tafi son zama ba tare da mutane ba..." Roshan ya ce "to ka kaita Bauchi wurin Aunty Yolash tinda ita kaɗai ce..." Nan ma Razhdeen ya ce "ba haka ba, shawara ɗaya ya yanke cewa zai kawo wata ta taya ta zama a gidan nan, akwai security da zai rinƙa kaita school ya kuma dawo da ita ba tare da kowa ya sani ba har ya dawo..." Roshan ya ce "okay amma waye zaka ajiye a gidan wanda zai rinƙa kula da ita?..." Razhdeen ya ce "akwai wata Christal Madam Blessing zan dawo da ita gidan nan ta cigaba da kula da Sarah har na dawo, zan rinƙa biyanta salary duk wata, sannan kaima zaka rinƙa zuwa kana duba ta..." Roshan ya amsa da cewa "toh shikenam Allah ya bamu ikon kula da ita yanda ya kamata..." Suna cikin hirar su kwatsam suka jiyo sautin jitar Ƴar Amana daga saman ɗakin ta. Razhdeen miƙe wa yayi ya nufi yanda ɗakinta yake domin indai yaji sautin jitar nan gaba ɗaya hankalinsa tashi yake, zuwa yake ya zauna dab da ita yana sauraron sautin, A falo ya bar Roshan shi kuwa tashi yayi ya tafi domin yasan dalilin ruɗewar twins ɗinsa... Razhdeen shigarsa cikin room ɗinta ya tarar da ita a tsakiyar gadon ta ga hawaye shaɓe-shaɓa kwance saman fuskar ta, Sam bai ji daɗin ganin ta acikin wannan halin ba, ya saba ganinta a cikin farin ciki idan tana kaɗa jita a wannan lokacin kuma kuka take. Shima haurawa saman gadon yayi domin ganin hawayenta dai-dai yake da ciran duk wani fata na jikinsa saboda shi yake jin zafin haka, ya rasa gane mai yake ji akan ta shin tausayinta yake yi ko kuma so ko kuma burgewa ? amsa ɗaya zuciyarsa ta ba da shine tausayin ta yake yi.. A ruɗe ya kai hannu kanta yana faɗin "Please ki dakatar da wannan kukan Sarah, it's okay bazan ƙara miki laifi ba, yanzu ma ki je ki kunna waƙar ki kinji ko..." Juya masa ƙeya tayi tana turo baki, jawota yayi tsakiyar faɗaɗɗen ƙirjinsa yana rarrashinta, ita kuwa ƙoƙarin ɗagowa take tana tutture shi ita a dole tayi fushi... Ganin bazata iya ƙwacewa ba yasa ta fara kai masa duka har da su cizo a kan dantsen sa, ko kaɗan bai ji zafin cizon ba sai cewa yake "Sarah are you mad? da girman ki kike cizo?..." Asan tashi tabar wurin ne hular kanta ya cire gaba ɗaya, zama tayi ta kafa masa ido jin hular ya cire, ji tayi kamar ta haɗiyi ranta tsabar takaicin cirewar hular domin ko zata yi wanka bata cire wa, Razhdeen ne ya kafa nashi idon akan ta, yana so yayi magana amma ya kasa tsabar mamakin yanda sumar kanta ya dawo kamar yanda yake, ita kuwa a tunanin ta har yanzu kanta a gwigwiye yake, fashewa tayi da wani sabon kuka ta tashi da gudu zata bar ɗakin yayi saurin riƙo ta tare da juyar da ita saitin gaban mirror, Ƴar Amana zaro ido tayi waje sosai kamar zasu faɗo ganin yanda sumar kanta ya dawo kamar ba'a Aske ba. Hannayenta biyu tasa a kan sumar tana cakwarkwayawa taga dai gashin ta ne da gaske, shima Razhdeen hannu yasa yana murza zirin gashin cike da mamakin ganin ikon ALLAH. Cikin wata uku gashi ya dawo yanda yake ba tare da kowa ya sani ba, kanta sanye da hula amma bata san an maido mata da gashi ba.. Ƴar Amana wani irin farin ciki ne ya wanzu mata lokaci ƙanƙani a ruɗe ta juya ta rungumi Razhdeen sosai tana tsallen farin ciki, shima kan shi Razhdeen ɗin abun ya nishaɗartar da shi domin a halin yanzu ganin Ƴar Amana a cikin farin ciki tamkar anyi masa bushara da gidan Aljanna ne, shima bai san lokacin da ya tsinci kan shi acikin murmushi ba, rungumar ta yayi yana shafar sumar kanta mai murɗi-murɗi kamar yanda yake a baya... A wannan ranar a tare suka kasance babu wanda ya motsa ko ina a cikinsu, Uncle Deen ne zaune a saman gado a yayin da ita kuma Ƴar Amana ta ɗora pillow akan cinyarsa tare da ɗora kanta akai, yana wasa da gashin kanta har bacci yayi awun gaba da ita dake yanzu dare ne already sun ci sun sha ba tare da wata matsala ba, yanzu misalin ƙarfe 10 ne na dare, Razhdeen sai da ya fahimci tayi nisa sosai a baccin ta tukun ya gyara mata kwanciya ya rufe ta da mayafi daga bisani ya kashe hasken ɗakin shima ya fice a ɗakin tare da kulle room ɗin da key ya nufi part ɗinsa... 🌝🌝🌝 "Wallahi tallahi bazai yu ina fama da kaina ki baro gidan mijin ki kizo ki ɗora mun wahala ba, ke wato ƴar hutu ko? to bari kiji ni ba boyi-boyin ki ba ce da har kina kwance sai dai na dafa ki ci ba, sai dai ki bar mun gida ehen..." Hajia Kilishi tana kuka ta ce "haba Uma Saratu ke fah ƙanwar mahaifiyata ce, shin idan baki riƙe ni ba wazai riƙe ni, mijina ya ƙi karɓa ta ko ina naje gudu na ake, ga a wurin aiki an kore ni..." ta ƙarasa maganar tare da fashewa da kuka.. Uma Saratu tana tsaye sai faman zabga mata harara take ta sau ajiyar zuciya tare da faɗin "kin san dalilin da yasa ake ƙin ki?..." Hajia Kilishi ta girgiza kai alamar tana son sanin dalili.. Uma Saratu ta cigaba da cewa "dalili shine lokacin da kike gidan mijinki duk danginki ƙin su kika yi saboda kin samu abun duniya, idan dangi suka je gidanki sun zamo abun wulaƙantawa kenam a wurinki shiyasa yanzu kowa ya fita sabgar ki, kuma babu mai zuwa yanda kike, kema kuma haka bakya ziyartar ƴan uwanki bare ƴaƴanki kuma ke kike hanasu zuwa saboda bamu da kuɗi da abun more rayuwa, nasan dai Chief mijinki yana son ƴan uwanki amma ke danginsa da danginki duk bakya ƙaunar su, kinfi son ki zauna daga ke sai mijinki da ƴaƴanki bakya son wani ya raɓe ku, yanzu kuma da ALLAH ya tashi jarabtarki sai kika rasa komai naki, babu miji, babu ƴaƴanki sannan babu kuɗi kuma kin rasa aikin ki, daman mijinki ne ya sama miki yanzu kuwa yasa an kore ki sai mu ga ta gadara, ai Allah ne ya taimake ki dana karɓe ki da kuma naji tausayinki, aikin banza aikin wofi nasan inda mahaifiyar ki da mahaifinki suna raye da tinin suma sun yar da ke saboda ke butulu ce mai manta alkhairi, gashi kin jawa kanki abun kunya labari ya baza ko ina cewa kina yawon bin hotel da Auren ki tir da halin ki wallahi, kuma gashi waɗanda kike bin su hotel suma sun gudu sun barki babu mai sauraron ki, hatta ƴaƴan da kika haifa a cikin ki tinda kika dawo gida babu wacce ta zo bare mijinki, ki ma fidda rai akan Chief domin shi ya riga da yayi Auren sa, ya Auro ƙanwar matarsa ta farko mutumiyar kirki, Idan kin gama kukan ki ga can wanke-wanke da shara suna jiran ki..." Uma Saratu tana kaiwa nan tayi ficewarta daga cikin ɗakin Hajia Kilishi wanda ya kasance iya katifa ne a shimfiɗe a ƙasi ko ledar ɗaki babu bare carpet.... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *21_ TO_25* Remain 7 days Razhdeen zai koma U.S. Ita kuma Ƴar Amana an saka ta a wani tsararren private school da ake koyan komai da komai, Makaranta ne na koyan karatun boko da Islamic a wani ɓangaren daban kuma ana koyar da rawa da kuma kaɗa jita, akwai waɗanda ake rubuta musu waƙoƙi ta turanci da larabci sai su bada sautin su da irin basirar da Allah ya basu, Ƴar Amana kasancewar ta bata iya magana balle a rubuta mata waƙa yasa take iya koyan rawa already ta iya kaɗa jitar ta. Da uniform ɗinsu na musamman tin safe idan security ya kaita school ba'a dawo da ita sai 6:00 na yamma, tana samun tsaro na musamman da kulawa, idan ka ganta kai kace ƴar gidan shugaban ƙasa ne, domin tin daga kalar suturar ta zaka gane cewa ba ƴar ƙananun mutane ba ce. Razhdeen ba ƙaramin kuɗi yake kashe mata ba, Ga kuma wacce ya ɗauko wato Madam Blessing mutumiyar kirki ce tana ganin Ƴar Amana taji yarinyar ta shiga ranta sosai, da duk kan alamu ba ƙaramin kulawa zata samu a wurin Madam Blessing ba.. Baiwar ALLAH ce kwance saman katafaren gadonta ido a lumshe kamar mai yin bacci amma sai dai ba baccin take ba, jin ana knocking ƙofar bedroom ɗinta ne yasa ta ɗan buɗe idon tana mamakin waye yazo mata a wannan lokacin. Ɗaga kanta sama tayi tana kallon agogon da ke manne saman bango, misalin ƙarfe 12 na dare, dasauri ta kalli bakin ƙofar zuciyar ta na bugun uku-uku, a hankali ta tashi ta nufi wurin ƙofar cikin kakkarwar murya ta ce "wa wa ye?..." Ji tayi an bata amsa da cewa "Ammata ni ne ki buɗe..." Haɗe rai tayi cikin fushi ta ce "me ya kawo ka ɓangare na?..." Cikin sassanyar murya ya ce "Please Ammata ki taimaka magana nake so nayi da ke mai muhimmanci..." Ta ce "shin gari ba zai waye ba ne?..." Ya ce "Dan ALLAH..." Jin kamar a cikin damuwa yake yasa ta buɗe masa, ganin a halin da yake ciki ne yasa ta firgita, yana kame da cikin sa da hannu bibbiyu ko miƙe wa baya iya yi, eyes ɗinsa duk sun kaɗa sunyi jawur, yana fitar da numfashi da ƙer, kamar wanda aka hankaɗo shi jiki na ɓari ya shugo cikin bedroom ɗinta, wuri ya samu a bakin gado ya zauna domin idan ya cigaba da tsayuwa zai iya faɗuwa ne... Baiwar ALLAH gaba ɗaya ta gama tsorita domin a halin da yake ciki kamar mutuwa zai yi, Murya na kakkarwa ta ce "mai ya faru da kai Yaya Roshan?..." Ɗagowa ya yi da rinannun eyes ɗinsa yana binta da kallo daga bisani ya ce "ke ke ce damuwa ta, ke ke ke ce matsala ta, Ammata dan ALLAH ki taimake ni ina cikin mawuyancin halin da bazan iya control kaina ba, mai na miki ne kike azabtar da ni? idan nayi laifi ki sanar mun ko zan samu salama acikin raina, wannan hukuncin yayi mun tsauri da yawa wanda ƙwaƙwalwata baza ta iya ɗauka ba, please Ammata nah..." Baiwar ALLAH tana tsaye a kansa cike da mamaki ta goya hannayenta a saman ƙirjinta fuska a haɗe ta ce "wai mai kake buƙata ne daga gare ni Roshan?..." Cikin sassanyar murya ya ce "ke! ke nake buƙata Ammata, da zaki mallaka mun kan ki da kin kawo ƙarshen matsala ta ..." Wani abu taji ya daki zuciyarta cikin nuna fushi ta ce "Roshan please stay away from me, kana buƙata ta amma ni sam bana ra'ayin hakan, ko ana dole ne? shin ni kake so ko biyan buƙatar ka?..." Haka lips ɗinsa yake kakkarwa haɗe da teeth ɗinsa kamar mai jin sanyi ya ce "ke ke ke nake so Ammata..." yana magana murya na ƙaƙƙafewa sakamakon tsananin ciwon cikin da yake fama da shi... Murmushi tayi sannan ta ce "to indai har da gaske kana sona inaso ka cire wannan batun daga bakin ka, kafin kayi Aure shin neman mata kake yi ne? nasan baka neman mata haka kake haƙuri har tsawon shekaru, to yanzun ma inaso ka cigaba da haƙuri ka zauna da ni a haka idan zaka iya..." Roshan ya ce "amma mai yasa kika yanke wannan hukuncin?..." Murya cikin tsawa ta ce "saboda bana sonka Roshan, bana jin sonka a cikin zuciyata, baka san irin raɗaɗin da nake ji a cikin zuciyata ba dana kasance inada igiyar Auren ka, Roshan idan nace zaka samu farin ciki daga gareni nayi maka ƙarya domin nima an datse mun nawa farin ciki, inaso mu cigaba da zama haka cikin ƙunci nake ga hakan zai fi..." Roshan ji yayi kamar ana kwaɗa masa guduma a tsakiyar kansa lokaci guda ya fara jin hawaye suna masa go slow a saman kuncin sa, girgiza kai yayi tare da faɗin "kin zalunci kanki da baki sanar mun tin kafin a ɗaura Aure ba, sannan kin zalunce ni da kika kasa furta mun abinda ke ranki har kika bari aka ɗaura Aure, amma dan ALLAH inason sanin dalilin da yasa bakya sona?..." Baiwar ALLAH ta ce "duk wata hanyar da yakamata na bi don na nuna maka cewa bana sonka na bi hanyar amma ka kasa fahimta, ance labarin zuciya a tambayi fuska amma kai duk da hakan baka gane ba saboda a lokacin ƙwaƙwalwarka a toshe take bata gane farin cikin mutum da kuma baƙin cikin mutum, kai kanka kawai ka sani, farin cikin ka kawai ka sani, You know what? bari na sanar maka wani abu da baka sani ba, ina damuwata kake son sani ko? to yau zaka sani..." Ƙarasawa gabansa tayi ta durƙusa da gwiwowinta tana fuskantar sa a yayin da shi kuma yake zaune a bakin gado. Ta ce "Yaya Roshan kayi haƙuri da abinda zaka ji daga bakina duk da nasan zaka ji ba daɗi amma rashin daɗin nake so kaji kamar yanda nima ba'a cikin daɗin nake ba, tin farko zuciyata da kai ta fara aminta amma daga ƙarshe labari ta sauya zuwa kan Razhdeen..." Cikin rashin fahimta Roshan yake binta da kallo ya ce "bangane mai kike nufi ba..." Ta ce "Razhdeen ya saye mun zuciyata, shi nake so, kuma nake son kasancewa tare da shi, har yau har gobe son sa bai ragu a cikin zuciyata ba..." Roshan wani irin zazzaɓi ne yake shirin rufan sa murya na kakkarwa ya ce "amma meyasa baki sanar tin da wuri ba? mai yasa zaki cutar da zuciyarki? kina son Ɗan uwana amma kin kasa sanar wa kowa why? hatta shi kan shi bai sani ba, inda kin sanar mun wallahi bazan bari ayi Auren da ni ba, ina sonki har cikin zuciyata amma jin irin son da kike wa twins ɗina yasa na ƙara sonki, Ammata bazan bari zuciyarki ta cigaba da azabtuwa ba, zan sama miki mafita, ki kwantar da hankalinki Okay..." Lokaci guda taji wani irin matsanancin kuka ya yanko mata, kwantar da kanta tayi kan cinyarsa tana kuka, shima za mo wa yayi ƙasi ya ɗago da fuskarta suna fuskantar juna ya ce "kukan mai kike? ba nace ki kwantar da hankalin ki ba, ina dai Razhdeen kike so? to ki yi haƙuri zaki same shi..." Ya ƙarasa maganar tare da fashe wa da kuka shima ya rungumota jikinsa duk kukan suke babu mai rarrashin kowa a cikin su... Bayan kwana biyu da faruwar haka Roshan yana zaune a falon Meeting ɗin Abbah da shi Abbah ɗin, Roshan ne yake son sanar wa Abbah halin da Baiwar ALLAH take ciki na tsananin son Razhdeen da kuma yana son sanar wa Abbah cewa zai haƙura da ita domin sama mata farin cikin ta, tunani ya zurfafa daga bisani Abbah ya katsar da shi da cewa "mai yake faruwa ne Roshan?..." Roshan cikin tsananin damuwa ya ce "Abbah daman ina so zan yi magana da kai ne..." Abbah ya ce "ina jinka Roshan! naga kamar kana cikin damuwa please tell me my Son..." Lokaci guda sai ga hawaye shaɓe-shaɓa akan fuskar sa kamar wanda yake jira ayi masa magana, kuma daman yana maƙale da hawayen.. Abbah ya ce "Subhanallahi Roshan kuka kuma? kai ɗin? dan ALLAH ka taimaka ka sanar mun bana so ka rinƙa jefa kan ka cikin damuwa kasan kana da matsalar heart, ka duba kamar marar lafiyan da yayi shekara a kwance duk ka bi ka rarrame..." A hankali Roshan yake motsa lips ɗinsa waɗanda suke ta faman kakkarwa kamar mai jin zunzurutun sanyi, da ƙer ya iya cewa "A A A Abbbah, please help me my heart so pain........!!!" lokaci guda ya fashe da wani irin raunannen kuka har sai da ya za me ƙasin carpet, ya kifar da kansa a ƙasi ba abinda yake sai kuka.. Jikin Abbah ne ya fara ɓari gaba ɗaya ya tsorita da ganin Roshan acikin wannan hali, cike da mamaki ya nufo wurin da yake shima ya durƙusa yasa hannu yana ƙoƙarin ɗago shi. Abbah Ya ce "shin Daughter ce ta mutu? ko kuma tana kwance ne a gadon asibiti? ka sanar mun mana..." Roshan rungumar Abbah yayi jikinsa duk ya ɗau zafi murya na kakkarwa yake faɗin "Abbah Ammata bani take so ba, gaba ɗayan mu babu mai kwanciya hankali, ni bana cikin farin ciki itama haka, ina matuƙar ƙaunar Ammata amma ita sam ba ni ne a gaban ta ba, tinda muka yi Aure tsawon wata uku zuwa huɗu yanzu bamu taɓa raya sunnah ba please Abbah inaso na bar duniyan nan, am really tired of this would, wannan duniyar cike take da ruɗani da tashin hankali Abbah, ina da abubuwan more rayuwa amma bani da kwanciyar hankali Abbah..." Abbah shima idanuwan sa ne suka cicciko da hawaye tsananin tausayin Roshan ne ya ziyarci cikin zuciyar sa, kwantar da kan Roshan ya yi saman ƙirjinsa yana bubbugan bayansa alamar rarrashi tare da faɗin "it's okay my Son, everything will be come easy, know tell me what's going wrong?.." Roshan kan sa a kwance saman ƙirjin Abbah ya ce "i told you Abbah, Ammata bani take so ba, Auren dole akayi mata..." Abbah ya ce "shin aina kaji wannan batun, ita ta sanar maka?..." Roshan ya ce "yess Abbah ta sanar mun duk abinda ya ke ranta, bata sona..." Abbah ya ce "whattt? to amma ya akayi hakan ta faru, bata sonka kuma akayi Auren? shin waye a ranta har ta kasa karɓar soyayyarka kuma ta kasa baka haɗin kai...". Ɗago wa yayi daga kwancen da yake akan Abbah, da rinannun eyes ɗinsa yake kallon Abbah sannan ya ce "Razhdeen ne a cikin zuciyar ta, shi take so kuma take muradin ya zamo mijinta uban ƴaƴanta..." ya ƙarasa maganar yana sakin ƙayataccen murmushin baƙin ciki da kuma farin ciki... Abbah gaba ɗaya ya gama ruɗe wa, cike da mamaki ya ce "amma shi Razhdeen bai taɓa sanar mun wannan maganar ba, ko a bakin wani ban taɓa jin Razhdeen da Daughter suna soyayya ba... Roshan ya ce "Abbah ka gane zancen mana, ba soyayya suke ba ita ce take sonsa amma ta kasa nasar masa, ta kasa fitar da abinda yake cikin cikinta da haka har aka ɗaura mana Aure, shi kan shi Razhdeen bai san tana son sa ba..." Ajiyar zuciya Abbah ya sauƙar yana jinjina kai daga bisani ya ce "Roshan!.." Roshan ya amsa masa cikin sassanyar murya. Abbah ya cigaba da cewa "shin wani hukunci kake son ɗauka?..." Roshan ya ce "Abbah ni na yanke shawarar rabuwa da ita, in yaso sai a Aura mata Razhdeen duk da nasan da wuya ya yarda da hakan, amma zan lallame shi akan ya yarda ya Aure ta, ina son farin cikin ta sosai, a halin yanzu ita ɗin marainiya ce bata da kowa sai mu..." Jinjina kai Abbah ya yi daga bisani ya ce "shikenam duk yanda ka yanke shine dai-dai, hakan na nufin zakayi sadaukar da soyayyar ka wa ɗan uwanka domin ka sama mata farin ciki, kai baka damu da naka farin ciki ba, shikenam inaso a yanzu kowa ya hallara a babban falon cikin gida, kaje ka ƙira matar takan, nima yanzu zan ƙira Razhdeen yazo yanzun nan..." Roshan tashi yayi da ƙer yana jan ƙafa da haka ya fice, shima Abbah wayar sa ya ɗau ya danna ƙiran number Razhdeen cikin sa'a kuwa lokacin wayar tana hannunsa ya ɗauka da sallama a bakin sa.. Abbah zuciyarsa a hargutse ya ce "kana ina Razhdeen?..." Razhdeen ya ce "ina gidana..." Abbah ya ce "okay I want to see you right now..." In other side Razhdeen ya ce "but what happen Dad?..." Abbah ya ce "kar ka damu idan kazo zaka ga komai a idonka..." Razhdeen amsa masa yayi tare da faɗin "Okay..." ya katse ƙira yana mamakin ƙiran gaggawar da akayi masa kuma da safe yaje ya gaishe da su Abbah, babu yanda ya iya haka ya bar duk abinda yake ya ɗauki key ɗin motar sa zai fita, A falo ya tarar da Ƴar Amana dake yau ba school ranar hutu ne, ta zuba wa plasman ido tana kallo kai kace ba kurmiya ba ce, bata ankara ba taji an manna mata kiss akan goshi da sauri ta ɗago tana bin sa da kallo, murmushi ya sakar mata tare da faɗin "take care my Beb, I'll be back..." Itama murmushi ta sau idonta akan sa, ga gashin kanta yanda ya bazu akan gadon bayan ta... Kaɗa mata key yayi sannan yasa hannu zai buɗe ƙofa ya fice ya ji Madam Blessing tana faɗin "sai ka dawo Major..." Ba tare da ya juya ya kalle ta ba ya ce "thank you..." daga nan ya yi tafiyar sa. Kowa ya hallaru a babban falon gidan Abbah duk da yanzu basu da yawa a gidan, daga Abbah ne sai Ammy sai uwar masu gida da Ƴar tinny itama yau ba school ga Roshan shima a zaune gefe guda, waɗanda ake jira Razhdeen ne sai Baiwar ALLAH wacce aka ƙira ta tin ɗazu bata samu damar zuwa ba, Abbah ne ya kalli Roshan sannan ya ce "Roshan kaje ka taho mun da Daughter ina tunanin tasan ƙiran akan maganar ta ne shiyasa ta ƙi zuwa..." Roshan ya ce "okay tam..." ya tashi zai bar falon. Razhdeen parking ya yi a gurguje ya buɗe murfin motar sa ya fito dai-dai lokacin da Baiwar ALLAH itama ta iso part ɗin, bakin get ta nufa idonta akan Razhdeen wanda shima wurin ya nufo shima ita yake kallo yana saƙe-saƙe a ransa, a gaba da baya suke ita tana gaban sa a yayin da shi kuma yake ta bayan ta baifi nan da ɗan rata kaɗan ba ya iso ta, tafiya take ba tare da ganin gaban ta ba, idonta akan sa bata san ta iso bakin get ɗin mashigar compound ɗin gidan ba, kawar da kansa yayi daga ganinta yasan ta iso bakin get ɗin amma bai dakatar da ita daga ganin sa ba domin ya daɗe da tabbatar da cewa Baiwar ALLAH taɓaɓɓiya ce ta fara haukacewa tin lokacin da ya kaita hospital. Kan ta ne yayi wani irin mungun buguwa da ƙofar get mai ƙarfin gaske, wani irin gigitaccen ƙara tayi tare da yo wa baya zata faɗi har ta saddaƙar kwatsam taji an riƙo ta, idonta a ƙarƙame a matuƙar tsorace ta cakume shi sosai jikinta har wani ɓari yake tana sauƙar da numfashi da ƙer, kallonta ya tsaya yi yana kallon kalar riƙon da yayi mata, caɗaf ya ɗaga ta yayi mata ɗaukar jaririya wanda shima kansa bai san yayi mata irin wannan ɗaukar ba, domin a yanda tayo baya zata faɗi inda bai yi saurin ɗaukar ta ba sai dai a ɗauke ta sumammiya, a hankali take buɗe eyes ɗinta tana so taga a hannun wa take, idanuwanta ne suka sauƙa akan kyakkyawan fuskar Roshan mai ɗauke da ƙayataccen murmushi, zaro ido waje tayi ganin a hannun Roshan take, ƙoƙarin sauƙa daga ɗaukar da yayi mata take, a hankali ya sauƙar da ita, waiwaye ta soma yi tana duba yanda Razhdeen yake domin tasan shine a wurin. Roshan da ya fahimci Razhdeen take duba wa ya ce "tin tinin ya yi wuce war sa, domin inda Allah bai kawo ni da wuri ba ina tunanin yau sai dai kiyi kwanan hospital... Abunda ya faru shine a lokacin da ta bugu da get tayi baya a ruɗe zata faɗi ƙasi shi da kansa Razhdeen ya kauce mata ko sauraronta bai yi ba balle ya yi gaggawar riƙo ta, kafin faruwar haka kuwa Roshan daman ya fito bakin get ɗin ganin yanda take ta kallon Razhdeen ne yasa ya tsaya cakk yana binsu da kallo, ganin tana shirin kaiwa ƙasi ne yasa ya taho da gudu yayi mata ɗaukar luɗa kafin taje ƙasi, shi kuma Razhdeen ko kallon yanda suke bai tsaya yi ba ya buɗe get ya shige ciki... Baiwar ALLAH tsaya wa tayi tana tariyo abinda ya faru, bayan da tayi zata faɗi da akan Razhdeen zata faɗa shi kuwa yayi saurin kauce mata yabi ta gefen ta, tabbas in ba dan Roshan ba Razhdeen bazai taɓa tallafa mata ba, rufe eyes ɗinta tayi sosai tsananin kunya ne ya ishe ta, sai yanzu ta fara jin ciwon kai sakamakon buguwar da tayi, kama kanta tayi tana faɗin "wayyo kai na..." Roshan ne ya ce "na ɗauke ki ne?..." ta ce "no I have leg, I'll walk by myself..." Murmushi ya yi tare da faɗin "okay fine..." Tayi gaba yana binta a baya da haka suka shige, a falo suka tarar da su Abbah da Razhdeen yana zaune sai pressing phone ɗin sa yake, Roshan ne shima ya zaune dab da Razhdeen, itama Baiwar ALLAH zama tayi a kusa da Uwar masu gida... Abbah ne ya soma magana yana faɗin "ba komai ne yasa duk na tara ku ba sai dan na sama wa iyalai na Dawwamammiyar farin ciki na har abada, akwai wani labari da naji wanda yayi matuƙar ƙona mun rai ya kuma saka ni cikin ƙunci, na shiga tashin hankali matuƙa dana ji kalar rayuwar da ma'aurata biyu suke yi na rashin wanzuwar farin ciki da zaman lafiya..." Ƙirjin Baiwar ALLAH ne ya yi wani irin bugawa da ƙarfin gaske jin wannan batun tasan da su Abbah yake, Uwar masu gida ne ta kalli Baiwar ALLAH domin ta fahimci babu zaman lafiya a tsakaninta da Yaya Roshan kuma tasan Roshan bashi da damuwa sai dai matsalar daga wurin ta ya fito... Razhdeen dai yana zaune ya kasa fahimtar komai game da abinda Abbah yake faɗi.. Abbah ne ya kalli Baiwar ALLAH sannan ya ce "Daughter Roshan ya sanar mun duk halin da kuke ciki, ya buƙaci rabuwa da ke domin ya sama miki farin cikin da kike nema..." Nan Abbah ya kwashe duk maganganun da Roshan ya sanar masa ya faɗe su yana kallon Baiwar ALLAH ya ƙarisa maganar da cewa "Shin duk maganar da ya faɗa gaskiya ne?..." Zaro ido Baiwar ALLAH tayi tana ƙoƙarin haɗiye ranta tsabar tsananin fargaba da tsoro ga yanda Abbah ya fito mata da sirrin da take ɓoye wa a gaban mutanen gidan... Razhdeen wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne ya ziyarci cikin zuciyar sa jin yanda Baiwar ALLAH take wulaƙanta masa twins sannan har take furta cewa bata son shi, jin yanda ta furta wa Roshan cewa shi take so yasa gaba ɗaya yaji ya tsani yarinyar, sai kuma ya tuno da maganganun da take ta furtawa a gadon asibiti... Abbah ne ya ce "bazan takura miki akan dole sai kin zauna da Roshan ba amma ina mai sanar miki cewa duk wanda ya nuna yana sonki tsakani da ALLAH to shine Abokin rayuwa, amma indai ke kike so kuma ba'a son ki to rayuwarki tana yawo a tsalallakun gajumare ne, yanzu ina so ki furta da bakin ki kina son Razhdeen..." Da sauri ta ɗago tana kallon Abbah ido sunyi jawur tsabar kuka, ta kalli Roshan taga shima kallon ta yake sannan ta maida idonta kan Razhdeen a yayin da shi kuma Razhdeen idonsa suke kan Abbah jin tambayar da yake mata... Abbah ne ya sake maimaita wa da cewa "kina son Razhdeen ne kamar yanda kika faɗa ko kuma?..." Girgiza kai tayi tana shaƙar numfashi da ƙer cikin kuka ta ce "zan cigaba da zama a gidan mijina..." Abbah ya ce "a'a Daughter kar ki cuci zuciyar ki da kuma zuciyar wanda yake miki hallaci, nasan tinda kika furta masa cewa bakya son sa to kuwa bakya so ɗin dan haka a yau Roshan zai baki takardar sakin ki, da zaran ki kammala iddar ki za'a Aura miki Razhdeen, zan dakatar da tafiyar sa ƙasar U.S har sai an ɗaura muku Auren kafin nan..." Baiwar ALLAH ba abinda take sai kuka domin tasan zai yi wuya Razhdeen ya amince, inda zai yadda to da kuwa tafi kowa farin ciki... Abbah ne ya kalli Razhdeen sannan ya ce "Razhdeen kana dai jin abinda yake faruwa ko, bana buƙatar zaɓinka domin zaɓin marainiyar nan shine zaɓi na, ko ka so ko kar ka so dole zaka Aure ta tinda har Ɗan uwanka ya goyi bayan haka..." Da sauri Razhdeen ya miƙe tsaye yana huci kamar wani kuntaccen zaki, har eyes ɗinsa sun rine yana motsi da lips ɗinsa a hankali ya ce "God forbid, that's not comp...." Bai ƙarasa furta kalmar da zai fito daga bakin sa ba Abbah yayi saurin daka masa tsawa da cewa "You'll never escape for this choosing, dole ka Aure ta tinda ta nuna kai take so, uban waye ya ce ka rufe junanku a cikin bedroom na tsawon one week? daga kai sai ita, ita mace ce a koda yaushe kai take gani a cikin ƙwayar idanuwanta, idan zata kwanta bacci sai ta fara tozali da fuskar ka haka nan da zaran ta farka fuskar ka shine madubin ta, so know tell me how comes bazata kamu da sonka ba a halin da kuka kasance a tare? wanda nasan kaima ƙarya kake kace baka ji komai akanta ba, Razhdeen don't tell me the lie I known you too u really loving her..." "Father I don't love her and I'll never love her in my life forever and ever..." Razhdeen ne ya furta hakan tin kafin Abbah ya ƙarasa iddasa maganarsa. Abbah ya ce "to amma meyasa ita take sonka?..." wani irin kallo Razhdeen ya watsa mata mai haɗe da harara kafin ya ce "she losses her mind that's why..." Cike da mamaki Abbah ya ce "Deen what are you talking about?..." Tinda Razhdeen yake a wayonsa bai taɓa zubda ƙwallah ba sai yau shi kanshi Abbah sai da ya girgiza idonsa akan sa, shima Roshan miƙewa yayi tsaye ganin hawaye kwance saman fuskar Deen, Razhdeen ya ce "bana sonta kuma bazan taɓa sonta ba har abada balle na Aure ta, Dad tell her bata samu mijin Aure ba indai ni zata Aura, now I hate her and if you post me to marry her I'll hate myself too..." Abbah a firgice ya kalli wurin da Baiwar ALLAH take a zaune tana kallon ƙasin carpet ba abinda take sai kuka, Abbah bazai iya juran ganinta a cikin wannan halin ba haka yasa ya girgiza kai ya maida kallon sa kan Razhdeen tare da faɗin "Deen dole zaka Aure ta, idan kuma ka azabtar da ita ko kuma ka kasa biya mata hakki zan iya tsine maka Albarka..." A gigice Razhdeen ya ɗago da jajayen idanuwansa waɗanda suka sha kuka yana kallon yanda Abbah yake, jin kalmar da Abbah ya furta yasa kansa ya fara juyawa wani irin hajijiya ne yake shirin ɗaukarsa.. Roshan shima zaro ido yayi yana kallon Abbah cike da mamaki, Uwar masu gida itama a ruɗe ta toshe bakinta da hannayenta biyu tana kukan baƙin ciki, bata taɓa jin haushin wani matuƙa ba sai yau daga Mahaifiyarta sai kuma Baiwar ALLAH... Ammy ta ce "Amma Abban yara...." bata ƙarasa maganar ba ya ɗaga mata hannu alamar ta dakata.. Ya ƙasara wurin da Razhdeen yake tsaye domin zama ya gagare shi, tsayawa yayi a gaban sa tare da faɗin "zaka sake bijire wa maganata a karo na biyu ko? Ƴar uwarka Amina ta bijire mun ta bi zaɓinta ta guje ni, kaima you can do that, now choose your's shin zaka bi zaɓin ranka ne ko kuma zaka yi abinda nace? idan har zaɓin ranka ka zaɓa kaje kaima na sallame ka..." Abbah ya ƙarasa maganar yana zubda ƙwallah shima, Razhdeen lips ɗinsa ne yake kakkarwa a hankali ya furta "Dad..." Abbah ya ce "not your Dad har sai ka zaɓi ɗaya a cikin biyun nan, shin zaɓinka ko zaɓi na?..." Razhdeen yana kuka ya matso dab da Abbah ya riƙe masa hannayensa biyu yana kuka ya ce "Dad you are my life and the something happen to my life I'll even to be leave, na amince zan Aure ta amma zaɓinka ne Abbah is not my chosen..." Abbah ya ce "Deen are you sure are you going to get engagement with her ?..." Razhdeen ya ɗaga masa kai tare da faɗin "bazan taɓa bijire maka ba..." Razhdeen wani irin tsanar Baiwar ALLAH ne ya ziyarci zuciyarsa lokaci guda, ji yake kamar ya murɗe mata wuya tabar duniya, yayi matuƙar dana sanin haɗuwa da ita, tinda yake bai taɓa jin tsanar wani abu ko wani ko wata sai yau akan Baiwar ALLAH, Abbah rungumarsa yayi yana faɗin "thank you very much my son..." Shima Razhdeen rungumar Abbah yayi, Baiwar ALLAH ce ta ɗago da manya-manyan idanuwanta waɗanda suka canza kamannu ta ɗora su akan Razhdeen wanda yake rungume da Abbah, lokaci guda taji zuciyarta yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske ganin irin kallon da Razhdeen yake mata na tsananin tsana... Razhdeen idonsa akan Baiwar ALLAH yake maganar zuci yana faɗin "this is the first time that you make urself my Enemy, you are my enemy, I hate you and I'll never love you in my life, I hate you..." Ga yanda ya zazzaro eyes ɗinsa waje sunyi matuƙar canza launin ja ya kasa ƙibta idonsa akan ta, itama haka take kallonsa ido a zazzare tsananin tsoro ne da fargaba suka bayyana akan fuskarta, wani irin yawu ta haɗiya na tsoro, ba ƙaramin kwarjini ya yi mata ba... Roshan idonsa akan Razhdeen ganin yanda yake mata kallon tsana da baƙin ciki gaba ɗaya jikinsa ba ƙaramin sanyi ba, dole yasan Baiwar ALLAH zata sha wahala sosai a hannun Razhdeen... Abbah ne ya raba jikinsa daga na shi yana faɗin "idan ka taimaki marainiya kaima Allah zai taimake ka..." Ya kalli wurin da Roshan yake sannan ya ce "Roshan kayi haƙuri ka bata takardar sakin ta..." Shima Roshan ba abinda yake sai kuka yana daga tsaye ya ciro wata farar takarda a cikin aljihunsa ya nufo yanda Baiwar ALLAH take a zaune ya ce "Ammata yau burinki zai cika, ga takardar raba Aurenki da ni..." Tana kuka ta miƙe tsaye itama tana fuskantar sa tasa hannu ta karɓi takardar idonta akan Roshan sai da ta dai-daici tsakiyar paper ta raba gida biyu, haka ta yayyaga takardar tana kuka ta ce "Yaya Roshan kayi haƙuri zan cigaba da zama da kai..." Taje gaban Abbah ta durƙusa gwiwowinta ƙasin carpet tana kuka ta ce "Abbah ka gafarce ni, Uncle Deen baya sona bazan iya zama da shi ba, zan cigaba da zama da wanda yake sona har cikin zuciyarsa, zan canza hali na, zan masa biyayya yanda ya kamata..." Abbah ya ce "kin tabbata har cikin zuciyarki abinda kike faɗi?..." tana kuka ta ce "da gaske nake Abbah..." Abbah ya ce "Alhamdulillah shikenam ki kwantar da hankalin ki mahaƙurci mawadaci yanzu wanda zai sama miki farin ciki shine ya dace dake Daughter..." Jinjina kai tayi tana sauraron Abbah, Roshan murmushi yayi ganin yanda ta sauya ra'ayi amma yasan ba har cikin zuciyarta ba, tayi hakan ne saboda gudun matsalar da zata shiga nan gaba tinda itama kanta tasan Razhdeen ba sonta yake ba, tsoronsa da fargabansa ne yasa tayi gaggawar janye ƙudirinta... Razhdeen murmushin gefen baki yayi na mugunta a cikin ransa ya ce "is better for you..." Razhdeen ya buɗi baki yayi magana yana faɗin "tomorrow early morning I will travel to U.S..." Abbah ya ce "lokacin yafiyarka bai yi ba naga..." Ya ce "Yes! zan tafi tin yanzu nayi muku sallama domin ba lallai na dawo ba, da sassafe zan wuce airport..." yana kaiwa nan ya juya zai tafi, Abbah ya ce "Are you Angry with your Dad?..." Razhdeen ya ce "no..." a takaice Abbah ya ce "okay zan tarar da kai a airport goben.." Razhdeen ya ce "ok..." daga nan ya yi tafiyar sa... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *26_ TO_30* Razhdeen shigar shigar motarsa yayi ya zauna yana riƙe da sitiarin motar tsabar ƙololuwar baƙin cikin Baiwar ALLAH ne yasa ya kasa jan motar. Baiwar ALLAH ne itama ta fito tana sharar hawaye ta nufi part ɗinta bata ma lura da Razhdeen na wurin ba, shi kuwa idonsa akanta ganin bazai iya kyale ta haka ba yasa shi buɗe murfin motar sa ya nufi part ɗin Roshan.. Baiwar ALLAH bayan shigar ta cikin falonta zama tayi a kujerar falon tana sabinta kukan ta, tana cikin wannan halin ta soma jin ana knocking ƙofar falon, da sauri ta share hawayen tayi tunanin Roshan ne bata so ta nuna masa damuwarta saboda kar ya ƙara samun Abbah da maganar, buɗe ƙofar tayi kwatsam ta tarar da Razhdeen a tsaye a bakin ƙofar yana mata wani irin kallo na ƙasƙanci wato kallon up and down... Kutsawa yayi ya shige ciki a yayin da ita kuma take ja da baya domin ba ƙaramin ƙwarjini yake mata ba, ma ta nuni yayi da ta zauna a kujera ba musu haka ta zauna eyes ɗinta akansa shima jawo glass table yayi ya zauna a front ɗinta suna fuskantar juna, fuska a haɗe ya ce "ki kalli cikin eyes ɗina kiga shin nayi kala da abokin wasan ki?..." Shuru tayi bata bashi amsa ba sai kallonsa da take ko ƙibta idon bata yi, cikin fushi ya cabki wuyanta ya riƙe sosai yana zazzaro mata manyan eyes ɗinsa tare da faɗin "ke ko a ƴar aikin matata bazan ɗauke ki ba domin bakiyi kala da wacce zata zauna a gidan da nake ba balle na haɗa jinsi da ke, kinyi kuskure sosai da kika nuna kina sona domin ciwon haukarki ne yake rinjayarki, naso baki janye ƙudirin ki ba wallahi tallahi nayi niyar nasa hannu na murɗe miki wuya har sai kin bar duniyan nan, bana sonki! na tsane ki, ki janye jikinki daga gare ni sannan ki kawar da idanuwanki daga yanda nake idan ba haka ba zan kashe ki ne har lahira, nonsense girl ƙazama marar hankali, wawiya dabbiya..." Baiwar ALLAH ƙirjinta ne yake wani irin bugawa da sauri ta kawar da fuskarta gefe tana rufe da eyes ɗinta taji zagi kala-kala da cin mutuncin amma babu cin mutuncin da yafi ƙona mata rai kamar na Razhdeen, jin yanda yake ta faɗa mata maganganu yasa zuciyarta hargutsa a gigice ta cabki kwalar rigarsa tare da miƙe wa tsaye tana kuka ta ce "Uncle Deen don ina sonka bashi zai sa na tsaya kana faɗa mun maganganu son ranka ba har kana sako iyayena a ciki waɗanda basu san a wani hali nake ciki ba shin sun mutu ko suna raye Allahu A'alamu, dan ALLAH kaji tsoron Allah ka dai na azabtar da zuciyar da ta amince da kai, don ina sonka bashi zai sa ka wulakanta ni ba..." Razhdeen ganin yanda take riƙe da kwalar rigarsa wanda tinda yake mace bata taɓa sa hannu da niyar riƙe gaban rigar sa ba hatta namiji balle mace a fusace yasa bayan tafin hannunsa ya zabga mata mari rai a ɓace, A gigice ta faɗa kan kujera tare da sakin wata ƴar ƙara, tana riƙe da gefen fuska wani irin kuka take ta cin rai da takaici a fusace ta juyo tare da kai hannu zata rama yayi saurin riƙo hannun ta cike da mamaki ya ce "whattttt? Ni zaki mara? ni ne zan bari hannun mace ya sauƙa akan fuskata da niyar mari ? impossible..." ya ƙarisa maganar tare da wurgata kan kujera ya cabko sumar gashinta yana murmushin takaici ya ce "idan akwai macen da nafi tsana a rayuwata to bazai wuce ke ba, you are my enemy..." yana iddasa maganarsa ya juya zai tafi har ya isa bakin ƙofa yaji ta furta wata kalma wanda ya dakatar da shi, ƙara maimaitawa tayi ta ce "yes me too I hate you, sam baka daraja mata especially wacce ta nuna damuwarta akan ka kafi wulakanta ta, amma ka sani duk abunda kayi kaima sai an mata, kamar yanda ka ƙuntata mun kaima wata rana sai kayi kuka cir da idanuwanka, wata rana saika durƙusa a gaban mace kana bata haƙuri a yayin da ita kuma take wulaƙantaka, wallahi ina maka wannan fatan kuma ka rubuta ka ajiye domin maganata a rubuce take, Razhdeen ko kaɗan bana jin tsoronka kaje bana son ƙara ganin fuskar, na gama maka komai tinda na Auri ɗan uwanka..." Wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne yake ziyartar cikin zuciyar Razhdeen, a yanda yake jin kansa ji yake kamar yaje ya murɗe mata wuya cikin zafin rai ya nufi yanda take a zaune bai iya aikata mata komai ba sai dunƙule hannunsa da yayi da ƙarfin gaske ya doka akan glass table na tsakiyar falor har sai da table ɗin ya dagargaje, hannunsa ne ya tsatstsage sai zubar da jini yake cikin zafin nama ya saito da gwala-gwalan eyes ɗinsa sai tin nata, a zabure ta ƙara mannewa da jikin kujera cikin tsoro da fargaban yanda ta gànshi lokaci guda ya canza kamar horror fuska yayi jawur tsabar ransa yayi matuƙar ɓaci, cikin dirarriyar murya ya ce "me kike taƙama da shi? saboda kina da ɗaurin gindi a wurin Abbah shine zaki rinƙa yin abubuwa kamar wacce kike da alaƙa da mu, ki kama kanki domin zan iya yi miki rauni a yanda nake jin kaina yanzu..." wani dogon tsuka yaja sannan ya fice daga falon gaba ɗaya, har ya fice Baiwar ALLAH bata daina ganin bakin ƙofar ba domin ba ƙaramin razana tayi ba ganin irin bugun da yakai wa glass table ɗinta har sai da ya dagargaje.. Allah yaso akwai abun bugu a wurin da a ita zai kai bugun nan.. Wani irin haɗiyar yawu tayi sannan ta ƙara fashewa da wani irin matsanancin kuka a haukace ta soma wurgi da filillikan kujerun falon tana kuka tana faɗin "Nima bana sonka na tsane ka wallahi, you bastard, you are crazy and you are my enemy, you broke my heart Razhdeen why? why? why???...." Na ta ƙara fashewa da kuka, da iya ƙarfinta ta ɗauki glass table wanda yake a fashe ta wurga saitin plasman dai-dai lokacin da Roshan ya shugo da sallama a bakinsa ganin yanda plasman ya faɗo ƙasi a fashe yasa shi cewa "subhanallahi me zan gani haka?..." bin falo yake da ido ganin yanda tayi kaca-kaca da falon, Baiwar ALLAH da gudu ta wuce bedroom ɗinta tana kuka, Bin ta yake da kallo a tunaninsa rashin son zama da shi ne duk ya jawo haka, girgiza kai yayi tare da sauƙar da nannauyar numfashi ya ce "daman nasan baki haƙura da ƙudirinki ba Ammata, kinyi haka ne saboda ki faranta wa Abbah amma ba'a son ranki ba, amma Insha Allahu zan kawo miki good idea wanda zaki samu Dawwamammiyar farin ciki mai ɗorewa indai rabuwa da nine zai kawo miki farin cikin ki kar ki damu..." Shima Razhdeen a fusace ya fizgi motar sa yabar gidan gaba ɗaya... Bayan sallar isha'i da misalin ƙarfe 9 Baiwar ALLAH ce take zaune a falo idonta akan plasman ɗin jikin bango tana kallo amma sai dai hankalinta baya jikinta domin wani dogon tunani ta zurfafa, bata taɓa jin haushin Razhdeen kamar yau ba, gaba ɗaya taji ya wanke mata a rai especially idan ta tariyo maganganun da ya gaggaya mata, wani irin tsuka taja wanda har ya fito fili a cikin zuciyarta take faɗin "gwara na cigaba da zamana a gidan mijina domin hakan shi yafi mun alkhairi saboda bazamu taɓa dai-daita da Uncle Deen ba... tana cikin wannan maganar zuci kwatsam taji muryar Roshan yana faɗin "Ammata gimbiyar mata..." ya ƙarasa maganar tare da zama a kusa da ita idonsa akanta ya kuma cewa "idan ban takura miki ba ina so nayi magana da ke..." Itama Baiwar ALLAH bin kyakkyawar fuskarsa tayi da kallo, girgiza kai tayi alamar babu matsala. Gyara zama ya yi yana fuskantarta da murmushi akan fuskarsa ya ce "kiyi haƙuri Ammata nasan ina takura miki sosai, amma nasan amince da zama dani da kika yi a dole ne ba'a son ranki ba, amma na kawo wata mafita kuma nasan zaki ji daɗin haka sosai amma sai dai zaki ɗan ƙara haƙurin zama dani kafin aci nasara..." Baiwar ALLAH zuba masa ido kawai tayi tana son jin wani irin magana zai furta mata, Roshan ne ya cigaba da cewa "ba tare da kowa ya sani ba daga ni sai ke zamu tsara, zakiyi haƙuri ki zauna da ni na tsawon shekara biyu ba tare da mun kusanci juna ba duk da nasan ba amince dani zaki yi ba kamar yanda muke zaune a haka, idan har lokacin yayi na tsawon shekara biyu aka ga bakida ciki to za'a fara zargin ko ke bakya haihuwa ko dai ni, zan nuna cewa nine bana haihuwa kinga kuwa Abbah zai yanke cewa na rabu da ke domin kije ki Auri wanda zaki haihu da shi, nima zan goyi bayan haka! Abinda ba yanke kenam amma ki ƙara haƙuri da zama dani kinga zuwa lokacin nasan Razhdeen zai dawo daga U.S tinda shima two years zai yi..." Baiwar ALLAH jin abinda Roshan ke faɗi ne yasa ta haɗe fuska rai a ɓace ta miƙe tsaye ta bar falo ta koma bedroom ɗinta, ita a halin yanzu bata buƙatar jin sunan Razhdeen duk da har yanzu akwai son sa a cikin zuciyarta amma tayi alƙawarin zata fara cire shi a ranta... Roshan binta yayi da kallo tare da girgiza kai a fili ya furta "nasan shekara biyu yayi miki nisa tinda a yanzu baki ƙi na rabu da ke ba, amma wannan shine shawara mai kyau ba tare da an zargi wani abu ba..." Bayan sallar Asuba ne Razhdeen ya gama shirya komai tafiya ƙasar U.S ta kankama, a harabar gidan sa ya tsaya murfin mota a buɗe yana shirin shiga za'a kai shi airport domin su Abbah da Roshan tare da sauran ƴan gidan duk suna airport suna jiran isar sa suyi ban kwana, Ƴar Amana ce take ta fama kuka tana ƙoƙarin ƙwace wa daga riƙon da Madam Blessing tayi mata tana son bin Razhdeen yanda zai je, Razhdeen bai so ya tafi yabar Ƴar Amana ba domin ji yake kamar zai rasa ta ne har abada, yana cikin kukan zuci ya shige motarsa security ya yi driving ɗinsa suka tafi... Ƴar Amana ganin an buɗe gate sun tafi yasa ta fizgewa da ƙarfin gaske daga riƙon da Madam Blessing tayi mana tare da wurgar da bebin robar ta cikin fushi ta koma cikin falo tana hawaye, tsaya kallon da Madam Blessing tayi domin al'amarin Ƴar Amana sai Allah shima kan shi Razhdeen ɗin a hankali yake bi da ita... A ɓangaren ɗayan gidan kuma duk sun tafi ganawa da Razhdeen banda Baiwar ALLAH wacce ta kasance ita kaɗai a gidan bata je ko ina ba..... *HIP_HIP_HIP_HURRRRYY* *DAN ALLAH MASOYA KUYI HAƘURI DA JINKIRIN DA NAKE MUKU NIMA BA'A SON RAINA BA NE,* *EXAMINATION NAKE RUBUTAWA KUMA INA BUƘATAR NUTSUWA DOMIN KASAN ABUNDA ZAKA RUBUTA A ƊAKIN JARABAWA, KULLUM INA CIKIN KARATU, KULLUM SAI MUN SHIGA EXAM* *KU MUN UZURI DAN ALLAH KOMAI LOKACI NE KAMAR YANZU ZAN GAMA LITTAFIN GABA ƊAYA NASAN A MATSE KUKA🙏🙏* *GA SHORT PAGE* *BANIDA LOKACI AMMA GOBE IN SHA ALLAHU ZAN SAKE YI MUKU UPDATE TINDA BA EXAM..*.. asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *31_ TO_35* _________ONE YEARS AGO_________ Abbah yana zaune a babban falo tare da iyalansa, Ammy da Uwar masu gida da kuma Ƴar tinny dake kwance saman cinyar Ammy matar Abbah domin yanzu har ta fitar da Momminta daga cikin zuciyarta, dake tana samun kulawa sosai a wurin Ammy lokuta da dama tare suke kwana shi kuma Abbah ya koma part ɗinsa, Suna zaune a falon sai ga Roshan da Baiwar ALLAH sun shugo falo a tare bakin su ɗauke da sallama daman wasu lokuta sukan zo ziyarta su Abbah duk da a gida ɗaya suke... zama suka yi suma bayan sun gaggaisa da su Abbah, Ammy da murmushi akan fuskarta ta kalli Baiwar ALLAH ta ce "Daughter Abbah meyasa kwana biyu bakya shugo wa ne?..." Baiwar ALLAH kai a sunkuye ta ce "wallahi Ammy bana jin daɗin jiki na ne shiyasa..." Ammy ta ce "ayyah ban sani ba ai da zan je na duba ki, kuma naga Ummy tana zuwa part ɗinki amma bata sanar mun ba..." Baiwar ALLAH ta ce "ai itama bata sani ba..." Ummy uwar masu gida tana gefen Abbah cikin zolaya ta ce "kodai kodai mun samu ƙaruwa ne..." Zaro ido waje Baiwar ALLAH tayi tana faɗin "ƙaruwar mai?..." Ammy ce ta fara yin dariya ganin kallon da Abbah yake yi wa Uwar masu gida har da taguminsa jin yanda ta taƙarƙare ta zuba zance, girgiza kai yayi tare da faɗin "Allah ya shirya mun ke Mamana..." Rufe fuska tayi tana dariya domin sai yanzu take jin kunyar abinda ta faɗa... Ita kuwa Baiwar ALLAH kallon Roshan tayi ta gefen ido tana maganar zuci cewa "taya zan samu ciki alhalin a ƙaurace muke da juna, yau tsawon shekara guda da Auren mu amma ko a gado ɗaya bamu taɓa kwanciya ba, abun yana damu na wallahi, shi ya ce indai bani na neme shi ba bazai taɓa nema na ba, Ni kuma kunyar hakan nake, hmmmm! meye makomata a wurin Ubangiji na? shin laifi nake aikatawa kodai? dole zan nema wa kaina mafita domin a halin yanzu ina matuƙar ƙaunar mijina Roshan, yafi mun duk wani namijin da zan Aura, bazan taɓa rabuwa da kai ba Roshan..." Shi kuwa Roshan Abbah ne yake tambayarsa cewa "ina dai babu wata damuwa a tattare da zamantakewar ku na Aure?..." Da murmushi akan fuskar Roshan ya ce "babu komai Abbah muna zaune cikin ƙoshin lafiya..." Ya ƙarasa maganar yana kallon Baiwar ALLAH wacce itama shi ɗin take kallo domin yasan tana cikin damuwa na rashin son zama da shi wanda ba hakane a ranta ba, Baiwar ALLAH ta kasance mace ce mai zurfin ciki sai dai abu yaita damunta a ranta amma bazata iya sanarwa ba, ita a ranta tana son Roshan ya kasance da ita a matsayin matarsa ta Aure, burinta shine su zauna su cigaba da soyayyarsu kamar yanda ma'aurata suke kowa a cikin farin ciki, Roshan ganinta a cikin damuwa hakan na nuna masa cewa haƙurin zama da shi kawai take, especially idan ya tuno cewa twins ɗinsa take so, cije lips ɗinsa yayi yana kukan zuci domin yana da kishi sosai wanda bazai iya cigaba da zama da ita a haka ba, shi har yanzu baya ɗaukar kansa a matsayin mai Aure domin duk abinda ake samu a cikin Aure har yanzu bai same shi ba... Ko wannen su da abinda yake tunani a ransa, ita Baiwar ALLAH tana tunanin neman mafita yanda zata nasar masa cewa tana masifar son sa, shi kuma yana tunanin lokaci yayi kawai ya rabu da ita... Bayan nan Roshan ne ya tashi tare da faɗin "Abbah zan wuce wurin aiki na sai na dawo..." Abbah ya amsa masa cikin kulawa da cewa "Allah ya kiyaye a dawo lafiya..." Shima Abbah tashi yayi yabar musu falon suka cigaba da hirar su, ita dai Baiwar ALLAH a dole take iya yin magana... ____________________________________ Aunty Yolash ce take zaune a wantalelen falon ta dake garin Bauchi tana tare da wata ƙawarta wacce ta kawo mata ziyara, Knocking ƙofar falo aka shiga yi murya ciki-ciki Aunty Yolash ta ce "waye?" Daga waje ne Mai gadinta ya ce "Hajiya kin yi baƙuwa ne..." ta ce "daga ina?..." Mai gadi ya ce "wallahi ban sani ba Hajiya..." ta ce "ok ka ce ta shugo..." Mai gadi ya amsa mata tare da komawa bakin gate.. Aunty Yolash suna zazzaune suka ji an turo ƙofa da sallama a bakin matar da ta shugo, cike da mamaki Aunty Yolash ta miƙe tsaye baki ya gagara rufuwa ta ce "wa nake gani kamar Hajiya Kilishi..." Hajiya Kilishi murmushi tayi tana faɗin "wallahi Ni ce, kinyi mamakin gani na a garin Bauchi ko?..." Aunty Yolash ta ce "gaskiya kam saboda naga baki taɓa taka ƙafarki kinzo mun ba, nasan yanzun ma uzurinki ne ya kawo ki..." Hajiya Kilishi ta ce "ai ko ba uzuri zan iya zuwa miki ai..." Aunty Yolash taɓe fuska tayi ta ce "Banga alama ba saboda tin ana tare ma baki zo ba balle yanzu da ba'a tare..." Hajiya Kilishi sunkuyar da kanta ƙasi tayi tana shirin zubda ƙwallah, Ƙawar Aunty Yolash Hamdiyya ta ce "haba ke kuma Yolash ba'a haka bai kamata ba sam, mata ta taso daga yanda take tazo wurinki ki tsaya kina gaya mata magana ko wurin zama baki bata ba balle kayan drinks..." Aunty Yolash ta ce "ai nasan uzurinta ne ya kawo ta Bauchin..." Hamdiyya ta ce "to ko uzurinta ne ya kawo ta ai ta mutuntaki ne yasa ta zo har yanda kike, inda wata ce ai tafiyar ta zata yi baza ma ta kalli hanyar gidan ki ba...". Aunty Yolash kallon Hajiya Kilishi tayi sannan ta ce "ko dai kin yi bazawari ne anan Bauchi shiyasa kika kawo masa ziyara..." Hajiya Kilishi dai kai a sunkuye ta kasa ɗagowa balle ta haɗa ido da Aunty Yolash, Aunty Yolash ce ta kalli Hamdiyya ta ce "wannan ɗin dai Hajiya Kilishi ce matar Yayana General wanda ya rabu da ita...." Hamdiyya sake baki tayi tana kallon Kilishi cike da mamaki ta ce "wannan ɗin Hajiya Kilishi ce? Innalillahi naga duk ta rarrame kamar mai HIV ga fuska ta kokkoɗe tayi fiyau, ai ni bangane ta ba wallahi, duk meya faru da ita haka?..." Aunty Yolash ta ce "Nima ina zan sani, kamata yayi yanzu muga kin ƙara murmurewa kinyi ƙiba sakamakon ba'a takure kike ba, zaki iya fita duk san da kika ga dama ki dawo gida duk lokacin da kike so babu mai takura miki, kinsan General yana takura miki baya barinki kije duk yanda kike so yanzu kuwa kura ta mutu muyi wasa, yanzu kuma naga akasin haka sosai da duk kan alamu kina cikin tashin hankali Hajiya Kilishi, Kinga duk taƙamarki da izzarki da girman kanki yau ke ce a gaba na kina zubda ƙwallah?..." Hamdiyya ta ce "Kinga Yolash ki ce ta zauna mana tin shugowar ta take tsaye babu daɗi, ko ba komai ai an haɗu tunda akwai yara a tsakani..." Aunty Yolash ta ce "Ok ki shigo ki zauna..." Hajiya Kilishi ce ta ƙarasa shigo wa ciki ta zauna a ƙasin carpet, Aunty Yolash ta ce "a'ah tashi ki zauna akan kujera, ni bana wulakanta mutum duk wanda yazo gidana zan karɓe shi hannu bibbiyu yawwa..." Hajiya Kilishi ta tashi ta zauna akan kujerar falo ba tare da ta ce komai ba. Hamdiyya ce ta tashi tana faɗin "Ni zan koma gidana na bar yara su kaɗai..." Suka yi sallama Hamdiyya ta tafi tana mamakin ganin Hajiya Kilishi a cikin wannan halin... Aunty Yolash ce ta ƙwalla ƙiran ƴan aikin gidanta tare da sanar musu cewa su kawo wa baƙuwarta abinci da kayan drinks, Bayan ƴan mintuna sai ga su da kayan abinci da su fruit da drinks sun ajiye akan table ɗin tsakiyar falo tare da jan yo shi gaban Hajiya Kilishi, sai da Hajiya Kilishi ta gama cin abinci da sauran kayayyaki tukun ta fuskanci Aunty Yolash, Itama Aunty Yolash kallonta take tana son jin mai ke tafe da ita... Bayan Hajiya Kilishi ta ci tayi nak sai kawai ta fashe da kuka, Aunty Yolash ta ce "ha'a lafiya kuwa?..." Durƙusawa Hajiya Kilishi tayi da gwiwowinta tare da haɗe hannayenta biyu tana roƙon Aunty Yolash da cewa "Dan girman Allah Auntyn yara inaso ki mun wani taimako ba dan hali na ba, kamar yanda Allah ya rufa miki asiri dan ALLAH nima ki taimake ni ki rufa mun nawa asirin..." Aunty Yolash ta ce "kema Allah ya rufa miki asiri sai dai kece kika tona wa kanki asirin, abun ya ban mamaki shin wani irin taimako ne kike so nayi miki har da durƙusawarki wanda tunda kike baki taɓa yin gigin yin haka ba..." Hajiya Kilishi tana kuka ta ce "dan Allah kiyi haƙuri akan abubuwan da na aikata miki, nasan ban kyauta miki ba amma ki gafarce ni..." Aunty Yolash murmushi tayi tare da faɗin "nasan ba wai neman gafarata kika zo yi ba, akwai abinda ke tafe dake, Ni indai nine za'a zauna lafiya ƙalau ba tare da ɓacin rai ba don haka komai ya wuce a wuri na, shin wani taimako kike so nayi miki indai baifi ƙarfi na ba zan taimaka miki, Sannan ki tashi ki zauna akan kujerar bana son durƙusawarkin Nan..." Hajiya Kilishi tana sharar hawaye ta tashi ta zauna tare da faɗin "bazai ma fi ƙarfin ki ba, nasan kina ɗaya daga cikin waɗanda zasu faɗi magana General ya ɗauka ko shawari haka, kina ransa sosai, yana matuƙar ji dake...." Aunty Yolash ta katse ta da cewa "duk nasan wannan wa'azin just go ahead..." Hajiya Kilishi ta cigaba da cewa "Auntyn yara inason komawa gidan mijina, wallahi ina son kasancewa tareda mijina da kuma ƴaƴana, ina shan wahala sosai a gidan da nake, ga bani da kuɗi yanzu abincin da za'a bani ma ƙyashinsa ake wani sa'in ba'a bani, gidan mijina ya fi mun kwanciyar hankali, wallahi nayi nadamar abubuwan da na aikata a baya, nayi kuskure wanda yanzu nake son gyarawa..." Ajiyar zuciya Aunty Yolash ta sauƙar tare da faɗin "hakane bawa yakan aikata kuskure daga baya yayi nadamar abinda ya aikata, amma ina so ki sani cewa duk wanda ya tuba don wuya ba lada haka tushen hausar take amma tinda har kika gane gaskiyar lamarin duk ba laifi, amma a gaskiya komawa gidan General zai miki wuya domin a halin yanzu Yayana ba macen da yake jin daɗin tarayya da ita sai Amaryarsa, zai yi wuya ya zauna da wata mace bayan ita, kuma shi daman baya son zama da mata biyu kasancewa shi ba mazauni bane, shin a cikin maganar ki taimakon mai kike so nayi miki?...." Hajiya Kilishi tana kuka ta ce "inaso ki sa baki General ya mai dani gidansa..." Aunty Yolash ta ce "kai kai kaiiii ai duk yanda nake da General bazai taɓa yadda da wannan batun ba hasali ma ki ja mun baƙin jini a wurin sa, ga nan abokansa kije ki same su mana..." Hajiya Kilishi ta ce "kab abokansa waɗanda na sani babu wurin wanda banje ba amma ya ƙi sauraronsu akan batun, bansan wani irin zuciya ne da shi ba..." Sauƙe numfashi Aunty Yolash tayi tare da faɗin "ke ma bakya jin magana Hajiya Kilishi, ke kika jawa kanki komai wallahi duk abinda ya faru laifinki ne, inda ace kin kama kanki da mutuncinki a gidan mijinki da duk hakan bata faru ba, me zaisa kiyi abinda har Aurenki zai mutu? kin dai san General yana da matuƙar haƙuri amma idan aka kai shi maƙura baya taɓa sauƙowa akan abu, kuma idan ya cire abu a ransa baya taɓa maida shi, kin ƙure shi sosai, kinsan babu wanda zai iya riƙe ki mai zai sa ki bar gidan mijinki? kowa yana rufawa kansa asiri amma ke kina ƙara bankaɗawa kanki asiri, Ni a koda yaushe ina baki shawara bawai bana sonki bane amma kika ɗauki ƙiyayya kika ɗora mun, gani kike babu maƙiyiyar ki kamar ni, Ni kuma ina zaune da mutum da zuciya ɗaya ne, kuma wallahi wannan ranar nake guje miki kuma gashi yazo shin meye amfanin haka?..." Hajiya Kilishi babu abinda take sai kuka ta ce "bayan fitowa ta daga gidan mijina ba ƙaramin wahala nake sha ba, kowa ya kasa riƙe ni, da farko a gidan ƙanwar mahaifiyata nake zaune amma itama daga baya ta kore ni wai bazata iya riƙe ni ba, sai na koma gurin baffana shima matansa sun hanani zama a gidan, duk zuriya babu yanda ban zagaya ba amma an rasa wanda zai riƙe ni daga ƙarshe dai zaman Abuja ya gagare ni saboda babu yanda zan shiga ga tsadar rayuwa ga bani da kuɗi, abincin da zan saya na ci gagara ta yake, yanzu haka ina zaune a garin suleja na kama gidan haya, to kuɗin da zan biya babu kuma watannin biyan kuɗin ya ƙare, bansan da wanne zan ji ba, shin da kuɗin abinci yau da kullum ko kuma kuɗin hayan gidan da nake?..." Hajiya Kilishi ta ƙarasa tana fashewa da kuka. Aunty Yolash sarkin tausayi ba ƙaramin tausaya mata tayi ba, ta ce "ke nam babu yanda zaki je ki zauna? abincin da zaki ci gagaranki yake shin ina Alhajan ƙawayenki matan manya-manyan masu kuɗi? shin kina nufin ki ce bakida bazawarai? to ma ina wanda kike bin sa hotel bazai iya taimaka miki bane?..." Hajiya Kilishi dakatar da yin kukan tayi tana faɗin "yanzu na gane su waye masoyana da kuma maƙiyana, ƙawaye na suna hulɗa dani ne saboda kuɗina da kuɗin mijina, basa kula talakawa idan suka fiskanci bakada komai ka tsiyace daga nan zasu raba hanya da kai duk haka suke, suna ƙawance da wacce take da kuɗi, kuɗi sai kuɗi to ni kuma yanzu banida komai, aikin da nake yi ake biyana maƙudan kuɗaɗe kamfanin General ne kuma ya sallame ni, ko ba kuɗin salary General baya barina ba kuɗi, Bazawarai kuma su waye zasu zo mun? idan kinga mutum yazo mun to bada niyar Aure yazo ba sai da niyar iskanci, Ni kuma na shiryu bazan iya bada kaina ba saboda kuɗi duk da wahalar da nake sha, duk kowa ya gujeni, wasu sunyi blocking number na wasu kuma idan na ƙira su basa picking, wai daman haka rayuwar take?...." Ta ƙarisa maganar tana kallon Aunty Yolash, Aunty Yolash ta ce "yanda kika yi dai haka akayi miki, Allah ya ɗanɗana miki kiji yanda sauran mutanen suke ji da zaran sun zo neman taimakon ki, shin ba haka kike yi ba? idan kina tare da mutum da zaran ya rasa wani abu shikenam zaki nemi hanyar barinsa a cikin ƙunci maimakon ki taimaka masa, hatta ƴan uwanki bakya taimaka musu shiyasa suma yanzu bazasu iya taimaka miki ba, kar ma kiga laifinsu domin ke kika fara ɗanɗana musu raɗaɗin haka, duk wani ɗan uwanki da zaran yazo yanda kike zaki nemi kici masa mutunci sannan ki kore shi, wallahi ban taɓa ganin mata marar wayo ba sai ke, ai inda Ni ce a mazanninki babu wani ɗan uwana da zaiyi kukan talauci, jansu zanyi a jikina suma su ci arziƙi saboda nasan wata rana wani abu zai iya faruwa dani wanda dole sai ƴan uwana ne zasu mun, amma ke daga ke sai ƴaƴanki bakya son wani ya raɓi jikinki, ga shi yanzu kin ci ke kaɗai sannan kina shan wahala ke kaɗai yanzu meye amfanin haka?..." Hajiya Kilishi ido yayi jawur fuska a kokkoɗe ta ce "nayi nadama bazan ƙara aikata makamancin abinda na aikata a baya ba..." Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai kin san masu sonki da kuma waɗanda basa sonki..." Hajiya Kilishi tayi saurin katse ta da cewa "indai ata ɓangaren ƙawaye da kuma abokai babu masu Sona tsakani da ALLAH, ƴan uwana kuma daman haushi na suke ji shiyasa suka kasa taimaka mun..." Aunty Yolash ta ce "tam yanzu dai idan Allah yasa kika koma gidan General babu ruwanki da wani ɗagun kai da girman kai da wulaƙanci da kuma masifa ki kama kanki, kinga wacce take zaune yanzu babu ruwanta batada tashin hankali, idan wani abu ya ɓullo za'a ce ke ce..." Hajiya Kilishi ta ce "ai babu abinda zai faru Insha Allahu, zan riƙe abokiyar zamana hannu bibbiyu..." Aunty Yolash murmushi tayi sannan ta ce "Ni na manta ashe dai kince bakya son zama da kishiya..." Hajiya Kilishi ta ce "wallahi ruɗin duniya ne amma ni yanzu General ko mata uku ya jera to zanje na zauna ata huɗun..." Aunty Yolash ta ce "to shikenam gobe Insha Allahu zan shiga jirgi naje Abuja na same shi da maganar duk yanda ake ciki zanje har yanda kike a sulejan na sanar miki..." Hajiya Kilishi bata san lokacin da ta washe baki ba na farin ciki ta ce "Nagode sosai Auntyn yara Allah ya saka da ALKHAIRI..." Aunty Yolash ta ce "kar ki damu, a rayuwata na tsani ganin uwa ta fita tabar ƴaƴanta a gida ina jin takaicin haka, amma sai dai ƙaddara ta riga fata, za'a san yanda za'ayi Insha ALLAHU...." Hajiya Kilishi cikin nuna farin ciki ta miƙe tare da faɗin "shikenam Auntyn yara Ni zan koma suleja..." Aunty Yolash ta ce "ok muje na sauƙe ki a airport to..." Hajiya Kilishi ta ce "a'ahh bani da kuɗin hawa jirgi, zanje na shiga mota..." Aunty Yolash gani ɗaya tayi wa Hajiya Kilishi tasan bata da kuɗin motar ma kawai tayi iya kuɗin zuwa ne, Ta ce "shin kina da na motar ne?..." Hajiya Kilishi sunkuyar da kanta tayi ƙasi tare da girgiza kai, Aunty Yolash ta ce "Ok kar ki damu, idan kika ce mota zaki shiga zaki yi dare ne, muje kawai na biya miki na jirgin..." Aunty Yolash ta haura saman upstairs yanda room ɗinta yake taje ta ɗauko wasu maƙudan kuɗaɗe a cikin baƙar laida ta sauƙo tare da miƙawa Hajiya Kilishi tana faɗin "ga wannan kije ki biya duk kan buƙatunki da su, ki biya kuɗin haya sannan ki sayi kayayyakin abinci da dai sauran abubuwan da kike buƙata..." Cikin nuna farin ciki Hajiya Kilishi ta karɓa tana godiya haɗi da cewa "wannan ai zan daɗe ina amfana da su.." Aunty Yolash ta ce "to muje na biya miki kuɗin jirgi ..." A tare suka fita Aunty Yolash ta ja su a mota sai airport.... ___________________________________ A bangaren Ƴar Amana kuwa har zuwa wannan lokutan fushi take da Razhdeen saboda ya tafi ya barta, ma sha ALLAH sai haɓaka take tayi, a shekara ɗaya ta zankaɗe tayi tsayi ga dirin jiki kamar wacce ake hura mata iska, fatar jikinta kuwa kamar zaka taɓa jini ya fito tsabar farin da tayi ba ƙaramin kyau tayi ba, ga gashin kanta a baje kamar wanda ake ƙara jansa sai tsayi yake yana tafe da murɗi-murɗinsa, ta ko ina a jikinta ya ciko hatta breast ɗinta sun fito sun cicciko, ƙugunta kuwa ba'a magana daman kuma can Ƴar Amana ba siririya bace da ɗan dirinta balle yanzu ta haɗa da cikar budurci, hips ɗinta irin mai shape ɗin kifi ne. Tana zaune a falo tana kallo kwatsam taji Madam Blessing ta zauna kusa da ita tana shirin miƙa mata wayar hannunta, da sauri Ƴar Amana ta ture wayar tare da miƙe wa tabar falon ta koma room ɗinta domin tasan Razhdeen ne yake son yin video call da ita, tinda Razhdeen ya tafi tsawon shekara guda Ƴar Amana bata taɓa yadda sunyi video call ba shi kuwa kullum sai ya ƙira madam blessing akan ta haɗa shi video da Saararsa amma fur Ƴar Amana taƙi yadda hatta photo bata taɓa yadda tayi ba tinda Razhdeen ya tafi saboda tasan indai ta ɗauka sai madam blessing ta tura masa, kullum sai yayi complain akan a turo masa photon Saarah amma Ƴar Amana taƙi, har takai ta kawo yanzu indai taga waya a hannun madam blessing bata yadda ta zauna a kusa da ita saboda kar ta ɗauke ta a photo, a tunanin ta indai yaji zafin haka zai dawo. Madam Blessing bayan Ƴar Amana tabar falon girgiza kai tayi ta cigaba da magana da Razhdeen tana faɗin "Yallaɓai indai kana son ganin Saarah gwara ka ware lokaci ɗaya kazo ka koma, nake gaya maka in kaga yanda yarinyar nan ta girma saika kama baki, ba ƙaramin girma tayi ba amma sai dai har yanzu bata fara period ba, amma tana dab da farawa saboda ta cika sosai, amma Yallaɓai a tunaninka zata yi shakara nawa?..." Daga ɓangaren Razhdeen wanda yasa computer a gaba domin da shi yake video call ya ce "ina tunanin bazata wuce 17 years or 18 ba, Madam! Sarah yarinya ce ƙarama just girman jiki ne kawai..." Madam Blessing ta ce "okay zan fara sa mata ido saboda tana dab da farawa ai lokacin ta yayi..." Shima Razhdeen cewa ya yi "ki kula mun da ita sosai, ki fara gwada mata yanda zata yi kafin ta ankara da shi domin zata iya tsorita duk lokacin da abun yazo..." Madam ta ce "okay kar ka damu tinda tana jin abinda ake ce mata mayar wa ne bazata iya ba ai da sauƙi..." Razhdeen ya ce "about her school ina tana gane karatu?..." Madam Blessing ta ce "sosai ma, wallahi nake gaya maka inda ace yarinyar nan tana magana ba ƙaramar yarinya mai ilimi da fahimta za'ayi ba, yanzu ma tin daga kan note ɗinta zaka gane tanada ilimi..." Razhdeen murmushi yayi ba ƙaramin jin daɗin hakan yayi ba, ya ce "good..." Madam Blessing ta kuma cewa "Yallaɓai zan maka rainonta yanda ya kamata, gashi kun dace sosai, miskilancin ku ɗaya da kuma zafin rai..." Razhdeen ya ce "me kike nufi?..." Ta ce "tana gama school kawai ka Aure ta tin kafin a rigaka..." Tsuka ya ja tare da faɗin "You're very stupid Madam Blessing, this younger girl kike mun maganar Auren ta? look ina kiwatata ne saboda na ɗauke ta a matsayin ƴata..." Madam Blessing zaro ido waje tayi tare da faɗin "ƴarka dai? No don't said that, me laifin kace ƙanwarka amma ƴa ai babu Aure a tsakani kenam..." Razhdeen ya ce "look wai waye ya ce Auranta zan yi ne? Nigeria people kuna da matsala sosai, Ni akwai wacce nake son Aura anan ƙasar U.S kuma Soja ce..." Madam Blessing ta ce "Yallaɓai Are You serious?..." Kafin ta ƙara cewa wani abu Razhdeen yayi saurin katse wayar, Madam Blessing girgiza kai tayi tana murmushi domin tasan Razhdeen ba wata budurwar da yake da shi kawai ya faɗa ne... Washe gari da safe Ƴar Amana ta sauƙo falo cikin shirin kayan uniform da jakarta a goye a baya, tayi gyaran gashin ta tayi rolling donut da gashin, ga ta gaban gashin ta gyara da Gel daman su school ɗinsu ba'a saka hijab ko hula ko kuma gyale haka nan ake barin gashi a waje, shiyasa ko wacce take ƙoƙarin gyara gashin ta, da masu tsara kitso da kuma masu saloon su gyara gashin, ita ƴar Amana bata kitso sai dai Madam Blessing ta kaita wurin saloon a gyara gashin, Style ɗin uniform ɗinsu kuma doguwar riga ne zuwa gwiwa baya sauƙa ƙasi sai sapa da thorns mai tudu, makarantar akwai gasar fashion dake private school ne na ƴaƴan masu kuɗi, Ƴar Amana bayan ta gama shirinta zuwa tayi ta zauna akan dinning table daman an haɗa mata abinci kala-kala masu kyau da gyaran jiki shiyasa take ta haɓaka kamar yeast, madam Blessing ba ƙaramin gyara Ƴar Amana take ba kamar ƴar cikinta haka take ji da ita, bayan ta kammala breakfast goya jakarta tayi mai bala'in tsada sannan ta ɗauki lunch bag ɗinta wanda a ciki haɗin abinci ne masu rai da lafiya da kayan fruits, Madam Blessing rakata tayi har harabar gidan yanda security yake jiran fitowar ta, Ƴar Amana babu a wanda tayi wa alamar magana kai tsaye mota ta shige ta zauna a back seat ta ci boom kamar wacce ba'a halicce ta da fara'a ba, haka security ya ja mota suka fi ce... Madam Blessing ɗaga mata hannu take tana mata fatan alkhairi amma Ƴar Amana ko kallon yanda take bata yi ba, Razhdeen yasa tana fushi da kowa daman can ba'a taɓa ta ba yata ƙare balle an tsokano ta.... Abbah kuwa har an sanar masa cewa akwai mutane a gidan da Razhdeen yake kafin ya ankara kuwa Roshan ya sanar masa cewa akwai wacce ta karɓi aron gidan ne zuwa nan da shekara biyu kafin Razhdeen ya dawo.. Abbah ne ya amsa da cewa "okay na fahimta..." A ranar yau ne Aunty Yolash tazo Abuja zata cika wa Hajiya Kilishi alƙawarin da ta ɗaukar mata na cewa zata same shi... A falon Meeting ɗin Abbah Aunty Yolash ta same shi zaune yana daddanna computer sa, zama tayi tare da gaishe shi, ya ɗago yana murmushi ya ce "Auntyn yara yau kece a garin Abuja?..." Tana dariya ta ce "wallahi kuwa Yaya na shiga ciki ai Ammy take sanar mun cewa kana nan falon ka..." Abbah ya ce "tamm akwai problem kenam tinda har kika kasa jirana a can public falo..." Aunty Yolash ta ce "ai daman Yaya maganar da zamuyi yana buƙatar sirri ne..." Abbah ya ce "meya faru ne Auntyn yara?..." Aunty Yolash har fargaban fara tuntuɓar Abbah take da maganar domin tasan ba ƙaunar jin zance Hajiya Kilishi yake ba, zuciyarta ne ya fara bugun uku-uku tana haɗiyar yawu ta ce "Daman! Daman!! akan magana mai muhimmanci ne..." Abbah ya ce "yadai? Ina jinki..." Aunty Yolash ta fara da cewa "Yayana Allah S.W.A ma muna masa laifi kuma ya yafe mana, mu kasance masu haƙuri a rayuwa, muyi koyi da manzon Allah S.A.W...." Abbah shafa farin gemunsa ya fara yi yana faɗin "too gama mun wa'azi tukun sai ki gayi abinda ya kawo ki ko..." Aunty Yolash ta ce "Yaya shin idan mutum yayi maka laifi kuma yazo neman gafarar ka shin zaka haƙura ko kuma ?..." Abbah kwata-kwata bai kawo maganar Hajiya Kilishi a ransa ba, shi har ya manta da wata Kilishi kuma bayan haka Aunty Yolash bata taɓa masa maganar ta ba balle ya kawo haka a ransa, Ya ce "indai yayi laifi kuma daga baya ya gano kuskurensa ya nemi a ayafe masa da gaske har cikin ransa mai zai hana a yafe masa, ai akwai laifukan da muke yi wa Ubangijin mu a sanin mu ko ba'a sanin mu ba mu roƙe shi kuma ya yafe mana balle mu marasa tunani, indai akwai zuciyar musulunci zan yafe masa mana..." Aunty Yolash ta ce "Alhamdulillah haka nake son ji, nasan Yayana akwai tawakkali da yafiya da juriya..." Abbah ya ce "Ni fa na tsani jan rai idan zaki faɗi magana kin rinƙa jan zance kenam..." Aunty Yolash ta ce "sorry Yayana daman inaso ka yafewa Hajiya Kilishi abinda ta aikata maka, ta wakilce Ni akan nazo na baka haƙuri tayi nadama, kuma wallahi Yaya da gaske take kaga yanda ta zama kuwa kalar tausayi, wai tasan idan tazo yanda kake korar ta zakayi shiyasa ta turo Ni..." Abbah yayi mamakin jin wannan magana daga bakin Aunty Yolash domin yasan ba shiri suke yi ba, Ya ce "aina kika haɗu da ita?..." Aunty Yolash ta ce "jiya har Bauchi taje ta same ni da maganar..." Jinjina kai Abbah yayi tare da faɗin "zan yi maganin wannan matar indai bata daina bin Abokaina da ƴan uwana ba, na ce bazan dawo da ita gidana ba amma sam ƙwaƙwalwarta na kifaye ne, Ni ban iya zama da mata biyu ba, kuma bazan fara ba tunda da yarinta ta banyi ba balle yanzu da tsufa ta soma kamani..." Aunty Yolash ta ce "Yaya ka yafe mata Please..." Abbah ya ce "Ni indai nine taje na yafe mata duniya da lahira tin ba yau ba, wallahi na yafe mata, alaƙa ce dai na yanke..." Aunty Yolash kamar zatayi kuka ta ce "Yaya ka dawo da ita kan Ƴaƴanta..." Abbah ya ɗaga mata hannu yana faɗin "Kinga Yolash in ba so kike na ci mutuncin ki yanzu ba kibar mun wannan maganar..." Aunty Yolash ta ce "haba Yaya matar nan baka san irin wahalar da take sha ba, ga babu yaranta a kusa da ita balle taji sanyi a ranta, ka rabata da komai hatta aikinta da take yi tana samun Salaryn ta ka kore ta shin ya kake so tayi ne, tana ta bin duk ƴan uwanka tana neman gafararsu akan abubuwan da tayi musu sannan tana neman alfarmar a baka haƙuri ta dawo, ita ko ya ya ne zata zauna a haka, yanzu wallahi asirinta a bankaɗe yake..." Kafin takai ƙarshen maganar ta Abbah ya darara mata tsawa da cewa "you're very stupid Khadijah..." Zaro ido Aunty Yolash tayi tana kallon Abbah wanda ya ambaci asalin sunanta wanda tinda yake bai taɓa ƙiran sunan ba sai yau, cike da mamaki take bin sa da kallo zuciyarta na bugun uku-uku domin ransa ba ƙaramin ɓaci yayi ba... Abbah ya cigaba da cewa "Na rantse da sarkin dake busa mun numfashi idan ban yanke alaƙata da ke ba ki canza mun suna wallahi tallahi...". Ba Aunty Yolash ba hatta Ammy wacce shugowarta kenan tana ɗauke da try ɗin lemuka ta kawo musu jin kalmar da Abbah ya furta ne yasa ta sakin try ɗin drinks a ƙasin carpet tsabar firgici.. Abbah ya cigaba da cewa "ki je ki tambayi wasu abokai na duk na fita shirginsu sakamakon yawaita mun maganar Kilishi, nace bana sonta bazan dawo da ita ba ana dole ne?..." Aunty Yolash miƙe wa tsaye tayi tana faɗin "Allah ya baka haƙuri Ni na tafi..." Abbah ya ce "ki tafi mana, kar na sake ganin ƙafarki a gidan nan iskancin banza kawai..." Ammy ranta ya sosu sosai jin abinda Abbah ya ke faɗi kuma duk saboda an kawo masa maganar Hajiya Kilishi, Ammy ta ce "wai Abban yara shin ba'a yafiya ne? ka dawo da mata kan ƴaƴanta mana ya zaka raba uwa da ƴaƴanta..." Abbah ya kalle ta a fusace ya ce "kema ko? ke ma ko? ke ma ko to wallahi ke ma kika mun maganar ta zaki koma gidan ku ne..." Ammy dafe ƙirji tayi ido a zazzare ta ce "subhanallahi, A'uzubillahi Minal shaiɗani rajin, wannan kalmar tinda nake a duniyan nan a kuma zaman Aure da nayi ban taɓa jin a furta mun ita ba sai yau, a rayuwata bana fatan dan na samu matsala da mijina na koma gidan mu Allah ya kiyaye mun ganin wannan ranar, ina fatan dana ga wannan ranar gwara Allah ya ɗauki numfashi na, ban taɓa samun matsala da mijina ba balle ya kore ni gidan mu, kuma haka ƴar uwata maman su Razhdeen kaine shaida bata taɓa complain akan matsalar da kuka samu ba balle take gida har ta cika da imana, haka Nima har nayi rayuwa da mijina marigayi bai taɓa korata gida ba, Amma yanzu ka furta mun wannan kalmar...." Ta ƙarasa maganar tarar da fashe wa da kuka ta juya da gudu ta koma part ɗinta tana kuka, Uwar masu gida ganin Aunty Yolash ta fito daga part ɗin Abbah tana kuka yasa hankalin ta tashi yanzu kuma ta sake ganin Ammy tana kuka ta wuce part ɗinta nan ne hankalin ta ya ƙara tashi can sai ga Abbah ya zo ya wuce part ɗin Ammy domin hankalinsa ba ƙaramin tashi yayi ba ganin hawayen Mar'atussaliha.... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *36_ TO_40* Misalin ƙarfe 10 na dare Roshan yana kan sallaya bayan ya kammala sallar lafilfilinsa yana jan carbi a hankali bakinsa motsi, jin knocking ɗakin da yake ne yasa shi ɗago da kansa yana kallon bakin ƙofar, miƙewa yayi cikin farar jallabiyar sa ba tare da ya tambaya ba ya buɗe ƙofa, ganin Baiwar ALLAH yasa shi mamaki domin tinda take a cikin gidan nan bata taɓa zuwa ta buga masa ɗaki ba ko hanyar wurin bata yi, cike da mamaki ya ce "Am lafiya kuwa yau na ganki a part ɗina?..." Baiwar ALLAH ba tare da ta bashi amsa ba ta ƙarasa shugo wa ciki, kamar zatayi kuka haka take bin sa da kallo ta ƙudurta a ranta cewa yau kam zata sanar masa gaskiyar abinda ke ranta domin bazata iya cigaba da zama a haka ba, ko ganin yanda su Abbah suke shan soyayyarsu da Matarsa abun yana bata sha'awa, Zuwa yayi ya tsaya a gabanta yana mata kallon ƙurilla ya ce "meya faru ne?..." Yamutsa fuska tayi tare da faɗin "sai wani abu ya faru tukun da na zo ɗakin ka?..." Ya ce "to ai naga baki taɓa zuwa bane shiyasa dole abun zai ban mamaki tsawon shekara guda ana tare..." Tana son sanar masa amma sai dai bazata iya ba kawai sai ta fake da cewa "daman, daman naji motsi ne a ɗakin da nake Ni kuma ina jin tsoro..." A ruɗe ya ce "motsi kuma? muje na duba miki..." Haka ya riƙe hannunta suka nufi waje kai tsaye part ɗinta suka nufa, yana zuwa ya soma Dube-dube amma bai ga alamar motsi ba. Ita kuwa zama tayi a bakin gadonta ta wani zuwa masa ido sai sakin murmushi take, wani irin kallon so da ƙauna take masa wanda ita kanta bata san tana masa ba, Juyowar da zai yi yaga ta zuba masa ido sai kallonsa take ba ƙaƙƙautawa, kaɗa mata yatsunsa yayi a sai tin idonta, a firgice ta dawo hayyacinta tana sauƙe nannauyar numfashi, ya ce "Are You Okay?..." Jin tambayar da yayi mata ne yasa ta dafe goshinta tana faɗin "kai na ciwo..." tayi haka saboda kar ya gano ta... Ya ce "ok sorry bari na kawo miki magani..." yana kai wa nan yayi ficewar sa, can ba jumawa sai gashi da magani haɗi da gorar ruwa yana zuwa ya miƙa mata. Hannu tasa ta riƙe hannun idonta akan sa, Roshan ganin hannunsa ta riƙe ba gorar ruwan ba yasa shi cewa "kin riƙe mun hannu..." Sunkuyar da kanta tayi ƙasi tare da faɗin "yi haƙuri..." ta karɓi gorar ruwan da magani.. Ya ce "ki sha maganin ina zuwa yanzu..." ya buɗe ƙofa ya fice da sauri da duk kan alamu yayi mantuwa ne, Baiwar ALLAH bin bayansa tayi da kallo tare da sakin murmushi, ta ɓaro magani sannan ta miƙe tsaye ta nufi kan mirror ta ɗauki biro a tsakiyar magani ta rubuta farkon harafin sunan Roshan wato ("R") har takai maganin sai tin bakin ta kawai ta dakatar, tunowa tayi shima Razhdeen farkon sunansa kenam, yamutsa fuska tayi tare da sa biro ta ƙara harafin O a gaban R tana nufin ROSHAN kenam tasau murmushi ta kai maganin bakinta tare da korawa da ruwa ta haɗiye. Roshan ne ya shugo ɗakin yana waya daga ƙarshe ya katsar idonsa akan Baiwar ALLAH wacce itama shi ɗin take kallo, buɗar baki yayi ya ce "shikenam yanzu babu wata matsala ko? Ni zan koma part ɗina..." Baiwar ALLAH ji tayi zuciyarta ta buga domin bata so yayi nesa da ita, ya juya zai tafi kenam yaji tana kuka tare da faɗin "wayyo kaina ciwo, hajijiya nake ji..." Juyowa yayi ya kalle ta yaga tana shirin faɗuwa ƙasi da gudu ya nufi yanda take ya rungumota tare da faɗin "sannu ko ina kinsha maganin?..." Itama riƙe shi tayi sosai tana faɗin "ka taimake ni zan mutu..." Kwantar da ita yayi akan gado ya ce "ki kwantar da hankalinki babu abinda zai same ki, kiyi bacci kinji ..." ya rufa mata mayafi sannan ya juya zai tafi yaji ta riƙe masa hannu.. Juyowa yayi yana kallonta kamar zatayi kuka ta ce "ina jin tsoro dan ALLAH yau ka kwana anan..." Sakin murmushi yayi tare da faɗin "Ok shikenam ba damuwa..." ya ɗauki pillow daga kan gadon yana faɗin "barin naje na kwanta akan doguwar kujeran can..." Nan ma ƙara riƙe masa hannu tayi ta ce "can you sleep with me?..." Cike da mamaki ya ce "whattt?..." cikin ƙiƙƙina ta ce "ina nufin anan..." ta nuna masa bakin gadon.. Kaɗa mata kai yayi ya ce "okay..." ya ajiye pillow sannan ya kwanta ata baki-bakin gadon, ita kuma tana ta bayansa murna take yau zata kwana gado ɗaya da Roshan... Ta ce "Am ka manta baka kashe ligh ba kuma ni bana iya yin bacci da haske..." Tashi yayi yaje ya kashe ya dawo ya kwanta kamar yanda yake ya juya mata baya... Yana tunanin abubuwa da dama a ransa, yana jin wani abu akan Baiwar ALLAH amma haka yake jure wa, yana maganar zuci ya ce "inasonki Ammata amma haka zan bawa zuciyata haƙurin rashin ki, kina so ki Auri twins ɗina kuma lokaci nake jira na rabu dake kije ki Aure shi, nayi alƙawari a kaina cewa bazan taɓa saninki a matsayin ƴa mace ba domin inada kishin da bazan iya yin sharing ba, bazan iya Auran mata kuma bayan na gama saninta a matsayin ƴa mace daga baya nazo na rabu da ita ba, wani kuma daban yazo ya Aure ta i can't, Ammata indai zaki zauna dani har ƙarshen rayuwar mu wallahi ko a yanzu kika nuna mun buƙatarki a shirye nake dana kusance ki, amma in har ƙudirin ki yana nan na Auran twins a gaskiya ko zamuyi shekara ɗaki a haka bazan iya kusantarki ba, bana son sharing! bana son sharing, bana son sharing..." Yana cikin wannan surutan a cikin zuciyarsa kwatsam sai ji yayi Baiwar ALLAH ta rungumoshi ta baya, Shuru yayi yana jin yanda ta manno jikinta jikin na shi, wani irin haɗiyar yawu yayi tare da ƙarƙame idanuwansa baya so ta tayar masa da feeling shi kuma bazai iya kusantarta ba, haka yake cikin wannan halin yana jurewa tare da jero Addu'o'i har bacci ya yi awun gaba da shi. Ita kuwa Baiwar ALLAH kasa bacci tayi a tunanin ta Roshan zai juyo gareta ne sai kuma taga akasin haka ko ƙwakƙwaran motsi bai yi ba, tayi takaicin haka sosai domin ba haka taso ba, tana rungume da shi tana ta saƙe-saƙe a ranta, jin alamun yayi bacci yasa ta ɗan juyo da shi tana ƙarewa fuskarsa kallo can ta sumbace shi akan goshi, ta ɗago sannan ta ƙara sumbatar sa a gefe da gefen fuskarsa, daga ƙarshe ta ɗora lips ɗinta akan nashi tayi masa wani irin hot kiss wanda sai da ya ɗan motsa yana shirin buɗe eyes ɗinsa, ɗagowa tayi tana kallonsa shi kuwa ya ƙara zarce wa da yin baccin, itama kwantar da kanta tayi kan ƙirjinsa da haka har bacci ya ɗauke ta... Sys.Out.PrintIn ("WASHE GARI"); } Aunty Yolash ce a cikin jirgi ta miƙi ƙasar Jidder tana son samun Mai martaba akan maganar Abbah da Hajiya Kilishi ko shi zai iya sauraronsa.. ______________________________________ Aunty Yolash ce zaune a babban falon cikin gidan tana tare da INDO second ɗin Mai martaba a yayin da ita kuma Maamie tana can part ɗinta, Hira suke sosai suna shan dariyar su domin Aunty Yolash da Indo jinin su ya haɗu sosai, suna cikin shan hirar su sai ga MAAMIE ta sauƙo daga upstairs idonta akan Aunty Yolash duk tana wani binsu da harara, sauƙo wa tayi ta nemi wuri ta zauna tare da ɗora ƙafa ɗaya akan ɗaya tana tauna ciwgim, Aunty Yolash ce ta kalleta tare da sakin murmushi a ranta tana faɗin "mun ga Hajiya Kilishi ma kuma daga ƙarshe abun baiyi mata kyau ba, kowa da ranar sa kema wata rana sai kinyi kuka da idonki kinzo kina neman gafarar mutane..." ta ƙarasa maganar idonta akan Maamie, Maamie ce ta zaro mata idanu tana faɗin "lafiya kuwa Malama kike kallona ko dai akwai abinda na tare miki ne..." Aunty Yolash ta ce "naga kin shugo mana ba sallama ne..." Maamie ta ce "ke dakata nan fa yanki nane yawwa, gidan mijina gidana bazaki zo ki takura mun ba, ke asu wa har zakiyi magana akan banyi sallama ba..." Aunty Yolash ta ce "hakane kamar yanda kike gadarar gidan mijinki ne haka Nima nake gadara da gidan Yayana ne uwa ɗaya uba ɗaya, kuma hasali na fiki iko da gidan domin ke ko a yanzu aka baki takardar saki dole ki bar gidan, kuma mu ƙi maido ki in juninki rashin mutunci ne..." Maamie ta ce "ai wallahi bari kiji ni da gidan nan Auren zobe ne ba rabuwa sai dai mutuwa, in hassada kike mun ma gwara ki shanye abun ki..." Suna cikin wannan cacar baki sai ga Mai martaba ya shugo da sallama a bakinsa domin ya gama sallamar baƙin da yayi a falon masarautar, zama yayi yana fuskantar Aunty Yolash da murmushi akan fuskarsa domin ba ƙaramin farin ciki yayi ganin Autar ɗakinsu ba, gaisawa suka yi sannan ya ce "Yolash mutan boko yau ɗin boko ya barki kin kawo wa ɗan uwanki ziyara kenam..." Aunty Yolash ta ce "Yaya mai martaba inason zuwa daman amma ɗawainiya sun mun yawa..." Mai martaba ya ce "yanzun ma nasan akwai abinda ya kawo ki ai tinda ban ganki da akwatin zaman hutu ba..." Dariya tayi ta ce "wallahi a yau zan koma sai kuma idan na tashi zuwa da akwatin zan zo nayi muku hutu sosai..." Murmushi yayi tare da faɗin "Allah sarki ƴan uwa daɗi..." Itama murmushi tayi. Mai martaba ya ce "fatan dai kinci abinci ko?..." Ta ce "tin zuwa na Aunty Amarya ta kawo mun ina ci muna shan hira da haka na kammala..." Ya ce "Masha Allah haka ake so ai, yanzun me yake faruwa ne?..." Aunty Yolash ta gyara zama ta kwashe duk halin da ake ciki na Abbah da Hajiya Kilishi ta sanar masa, ta cigaba da cewa "Mai martaba ko dan ƴaƴanta a dawo da ita duk da yaran sun mallaki hankalin kansu, itama kanta Kilishi zata fi nutsuwa, a halin da take ciki inta cigaba da zama a haka ba'a san mai zata aikata zuwa gaba ba tinda indai wahala tayi wahala mutum zai fara neman mafita, to mafitan ne ba'a wani iri za'a nema ba, tinda ta nemi yafiyar mutane ta gyara halayenta sai a dawo da ita..." Mai martaba tayi gyaran murya sannan ya ce "hakane duk naji batun ki Insha Allahu zan je na samu Chief da maganar, sai dai matsala shine ba lallai ya aminta ba, kar yazo yana faɗa mun maganganu ne kinga shine gaba da Ni, kuma waɗanda suka girme shi ma bai fi maganar su ba, baffanun mu sun same shi da maganar amma fur yaƙi to ba lallai ne Ni ɗin ma yaji ba..." Aunty Yolash ta ce "a'a Yaya mai martaba kar ka karaya kaje ka lallame shi akan batun dan ALLAH..." Ya ce "toh shikenam idan kin tashi tafiya sai mu tafi tare Nima inaso na dawo a yau saboda inada uzurirruka a gabana sosai..." Aunty Yolash ta ce "ai Ni yanzu zan tafi..." Ya ce "to mu tafi tare..." duk suka miƙe akan zasu tafi, Maamie tana zaune ta ce "shikenam yarinya ƙanwar bayanka tazo zata kwashe ka ku tafi ba irin ɗan bada girman nan...". Mai martaba ya ce wa Aunty Yolash "ki sharar da ita kawai mu tafi..." Aunty Yolash bata kulata ba domin tasan inta biye mata zasu kaure da faɗa ne yanzu kuma bata da lokacin ta, haka suka fice Indo ta raka su har wurin parking, suka shiga mota security ya jasu suka tafi airport..... Bayan sun koma Nigeria, Mai martaba ne ya shiga gidan Chief ɗaya daga cikin sojoji wani ya kaishi har ciki da mota, ita kuma Aunty Yolash tana daga waje a cikin mota taƙi shiga gidan domin ba ƙaramin ɓata mata rai Abbah yayi ba, Mai martaba ne yake zaune a falon Abbah shima Abbah ɗin yana nan anyi dace yau bai fita ba, bayan sun gaisa ne Mai martaba ya ce "a gaggauce nazo domin a yau nake son komawa Jidder..." Abbah cikin nuna farin ciki ya ce "Tinda kuwa hakane nasan kaima akwai abinda ya kawo ka..." Mai martaba ya ce "sosai ma kuwa shiyasa ka ganni nayi zuwan bazata ai..." Murmushi Abbah yayi sannan ya ce "Yolash taje ƙasar da kake ko? nasan ƙarata takai kaima kazo kayi mun maganar wancan matar da yanzu ji nake kamar na hallakata ko ....? Mai martaba ya ce "duk abinda haƙuri bai baka ba rashin sa ba yanda za'ayi ya baka, duk abinda yayi tsanani a rayuwa haƙuri shine maganinsa, kuma ita gaskiya ba'a faɗa da ita, bai kamata ace duk wanda zai gaya maka gaskiya kayi faɗa da shi ba, kuma duk wanda zai yi maka nasiha akan abinda zai fissheka to kayi haƙurin zama dashi koda baka jin daɗin zama da shi ɗin, Ni nazo ne akan na baka shawarwarin da zai taimake ka a rayuwa a mazannina na ɗan uwanka bawai don na kai bane, ita wannan matar da kake gani tayi abubuwa da dama a rayuwa na rashin tunani amma yanzu da rayuwa ta sauyata mai ya kamata ayi mata? sai a yafe mata sannan a cigaba da zama da ita tinda ta gyara kurkuren da ta aikata..." Bai ƙarasa iddasa maganarsa ba Abbah ya dakatar da shi da cewa "shin na tambaye ka mana...?" Mai martaba ya ce "inajinka Chief.." Abbah ya ce "shin ba'a mutuwar Aure ne?..." Mai martaba ya ce "Anayi mana amma a dole badan ana so ba..." Abbah ya ce "to kuwa tinda na rabu da ita har abada bazan ƙara kallon yanda take ba balle tayi tunanin zan maido ta, kuma wallahi zanje na sameta ta fita shirgi na, ta daina bibiya mun ƴan uwa idan ba haka ba zan yi mata abinda batayi tunani ba, kuma da kuke cewa saboda ƴaƴanta na dawo da ita shin a tsirara kuka ga ƴaƴanta? ko kuma barinsu nayi da yunwa? to ko su yaran su ɗauka cewa uwarsu ta mutu domin baza su ƙara kusantar yanda take ba kada ta shafa musu baƙin hali da dabbanci, na rantse da sarkin dake busa mun numfashi duk wanda ya ƙara mun maganar na dawo da Kilishi wallahi sai nayi shara'a da shi domin bana son harkar shishshigi, kuma ko kaine idan na sake jin kayi mun maganar na dawo da ita wallahi zan yanke alaƙata da kai har abada..." Mai martaba cike da mamaki yake kallon Abbah ya ce "Subhanallahi abun bai kai ga haka ba, Allah ya huci zuciyarka Ni zan koma yanda na fito, na barka lafiya..." Mai martaba fita yayi yana fita ya tarar da Ummy a tsugune sai faman kuka take, tsugunawa yayi tare da ɗago kanta yana faɗin "Uwar masu gida ki kwantar da hankalin ki insha Allahu mamanki zata dawo..." Ta bayansu Abba ne ya fito yana faɗin "sai dai su haɗu a lahira domin ita da mahaifiyarta sai a mafarki, duk photunan Kilishi nasa an fitar mun da su a cikin gidan nan, a duniyar nan babu macen da ta sa hannu ta mareni sai ita na tsane ta..." Ummy cikin ɓacin rai ta taso tana kuka ta ce "wallahi Abbah banda sai a lahira kam, mahaifiyar mu tana raye amma ka haramta mana ganinta? duk ƙiyayya ai bazai sa ka raba mu da ita ba, idan kai baka sonta ai mu muna sonta tinda har ta shayar damu ruwan nonon jikinta..." Abbah a fusace yayo kanta zai dake ta Mai martaba yayi saurin riƙo shi yana faɗin "a'a banda dukan uwar masu gida domin daga baya zakayi nadama..." Ummy da gudu ta koma cikin babban falon gidan tana kuka, Ammy tayi rarrashin duniyan nan amma taƙi daina wa.. Abbah a fusace ya shugo yana balbala masifa ya kalli yanda Ummy take ya ce "ina kema kin koyi rashin kunya irin na yayunki dana uwarki ko? to kar ma ki fara domin karya ki zanyi a cikin gidan nan, ke har nawa kike? Uwar ki ce bazaki ƙara sakata a idonki ba na gaya miki..." Bayan ya gama surutansa ya haura part ɗinsa, Ammy ce ta cigaba da rarrashinta... Mai martaba bayan ya fita motar Aunty Yolash ya shiga rai a ɓace, Aunty Yolash murmushi tayi domin tasan matsalar shiyasa bata shiga ciki ba domin zata iya yiwa Abbah rashin kunya.. Airport suka nufa anan ta sauƙe Mai martaba kafin ya shiga jirgi ya kalli Aunty Yolash ya ce "zaku daɗe baku ganni anan Nigeria ba..." yana kaiwa ya shige jirgi, ita kuma Aunty Yolash wuce wa tayi kai tsaye Suleja taje daga nan ta wuce Bauchi... ★★★★★★ Bayan Aunty Yolash ta samu Hajiya Kilishi a garin Suleja zama sukayi suka tattauna akan maganar Abbah, Aunty Yolash kamar zatayi kuka ta ce "Hajiya Kilishi shawaran da zan baki shine ki cire Abban yara a ranki domin bazai taɓa mai dake gidansa ba, ki duba kika irin wulaƙanci da yayi mana Ni da mai martaba abun ba daɗi, kuma ya rantse cewa bazai taɓa kusantar yanda kike ba to kuwa kinga babu amfanin kiyi ta bibiyansa yana wulaƙanta ki, shi kaɗai ne namiji? ko shi ɗin ɗan gwal ne, to bari kiji inda nice wallahi ko ɗan gwal ne bazan kalli yanda yake ba balle ya samu damar wulaƙanta Ni, Ni mamaki ma kike bani har kina bibiyansa kina roƙonsa cab aini namiji baka isa ka samu wannan damar ba, bazan taɓa roƙon namiji abu shi kuma ya tsaya yana mun Rashin kunya ba..... asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *41_ TO_45* Aunty Yolash ta cigaba da cewa "duk da nasan ke kike da laifi Amma ai yanzu kin shiryu kuma kinyi alƙawarin bazaki ƙara maimaita kuskuren ba, ya kamata Chief ya dubi halin da kike ciki yayi haƙuri amma tinda bashida yafiya sai ki sharar da shi, dan Allah Kilishi ki zamo mai kamun kai, ki daina bibiyansa haka, ni duk abinda kike so ki ƙira wayata zaki same ni zan dauke miki duk ɗawainiyar ki kar ki damu, ki cigaba da addu'a komai mai wucewa ne, ki kwantar da hankalinki, ni yanzu zan koma bauchi domin ayyukana na bari nazo gurin da aka wulakanta ni, na tafi saina ji ki..." Daga nan Aunty Yolash ta koma Bauchi, ita kuwa Hajiya Kilishi a ranar ko rintsawa bata yi tsabar kuka, ba ƙaramin shiga damuwa tayi ba, ga yanzu ba halin ganin ƴaƴanta balle taji sanyi a ranta, idan taje yanda suke kuma Sojoji hanata shiga ciki suke sakamakon bin umarnin Abbah, ya sanar musu cewa idan suka ƙara barin Kilishi ta shiga masa gida duk saiya hora su... Ummy uwar masu gida itama ba ƙaramin shiga damuwa tayi ba na rashin ganin mahaifiyar ta tsawon shekara guda, ta samu Abbah akan tana son zuwa yanda take amma yaƙi barin ta, hakan yasa yanzu ko zuwa wurin da Abbah yake bata yi kullum a cikin kuke take, ga yanzu kwana biyun nan ta ƙi saka komai a cikin ta haka take zaune ba ci ba sha, ganin halin da Ummy take ciki ne yasa itama ƴar tinny ciki damuwa, yanzu a ɗakin Ummy take bata zuwa wurin Ammy ma balle shi kan shi Abbah, duk sun ƙaurace masa, Ammy ta yi magana wa Abbah yabar yaran su je suga mahaifiyar su amma Abbah ya dakatar da ita akan cewa babu ruwanta kada ta ƙara shiga cikin maganar, Roshan ganin halin da Ummy da ƴar tinny suke shima ya samu Abbah, yana faɗin "Abbah ka bari na kaisu idan sun gana da juna saina dawo da su..." Nan ma Abbah ya ce "bai yarda ba sai dai su mutu..." Kowa har yayi ya gaji. Wata rana Ummy ta fito falo kana ganinta kasan bata da lafiya ga duk ta rame tsabar jikinta babu ƙwari haka ta yanki jiki ta faɗi sumammiya, Ammy dake shirya abinci akan dinning tana hangota ta tafo da gudu tana ƙiran sunanta, dai dai lokacin da Abbah ya shugo, ganin Uwar masu gida a cikin wannan halin yasa yayo kanta a ruɗe, haka yasa hannu ya ɗago ta yayi waje da ita sai asibiti... Ummy Saida ta sha ledar jini da ruwa domin ba ƙaramin wahala take sha ba, sai da suka kwana tukun ta farfaɗo tana kuka tare da faɗin "ni ku kaini wurin mommy, nasan tana cikin mawuyancin halin, bana so na mutu ban ganta ba dan Allah, mommy na an rabani da ita kenan? ba zan taɓa yafe wa duk wanda ya rabani da Mahaifiyata ba wallahi...." tana kaiwa ƙarshe ta fashe da matsanancin kuka... Abbah yana tsaye yana jin duk maganganun da take faɗi ga kuma Ammy a zaune a gefen gadon da take sai Baiwar ALLAH itama tazo duba ta. Suna cikin wannan halin sai ga Doctor ya shugo Abbah ne ya ce "shin za'a iya sallame mu yanzu?..." Doctor ya ce "eh duk abubuwan da ya kamata ayi mata munyi yanzu komai normal..." Abbah ya ce "good, kinga uwar masu gida tashi muje ki shirya na kai ku wurin uwatta kun tinda kun fi sonta akan Ni..." ya kalli Ammy ya ce "ina Auta ta?..." Ammy ta ce "ta fita da Roshan ina tunanin gida suka nufa..." Ya ce "Okay zan kai su amma bazan bar yarana a hannunta ba domin da mutuncin su..." Ammy ta ce "kenam kana nufin kace ita uwar tasun batada mutuncin ne?..." Abbah ya ce "ko kaɗan babu..." Ammy shuru tayi tana gudun kar ta fusata shi domin yanzun ma a dole zai kai su ba dan yana so ba... Haka Abbah ya riƙo hannun Ummy ya ɗago da ita duk suka tashi suka fice, Bayan sun koma gida duk shirya wa sukayi har ƴar tinny Ammy ta shiryata, sai a lokacin hankalin Ummy ya dawo jikinta domin a halin yanzu tana muradin sanya mahaifiyar ta a idonta, kuma taji labarin tana shan wahalar rayuwa kowa ya guje ta.. Abbah shi da kansa zai kai su har garin Suleja... ★★★★★★★ Baiwar ALLAH ce a ɗakin Roshan tana gyara masa gadon kwanciyar sa, yanzu kwana biyun nan ita take masa komai, kullum sai ta je part ɗinsa ta gyara tare da wanke masa bathroom ta feffeshe ko ina da turare, sannan tayi girki ta shirya su akan dinning su ci tare, a baya kuwa sai dai ta ɗauki nata ta shiga room ɗinta ta ci acan shi kuma ya zauna a dinning ya ci shi kaɗai, yanzu kuwa zama take su ci tare, Abun ba ƙaramin mamaki yake bashi ba, a ransa yake faɗin "shin mai take nufi ne?..." A yanzun ma ta gama gyara masa gado ta juya zata fita kwatsam ta gànshi yana tsaye a bakin ƙofa ya goya hannayensa saman ƙirjinsa yana mata wani irin kallo na rashin fahimta, Itama tsaya kallonsa take daga bisani ya ƙarasa shugo wa ya zauna a bakin gado sannan ya kalle ta ya ce "ki zauna mana..." Itama taje ta zauna a wurin da ya nuna mata a kusa da shi, zama tayi jiki a sanyaye.. Roshan idonsa na kallon gabansa ya ce "naga kwana biyun nan kin canza shin meye a cikin zuciyar ki? tsawon shekara muna zaune ko da wasa baki taɓa zuwa part ɗina ba amma yanzu a kwana biyun nan meyasa? kinsan dole zan yi tunanin wani abu a raina, domin duk wanda ya ce baya sonka da safe babu wanda za'ayi da daddare ya komo yace yana sonka wannan ƙarya ne, saboda haka tin a baya kin nuna bakya sona ɗan uwana kike so kuma nasan har yanzu hakane a cikin zuciyar ki, kiyi haƙuri nasan na cutar da ke dana riƙe ki har zuwa tsawon wannan lokacin kinyi haƙurin zama dani a gida ɗaya, inda ace tin farko baki nuna cewa zaki zauna dani ba da yanzu kinada yaron ki jinin ɗan uwana Razhdeen domin a lokacin ya nuna ya amince kika kwabsa, gashi muna zaune zaman ba daɗi Ni ba ɗa kema haka ko kusantar junan mu bamu taɓa yi ba wai hakan muna zaman Aure, Insha Allahu sauran ɗan watanni kaɗan Razhdeen ya dawo da zaran ya dawo zan damƙa masa ke domin yanzu haka takardar sakin ki na nan a ajiye lokaci kawai nake jira...." ya ƙarasa maganar yana sharar hawayen da ya zubo masa, Itama Baiwar ALLAH kukan take jin maganganun da yake faɗa mata kuma alhalin yanzu ba haka bane a cikin zuciyarta, Cigaba da cewa yayi "zan roƙe ki wata alfarma shin zaki iya mun?..." Yayi maganar yana kallonta, itama kallonsa take tare da ɗaga masa kai, Jinjina kai yayi sannan ya ce "inaso ki daina shugo mun room, ki tsaya a yanda kike a baya, girki ne idan kika yi zan ci idan kina so zamu zauna a dinning muci kamar yanda muke yanzu, amma fake wa wuri ɗaya ne banaso domin nasan kaina banida juriya, kina cuta na sosai idan naga mun fake Ni kuma bazan iya aikata komai dake ba saboda nasan wata rana ke matar twins ɗina ne, bana so ya karɓi saura na, nafi so ya ɓare ki sabuwa a leda zan fi jin daɗin haka sosai, inaso idan na kusanci mace to ya zamana har ƙarshen rayuwata ita zan rinƙa kusan ta, saboda haka kiyi nesa da abinda zai sa mu fake wuri ɗaya, zan cigaba da shan lemon tsami na har Allah yasa mu rabu, Da fatan dai ban ɓata miki rai ba ko?..." Baiwar ALLAH ganin bazata iya juran kalaman Roshan ba yasa ta tashi tare da fashewa da matsanancin kuka ta bar ɗakin da gudu, kai tsaye part ɗinta ta nufa. Shima Roshan bai san lokacin da hawaye ya fara masa go slow ba domin ba ƙaramin ƙaunar Baiwar ALLAH yake ba, ya kasa cire ta a ransa kodan yana ganinta koda yaushe ne... ★★★★★★ Bayan isar su Abbah garin Suleja gidan da aka masa kwatance nan yayi parking a ƙofar gidan, gidan ne kana gani kasan gidan haya ne amma kowa da part ɗinsa, Har Ummy ta sauƙa daga cikin motar tayi gaba zata kutsa ciki Abbah yayi saurin riƙo ta yana faɗin "baki da hankali ne? daga ganin gida zaki shiga idan ba nan ne gidan kuma fa?..." Ummy tsayawa tayi domin a halin yanzu bata da wani buri da ya wuce taga mahaifiyarta.. Wani magidanci ne ya fito daga gidan da duk kan alamu shima a gidan yake da iyalansa, Abbah ne yayi masa magana yana faɗin "Dan ALLAH bawan Allah nan ne gidan da Kilishi take?..." Mutumin ya ce "eh dake part-part ne gidan ban san a wani ƙofa take ba, kuma akwai mata da yawa a gidan duk bansan sunayen su ba..." Abbah ya ce "okay matan duk bazaware ne ko matan Aure?..." Mutumin ya ce "duk matan Aure ne bazawara ɗaya ce ɓangarenta daban ita kaɗai..." Abbah ya ce "okay to wurin bazawarar muka zo..." Mutumin ya ce "nasan ƙofar da take muje na kai ku..." Abbah ya ce "a'ah kayi mana sallama da ita muna waje daga nan zamu wuce ne..." Mutumin ya ce "okay..." Sannan ya shige ciki, can ya fito ya sanar da cewa "tana fito wa..." Bayan wasu ƴan mintuna sai ga Hajiya Kilishi ta fito tana sanye da hijab ɗinta sai faman leƙe leƙe take tana son ganin wanda yazo mata sam bata lura da su Abbah ba, Sai ji tayi an rungume ta sosai, zaro ido tayi tana kallon Ummy wacce ganin ta yasa ta tafo da gudu ta rungume ta, A ruɗe Hajiya Kilishi ta furta "Ummy..." cike da mamaki take binta da kallo, Ummy tana kuka ta ce "Mommy yau gamu mun zo gare ki..." tayi maganar cikin nuna farin ciki, sai ga Ƴar tinny itama ta rungume ta, cikin farin ciki Hajiya Kilishi tasa hannu ta ɗaga ƴar tinny tana hawaye tare da faɗin "Nagode muku sosai yara na, kamar daman kun san ina cikin damuwa na rashin ganin ku a kusa da ni..." Ummy fashewa tayi da kuka tana faɗin "Mommy ki ga duk kin rame kin zamo ƴar ƙarama, Mommy baki da ƙashin wuya amma ki ga yanzu yayi miki sauƙa, meyasa zaki zauna cikin wahala Mommy..." Hajiya Kilishi tana kuka ta ce "to ya zan yi Ummy dole na zauna cikin wahala kinga fa kowa ya guje ni, Ni kaɗai nake zaune ba mai taimaka mun, sai yanzu da Auntyn ku Yolash take turo mun kuɗi, ita take biya mun gidan hayan da nake ciki yanzu..." Abbah yana jingine a jikin motarsa ganin koke-koken ya ƙi ƙarewa yasa shi cewa "kinga Madam kar ki raunana mun zuciyar ƴaƴa Please, muna son komawa..." Hajiya Kilishi sai yanzu ta lura da Abbah, kallon yanda yake tayi tare da faɗin "kayi haƙuri ku shugo ciki mana ku ci abinci..." Abbah ya ce "look ba wai zuwa muka yi mu zauna ba, just na kawosu su ganki, yanzu kuwa tinda kunga juna su zo mu tafi kawai..." Ummy ta ce "Abbah inason cin girkin Mommy..." Abbah cikin takaici ya ce "daman tinda kike kin taɓa cin girkin ta ne? tin da kika zo duniya kin taɓa ganinta a kitchen?..." Ummy ta ce "yanzu ina son cin abincin da ta girka da kanta..." Abbah ganin Ummy zata bijire masa yasa shi cewa "ok kuje ina jiran ku yanzu..." Hajiya Kilishi ta ce "kai ma ka shugo mana..." Abbah ya ce "kinga ba wurin ki nazo ba, na dai kawo yarana ne, amma mu shiga daman inason miki last warning akan bibiyan yanda ƴan uwana suke..." Hajiya Kilishi ta ce "tam..." tana ɗauke da ƴar tinny ta riƙe hannu Ummy suka shiga, Abbah shima bin bayan su yayi... Bayan isar su ciki Hajiya Kilishi ce ta jido girkin da tayi a flask tuwon shinkafa ne da miyan Alaiyahu yasha gyaɗa har da nama a ciki kamar wacce tasan da zuwan su, kuma dake yanzu Aunty Yolash tana turo mata kuɗi sosai, Ummy tana kallon Kilishi ta ce "Mommy ke fa zaki yi feeding ɗin mu..." Hajiya Kilishi ta ce "to rabin Rainah..." Ta wanke hannunta sannan ta soma basu abinci a baki duk su biyun da haka ta kammala basu suka ci suka ƙoshi, ta basu ruwa suka sha... Ummy ta ce "Mommy daman haka kika iya girki shine bakya mana..." Hajiya Kilishi murmushi tayi ta ce "kuyi haƙuri nayi kuskure a gafarce Ni yara na...". Ummy itama murmushi tayi ta rungumi mommynta tana faɗin "kar ki damu Mommy muna tare da ke..." Hajiya Kilishi ta ce "kuna jin labarin su twins ɗina kuwa?..." Ummy ta ce "su Aunty Pinky ai sun kusan dawowa, kwanan nan zasu yi graduation 🎓 na gama deegre..." Hajiya Kilishi ta ce "ma sha ALLAH, ina su Roshan da matar sa?..." Ummy ta ce "duk suna nan, Uncle Deen kam ya koma U.S..." Hajiya Kilishi kamar zatayi kuka ta ce "bakwa jin labarin Minal ko?..." Jan numfashi Ummy tayi sannan ta ce "tana can tare da mijinta nasan tana cikin ƙoshin lafiya tinda Marshall yana matuƙar ƙaunar ta..." Hajiya Kilishi ce ta kalli Abbah ganin yanda yake ta haɗa rai yana fushi, Abbah kuwa idonsa a gefe guda yana tunani a ransa cewa "anya kuwa wannan Kilishi ce? gaskiya rayuwa tana bugan ta kuma ina so ta ƙara bugarta da kyau, kuma naga ta sauya sosai kamar ba Kilishi ba..." Daga baya ganin tunanin ba shida wani amfani yasa shi yin gyaran murya yana kallon Kilishi ya ce "kalli Nam..." Hajiya Kilishi kallonsa take tana son jin wani irin warning za'ayi mata, Abbah ya ce "last warning da zan miki shine kar ki sake bibiya mun ƴan uwa da abokaina akan maganar komar dake gidana domin bazan taɓa mayar ki ba, kin fita kin fita kenam ba komawa, domin bazan kije ki sawa matata damuwa ba, nafi son na rinƙa ganinta ita kaɗai a gidana tana walwala, don haka ki dakatar da wannan shirmen nakin, idan ba haka ba wallahi tallahi kotu ce zata rabamu, a saboda ke na ɓata da abokaina da yawa da ƴan uwana, wacce nake ji da ita a raina ƙanwata Yolash kinsa na samu matsala da ita, a saboda ke Ɗan uwana ya taso daga wani country yazo wuri na amma rabuwar ba daɗi muka yi duk saboda ke, meyasa kike son shiga mun rayuwata kam? shin ana zaman Aure dole ne? nace banaso ana dole kam? Ni fa ba ƙaramin yaro bane da za'a zo ana damu na da maganar ki, to na rantse idan kika ƙara turo mun wani sai na ɗauki mataki na gaya miki...." Ya ƙarasa maganar yana zazzaro mata ido, Hajiya Kilishi tana hawaye ta ce "Chief...." Kafin ta cigaba ya katse ta da cewa "Chief ya mutu wani ne a madadin sa wato Ni ..." Hajiya Kilishi ta ce "to ai kai ɗin nake nufi Abban yara, tin daga lokacin dana tura Aunty Yolash shin na tura wani ne ko wata? daga ita ban ƙara tura kowa ba na kai kuka na zuwa ga mahalicci, ko shi Mai martaba Aunty Yolash ce ta tura shi ba Ni ba, idan kayi shara'a dani ai dole cewa za'ayi da uwar ƴaƴanka kayi shara'a, wannan sunan bazai gogu ba na cewa Ni uwar ƴaƴanka ce, kafin ka fara sharia da ni ka fara goge wannan sunan tukun, ka nema wa ƴaƴanka wata uwar a daina cewa ni uwar ƴaƴanka ce..." Abbah ya ce "tin tinin na goge wannan sunan domin na nema wa ƴaƴana uwa ta gari wacce ta fi uwar su, tana can ƴar aljanna kenam, tana bawa ƴaƴana kulawar da basu samu a wurin Uwar tasun ba..." ya ƙarasa maganar yana hararar ta, sannan ya maida idonsa kan Ummy yana faɗin "ku tashi mu tafi..." Ummy ƙara narkewa tayi a jikin Hajiya Kilishi ko ɗagowa ta kalli Abbah bata yi ba..." Abbah ya ce "ina miki magana kina jina..." Ummy ta ce "Abbah nafi son zama a wurin uwata ba'a wurin Uwar wani ba, duk uwar da za'a kawo mun baza tafi uwata ba kuma itama uwar tawan ƴar Aljanna ce da yardar Ubangiji..." Abbah ya ce "Uwar masu gida Ni kike gaya wa haka?..." Ummy ta ce "Uwar masu gida ta mutu wata ce a madadin ta wato Ni..." Abbah ya ce "ki tashi muje na ce..." Ummy ta ce "Abbah wallahi bazan tafi nabar Mahaifiyata ba, idan kana so na tafi sai dai mu tafi gaba ɗaya da ita, amma in har babu ita to Nima babu ni..." Abbah ya ce "to shikenam ki cigaba da zama a wurin natan, ke Auta taso ki bi Abbanki ma za..." Ƴar tinny babbar yatsar ta tasa a baki idonta akan Abbah itama ta kwanta akan Hajiya Kilishi tana faɗin "Oh -ohhh..." Abbah ya ce "ta so ma za zan siya miki yogurt..." Ƴar tinny ta ce "Oh -ohhh...." Abbah ya ce "Dan ubanki yau ɗin baza ki mun magana ba ne? Yau bakyaso ki kwana da Ammyn ki Koh?..." Ƴar tinny ta ce "eh ɗin yau da Mommy na zan kwana, Oh -ohhh..." Abbah ya ce "shikenam kun kyauta, yana kaiwa nan yayi ficewar sa, a fusace ya shige motar sa sai Abuja...." Ummy farin ciki kamar bazata mutu ba, daman shirin ta kenam inta samu tazo wurin mommynta ba koma wa kuma gashi shirin ta yayi kyau, Abbah yayi zuciya ya tafi, daman haka take so..." Itama Hajiya Kilishi tayi farin ciki sosai ganin yaranta a kusa da ita, yau da su zata kwana... ★★★★★★★★★ Ta ƙura volume waƙa a plasman tana kokkoyan rawar da suke, kuma rawar yana mata kyau sosai yanzu ta ƙwarai sosai domin ba rawar da bata iya ba, hatta kaɗa jita ta ƙaro training sosai ba ƙaramin kwarai wa tayi ba, ta ɓangaren karatu kuwa nan ma ba laifi sai dai tayi rubutu, ta iya na Hausa sannan ta iya na Turanci sosai, ta ɓangaren islamiyya kuma dake makarantar a haɗe take gaba ɗaya, bata iya bada hadda amma tana tattare su a cikin kwakwalwar ta. Tana cikin rawar sai ga Madam Blessing ta fito daga kitchen daman tasan sana'ar ta kenam hakan yasa ko sauraronta bata yi ba, Ƴar Amana ce taje da gudu ta kamo hannun ta tare da jawo ta gaban plasman tana mata nuni da suyi rawa, ba yanda Madam Blessing ta iya haka ta biye mata sukai ta tiƙar rawa sai da madam Blessing ta gaji ita kuwa Ƴar Amana kamar wacce ake ƙara mata petur, sai da waƙar taje ƙarshe tukun ta haƙura.. Bayan ta ci abincin da aka girka mata na gyaran jiki tashi tayi taje tasa wasu ƙananun kaya riga da wando irin na kwallo amma sai dai wandon gajere ne a iya cinya ya tsaya mata sai rigar wandon marar hannu gata jiki a dire abun ba'a cewa komai, gashin kanta ta tuttuƙe shi tayi donut da shi sannan ta sanya takalmi cover shoe mai igiya irin na ƴan wasan ƙwallo, tana kammala shirin ta kawai ta ɗauki ball ɗinta ta fice, tana wasan basket ball ne idan rana ta kama ranar Saturday da sunday wasu lokuta kuma takan yi wasan kabadi ita da madam Blessing, a filin wasa dake part guda a killace, wani lokaci kuma tasa kayan swimming pool ƴan ƙananu taje tana rayuwar kifaye a cikin ruwan, ko wani sati da kalan wasannin da take yi, sometimes kuma ta fita yawon shakatawa ita da Madam Blessing, suje super market su yo siyayya daga nan su je wurin wasan yara har gidan zoo sai sun gama zagaya wa sannan suke komawa gida. Madam Blessing ba ƙaramin kuɗi take cabka a wurin Uncle Deen ba hakan yasa take bawa Ƴar Amana kulawa ta musamman... Bayan sati ɗaya Madam Blessing ce ta haura saman ɗakin Ƴar Amana zata je ta tayata shirin tafiya makaranta domin ta kammala haɗa kayan breakfast.. Shigar ɗakin ke da wuya ta tarar da Ƴar Amana kwance ƙasin carpet ɗin ɗakin tana kame da cikinta ta tukwikwiye guri ɗaya, da gudu Madam Blessing ta ƙarasa gurin ta tana ƙiran sunanta, ai kuwa tana ɗago ta taga bata motsi ga ido a lumshe, ƙirjin Madam Blessing ne yayi wani irin bugawa da ƙarfin gaske sai ambaton "Jesus, Jesus take domin bata san me zata ga ya wa Razhdeen ba, kuma tsoron ta kar taje ta mutu, haka ta ɗagota daƙer tayi waje da ita, daƙer ta iya sauƙar da Ƴar Amana ƙasin down stairs domin yanzu tayi cikar da mace bazata iya ɗaukarta ba, madam Blessing niyar ta ta nufi hospital da ita, tana shirin barin falo sai ga Roshan ya shugo falon da sallama a bakinsa, ganin madam Blessing tana riƙe da Ƴar Amana yasa shi yowa kansu da hanzarinsa yake faɗin "me ya faru da Sarah?..." Cikin ƙiƙƙinar magana tsabar a ruɗe take ta ce "ban sani ba Nima, haka na same ta a sume..." Roshan duba ta yayi sosai ya ga jini ya ɓata farin wandon ta, girgiza kai ya yi sannan ya ce "ba sai an kaita asibiti ba ta fara period ne..." Yasa hannu ya karɓe ta tare da yi mata ɗaukar luɗa ya nufi ɗakinta, yana haurawa ya kwantar da ita akan gado sannan ya sanar wa Madam Blessing cewa "ki canza mata kaya sannan ki shirya ta, fatan dai kuna da pad?..." Madam Blessing ta ɗaga kai tare da faɗin "eh akwai pad..." Ya ce "to kisa mata, zan je na kawo alluran da za'ayi mata ta dawo setting, sannan tana buƙatar ledar ruwa domin naga ba ƙaramin jikkata tayi ba..." Yana ƙarasa maganar sai ga ƙira ya shugo masa waya, dubawa yayi yaga Razhdeen ne ya ɗauka yana sakin murmushi, kafin buɗe baki Razhdeen ya katsar da shi da cewa "ka je ka dubo mun Sarah meya faru da ita..." Roshan sake baki yayi yana jinsa yana mamakin taya yasan bata da lafiya, Roshan ne ya ce "kai da kake can taya kasan wani abu ya faru da ita?..." Razhdeen ya ce "haka kawai zuciyata take bugawa da kowani harafi na sunanta, gaba ɗaya na kasa kwantar da hakalina..." Roshan cike da mamaki ya ce "to pah, kwantar da hankalin ka yanzu haka ina gidan, ciwon mara take fama da shi na period, yanzu haka zan fita naje na kawo wasu magungunan da zata na sha da allurar da za'ayi mata..." Razhdeen ya ce "i known, daman nasan akwai abinda ya faru da ita, ba haka kawai zuciyata take bugawa ba kuma sannan na ƙira wayan Blessing yafi sau nawa she didn't answered dole zan damu, please you should better take care about her because she's my partner of mind, please bana so ta raunana sosai..." Roshan jinjina kai yayi sannan ya ce "okay don't worry the father of lover not soldier in dis time..." Razhdeen ne ya katse shi da cewa "who told you? kar kayi tunanin kawo mun maganar soyayya domin she is a younger girl how comes zan yi soyayya da ita, but ba ƙaramin raina mun wayo kayi ba twins..." Roshan yana dariya ya ce "Ni ne ma ka ke raina mun wayo ai my Man, ka mayar ni yaro ƙarami..." Razhdeen ya ce "Please ka dakatar da wannan shirmen nakan kayi mata video ka tura mun inason ganin a wani hali take..." Roshan kamar yanda Razhdeen ya ce hakan ya yi daga baya ya tura masa, a yayin da Roshan ya fice zai je nemo maganunnuwa, ta wani bangaren kuma zuciyar sa na kuka ganin yanda Razhdeen yake nuna matuƙar kulawa akan Ƴar Amana amma sam baya maganar Baiwar ALLAH, ita kuma shine a zuciyar ta, ganin son maso wani take kuma bata son zama a gidan mijin da Allah ya zaɓa mata yasa yake jin takaici.... Da wannan takaicin ya fice. Ata ɓangaren Razhdeen kuma ganin video yasa shi miƙewa tsaye daga zaune, ganin irin girman da Ƴar Amana tayi ta zama cikakkiyar mace, yarinyar da yake raina shekarun ta gashi har tafi wata mai shekara 25 cikar jiki, da breast da hips haɗe da ƙugu duk a cike, wani irin haɗiyar yawu yayi yana ƙareta da kallo kamar wanda yake gaban ta, girman yarinyar yarinyar ba ƙaramin mamaki ta bashi ba, yana cikin wannan tunanin yaji an masa magana ta baya, switch ɗin wayar yayi tare da juya wa ganin Madam Parveen ce ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da try ɗin kayan Abinci tana ƙoƙarin jera su akan dinning, cikin yaren turanci take faɗin "M.G Razhdeen meya faru ne naga ka miƙe tsaye..." Ba tare da ya furta komai ba ya koma ya zauna yana hasasho ƴar Amana, Madam Parveen ce ta ƙaraso cikin falon ta zauna a ɗayan kujera tana facing ɗin Razhdeen kamar zata yi kuka take faɗin "yanzu kaima zaka ce baka san yanda Mohandas ya shiga ba?..." Razhdeen ya ce "tinda har ya aiko muku letter cewar yayi Aure sannan babu wanda zai san a yanda suke ai shikenam sai kuyi haƙuri ku jira bayyanowar su, duk da nasan ba son ƙanwata Minal kuke ba kuma most especially ya musulunta ba tare da sanin ku ba, duk wannan abubuwan da ya aikata ban san da su ba, ban san ya musulunta ba sannan ban san yayi Auren sirri da Minal ba sai labarin tafiyar su naji..." Madam Parveen hawaye ne yake gangaro mata ta ce "shikenam yanzu a cikin yara uku bana tare da guda biyu? iya ɗaya nake da shi yanzu, Rakesh nake gani naji daɗi, Amreesh na rasa ta tin tana yarinya, yanzu kuma Mohandas shima ya guje ni, Ni in har zai dawo gare Ni na amince ya zauna da matar sa sannan ya zauna cikin musuluncin da ya zaɓa...." Ta bayanta taji an katse ta da cewa "impossible, Mohandas tinda ya musulunta to yabar family na, sannan tinda har yayi Auren sirri hakan ma da ƴar maƙiyi na to ya aikata babban laifi saboda haka na sallame shi, don haka ko da shi ko ba shi we are completed family..." Duk wannan maganganun Daddyn su ne ya fito daga part ɗinsa yake faɗin haka wato "Chief Of Defence Staff" shugaban sojojin ƙasar U.S ya ƙarasa maganar tare da zama shima akan kujera. Madam Parveen kallonsa tayi tare da faɗin "we are not complete, Mohandas he's my first born bazan taɓa cire shi a raina ba ina kan son sa har gobe, sannan my last born na rasa ta since how comes zaka ce we are completed? why? tell me your reason..." Daddy ya gyara zamansa sannan ya ce "You want me to tell you my reason abi, okay the firstly my daughter Amreesh she has already passed, ta mutu kuma bamu isa mu dawo da ita ba sai dai mu tuna ta sannan muyi mata addu'a, shi kuma Mohandas ya bijire mana yayi tafiyar sa that means yanzu baya buƙatar mu tinda mun gama masa komai, munyi sanadiyar kawo shi duniya sannan mun masa gata yanzu kuma mun gama masa amfani, Na fitar da shi daga cikin ƴaƴan da na haifa..." Rakesh ne ya shugo shima jikinsa a sanyaye jin abinda Daddynsu yake faɗi, dawowar sa daga wurin aiki kenam gashi sanye da kakin soja a jikinsa, Gaishe su yayi zai zauna kenam Madam Parveen ta dakatar da shi da cewa "your welcome my Son but kaje ka rage kayan jikinka sai kazo mu je dinning..." Ko ƙara kula Daddy bata yi ba saboda yanzu zaiyi abinda zai sa suyi faɗa, kowa yana ji da aikin ɗamarar sa. Daddy ne ya kalli Razhdeen tare da sakin murmushi ya ce "M.G my best soldier naga aikin da kayi jiya ya burge ni sosai, kayi ƙoƙari..." Razhdeen ya ce "thank you Dad..." Razhdeen ne ya kuma yin magana yana faɗin "Dad Please i want to ask you something..." Daddy ya ce "okay go ahead..." Razhdeen ya fara magana da cewa "meyasa kake gava da mahaifina sannan baka son haɗa jinsi da shi amma kuma Ni ka ɗauke ni tamkar ɗan ka, ko kaɗan baka son ɓacin raina, a koda yaushe ja na kake a jikinka kuma nasan iya Ni kaɗai kake so acikin yaran mahaifina i don't know why...." Madam Parveen ce ta kalli Chief domin ta daɗe tana bashi haƙuri akan yaje su sasanta kansu ko dan saboda Razhdeen, Razhdeen bai taɓa masa wannan tambayar ba sai yau, Shi kuma Chief Of Defence ya ce "bazai taɓa zuwa yanda Chief Of Army's Nigeria yake ba sai dai idan shine ya fara zuwa yanda yake domin a cewar sa ai shine sama da shi... Daddy ya kalli Razhdeen sannan ya ce "idan a tsakanin kai da Rakesh ku ka samu matsala a wurin aikin soja shin acikin ku wa ya kamata wani ya gurfar da kai ya nemi yafiya?...." Razhdeen jin a wurin aiki suka samu matsala yasa shi cewa "Rakesh ne ya kamata ya fara neman maslaha domin Ni ne sama da shi, kuma bugu da ƙari a wurin aikin ne ba'a ordinary place ba..." Daddy ya ce "Good my best, to shi Abbah ku yayi laifi amma girman kai yasa ya kasa neman sulhu tin tsawon shekaru domin tin ina Nigeria da zama yanzu shekara 23 kenam, i swear to God in har ya zo ya nemi sulhu zan yafe masa tunda a ƙasa na yake..." Jinjina kai Razhdeen yayi sannan ya ce "but meya haɗa ku?..." Daddy ya ce "tin a Nigeria nine Ogansa, sun fita aiki yaje ya jefar da bindigarsa, ganin ina mutunci sosai da shi kuma a lokacin abokai muke sai dai igiyar mu ba ɗaya ba yasa na ce sai dai yayi abu biyu na ɓatan gun a wurinsa, zaɓi biyu ko yasa hannu a takardar Apologize letter ya bada haƙuri kenam albarkacin ina tare da shi, inda ace wani ne daban dole sai ya biya ko kuma a kulle shi, sannan nace ko ya biya kuɗin gun in yaso ya biya rabin kuɗin ni kuma saina taya shi biyan rabin shin banyi masa halacci ba ? to a lokacin sai ya ɗauki takardar bada haƙuri ya yage a gaba na sannan ya sanar mun cewa wai ina so na tozarta shi ne yasa na bashi takardar saka hannu, sannan ya ce ba zai biya kuɗin ba tinda wurin yaƙi yake kuma a lokacin anji masa rauni a ƙafa daƙer yake iya tafiya a lokacin, mahaifinku ya gama mun rashin kunya sannan ya fice a office ɗina yana ganin bazan iya koransa daga aikin soja ba amma kada ya manta nima fa inada Oganni, bayan kwana biyu ban san ya akayi ba ashe sauran shuwagabannin sunji labarin abinda ya faru na ɓatan gun mai bala'in tsada hakan yasa suka sa aka kamo mahaifin ku suka kulle shi na tsawon wata uku, hakan ma Ni nayi shige da fice nasa aka fito da shi daƙer domin tsawon zaman da zai yi a kulle tsawon shekara uku ne amma saboda jajircewar da nayi yasa na fito da shi a cikin wata uku, a lokacin ba ƙaramin kashe kuɗi nayi ba, dukiyata haka na ɗauka ina zubar da su duk a saboda mahaifinku ya fito daga uƙubar da yake, Ashe shi a tunaninsa nine nasa aka kulle shi, amma bai san Ni nayi ƙoƙari na fito da shi ba domin hanawa nayi a sanar da shi har yau bai sani ba, kuma wallahi Ni babu yanda za'ayi nasa a kulle shi duk girman laifin da ya mun domin tin muna primary muke tare, muka yi Junior tare har muka yi secondary, daga nan muka rabu na je nayi deegre da master ɗina a anan ƙasar U.S na soldier, kuma na riga mahaifinku shiga soja bayan wasu shekaru shima ya shiga, bayan ya fito daga maƙarƙama ya same ni anan ma ba ƙaramin matsala muka samu ba abunda yasa na biye masa kuma shine ya ƙirani da Arnen banza kuma ina mazannin Ogansa, daga lokacin na fusata munyi faɗa sosai daƙer aka raba mu, har an bashi takardar barin aiki saboda yayi faɗa da Ogansa nasa aka dawo da shi wurin aikinsa, kuma matakin da yake yanzu na chief Of Army's shine matakin da nake a lokacin, bari na nigeria bayan an ƙara mun matsayi aka dawo dani nan ƙasar Austrolia a wani za'a bada matsayi na a nigeria nasa aka bawa mahaifinku duk zaman gavan da muke, amma har yau bai sani ba, Sannan kai kuma a lokacin da za'a ɗauki sojoji anan ƙasar na bada sunanka aka aika maka can Nigeria nasan har yau mahaifinka bai san cewa ni ne na ɗauke ka ba, sannan na kai ka matsayin da a lokacin baka kai kaje ba, kuma sai akayi sa'a kana aikin da ya kamata, na kuma ɗauke ka tamƙar ɗan dana haifa, nake jan ka a jiki har muka shaƙu sosai ka kuma ɗauki nan gidan tamkar gidanku, Kuma dake daman tin kuna yara kai da twins ɗinka Roshan kuka shiga zuciyata, ina masifar son twins a rayuwata, ko zan yi gava da mahaifinku da kuma sauran to ku kai da Roshan bazan taɓa ɗaukar ku a haka ba, Daga lokacin nasan cewa Christal sun fi musulmi haƙuri da juriya da kuma tawakkali duk da nasan a cikin musulman ba duk haka bane, to kaji dalilin samu matsala ta da mahaifinku...." Jinjina kai Razhdeen yayi domin a halin yanzu bashi da bakin magana tinda kowa yasan Abbah ne bashi da gaskiya, kuma Chief Of Defence yayi musu ƙoƙari sosai ya yi halacci ba ɗan kaɗan ba.... Duk maganganun da Chief yayi ashe Razhdeen yana yin recording domin tin kafin nan ma yasan Abbah ne da laifi, yayi recording ne saboda akwai lokacin da zai kunna wa Abbah ya ji irin alkhairi da Abokin gavan sa yayi musu a lokacin da yake cikin gava da shi, domin Razhdeen ba lallai ya iya bayyanar da wannan bayani ba hakan yasa yayi recording... Madam Parveen ta ce "Allah ya dai-dai ta tsakanin ku tinda yanzu kun fara haɗa zuriya ɗaya..." Daddy ya ce "damuwa ta bawai Auran yarinyar da Mohandas yayi ba ne, babban damuwar shine guduwar da yayi kuma Ni har cikin zuciyata bana son musulunci..." Madam Parveen ta ce "Ohhhh ka manta ranar abunda kace?..." Daddy ya ce "what?..." Ta ce "ka ce inda ace Daughter ka Amreesh tana nan da ka Aurar da ita a Razhdeen, shin ba haka kace ba?..." Rakesh yana zaune ya ce "ey tabbas duk muna nan har shi kan shi M.G Razh..." Razhdeen dai girgiza kai yayi yana ƙwaƙulo murmushi domin tin lokacin da aka haifi Amreesh Chief yayi alƙawarin ta a Razhdeen, kuma shima Razhdeen yaso Amreesh tin tana yarinyar ta, saboda ita kullum yake zuwa gidan su tin suna Nigeria kafin Abbah da Daddy su samu matsala, Amreesh ba ƙaramin shiga cikin zuciyar Razhdeen tayi ba, tin daga lokacin yayi alƙawari a kansa cewa babu yarinyar da zai Aura in ba Amreesh ba, ya ɗau alƙawarin zai jira ta har ta girma, yana da ƙwarin gwiwa sosai akanta domin Daddynta shima ya sanar cewa yayi Alƙawari idan Amreesh ta girma zai sa ta musulunta sannan ya Aura mata Razhdeen ya kuma cewa da sharaɗi ɗaya, A lokacin kowa yana son jin wani irin sharaɗi ne wannan kuma har Abbah mahaifin Razhdeen shima ya amince indai har zata musulunta zai amince Razhdeen ya Aure ta. Daddy ya sanar cewa "yana son Amreesh tayi aikin soja itama..." Razhdeen ya amince da batun domin shima yana son macen soja... Har zuwa yanzu akwai photunan Amreesh da yawa a wurin Razhdeen tin tana yarinya ƴar shekara uku... Gyaran murya Daddy ya yi sannan ya ce "idan na ɗau alƙawari bana karyawa, ƙudiri na har yanzu yana nan, ko a yanzu Allah ya bayyano mun da Amreesh zan Aurar da ita a Razhdeen ne..." Daddy ya kalli Razhdeen sannan ya ce "M.G kar fa kace abinda ya hanaka yin Aure saboda Amreesh ne..." Jikin Razhdeen ne ya yi sanyi haka yake jin zuciyar sa tana bugawa, lokaci guda fuskar Amreesh ya fara masa gizo lokacin da take yarinya ga kalar dariyar ta irin na yara sai ƙyalƙyalewa take da dariya a yayinda yake lilata a lilon wasan yara, wani irin haɗiyar yawu yayi sauran kaɗan hawaye ya gangaro masa yayi saurin goge wa. Kowa a wurin ya lura da damuwar da Razhdeen ya shiga lokaci guda kuma an san duk akan Amreesh ce domin kowa yasan tsananin so da ƙaunarta da yake... Razhdeen ya kalli Daddy sannan ya ce "har yau har gobe ina tsananin ƙaunar Reesh, ina son Reesh nasa a raina itace matar da zan Aura kuma har kullum ita nake kalla a matsayin nan, hakan yasa babu wata mace a gaba na, babu macen da nasa a raina cewa zan Aura har yanzu, kullum mafarki na da tunani na shine Reesh zata dawo gare ni ne, har yau ban daina neman ta ba, ina aiki na amma kuma ina bincikar yanda take, har yanzu ban yadda cewa Reesh ta mutu ba, na rantse da sarkin dake busa mun numfashi wallahi tallahi Reesh tana nan a raye, har yanzu ɓangare guda na zuciyata wanda na sadaukar wa Reesh tana kan bugawa hakan na nufin Reesh tana nan a doron duniya, zuciyata gida biyu ta kasu ɓangare guda na Reesh ce ɗayan ɓangaren kuma...." Lokaci guda ya tuno da Ƴar Amana videon ta daya kalla ne ya faɗo masa a rai sai kuma yake hasasho fuskar ta, Girgiza kai yayi cikin sassanyar murya ya ce "gaba ɗaya zuciyata ba tawa bace...." Lokaci guda hawaye duk ya wanke masa fuska, a ruɗe ya miƙe tare da nufan hanyar fita, Madam Parveen a rikice ta ce "Razhdeen abinci kazo mu ci kar ka tafi da yunwa....." Lokaci guda itama ta kife ƙasin carpet tare da rausa uban ihu tana faɗin "ku nemo mun Amreesh ɗin ta, tana raye wallahi, Allah yasa tana rayeee, wayyo Amreesh ɗinta...." Daman tana maƙale da kukan ta ganin bazata iya riƙe wa ba yasa ta fara kuka na gaske, Rakesh ne yayo kanta ya ɗago ta yana rarrashinta shima yana kukan, Daddy shima a cikin damuwa ya miƙe ya koma cikin room ɗinsa, yana jin takaicin ya kasa cika wa Razhdeen alƙawarin da ya ɗaukar masa gashi har zuwa yanzu Allah bai ƙara basu haihuwa ba balle in ya ƙara samun mace ya ba shi...... Tin daga lokacin aka fame wa Razhdeen ciwon da ke cikin zuciyar sa, yanzu da Amreesh yake kwana sannan ya tashi da ita a cikin zuciyar sa, ya kuma ƙudurta a ransa cewa zai cigaba da jiran Amreesh har ta bayyana, ya furta cewa "in har yayi Aure kafin bayyanowar Amreesh to sai dai rabin zuciyarsa ce ta daina harbawa nan ne zai san Amreesh ta mutu.... ★★★★★★★ A ɓangaren Abbah kuwa damuwa na yau daban na gobe daban ƙarfi da yaji Uwar masu gida da Ƴar tinny sun ƙi dawowa yau tsawon wata guda, da haka har ya haƙura ya barsu... Da misalin ƙarfe 9 na dare Abbah ne yake zaune a falo shi da Ammy ga kuma Baiwar ALLAH itama a zaune domin yanzu mafi lawanci tafi zama a part ɗin Abbah saboda rage kewa, Roshan ya nemi ta nesanta kanta daga gare shi hakan yasa tin safe in tazo part ɗin su Abbah bata komawa part ɗinta sai ƙarfe 10 na dare, shima Roshan baya wuni a gidan saboda kar a fahimci wani abu rashin zamansa a gida shi zai sa a kau da ido akan daɗe War da Baiwar ALLAH take a part ɗin su Abbah, Suna zazzaune sai ga ƙiran wayan Abbah, yana dubawa sai yaga ƙiran su Pinky da Rukky ne dake can ƙasar London, Yana ɗagawa yaji muryar Pinky suka gaisa take sanar masa cewa "gobe zasu yi graduation..." Abbah ya nuna farin cikin sa sosai ya ce musu "Insha Allahu gobe zaku gan mu mun zo London..." Ta ce "tam Abbah sai kun zo..." ta kuma cewa "yawwa Abbah daman muna son sanar maka wani albishir..." Abbah ya ce "my Twins female ina sauraron ki..." Gashi yanda yasa wayar a speaker kowa na falon yana ji dake iya Ammy ne da Baiwar ALLAH. Pinky ta ce "kafin nan dai Albishirin ka..." Abbah ya ce "goro fari tass..." Pinky ta ce "Abbah Ni da Rukky mun fahimci juna zamu yi Aure..." Cikin rashin fahimta Abbah ya ce "kuna nufin kun samu mijin Aure ne?..." Pinky ta ce "a'ah Abbah Ni da Rukky ne zamu Auri juna saboda anan makarantar mu duk haka suke yi suna Auran junan su, namiji ya Auri namiji haka itama Mace ta Auri mace wallahi kuma fa Abbah kar kaga yanda ake dacewa da juna har party ake yi, mu ma za'a ɗaura mana Auren ina zaku zo partyn bikin bayan graduation ɗin ?...." Abbah jin kansa yayi ya tafi zuuuu ya rasa ganewa hajijiya ne ko kuma mai? Ammy da Baiwar ALLAH kallon juna suka yi cikin zaro ido waje jin abinda Pinky ke faɗi.. Pinky ta ce "Hello Abbah kana ji na kuwa..." Abbah ya ce "wait! wait wai kina nufin ke da Rukky zaku Auri juna? kuma haka ku ka ga anayi?..." Pinky ta ce "eh mana Abbah ai shiyasa nake cewa Nigeria ƙauye ne duk basu waye ba, domin ban taɓa ganin anyi ba..." Abbah ya ce "kenam iya Auren ku ka ga anayi? idan akayi Auren mai ake yi?..." Abbah yayi tambayar nan ne saboda yasan shin suna aikata mummunan aiki ne ko kuma... Pinky ta ce "idan akayi Auren Ni zan zama miji ita kuma Rukky mata ita zatana mana girki da aikin gida, Ni kuma sai ina fita yawo na, bayan wasu shekaru sai mu haifi ƴaƴan mu...." Abbah ya ce "kenam kun taɓa sanin junan ku yanzu haka?..." Pinky ta ce "kamar ya Abbah ban gane ba..." Abbah ya ce "kamar dai miji da mata su kwana gado ɗaya har suyi sex kun taɓa? ai dai kinsan sex kam..." Pinky ta ce "haba Abbah wannan ai sai an ɗaura mana Aure a school ɗin kafin nan, cab ai mun san haramun ne yin sex kafin Aure shiyasa zamu jira muyi Auren...." Abbah ya ce "kenam Auren da zaku yi ku biyu ke da ita ba haramun bane ba ko?..." Pinky ta ce "Abbah ka taɓa jin Aure ya zama haramun? ai ko wani irin Aure halal ne, Auren Mace da namiji halal ne haka Auren namiji da namiji shima halal ne haka kuma Auren mace da mace shima halal ne, saboda hakane yasa na sanar maka ko kuma zaku zo hidimar bikin..." Zuciyar Abbah ne yake bugun uku-uku cikin tsoro da fargaba ya ce "wannan gaskiya ne, zancen ki hakane Malama Balkisu, Yanzu abinda nake so da ku shine kuzo ayi bikin nakun a cikin ƴan uwanku domin abun alfahari ne ace ƴan uwa sun taru a gidan ku saboda Auren ku ko..." Pinky ta ce "Abbah ga ƙawayen mu anan har yaushe sai mun koma Nigeria ƙauye kuma..." Abbah ya ce "haba Balkisu baki ga Yayan ku Roshan shima a gida yayi Aure bane, dan ALLAH ku dawo kuyi Auren nan, Ni zan ɗauki ɗawainiyar komai da komai duk abinda kuke so, na tanadar muku da gidan da zaku zauna, in ma bazaku zauna ba zan kai ku ƙasar waje kuje ku huta duk ƙasar da ku ka zaɓa...." Pinky ta ce "gaske Abbah wow munyi farin ciki sosai...." Abbah ya ce "yanzu abinda nake so da ku shine graduation ɗin ma ku bari sai kun dawo gida sai a haɗa da bikin ku Koh?..." Pinky ta ce "ai gobe ne graduation ɗin..." Abbah ya ce "eh gobe da sassafe ku hau jirgi ku dawo da wuri kun ji Daughter's ɗina...." Pinky ta ce "to shikenam Abbah zamu fara shiri tin yanzu gobe zaku gan mu a Nigeria..." Abbah ya amsa mata cikin kulawa amma cikin zuciyar sa tafasa yake kawai jurewa yake.... Sai bayan sun kammala wayar ya ɗorata akan ƙirji yana sauƙe nannauyar numfashi har zuwa yanzu ƙirjinsa bugawa take, a ransa yana faɗin "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un, Allahumma ajurni fi musibati wa akhlifli khairan minha, wannan wani irin ƙalubale nake fuskanta ne kam, duk ƴaƴa babu na gwara, ɗaya tabi saurayi sun gudu wacce take ji da ita ta zaɓi uwarta tare da Auta ta, ga kuma sauran biyun suna son kauce hanya wai Auren jinsi..." haka yake ta wannan tunanin a ransa... Ammy ta ce "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un, waɗannan yaran basa jin magana, gwara da kayi musu kalamai cikin kulawa da fahimta, inda ace kayi musu magana ta zafi yanda kake cikin damuwan nan ai ba'a san mai zai faru ba, gashi yanzu cikin lallami zasu dawo hankali a kwance....." Baiwar ALLAH kam abun ma dariya yaso bata, kamar waɗanda basu shiga islamiyya ba, kodan rayuwar can ta chanza su sosai, dan ma Aski yazo gaban goshi sun kammala school ɗinsu, Abbah a yanda hankalinsa ya tashi nan ai ko basu gama school ɗin ba ma zai cire su a makarantar.... *MA SHA ALLAH* *DAGA WANNAN SAI LAST PAGE SAI KUMA MU SHIGA BOOK 3 TAKUN ƘARSHE..."* *WAƊANDA SUKA BIYA KUƊIN SU NA BOOK 3 300₦ ZAKU GA NA FARA SAKA KU A PAID GROUP, ZUWA NEXT WEEK ZAMU FARA BOOK 3 TAKUN ƘARSHE...* *DALILIN DA YASA NA ƊAGA SAI NEXT WEEK SABODA WAƊANDA BASU BIYA BA SU SAMU DAMAR BIYA KAFIN ZUWA LOKACIN, SABODA A FARA A TARE...* *GOBE INSHA ALLAHU ZAMU YI LAST PAGE* *ASMA'U MUHAMMAD AUWAL* *9065443871 OPAY BANK* *PAY 300₦ ONLY 👌* *SHAIDAR BIYA TA WANNAN NUMBER 09065443871* *DAGA YAU ZUWA KULLUM I'M AVAILABLE* *09065443871 CALL OR WHATSAPP* *TO MASOYA KAMAR YANDA NA SUBURBUƊO MUKU TYPING NIMA INASO KU SUBURBUƊO MUN SHARHI😅😅😅* FATAN ALKHAIRI 🙏 asmeetah writer ✍️ 🤦‍♀️ *MAƘIYI_NAH*🤦‍♀️ *MY ENEMY _* 🫦 مقىينا 🫦 Mallakin أسماء محمد أولا 🥳 Asmeetah (giaɗe writer) https://www.facebook.com/61556643936657/posts/122103978398221464/?substory_index=1596987511055341&mibextid=rS40aB7S9Ucbxw6v 💪 *JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*💪 ✍️ (J.W.A) _Rubutu baiwa ce daga Allah, jajirtattu ne kawai kan iya amfani da wannan ƙasaitacciyar baiwa su sauya tunanin al'umma cikin sauƙi_.✏️ STEP TWO 👇 *46_ TO_50* *THE END OF BOOK TWO* *wannan shine ƙarshen littafi na biyu sai mun haɗu a littafi na uku wato takun ƙarshe...* *Ku biya kuɗin ku domin samun cigaban littafin 300₦ 👌* *Domin samun ƙarin bayani a tuntuɓe ni ta wannan number* 09065443871 call or whatsApp .... Bayan Dawowar su Pinky da Rukky da kwana biyu suka ga Abbah ko sauraron su baya yi abun sai ya basu mamaki, Pinky ce tayi ƙarfin halin zuwa har part ɗin Abbah ta same shi yana zaune akan sopa kansa na kallon sama da duk kan alamu dogon nazari ya shiga, jin sallama yasa ya ɗago yana kallon wacce ta shigo. Pinky zama tayi a gefen Abbah tana gaishe shi, Abbah amsa mata yayi tare da faɗin "ji ta kamar ta Allah..." Pinky ɗago wa tayi tana kallon Abbah cikin rashin fahimta, Abbah cewa ya yi "tashi kije ki ƙira mun ƴar uwarki kuzo tare..." Pinky cikin murna ta tashi tana magana a cikin ranta haɗi da cewa "yawwa Abbah yanzu za'a tattauna akan batun party graduation da kuma engagement ɗin mu Ni da Rukky..." Abbah bin bayan ta yayi da kallo yana girgiza kai domin ba ƙaramin tausayawa yaransa yake ba... Bayan wasu mintuna sai ga Rukky sun shigo duk suka zauna akan carpet suna sauraron abun da Abbah zai sanar musu... Abbah ne ya buɗi baki ya ce "Balkisu, Ruƙayyat ban taɓa sanin cewa ku dabbobin tumakai bane sai yau...." Kallon juna suka shiga yi cikin rashin fahimtar Abbah, Pinky ta ce "Dabbobi dai?..." Abbah ya ce "ai kun fi dabbobin ma dabbanci domin su dabbobi basa taɓa zama mutane amma mutane sukan zama dabbobi to ku kuna daga cikin su..." Rukky ta ce "innalillahi....." Bata ƙarasa ba Abbah ya darara mata tsawa da cewa "ki mun shuru dallah, ke kinsan innalillahi kuwa? Inda kun sani da baza kuyi ƙoƙarin aikata ɓarna a doron ƙasa ba, inda ace ban saka ku a islamiyya ba sai naga laifin kaina amma yanzu na rigada na sauƙe hakkin ku a kaina sauran abu ɗaya ya rage shine na samu na Aurar da ku, amma saboda daƙiƙancin ku wai har kuna ƙirana a waya cewa zaku yi Auren jinsi abu ko daɗin faɗi babu, in banda rashin ilimi da jahilci tin daga furucin sunan zaku san cewa wannan baya daga cikin addinin Musulunci, a cikin litattafan musulunci aina ku ka taɓa jin an sanar cewa ayi Auren jinsi?...." Rukky ta kalli Pikky tana hararar ta cikin ranta tana faɗin "ai daman nace kar ki sanar wa Abbah ki kayi kunnen uwar shegu..." Abbah ne ya zaro ƙaramar bindigar sa daga aljihu tare da kunna kunamar bindigar ya sai ta su. Pinky da Rukky gaba ɗayan su baya suka ja suna zazzaro ido waje a tsorace, Abbah ya ce "ko ku sanar mun gaskiya ko kuma yanzu na aika ku lahira kuje can ku cigaba da shirmen ku domin ba'a gabana zaku yi wannan ta'addanci ba..." Rukky kamar zatayi kuka ta ce "Abbah wallahi zan faɗi gaskiya..." Abbah ya ce "to inajinku..." Pinky ta ce "Abbah ai baka faɗi maganar da zamu faɗi gaskiyar ba..." Abbah ya ce "ku faɗa mun gaskiya magana ɗaya shin kuna maɗigo? wallahi idan naji ƙarya daga bakin ɗayan ku saina harbe ta..." Rukky ta dafe ƙirjinta tare da faɗin "wallahi tallahi na rantse da mahalicci na bamu taɓa aikata irin haka ba tinda muka zo duniya, maganar gaskiya kenam..." Itama Pinky ta ce "Abbah me zai sa mu aikata wannan abun, mun san dai sai anyi Aure akayi..." Abbah ya ce "maɗigo ɗin dan ubanki?..." Da sauri ta girgiza kai cikin nuna tsoro.. Suna cikin wannan halin sai ga Ammy ta shugo tana murmushi tazo har yanda suke ta ɗago su idonta akan Abbah ta ce "kayi haƙuri Abban yara irin wannan a hankali ake binsa, ka ciro bindiga ai tsoro ma bazai barsu su faɗi gaskiyar ba, Ni zan je da su zamu yi magana ta fahimta sannan ayi musu nasiha a ƙara tunatar da su abubuwan da addinin musulunci ya ƙunsa..." Abbah cikin ɓacin rai ya kawar da kai ko sauraronsu bai yi ba, haka Ammy ta fita da su.... Garin Suleja Ummy da Ƴar tinny har sun murmure na ɗaukin ganin mahaifiyar su, suna zaune cikin ƙoshin lafiya, ga Aunty Yolash kusan kullum sai tayi musu aike domin ba ƙaramin farin ciki tayi ba jin yara biyu sun dawo wurin mahaifiyar su ko ba komai zasu ɗauke mata kewa kuma zata rage tunanin Abbah.... Bayan wasu kwanaki Pinky da Rukky gaba ɗaya basa jin daɗin zaman gidan domin gidan ya yi shuru kamar ba mutane ga rashin ganin ƴan uwansu ko ba komai zasu ji daɗin zama idan suna kusa da ƴan uwan, Minal ta tafi ga Ummy da ƴar tinny suma sun gudu wurin Maman su, ga Baiwar ALLAH basa shiri balle suje part ɗinta, su kuma baza su iya zama da Ammy suyi hira ba hakan yasa suka yanke shawara suma zasu gudu wurin Mamansu, gashi graduation ɗin da zasu yi ba'ayi ba Abbah ya yaudare su a cewar su.. Ganin ba wata mafita saboda ta ko ina a cikin tsaro yake, shawara ɗaya suka yanke cewa zasu sanar wa Abbah cewa zasu kai wankin kayansu tinda yaƙi kai su wurin Maman nasun. Kamar yanda suka tsara haka suka samu Abbah cewar zasu kai kayan su gidan wacce take musu wanki, Abbah ya ce "meyasa ita ɗin bazata zo tayi anan gidan ba sai an kai mata, bana so kayan ku suna fita can wani wuri..." Pinky ta ce "Abbah wai bata jin daɗin jikinta ne shiyasa zamu kai mata duk sanda ta miƙe zuwa gobe ko jibi sai tayi mana sannan ta goge sai ta kawo mana..." Abbah ya ce "to kuje Security ɗaya ya kai ku sai ku dawo da wuri..." Suka amsa sannan suka fita daga falon sa.. Already sun ciccire kayansu daga akwati sun maida su cikin babbar jaka wuri ɗaya yanda baza'a gano su ba. Security ne ya ɗauke a mota ya kai su har ƙofar gidan mai musu wanki, a ƙofar gidan yayi parking da mota su kuma suka shige gidan, ba tare da matar gidan tasan da zuwan su ba haka suka bi wata ɓoyayyar hanya dake cikin gidan suka fita ta can suka gudu... Security dai waran awan sa uku yana tsaye jiran fitowar su amma shuru, ganin zaman yayi yawa yasa ya fara kwaɗa sallama dake matar tana da miji... Matar ce ta fito tana sanye da hijab ɗinta har ƙasi ganin ɗaya daga cikin security gidan Chief ne yasa ta durƙusawa har ƙasi tana gaishe shi, ya amsa mata a mutunce sannan ya ce "wai waɗannan yaran sun manta dani a waje ne?..." Matar ta ce "wasu yaran?.." Security ya ce "ha'a su Pinky yaran Chief tin ɗazu na kawo su da jakar kayan wankin su...". Matar ta ce "ai ni basa kawo mun wanki sai dai naje har gida nayi musu saboda tsaron da Chief yake basu, amma ya akayi yau ɗin aka barsu su kawo wanki, kuma Ni ina gidan banji motsin kowa ba innalillahi..." Security ya ce "na shiga uku yau sun jawo mun tashin hankali..." Matar ta ce "amma tin yaushe suka shiga?..." Security ya ce "yanzu waran awa huɗu fa duk ina tsaye zaman jiran su..." Suna cikin wannan halin sai ga mijinta ya dawo nan ta kwashe ta sanar masa halin da ake ciki, Mijin ya sanar wa security cewa "ka shigo Mu dudduba ciki ko sun ɓuya ne, domin akwai matsala in ka koma ba tare da yaran nan ba..." Haka suka shiga ko ina sai da suka dudduba amma ba motsin su, sai daga baya aka gano cewa ta ƙofar baya suka fice ganin wani ɗan ƙaramin ƙofa a buɗe. Security hannu ya ɗora a kai tare da faɗin "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un yau mai zan ce wa Chief..." Matar ma haka take ta salati tana jero Addu'o'i domin abun ba ƙaramin bata mamaki yayi ba, tana tunanin taya suka san da wannan ƙofa alhalin basu taɓa ganin wurin ba... Mijin matar ne ya dafa kafaɗarsa Security sannan ya ce "ka kwantar da hankalin ka kaje ka sanar masa yanda al'amarin ya faru, ai ba laifinka bane tinda ba daga hannunka suka fece ba, idan suka dawo su kuma zasu yi bayanin yanda suka je...." Security ya ce "shikenam ba damuwa amma ina neman alfarma ɗaya ina so na tafi daku domin ku zamo mun shaida..." Suka ce ba damuwa haka suka shiga mota suka tafi... ★★★★★★ Pinky da Rukky kuwa har sun isa garin Suleja, sai da suka isa tukun suka nemi wayar Ummy domin Mommyn su ta chanza sim, Ummy tayi farin ciki sosai jin labarin su Pinky sun zo, haka Hajiya Kilishi ta rinƙa tunani a ranta cewa "anya da sanin Abban su suka zo? amma kuma akwai security mai kai su ko ina zai yi wuya su tafo ba tare da sanin kowa ba..." haka take wannan tunanin a ranta. Bayan sun zo har suka shiga gidan da Ummy ta kotanta musu domin yanzu tasan duk wani lungu da saƙo na unguwar yanzu a free take... Pinky da Rukky suna shiga gidan bayan sun je part ɗin da Mommyn su take suna ganin ta haka suka rufa da gudu suka rungume ta suna farin cikin ganin mahaifiyar su, sunyi matuƙar kewar juna sosai haka rayuwa ta dawo musu kamar sabuwa... Abbah bayan yaji wannan mummunan labarin ya firgita sosai sannan zuciyarsa ta sosu matuƙa bayan yayi bincike ya gano cewa yaran guduwa suka yi wurin mahaifiyarsu can garin Suleja, Abbah kamar yayi hauka haka ya shiga ƙuncin rayuwa, haka ya yanke hukuncin cewa bazai taɓa zuwa yanda suke ba tunda sun zaɓi su rabu da shi.... ★★★★★★★ Bayan wata guda da wasu kwanaki gaba ɗaya Abbah ya fita hayyacinsa damuwa ya yi masa yawa har sai da ya kwanta rashin lafiya hawan jininsa ya tashi, daga baya ya samu sauƙi sai kuma ya yanke hukuncin zuwa ya gano ƴaƴansa dake garin Suleja idan da hali yana son ɗauko su gaba ɗayansu. Washe gari da sassafe ya tayar da tafiyarsa zuwa Suleja, misalin ƙarfe 12 zuwa 1 har ya isa, a ƙofar gidan yayi parking sannan ya yi magana a wani yaro yana ƙofar gidan yaron ya yi masa kwatancen yanda part ɗin hajiya kilishi yake, Abbah bai jira wani excuse ba haka ya kutsa ciki, yabi hanyar yanda part ɗin yake ba mistake yana tura ƙofar mashigar part kwatsam sai ya tarar da hajiya kilishi a gaban murhun gawayi ga tukunya akan murhun alamu sun nuna girki take yi ga ba kowa a tsakar gidan sai ita kaɗai. Ummy uwar masu gida ta tafi ɗiban ruwa acan bakin fanfo amma a cikin gidan yake can wani ɓangare daban, Pinky da Rukky kuma sun tafi bakin hanya suyo kifin da zasu yi miya da kayan vegetables, ita kuma Ƴar tinny tana cikin ɗaki tana ta shan baccin ta akan katifar da iya ita kaɗai ne a ɗakin sai ledar tsakar ɗaki, wurin kwanciya duk yaran ne suke haɗuwa akan katifar su kwanta dake ƙatuwa ce katifar ita kuma Hajiya Kilishi shimfiɗi take a ƙasin ledar ɗakin ta kwanta haka suke inganta rayuwar su ba takuri da tsangwama... Hajiya Kilishi tana zaune ɗaga kanta da zata yi kwatsam sai suka haɗa ido da Abbah, kamar a mafarki a gigice ta miƙe tsaye cike da fargaba da tsoro domin tasan akan yaran yazo, ga su Pinky sun sanar mata cewa gudowa suka yi, tayi dasu akan su koma amma fur sun ƙi da haka ta haƙura ta barsu, Hajiya Kilishi idanuwanta ne suka cicciko da ƙwallah domin tasan duk laifin akanta zai ɗora wa kuma bata san da wani kalar wulaƙanci yazo ba.. Abbah cikin fushi da haɗe rai ya ce "ina kika kai mun yara?..." Hajiya Kilishi ƙiƙƙina ta fara yi tana tunanin mai zata fara ce masa alhalin tasan yaran basa fita ko ina acan gidan su balle a aike su, "Am amm Auta tana bacci a cikin ɗaki..." Kafin ta iddasa maganar ya katse ta tare da darara mata tsawa yana faɗin "nace ina yarana suke? kada ki kuskura kice mun kin aike su domin ranki zai yi mungun ɓaci a yanzun nan, kin dai san bana aikan yaran, idan wani abu ya faru da yarana kiyi kuka da kanki sannan idan kika kuskura aka sace mun yara wallahi sai kin ƙwammace baki zo duniya ba..." Hajiya Kilishi hawaye ta soma zubar wa domin tasan yaran aika suka tafi itama ba'a son ranta ba, su suka ƙi barinta tana fita aikan da kanta.. Abbah ya buɗe baki zai yi magana sai yaji sallama ta bayansa, da sauri ya waiwaya domin yasan ɗaya ne daga cikin su, ganin Uwar masu gida da bucket na ruwa a kanta yasa shi zare farin glass ɗin dake kan dararan idanuwan sa, cikin ɓacin rai ya furta "whattt?..." Ummy ganin Abban su yasa ta wuce shi da sauri ta sauƙe bucket ɗin ruwan taje ta rungumo Mommynsu tana rarrashinta ganin yanda take ta zubar da hawaye.. Abbah ya ce "uwar masu gida shin baki ga Abbanki bane?.." Ummy ta ce "sannu da zuwa Abbah, amma dan ALLAH kar kaga laifin Mommy domin mu muka zaɓi mu zauna da ita ba wai ita ce ta riƙe mu ba, kar ka sa mana ita kuka tana cikin farin ciki..." Abbah ya ce "to meyasa ku ka zaɓi ku zauna da mahaifiyar ku akan Ni mahaifinku wanda zanfi baku kulawa sama da ita..." Ummy ta ce "Abbah kayi haƙuri mahaifiyar mu ita ce sama da kai a wurin mu, domin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama yana umartar mu da mu bi uwa, mu bi uwa! mu bi uwa!! mu bi uwa!!! har sai da ya maimaita sau uku kafin nan ya ce mu bi uba, don haka zamu fi samun farin ciki mai ɗorewa idan muna tare da mahaifiyar mu..." Abbah ya ce "hakane uwar masu gida amma ki zauna a gaban mahaifinki shine mutuncinki da darajar ki wanda ko neman Auren ki akazo yi uwa bazata bayar ki ba dole sai da uba ko ƴan uwan mahaifin ki, ke da ƴan uwanki duk wani abun more rayuwa da kuɗi kuna samu daga wurina bana takura muku...." Ummy ta ce "Abbah ka sani fa inda ace kuɗi suna dawwamar da mutum cikin farin ciki da Babbar Yayar mu bata gudu tabi mijinta ba saboda tasan duk da kuɗin da take da shi bazai taɓa sanya ta cikin farin ciki ba, haka zalika inda kuɗi sune kwanciyar hankalin mutum da baka kasance cikin damuwa da kaɗaici ba to haka mu ma kuɗi bazai taɓa sanya mu cikin farin cikin ba without our mother, because our mother she's our happiness...." Abbah shuru yayi yana kallon Ummy ya ma rasa mezai ce mata, yana cikin nazari sai ga Pinky da Rukky sun shugo sunata shan hirar su na school da suka baro, idonsu ne ya sauƙa akan Abban su da gudu suka wuce shi suka je duk suka ɓuya a bayan Mommynsu suna faɗin "Please Mom please kar ki bari ya tafi da mu please..." Hajiya Kilishi kanta na kallon ƙasi ta kasa cewa komai domin yanzu Ummy ta fi su baki gaba ɗayan su, Su Pinky su kam sai dai masifa da munafurci da rashin mutunci ga kuma tsoro, amma ita Ummy akwai ta da iya zayyano da zance wanda ko mai shekara 40 bazata nuna mata iya magana ba, domin tinin zata saye zuciyar mutum da kalamanta ko masu daɗi ko akasin haka..... Abbah ya ce "to yanzu mai ku ke so ayi?..." Ummy ta kalli su Pinky ta ce "kune Auntys shin ya ku ke so ayi?..." Daga Pinky har Rukky duk kasa yin magana suka yi daga sun haɗa ido da Abbah sai suyi saurin sunkuyar da kansu ƙasi kamar wasu marasa gaskiya, Ummy ta ce "Abbah akwai yanda za'ayi amma mu shiga cikin ɗakin mana Abbah kana ta tsaye tin ɗazu..." Abbah ba yanda ya iya haka ya shiga ciki, duk suma suka shige, Ummy ta ce "Abbah ka zauna a bakin katifar mana..." Nan ma ya zauna yana binsu da kallo. Ummy ta tsaya tare da kama kunkumi ta ce "kash ga ba'a kammala girki ba ai da an kawo wa Abbah..." Abbah ya ce "no bana buƙatar komai..." Ummy ta ce "Abbah to bari a kawo ruwan sha.." Nan ma ya ce "a'ah..." Ummy ta ce "tam shikenam Mommy kema zauna domin akwai maganganu masu mahimmanci da zamu tattauna akai..." Kowa ya nutsu yana sauraron Ummy domin ita kanta Hajiya Kilishi bata san wani irin magana Ummy zata sanar ba.. Ummy tana zaune a ƙasin ledar ɗakin kusa da Mommyn su, suma twins suna gefen Mommy domin duk cikinsu kowa ba son yin nesa da ita yake ba, sai Ƴar tinny dake bayan Abbah a kwance kan katifa.. Ummy tana kallon Abbah ta ce "Abbah..." Abbah ya amsa mata cikin sassanyar murya domin har yanzu jikinsa bai gama warkewa ba. Ta ce "dole a cikin abu biyu ayi ɗaya ko a rasa ko kuma a samu shine kawai..." Abbah ya ce "muje zuwa Uwar masu gida..." Ummy ta cigaba da cewa "idan kanaso mu kasance da kai cikin farin ciki da annashuwa to dole sai muna tare da mahaifiyar mu a kusa, in har zamu bika mu tafi to dole sai da mahaifiyar mu, ƙafar ta ƙafar mu, Idan kuma hakan bazai yu ba to zaka iya barin mu anan in yaso idan kana son ganin mu zaka zo ka gan mu amma da sharaɗin bazaka ƙuntata wa mahaifiyar mu ba domin ba wurinta kazo ba, wurin mu kazo, idan kuma tafiyar tayi maka nisa ai kanada gidaje a cikin Abuja sai ka kai mu can mu zauna da mahaifiyar mu, amma baza mu taɓa yin nesa da ita ba sai dai mutuwa...." Abbah kawai tsaya kallon Ummy yayi tana ta zayyano da zance, daga bisani ya ce "okay duk naji abinda kika ce an ɗauke ku har ita na maida ku gidana domin hankali na bazai taɓa kwanciya idan bana ganin ku a kusa dani, gani nake wani abu zai faru da ku especially idan kuna fita yawo koda yaushe dole wasu samari zasu dakatar da ku daga lokacin da ku ka fara tsayawa da wani namiji a titi shikenam rayuwar ku ta fara tafiya, especially Balkisu da Ruƙayyat sun fiye rawan kai dole sai idanuwa na suna kansu, idan suka yi nesa dani hankalina bazai taɓa kwanciya ba, dan haka na zaɓi ku koma gida yanda zaku samu tsaro na musamman..." Pinky da Rukky farin ciki kamar zasu fidda fikafiki su fura da Mommynsu jin da ita zasu koma gida.... Ummy murmushi tayi sannan ta ce "Abbah nayi farin cikin jin haka amma sai dai akwai abu a ƙasa...". Abbah ya ce " to sarkin ƙorafi ina jinki..." Ummy ta ce "in har Mommy zata koma gidanka to a tabbatar an maida Auren ku domin bazata taɓa komawa gidanka babu Aure ba, kayi haƙuri Abbah..." Dogon numfashi Abbah ya ja sannan ya ce "Uwar masu gida meyasa kike haka ne? meye laifi don ta koma gidana da zama ba tare da Aure ba? duk wata ɗawainiyar ta zan ɗauka, ci da sha sutura kuɗin kashe wa duk zan bata, sannan zan mayar ta wurin aikin ta..." Ummy ta ce "duk da haka Abbah domin idan ta zauna da Auren ta zata fi yin daraja a idon mutane, bayan haka Mommy ba tsufa tayi ba balle ace tayi tsufar da bazata yi Aure ba, idan ka barta a haka zaka cutar da ita ne, kuma sannan idan tana gidanka babu wanda zai zo neman Auren ta kuma mu ma bason ta Auri wani muke ba, nasan Ammy bata da matsala zata yi farin cikin kasancewa da Mommy, please Abbah wannan shine Alfarmar da zakayi mana, sannan ka jawo mana mutunci Please..." Abbah ya ce "shikenam idan har kasan shi zai sa kuyi farin ciki sannan ku zauna a inuwar mahaifinku nima na amince amma saboda ku..." Ummy tsabar murna bata san lokacin da ta tafo ta rungumi Abbanta ba, duk sauran haka suka tafo duk suka rurrungumi Abbah.. Ummy ta hango Mommynsu tana zaune kai a sunkuyar ita kaɗai sai zabga murmushi take.. Ummy ta ce "Mommy ke ma tafo gurin mijinki mana..." Hajiya Kilishi ta girgiza kai tana dariya, dai dai lokacin ƴar tinny ta tashi daga bacci, ganin Abbah yasa ta nufo wurin sa da gudu tana faɗin "Abbah nah! Abbah nah..." ta rungume shi... A yau suka magantu Abbah da Hajiya Kilishi suka fahimci juna da cewa tayi alƙawarin bazata sake ƙuntata wa kowa ba, zata yi ƙoƙarin ganin ta zama mutumiyar arziƙi, kuma zata cigaba da zama a gidan mijinta har ƙarshen rayuwar ta... Gaba ɗaya hamdala suka yi Abbah sai da ya jira aka kammala girki sannan suka ci su ka sha, kuma a wannan ranar Abbah zai tattare su a mota ya tafi da su tinda ba wani shirgi ne da su ba, duk wasu kayan ɗakin Hajiya Kilishi ta sayar da su taci abinci da kuɗin, Kafin su tafi sai da Abbah ya biya kuɗin hayan gidan da suka zauna sannan suka fiffito da akwatina da jakakkuna kowa ya kasance cikin shiri tsab, daga nan suka nufi Abuja... ★★★★★★★ Baiwar ALLAH gaba ɗaya garin ya yi mata zafi, tayi kukan har ta gaji, ga yanzu duk halin da zata shiga bata samun mai rarrashin ta, domin Roshan ko leƙa ɗakinta baya yi sannan itama bata zuwa yanda yake, suna gida ɗaya amma sai suyi kwana biyar basu haɗu ba... Tana kuka tana tura kayayyakinta cikin akwati domin a halin yanzu bazata iya cigaba da zama a haka ba, ta yanke hukuncin barin gidan gaba ɗaya, ta shirya kayanta tsab ta fito falo hannunta riƙe da takarda da biro, ajiye akwati tayi a falo ta nufi part ɗin Roshan, a hankali take knocking cikin ƙanƙanin lokaci sai gashi ya buɗe fuskar nan tayi fiyau ga yayi fari tass kamar ba jini a jikinsa da duk kan alamu bashi da lafiya ne.. Ganin Baiwar ALLAH yasa zuciyarsa bugawa ganin hawaye shaɓe-shaɓe a fuskarta, a hankali yake motsi da lips ɗinsa ya ce "meya faru da ke?..." Miƙa masa takardar hannunta tayi tare da biro tana kuka ta ce "ga shi nan, ban ga amfanin irin wannan zaman ba, dan ALLAH yau a kawo ƙarshen zaman nan Ni na gaji, wani sa'in har manta wa nake da inada Aure, dan ALLAH yau kam ka sallame ni, gidan zan bari gaba ɗaya, zan fita naje na nemo iyaye na..." Roshan ya ce "ki kwantar da hankalin ki Razhdeen ya kusan dawowa..." Cikin ɓacin rai ta katse shi da cewa "Ni babu ruwana da wani Razhdeen ban sanshi ba, dan Allah Yaya Roshan ka dawo hayyacin ka, ka tantance abunda nake so da kuma abunda bana so, amma yanzu komai yazo ƙarshe, yanzu dai ka sallame ni kawai...." Lumshe idanuwansa yayi cike da damuwa ya ce "shikenam.." yasa hannu ya karɓi takardar da biro ya juya zai je ya rubuta mata, wani irin suka yaji zuciyarsa tayi tare da bugawa da ƙarfin gaske a firgice yasa hannu ya dafe sai tin zuciyarsa yana shirin kaiwa ƙasi. Ganin yana shirin faɗuwa yasa Baiwar ALLAH shugowa ciki da gudu tayi saurin riƙo shi tana ambatar sunansa "Yaya Roshan! Yaya Roshan dan ALLAH ka daina Please ka tashi bana son irin wannan wasan..." Shi kuwa lokaci guda idanuwansa suka fara ƙaƙƙafewa yana fitar da numfashi daƙer, ga yanda yake sama da ƙasa da ƙirjinsa alamun bugawa yake sosai, Baiwar ALLAH fashe wa tayi da matsanancin kuka tana faɗin "dan Allah Yaya Roshan ka tashi, wannan wani irin wasa ne haka, bana son kalar wasan nan, ni idan baka son rabuwa da ni zan cigaba da rayuwa da kai a haka, nima ba son rabuwa nake da kai ba, ka rufa mun asiri dan Allah..." Tana cikin wannan halin yana kwance saman cinyar ta sai ga wani irin jini ya burtso masa daga cikin bakin sa.. A ruɗe Baiwar ALLAH ta zaro manya-manyan idanuwanta ta ce "na shiga uku Yaya Roshan..." wani irin tari yake yana Amar da jini, eyes ɗinsa har sun chanza color sun koma green, jikinsa gaba ɗaya ya koma yellow alamun babu jini a jikinsa, yana kaiwa ƙarshen tarin sa numfashin sa ya ɗage gaba ɗaya, sai wuyansa da ya karye..." Hannu ta ɗora aka ta zabga wani irin gigitaccen ihu tana faɗin "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un Yaya Roshan ɗina, wayyo nashiga uku Dan girman Allah ka tashi, Yaya Roshan ka taimake ni ka tashi wallahi ina sonka, ina matuƙar ƙaunar ka mijina, ina sonka mijina wallahi, bazan iya kasancewa da kowa ba inba kai ba, wallahi idan ka mutu Nima rayuwata bata da wani amfani Yaya Roshan..." ★★★ Abbah kuwa suna isowa cikin gari basu tsaya a ko ina ba sai a babban masallacin juma'a anan ya sanar da ɗaurin Auren sa da za'a gabatar a yau Jumma'at, ya ƙira manya abokansa a waya, ya sanar musu cewa yana gayyatar su zuwa masallacin juma'a, waɗanda ya gayyato basu san meye dalilin ƙiran su ba sai da suka zo tukun suke jin labarin ɗaurin Aure, za'a mayar da Auren sa da uwar ƴaƴansa Hajiya Kilishi ba tare da wasu daga cikin mutanen sa sun sani ba, sai iya waɗanda yake da kusanci da su, anan ya bayar da sadaki ya wakilci wasu a mazannin wakilai ga kuma shaidu... Hajiya Kilishi da ƴaƴanta kuwa suna cikin mota suna jiran zuwan Abbah domin ko su basu san a yanzu za'a mayar da Auren ba.. Suna zaune sai suka hango Abbah da abokansa waɗanda ya gayyato sun nufo motar, har an kammala ɗaurin Aure cikin ƙoshin lafiya, Bayan isowar su Abokanan Abbah fatan alkhairi suka rinƙa musu tare da nasihohi da wa'azi especially Hajiya Kilishi an fi ja mata kunne kafin daga baya Abbah ya ja su suka nufi gida, amma yaso ace ammy ta sani bawai ta gani kai tsaye ba, amma babu yanda ya iya gwara ayi abu a wuce lissafinsa... Hajiya Kilishi ta sha mamaki sosai da taji a yanzu har aka maida Auren ta, ba ƙaramin farin ciki ta shiga ba, anan ta ƙara jinjina wa ikon Allah, Addu'ar ta yayi tasiri lokaci guda Allah ya karkato mata hankalin Chief... Suma yaran ba ƙaramin farin ciki suka shiga ba... Wayar Abbah ne ya fara ringing ganin Razhdeen ne yasa shi sakin murmushi ya ɗaga yana faɗin "Ogan Sojoji ya akayi ne?..." Razhdeen cikin sassanyar murya ya ce "Dad me yake faruwa ne?.." Abbah ya ce "me ya faru?..." Razhdeen ya ce "gaba ɗaya hankali na ya kasa kwanciya, zuciyata sai bugawa take, i think so akwai wani mummunan abu da yake shirin faruwa a gida..." Gaban Abbah ne ya yanke ya ce "mummunan abu kuma Razhdeen? a'a babu wani abu da ya faru duk muna cikin ƙoshin lafiya..." Razhdeen ya ce "where is my twins?..." Abbah ya ce "na bar shi a gida cikin ƙoshin lafiya..." Razhdeen ya ce "okay fine..." Yana kaiwa nan ya katse ƙiran. Abbah shima hankalinsa kasa kwanciya yayi jin abinda Razhdeen ya sanar masa domin in irin haka ta faru da Razhdeen to akwai abinda ya faru ko kuma zai faru, most especially idan abun akan Roshan zai faru... Haka Abbah ya ƙarawa motarsa gudu yana son isa yaga shin da gaske ne abinda Razhdeen ya sanar masa ko kuma! In har ya haɗu da Roshan cikin ƙoshin lafiya to sai dai akan wani nashi ne abun zai faru... Cikin lokaci ƙanƙani Abbah ya isa gida, a rikice ya shige bayan an bubbuɗe masa gate gate ɗin da suke gidan. Su Ummy ne suke ta tambayar sa meya faru amma Abbah ya kasa basu amsa sai ya tabbatar da idonsa.. Abbah bai tsaya a ko ina ba sai a part ɗin Roshan ko tsaya sauƙe su Hajiya Kilishi bai yi ba, yana sauƙa ya nufi cikin babban falon gidan, suma sauran haka suka bi bayansa, suka tarar falon ba kowa, Abbah ya kalli Ummy ya ce "shiga ciki ki ƙira mun Daughter..." Ummy ta nufi part ɗin Baiwar ALLAH, can ta dawo tana faɗin "Abbah bata nan fa..." Abbah ganin tsayuwar bashi da amfani yasa shi nufan room ɗin Roshan domin yafi son yayi ido huɗu da shi, yana zuwa ya samu ƙofar ɗakin a buɗe, ganin Baiwar ALLAH tana rungume da Roshan a ƙasin carpet yasa shi ƙarasa shiga da sauri yana faɗin "lafiya kuwa Daughter me ya faru da shi..." Ɗagowa tayi da jajayen idanuwan ta waɗanda suka kaɗa sukayi jawur tsabar kuka ga bakinta duk jini yanda ta haɗe bakinta da na Roshan tana hura masa iskar bakinta ko numfashin zai dawo... Abbah ganin halin da Roshan yake ciki ne yasa shi firgita yayo kansa da gudu yana "faɗin innalillahi wa inna'ilaihi raju'un ashe gaskiyar Razhdeen, gaskiyar Razhdeen, ciwon sa ne ya tashi..." Haka yasa hannu ya ɗago shi yana faɗin "Daughter taya ni ɗaukar sa mu fita..." Itama Baiwar ALLAH hannu tasa suka ɗago shi, suka fice falo da shi, su Ummy ganin halin da Roshan yake ciki ne yasa duk suka nufo su... Ba ƙaramin tashin hankali suka shiga ba Abbah ko leƙa gidan sa bai yi ba haka ya ƙara shiga mota security ɗaya yaja su suka nufi hospital, Baiwar Allah hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ganin haka ne yasa Abbah ya dakatar da ita suka tafi iya su biyu daga Abbah sai Roshan da kuma security, Gaba ɗayan su kuka suka soma yi domin a halin da Roshan yake ciki ba mai cewa yana da rai, haka suka shige cikin gidan tamkar anyi musu mutuwa, duk a falo suka zazzauna Hajiya Kilishi ta zabga uwar tagumi tana tunani kala-kala a ranta, maimakon tazo ta samu kowa cikin ƙoshin lafiya sai kuma ta tarar da wani tashin hankali, tana cikin wannan tunanin taji Pinky tana faɗin "ai duk kece kika jefa shi cikin wannan mun sani, wancan lokacin ma saboda ke ciwon zuciyarsa ya tashi..." tana nuna Baiwar ALLAH cikin ɓacin rai, Baiwar ALLAH damuwar da yake kanta ma ya ishe ta haka take zubda hawaye ba ƙaƙƙautawa... Hajiya Kilishi idonta akan Pinky ta ce "kina ganin halin da take ciki amma kina gaya mata cewa ita ta jawo? mijinta ne fa taya zatayi sanadiyar mutuwar sa, haba Balkisu ki koyi iya magana dan ALLAH...." Pinky ta ce "to naga bata sonsa wai Uncle Deen take so shine take son hallaka shi..." Ummy ta ce "innalillahi wai meyasa hakane Aunty Pinky dan Allah ki bar mu da abinda yake damun mu..." Hajiya Kilishi ta ce "muyi Addu'a Allah ya bashi lafiya shine kawai, a yanzu dai babu wanda yasan gaibu sai ALLAH..." Suna cikin wannan halin sai ga Ammy ta fito daga part ɗinta tana sanye da hijab har ƙasi da carbi a hannunta, jin motsin mutane ne yasa ta fito domin ganin su waye ne saboda tasan gidan shuru yake ba kowa... Ƴar tinny ganin Ammy yasa ta rufa da gudu tana faɗin "Ammy nahh..." Ammy ta rungumi Ƴar tinny tana dariya, tayi matuƙar farin cikin ganin yaran gidan sosai. Ta ce "Auta ki ka gudu kika barni ko..." Ƴar tinny ta ce "Ammy wurin Mommyna naje.." Ammy ta ce "Ayyah fatan kin samu Mommy cikin ƙoshin lafiya ko?.." Ƴar tinny ta ce "ai tare muka zo da ita, gata can..." ta nuna ta da yatsa. Ammy bata yi tunanin har da uwar aka dawo ba domin bata lura da ita ba, haɗa ido suka yi Ammy tasau murmushi tare da nufan wurin tana riƙe da hannun Ƴar tinny, tana zuwa wurin ta durƙusa a gaban Hajiya Kilishi tana gaishe ta Ta ce "ina wuni Aunty, fatan kin iso lafiya..." Hajiya Kilishi fuska a sake ta ce "lafiya ƙalau Amaryar mu, nagode sosai kin riƙe mun yara cikin mutunci..." Ammy ta ce "ba komai wallahi, ai ƴaƴa na kowa ne..." ta cigaba da cewa "ashe kun zo Ni ban san yau zaku dawo ba ai da anyi muku tanadi na musamman..." Pinky tana farfara ido ta ce "an maida Auren Mommy da Abbah yanzu ta dawo gidan mijin ta..." Ammy cikin nuna farin ciki ta ce "Masha Allah, Allah mun gode maka, wallahi naji daɗin hakan sosai, duk da bai gaya mun ba amma nayi farin ciki..." Pinky ta ce "ai ba dole ne sai an gaya miki ba..." Hajiya Kilishi wani irin harara ta wurga wa Pinky tana faɗin "bana son iskanci fa, abokiyar ki ce ko kuma dake take maganar ta..." Pinky kawar da kanta gefe tayi tana tura baki... Hajiya Kilishi ta kalli Ammy tana murmushi ta ce "wallahi kuwa mu ma bazata akayi mana, ban san da Auren ba sai bayan an ɗaura..." Ammy ta ce "naso ya sanar mun dawowar ku ai, da an shirya muku girke-girke na musamman..." Hajiya Kilishi ta ce "ayya kar ki damu, mun zo mun tarar da wani tashin hankali, Roshan ba lafiya yanzu haka sun nufi hospital ciwon zuciyarsa ta tashi..." Ammy dafe ƙirji tayi tana faɗin "subhanallahi wallahi ban sani ba..." sai yanzu ta lura da Baiwar Allah dake ta kuka fuska tayi jawur, Ammy tayo kanta tana faɗin "Allah sarki kiyi haƙuri Daughter Insha Allahu zai samu sauƙi..." Wayar Ummy ce ta fara ringing tana duba wa taga Uncle Deen ne, ɗagawa tayi tare da yin sallama, Daga ɓangaren Razhdeen cewa yayi "wai meyasa Abbah baya picking call ɗina ne sannan ina ƙira Roshan shima baya ɗaga wa why?..." Ummy tana kuka ta ce "Uncle Deen su Abbah suna hospital ciwon heart ɗin Yaya Roshan ne ya tashi, sun tafi ko motsi baya iya yi sai aman jini yake..." Razhdeen cikin tashin hankali ya ce "whattt?..." daga nan ya katse wayar... Hajiya Kilishi ce ta ce "anya bamu bisu asibiti ba? muje mu gano ya ake ciki..." Ammy ta ce "gaskiya kam..." Har sun miƙe zasu fita sai ga ƙiran wayan Abbah ta wayar Ummy nan ma ɗagawa tayi tana faɗin "Abbah gamu nan zuwa..." Abbah ya ce "No ku zauna domin ko kun zo ba samun mu zaku yi ba, yanzu haka muna airport zamu fita ƙasar waje domin sai anyi masa aiki..." yana kaiwa nan shima ya katsar da ƙiran... Ummy ta ce "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un ciwon Yaya Roshan yayi tsanani dole sai anyi masa operation a heart ɗinsa, yanzu haka suna airport zasu fita ƙasar waje...." Baiwar ALLAH tana jin haka data fashe da wani irin marayan kuka ai kawai ta nufi bakin ƙofa da gudu ta fice.. Duk bayanta suka bi suna faɗin "ki dawo Daughter ina zaki je kuma..." Gudu na gaske take ta buɗe gate ɗin farko ta fice, tana zuwa gate na biyu nan ma ta buɗe ta wuce security da gudu, bayan ta suka bi suma suna faɗin "lafiya kuwa me yake faruwa ne..." ai kuwa nan da nan ta iso gate na uku wato babban gate nan ne bazata iya buɗe wa da kanta ba haka take bubbugawa tana ihu, har sauran security suka tarar da ita, sai ga su Hajiya Kilishi da Ammy da sauran suma sun iso ta, Sojojin dake waje jin yanda ake ta bubbuga gate yasa su buɗe wa suna faɗin "who's here?..." Ganin mutanen gidan ne yasa su cewa "meyasa ku ka fito?..." suka yi magana fuska a haɗe ba alamun annuri ga jajayen idanuwa... Ai kuwa Baiwar Allah bata tsaya sauraronsu ba ta zille ta tsakiyar su ta wuce, gudu take bana wasa ba, suma haka sojojin suka bita suna faɗin ta dakata amma ko sauraronsu bata yi ba, ai kuwa tana cikin wannan halin sai ta ƙara tarar da asalin babban gate ɗin gidan gaba ɗaya wanda daga shi shikenam sai outside, anan kuma sojojin dake wurin sun fi goma banda waɗanda suke ta waje, Baiwar Allah ganin bata da wata mafita kawai ta durƙusa gwiwowinta a wurin ta fara zabga uwar ihu, duk sojojin suka kewaye ta suna tambayar ta meke faruwa amma ta kasa yin magana sai cewa take "Ku barni naje na gano mijina dan Allah, inason ganawa da shi kafin su shiga jirgi, mijina nake son gani..." Wani soja ne ya ce mata "kiyi haƙuri ki koma ciki domin jirginsu har ya tashi sun tafi..." Su Hajiya Kilishi da Ammy kam tin a gate na biyu suka dakata domin ba ƙaramin gajiya sukayi ba, daƙer su Ummy suka ƙaraso wurin gate na huɗun yanda Baiwar Allah ta dakata suma ɗin ba ƙaramin gajiya suka sha ba.. Daƙer aka rarrashi Baiwar Allah ta haƙura suna shiga mota aka komar dasu can cikin gidan amma ta kasa dakatar da kukan.... A haka suka wuni har zuwa dare kowa a cikin damuwa yake, Misalin ƙarfe 9 na dare duk suna zazzaune a babban falo sai suka ji an turo ƙofar falo da ƙarfi, a matuƙar tsorace duk suka miƙe tsaye idonsu akan bakin ƙofa ganin mutum sangamgam gashi a kwance saman bayansa sai haki yake domin a ruɗe ya iso, kana ganinsa kasan ba'a cikin hayyacinsa yake ba, Ummy ce ta ƙaraso yanda yake tana faɗin "Uncle Deen..." ta ƙarasa tana kuka... Duk suma suka nufi yanda yake a tsaye suna ambatar sunansa, banda Baiwar Allah dake zaune tayi tagumi ko kallon yanda suke bata yi ba... Razhdeen ya ce "wani hospital suke?..." Ammy ta ce "sun fita ƙasar waje sai anyi masa aik..." Cikin tashin hankali Razhdeen ya ce "which country?..." Ammy ta kalli Ummy ta ce "wani ƙasar waje Abban ku ya ce miki sun je?.." Ummy ta ce "wallahi bai gaya mun ba..." Hajiya Kilishi ta ce "Razhdeen ka jira zuwa nan da kwana biyu zasu dawo...." bata ƙarasa maganar ba ya katse ta da cewa "i can't wait..." Haka yake zarya a cikin falon yana trying number Abbah amma baya shiga, duk wasu numbobin da yake tsammanin zai samu labarin su Abbah amma basa tafiya, cikin ɓacin rai da takaici haka yayi wurgi da wayarsa sai tin plasman, nan danan wayar ta fashe, hatta plasman ɗin ma ya samu rauni domin da iya ƙarfinsa ya wurga, durƙusawa yayi da gwiwowinsa yana cakurkuɗa sumar kansa lokaci guda ya zabga wani irin gigitaccen ihu, ai kuwa nan da nan kamar wani mahaukaci ya fara wargaza falon yaje ya janyo plasman yayi wurgi da shi, yaje ya buga glass dinning har sai da shima ya dagargaza shi, Baiwar Allah ganin zai iya ji mata rauni yasa ta tashi ba shiri taje ta ɓuya a bayan Ammy... Hajiya Kilishi ce tayi ƙarfin halin zuwa har yanda Razhdeen yake a durƙushe itama taje ta tsuguna tana ambatar sunansa a hankali "Razhdeen! please ka kwantar da hankalinka Roshan zai samu sauƙi, ai cuta ba mutuwa ba ne..." Razhdeen fuskar nan tayi jawur haɗi da idanuwansa haka ya ɗago su a shanye yana faɗin "ciwon nan yaushe zai warke na har abada? meyasa ciwon bazai dawo kaina ba?...." A zabure cikin tsawa ya ce "wai shin meye silar faruwar haka? waye yayi sanadiyar tashin ciwon sa? nasan haka kawai ciwon sa baya tashi sai da dalili, who....?..." Ita kan ta Hajiya Kilishi sai da ta tsorita da tsawar sa nan... Baiwar Allah haka take cakumar Ammy ta baya tana ɓuya zuciyar ta na harbawa da ƙarfin gaske... Baiwar ALLAH bata ankara ba taji an jawo ta tare da yin wurgi da ita a tsakiyar falon, a ruɗe ta ɗago tana kallon Razhdeen wanda yayo kanta yana faɗin "me kika aikata masa? nasan bakya ƙaunarsa fatan ki shine ki rabu da shi, kina son kashe mun ɗan uwa ko?..." ya cabko sumar kanta a fusace tare da ɗago da kanta yana kallon fuskar ta ya ce "kafin ki kashe mun twins wallahi sai kin rigashi tafiya lahira..." Gwara kanta yayi da jikin kujera ya nufi kitchen cikin ƙanƙanin lokaci ya fito hannunsa riƙe da wuƙa... Gaba ɗayan su zaro ido suka yi suna kallon Razhdeen, ganin ya fito yana riƙe da wuƙa, yana zuwa ya ɗaga hannunsa zai caka mata wuƙar ta zabga wani irin gigitaccen ihu, dai dai lokacin da Abbah ya shigo a ruɗe ya ambaci sunansa " *RAZHDEEN*" .. Dasauri ya ɗago tare da kallon yanda yaji an ƙira sunansa domin kunnensa sun jiyo masa sautin muryar Abbah ne.. Ammy kuwa tinda Razhdeen ya ɗaga wuƙa ta ƙanƙame idonta zuciyarta na bugun uku-uku... Hajiya Kilishi kam ja da baya tayi sauran kaɗan ta faɗi ta baya badan Pinky tayi saurin riƙe ta ba... Ummy itama ihu ta zabga tare da faɗin "Uncle Deen..." Abbah a ruɗe ya shigo falon tare da nufan yanda Razhdeen yake yana faɗin "da hankalin ka kuwa Razhdeen? shin ka haukace ne?..." Baiwar Allah tana kuka ta tashi da gudu ta nufi yanda sauran suke a tsaye Ammy tayi saurin rungumo ta tana rarrashinta... Abbah ya ce "kawo wuƙar nan, wa ya gaya maka itace silar kwanciyar sa jinya?..." Abbah ya karɓe wuƙar yana bubbugan kafaɗar sa cikin rarrashi... Razhdeen kuka ne ya kuɓuto masa Abbah yayi saurin rungumar sa tare da faɗin "ka kwantar da hankalinka Roshan ya farfaɗo cikin yardar Allah, domin har anyi masa aiki anyi treat ɗinsa sosai, kasan asibitin ƙasar Ethiopia muka je, su kuwa aikinsu ba wasa..." Razhdeen ya ɗago yana kallon Abbah sannan ya ce "yana ina Abbah? inason ganin twins ɗina..." Abbah ya ce "na baro shi acan cikin kulawa, gobe zan koma Insha Allahu..." Razhdeen ya ce "inason ganin shi..." Abbah ya ce "okay don't worry..." ya ciro wayar sa tare da dialing call wani ma'aikaci daga can hospital.... cikin ƙanƙanin lokaci aka ɗauka daman video call ne, Abbah ya ce "ina buƙatar ganin Roshan..." daman suna kusa da shi domin sune masu bashi tsaro, Roshan ne ya bayyana akan fuskar wayar yana kwance kan gado ya na sanye da oxygen, Abbah ya nuna wa Razhdeen yana faɗin "ka gànshi nan yana cikin kulawa..." Razhdeen ya karɓi wayar idonsa akan Roshan wanda eyes ɗinsa suke lumshe kamar mai yin bacci, ga yanda fuskar tayi fiyau ya ƙara yin kyau sosai... A hankali Razhdeen ya furta "My twins..." A ɓangaren Roshan kuwa jin an ambaci sunansa kamar muryar Razhdeen yasa shi buɗe eyes ɗinsa a hankali, yana kallon screen ɗin wayar dake yana sanye da oxygen ba halin yin magana sai ido, ga babu riga a jikinsa sai tin zuciyarsa alamun anyi aiki a wurin... Razhdeen murmushi yayi ya ce "Quick recovery my lovely twins..." Shima Roshan ɗaga masa kai yayi alamar amsawa, Abba ne ya karɓi wayar yana sanar da sauran ƴan gidan akan suma su zo su duba shi, kowa yazo ya duba shi banda Baiwar Allah dake tsaye gefe guda har yanzu ta kasa dawo wa hayyacinta, sai da Abbah yaje har yanda take ya nuna mata Roshan yana faɗin "Daughter kinga mijin nakin ..." Baiwar Allah idonta akan Roshan ga yanda hawaye yake faman zirya akan fuskarta, Razhdeen kuwa wani irin kallo yake watsa mata na ƙiyayya da tsana.... Washe gari da safe Abba ne zai koma Ethiopia wurin Roshan har Razhdeen ya shirya zasu tafi tare Abbah ya bashi haƙuri akan ya zauna da iyalansa domin suma bazasu juma ba... Razhdeen ya ce "Dad inason ganin twins..." Abbah ya ce "ka kwantar da hankalinka yanzu jikin yayi sauƙi Insha Allahu yana samun ɗan sauƙi zamu dawo..." Daƙer Abbah ya rarrashi Razhdeen ya zauna shi kuma Abbah ya nufi airport.... Razhdeen yana tsaye shima Ƴar Amana ta faɗo masa a rai domin jiya bai samu hankalin zuwa gidan sa, A lokacin ya shiga mota shima ya tafi.. Yana isa gidansa a falo ya tarar da wata zugegiyar yarinya tana zaune idonta akan plasman, a hankali ya ƙaraso yanda take tsaya kallonta yayi kamar bai santa ba domin ba ƙaramin chanza masa tayi ba, A hankali ya furta "Sarah..." waiwayo wa tayi ta tsaida idonta akansa, tana kallonsa ta zaro ido waje cike da mamaki ta miƙe tsaye bata san lokacin da ta rungume shi ba, shima rungumarta yayi sosai tare da ɗagata saman kafaɗar sa, ta ɗago suna fuskantar juna da murmushi akan fuskarta ya ce "my Sarah I missed you..." Haɗe rai tayi tana shirin yin kuka lokaci guda ta fara kai masa duka akan ƙirjinsa kuma yana ɗauke da ita yaƙi sauƙe ta, da haka ya haura da ita upstairs, daman ita kaɗai ce a gidan madam Blessing bata nan, Daga baya aka shigo da jakakkunan sa... Suna shiga ciki ya sauƙe ta akan gado fuska ɗauke da murmushi yana ja mata hanci, itama Ƴar Amana ba ƙaramin farin ciki ta shiga ba ganin Razhdeen domin tana muradin ganinsa, haka a wannan ranar suka sha soyayyar su Domin bazan ce hira ba🤨. ★★★★★★★ Bayan wata biyu... Ƙasar Jidderh. Ramlat da Maamie yanzu zaman gava suke ta zabgawa babu mai kula kowa sannan Ramlat ta haɗa kai da Indo Amaryar Mai martaba hatta girki tare suke yi, haka zasu zauna su sha hirar su amma da zarar Maamie ta shigo falon sai Ramlat ta bar wurin, Maamie tayi zaryar zuwa wurin bokan ta akan ta juyar da ƙwaƙwalwar Ramlat akan sai abun da ta ce mata amma har yanzu ba'ayi nasara ba, domin haɗewar da tayi da Indo yasa ta koyi yin ibada sosai, sallar dare da karatuttukan Alkur'ani da sauran litattafan addini, Mai martaba ya yi wa Ramlat faɗa akan ta dawo kula Yayarta amma fur taƙi sai cewa tayi "babu abinda take ƙaruwa da shi a wurin Maamie sai jahilci don haka yanzu ta dawo hannun Indo..." Abinda yasa Ramlat ta koma wurin Indo shine a lokacin da sukayi faɗa Maamie korar kare tayi wa Ramlat akan tabar gidanta tunda gidan mijinta ne... Shine dalilin da yasa Mai martaba ya ce ta zauna a part ɗin Indo, shi ya karɓe ta... Dalilin faɗansu kuwa shine Maamie ta dage akan sai Ramlat ta koma Nigeria taje tana shishshigewa Razhdeen ko hankalinsa zai karkata kanta kuma haka bokanta ya sanar mata akan dole sai Ramlat ta koma gidan Chief da zama, Ita kuma Ramlat ta ce "nan duniya bazata ƙara shiga shirgin Razhdeen ba domin bazai je ya hallaka ta ba ita kuwa maamie tana gidan mijinta, hakan yasa suka fara musayar yawu har Maamie tayi wa Ramlat dukan tsiya, saboda Ramlat taƙi amince da Razhdeen dalilin haka yasa Maamie ta kori Ramlat shi kuma Mai martaba ya ce ta dawo hannunsa sannan ya bayarta a Indo .... Kuma Ramlat tana mutunta Indo sosai daman can tanada hankali zugar Maamie ne yasa ta fita a ran kowa, Maamie ta shafa mata kashin kaji.... A wannan ranar ne Mai martaba ya gayyato Ramlat zuwa babban falonsa na masarauta akan zasu tattauna akan wani mahimmin magana, Ramlat ce a durƙushe a gaban Mai martaba tana sauraron abinda zai ce mata.. Mai martaba ne ya fara kora jawabinsa kamar haka "Ramlatu abinda nake so dake shine yanzu ke ba ƙaramar yarinya bace, kin mallaki hankalin kan ki kuma kinsan mai yake miki ciwo, Yayarki ta dage akan ki Auri Razhdeen ita damuwarta shine zaɓin ranta bawai zaɓinki ba, kuma har ga Allah yakamata ki so wanda yake sonki, duk da Razhdeen ɗa ne a wurina amma tunda baya sonki bana goyon bayan ki Aure shi duk da nasan ba Auren nakin zai yi ba, yanzu abinda nake so dake shine a cikin waɗanda suke sonki da Aure ki zaɓi mutum ɗaya wanda ya kwanta miki a rai..." Ramlat tayi shuru tana sauraronsa daga baya ta ce "Abul har cikin zuciyata ina son Yaya Roshan amma nasan shima ba sona yake ba dole zan haƙura acikin samari na zan zaɓi ɗaya, aban lokaci zuwa nan da kwana biyu Insha Allahu zan fitar..." Mai martaba ya ce "Masha Allah..." kafin ya ƙara furta wata magana yaji wayarsa tana ringing, dubawar da zai yi sai yaga number Abbah, ɗagawa yayi suka gaisa ya kuma tambaye shi jikin Roshan duk da har yanzu basu koma Nigeria ba, daga baya Abbah yake sanar masa cewa "mai martaba daman inason sanar maka da wani abun mamaki ne..." Mai martaba ya ce "lafiya dai ko?..." Abbah ya ce "yanzu haka muna Ethiopia gobe Insha Allahu zamu koma Nigeria jikin Roshan yayi sauƙi sosai an sallame mu, amma ya sanar mun cewa wai zai yi Aure na zaɓa masa matar da zai Aura..." Mai martaba ya ce "to ikon Allah ita kuma matar sa fa?..." Abbah ya ce "wallahi ya ce haka kawai yake son ƙara Aure, amma yace duk matar da muka zaɓa masa shi zai zauna da ita, shine nace bari na tambayeka ko ita Ramlatu tana sonsa ne ko kuma?..." Mai martaba ya ce "yanzu maganar da nake da ita kenan akan ta fitar da mijin Aure amma ta nuna mun cewa ita har cikin zuciyar ta tafi son Roshan..." Abbah ya ce "shikenam faɗuwa tazo dai dai da zama, Insha Allahu muna dawowa zamu samu zama, tinda shi Roshan halinka ya ɗauko marasa son zama da mace ɗaya..." Dariya Mai martaba yayi sannan ya ce "mai son zama da mace ɗaya yau dai an wayi gari mata biyu gare shi...". Murmushi Abbah yayi tare da katsar da wayar.... Mai martaba ya dubi Ramlatu sannan ya ce "kukan ki yazo ƙarshe Roshan yana son ƙara Aure shine Abbansa yake tambayar ki...." Ramlat ta ce "Abul kana nufin Roshan Ni zai Aura?..." Mai martaba ya jinjina kai yana ɗauke da murmushi... Ramlat har da sujjadar ta tsabar farin ciki, ta rinƙa hamdala tana gode wa ALLAH, tare da faɗin "Allah ya amshi addu'a ta, ashe addu'a tana da rana, tabbas na yadda cewa boka ko malami basu isa su tsara abinda Allah bai tsara ba...." Mai martaba shima fatan alkhairi yayi mata sannan ya bata umarni da ta tafi... Ramlat tana koma wa falo ta tarar da Indo da Maamie suna zaune a kujerar falo babu mai cewa kowa komai, da gudu Ramlat ta ƙarasa wurin Indo da gudu tana dariya tare da faɗin "Albishirin ki Aunty Aisha..." Indo ta ce "goro fari tass meya faru kamar anyi miki albishir da ƙasa mai tsarki..." Ramlat ta ce "Aunty Aisha Yaya Roshan zai ƙara Aure kuma Ni zai Aura, kuma Allah yasa naga tsinannen bokan da ya isa ya raba yaga ikon Allah, tinda Allah ne ya tsara babu mahalukin da ya isa ya raba..." ta ƙarasa maganar tana kallon Maamie wacce take ta kumbura, ita takaicin ta Ƙanwarta wacce suke uwa ɗaya uba ɗaya yau ta gujeta ta koma hannun kishiyar ta... Itama Indo ba ƙaramin farin ciki ta shiga ba tana faɗin "Masha Allah! Allah ya sanya alkhairi..." Maamie a fusace ta miƙe tare da jan wata doguwar tsuka ta haura saman upstairs can room ɗinta .... Ramlat ta ƙara volume da cewa "bin maganar bokaye da malamai dai rashin imani ne da jahilci..." Indo ta maki cinyarta tana girgiza mata kai alamar kar ta sake faɗin haka.... ★★★★★★★ Bayan isar su Abbah Nigeria a babban falon Abbah suka zauna kowa sai dai yaje can ya gaishe da Roshan domin baya son hayaniya shiyasa ya fake a part ɗin Abbah wanda ba kowa ne yake zuwa can ba... Razhdeen shima yazo duba twins ɗinsa duk da ya je har ƙasar Ethiopia duba shi, a falo suke zaune suna shan hirar su yanzu Roshan yayi garau, Daman ya dawo da niyar zai sallami Baiwar Allah sannan ya yi Auren sa yayi alƙawarin duk matar da aka zaɓa masa zai yi haƙuri ya zauna da ita indai tana son sa, domin bazai ƙara Auran wacce bata sonsa ba, kuma yayi tunani a yanzu abinda kake so ba shine alkhairi ba, sai wanda Allah ya zaɓa maka.... Suna zaune a falon Abbah shi da Razhdeen sai suka ji yo sallama, Roshan ne ya juya yana kallon bakin ƙofa ganin Baiwar Allah ce yasa shi kawar da kansa gefe tare da amsa sallama domin shi daman Razhdeen ko ɗagowa yayi ya kalleta ma baiyi ba balle ya amsa sallamar ta... Baiwar ALLAH ganin yanda Roshan ya sauya mata ne yasa ranta sosuwa, babu yanda ta iya haka ta durƙusa har ƙasi tana gaishe shi da jiki... Amsa mata yayi cikin sassanyar murya daga ƙarshe ya miƙe tsaye dai-dai lokacin da shima Razhdeen ya miƙe zai basu wuri. Roshan ya kalli Razhdeen sannan ya ce "ha'a My man ya dai ka tashi? nayi tunanin zaku ɗan fahimci juna ne...." Razhdeen fuska a haɗe ya ce "what do you mean?..." Roshan ya nuna Baiwar ALLAH yana ɗaga masa kai, Dogon tsuka Razhdeen ya ja sannan ya fice shima Roshan bin bayan Razhdeen yayi yana ƙiran sa da haka duk suka bar falon, sai iya ita kaɗai a falo itama daga baya ta tashi ta fice.... Bayan kwana sati da dawowar Roshan gyare-gyare aka fara yi a part ɗinsa gaba ɗaya part ɗin an sauya kalan pantin gidan, duk kayan furniture an chanchanza su saboda Abbah yaje har ƙasar Jidder sunyi magana sosai da mai martaba akan bikin, sannan suka yanke cewa next week za'a ɗaura Aure, Abbah ya ce duk wasu ɗawainiyan kayan ɗaki da sauran abubuwan duk ya ɗauke nauyinsa zai yi, Ramlat farin ciki kamar bazata mutu ba, amma sai dai Roshan bai ƙira wayanta ko sau ɗaya ba sannan idan ta ƙira baya ɗagawa, sai abun yake bata mamaki.... Pinky da Rukky suma murna Yaya Roshan zai ƙara Aure kuma Ramlat zai Aura daman ƙawarsu ce, kuma ba son Baiwar Allah daman suke ba... Ummy ce kawai ƴar ɗakin Baiwar ALLAH.. Gaba ɗaya Baiwar ALLAH ta kasa kwantar da hankalinta, duk abin duniya yabi ya ishe ta ga yanzu Roshan zai ƙara Aure, ita kaɗai tana kwance akan gadonta sai sharar kuka take ga wani irin kishi da yake damun ta... Tana cikin wannan halin taji ana knocking ƙofar bedroom ɗinta da sauri ta tashi tayi tunanin Roshan ne domin tinda ya dawo ko kallonta baya son yi balle ya saurare ta kuma tana muradin jin muryarsa... Tana buɗe ɗakin ta gànshi yana tsaye sai ƙare ta yake da kallo, ita kuma goge hawayen fuskarta ta soma yi tana sakin murmushi, ko kulata bai yi ba haka ya shige ciki ya zauna a bakin gado ta, kallonta ya yi sannan ya ce "zauna mana..." itama zama tayi a bakin gadon zuciyarta na bugun uku-uku domin tana fargaban jin abinda zai ce mata yanda taga fuskar sa nan babu annuri.... Cije lips ɗinsa na ƙasi yayi cikin takaici ya ce "a ranar da na kwanta rashin lafiya kinje room ɗina da buƙatunki na cewa na rubuta miki saki ko?, ban manta ba kuma ina sane da abun a raina domin ina jinya ma da abun nake kwana kuma take tashi, kuma nayi miki alƙawarin sai Razhdeen ya dawo kuma Alhamdulillah ranar ta zo, yau zan sauƙe nauyin dake kai na dalilin da yasa na nemi yin Aure kenam, zan rabu da matar da bata sona sannan zan Auri wacce take sona kuma take son kasancewa dani har ƙarshen rayuwar ta, Kiyi haƙuri Ammata sakamakon ɓata miki lokaci da nayi yanzu dai ganan takardar sakin ki da kike nema...." Ya zaro wata farar takarda ya miƙa mata, wani irin yawu Baiwar ALLAH ta haɗiya kamar wacce zata haɗiyi ranta, zuciyar ta wani irin ƙuna yake kamar wanda aka dasa mata garwashi, lokaci guda hankalinta ba ƙaramin tashi yayi ba.. Roshan ya ce "karɓi mana akwai ayyuka a gabana kinsan next week Aure na, ina buƙatar yin wasu shirye-shirye..." Baiwar Allah juyowa tayi tana kallon takardar hannun sa ga hawaye yaƙi tsayuwa mata, Hannu tasa ta karɓa ta ɗago tana kallonsa shima kallonta yake, idan ta akansa haka ta saita tsakiyar takardar ta ɓe ra shi gida biyu sannan ta ƙara yaga wa, haka ta yayyaga takardar idonta yayi jawur... Kallonta yake cike da mamaki, bayan ta kammala tayi saurin shige wa tsakiyar sa ta rungume shi sosai tana kuka tare da faɗin "Yaya Roshan bai kamata ka ɗaukar mun wannan hukunci ba, wallahi bazan taɓa saku wa ba ina nan tare da kai, tin kafin a kawo wannan lokacin nake nuna maka irin son da nake maka amma ka kasa fahimta ta, na koyi shiga ɗakin ka ina maka gyara saboda na nuna maka soyayyata amma ka dakatar da ni, duk wasu abubuwan da ya kamata ace ka fahimci ina sonka amma ka kasa fahimta, wallahi ina sonka Yaya Roshan har cikin zuciyata... ta ƙarasa maganar tare da fashewa da matsanancin kuka, Shima Roshan rungumar ta yayi sosai a jikinsa yana kuka domin ya fahimci halin da take ciki yanzu, shima ba son rabuwa yake da ita ba, gaba ɗaya kuka suke babu mai rarrashin kowa, sai daga baya Roshan ya ɗago ta yana faɗin "it's okay, yanzu na fahimce ki, amma meyasa kika kasa sanar mun tin lokacin, har kika cutar da zuciyar ki da kuma tawa? zurfin ciki ko? Ammata ina sonki sosai..." Itama ta ce "Nima haka Yaya Roshan..." Murmushi ya yi sannan ya ce "to maganar Aure na fa? zan iya dakatar wa tinda muradin raina ta dawo gare Ni...". Baiwar ALLAH ta ce "Yaya Roshan kowa yasan zakayi Aure, kuma Abbah da Uncle mai martaba sun tsayar da maganar bai kamata lokaci guda a watsa musu ƙasa a ido ba tinda kai ka buƙaci yin Auren..." Roshan ya ce "to ai bana so nayi miki kishiya...". Baiwar ALLAH ta ce "Abokiyar zama dai, baka ga Mommy da Ammy yanda suke zaman lafiya ba, kullum Abbah a cikin farin ciki yake sun haɗe kansu..." Roshan ya ce "shikenam amma kinsan dai kwanan nan zan koma ƙasar Egyph da aiki shekara biyun da aka yanke mun yayi zan koma, zan tafi da ɗaya daga cikin ku amma son samu ace ke kaɗai ce dani, gaskiya Ammata banji daɗin ƙin sanar mun da kika yi ba, har sai da na nemi Aure tukun zaki sanar mun abinda ke ranki why?..." Baiwar Allah ta ce "kayi haƙuri mijina nayi laifi sannan na aikata kuskure a yafe mun dan Allah..." Roshan ya ce "na yafe miki Ammata nah...." ya ƙarasa tare da ja mata hanci suka sake rungumar juna.... A wannan ranar basu rabu da juna ba a haka suka kwana ɗaki ɗaya sannan gado ɗaya amma kuma basu raya sunnah ba sakamakon wani ɗan matsala da aka samu, a wannan ranar Baiwar Allah ta tashi da period ɗinta, amma ba haka aka so ba.. Bayan kwana biyu biki yana ta matso wa Roshan kuma da Baiwar Allah soyayya tana ta ƙaruwa... Rana yata yau da sassafe Baiwar ALLAH tana shirya dinning shi kuma Roshan yana shan baccin safen sa bai samu tashi ba, Sai taji an yi knocking ƙofar falo, ɗaga kai tayi taga agogo yanzu ƙarfe 6 ne na safe a ranta ta ce "waye da sassafen nan..." zuwa tayi ta buɗe bayan taji an ɗan dakata da yin knocking, tana buɗe wa bata ga kowa ba sai wani baƙin leda da ta gani an ajiye a ƙasin ƙofar, lelleƙa ko ina tayi bata ga kowa ba daga baya ta ɗauki ledar ta koma ciki tare da rufe ƙofar... Pinky da Rukky ne suka ɓuya suna leƙenta har ta koma ciki bayan sun tabbatar ta ɗauki ledar amma ba haka suka so ba, sun so shi Roshan ne ya fito ya ɗauka, haka suka bar part ɗin suka koma can part ɗin su .... Baiwar Allah room ɗinta ta shiga ta zauna a bakin gado ta ciro abun leda taga wani ƙaton gift ata baya an rubuta "from Baiwar ALLAH..." Abun kuma sai ya ɗaure mata kai cike da mamaki take faɗin "Ni kuma?..." tana buɗe ledar jikin gift ɗin taga wani danƙareren abaya mai sheƙin gaske ga kuma wata takarda ta faɗo, cikin da mamaki ta ɗauka tareda buɗe takardar ta soma karanta wa kamar haka "Amincin Allah ya tabbata a gareki gimbiyar mata, kiyi haƙuri a bisa abubuwan da nake miki a cikin mutane nake nuna bana sonki, kema kinsan ina matuƙar ƙaunar ki domin bazan iya ɗanɗanar zuman ki na barki haka kawai ba, kina da zaƙin da ba ko wata mace ce take da shi ba, please haɗuwar mu a hotel ina jiranki da yamma, tinda Roshan ya dawo dole sai a hotel zamuna haɗuwa, kar ki bar Roshan ya sani domin ni da kaina zan zo na ɗauke ki ba tare da kowa ya sani ba, sannan ga saƙon Abayar da kika ce na kawo miki, ki kula mun da kan ki, *DAGA MASOYINKI RAZHDEEN TWINS ƊIN MIJINKI....* " A zabure Baiwar ALLAH ta miƙe tsaye hawaye duk ya wanke takardar domin tinda ta fara karanta wa take zubar da hawaye tsabar takaicin sharrin da aka ƙulla mata saboda a rabata da mijinta, cikin kuka take furta "innalillahi wa inna'ilaihi raju'un na shiga uku wannan wani irin ƙalubale nake fuskanta a rayuwa ta ce, haba Razhdeen ka rasa wani irin sharri zaka yi mun sai na zina? Ƙiyayyar da kai haka daman wayyo Allah nahh..." Da gudu ta shige toilet ta yayyaga takardar sannan ta sa a toilet tayi floshing ɗinsa, ta fito tana kuka ta ɗauki rigar da ledar gift ɗin ta zura a cikin baƙar ledar tana ciki, Ba shiri ta ɗauki mayafinta ta fice, ta yanke cewa zata je har gidan Razhdeen ta same shi, yau sai ya faɗa mata dalilin da yasa ya yi mata irin wannan sharrin sannan ta bashi rigar sa, har ta tsara irin cin mutuncin da zata yi masa, sai kuma yanzu take jin takaicin yaga takardar da tayi domin shi zai zamo mata shaida amma tayi hakan ne saboda gudun kar wani ya gani especially Roshan, duk da tasan Razhdeen yayi hakane saboda Roshan ya gani ya raba Auren su, wani irin ƙololuwar baƙin ciki ne a ranta, bata taɓa jin tsanar Razhdeen ba sai yau, zata je gidan Razhdeen ne ta dawo kafin Roshan ya farka daga bacci, Zuwa tayi ta samu Security ɗaya ta sanar masa cewa Roshan ne ya aike ta gidan twins ɗinsa ya kaita da mota, security jin yanda ta tsara masa zance yasa shi yadda ya ɗauke ta a mota suka tafi... Su kuwa Pinky da Rukky su suka zauna a ɗaki suka shirya rubutunsu saboda suna so su haɗa Roshan da Baiwar ALLAH rigima har su rabu, idan Roshan ya sake ta sun san Razhdeen ba Auranta zai yi ba, su suke kwata-kwata tabar gidan su ta je ta nemi iyayenta... Sunji haushi sosai da ba Roshan bane ya ɗauka domin in har shine dole zai sanar wa Abbah halin da ake ciki, shi kuwa Abbah zai kori Baiwar Allah ne bayan Roshan ya sake ta, shi kuma Razhdeen sai dai Abbah yayi fushi da shi na wani ɗan lokaci amma bai isa ya kore shi ba, duk abinda suka shirya ba hakan ne ya faru ba, amma zasu sake shirya wani plan ɗin a cewar su ..... Baiwar ALLAH bayan sun isa gidan Razhdeen security gidan ne ya buɗe musu suka shiga bayan yasan motar gidan Chief ne, A wurin parking aka Parker motar, tana riƙe da ledar tayi saurin fita da cikin motar ta nufi ƙofar babban falon gidan cikin fushi... Shi kuwa Razhdeen yana zaune a falo yana jiran fitowar Ƴar Amana zai kaita school domin yanzu tinda ya dawo yake kaita da kansa saboda tsaro, yanzu ya ga ba ƙaramar yarinya bace tana buƙatar tsaro domin ko security yanzu bai yadda da ya rinƙa kaita ba, ya kasa yadda shin kishinta yake ne ko kuma duk a cikin tsaro ne.... Ƴar Amana tana can room ɗinta tana ta faman gyare-gyare da shirye-shirye ta kammala saka uniform ɗinta tsab sai kallon mirror take domin tana so koda yaushe ta rinƙa burge Razhdeen, domin taga duk lokacin da suke tare yana rikice wa sosai a kanta ita kuma hakan burgeta yake domin ba ƙaramin jinsa take a ranta ba, wuni guda idan bata gan shi ba ta rinƙa shiga damuwa kenam, yanzu ko a makaranta bata nutsuwa tayi karatu sai fuskarsa ya rinƙa mata gizo, a koda yaushe tunaninsa take, tunani yaƙi ƙarewa ta rasa gane kanta, tana jin wani iri sosai akan sa, ko bacci zata yi sai ta daɗe tana kallon fuskar sa tukun ta iya komawa room ɗinta, (Baƙuwar lovayya kenam 😁😁) Tsayawa tayi a gaban mirror bayan ta gama shirinta tsab tana kallon kanta amma sai dai hankalinta ba'a kanta yake ba ta shiga dogon tunani kuma tunanin bazai wuce Razhdeen ɗin ba.... Baiwar ALLAH tsayawa tayi a bakin ƙofa tana bubbuga ƙafar falo da ƙarfin gaske domin a cikin ɓacin rai take bugawa tana zumuɗin yazo ya buɗe ta yi masa wankin babban bargo... Yana zaune haka yake jin bugun ƙofa kamar za'a ɓalla ƙofar tsabar ƙarfin bugun, Haka shima ya tashi a fusace yayi bakin ƙofar zai buɗe domin ya ci alwashin kowa waye zai ya zabge shi da mari indai ba Abbah ko Roshan ba..... *ALHAMDULILLAH* *ALHAMDULILLAH* *ALHAMDULILLAH* *ALHAMDULILLAH ALA KULLI HALI....* *ALLAH NA GODE MAKA DAKA KAWO MU ƘARSHE BOOK 2 NA LITTAFIN MY ENEMY WATO MAƘIYI NAH...* *MU HAƊU A LITTAFI NA 3 WATO MY ENEMY TAKUN ƘARSHE...* *WAƊANDA BASU BIYA KUƊIN BOOK 3 BA KU SAMU KU BIYA TINDA WURI...* *ASMA'U MUHAMMAD AUWAL* *9065443871, OPAY BANK* *PAYMENT 300₦...* *MA SHA ALLAH...*