[6/28, 1:46 PM] Sis Asma: BISMILLAH 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 1️⃣ Official By AsmaBaffa Copy By Zainab Butalawa Littafan Dana rubuta GASKIYA CE MARAICIN RAHMA MA'AIKACIYAR GOMNATI CIRANIN AMANA DUK INDA TA FADI KAMARSU CE DAYA KASUWANCI NA JIN DADI SABO ME MAGANI TUBABBIYA HADIN KAI RASHIN SA'A YAR KWANGILA ADDUAR KAWA TA GYARU GIDAN GWAURO/DAN NAZIA DANGIN RABI DUNIYATA AMNA MAFARKIN FARIDA WARE BAIKO..... INA GODIYA GA ALLAH DA YA BANI IKON FARA SABON NOVEL DINA KAMAR YANDA MUKA FARA LAFIYA ALLAH YASA MU GAMA LAFIYA TARE DA NI DA KU FANS ALLAH YA BAMU LAFIYA DA TSAWON RAI MAI AMFANI. WANNAN NOVEL BANA KUDI BANE DAN NISHADINKU FANS ALLAH YA BAR KAUNA DAN ALLAH A DINGA ZUBA SHARHI MUNA RAKASHEWA KAMAR YANDA AKA SABA🤣 WANDA SUKE GROUPS DINA DA WANDA NAKE GROUPS DINSU DA MA WANDA BAMA GROUP DAYA DUKKAN MASOYA NOVELS DINA INA MIKO GAISUWA INA DANNO MUKU GODIYA ME TARIN YAWA. WANDA NA BATAWA RAI A YAFE MIN NIMA DUK DA NASAN AN FITAR MIN DA NOVEL DIN KUDI NA YAFEWA KOWA 🤣 WARE BAIKO KACOKAN SADAURKARWA NE GA KAWATA 'YAR ARBARKA 🌹AIDA MAMAN TASNIM🌹 Page Dinku ne manya manya UMMI DEEJAT AUTA BESTYNBEELAT MAMAN SAMHA UMMUN SADDEEQ MOMCY MAMAN SADIQ FANCY HONEY RAHMA Gudu take Yaya Sulaiman na binta da katuwar bulala Yana tsula Mata,ihu take tana gudu cikin masifa Sulaiman yace wallahi kinji na rantse sai kinje makaranta,Yar iskar yarinya kullum sai da duka za a raka ki school,Bata fasa gudun ba shima Bai fasa binta Yana duka ba tana haki Hadi da ihu Tace wallahi bazan je ba nace muku bana son makaranta bana so amma baza ku saurareni ba,Ni da Makaranta bama mutunci ba kawaye bane bana sonta. Zanci ubanki cewar Sulaiman mutane suna ta kallonsu wurin 10am lokacin da a ake rakata da bulala makaranta in da sabo mutane sun Saba gani sabo da basa ganin budurwar a mai hankali shi yasa bata Shiga safgar kowa itama ba a kulata. Shaffff....Sulaiman ya shabda Mata bulala again a Haka ya rakata har School,tana wallahi bazan Gane komai ba,na fada muku bani da kwakwalwar karatu ko wanne iri ne,ni karatu baya shiga kwakwalwata bazan Gane ba tana fadan Haka har ta shiga aji,Malam Yana ciki ko kulashi Bata Yi ba ta fada ciki da kalar tafiyarta wata iri ta saki jiki wani shakwaf sannan ta rankwafa gashi ko Ina jefa kafarta take haka take tafiya ita ba tafiyar maza ba kuma baza ace tafiyar mata take yi ba babu Wani gwalli ko yanga. wuri ta samu ta zauna Jakarta tana saman cikinta hijab din ya karkace gefe,a jikin window ta zauna ta bude tare da zura kanta waje tana kallon compound,Malaman sun rigada sun Saba da halinta ba Wanda ke kulata Haka Malam ya gama darasinsa na mathematics Zai fita ta juyo ta zabga Tsaki tace Sannu sai kaje ka Nemo X din da kanka,kullum kuce 2a-2b = 2ab find x waye zai nemo muku x din ita x din gidan wa take tafiya? Kullum a,b,s suna aji suna hutawa a saman allo ita x da kullum ake cewa a nemota Ina take tafiya ko yawon banza ita take tafiya? Idan mutuniyar arziki ce tayi zamanta a aji mana mu dinga kallonta,Malamin Takaici yasa ko kulata baiyi ba ya fice abinsa,Yan aji suna ta Dariya Amma ko kallo Basu isheta ba sabo da bata da kawa a makarantar,A babban kauyen nasu ma kawarta Daya ce Sakina Shekarunsu Daya Amma Sakina ita bata tsaya Wasa ba da wuri ta gama karatun secondary tuni ta Kama sana'a,ita Kuwa Har yanzu a Ss3 take nna ta Mata repeating har takai shekara 21years yanzu a haka,sabo da garinsu babban Gari ne na gaske sai dai Kawai local government din nasu ba a cikin birni take ba a wajen garin Adamawa take shi yasa gaskiya da wayewarsu da ci gabansu sosai kamar ba Yan Kauye ba banbancinsu babu yawa Dana cikin birni. Yarinya ce karama Yar Fara kyakyawa a kalla zata Kai 6yrs,saman bene ta hauro da gudu sanye da Yar gown iya gwiwa me siririn Hannu pink cikin kyakyawan gidan take tafiya da gudu har ta shige wani lafiyayyen bedroom Wanda ya gaji da tsaruwa,tana Shiga tayi Sallama tare da cewa Yaya Nabeel Wai me ya sameka? kyakyawan Matashin Wanda aka Kira da Nabeel Amma kowa yafi saninsa da Lele sabo da Haka Iyayensa ke kiransa, juyi yayi a saman makeken bed dinsa ya sake kankame pillow tare da lumshe Ido ya bude tarrr saman Yar Yarinyar nan da alama kanwarsa ce Yace Fadila Jeki ki fadawa Mimi da Affa ki basu shawara kice ayi min aure na girma,na Gama degree Ina da aikinyi me Zan jira Kuma, Yar yarinya Bata ganewa ta kyalkyale da dariya tace Yawwa Yaya Nima daga Nan sai a hada da nawa, muyi tafiyar mu tare ko,wanda aka Kira da Yaya ya hade rai yace nine na girma ke yanzu me Kika sani,kunya nake ji kije ki fadawa Affa da Mimi karki sake kice Ni na turo ki shawara Kawai Zaki basu,kice ya kamata a Fadawa su Kawu tunda Kinga sune Yan Uwan Affa sune zasu wuce gaba sai kice a fada musu su wuce gaba ayi auren Nawa,Dariya Yarinyar Fadila tayi cikin maganarta da ba Wani fita take ba sabo da yarinya ce sosai tace Yaya Yar karama ce fa Ni ai Mimi baza su yarda ba Bazan sake kulaki ba Indai Baki je kin fada ba,Yarinyar Haka ta kwashe da gudu harda faduwa tana cewa Zan fada Yaya,part din Affa tayi ta Iske Mimi a can tana Shiga tace Affa Wai ayiwa Yaya Nabeel aure amma Ni dai bazan fada muku shi yace ba,gaskiya ba shine Yace ba,Dariya ta basu Affa Kuwa Nan take ya hade rai yace shine ya turo ki,na rasa me yake damun Yaron Nan Ina so yayi Ilimi me zurfi amma shi ba yaso shi yasa nace Yan Uwana su Kara maida shi kasar waje karatu Ya koma yayi Masters an waye yanzu bai Isa ba a sati biyu Inshaallah zai bar kasar Nan Zan samu yan Uwan nawa,har yaushe Nabeel ya girma,har yaushe ya San wani aure me ya sani yaro ayi Masa aure Dan Kawai yaga Allah ya hore mana,a banza Muka Tara kudin yasan wahalar da Muka Sha,Ina laifin ma idan ya Kai matakin masters ya gama a yaso aure da wuri yace ayi Masa amma ko Degree biyu babu comon degree da kowa Yana da shi.. Ka bi a hankali dan Allah ai ba haramun bane Kuma Nabeel ai ya Isa aure akan a barshi Haka ayi Masa Mana ai karatu baya Hana aure,29yrs fa Tunda kaga Yana Haka akwai dalili cewar Mimi,Affa da Bala'i ya tasowa wa Mimi ai dama ke kike lalata shi to wlh ko me zaiyi bai Isa na janye maganata ba karatu zaiyi Likita nake so ya zama,Taya za a kaishi waje a kashe kudi akan ya Zama likita Dan iskan yaron Nan sai yaje ya karanta Engineering ya dawo, Kuma nace Kar ya fara sana'a sabo da Matukar Yana Kama kudi bazai ilimin ba amma karshe sai gani nayi ya hada gwiya da turawa ya kawo motocin aikin titin kwalta gashi Nan yanzu yaje Yana ta faman tara kudi baya Jin magana ta,sai kyale kyale da Hawa motoci Yana Wasa da kudi ga Kanina can Yana Gina Masa tankasheshen asibiti,to idan ba nan ce hanyar cin Abincinsa bafa Haba Affan Fadila ku dinga rage wannan yahudancin Kar ya halakar da ku,Tsaki Yaja tare da furta sai Naga Wanda ya Isa nace ae yace a'a ya fice abinsa. A bakin kofar Palon ya Iske Lele ya Sha wata kafirar shadda milk ga Uwar suma taci kudi,Baffa ya kalle shi ya tabe baki yace Lele kalleka a haka Kamar wayayye Kamar Dan boko Kalar Ilimi, zubin Doctor Allah ya maka Amma ka Raina baiwarka ka zabi aure ka Isa kasa nayi abinda banyi Niyyar ba,ko da kudinka zakayi wallahi baka Isa ba bare ace Ni Zan maka dole, karatu zakayi kayi shiri Us zaka tafi verysoon bani da arzikin fitar da Kai waje nasan kana da kudi kaima Nabeel Allah ya baka amma Yan Uwana zasu yi,matsa ka bani waje shashasha ba abinda kuka sani sai aure kuyi ta yiwa Mata ciki kuna sakinsu to ba a gidana ba,yaro da Kai 29years kace Aure. Nabeel har Affa ya Gama Bai ce komai ba har ya tafi ya shiga shirgegiyar motarsa driver Yaja,Nabeel ciki ya Shiga wajen Mimi dinsa. Nabeel lele Yana shiga wajen Mimi kunya ta lullube shi sabo da Yana da kunya shi kam,Lele meke damunka haka?Kamar zai narke yace Mimi wlh aure nake so ki Masa magana please ni ko da wace ayi min tunda bani da budurwa, Fadila ya cafka yace haka nace kice ba shawara nace ki basu ba ya zuba Mata rankwashi ta saki ihu ya tashi ya fice abinsa cikin Fushi da zuciya shima wata damfareriyar mota ya Shiga wacce tafi ta Affa tsada da kyau gata Fara driver ya tukashi ya fita sabo da Yana da meeting,a gidan motoci ne sunfi shida Guda hudu na Nabeel ne,Daya ta Mimi,biyu na Affa. Sai dare Bayan Affan Nabeel Lele ya dawo ya huta yaci Abinci Mimi ta samu mijin nata cike da kwantar da Murya take Masa Nasiha tace Dan Allah Affan Fadila kayi Hakuri a fara yiwa Yaron Nan auren Nan tunda Yana so Kuma Allah ya hore mana tunda kaga ya matsa wlh akwai dalili Kar mu Bari ta sanadiyar Haka tun Yana Hakuri ya Gaza ya fada wani shashancin daban kasan dama fa ya koyo Shan giya a turai Yana Sha sama sama,yaran zamanin Nan sai Allah,Affa yace bashi da hankali Dan ubansa yayi iskancin Mana ai duniya ce,a'a kayi tunani a duba abin Nan fa,a Haka ta dinga lallaba Affa har ya Amince akan Nabeel ya Fadi wace yake so zai aura masa,ranar Nabeel murna kamar sai dai Kash bashi da wacce yaji Yana so a duniya Kuma babu macen da suke shiri da ita sai Basma Yar gidan Kanin Babansa sun danfi mutunci tunda Haka ne shi ba Wai auren soyayya zaiyi ba auren rage zafin sha'awa zai dinga manage da ita kafin Nan gaba ya samu nutsuwa ya Nemo wacce yake so a sake daura Masa aure ya rike Mata biyu,Nan take Kawai yace ai Basma yake so,Affa yaji Dadi Haka da ya sanarwa Kaninsa da Yan uwa sunyi murna Bayan kwanaki aka Kai kudi tare da yin baikwo... Nabeel sai murna yake zaiyi aure,Basma Kuwa ta Dade tana kaunar Nabeel tunaninta bazai so ta ba shi yasa tayi Shuru yanzu Kuwa ji take tafi ko wacce mace sa'a a duniya,sabo da samun Miji irin Nabeel sai yarinya me yawan azumi da Sallar dare,Haka Nabeel Kam yake nishadinsa Amma Bai damu da wata Amarya ba a Haka gani yake wani mugun so ne ya kamashi. Yana gida abokinsa Ammar ya shigo yace Wai da gaske auren za ayi maka? Maganar da na fada maka a waya baka yarda ba kenan? No Lele yanzu dama soyayya kake? Baka da hankali ammar baka San love ba,Kuma Nifa kasan Sha'awa ce dani,lafiya tayi min yawa badan ma Ina mafarkin na dan rage ba ai da tuni sai ta Allah,ayi min auren yafi tun kafin na Fara barbare Yaran wasu. Wai Affa Kuma a kaini turai kasan Allah bazan iya tsallakewa ba Ina ganin turawa da Mata kyawawa wallahi sai na Yi wannan Karon,Dariya sukayi Ammar yace tun baka San hanyar wajen ba kenan Ina ga ka dandana,Lele yace uban waye yace Zan kasa Gane Hanya,gashi Nan muna ganin jarirai Mata ba Kaya idan ana musu wanka nasan hanya Ina zuwa nasan inda Zan bi. Ammar Yana ta Dariya yace Ni Kuwa kyankyamin Mata nake idan na tuna ta Nan suke jinin haila sai naji Takaici,Dariya Nabeel Lele yayi kyawawan hakoransa Suka bayanna,ya shafa dogon hancinsa tare da motsa Dan madaidaicin lips dinsa jajaye dasu abinka da fari yace Ni bana kyankyami wlh,Nifa jinin ma birgeni Ni yake musamman idan na tuna ta hanyar da yake Fitowa sai Naga shi Kam jinin yafi kowa sa'a a duniya duk wata zai ta sintiri a wajen,Da nine ai ba Haka ba,Ni so nake ma naji mace tanayin period sai naji wani kaunarta Naga tana wani birgeni har wani kyau suke karawa,Ammar ya dinga dariya harda buga kafa,inda Nabeel yayi sa'a akwai addini da tsoron Allah kowa yasan wannan duk maganarsa a wajen abokinsa yake Masa Wasa amma Mata ma basu isheshi kallo ba. Ammar yace mamaki kake bani Nabeel yanda kake da tsananin kyau ga class jibi yanda Mata ke son alaka da Kai,Kai da zaka ji Mata Basu dameka ba sai kafi kowa son Mata Kuma ka bani kunya,Nifa ba wali bane Dan uwarka Ammar ni Kawai Ina so a min aure idan ba Haka ba wlh na Fara bin mata Ina da kudi ka sani,Allah ya tsare cewar Ammar, Yar hirar da sukayi da Ammar shi Nabeel tuni ya fada wani yanayi,suna Haka sai ga Yar school din su Nabeel tazo Meena,Tare sukayi secondary da su Nabeel tana mugun kaunar Nabeel,Meena kyakyawa ce baka da ita Masha Allah,tana zuwa wurin Mimi ta wuce Suka gaisa sannan ta fake da gaisar da Mimi tazo amma a zahiri wajen Lele take zuwa. Sai da Mimi tace Bari a Kira Miki shi,Meena tace da kin barshi ma,Haba ai ko gaisawa sai kuyi a waya ta Kira Lele kazo ga Meena tazo,Takaici ya lullube Nabeel Haka Kawai shi baya son Ana Shiga harkarsa Matukar ba shine ya shiga taka ba,Tsaki Yaja tare da mikewa Yana gyara wandonsa Jean Dake Shirin faduwa kasa sabo da gayu,Ammar yace ba sai kaje ba ku gaisa ko Dan Kugunta ta goga maka ka samu yau ka samu bacci,Allah ya kiyaye ance ma Dan Iska ne Ni Dan Ina son Abu sai na lalata kaina,Haka yaje suka gaisa da Meena ba sakin Fuska ko kadan. Daga lecture ta fito a birnin Abuja,Mota ce tazo ta dauketa me kyau, har taje gidansu Ranta a bace yake,cike take da Jin haushin Dan class dinsu Nabeel Wanda yanzu Haka da shi suke zana final year exam,ta kulle a Ranta yau sai taci Masa mutunci,Dan Kawai tace Yana Dan birgeta shine zai zageta a wajen kawayenta shi yasa Tace to wlh yau dole na nuna Masa ni waken suya ce na gagari kwari,Wayarta me tsada ta jawo tare zagawa bayan garden inda babu Wanda zai ji me zata ce,a zuciye ta shiga Neman Number Nabeel Amma bata samu ba,Nan take ta Kira kawarta bata jira me zata ce ba tace Turo min number Nabeel please,Maryam tace Allah yasa nima Ina da ita,ai Kuwa idan duk Kano Zaki zage sai kin Nemo number Nabeel a garin Nan.. Dariya tayi tare da kashe wayar tasan Halin kawarta Kawai data tashi turo mata number Nabeel sai ta canja number karshe ta turo mata da wrong number, bata sani ba kawai ta Danna Kira sai da ta Kira sau biyu Bai daga ba kafin daga bisani aka kashe Kiran aka kira ta back,Tsaki taja tace karyar banza wai su masu kudi. Gabanta ne ya yanke ya Fadi Jin wata Murya me Dadi da taushi Sam ba irin muryar Nabeel din Data sani ba,Tsaki taja cike da ruwan masifa tace Malam ka Bude Murya aikin banza Dan Iyayi Kai har ka kana da damar da zageni waye Kai,Hey pls who are you? Basma ce dan iyayenka,Dan kaga Family Dinku masu kudi ne Kai kana da damar kace Wai kaga Alama sonka nakeyi,me zanyi da Kai samari Nawa ne ke bi na,daga yabonka sai kace sonka nakeyi harda cewa me zaka ci Dani talakawa ai shi yasa Naga Kai Ubanka da arziki aka haife shi,waye pls aka sake cewa ta waya,cike da bala'i tace nace Basma ce,what? Na cikin Wayar ya furta shima,shima yace Basma Ni Nabeel kike zagi Haka? Ita ma Basma bata gane ba Nabeel din da take Nema bane, tace ae an zageka Kai din banza akan na yabe ka sai aka ce sonka nakeyi Kai ka Isa na soka waye Kai,yaro da Kai me zaka tsinana min mutumin da ko tsaiwar minti goma baka iyawa jiki duk a lankwashe Kamar Dan daudu banza gara ajawo kit ta kashe Wayarta. Nabeel ransa ya baci shi Basma zata zaga sabo da Yace zai aure ta ai Kuwa ko sama da kasa zata hade ya fasa wlh,Fitowa yayi a fusace sai dakin Affansa Yana zuwa yace Affa na fasa auren bana kaunar Basma yanzu ko kadan Kawai a ware baikon da aka Yi wlh ko Zan mutu bazan auri Basma ba,Affa dama dan Nabeel ya nace ne Amma shi Bai son auren ga Basma Yar Kaninsa ce sai yace,Kai kace kana so ka sani bazan iya tunkarar Yan Uwana da Maganar ba kaje ka samu shi Kawunku da kanka ka fada Masa dalilinka ba ruwana Nabeel yace ai Kuwa zanje yau sai an ware baiko Tunda Basma ta Kira classmate Dinta Nabeel taci mutuncinsa sai washe gari tana zuwa makaranta suka ga Nabeel shi da abokansa su Uku suna hira,tare suke da friends Dinta Yana ganinta ya yatsina kyakyawar bakar fuskarsa Nabeel din Basma na school wankan tarwada ne kyakyawa,Kawarta Maryam ce ta Masa magana Malam Nabeel Baki ya washe tare da furta Yan Mata sai kace wani Babban mutum haushi ya bawa Basma ta Masa wani kallon banza sai Kuwa yace Basma ba magana? Ko kallonsu Bata Yi ba,su Nabeel suna tafiya ta kalli kawayenta tace shege ai yaci zagi na Gama da shi nayi Masa fata fata,mamaki sukeyi yanda take da shariya ba komai take tsayawa ta saurara ba amma akan Nabeel ta zauna tana masifa. Maryam ta kalleta da zolaya tace Kuma Nabeel din shine Wanda Kika Kir....kafin ta rufe Baki tace shine Mana harda wani makale murya Yana min yanga Ni Kuwa na Masa gaja gaja na kashe wayata Wai harda tambaya what...Basma ni Nabeel kike zagi? Ni Kuwa zagi ta Uwa ta uba na Masa shine fa Kika ga ya tsorata yanzu Yana washe min Baki,kin San ni ban iya Fushi,Maryam tana ta mamaki sabo da ita tasan tabbas ta canja number Daya a number din Nabeel amma gashi Basma ta tabbatar ta samu Nabeel a waya, tunanin ko dai data ji Wrong number ne ta nemo wajen wasu Haka Maryam ta bawa kanta amsa. Basma tace ai Nabeel ya shiga Uku Dani ya tsokano tsuliyar dodo yanzu Bari na kirashi da Daya layin Nawa na Raina Masa wayo,Wayarta ta zaro tare da Nemo number data Kira jiya,sai data Yi bugu biyu kafin a dauka sai taji an kashe an Kirata back,muryar Nan me Dadi ta sake dukanta Tace Nabeel ka daina wannan Iyayin kasanni na Sanka Ni ba birgeni kakeyi da wannan muryar ba ka fito min a mutum,Nabeel ya Gane muryarta Kawai Yaja Tsaki tare da kashe wayarsa lokacin Yana tare da ma'aikatansa Yana musu bayani akan wani aiki, Engineer kenan. Adamawa state matashiyar budurwar ce ta sake fitowa sanye da uniform maroon and white wow kyakyawa da ita karshe,skin dinta chocolate me haske baza kace Fara Kar ba Kuma baza kace da ita baka ba,yanayin dirinta gwanin birgewa Haka fuskarta da komai nata me kyau ne, da kuka ta fito daga Dan kyakyawan gidansu na bulon siminti,kaf kauyen ba gida me kyan nasu gidansu na bulon siminti a sumulmule yasha paint green, ciki harda tiles zata Kai 19yrs wuyan Hijab dinta ya karkace Bari daya,jakar makarantar nata ta ratayota ta Gaban Dan guntun hijab din nata,tana gudu tana kuka matashin yayanta Yana binta da bulala suna ta gudu a Gari ana kallonsu. Tana gudu tana magana wallahi bazan je makaranta ba,nace muku bana son makaranta Ni,ai ba Dole bane,ko dole sai anyi karatu ake samun ci gaba,Wanda yake binta da bulala yace wallahi dole sai kinje makaranta Dan ubanki,Ni bazan je ba wlh ka rabu Dani bana son makaranta Ni Kuma ko ka kaini sai na gudo,saurayin Allah ya bashi sa'a ya cafketa ya dinga tsula Mata bulala tana ihu amma tana kuka tana cewa bazan je makaranta ba Ni bana son makarantar ta sake kwashewa da gudu ya bita Ana ta kallonsu dama an Saba ganinsu kullum da safe sai ya rakota da gudu suyi ta gudu Amma baza taje ba,sai da ya Rakata har makaranta da bulala suna gudu tana ihu sannan ya dawo gida Yana masifa. Wani dattijo da matarsa suna zaune a tsakar gida Yana bala'i Papa wannan Yarinyar dole sai an dau mataki a kanta,ka duba girmanta mate dinta duk wasu sun Gama secondary da 3yrs Amma ita 21yrs har yanzu tana ss3 sabo da rashin zuwa makaranta gashi har yanzu Bata iya karatu da rubutu ba ko sunanta Bata iya rubutawa ba. Sai lokacin Wanda aka Kira da Papa yayi magana yace Abita a hankali Dan Allah kaga bani na haifeta ba Yar Dan Uwa na ce marainiya ce Bata da Uwa da uba nine komai nata bana so ta kalle mu a wasu marasa Imani a kanta,a bita a hankali,Matar Papa Kuwa tana gefe Baki ta tabe Tace ai Indai Hamida ce zaku gaji wannan Yarinyar karshe ta lalace Matukar Baku bi shawarar Dana Baku ba to wallahi zaku Yi kuka,ku samu wani dattijo ku aurawa shegiya. Tsawa Papa ya daka Mata Haba Mero yanzu idan yarki ce Zaki so Haka ta faru? to saurara kiji Hamida amana ce a wajena Kuma na dauka sai na sauke amana,dama ke kike gida ke ya Dace ki kula da tarbiyyarta amma bakya Yi,baki Mero ta tabe tace to shike Nan zamu gani ai,Tsaki Yaja ya fice abinsa da takaicin mero sabo da Sam ba ruwanta da Hamida tsakaninsu sai dai ta kallo duk da cewa bata takura mata. Hamida Kuwa ko taje makarantar bata saurarar komai a makaranta kawarta guda Daya ce Sakina Kuma Sakina ita tuni ta gama secondary babarta take rakawa kasuwa tallan Masara dafaffiya. Washe Gari da safe Haka Dan gidan papa Kanin baban Hamida kenan Wanda ke dukanta sai taje makaranta Sulaiman ya sake rakota da bulala suna gudu tana gudu tana bana son makaranta Ni bana son makaranta bazan je ba bana so,Yana dukanta tana gudu a Haka ya Rakata makaranta,Amma dukan ko a jikin Hamida,duk Sanda aka tashe su daga makaranta sai dai ta tsaya a Hanya tayi ta Wasa kafin tazo gida lokacin Islamiyya yayi Haka Islamiyya ma Sai ansha fama ake rakata da bulala itama ba abinda ta sani,Bata Jin magana. Yau ba school Sunday Hamida ta shigo sanye da Riga da skert na shadda sun Mata kadan ma amma haka take sa abinta tana tafiya a hankali ta daga kai sama hannayenta suna harde a bayanta tana kalle kalle tana wani taku na gadara,Daga gidan ubanwa kike? Wacce suke Kira da Ummi ta tambaya,ko gazau Hamida bata Yi ba Kuma bata fasa kalle kallenta ba,dake nake Hamida daga Ina kike? Har gaban Ummi Hamida ta karaso tare da furta Ummi akwai Kuwa abinci,harara Ummi ta zuba Mata tare da furta ba abinda Kika sani sai yawon banza da tsayawa Kika Yi Kika koyi karatu da rubutu ya fiye Miki amma even ordinary Hami baki iya rubutawa ba bare a kai ga kin rubuta Hamida,daurin zaninta Ummi ta gyara tace ya kamata kiwa kanki fada,Hamida kisan me kike duk garin Nan a mahaukaciya suke kallonki ba a Miki kallon me hankali. Dan baki Hamida ta turo tace Wai me Kika dafa ne Aunty dake ita in taga Dama Aunty take Kiran Ummi shi Kuma Papa tace uncle,Tsaki Ummi taja tayi tafiyarta abinta. Kitchen Hamida ta wuce tare da eban abinci taci ta cika cikinta sannan ta kalli Ummi dake tace gasarar Koko tace ni Yar kasuwa nake so na Zama bana son boko bana kaunarsa ki fadawa mijinki,ko kulata Ummi Bata Yi ba itama Hamida ficewa tayi tana fito fiii fiiiii...sai kace tantiran maza. Papa Yana shigowa Ummi ta kalli inda yake Jin Yana tambayar Ina Hamida ta Shiga,Baki Ummi ta bude tace wallahi kaine farkon lalata Hamida kana tunanin hakan gata kake Mata sabo da Kar ka takura mata bata da Iyaye sun rasu sannan Yar dan uwanka ce,abinda take so shi takeyi,abincin da take so shi take ci,gaba dayanmu koko muke Sha Amma Hamida shayi lafiyayye kake siya Mata kullum,Bata San babu ba,sutura me tsada ita kadai kake siya mata,duk yaranka na cikinka makarantar Gomnati sukayi amma Hamida makarantar kudi takeyi me tsada,bata cin tuwo sai abinda take so,Ni ban taba ganin dan an mutu an barwa mutum ya ba Yana Haka sai a kanka,kowa bai iya tarbiya ba sai Kai ai shike Nan gaka ga Hamida nan. Tsaki Papa ya ja tare da furta kayan sawar Hamida kala Nawa ne kwata kwata? Sannan atamfar dubu uku sune masu tsada,ke da kike mace uwa kece me Basu tarbiyya ai yaranki kadai Kika sani,Hamida bakya sa Ido akanta ke wanne kokari Kika Yi sai burinki na aurawa ko tsoho ne Hamida,ko wanne Hali ta shiga ba ruwanki,yo me ya ruwana tunda Yarinyar mahaukaciya ce bata san ciwon kanta ba cewar Ummi,Tsaki Papa Yaja ya wuce ciki Kawai sabo da Yana da sanyin hali. Ayi Hakuri da typing Error Basma ya kano ce na manta nasa Abuja bazan iya komawa baya ba fans. AsmaBaffa [6/28, 1:46 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 2 Official By AsmaBaffa Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne ASMAU SANI LATEEPHA RUKEY MUAZ NICE GIRL HAJIYA ABOU KHADIJA DANDUME KHADIJA A HAMZA HADIZA MUKHTAR Basma Hamza Kabir shine cikakken sunan Basma,Yan asalin maiduguri ne kanuri,su biyu iyayenta Suka Haifa babbar yayarta Aunty Maryam sai ita, bayan sun taso cikin rufin asiri domin babansu babban likita ne sunyi karatun Boko sosai Yan Boko ne na gaske Aunty Maryam tana Gama degree ta samu mijinta Salisu,Salisu shima ya Gama degree baida burin aikin Gomnati ya samu Aiki a company na MTN Kano sabo da burinsa siyasa Kuma a cikinta yake Allah ya hada su da Maryam lokacin Maryam ta samu Aiki a ministry of health sannan aka musu aure. Ana auren Maryam ba dadewa babansu ya rasu,bayan ya rasu da wata Daya Mamansu ciwon zuciya ya kamata itama ta bishi ya Zama sai Basma Kawai ganin Haka Yan Uwa suna son daukan Basma Salisu yace ta tattaro ta dawo kano gidansa zai hada ya rike ta zauna a hannun yayarta Maryam. A Haka Basma tana zaune har ta Gama secondary school ta shiga University lokacin Maryam tana da yaranta maza biyu mace Daya,a yanzu Basma tana final year a University zasu zana final exam. Basma abinda taga Dama shi takeyi Bata da takura ko wani Abu tana da ilimin addini sosai,Bata da wani Hali na banza sai son Wanda ya waye sannan me kudi,Bata da burin da wuce ta samu saurayi matashi kyakyawa me kudi Dan gayu me ilimin Boko,tana da kyankyamin Wanda Bai waye ba,ko baka da kudi Matukar ka waye to Basma zata je da kai. Basma kyakyawace Fara tas Yar gata da mugun tsayi da kaurinta,tana da jsauray dai ita ba laifi sosai ta hadu ga iya daukan wanka ko a school maza na gasar kula Basma,Bata da kunyar zagin mutum duk girmansa Amma sai ka shiga gonarta. Bangaren samarin Basma Kuwa duk Wanda yace Yana sonta Matukar Yana da Mata sai ta Masa karya zata aure shi Amma sai ya saki matarsa ta gida,wasu shashashun sai su Saki kuma sai Taki aurensu,akwai mazan da yawa an musu baiko wasu an sa Rana Amma Indai Basma ta sani Kuma suna alaka da Angon sai tayi amfani da kyawunta wajen wasu Wanda Basu da hankali tasa an fasa auren sun dawo suna Sonta karshe ta Kori mutum. Gashi Kamar tsafi kowa Sonta yake Yi akanta sai mutum ya fasa auren budurwarsa sai ya sheka yaga ba kwaya,Basma Kenan. Nabeel number da Basma ke kiransa tana zaginsa ya duba a Whatsapp yaga dalleliyar budurwa Yar gayu ita ma Basma sunanta sai dai ita tasa Real Basma,ita Kuma Basma Yar uwarsa Basma luv tasa Kawai,Takaici da nadama ta Kama Nabeel yanda anyi magana zai auri Yar uwarsa ba bincike ba komai yace ya fasa,Tsaki Yaja yasan da kunya ya koma yace ga Matsalar iyayensu zafi ne dasu gaba daya,Magana yayiwa Basma ta Whatsapp dama tayi saving number tana Hawa Online taga wani hadadden guy ta zaci wani ruwa biyu ne ko Dan wani Kasa ne,Nan take ta fara kaunarsa taga mijin da take mafarkin samu fadawa tayi a saman bed ta fara birgimar murna. Aji ta ja sosai Bata kula Nabeel a time din ba,Lele uaga Shuru sai shima ya share da kanta ta dawo ta Masa magana Suka Fara chat Nan ta Gane tabbas ba Nabeel din school dinsu bane ,a hankali a hankali Suka Fara mutunci Suka fada soyayya da gaske takanas yaje har kano wajen Basma ta gama tafiya da Nabeel,zuwa Daya biyu yace za a kawo kudin aure,Haka ya dawo ya tasa Affa a gaba sai da aka Kai kudin aure ana bincike sai aka gano ashe ma Maman su Basma data rasu kawar Mimi ce sosai sun Sha zuwa Makkah tare a can Suka hadu, Nan aka Sa rana aka yanke biki Nan da wata tara Basma ta zarma da yawa sai love duk ta zake hakan yasa duk ta fatattaki samarinta sai iya Nabeel Wanda zata aura Kawai suna ta soyayya,Mimi suna ta zumunci da Dangin Basma,Wannan yasa Basma har gidan su Nabeel take zuwa ta danyi sati daya sabo da Mimi ke tursasata sai tazo,suna zuba love Nabeel ya samu babbar kwangilar aikin titi a Adamawa state a kalla sai ya kwashe wata hudu a can idan aikin Bai gamu ba sai ya Kai 5mnths. Mimi ya samu a part dinsa yace Mimi banji dadin saka ranar auren Nawa har Nan da wata tara ba kusan 1year fa Mimi su Affa sunki ganewa sabo da bai so nayi auren sai karatu,Mimi danta ta kalla tace Nabeel ka rufawa kanka asiri ka rufa min kaga a hakan ma da kyar ya amince kayi auren to kayi Hakuri a haka 9mnths kamar yau ne fa,ko wata Matsalar ce? Kunya yaji yace ba komai to Mimi Allah ya kaimu,yanda kake addininka ka dage na Sanka ba Wasa,alcohol naga ka daina Sha ko? Mimi sai fa nayi wata uku ma ban Sha ba sabo da tana sawa Ina son aure Kuma Kinga Affa ba Yi min zaiyi ba shi yasa na hakura da Sha sai jefi jefi shima Inshaallah Zan daina gaba daya,yawwa Lele ai nasanka kana da tsoron Allah to ka Kara akan na da, Inshaallah Mimi ya furta tare da gyara kwanciyarsa saman kujera Yana latsa wayarsa. Affa ne ya shigo tare da gallawa Nabeel harara yace kayi asara wallahi yaushe zaka tafi Adamawan? Gobe Inshaallah cewar Lele,baki Affa ya tabe yace Saura ka gano wata a can kace a fasa da wannan Dan iskan yaro marar Jin magana,Mimi tace wallahi ka daina iskance min yaro akan yaki komawa turai karatu so kake wani bala'in ya fada Masa kullum kana zaginsa kana ce Masa Dan Iska,Tsaki Affa ya ja tare da haurawa sama ya bar Mimi rai bace,Fadila ce ta dawo daga school da gudu ta Fado palon tare da fadawa jikin Nabeel Yana Mata oyoyo tayi wajen Nanny ta barsu ko Mimi bata kula ba. Nabeel uban wanka ya hada komai tsab da sabuwar motarsa fara ya tafi wacce ya siyeta da kudinsa duk da cewa motarsa ba Daya ba,a wani Hotel karami kusa da kauyen yayi masauki,Yana can suna ta Aiki a wani babban titi Wanda ya ratsa ta wani kauye wannan titin yakewa Aiki da motocinsa yaransa ma'aikata suna ta fama shi Kuwa Yana mota Yana Shan ac,Sam Nabeel baison wahala ko kadan kana ganinsa kasan Yana hutawa. Fitowa yayi daga motar hannunsa dauke da ruwan roba yasha farar shadda Yar ubansu yayi mugun kyau abinka da me kyau ya Gama hadewa kana ganinsa ba sai an fada ma ba kasan shine ogan,Hamida ce da gudu ta fito misalin 10am da uniform dinta hijab din ya karkace gefe tana gudu har kullum Sulaiman Yana binta da bulala Yana dukanta Yana dole makaranta tana wlh Ni baza Ni ba kome za ayi nace muku bana son karatu Ana ta kallonsu ta ci birki a Gaban motocin aikin Nabeel Tace wallahi sai dai kashe shi Ni ba inda Zan Dara daga Nan tana kumbura baki da sangarta,Sulaiman yana hankadata amma Taki tafiya,Nabeel Yana kallon ikon Allah baiyi Niyyar magana ba sabo da gadararsa,da kyar dai ya daga musu Hannu yace hey...hey Mene ne? Sulaiman da huci yace kana gani bawan Allah Wai Kamar wannan ta kusa shekara ashirin da daya amma baza taje makaranta ba har yanzu tana ta maimaita ss3 mate dinta duk sunyi nisa a university wasu sunyi aure to wallahi billahillahillazi la Ila ha illahuwa kaji rantsuwar musulmi sai taje school dole bazan taba bari ta lalace ba,Yar iskar yarinya Sulaiman ya sake tsulawa Hamida bulala ta saki Kara sannan ta daka yatsa sama tana girgigaza da kirji Tace to Ni Kuma na rantse da ubangin alarshi bazan je ba,Haka Kawai nace Ni bazanyi boko ba bana so bana so dole ne bazanje ba ni kam. Sulaiman zuciya ta hangulo Masa ya fara dukan Hamida,Nabeel ne da muryarsa me dadin sauraro yace ya Isa tare da rike Sulaiman yace ai ba a duka,duka ai baya gyara mutum lallabata zakuyi,kafin ya rufe Baki Sulaiman yace wannan Yar iskar ce zata ji lallaba? Calm down karka sake dukanta Ni Zan Mata magana zata je school, Sulaiman yace ka tabbata? Nabeel yace yes of course,Zan gani ya koma gefe can,Nabeel ya danyi murmushinsa me Kayatarwa tare da kallon Sulaiman ya Dan daga murya yandazai ji shi ya furta don't worry I will talk to her. Sulaiman a ransa yace kayi ma gani,Nabeel a nutse Yana birnancinsa yace me yasa bakya son zuwa school? Hamida tana Wasa da Hijab dinta cike da tabara tace wallahi Ni bana son makaranta,Allah bai sa min Sonta ba,ba kawaye bane ni da Makaranta na tsani karatu,ka ganni dakikiya ce bana ganewa ,ko an koya min bana ganewa,idan naje aji wannan Malam yace kaza wancan ma yace kaza sai na ji kaina Yana juyawa yuuuuuu ta fara juya kanta a baban Nabeel. Yace to makaranta tana da amfani...kafin ya rufe baki tace ni nace Bata da amfani a kaina kaga ta turowa Nabeel kanta tare da fige hijab dinta da dankwalinta, gashi baki wuluk me tsayi da santsi ya bayyana tace daki kaji tana bubbuga kanta da Hannu Tace kaji Kara to Haka yake Kamar dutse baya jin komai a kulle yake ba fili ko daya a ciki da har Zan Gane ta furta tana maida hijab dinta. Ka tambayi dan Uwa na wallahi na fada masa bana so,Wait wait Nabeel ya dakatar da ita yace ilimi Yana da amfani yanzu idan banyi ilimi ba Zaki ganni a wannan matakin? Amma kalleni kalli motata Ina da wasu da yawa a gida Kinga duk karatu ya bani sabo da Haka kije makaranta,Yana Magana ko kallonsa bata Yi wasanta ma takeyi tana kalle kalle sai da ya Gama tace Ni nasan kaina Allah bazan iya komai ba bana ganewa bazan iya ba ni gaskiya so nake na Zama Yar kasuwa anfi saurin samun kudi,gaka kaima kana ta business,No..no Ni ba kasuwanci nake ba ilimi ya kaini cewar Nabeel,duk yayi yanda Hamida zata fahimce shi Amma Taki sai cika masa kunne ma da tayi da surutu sabo da bata magana a hankali,sai yace it's okay na Miki alkawari ni Kuma Indai kinje school Zan Baki dubu Daya kullum,duk ranar da kika je school to kizo Zan Baki dubu Daya cikin sauki ba tare da kin Sha wuya ba. Zabura tayi da sauri ta juya ta kalle shi Suka hada Ido ta washe Baki tare da cewa Dan Allah da gaske kake?, Idan kina ganin karya nake Bari a fara Nan take ya zaro rafar Yan dubu dubu yace ga kudi kin gani,1k ya zaro ya mika mata yace mu Fara daga yau,a Nan nake Aiki kullum Ina wannan titin naku,Dubu Daya ta karba Hannu na rawa da karfi tace ka tabbata kayi alkawari? Yace ae ai ban Miki Kama da Yan karya ba,idan ka karya alkawari Al'quran sai na karya Nawa zanje dai school Amma sabo da kudi,Kuma tsakani da Allah bazan rufe ka ba bazanyi karatun ba bazan gane ba,duk Nabeel ya gaji da cecekuce yace naji Kawai kije school ki zauna a class har a tashi kizo ki karba 1k fine,Dariya ta kyalkyale da ita ta Kara wani kyau sosai dama gata me shegen kyau Kalar skin dinta me kyau baza ace Mata baka ba Amma Kuma baza a kirata Fara tar ba,Yar cif cif da ita sura me kyau komai nata dai dai Allah ya Mata Kira. Da sauri tace da Dan uwanta Kai Sulaiman kake ko Sule na tafi school Allah ya taimakeka,ta tsani Sulaiman sabo da yanda yake dukanta sai taje makaranta dubunta Guda ta Bude tana tafiya tana kallonta Dan bakinta a washe da gudu ta kwashe har zuwa school. Haka a class tunda ta shiga aji ta bude window gefenta ta kurawa waje Ido Haka malamai Suka barta sukayi darasinsu aka tashe su sabo da Hamida sun gaji da halinta Bata tsoron uban kowa ba kunyar kowa take ji ba bata Jin magana,Bata da rufa rufa komai ke ranta Kawai fada zata yi ko Mene,ko a gidansu an yarda ita bata karya. Washe Gari ana tashinsu Nabeel ya manta da ita da gudu ya ganta ta taho wajensa hijab din a hannunta da takalminta Sandal duk a Hannu sai dai fes take ,Yana nunawa masu Aiki a motoci yanda zasuyi sai gata tazo da gudu tana dariya tace yawwa an taso mu a bani na tafi, Rana ta dameshi ya gaji yau sanye yake da kana Nan Kaya yayi kyau kallo Daya ya Mata ya zaro dubu Daya ya Mika Mata Tace na gode Allah ya biya ta sake arcewa da gudu da kallo Kawai ya bita tare da girgiza Kai yace Kauye kenan yaci gaba da uzurinsa Yana Gamawa ya tuka motarsa zuwa masaukinsa Hotel karami Dake kusa da kauyen,yana shiga room dinsa yayi order abinci sannan ya fada saman bed Yana huce gajiya,wanka yayi tare da Sallar la'asar ya kunna kallo Yana kallon ball har aka kawo Masa abincinsa yaci ya kwanta bacci ya kwashe shi. Basma zaune take a dakinta me kyau tare da kawayenta suna ta zuba Hira tana Basu labarin Nabeel dinta abin kaunarta,cikinsu Amal tace Basma Angon naki yayi tafiya Wai kin shiryu ne an daina cutar samari,Basma tana Dan yanga ta manyan Yara tace wallahi Allah ya shiryeki duk Wanda na yaudara na Basu Hakuri sun yafe min yanzu Haka Ahmad ne Kawai Wanda ya Soni da gaskiya ai Kun San yayi aure wlh matarsa wajen nakuda ta rasu yanzu ya koma Dubai Karo karatu na rasa contact dinsa bare na Nemi yafiya yanzu Ni abinda ya dameni rashin Nabeel Kun San so kana so ka dinga ganin masoyinka a kusa,tafawa sukayi shegiya ko dai Kuna Dan romance ne? Basma ta yatsina fuska tace duk samarin da nayi da Ahmad Kawai nasan Yana min abubuwa masu sweet Amma yanzu na tuba sai dai da Nabeel zaiyi min Dana ji Dadi Kun San Body no be firewood,wlh Nabeel ko Hannu bai taba rike min ba sai kace Dan Kauye, gashi dai kyau karshe ga wayewa da komai ya hada Amma wallahi ko hannuna Bai taba rikewa ba,kunsan ko jikina na Dan matsa sai ya janye jikinsa gashi a Baki Yana ta nuna min kauna amma ba komai Allah ya kaimu ayi aure sai ya min Amma har ga Allah da kyar nake kaiwa Dariya sukayi suna tafawa. Basma Tace ai Ni Ina son Namiji me class irin Nabeel,ga addini,ga tsoron Allah ba ruwansa da Mata sai Ni kadai,ai Yana bala'in so na,Kun San na yarda da kaina nice fa ware Baiko idan na rabi namiji ko Saura sati bikinsa a Rana Daya Ina rusa auren bare Kuma na tuba,nice fa da kaina nake sonsa ai ya shiga Uku ya Gama yawo,Nabeel na Gama sa Masa takunkumi ba wacce ta Isa shima bai Isa ba,inda Allah ya taimaka ma ban damu ba Kauye ya tafi aikin,wallahi tausayi yake bani Kamar Nabeel Dina a Kauye ga yanda yake bani labarin garin titin da yabi ta garin abin ba dadin ji,da ace birni ya tafi ai da na shiga uku sai Allah yasa Kauye ne ba wacce zai gani ta birge shi, Allah dai ya kaimu bikin yace in munyi aure ko Ina zaije kafata kafarsa. Shewa sukayi Suka tafa suna ta Shan labarin Basma. Tunda Nabeel yayiwa Hamida Alkawari kullum sai ya cika Kuma Bata kashe ko kwandala Tara kudin take ta Yi zata kafa jari ita dole sai ta Zama Yar kasuwa,Papa da Ummi da sauran Yan gidan suna mamakin yanda Suka ga Hamida kafin kowa ya tashi ta tashi tayi shara da wanke wanke da aikinta tayi Shirin school ta tafi Basu San ana Bata kudi ba sai mamaki suke Sulaiman yace ban yarda da yarinyar Nan ba Sam Ummi sai naje na duba makarantar,Itama Karima kanwar Sulaiman wacce ta Gama Degree an kusa bikinta ma tace makaranta take zuwa Allah yasa hakan ya Dore,Ummi Kuwa tabe Baki tayi Kawai Tace ummm sabo da Bata dauki Hamida a yarta ba,da yaranta Kawai take kula duk abinda Hamida zatayi tayi ba abinda ya shafeta ita Kuma Bata Mata mugunta Kawai dai Bata sa Ido akan tarbiyar Hamida sai ta yaranta,Wanda ya damu da inganta rayuwar Hamida Papa ne da Sulaiman babban Dan Papa. Bangaren Hamida Kuwa da Nabeel sosai take Jin dadin kyautar Nabeel gashi kyawunsa Yana birgeta sai tayi ta kallonsa tana Jin Dadi,Ana taso su ta taho yau Kuma wata tafiya take Kamar Namiji ba ruwanta da wani ita macece,tayi sa'a lokaci motarsa ta yanko yau Bai Zo da wuri ba,Ganin motarsa fyalleliya da gudu ta bi bayan motar ta tana tura motar Dake tuki yake da slow zaiyi parking,Yana parking ya fito yaci uban kana Nan Kaya yasha kyau harda glass hadadde,Hamida ta kalle shi tana ta faman Dariya Kamar zararriya Tace Sannu da zuwa kyakyawan Dan Uwa,kasan ka Zama Dan uwana,Kyakyawan Oga Bari na goge maka motar kaga Nan ka shiga chabi Nan take ta zare hijab dinta tana goge Masa mota da sauri yace no...no Bari Zan kaita car wash,ai da ka Bari na goge maka Kyakyawa tana ta faman washe Baki yace no barshi a gabansa ta dawo ta tsaya tana wulwula hannaye tare da Sosa wuyanta yace Ahmm...mene ma sunanki? Baki ta bangale Tace sunana na gaskiya Hamida amma da hausa Ana ce min Hamidatuwa,sunana na turanci Kuma Hamdy Amma zaka iya kirana da Hamida Hamdy Baby ae kwarai ehe yawwa,kallonta yayi Karo na biyu yanda take magana ba ko Jan numfashi ga sangarta da shagwaba Haka take magana,Hamida yace Naga dai kina zuwa school yanda nace yau harda bonus Zan Baki gashi karbi ya Mika Mata har 3k,ta kalleshi ta kalli kudin tace yau fa Weekend ba school gaisheka nazo Kawai Amma ka bani har dubu uku,yace ae Baki nayi ai kina yin abinda nace yanzu idan Naga kina kokari kina fahimtar abinda ake koya Miki Zan Baki kyauta Babba wacce tafi wannan,Me nace Dake Rannan? Tace kace idan nayi kokari Ina karatu zaka bani kyauta babba,Good ya furta tafi gida karki tsaya wasa,ta Kura Masa Ido yace I said Go, Tace Okay Sankiyu sir Wai Thank you take nufi,Fuska ya Bata yace ba Sankiyu ake cewa ba thank you Fadi naji,ta sake cewa sanki...kafin ta karasa yace no kalli lips Dina thank you,thank thank thank you,ta kasa ta sak cewa sanki..no,thank,Tace sank again ya gaji yaga dakikiyace ta karshe yace abeg go home tafi I'm tired. Tana kallonsa Tace in tafi kace? Yace ae Yana yatsina fuska zata Kara Masa surutu ya daka Mata tsawa,Ta juya da sauri ta kalli ma'aikatansa Tace Kai kunci kwalabar gyatiminku dukan ku nasan ba a son ranku oganku yake bani kudi ba sai dai ku mutu wooooo....Kunga an bani dubu uku kwana Nan Zan iya siye kawunanku,Daya a ciki ya dura Mata mahaukaciya Tace wullu wullu tana ta musu gwalo ta arce da gudun tsiya.. Gidansu ta shiga suna zaune a tsakar gida Sulaiman Yana ta game shi da kanwarsa Tace mutum kullum yace a tafi makaranta Wai a Haka anyi makaranta ana gida kullum,ko Zama batayi ba ta sake Fitowa ta fice da sauri Kamar Namiji wajen kawarta ta tafi ta iske sun dawo daga kasuwa Suka zauna suna Hira, Tace yawwa Sakina na manta ban fada Miki ba Ina Yaya Sulaiman kin San yanda yake dukana sai naje makaranta? Sakina Tace ae Kamar yanda kuka Saba,yawwa Rannan ya biyo Ni Yana ta duka na Sai naje school sai muka bi ta wajen sabon titin da akeyi inda katafila suke? Sakina Tace na Gane Ogansu na wajen ya dinga yiwa Yaya Sule fada yace a'a ba Haka ake ba karka sake dukanta Nan Ogan Nan ya dinga fada min kalami me dadiiiiiiiiii ta wani ja sanna taci gaba amma duk na manta abinda yace abinda na rike kawai a kaina yace kullum in naje school zai bani dubu Daya,Sakina Tace ke ki Bari Dan dan Allah? Wallahi Kuma Yana ta bani yau ma harda bonus,Sakina ta mikawa Hamida dafaffiyar Masara suna ci Sakina Tace dubu Daya a wata Kinga dubu talatin kenan,ai ihu Hamida ta kwala tace na Zama Hajiya kinga sai na Fado kasuwarku Nima Ina Saro Masara a gona Ina kaiwa kasuwa,tafawa sukayi harda shewa,ai ko Papa baya samun kudi haka gashi yana da kirki gashi kyakyawa na sosai fari Kar da shi,Kin San fa Yaya Sulaiman duk dukana da yake nasan baici exam ba shima,ya akayi Kika sani? Sakina ta tambaya, Tace ke idan yaci jarabawa Zaki gashi ganshi a zaune a gida bashi da Aiki sai game babu aikinyi,ba Wani ilimi da yayi in ma yayi ban yarda ba,yanzu Baki ga kyakyawan Yaya yake ba Yana Dan lallaba Ni ba irin yanda ko a Gari ake min kallon marar hankali ba,Dariya Sakina tayi Tace ko dai son kyakyawan Yayan naki kike yi? Ba Wani so Kawai dai Yana da kyau ai nafi son dubu dubu dai Dariya sukayi suka dinga hirarsu sannan ta tafi. Kamar kullum yau tazo sanye da Uniform an taso su da gudu ta karaso hannunta ya fara hangowa an manne shi da bandage bai ce komai ba Hamida tace Yaya Kyakyawa kaga hannu na kofar Hannu ce ta datse min yatsa,eyya sorry ya furta tare da zaro kudi ya Mika mata dubu daya yaci gaba da magana da ma'aikatansa sai taji yace hotel Zan koma Zan Yi wanka. kusan kullum Hamida tazo sai taji yace wanka zai je yayi,Yana bata mamaki ko sau nawa yake wanka a rana oho, ta juya zata tafi sai ta juyo tare da kwala masa kira Yaya Kyakyawa agwagwa tana gaishe ka,Bai gane nufinta ba ya zaci shirmenta ne ba tare da ya dago ba yace kice Ina amsawa na gode,Dariya ta kyalkyale da ita bai sake ko juyowa ba itama haka ta tafi da sauri gida tana tuntsira dariya. Littafin Nan ba a farko za a Sha Dariya ba sai gaba Fans AsmaBaffa [6/28, 1:46 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 3 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM page naku ne BASMAM GLAMOUR MOM ABDALLAH NAFEE UMMU LATEEPHA SA'ADATU TIJJANI MMN UMMEE Yau Monday yazo wajen leburorinsa sanye yake cikin shadda sky dinkin cif cif shi Yana jikin mota ya Kara waya a kunnensa Yana waya da Basmansa suna zuba love Hamida ta taso daga makaranta ta lallaba ta bayansa Wai zata bashi tsoro tayi Masa Cakulkuli da sauri ya juyo fuskara a murtuke Kamar an Aiko Masa da mutuwa nan take ta Shiga hankalinta taji tsoronsa sosai,waya yake Yana daga Mata hannu alamun tayi Shuru amma dariya Kawai take kamar itace take wayar,ta koma surutu tana to kayi hakuri Yaya kyakyawa bazan sake ba,Basma ta cikin waya Tace wace wannan? Yace no cikin yarana nane akwai wani me zubin Yan daudu to shi ya yazo,Basma taja tsaki tare da furta Allah ya wadaran halinsa, Hamida bada ita ake ba Amma sai dariya take haka Kawai. Da sauri yace idan na koma hotel Zan kiraki ya datse wayar,Yana gamawa ya daure Fuska kamar an aiko Masa da mutuwa ya kalli Hamida Nan take ta nutsu yace yaushe kika Raina ni? Yaushe muka fara Haka da ke?Zaki zo ki taba min baya sa'anki ne Ni shashasha,Baki ta kumbura cike da shagwaba tace kayi Hakuri bazan sake ba,ka yafe min,Nan take yace ya wuce tare da zaro dubu Daya yace oya take jeki,Tace ya Naga kamar baka hakura ba ta furta da agwagwaba,yace na hakura karki sake Tace to,tafi to tace Zan tafi ai kaje dani Naga gidan da kake Zama dan Allah. Bafa a gida nake ba a hotel nake Zama Aiki ya kawo Ni na kusa tafiya ma,Ina zaka tafi? yace can state dinmu Nan ba state dinmu bane Aiki ya kawoni Kuma aikin ma nayi tunanin zai dade Amma gashi mun kusa na kusatafiya gida,Kuka Hamida ta kece da shi ta Fadi a kasa ta fara birgima da burburwa tana Shure Shure ganin zata tara masa mutane Yace ke..ke..ke tashi mene? no ..no..no.. stop crying ai ba yanzu Zan tafi ba da sauran kwanaki Kuma ko na tafi zandinga Aiko Miki da kudinki okay, sai lokacin tayi Shuru ta Mike tana share hawaye ta juya jiki a sanyaye tafi gida,yau Rai a bace tana kuka ta Shiga gida,Ummi ta samu da Papa ga Yar Ummi itama suna ta Bude kayan auren Karima ana gani Suka ga Hamida ta shigo da kuka,Sulaiman yace ke Kuma lfy? tana shesheka tace ba..ba..ba..Yaya kyakyawa ne yace zai tafi garinsu ba wallahi bana so ya tafi,Karima ce ta Mike ta dakko ghana must go ta kayan Hamida ta fito da ita ta bude kudi Yan dubu dubu da take Tarawa suka bayyana kowa ya saki salati Wajen kayan Hamida ta karasa ta kwashe kudinta tas a hannunta,Papa a nutse yace Hamida a Ina Kika samo wannan kudi Haka? Ba tare da shakkar komai ba tace kawu wani ne ogan masu aikin titi yace Indai Ina zuwa makaranta kullum zai bani dubu daya har bonus ma yake Kara min da yaga Ina yin abinda yace kuma baka ganshi ba kyakyawa wallahi Kamar balarabe,ai kudin ma basu kenan ba akwai ragowa so nake na Tara na kafa sana'a mu Zama masu kudi bari na dakko wancen kudin na tuna da gudu ta nufi hanyar daki Tace ku matsa daga hanya Kar na kade ku,ganinta da gudu yasa Karima da Sulaiman Suka watse daga saitin Hanya ta wuce ciki sai gata ta Kuma Fitowa da dubu biyu da dari biyu,Tace wannan na jiya ne ya bani dubu uku,to Nan ya Naga dubu biyu da dari biyu Papa ya tambaya, Tace Yi Hakuri na manta na bawa Sakina a ciki Zan siya Masa kayan marmarni na Kai Masa sabo da mutuncin da yake min. Kirji Ummi ta dafe Tace papa Ina tsoro karfa Yarinyar Nan ace Dangerous part dinta yake tabawa Yana Bata kudi ka tsawatar kar a samu matsala,da sauri Hamida ta girgiza Kai tace a'a..a'a wallahi ba abinda yake tabawa nawa Dangerous part Dina suna Nan lafiya ba abinda ya dame su,papa yace ki dai kula na fada miki, ai nasan Papa duk gidan Nan Kai kadai kake kaunata bari na kwashe kudina Kar ma a sace min barayi sun San kansu ehe ta furta tana kallon Ummi, ta kwashe kudinta tare da zubawa a wata karamar jaka tace yace ya kusa komawa garinsu ma Kuma bana so ya tafi. Baki Suka tabe suna binta da kallo tana fita wajen Sakina ta wuce ta Bata labari Yaya Kyakyawa yace ya kusa tafiya ta fada da Kalar tausayi ta zuba uban tagumi tace zanyi kewar sa,Sakina tayi Dariya Tace kewarsa ko ta kudi? Tace ta Yan dubu dubu gaskiya nafi son kudin sai suka kwashe da dariya,Hamida tasa hannu a baki tana Murmushi, fita sukayi kasuwa ta siyo Masa abarba da Ayaba,sannan Suka je gona tare da tsinko masa lafiyayyun mangoro da yawa tace a hada Masa da goruba da giginya,Sakina tace na shigai Yan birni basa ci bare Namiji tace a dai hada da su na Kai Masa kafin ya bar gari Nima nayi Masa abin kirki yanda shima yake kyautata min yana bani kudi kullum ba irin Sulaiman ba da yake dukana kullum. Haka Suka cika wata leda Viva da kayan marmari Suka tafi yau da Sakina za a aje ta Kai gaisuwa wajen Yaya kyakyawa. Ai Kuwa Yana jikin mota a tsaye Yana latsa katuwar wayarsa Yamma tayi ya gaji sosai,da gudu Suka fyallo kayan Yana Kan Hamida suna zuwa Sakina tunda tayi arba dashi ta rikice sabo da mugun kyansa da iya wanka ga kwarjini ita bata taba kawowa haka Yaya kyakyawa yake ba ta zaci shirmen Hamida ne,Hamida ta kalli Sakina tace Kinga Yaya kyakyawa durkusa sosai ki gaisa shi Mana,Sakina duk ta rude ta durkusa har kasa tare da furta Ina yini,Nabeel yace ahh na zaci sister dinki ce lafiya Alhmdllh Kawai yace,Hamida da leda a kanta tana haki tace kaganta itace sakinan Dana ke ta baka labarinta kalleta sosai kawata ce ke Sakina juya ya kalleki sosai Sakina ta juya baya ta sake juyowa Shi dai Nabeel ko kallon wata Sakina baiyi ba yace Hamida lafiya yau ba school na ganki da yamman Nan Kuma ma ai na baki kudinki,ledar ta sauke da kyar tana Nishi Tace gashi kayan marmari na kawo maka kasan a kauyen Nan muna da kayan marmari da yawa shine na siyo maka wasu Kuma muka samo a gonarmu kayi Hakuri ba yawa,Ledar ya Dan buda ya gani dariya ta kamashi a ransa harda goruba da giginya yace Ina Kika samu kudi har kike wahalar da kanki wajen siya min Abu,Dariya ta kyalkyale Tace ai kadan ne ba yawa kana kyautata min shine Nima nace bari a cikin kudin da kake bani na siya maka dan wannan,Murmushi yayi tare da kallonta yace na gode kina da kirki Ashe? da sauri tace ei wallahi Allah ya bamu,shi dai ya saka cikin mota ya tafi itama ta juya taga ba Sakina Ashe tuni Sakina tsoron kyawun Yaya kyakyawa da kwarjininsa ta gudu ta buya a bayan wata bishiya sai da ta tabbatar ya tafi sannan ta fito Suka tafi gida suna surutunsu. Washe gari da sassafe Bata je school ba wajen aikin Nabeel ta wuce sanye da Uniform dinta yasha wanki da guga tasan da safe yake Fitowa tana zuwa ta ganshi da wani littafi Yana nunawa maaikatansa tace Ina kwana Yaya kyakyawa, Bai San da zuwanta ba daga sama yaji gaisuwa Kawai, Alhmdllh lfy sauri nakeyi jiya banyi bacci ba Ina Aiki komawa zanyi hotel na kwanta,Nan take Hamida tace Dan Allah ka tafi Dani na gani yace no....akwai school faduwa to tayi ta zube a kasa tana burburwa da Shure Shure tana kuka ta cika wajen zata Tara Masa mutane,yace ahh... see me see trouble, okay fine kije school ki dawo sai kizo,wani sabon kukan ta saki tare da cukwikwiye hijab dinta da kyar ya lallabata yace muje amma alkawari Muna zuwa idan Kinga masaukina Zaki wuce school da sauri tace ae na yarda, Mota ya bude Mata ta Shige da sauri wani kamshi da sanyi ya ratsata ta dinga kalle kallen cikin motar tana kyalkyala dariyar farin ciki Yana tuki tana ta shafa kujerun mota tana cewa yeee dadi ta saki ihun da ya tsorata shi,Oh God ya furta Yana ta kallon shirmenta ta glass dinsa,sai da sukayi tafiya me nisa Kamar zasu shiga birni sannan Suka Isa hotel din. A wajen dan birni yasan hotel din ba na kirki bane sai manage,room dinsa Suka shiga ita a wajen Hamida Aljannar duniya take gani ,Yana Bude kofa ta Riga shi Shiga ciki sai kallon dakin take tana washe baki ta fada saman bed tana wash Dadi,Nabeel ya shigo daga baya tare da Zama a gefenta hannunsa a saman cinyarsa yace tashi to ki tafi school da sauri tace Ni yau bazanje school ba Nan ce school Dina a Nan Zan zauna tare da Kai,da sauri yace a'a ba kyau mace da Namiji su kebe kin sani Kuma alkawari Kika min gani Kawai zakiyi ki tafi school,da sauri tana girgiza kafada tace a'a Ni bazanje ba ta kwabe fuska da karfi ta saki kuka,yace okay okay naji Ni bacci zanyi ki nutsu karki har gitsa min room,Baki ta washe tace to,komawa tayi saman drower ta bed din da Jakarta a rataye ta cikinta ta zauna,sai ta cire school bag din ta taka bed din da takalminta ta Mike tsaye wani kallo da ya watsa Mata ba shiri ta koma ta zauna inda ta tashi ta nutsu. Tace Yaya kyakyawa kalli mudubinka Kamar na Mata ai gwara da kacewa ma'aikatan hotel Ni kanwarka ce kaga duk Sanda Naga dama Sai na dinka kawo ma ziyara,ki min Shuru ko Yana Mata shouting tace to nayi Shuru,sai ta sake cewa na kwanta a bed din dan Allah? Hade rai yayi Kawai yasa ta nutsu. Toilet ya shiga tare da watsa ruwa ya fito sanye da jallabiya fara yayi kyau sosai da sosai sai binsa take da kallo,tana gani yayi Sallar nafeela da adduoi sannan ya haura saman bed sai bacci ya manta ma Hamida na Nan,ganin yayi bacci ta lallaba ta Gama tabe tabenta na kayansa sannan ta dawo gabansa ta durkusa a kasan bed ta kafe shi da Ido tana ta faman kallonsa Kamar mayya a ranta tana ayyana kyawunsa har ta gaji tana haka ta kwashe wasu Hours Bata sani ba har wurin 2pm gashi tana Jin yunwa sai lokacin ya farka tana ganin Haka ta koma inda take zaune saman Drower da gudu ta zauna ta wani nutsu ya rigada ya kamata,Yana tashi order ya Mata take away a hotel din da muryar bacci yace lokacin tashinku yayi tashi ki tafi gida,Ni bazan tafi ba a Nan Zan zauna da Kai na dawo Nan da Zama,tsawa ya buga Mata tashi nace ba shiri ta Mike a zabure Tace dan Allah ko Awa biyu ka karamin na zauna da Kai Ni nafi sonka,Tsaki Yaja yace kalleni ta Kura Masa Ido yace nace No..a'a da babban baki Ina jakar makarantar ki? ya dakko ya bata tare da Mika Mata dubu biyu ta tsaya galala Tace Naga banje school ba me yasa ka bani kudin Kuma har da yawa?kudin napep ai kin San gida tashi ki tafi ki shiga Napep aiki zanyi a computer kina takura min,karba tayi Tace na gode ta dauki take away dinta ta fita tun kafin ta Isa titi ta Bude abincin jullof rice da Rabin kaza ga lemo ga ruwan roba, ai a hanya ta fara ci tana tafiya tana ci a haka ta tare napep Suka koma kauyen tana napep tana ci har ta Gama ta shanye ruwanta da lemo ta jefar da tarkacen tana ta bawa me napep labarin Yaya Kyakyawa har ya sauketa a gida,tunda taga masaukinsa kusan kullum idan aka tashi daga school da Yamma likis Bayan tasan ya koma masauki sai taje can tayi ta surutu ya Bata abinci taci ta koshi ta dawo gida, masu hotel duk sun zata da gaske kanwarsa ce sun ganta itama kyakyawar gaske. Yau Sunday da sassafe ko tashi baiyi daga bacci ba ta shirya ta tafi da kayan gida sanye take da Atamfa maroon Riga da skert harda Dan hijab dinta Yana kwance da Yamma saman bed dinsa Yana chat da Basma sabo da biki Yana ta matsowa har Saura wata Uku sannan Saura sati Daya Kuma ya koma state dinsa ya Gama kwangilarsa duk da cewa Yana Dan zuwa weekend Watarana,bugun kofa yaji Kamar za a ballata yace waye?Dan Kar ya hanata shiga tayi Shuru Haka Yaja Tsaki ya Mike sanye da kayan baccinsa Riga da wando ruwan Toka wasu silk yayi kyau Yana budewa ta Fado ciki da gudu tana tsalle tana dariya,harara ya watsa Mata yasan rigimarta bai son surutu yace daga Ina? Ko karyawa banyi ba na taho wajenka,me Zaki iya ci? Tace komai ma zanci ai sai yasa aka kawo Mata jullof din taliya taji Naman kaza ga ruwa da lemo,shi Kuma yace a kawo Masa kwai da slice bread sai tea da kwai,Tace inye Yan gayu Breadi me yanka yanka San min,Murmushi yayi kadan tace yau kayi Dariya kayi kyau,shareta yayi ta baje a tsakiyar bed ta Mike kafafu abincinta Yana tsakiyar cinyoyinta ga cokali me yatsu duk ta kasa eban taliyar da shi abinka da ba a Saba ba,yaga ta hada zufa ta gigice tayi tayi ta ebo taliya da fork ta kasa Yana ta kallonta da mamaki ganin zata Bata Masa bed yace Hamida taji wani sunanta me Dadi yafi kowa iya fada yace ba Haka ake cin abinci da fork ba Bari na koya Miki karbar fork din yayi Yana nannado taliya a jiki tana kallonsa yace Haka akeyi fa kin gani Haka jikinsa Kamar zai hade da nata kamshinsa ya Gama cikata har Bata so ya matsa. Ta gwada tayi tayi ta kasa yace akan ki Bata min bed kawo spoon din ya karbe ya ebo ya nufi bakinta ya fara bata a Bakita idan ya bata sai dai ta zuki taliya ta cuno Baki gaba tace tsaya Yaya kyakyawa kaga Ni kalla ta zuka zuuu...tana Dariya kalla Kamar na hadiyi miciji,yace na gani ba a hadiyar miciji tace to,sauri kici karki sa tea Dina yayi sanyi Yana Bata da sauri amma sai ta tsaya tayi Wasa da taliyar kafin taci,ya Kuma ebowa ya Kai bakinta ta sunkuyo da kanta ta kansa spoon din sannan ta figi taliya guda biyu ta zuka zuuuu tare da cuno lips wani kyau takeyi Yana kallonta a Haka ta Gama ci ya karya shima sannan yace Aiki zaiyi a system ta tashi ta tafi gida hakan ma Sai da ya Bata Rai sannan ta tafi,yace ki tabbatar kinyi Sallah a gida Tace ai dama. Tana tafiya yace Alhmdllh sai na huta Haba yarinya sai sangarta da tabara Nan ya huta,duk garin ko Papa ba Wanda ya Isa ya fadawa Hamida taji sai Yaya kyakyawa,Nabeel duk abinda yace zata ji Amma banda kowa Bata tsoron kowa. Ummi ce ta samu Papa sabo da Papa akwai sanyin Hali ba takura tace ya kamata ka sa Ido akan Hamida Kar ta dakko Mana magana yanda Yarinyar Nan take gantali ba a San fa Ina take zuwa ba,suna Haka sai ga Sulaiman shima ya tsinci zancen yace Papa yanda kake kyale Yarinyar Nan tana abinda taga dama bai Dace ba,Kar ta shiga wani hali Papa bana son Hamida ta lalace,Papa yace nasan Hamida baza ta aikata wani Abu da ya sabawa musulunci ba,duk da bata da ilimin addini amma dai dai gwargwado tana kokari, na yarda da yanda Hamida bata Wasa da sallah ga adduoi Inshaallah ba abinda zai faru Ina Mata kyakyawan zato a bita a hankali yarinya ce,Ummi wata Sallar kirki Hamida ta iya hmmm ayi ma gani,Sulaiman yace Ummi ki dinga fadan Alkhairi akan Hamida duk da bake Kika haife ta ba a gidan nan ta taso Kuma hakki ne a kanmu,Karima Dake wanke wanke Tace hakane wallahi ga bikina Saura kwana Uku amma Hamida ba Wanda ta gayyata Harkar gabanta take Hamida ba hankali ko Ina take yawan zuwa yanzu oho haka suna kallo ta shigo ta wuce su ba Wanda ta kula sai Papa Tace Sannu Papa me kaunata ta Kara gaba. Bayan kwana Uku Haka aka gama bikin Karima ko daya Hamida bata Zama tana can tana zuwa wajen Nabeel taci ta koshi ya bata kudi ta dawo Haka sabo da dubu Daya ana biki bata fasa zuwa makaranta ba har mamaki ake duk da cewa Bata gane komai. Ana gobe Nabeel zai koma garinsu Kaduna Hamida tazo room dinsa da Yamma sanye da doguwar Riga da gani Yar kanti ce dark blue me kyau ta dameta daga sama kasa ta bude ta fito da kirarta sosai kirjin Nan a cike fam ga hips tayi kyau,ko mayafi Bata yafa ba sabo da rashin hankali,shi Nabeel Bai dauketa a wata me hankali ba shi yasa yake kyaleta,tana shigowa ta ganshi da Riga t-shirt sai 3qrt,yace Hamida kece da yamman Nan,tana dariya irin ta wawaye Tace ae Ina wuni yace lafiya Yana gefen bed Yana Danna waya Tace na hau gadon? Yace ke da kike har bacci sai yanzu Zaki tambayeni,me Zaki Sha bani da drinks yau a fridge Hamida Tace komai ma Zan Sha,yace tab bani da komai sai giya Tace laaaa dama kana Shan giya? Yace ae kadan ba bana Sha da yawa Ni a kasar waje na koya tace bani Nima Zan sha,yace kin taba Sha ne? Tace ae to ban dai taba Sha ba amma duk abinda kake Sha ko wuta ce Zan Sha Nima,Baki ya tabe ya dakko kwalabar giya a fridge dinsa tare da tsiyaya Mata Yar kadan a kasan glass cup Wanda kurba Daya ce yace iya Yar wannan Zan baki,ta karba Tace Yar wannan dan Allah Kara min yace bazan Kara ba so kike ki bugu iya wannan Isa maza shanye ki bani cup Dina,tunani ya lula ko me ya tuna oho sai ya fisge cup din yace ba kyau na tuna Nima so nake na daina, shi kuwa cup guda ya cika da ita ya zauna a gefen bed Yana korawa,,Hamida Kamar walkiya ta dauke wacce ya kwace ya dora a saman mudubi. Dan kadan ta zuga ta zaro harshe waje tace ahhhhhhhshs.. shiiiiiiii.... da karfi Tace zafi da daci wani abu ne ciki Yake Yama yama yama, Murmushi yayi yanda take wani Dan zuka tana zaro harshe,yace nace karki Sha bakya Jin magana Zan daina kulaki,Yi Hakuri ta furta da kalar tausayi. Kallonta yayi yace nace karki Sha ko, Mene haka Wai ko baki da hankali ne Tace da hankalinta Yasin,Murmushi ya saki yanda take magana da wawanci Kuma da karfi,a Haka tana Wasa ta shanye abarta,Nan take taji kanta na juyawa,shi kuwa ogan Yana Gama Sha yaji sha'awa ta kamashi Kamar zaici babu sabo da sha'awarsa ya rage Shan giya Amma yau ya Dan Sha ga mace a kusa sai ya Mike sosai Kamar Abu zai fasa wando ya fito,Ita Kuwa Hamida kanta sai juyawa yake ta kwanta ta baje a saman bed,kallonta yake da sha'awa Bai taba Zina a duniya ba Kuma baya ko kawo abin a Kansa Amma yau Kam yaji bazai daure ba gwara ya samu ya rage zafi a jikin Hamida bazai lalata ta Mata rayuwa ba amma zai romancing nata ko zai ji sauki. Shi Kansa Nabeel baya hayyacinsa yace na ce da Affa ya min aure da na huta sai na koma gida a yau Zan bi flight wannan boko ya cuceni,Hamida Kuwa Kai sai juyawa yake Tace wayyo Yaya kyakyawa wayyo duniyar zata kife mun shiga Uku muma Allah ya Aiko mala'ika gashi Nan za a kife duniya,shike Nan gashi Nasha giya na Shiga Uku wuta Zan wuce babu gargada, yau Zan Sha almudun bakin karfe,sama ta kalla wayyooo Allah na Shiga Uku ashhadu Allah Ila ha illallah wa Anna muhammadan rasulillah,Allah na tuba...Allah na tuba...Yaya muyi kalmar shahada ko zamu cika da Imani idan yaso in mun je can a tittike mu daga baya dai ma shiga Aljana,Ina ta sa Rai Zan zauna a GRA a Aljanna Ashe kauyenta zanje. Innalillahi Yaya kyakyawa rikeni shike Nan,Hamida tana ta surutu amma ba ta ita yake ba ta kansa yake saman bed din ya haura a hankali ya Kama hannunta Yana Dan murza yatsunta Hamida tana feeling abu amma ta kasa magana itama a hankali ya fara murza wuyanta a nutse cike da sha'awa,tana kwance ta kalli sama ya koma Samanta ya Mata runfa gaba daya kamshi da abinda yake Mata yasa tayi luf a nutse ya sauke lips dinsa a nata ya shiga tsotsa da salo Yana bin jikinta da Hannu Yana shafawa wani irin dadi yake ji marar misaltuwa abinda bai taba Yi ba a rayuwarsa. Hamida ma dadi ta fara ji baza ta iya hasala komai ba,a hankali ya zare Mata Riga wow Albarkatun kirjinta Suka bayyana manya gasu a tsaye sumul sumul masu haske da kyau Nan take ya Kara haukace Mata sai data tsorata yanda yake Sha Yana murza su son ransa Kamar ya bada sadaki,hankalinsa gushewa yayi itama Hamida tana Jin Dadi ya fara karanta Mata wasikar jaki Yana sambatu Yana Mata tambayoyi da gani kasan baya hayyacinsa,mutum me aji da kula da addini irin Nabeel amma ya kasa,yace kina Jin dadi? Hamida tace ae cikin kunya,da kyar ta jawo bed sheet ta danne iya fuskarta sabo kunya,Amma Nabeel yace ki budemin Naga idanunki kinyi kyau,Hamida ta mato ta sake boye Fuska Yana ci gaba da murzata a haukace kamar zaki,kafin kace me Hamida ta jike sharkaf da ni'ima,hakan ya sake tunzura Nabeel Hamida ita kanta dadi ya tafi da ita sai Nishi take Tace kaji Ina ta Nishi Ni na rasa dalili,banza ya Mata sai da duka hankalinsu ya gushe sannan ya nemi Hanya Hamida ba hankali ba wayo sannan ba tunatar da ita ko wani abu ba Kawai ba zato taji Yana kokarin shigarta ita bata ma gane me yake kokarin Yi ba sabo da Bata San komai ba babu Uwa me nusar da ita,da kyar da wahala ya samu ya Buda ya shigi Hamida yaji ta a matse gam gam virgin. Yayi mamaki sabo da ganin ta saki jiki ya zaci tunda mahaukaciya ce tana bin maza ko wasu mazan sun lalata tunda ya ganta Kamar dabba sai yaga ba haka ba,ita Kuma tana Jin radadi sai dai tace wayyo wallahi zafi zanyi kuka na shiga Uku na,wayyo Papa ka bari,Yaya kyakyawa Mene ka sa min haka Zan mutu wayyo Ummi wayyo Yaya Sulaiman,Wai mene wannan kake min,Ina baya jinta sai wasikar jaki da ya shiga karanta Mata,ganinta da gaske yake yana ta faman furta mata I love you,Ina sonki,Zan daukeki mu tafi birni Zan dawo na tafi dake Ina sonki,Dausayinki da Dadi my love,you are so sweet,Hamida zafi yasa giya ta saketa tuni,ai Kuwa sai da ya kawo ya juyewa Hamida komai a ciki sannan ya zare jikinsa ya kifa Kansa a saman bed,duk da Zina yayi amma ya tsinci Kansa a farin cikin da bai taba ji ba a duniya,tsoron Allah ne ya kamasa,ya kwanta ruf da ciki Yana hutawa muryarsa na rawa ya Shiga tuba ga Allah Yana Astagafirilla.. Astagafirilla wa atubu ilaih, Innalillahi wa Innalillahi rajun,oh my God me na aikata Allah na tuba idan ya fada sai Hamida ta amsa itama ta fada,duk abinda yake fada na tuba ga Allah sai itama ta fada kamar me Waka da amshi suna ta yin haka,ya dago ya kalli Hamida ya sauka kasa da sauri yayi Zaman dirshan tare da Dora Hannu a jikin bed din yace kin jawo min masifa ba a so Namiji da mace su kebe na ukunsu shedan ne,nace bana so kizo bana so Kika ki ji kike zuwa wajena ko yaushe gashi nayi abinda ba naso yanzu me Zan cewa Allah,nayi Zina da kaina ya dafe goshinsa sai ga hawaye na bin kumatun Nabeel. Hamida ta yunkura zata tashi tana lullube da towel ta kasa tashi a hankali ta jawo rigarta wacce duk ta yamutse ta lallaba ta saka, sannan tayi magana a nutse sabo da tayi laushi ya Bata wahala,a hankali Tace badai wannan abin da ka min ba kyau ba? Wani haushi ta bawa Nabeel ya kalleta Kawai tunda ita ta ja Masa,yanzu Yaya Kar dai ace wannan ce Zinar da nake ji ana fada a Islamiyya Watarana idan an korani makaranta? Ka fada min na sani Wai babu kyau Allah ya Hana? Kar dai duk bala'in da naji ana yiwa mazinaci a lahira shine zai hau kanmu? Illar jalhilci kenan ga abinda akecewa kije makaranta amma kinki yarda ga irinta,da kina da hankali ai ko a kawayenki Zaki ji a class. Hamida ta zaro Ido yanda yake Mata masifa,yace idan Allah ya yafe Mana ke nake ji yanda na lalata Miki rayuwa ashe baki taba Yi ba,Hamida hankalinta kwance tace Indai dan ta nine Yaya kyakyawa karka damu wallahi na yafe maka ko mene ba komai karka damu ko Mene ba matsala,da sauri ya kalleta ya zaci zata tsane shi sai yaji akasin Haka Kuma ko a jikinta,sai ya danji sanyi kadan,a hankali shima yace kin iya wankan tsarki? Tace na Iya Karima ta koya min wata uku dana Fara period Kawai taimaka min na tashi nayi wanka na tafi gida Kar dare yayi Sulaiman sai ya min duka. Mikar da ita yayi tace wayyo wallahi Dausayina zafi Dariya ta bashi ya danne wato ta rike Sanda ya fada Mata lokacin baya hayyacinsa a hankali tana takawa Yana ce Mata sorry...sannu har toilet tana wayyo dausayi tana wani dangwala kafa yace da ruwan zafi Zaki gasa ya koya Mata tace Yaya wato shi dausayi abin kadan sai ya kwararrabe Wai Ni Yaya kunya wallahi inafa kallon tsaraicinka na shiga Uku walakiri zai ci uwar mu Yasin,Yace dan Allah istigifari kullum kinji Tace to ai dole amma karka damu fa ba matsala ya wuce ai Kaine Yaya kyakyawana,yasan ba hankali gareta ba ya gwada Mata yanda zata gasa jikinta ta shiga tare da rufe kofa,saman bed din ya kalla duk jini. Tsoron Allah ya sake kamashi Yana mamakin Kansa daga ranar yace Allah nayi Alkawari bazan sake Shan giya ba har abada,Hamida haka tayi yanda yace sannan tayi wanka da sabulu ta fito,Ya ganta ta maida rigarta tayi fresh yace,phone Number dinsa ya rubuta Mata yace gashi idan da wata matsala kina kirana a waya,ya zaro kudi dubu goma ya bata yace gashi Kya siyi wani abin,kin karba tayi tace Wanda kake bani kullum Ma Yaya sun isheni karkace Dan kayi wannan zaka ba Ni wani kudi na yafe ma wallahi a raina ba komai sai dai mu tuba ga Allah Kawai sannan muji da yanda walakiri zai narke mu da sanduna,daga Haka ta bude kofa ta tafi gida tana tafiya Kamar Yar kaciya kafafu a tale da kyar take takawa,shi kuwa wanka yayi ya dauro alwala ya fara nafeela Yana tuba kamar ba gobe. Hamida da tafiyar a gwagwa ta shiga gida ba ko sallama ta iske Sulaiman da Papa suna Maganar Ina ta shiga Suka ga shigo talau talau da kyar take tafiya tana gwalewa,Sulaiman yace Ina Kika je dan ubanki da sauri tace ba inda naje amm..daga gidan Sakina,Bata Saba karya ba shi yasa ta daburce,yace Papa yanda Yarinyar Nan take magana ban yarda da ita ba,Papa yace na yarda dake Hamida amma banda yau,me ya sameki kike tafiya haka? Tace faduwa nayi na bige kafata Nan take Papa yace to za a siyo magani kinji Sannu Amma duk da Haka Bai yarda ba. Sulaiman zaiyi magana yace kyaleta a dinga binta a Sannu yarinya ce Yar Dan uwana ce bana son na ci Amana wajen gallazawa jininsa Inshaallah ba abinda zai faru da Hamida,Sulaiman ba yanda ya iya Haka zance ya wuce. Nabeel Kuwa a ransa ya tabbatar shi da wannan kauyen har abada bazai sake zuwa ba ko wanne kwangila ce bazai karba ba Indai a Kauyen ne,baya fata ya sake haduwa da Hamida, da sassafe ya hada nasa ya nasa yabi flight sai Kaduna motar ma driver ya Kira yazo ya daukar Masa ita,Yana dawowa Basma tazo gidan zatayi sati Uku sabo da zata Fi ganinsa kullum ta sake sace zuciyarsa ta karasa dasa kaunarta a wajen Nabeel sannan zasu Fi Shan love,Nabeel yasan da zuwanta kafin ya dawo tana gidan,shima yasan yayi missing dinta ita yake da burin gani ya manta ma da wata Hamida a duniya. Sharhi Dan Allah fans AsmaBaffa [6/28, 1:46 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 4 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne MOM ANEESA MBELLO COOL LIFE HAUWANCY S Y SAGAGI MRS MUKHTAR MRS SURAJ MAMAN DR NANA KHADIJA MUHAMMAD PHATTMAH NAFEESAT UMAR MUHAMMAD DIDI SALMA Tunda ya dawo ya manta da wata Hamida da abinda ya faru garesu sunan garin ma baya son ji,Kawai ya koma office dinsa da aiki sai kuma soyayyarsu da suke zubawa shi da matar da zai aura wacce an kusa bikinsu Saura wata hudu,yau Weekend ba inda Nabeel ya fita Mami ta basu waje a Palo shi da Basma suna Hira,Basma tana yanga tana Masa fari da iyayi tace Baby baka bani labarin Kauye ba like ya kauyen yake mutane da kake hangout with etc,hmm Kawai Nabeel yace ni ba ma abocin magana bane,da shagwaba Tace please,yayi Shuru common Beb,Yana Dan Murmushi yace garin ba Dadi,bana kaunarsa ban son komawa har abada,Baki ga Hotel din da nake manage ba babu Dadi ga nisa,sannan banyi aboki ko Daya ba bani da kowa a can ni kadai nayi rayuwata sai Yara na Kuma mun dawo dasu,Basma tana dariya Tace ai shi yasa na tsani Kauye da mutanen Kauye Sam basuyi ba,sorry naji tausayinka Baby kasha wahala, Affa baya son auren da Nabeel zaiyi yafi so ya tafi Karin karatu amma tunda yaga Basma Yar Boko ce harda degree ya danji sanyi shi baya son hada alaka da marar ilimi Wanda baiyi degree ba,son samu dansa ya auri me PhD ko masters ya Raina degree yace na kowa ne gama gari,Abba ne ya shigo Yana waya da babban abokinsa Prof yace karka sake kayi Mata aure ba tare da degree ko masters ba an waye ai mazajen sunfi rike yaran Mata da daraja,Prof ta waya yace ta kulle kanta sai kuka take,Affa yace ka kyaleta duk kukan soyayyar banza take zata daina kayi kokari ka tura Yar banza Russia inda Nabeel yayi karatu sanyi ma ya isheta,Suka Yi Dariya ta manyan Yan boko, Affaa Yana gama waya ya kalli su Nabeel yace tunda Kai ka zabi soyayya a Kan Ilimi wallahi ka sake turancin daka iya ma Sai ka manta ya kamata na nema maka lecturing sabo da ka dinga Kara ilimi,Zama baka buda kwakwalwa ba kyau,Nabeel yace nifa Aiki na ya ishe Ni dan Allah Affa,yace ai sai kayi ta Yi dan banzan yaro Kai sai aure dan Degree ma da kyar ka Gama to sai na siyo ma littafan turanci kana karatu sabo da shi yare idan ba a Yi mantawa ake,to Kawai Nabeel yace a ransa yace duk turancin da nake ji sai na damu kaina,Amma Haka Affa ya ebo Masa manyan littafan darusan turanci manyan grammar Wands yake koyawa dalibai sunfi goma wasu duma duma masu uban girma yace ka dinga bita Kuma Zan dinga maka Exam na gani kana karantawa ko a'a,Basma tana ta dariyar Affa tace yawwa Affaa kaga ya dinga koya min Nima Affa yace hakan yayi kyau karki biye Masa ki Tara ilimi ko kina dakin miji Tace to Affa,sama ya haura part dinsa ya barsu. Hamida tunda Nabeel ya tafi ta fara tunaninsa tana tuna yanda ya dinga kula da ita da,idan ta tuna abinda ya Mata na love sai Murna dafarin ciki su kamata,duk yawanta da rashin tunanin Yaya kyakyawa ya hanata sukuni duk yan gidansu mamaki suke,Hamida Nan ta Gane ba Yan dubu dubun Nabeel take so ba shi take kauna sosai,idan ta tuna cikin sambatunsa yace Yana sonta zai kaita birni sai farin ciki ya mamayeta,wajen Sakina taje tace Sakina wallahi son Yaya kyakyawa nake na Gane ba kudinsa nake so ba,Sakina Tace yau mun boni Anya Hamida zai so ki Kuwa? Hamida Tace zanje na Kira wayarsa ai Sanda Yana min wannan abin Dana Baki labari yace Yana so na zai kaini gidansa,Sakina tace ahhhh to da gaske yake kije wajen Kira na kudi a kauyen Nan yanda ba Wanda zai San Kuna waya ki nemeshi. Hamida da shagwaba cikin muryar kuka tace wallahi Ina sonsa Sakina kewarsa nake,tunaninsa Yana azalzalata a Raina dole naje daga Nan ta kwashe da gudu sai business center Dake kauyen,Ashe Nabeel number tsohuwar Telephone dake palonsu ya Bata Wanda yanzu ma ba a kulata,Don baya so ko a waya ya sake Jin Hamida,yasan idan zata Kira sau dubu Mimi zata samu ta daga telephone din shi baya kusa,Ita kanta Mami Bata fiye kula Wayar ba,wajen Zaharaddeen ta karasa Wanda suke cewa Deeni me waya. Notumber ta bashi a takarda tace ungo Deeni Kira min number Nan sauri na matsu naji muryar Yaya kyakyawa,Deeni yace ah Hamida yau Kuma waye Haka Tace ba ruwanka karka bata min lokaci sauri nake naji shi,Deeni ya Danna number tana ta ringing ba a daga ba lokaci ba kowa ma a palon,ko masu Aiki suna kitchen,yace tana ringing ba a dagawa Hamida Tace dan Allah sake Kira kayi ta Kira nasan zai daga idan ya gani yasan nice Hamida nake Kira,Deeni ya bude baki yace bazai gane kece ba tunda bada number dinki Kika Kira ba number ta zai gani,Hamida tace karya ne bai Sanka ba ni ya sani Yaya kyakyawa Nawa ne ni kadai, ni kana Kira yasan nice Hamida nake Kira zai daga,Deeni yace baki gane ba tunda a wayata aka sa number aka Kira number ta zai gani,Hamida bata ganewa Sam tace karya ne na rantse da Allah ya san nice zaka kwace min Yaya Kyakyawa ta fashe da kuka, iya yanda Deeni yaso ya ganar da ita ta kasa fahimta ita tunda ta Kira dole yasan itace. Deeni yayi Dialing number yafi sau ashirin ba a daga ba,Har gajiya yayi ya idan ya Danna waya sai ya Bata ta Kara a kunne taji wayam ba a daga ba,Tace sauri ka sake dannawa zai daga nice fa Hamida ya Sanni,wasu sunzo zasuyi Kira Hamida ta Hana kowa ga Wayar ba a dagawa,Deeni ya hayayyako Mata da masifa ki jira sai wasu sunyi Kira baza ki kashe min ciniki ba,Hamida Tace bari Zan jiraka ta koma gefe ana uwar Rana amma ta zauna a kasa tana jira har sai da Suka hama sannan ya Kuma trying yafi sau goma ba a daga ba yace kije gobe ki dawo a gwada ko zai daga,Hamida ta fashe da kuka ta durkusa a kasa tana rokon Deeni tana magiya dan Allah Deeni ka taimaka min Dan Allah ta rushe da kuka,Deeni ya lallabata akan zai gwada idan an daga zai kawo Mata Wayar sai lokacin ta hakura tana zubawa Deeni godiya ta tafi gida. Deeni yace jaraba wannan waye take son magana da shi Haka,washe gari tayi Shirin makaranta da Uniform sabo da tasan yace ko ya tafi ta dinga zuwa makaranta Kuma ta dinga karatu ta cika alkawari makaranta Akan lokaci boko da Islamiyya sabo da Nabeel ne yace. Ana taso su daga makaranta da uban Rana direct ta zarce wajen Deeni Nan ma ya gwada yafi sau dari tana ta ringing ba a dagawa,tana ta jin yunwa amma Haka tun tana iya tsaiwa har ta samu ta zauna,Deeni yaga ta bashi tausayi lemonsa na kwalba ya Bata ta shanye yaci gaba da gwada Mata har wajen magriba Haka ta koma gida jiki a sanyaye,washe Gari da kuka ta tafi gidan su Sakina,Sakina Tace lafiya? Tace Yaya kyakyawa ne ta sake rushewa da kuka Tace Ina ta gwada wayarsa yaki dagawa,yasan bazai daga ba ya bani number,Wallahi Sakina Ina sonsa na rantse da Allah bani da sukuni sai tunaninsa,Sakina taji tausayin kawarta sai Fara lallashinta Tace watakil Aiki ne ya Masa yawa zai daga ne kinji kije a Kara gwadawa Tace to ta koma wajen deeni da Yamma sanye da uniform na Islamiyya,Nan ma an gwada ba a daga ba,lokaci Mimi Wayar ta isheta da Kara sai ta duba taga kullum Kira Kamar hauka Kuma ikon Allah sai bata nan ake Kira ko masu Aiki basa wajen ake kira shi yasa ba a dagawa tunda ita ko yaushe tana fita wajen aiki,Tace ko waye oho Haka ta ajiye waya bata Kira back ba. Nabeel Kuwa ya manta da wata Hamida ma a duniya,Deeni dama yayi Saving number cikin dare 12am ya gwada Kira lokacin Kuma Nabeel ya dakko ruwa kenan zai haura sama yaji waya tana ta ringing yace waye Kuma Haka cikin dare sai yaje ya daga,Suka gaisa yace dama Hamida ce take zuwa Kiran number dinka Muna ta Kira kullum ba a dagawa yanzu karfe Nawa za a dame mu da Kira sai Kuma yace ohhhh Hamida ta kauyen Hamdala Adamawa? Deeni yace ae,yace Fine ya take? Deeni yace lafiya Lau take yace okay karfe Daya ka Kira lokacin na dawo daga office,Deeni yace to Zan fada Mata na gode ya kashe,Nabeel ya kalli Wayar Yace Hamida rigima dama Bata manta Dani ba Baki ya tabe tare da haurawa sama. Hamida Kuwa tun tana zuwa har an kwashe sati ba a dagawa har ta hakura ma da kira,an tasosu daga makaranta Deeni ya hangota tana ta Wasa a hanya tana shirme,Kira ya kwala mata Hamida Zo,ai tana ganin Deeni ta famfaro da uban gudu tana zuwa yace jiya Wanda kike Nema ya daga na gwada Kira da dare yace karfe Dayan Rana ki Kira gashi har karfe biyu tayi Ina ta nemanki Ina makaranta,Ai wata uwar raruma da cafka ta kaiwa Wayar Deeni,yace ki nutsu tsaya a Kira ai ban Danna number din ba,Tace kayi sauri Deeni ya Danna number Kiran duniya tana ringing ba a daga ba,Hamida harda karbar Wayar ta Kara a kunne da wani style ta zauna a jikin bishiya har ta katse Karo na bakwai ba a daga ba,A fusace ta Mike Tace wallahi na hakura nayi zuciya har abada bazan sake kiransa ba,ta juya ta tafi tare da yin ball da kujerar Deeni ta Zama Yana tsaye ta hankade shi ta wuce tace dakai da Wayar Allah ya tsine muku shegu asararu har ta bace tana dannawa Deeni da Wayar zagi kala kala,shidai da kallo ya bita Kawai. Yaya kyakyawa Yana ranta Amma ta dauki alkawarin har abada baza ta sake gwada number dinsa ba,Kuma taci gaba da zuwa makaranta, Assignment aka basu na maths ta fito tsakar gidansu tana so tayi Amma ta kasa Bata iya ba,Tace na rasa wannan jaraba ta X kullum a aji ace 2a,2s,2d su kullum a aji suna Nan 2a is i kwantu (=) kaza Amma jaraba x kullum sai ace a Nemo x,find x ta daki littafin da masifa Tace Wai gidan ubanwa x take zuwa ne,x Ina Kika tafi gantali ki dawo na saki a rubu a ganki shegiya munafukar banza ke kullum a munafunci kike gidan ubanwa kike zuwa ne xxxxxxxxx ta furta da karfi,Sulaiman ne ya fito yaga shirmen da take. Yace Mene?Tace kaga Assignment aka Bamu kullum a aji sai kaga 2a,2s da sauransu suna ta hutawarsu a a class a Kan Allo Amma kullum sai ace a Nemo x,find x gidan ubanwa take zuwa Dan Allah Sulaiman Ina take zuwa ne? Rankwashi Sulaiman ya zuba Mata yace banza kawo na koya Miki simple Abu,ance 5a-2a= me Kika rubuta a gaba ban Gane ba Nan kince find x baki copying dai dai ba Tace ai 3 ne Nan,yace to sunce find x Tace ai shine nake nemanta Ina take zuwa ita? Ko wani garin Zan je na nemota? Wai baza ki saurara na koya Miki ba,Shuru tayi tare da kurawa littafin ido Nan Sulaiman ya koya Mata da kyar ta gane Tace abin ne Ni kaina juyawa yake bana fahimta amma ya zanyi tunda Yaya Kyakyawa yace nayi ai dole nayi, Haka dai take ta zuwa school sabo da son Nabeel karshe ma ta gaji amma dai tana zuwa abinta Haka rayuwa ta kasancewa Hamida. Nabeel Kam soyayyarsa da Basma kullum sai gaba take biki na matsowa a Haka aka kwashe wata hudu biki Saura Yan satikai,lokacin Kuma Hamida tayi wani fari tayi kyau sai Yawan bacci da ci Kamar gara yanzu zata ci abinci yanzu zata ji yunwa,ga cikinta da taga Yana ta kumbura bata San dalili ba gajiya tayi da kumburar da yake ta samu Sulaiman Yana buga Game a waya tace Yaya Sule,yace Mene ne Fadi tace wallahi kaga cikina kullum kumbura yake na rasa dalili tunani na ko Kashi ne a ciki Amma Kuma banga canji ba Amma kullum wallahi kumbura yake ko wata cutar ce tana magana tana bubbuga cikinta,Karima lokacin tazo yinin gida daga birni ba Wanda ya kawo komai, Sulaiman yace kina cin uban abinci Haka Kamar jaka ba Dole cikinki ya kumbura ba karki raina min hankali. Hamida Tace abin Nan wallahi bana lafiya bane ta tafi wajen Karima Tace sister bani da lafiya Kinga cikina kumbura yake,Karima taji tausayinta Tace karki damu sis Zaki warke kinji Tace to ta wuce daki a sanyaye,bayan ta tafi Karima tace anya Kuwa ba ayar tambaya a wajen Hamida Yaya? Sulaiman yace ke ku rabu dani ke shirmen Hamida ne baki sani ba,Shuru Karima tayi ta share itama,Hamida Kuwa kullum bubbuga cikinta take tana tabawa taji yayi tauri ya kumbura,wajen Sakina taje tana zuwa tace Sakina Fara kawo min abinci da yawa,Sakina tasan yanzu kawar ci take da yawa a tire ta zubo Mata shinkafa da Miya Hamida ta fara ci ko spoon a gefe ta ajiye shi Kamar wani zai kwace haka take ci,ta cika naki da shinkafa Tace Sakina kin San yanzu cikina kumbura yake kullum na rasa dalili ga uban ci,ga bacci na fada a gida ba Wanda ya saurareni,Sakina Tace kodai Yaya Kyakyawa kike kewa? Cikin Fushi Hamida tace dan Allah na rokeki Kar ki sake zancen Yaya kyakyawa a gaba na bana so,Indai kina so mu shirya bana son zancensa mutumin da in an Kira bazai daga ba ya manta dani,Nima so nake nayi rayuwata karki sake min zancensa. Sakina Tace kiyi hakuri,Hamida taci gaba da cin abincinta tana danne son Nabeel Amma Ina sai hawaye zirrrrrrr....zuciyarta ta karye sosai sai kuka wiwi Wanda Sakina bata ji dadin hakan ba,kwantar Mata hankali tayi sannan tayi Shuru tana cin abinci tana ajiyar zuciya tace me danwake ta fito Kuwa Zan biya na siya,baki bude Sakina tace baki gama da wannan ba kina tambayar abinci Anya lafiya Kuwa,Hamida Tace nace bani da lafiya kullum ci nake karawa ga cikina na girma ba Wanda yake saurarata bare a kaini asibiti yanzu ma fa na Fara Jin kamar Abu na motsi Sakina tayi Dariya,Sakina ki saurara wallahi ba Wasa nake ba,Sakina Tace ko micijin cikine ke damunki? Tace watakil Haka Suka gama ta biya ta siyi danwakenta duk cikin kudin data tara Wanda yake bata. Kafin ta shigo gida sai da ta siyo lemon kwalba da bread kafin a Gama girkin dare,Ummi tana ta mamakin abin bmma bata kula ba ko kadan,abu kullum chi gaba yake abin na damun Hamida,ta gaji ta iske Ummi tana wanke wanke Tace Ummi,da masifa ta juyo mene Kuma? Tace Kinga wallahi kullum cikina girma yake karawa Kuma sai naji ana motsi a ciki Kamar ana fada sai naji rududu ana fada a ciki sai naji dam daram sai naji dam dam,daram,sai naji Usha usha,Ummi ta firgita ta Mike tsaye tare da furta duk a cikinki ake wannan hargitsin,Hamida da sauri tace uhm... Ummi Tace bude cikin dan ubanki na gani,da sauri ta Bude Mata ta Kare Mata kallo sannan ta Danna marar Hamida na take ta saki ihu,Ummi sai ta Dora Hannu aka tace mun shiga Uku Hamida....Dan ubanki Hamida Ciki ne Dake,Hamida ta Lula tunani Tace Yaya kyakyawa ne na tunaaaaaaaa,Ummi ta kurma ihu Tace Shike Nan kin tozarta mu a idon duniya. Hamida ba Wani shakka ko kunya tace lokacin da naje hotel wajensa ne ban taba ce muku Ina zuwa ba sabo da idan na fada nasan Zaku hanani shi yasa nake zuwa a boye,Amma sau daya Yaya kyakyawa yayi min nidai ya fara tattaba min dangerous part Ina Jin Dadi na biye Masa baki gani ba Ummi ya dinga taba min Nono wallahi Dadi tunba ya fara shansu ba Ni Kuma sai na kasa hanawa har ya samu ya sa min wani Abu me zafi ya fara Haka kingani ta dinga gwadawa Ummi Tace Ina Jin zafi Ina Jin Dadi Dadi,nace Yaya kyakyawa ka daina yace da Dadi,Kuma yace Yana so na zai Zo ya daukeni mu tafi birni, har ma yace Ina da dadi, Takaici da kunya ya kashe Ummi tace yaushe yace Yana sonki tace Sanda Yana yin abin ya fada min ta furta ko a jikinta Kamar cikin sunna har wani Murmushi take. Ummi sai ta Nemo Napep ba Wanda ta gayawa tasa Hamida a gaba har asibitin Dake birni akayiwa Hamida test har sau Uku an tabbatar ciki ne na wata hudu,suna dawowo ta Kira Karima Tace tazo gobe da meeting lallai,Sannan ta sanarwa su papa tare da bashi result ya gani,washe Gari da safe Karima tazo sai Suilaman, Papa da Ummi,Papa yace Hamida duk naji komai,Hamida Tace kayi hakuri Papa mun tuba ban San Haka ake cikin ba,Ummi tace dabbar Ina ce Baki San ko ya aka samu matsala ba ciki Zaki dauka mahaukaciya dabba,karamar yarinya ce ke a'a tunda yarinya ce ke mahaukaciya Zo kici gaba da Shan Nonon uwarki. Sulaiman yace yanzu ta Bamu number a kirashi Kuma dan Allah mu binne zancen Nan iya mu Kar wani ya fidda Maganar nan ta bazu a Gari abin kunya ne, Karima har da kuka ta tashi Kawai ta koma birni gidan mijinta,Yaya Sulaiman shima dakinsa ya shige ya rage Saura Papa da Ummi,Ummi tace munafuka kullum ki damemu da Yaya kyakyawa Yan Yan Yan.... Ashe abinda kike kenan. Papa yace Dan Allah Abu ya Riga ya faru kema Hadiza kinfi kowa laifi bakya sa Ido a kanta na fita Ina Nema Ni Zan zauna na lura da gida,mace itace jigon tarbiyyar Yara,da ace kin Mata tarbiyyar da haka baza ta faru ba,Amma kin watsi da ita ta taso Bata San komai ba a zamanin Nan ace Hamida kamarta Bata San Mene Zina ba,Ummi Tace ohhhh yanzu wato ta kwabe zaka dora min laifi sanda nace a lura kar ta dakko masifa me kace Nan Papa da Ummi suka Fara fada,Hamida da sauri tace duk kowa yayi Shuru Dan Allah ta dafa kafadar Ummi da Papa tace karku yi fada akan abinda nayi,Ummi kiyi hakuri ba fada ku zauna lafiya kamar yanda na sani na dauki laifi,zanji da komai kuyi Hakuri na dauki kaddara magana ta Kare ba abin damuwa bane,Papa yace bani number da ya baki,Hamida ta dakko number tace gata Tsautsayi ne Papa wallahi Yaya kyakyawa ba fan Iska bane Kawai tattaba Ni ya Fara na Fara Jin dadi daga Nan ya as min Abu.. Papa ne ya make Mata Baki tayi shuru,Ummi Tace kaji da kunnenka fitsarar da take iya fada ku karke na barku Kai da ita Ummi ma ta fada dakinta tabar Papa da Hamida suna kokarin kiran number Hamida tana cewa nasan kana so na Papa ka yarda dani zaka yarda da zance na wallahi sau Daya mukayi,shima cewa yayi Ina da Dadi...Papa ya sake bige Mata Baki Amma bata hakura ba Tace Naga duwawunsa ma fari tasssssss Papa tana dariya,yace Zan tattakaki ,sannan tayi Shuru. Lokacin Basma an fito Palo ana kallo Kamar gidan ubanta ko kunya kullum ana gidan Saurayi Dan Kawai ana da dangantakar da abota da maman saurayi,waya tana Ringing ta Mike ta daga yace hello da iyayi,Ai Kuwa Hamida Tace aloo...aloo...Yaya kyakyawa nice Hamida ta kauyen Hamdala dake Adamawa samu ciki,cikin gaske sabo da abin Nan da ka min a hotel...aloooo Yaya kyakyawa Ina da cikinka tana fada tana wani Jin Dadi tana farin ciki taci gaba Ina da cikinka na wata hudu abin Nan daka min a hotel to ciki ya shiga na samu cikinka na gaske gashi danka Yana ta motsi yace a gaisheka...Basma tasan sunan garin da yaje aiki tabbas wannan ba karya sai ta sandare a Nan. Papa ne ya kwace wayar yace nine Baban Hamida na kauyen Hamdala Adamawa ki fadawa dan uwanki 'yata tana da cikinsa ki isar Masa da sako,Basma sakin wayar tayi jiki na rawa hawaye na bin fuskarta mami tazo ta sameta,Tace lafiya? Nan Basma tana uban kuka ta zayyanewa Mimi komai itama Mimi sai kuka,Affa na shigowa Mimi ta sanar Masa komai. Yace bari a Kira Nabeel Affa ko a jikinsa, Nabeel Yana Office bai San me ake ba ya dawo yayi parking ya shigo Basma ba Hakuri Nan take tarbeshi tana kuka Tace mayaudari azzalumi,mazinaci to ka sani Hamida ta kauyen Hamdala Adamawa tana Nan da cikinka na wata hudu,azzalumi macuci,mayaudari,mazinaci,bani ba Kai na fasa aurenka,Shima Nabeel Yana ji ya tabbatar akwai matsala hankalinsa ya tashi karya ta kare palon ya Koma ya samu Mimi Na sheka Kuka,Affa yayi tagumi. A gabansu ya durkusa Mimi tace kayi mamaki ne marar tarbiyya, yanzu tarbiyyar kenan duk addinin naka to sun bugo waya,Affa ya dagawa Mimi hannu tare da cewa dakata,Nabeel ya Kira sunansa ya amsa a hankali yace tambaya Zan maka tsakani da Allah fyade kayi ma yarinya ko Kuwa dama itama tanso kuka aikata? Nabeel cike da kunya yace ba fyade bane tana so,Affa ya saki ajiyar zuciya tare da furta Alhmdllh wannan to da love za a kirashi,mu a matsayin mu na masu ilimi Love da ace fyade kayi da an samu matsala amma tunda tana so ya Zama love yaro ya Zama jikina,Kuma Ina sonsa. Mimi tace haba Affan Fadila sai kace ba musulmi ba,yaro ya aikata laifi Babba kace love ne, Affaa yace sai ya shirya Aurenta in ta Haihu,Kuma zamu dakkota a gobe Matukar kayi aure a gidanka zata zauna har sai ta Haihu ka aureta muma baza ta zauna a gabanmu ba sabo da gidana na mutane ne akwai tonon asiri a gidan aurenka zata zauna da ku tana haihuwa dole ka aureta. Nabeel ya zaro Ido hankalinsa ya tashi yace Ni gaskiya bazan iya auren matar da bana so ba,gata Yar Kauye,Bata waye ba,gaja da ita,Kuma ga rashin ilimi,kasan da hakan ka kwanta da ita ka Mata ciki,ai tun kafin ka yara da ita ya kamata ka tuna wannan Affa ya furta,karyar banza yake cewar Mimi kasan da Haka ka kulata algungumi,Ni dai Dan Allah a dakkota na yarda ta Haihu amma babu batun aure idan ta Haihu sai ta samu Wanda take so ta aura,Nima ba Sona take ba,Affa yace tunda kace haka shike Nan zamuje da Kai a rufawa iyayenta asiri mu dakkota Amma wallahi baza ta zauna a Gaban mu ba sai dai ku zauna gida Daya da Kai da ita da Basma. Basma tayi zuciya amma haka ya dinga bata hakuri har ta hakura zata aureshi a Hakasu zauna tare da Hamida kafin ta Haihu ta koma Gidan Affa,ranta Kuma ta kulle cin uban Hamida idan tazo. Basma washe Gari ta koma garinsu,ranar Kuma Affa da Mimi sai Nabeel suka tafi dakko Hamida tunda sun Kira Papa sunyi magana sosai shima yaji badi baya son ya tozarta a Kauye. Abin Mamaki Nabeel sai kace Bai San Hamida ba Haka ta fito sanye da katon Hijab har kasa ta tsuguna ta gyaida su ta zaci Nabeel ne na da tace Yaya kyakyawa Ina yini ka tafi ka barni tun Sanda kamin abin Nan ka tuna? Papa ne ya galla Mata harara sannan ya shigar da su Nabeel Palo aka sauke su da ruwa da abinci Hamida ta kawo musu tana rawar jiki sai Mimi da Affaa ta birge su yanda duk akan dansu take haka bayan abinda ya mata maimakon su ganta cikin damuwa sai Suka ga gidan ba Wanda ya nuna ko a Fuska sun dauki kaddara,Hamida kusa da Nabeel taje Yana Kan kujera ta zauna a saman hannun kujerarsa sabo da ta Saba da shi Su Affa suna magana da Papa da Ummi,Hamida tace Yaya kyakyawa cikinka ya girma Yaya kyakyawa in Bude kaji kamshin danka,Nabeel kunya ta sake rufe shi sai kunyatashi take zancen ma baya so na cikin amma ta dame shi da Iskanci a gaban Iyayensa. Mami taga alamar Yarinyar tarbiyya ce na Uwa bata samu ba shi yasa ta Zama wata kamar bata da Kan gado,Nabeel ne ya harareta tayi Shuru Wai,Tace to nayi Shuru bari na baka labari na Bayan tafiyarka yo ba sai cikina ya dinga girma ba kullum kullum,nace a'a Mene Haka ciki ka koma Amma yaki ji girma yake kullum gashi in ta cinye abinci yo ba sai motsi ba naji Ana hargitsi da yamutsi a cikin kina,Su Suna jinta dariya ta basu tace yo Kuma abu yaci tura naji Kura na tashi Ana Kai ruwana Ana wata walankeluwa a ciki,sai aka koma sufa a suuuuuu sai daram dam dam,Nabeel dariya ta kamashi ya danne da kyar su Mimi sai dariya suke su Kam,Hamida Tace Wallahi sai na Fara bacci na me dadi sai a farkar dani naji Ana birgima da alkafira a ciki,Mimi tace to munji dakko kayanki mu tafi a can birni Zaki haihu,Dama Papa ya fada Mata komai Murna fal ranta,Papa yace Kar ta dauki komai a can za a siya Miki duk abinda kike so ai Kuwa tace to,taje ta canja sabon doguwar rigar Lace dinta da Papa ya dinka Mata a birni,dinkin buba ne bazai takura Mata ba sai ta sa hijab dinta har kasa ta fito Tace na shirya,Dama nayi wanka Papa ya fada min komai,Mimi tace bakya shafa ko powder kenan?Ummi yace wannan shashashar ce zata Yi ai bata taba ko shafa man lebe ba,wanka Kawai take tasa kaya,Sulaiman yace gayu ai ya ma Kare dama ba Yi take ba bare yanzu data Zama bazawarar dole,kiyi a hankali dai can birni ne,Sule sule Sulele yayiwa Sulaiman Waka tasan ya tsani ace Masa Sule shine take tsokanarsa,Har mota suka rakasu,Baya ta shiga Nabeel ma ya shiga baya gefenta Mimi tana gaba Suka dauki hanya,Nabeel yace yanzu a mota zamu koma gaskiya Ni jirgi zanbi,Papa yace mu a mota zamu dawo Muna tafiya Muna kallon Gari ko 'yata,Hamida tafi so tabi Nabeel amma ya daure Fuska sai Kawai Tace ae, airport suka sauke Nabeel yabi flight sure kuma Suka tafi a mota,Hamida sai labarin Kauye take basu tana kalle kalle a mota,tana ta Bawa su Affa Dariya. Ko ya akayi tafiya sai an siya Mata abinci ciye ciye take a mota kafin suje Kaduna Nabeel ya koma gida har yayi wanka yaci abinci yana hutawa sai dare Suka Iso gida Hamida duk ta gigice tana kalle kalle,taga hadadden gida sai kallo bata taba ganin gida me kyau Haka ba sai yau,Nabeel Bai fito ba bacci ma yake abinsa. Sharhi fans AsmaBaffa [6/28, 1:46 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 5 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne NO LOVE THUWAIBATUL ASALAMIYYA RUKYALY SHAHRY AYUSHER UMAR YARO FATIMAMUHAMMADINUWA MADAME LAMINE AYEESHART MMN MEENAT MAMAN AHMAD UMMU KHALEEL SAFEEYAT MAMAN YUSRAH Hamida Tace kallo sai gobe da safe tana Shiga ciki ta daga Kai sama tana ta juye juye baki bude haka tayi sai da Mami ta jata Sama part dinsu tace kin fiye kallo muje kiyi wanka kici abinci ki huta. Haka ta kaita wani bedroom tace wannan ne dakinki ta nuna Mata toilet a ciki tare da gwada Mata komai sannan ta barta ta tafi nata dakin,Wanka tayi ta maida kayan jikinta ta fito,Mami ce ta kawo Mata wasu Abaya har kala Uku sababbi tace cire kayan Nan kisa wannan sabuwa ce tsaraba nazo dasu naga zasu miki,karba tayi Tace na gode Allah ya saka,Ni Guda ukun ma sun isheni bana son wani Kaya a Bari sai na Haihu a siya min naci bikin suna da sababbi,Mami tace to tunda jaka kike bukata ai ba matsala,Yar Aiki tasa ta kaiwa Hamida abinci har daki,Hamida ta kalli Yar aikin tace ke iceko Kun rage min abinci cikin dare nakan tashi cin abinci,me aiki tayi Dariya Tace akwai a flask Mimi tace a ajiye miki tace yawwa ta zauna ta fara dura abinci ta cinye tas. Ta fito tace bazan lamunci wannan dan plate ba ke me Aiki ta kwala Kira Me Aiki ta fito yace Wai ya sunanki ne? Matar tace Asabe,Hamida Tace Sannu Asabetutuwayye, Asabe tayi Dariya sabo matashiyar budurwa ce,Hamida tace Karo min abinci Yar Asaballiye ,Asabe ta sake shako Mata plate,a Palo ta zauna tv nayi tana kallo tana ci ta zauna a kasa ta Mike kafafu kwanon a tsakiyar cinyarta tana ci,Nabeel ne ya dauro Alwala zai fita Sallar Isha Hamida ta kalle shi yanda ya zuba kyau cikin dark blue jallabiya kamshi na tashi,Bai ko San da zamanta ba ya sakko kasa,Hamida tace Yaya kyakyawa yaushe Zan Fara zuwa awo kaga ya kamata musan me zamu Haifa a fara siyayyar kayan yara Kuma Dan Allah ka siyo Masa gado me lilo,ita ko kunyar cikin shege bata ji sai kace wacce ta girma a kudu garin arna,wato son cikin ma take haka ya furta a ransa ko kallonta baiyi ba ya bar palon. Hamida ta turo lips gaba tana gama cin abinci jaririn cikinta ya hau motsi tace jaba dan babansa ka dinga tausaya min kaji,yaro Yana motsi abu ya ishi Hamida haushi taji da masifa ta shafa cikin Tace wanne irin Iskanci ne wannan Dan wulakanci da rashin mutunci sai ka dinga hanani sakewa kaci Babanka Yaya kyakyawa, nace ubanka Yaya Kyakyawa,Yaro Yana ta motsi yaki ji,Nabeel ya shigo Palo yaji tace Kai Dan maye dan giya dole kayi ai giya muka Sha aka sameka dole ka dinga tambele na gane ka bugu da giya shi yasa,to dan uwarka Ni Hamida makwalwa Daya na Sha Babanka shine yasha cikin cup ta Nan ma gado tambele da maye. Wani zunkuli taji ta saki Kara tace wannan shine hukuncin Allah ya sauka a kaina fushin Allah ne ya jarabceni da yaro Dan Giya ba komai Allah na tuba,sai da Nabeel ya hama Jin haukar Hamida ta bashi Dariya sai gashi ya shigo Fuska ba Rahma ya zauna a kujera shima, tana sani tace yawwa Alhmdllh ga babanka ya shigo Yaya kyakyawa ta Kwabe Fuska zata Masa kuka tace wallahi giyar da Muka Sha tabi jinin yaron Nan tambele yake Kawai Yana tayi Marisa a ciki na,Tayi Marisa ta Sha Kafso Kawai yake, dariyarsa ya danne shima haka Kawai yaji Yana son dansa,yace tashi ki dan jijjiga shi,Mami ta fito kenan taji me Nabeel yace jijjiga yaro a ciki lallai Nabeel,Mami labewa tayi taji yace Yi Masa Waka,Hamida ta fara Dan tsalle tana baaaabanka Yaya kyakyawa yaci Dadi yaci bala'i,Nayi cikin shege a garinmu nayi cikin shege... a garinmu tana Waka harda tafi,Mimi yau ta tabbata wannan Yarinyar bata da hankali,Nabeel ta kalla tace taso muyi Enter Yaya,Harara ya galla Mata ko a jikinta tace Yaya ka tuna abin Nan da mukayi a hotel Ina cewa zafi tunda na samu ciki shi nake so a Kara min Kullum da kyar nake bacci,Ai zumbur Nabeel ya Mike ya rufe Ido da bala'i yace idan ke dabba ce jahila Ni Ina da hankali da dinma tsautsayi ne na tuba ga Allah,sannan baki da ajin da Zan saurareki dakikiya jahila bagidajiya,Kinga Nayi kala Dake ko na Dace da ke? To na kusa aure ki sani ba Ni ba ke karki sake min magana in ba dole ba, Fasika marar tarbiyya,Hamida bata taba sanin haka yake ba sai yau sai tsoronsa ya shigeta Amma sabo da Bata ji kallonsa tayi ta Masa signa da Ido tana kashe Masa Ido Daya tare da daga Masa gira. Palon ya Bari fuuuu cikin Fushi Mimi taji Dadi sabo da bata son komai ya sake faruwa tunda taga Hamida bata da hankali tabbas ba lafiyayya bace kwakwalwarta da motsi Tace Allah yasa ki Haihu sai mu maida ke garinku ki karata a fili Mimi Fitowa tayi ta ga alamar taji zafin kalaman Yaya kyakyawa tace je ki kwanta,Ranar Hamida bata Yi baccin kirki ba tana tuna maganganun Nabeel da ya yaba mata,tunda take a rayuwa yau ne karon farko da aka yaba Mata magana taji zafi har ta kasa baccin kirki. Washe gari Mimi tace kaje ka Kai Hamida awo ya kamata ta fara ganin likita,to Kawai yace zai fita Office ya dau mayen wanka Hamida ta kalle shi kadan a ranta tace ashe acan ba Wani gayu yake ba a Nan yake gayun,Hamida tasha abayarta ta tsala kyau sai ciki ya girma ya fito das dashi,Ko data gaisa shi ko amsawa baiyi ba Haka ta fuske da fara'a Tace muje kayi kyau,wani uban Tsaki ya buga Mata yayi waje tabi bayansa tana Siiiiiiiii minti Daya gaye siii...sii....Yana juyowa ya kwasheta da Mari ya nunata da yatsa yace wallahi duk ranar da kika sake kulani sai na kasheki na fada Miki last warning masu Aiki suna kallo,Yana zuwa mota ya Bude ya ebo kudi ya Watso Mata dauki ki tafi a kafa Kika fadawa Mimi bani na kaiki ba sai na yankaki, a kafa Zaki tafi har sai kinfita daga estate dinnan sannan kije ki Sami taxi stupid girl ya shiga labebiyar motarsa ya Kara gaba,Hamida tayi Dariya ta kwashi kudin ta samu me gadi yace dan Allah muje ka rakani asibiti Zan fara ganin likita. Me gadi Musa ya bita Suka tafi babu Wanda yasan zancen a gidan sai iya su Mimi amma Hamida suna tafiya da Musa dake matashi ne suna ta Hira a kafa tace Kai Musa cikin shege aka min fa a kauyen mu Musa ya kwala ihu tare da dora Hannu a Kai yace Ashe ke Yar Iska Ce Yar uwar su Mimi ce dole a kawo ki birni Ashe abin kunya Kika tafka yanzu sai Kika bude Masa cinyoyi wanne shegen ne wannan? Tace Yaya Kyakyawa ne,Oganku Nabeel,Musa ya sake kurma ihu yace shege karamin Alhaji ashe Kawai harka yake bajewa,yanzu ke in Banda shashasha ce sai ki bude Masa ai gashi Nan ya cuceki kece a ruwa Musa ya dinga tir Yana tsinewa Nabeel,yace nima da Zaki bani sai na Dan wake. Da sauri ta daure Fuska Tace koma gida bana so ka rakani zanje da kaina,Ashe kaima Dan iskan ne wallahi Zan durawa iyayenka zagi koma gida ka barni,Musa ya tsaya cak ita Kuwa turtsi turtsi taci gaba da tafiya ga Rana ga nisa ta hada zufa Musa yace to kardai ki hadu da wani Yaya kyakyawan ya Kara Miki ciki na biyu ki dawo Mana da double ciki,Tace sai dai ayiwa uwarka ba dai Ni ba,Musa Yana ji ta fara danno Masa zagi ya juya sai gida ita Kuma da tambaya take har asibitin Gomnati aka Mata duk abinda ya Dace ta dawo gida duk ta jikata haka napep ya ajiyeta ta bashi kudi ta dawo da takardunta da magunguna,Mami ganin da Nabeel Suka fita ko duba takardun bata Yi ba tace ya cikin naki tace komai lafiya ga magunguna an bani sunce duk laraba na dinga zuwa sai Nan gaba zayi min sauran test,Mimi tace a kula da Shan magani a ka'ida Tace to,Sai da taci abinci ta watsa ruwa sannan ta fita kallon gidan tana jinjina kyan gidan. Tunda Haka ta faru,Basma ta raina Nabeel Affa Yana Office din Nabeel suna tattaunawa sai ga Basma fuuuu ta Fado a gaban Affa har office taje taci kwalar Nabeel tace saura idan munyi aure ka dinga zagawa wajen karuwarka a boye ta zuba Masa maruka biyu tana zaginsa,Shi kuma sabo da yasan yayi laifi sai ya kyaleta. Affa yace baka haifu ba Lele mace tun baka aure ta ba tana cin kwalarka ta mareka,Nan take Affa yace wallahi baza ka aure ta ba na soke komai gwara ka koma wajen Basman kawunka Yar uwarka ta jini wacce zamu Haka mu rufe,Basma tace tafi nono fari ta kalli Nabeel tare da nuna shi da yatsa tace you fool sai na dau fansa zaka gani daga Haka ta juya fuu tayi waje.. Affa takaici yasa Kawai a daurawa Nabeel aure da Basma Yar dan uwansa tunda an gama kera Masa gida,Haka Affa ya sake rushe auren waccen Basma ya dawo da Basma Yar dan Uwa,da Yan Uwansa aka shirya komai,Suka rufe zance ko matansu ba Wanda Suka fadawa Haka Basma ta dinga murna dama tana son Dan uwanta duk da an fada Mata a sirri tare zasu tare da Hamida,Suka ce kaddara ce tunda tana sonsa tayi Hakuri ayi auren tunda an Gama komai,Haka aka daurawa Nabeel aure ba shiri Wanda shi Kansa a cikin nishadi yake zai auri Yar uwarsa dama suna shiri da Basma sabo da shi gani yake ai farko duk soyayya take da Basma Yar uwarsa da daya Basman,Dan ya rasa Daya ciki ba abinda ya dame shi Ana daura aure aka Kai Masa Amarya Affa yace tsuntsun da Yaja ruwa shi ruwa Kan duka Nan da sati Daya za a kawo Hamida ta zauna a gidanka Kai da ka Mata ciki ku zauna tare ka kula da Yar mutane har ta haihu,Bashi da zabi yasan yayi kuskure haka yayi Shuru shi yaji Dadi ma da aka ce ba sai ya auri Hamida ba. Basma tana mararin Ango shima Haka Bayan sun gabatar da Nafeela Suka ci abinci sannan sukayi Shirin bacci Amarya ansha kyau cikin kayan bacci gaba Daya Nabeel baya Jin wani sha'awar matarsa ya rasa dalili,Sam Sam baida feeling a kanta Haka ya tsinci Kansa,Haka abar tasa ma taki tashi tayi kwanciyarta lakaf abinta,mamaki da tsoro ya kamashi, Haka yayi wayo yace hutu zasuyi su baza suyi gaggawa ba Romancing Basma yayi sosai sai da ta gamsu Amma shi komai baiji na Sha'awa ba,abinda Ya daurewa Basma Kai kenan amma dake budurwa ce sai ta hakura,Haka suka kwashe sati guda sai dai romancing ya kasa komai Nan ya tabbatar baida lafiya,Basma ya fadawa gaskiya tace bari su Fara Neman magani yace to,Basma tace maybe Yar kauyen Nan ce Suka maka asiri,Nabeel yace oho Ni ban sani ba. Sati na cika Mimi da Affa da kansu Suka kawo Hamida gidan Nabeel sai Murna take ko banza zata dinga ganin abin sonta, Suka yiwa Basma da Nabeel Nasiha Haka Hamida ma,Basma sai kuka take Nabeel Yana Bata Hakuri yace karki damu na dan lokaci ne tana haihuwa zata koma garinsu ba sonta nake ba ke nake so haka ya lallaba Basma tace ba komai ai tana da amfani a gidan Nan ta Zama Yar Aiki na ba ruwana da cikin dake jikinta,Nabeel a ransa bai so Haka ba Amma ya zaiyi da matarsa baya son rabuwa da ita akan wata banza Hamida. Hamida tana jinsu ita ko a gyalenta Dariya ma take ta kalli Basma yanda taci kwalliya ta zuba kyau tana kamshi da gudu ta fada jikin Basma bayan su Mimi sun tafi,Ai Basma wani ihu da tsalle ta buga tare da komawa gefe tace oh my God Baby kana gani wannan kazamar ta taba min jiki,Ni ajikinki ce Dan uwarki nayi Kama da sa'ar ubanki,Nabeel yace ke me yasa jahila ce kalleki kazama ki hada jiki da matata kalleta fa,Hamida ta washe Baki Tace Naga tayi kyau ne gata kyakyawa ta H hadu shi yasa na rungumeta kina da kyau Aunty kin iya wanka,wata uwar tsawa ya daka Mata ke dalla rufe Mana baki,Basma tace Kinga kazama shiga kitchen gashi can akwai wanke wanke ki fara,in kin Gama kizo ki share ko Ina ki goge maza Kuma ki tabbatar yayi kyau,da Murna tana tsalle Hamida ta fada kitchen ta fara abinda akace dama ta iya tana Yi a gidan Mimi,tana gamawa Basma tace bazan iya cin abincinki ba Ina da me aiki,Hamida tayi Kamar zatayi kuka tace Dan Allah Zan dinga Miki girkin wallahi na iya a gida Ina Yi tace to ki gwada yau idan yayi Dadi sai na sallami me girki ta koma gidan Mimi dama daka can aka kawota.. Basma badai iya wanka da tsafta ba akwai Kam tasan makamar tsafta da gayu,ita dai Hamida tana son Basma birgeta takeyi Haka tayi girki sabo da Ummi tana sata girki a gida,Karima tana koya Mata na zamani,jullof din shinkafa ta dafa musu da nama ta shirya a dining,da sukaci Basma tasan yayi dadi amma sai tace bana son girki baki iya ba kwashe ki zuba a shara,Nabeel Yana gefe yace kema Honey Kya sa wannan girki,Hamida tace Wallahi karya kike na iya kawai hassada ce kafin ta rufe Baki Basma ta hankadeta ta Fadi ga ciki turus kuka ta fashe da shi,Nabeel har ransa Bai so ba amma Basma bata laifi sabo da shi Wai sonta yayi Mai yawa ne. Tsawa yayiwa Hamida dalla tashi mahaukaciyar banza,Hamida tana kuka da kyar ta iya tashi tace wallahi Ni ba mahaukaciya bace da hankali na kanta yayi zai mareta ta gudu dakinta,yau cikin dare Hamida ta fito ta nufi dakin auren Nabeel ta Fara buga kofa kamar zata ballata Yana rungume da Basma Yaja Tsaki tare da mikewa ya bude sai yaga Hamida tayi daura kirji a saman wata t-shirt,lafiya mene Kuma ya furta da bacin Rai,Basma ta leko tace ke Mene cikin tsakar dare?Hamida bata kula Basma ba Tace ahm Yaya kyakyawa wannan gadon ne yayi min Fadi Ni daya kaga fili fetal Haka nake birgima In gangara wannan corner na sake juyawa wannan corner me zai Hana kazo muje ka cike gurbin wajen Wallahi wani Abu ne yake min scrating a Dausayi na, Wai scratching take nufi,Ji yake kamar ya Mata dukan tsiya,yace Wai ke wacce irin mahaukaciyar jahila ce ne? Ni da ke min Dace? Da sauri Tace ae Mana abin da kamin wannan Zinar da mukayi wannan iskancin wallahi shi nake tunawa Ina Jin Dadi tunda na samu ciki abinda ka min nake so yanzu,Wani uban Tsaki Yaja Basma ta hankadeta baya ta Fadi sosai ta fashe da kuka,Nabeel Yana bala'i jahilar banza ya rufe kofs da sauri Basma tace come to me Baby I need you sabo da Nabeel Yana ta Shan maganin sha'awa Aiki tuni yake gwangwaje Basma da love kullum sai sun buga harka,Basma tana shafa sajensa da gemunsa Dan cut ,shi Haka Kawai baya sha'awar Basma sai ta bashi magani sannan,tace nasan kwana Nan Zan samu ciki sabo da Naga Kai gwarzo ne duka dauka kake ai yanzu Ina da ciki ma na sani Nabeel ya koma suka shiga farantawa juna rai abinsu. Hamida bata kukan bakin ciki bata tunani sai da aka kawota gidan Nabeel,cikin Daren ta fito wajen me gadi Sale suna tare da me sharar compound Inuwa sun Fara bacci Suka ga Hamida ta samu wuri ta zauna tana kuka sosai,Inuwa yace Allah sarki Matar Oga tana gallazawa Yarinyar Nan tausayi take bani,Sale Suma basu San wace Hamida ba,Inuwa yace ke Hamida lafiya kike kuka a wannan tsohon daren? Cikin kuka tace wai akan naji sha'awar Yaya kyakyawa shine naje nace abinda ya min na samu ciki ya sake min abin Yana damuna shine ya ci min mutunci ya zazzageni Yana min tsawa harda ce min Jahila,wannan mummunar matar tasa ta hankadeni na Fadi,Inuwa yace ban gane ba Nabeel ne ya Miki cikin?Hamida Tace ae tana kuka tace Kuma yanzu idan na tuna dadin abin nake ji shi nake so ya sake min Inuwa ya hangame baki duk da Bai Gama ganewa ba amma mamaki ya rufe shi haba biri yayi Kama da mutum,yace kiyi Hakuri Allah zai saka Miki koma ciki ki kwanta,ki dinga yawan Nafeela da karatun Qurani Zaki rage Jin sha'awar kinji?to tace tana sharbar kuka ta koma ciki takwanta tayi lamo a saman gado. Inuwa ne ya koma wajen Sale shugaban munafunci ya bashi labarin abinda yaji Hamida tace,Sale yace ai Kuwa gobe sai na gano gaskiya,Inuwa yace Sale Ni dai ba ruwana,Washe Gari Wednesday Hamida zata je awo da safe ta fito sanye da abayarta ciki Kato a gaba a Palo ta iske Nabeel Yana cike ciken takardu Basma tana saman cinyarsa, Hamida ta fito ya Dan kalleta Kamar ba itace jiya take kuka ba har ta manta da fara'a ta tsuguna a gabansa tace Yaya Kyakyawa Ina kwana? Lfy Kawai yace Tace yau ance...a'a likita jiya ta tambayeni tace Ina mijinki nace kana gida tace gobe kuzo ayi Miki scanning da antanital tace nazo da kudi ko na taho da Miji na nace bari na fada maka,Dama Hamida tuni ta fita harkar Basma bata ko Mata magana,Kura Mata Ido yayi har ta Gama yace okay ya zaro kudi masu yawa ya bata. Ta gaji da tafiya a kasa ga nisa kafin ta bar Estate din har ta hau main road sai da ta bari lokacin da Nabeel yayi Shirin fita Office Basma ma ta fito yau da ita zai fita zai ajiyeta a gidan Mimi idan ya tashi ya dakko ta,Suna Fitowa Hamida ta fito ba magana itama ta bude gidan baya zata shiga,Wata uwar tsawa Basma ta buga Mata Amma ko a jikinta har tasa kafa Daya Basma Tace sa'arki ce Ni da Zan hada mota dake Dalla malama fita ko so kike na Miki duka a Nan,Nabeel baiyi magana ba shi yasa Hamida ta koma zata Kuma shiga Basma ta hankadeta da uban karfi ta Fadi Nan ma ta saki kuka,Nabeel nan ya hau bala'i wa yace ki Shiga mota ki tashi malama ki tafi a kasa ki dinga Exercise yafi dacewa da lafiyarki ya furta ransa bai so ba, Ya shiga zai tuka mota Hamida bata hakura ba ta Mike zata sake Shiga ya fito a fusace ta arce cikin daki,sannan ya shiga Yaja mota Suka bar gidan,Ita Kuma ta fito ta fice a kafa har taje titi ta shiga Napep. Yau da Yamma likis su Nabeel suna ciki ta fito wajen masu gadi sale ne kawai Inuwa ya fita,Sale ya fara zolayarta Wai daga Ina kike ne?lokacin Nabeel yazo zai fito yaji Hamida tace daga Kauye aka kawo Ni Nan kasan Yaya kyakyawa ne ya min cikin shege a can shine akace idan nazo birni na Haihu sai na koma Kauye,Ai cikin shege ya min giya ya bani na Sha shima yasha Amma wallahi da Dadi kullum so nake a Kara,Kuma Yana Yi Yana Jin Dadi sai Naga ya kawo da wuri,Sale yace shege Oga Ashe baya tsoron Mata Kawai sha'aninsa yake Sha,Kai kalleki abinci me kyau Amma ta oga ce shi Kuma Yana wulakantaki abincin wani gubar wani,da Ni na sameki aurenki zanyi kalleki kyau iya kyau wallahi kinfi Aunty kyau da komai,Allah ya Miki Kira idan kin Haihu zanzo ayi Dani,Hamida tace wallahi ka rainani in banda Yaya Kyakyawa ya zubar min da mutunci wallahi Kai baka isa ka fada min Haka ba da tuni Kaine yaron gidana yanzu Amma ba komar rayuwa ce,Nabeel ne ya fito a fusace yace ke me kike fada Masa munafukai Kuna gulmata da gudu Hamida da sale Suka Ruga bayan katanga yasan Basu tafi ba ya leko yaji Hamida tace Kuma Naga Duwawun Oganku fari tassssssss ,wata ashar Nabeel ya duro musu Nan take Sale Ya fada bangarensu Hamida tabi ta kofar baya tayi garden da turtsetsen cikinta. Ko Sakina bata San me ya faru ba ance dai Yan Uwan Hamida sun tafi da ita birni,su kuma su Sulaiman suna Kiran Mimi da Affa suji lafiyar Hamida,Haka rayuwar Hamida ta kasance kullum cikin bakin ciki har cikinta ya shiga Wata takwas ya Girma sosai,kawayen Basma ne Suka Zo biki Kaduna Suka biyo ta gidanta su Uku suna ta Hira suna shewa duk Yan gayu,Sai ga Hamida sanye da t-shirt da zanin Atamfa ciki Kato a gaba ta fito ta tsaya akan kawaye Basma ta dinga bin kowacce da kallo tana daga musu gira Bata ce komai ba Kawai Ido Daya take kashe musu tana ta faman daga musu gira,Wannan ko itace me cikin mijin naki? Basma ta fesawa kawayenta Ashe tace Yana dawainiya da ita kaddara Haka nake zaman hakur....kafin ta karasa Hamida tace ai Yaya kyakyawa shine ya min ciki muka kwanta Yana shashafa Ni Yana ce min Ina da Dadi Yana so na zai aureni,har nono ya Yana taba.....Wata uwar tsawa Basma ta buga are you stupid Ina magana kina magana a Gaban kawayena lemon Dake glass cup ta watsa Mata a Fuska ta saki Ihu ta juya tayi hanyar dakinta,Basma tace Yarinyar Nan zata kashe Ni,Inteesar tace Haka kike fama da me cikin shege wacce cikin Mijinki ne Kuma kuke zaune gida Daya?Hamida zata shiga dakinta tace ai dai shine ya saka min abinsa me zafi Yana ta min Zina...Zina..Zina..Muna ta yinta sai Yaya kyakyawa ruwa ya taho sai Naga ya langabe ya gaji yayi shakaf,Ai Basma rarumar takalmi tayi tare da wulla mata, Hamida ta fada dakinta tuni. Inteesar Tace Wai kina gani za a Haifar Miki Dan shege wallahi to idan ta Haifa ta tafi kece za a barwa rainon Dan shege,Kuma yanzu Kuna gida Daya dama ya Saba da ita to wlh yanzu Yana lallabawa baki sani ba,Basma ki dau mataki karki Bari a haifi dannan. ga kwaya Nan da Zaki Bata yaron ya mutu a cikinta ta haifo shi matacce ko a Mata Aiki Kinga ba abinda ya hadata da mijinki sai ta koma kauyensu can lafiya kin huta. Halima tace kuma fa Haka ne Suka tafa gaba Dayansu dama Inteesar likita ce Nan take ta rubuta Mata wasu kwayoyi Tace wallahi Indai kin sa Mata a lemo ko kunu ta Sha Dan zai mutu a cikinta sai ta kusa mutuwa ma sannan ta haifo shi matacce,Tace dama mayyar kunu ce kullum sai ta Sha,to ki sa Mata ki dau mataki mu zamu tafi maji labari a waya jirgi zamu zuwa Abj time ya kusa,Drivern Nabeel tasa ya kaisu Airport a sabuwar motarta me tsada da Nabeel ya siya Mata,direct ta wuce chemist ta siyo kwayar da aka rubuta Mata,a Daren ta dama kunu lafiyayye Nabeel Aiki yasha Kansa baida time din kansa kullum da turawa suke meeting aikin Nasa kullum bunkasa yake,sai da kunun yayi sanyi sannan ta zuba kwayar a wani cikin juck ta iske Hamida tana zaune tana magana da danta na ciki tana Dan Yaya Kyakyawa Dan Allah ka daina naushin uwarka giyar Nan kadan kasha ka daina wannan mayen naka Haba Dan Daddy kullum baka Jin magana ka Bari Tam baka ji ko zaka Zo duniya ne sai na zaneka Kai wato baka da tarbiyya ko? Basma da yatsina Tace ga kunu can me Aiki tayi idan Zaki Sha in bakya Sha na zubar,Hamida ta washe Baki Tace Watarana kina da kirki Na gode Aunty ta Mike taje kitchen ta dakko juck din guda ta zauna a Palo tana Sha tana lumshe Ido Tace Baby Yana son kunu Basma tana ta Murna tana kallon Hamida tana ta bankar kunu,tace Aunty garin kunun ya fara lalacewa naji Kamar wari warin kwayar magani a ciki,Basma Tace Nima Haka naji Wai garin ta Bari a leda ta manta,Ahhhh Hamida ta furta tana Shan kunu ba ji ba gani Har taji kamshin Nabeel alamar ya fito, gaba daya ta rage kulashi sabo da wulakancin da yake mata,Kuma Idan Mimi ta tambayi lafiyarta sai tace lafiya suke zaune bata taba fadar aibun Nabeel sai dai ma ta yabe shi. Yana kallonta Bata kulashi ba,Basma Tace to Sai a tashi a koma daki mijina ya fito Kar kwadayi ya motsa karuwa,Nabeel sai yaji haushin Basma Amma baice komai ba,baya so ta dinga zagin Hamida sai yace ke tashi ki koma ciki ana Miki magana kinaji,bai so zageta ita Kuma ga naci Yana magana ta Mike da kyar ta koma dakinta sabo da duk abinda Nabeel yace Sai tayi duk duniya maganarsa kadai takeji Amma ko waye Bai Isa ya Sata tayi abinda bata Yi niyya ba sai Nabeel. Wanka tayi ta kwanta bacci bata farka ba sai da asuba tun jiya Bata sake Jin jaririnta yayi motsi ba,sai ta Shiga damuwa haka tayi Sallah da Addua ,tunda Gari yayi haske ta Fara Jin ciwon Mara har abin yafi karfinta ta fito gashi Nabeel ya fita itama Basma tana sani ta Nemi zuwa unguwa ta bar gidan dan Kar ma ta taimakawa Hamida idan ma ta mutu ba matsala Haka tafi so. Hamida Hijab tasa da kyar ta fito tana ihun kuka wayyo marata wayyo ba kowa a gidan sai Inuwa mutumin kirki matashi Ga Unguwarsu ta masu kudi ce ba kowa ba samun abin Hawa na haya sai an fita daga layin, Inuwa ya taho da gudu Yana subhannallahi duk yagigice tace ka kaini asibiti Inuwa Zan mutu,Inuwa ya kamata ya riketa sosai Suka fice daga gidan Haka ta rirrike Inuwa tana kuka tana zabgawa Inuwa duka tana kaci uwarka Inuwa,Ubanka Inuwa,ka rike min kuguna zai balle Inuwa ya tallafi kugu suna tafiya a kafa ciki a gaba tana ihu tana narkawa Inuwa duka tana zagin Inuwa a Haka sai ga wani matashi Baki kyakyawa ya gangaro da motarsa me kyau tausayi ya kamashi ya tsaya da sauri yace wannan haihuwa ce ku Shiga mu tafi asibitina likita ne ni,Duk Halin da Hamida take ciki Tace ance duk Yan birni Yan yankan kaine,Wayyo Inuwa uwarka....uwarka Inuwa...tsinanne Inuwa,ta kalli me motar tana Kaima kaima ubankaaaaaa......Haka aka sata cikin mota sai ta koma Kan me Mota,me Mota uwarkaaaaaaa....wayyoooo.....cikin shege nayi....na jawa kaina...Yaya Kyakyawa Uwarka Mimi...tsinanne Kaine kace da Dadi ka sa min Abu a cikin Dausayi na,Naga ta kaina... Innalillahi har Kauye yaje ya saka min ciki...nice nake zuwa Hotel wajensa....wallahi sau Daya mukayi.. zan mutu,Allah ka taimakeni Kar walakiri ya jibgeni,Tausayinta ya Kama matashin me Mota ya kaisu rantsatsen asibitinsa private,lokacin Inuwa ya samu ya sanar da Mimi,Nabeel kuwa Mimi ce ta fada Masa ai Yana ji yasa driver yayi Hospital da shi. Mimi tana ciki tana zuba kuka ta tari Nabeel tace ance kwayoyi tasha yaron ya mutu a cikinta Kuma kwayar har kisa take yanzu yarinya tana Nan likita yace sai Addua da kyar in zatayi rai gashi can ta haifo yaron matacce duk ya kusa narkewa a cikinta,sunyi iya yinsu amma taki farfadowa baka gani ba jini ne Kawai ke malala na karaya da Yarinyar Nan ance jini ake bukata da gaggawa,Hankalin Nabeel ya tashi gashi an hanashi shiga nan take ya haukace ya Kira Sale da Inuwa da ma'aikatansa gaba Daya maza Suka Zo gwajin jini harda shi Kansa Oga an gwada jini baizo Daya ba,Ana gwada jinin Sale yazo iri Daya Dana Hamida,Nabeel sai yayi tsalle ya dire yace Sam ba a Isa an sa mata jinin Sale ba,Sale yace ceton Rai nefa,Nabeel yace Kai Dan Iska ne Sale Dan duniya ne bazan yarda ta hada jini da Kai ba Zan sake Nemo mutanen kirki ba Kai ba da kake lalatacce dama Naga alama Sonta kake wallahi sai na koreka daga aiki,Nan Nabeel ya Kira wasu aka gwada aka samu mutane biyu,likita yace an sa Mata Daya yanzu a Nemo wani sai Tasha leda biyar,Nabeel yace ba dai na sale aka sa Mata ba ko? Wani likita ya bude baki yace Wai kishinka ne haka abin yayi yawa,Nabeel ya Bata Rai yace kanwata ce,Haka Ammar yazo shima ana gwadawa yayi dai dai da nata,Nabeela yace baza a sa naka ba kaima abokina nane Wai Ni me yasa Nawa baizo Daya da nata ba,a sake gwadani sai da suka gwada Nabeel sau Uku baiyi daya ba sai Mimice taci ubansa ya hakura aka ja na Ammar duk aka hada leda biyar ana ta sawa Hamida amma Bata farfado ba likita yace Inshaallah zata tashi abin yazo da Sauki. Sai lokaci Nabeel ya saki ajiyar zuciya Yana Addua,Inuwa da Abbas suna gefensa,Inuwa ya koma wajen Mimi Yana bata labarin yanda ya taimakawa Hamida zuwa asibiti yace Naci duka da zagi haka na tallafeta tana tallafe min kuguna Inuwa na rude kamar mace na koma na rirriketa na rike Kugunta Muna tafiy da..... Kawai Mari Inuwa yaji dama da haku ta ko Ina Nabeel Yana wallahi na koreku ku koma inda na dakko ku gidan Mimi Kar na sake ganinku a gidana lalatattu Yan Iska Zan dauki sababbin ma'aikata,Kana hauka ne Nabeel meye haka daga taimako,kina ji fa Kugunta ya rike Mimi, ya rirrekata ya hama taba Mata jiki wallahi ku koma gidan Mimi can kuci gaba da Aiki ba dai gidana ba,Baki bude ake kallon Nabeel,Mimi tace Allah ya shiryeka Inuwa ku dawo gidana dama can kuka Saba Suka ce to,Nabeel Yana huci ya fice daga asibitin jira Kawai yake Hamida ta warke yaci ubanta akan kashe Masa yaro data yi,Yana dan ba Dan sunna bane sai a kashe min yaro wallahi sai na dau mataki ya bude yaron a kwali ya ganshi kyakyawan gaske hawaye ya zubo Masa yace na kwallafa Raina akanka Baby an kashe min Kai wallahi ko waye sai Naga gatansa,Ammar ne ya karba aka sallaci yaro aka kaishi kabarinsa . Nabeel Yana komawa gida Basma tana baccinta hankali kwance abin ya bashi haushi,ransa a bace yayi wanka da Sallah ya zura jallabiya fara ya fito ya sake sawa driver ya fige shi sai gidansu Ya karbowa Mimi abinci ya Kai asibiti,Yana shiga Affa shima ya duba ta ya fita yace Mimi Bata farfado ba? Mimi tace har yanzu suna zaune har magriba ruwa da jini Kawai ake karawa Hamida,Nabeel da Mimi a asibitin suka kwana bata farfado ba har Mimi tayi wanka ta dawo shima Nabeel yayi wanka ya dawo an dai gyara Hamida fes tare da shiryata aka canja Mata sutura aka kaita dakin Hutu,Can Nabeel ya zauna ba kyafta Ido Yana kallo ko zata farka,Mimi ma Haka,jini da ruwa tare da allurai sun ratsa Hamida warkar ta Bude Ido a hankali gata da juriya ba komai ke damunta ba,a hankali ta Mike zaune ta kalli Nabeel da ya mike zunbur sabo da murna harda sakin Murmushi ba tare da ya shirya ba. Mimi tace Sannu Hamida ya jikin Tace lafiya kalau naji Ni Mimi Ina Dan Nawa ta tambaya a hankali cikin kunya? Mimi tace Allah ya Masa rasuwa bai Zo da Rai ba,tunanunsu Hamida zata Yi Murna ba bu Dan shege sai ta barke da kuka wayyo Dan Yaya Kyakyawa,Dana da Muka Sha wahalar samu yanda Nasha zafi da bacin Rai ga wahalar ciki yanzu shike Nan na tashi zero zikau shike Nan,Wallahi na shaku da Dana Ina son abina,Mimi da Affaa Kuwa sunyi murnar mutuwar yaron duk da basu San dalili ba,Mimi tace maimakon ki Murna Allah Yana sonki ya karbi abinsa yau kwananki biyu da haihuwa ya mutu an binne shi tun a ranar,Hamida ta rushe da kuka,Nabeel ma ya tuna yaronsa ya daura Kansa saman cinyar Mimi Yana hawayen rashin dansa,yace Mimi Dana kyakyawa ya mutu na Gama kwallafa Raina da yanda Zan Raine shi,Mimi ta saki salati,Hamida tace ba Kaine da kuka ba nice da kuka Ni nafi Shan wahala Dana ne, Nabeel ya dago da sauri yace Sanda aka Yi cikin ba kuka Kika Yi ba sai yanzu,Salati Hamida ta saki tace yaushe akayi Haka Ni dama tun farko Ina son Dana wallahi ban taba Fushi da shi ba,Ka manta a Hotel wallahi kuka ka Fara zaka ce ka fini sonsa,wallahi na fiki sonsa ke da kika Sha kwayoyi Kika kashe shi,Hamida tace wallahi Allah ban Sha komai ba ta fashe da kuka. Mimi tace yau na shiga Uku karshen duniya akan Dan shege ake wannan wayyo Ni Wayyo bala'in duniya ya fada gidanmu,Shuru sukayi da musun likitan da ya dakko Hamida tana nakuda shi Kam kaunar Hamida ta kamashi ya tausaya Mata gata me abin Dariya ga Uwa uba kyau shi Kam Nan gaba zaije Neman Aurenta ya Kara Mata ta biyu, satin Hamida Daya jiki yayi kyau Shi ya rubuta musu sallama Suka yo gidan mimi direct zata kula da yarinyar mutane,dama likita yace zata Sha wahalar haihuwa sabo da sau Daya akayi amfani da ita gashi karshe sai Aiki aka Yi mata aka Ciro yaron. Likitan da Kansa yake zuwa gidan Mimi Yana duba Hamida lokacin Nabeel ya Kai sati biyu Bai sake zuwa duba Hamida ba,ga Hamida har ta warware sai abinda ba a rasa ba na Wanda aka yiwa Aiki. Yau Sunday Doctor yazo duba Hamida zai tafi yace ko sunana Baki sani ba,tana Murmushi ta rakashi mota da katon Hijab dinta tana dariya Tace to ya sunanka me kirki? Yace Dr Ahmad sunana ya fito da katuwar Leda ta kayan makulashe ya Mika Mata kenan Nabeel ya shigo da mota driver ya fito ya Bude Masa kofa,Yana Fitowa tun kafin ya karaso ya dakawa Hamida tsawa tana Jin kamshinsa tasan shine Yace malam lafiya ke wuce ciki ko na tattaka ki,Hamida tana tsoro Tace abokina ne me kirki ai fusata yayi ya fatalar da ledar dake hannunta su ice cream Suka tarwatse ta kwashe da gudu gida,Ya kalli Dr yace karka sake zuwa wajenta,idan dubi ne ka gani ta warke bar Mana gida ko nasa a min waje da Kai,yace me yayi zafi Malam Yaja mota ya bar gidan shi kanshi Dr Ahmad kwarjinin Nabeel ya Masa yawa ko Namiji yasan Nabeel ya hadu. A fusace ya shiga ciki ga Mimi bata Nan a Palo ya iske Hamida ya fara bala'i Dan Iskanci har kin Fara bin samari,uban wa Kika sani a garin Nan da har Zaki Fara tara samari,so kike a Miki ciki ko,oh dama ai kina bukatar Namiji tunda kin fada min shine yanzu Zaki Fara ko? Amma kasan ba Yar Iska bace ni wallahi na rantse da Allah da Kai kadai nayi Kaine kadai ba Wanda na taba kulawa,to in ba so kike ki Kuma ba kin taba Yi shine Zaki dinga kula maza so kike wani ya sake canja Miki tunani? Eh.... ya furta da karaji Yana huci,Hamida Tace a'a da sauri sai kuka ta fara yace wa ya sani Sanda Zaki je Watarana dama ai sau Nawa kina fada min kina so a Kara Miki kina sha'awa kullum yanzu kin Haihu Naga Dan iskan da Zaki kula Ana Miki tarbiyya bakya ji,Tace yace zai sani a makaranta Nima Ina so inyi ilimi kutmar ilimi ya dura ashar,Naga ya Nemo Miki school wallahi sai na karya ki Kika sake wani gardi ya kawo Miki form Zaki ga abinda Zan miki,Hamida tace wallahi sai na karba Mari ya kifa Mata uban wa zai barki kije school wani ya sake Miki wani Abu ko wallahi Kika sake sai na maida ke kauye, Kuka ta fashe dashi ta Fadi a kasa yau iskancinta ya motsa ta dinga burbuwa tana kuka,Wayar charger ya fisgo ta Mike ta zura dakinta da gudu ta tsaya bakin kofa tace na dai ga Duwawunka ,Dariya ta bashi da kunya ya danne yace Zan kamaki,Ya juya zai fita tace Yaya Kyakyawa Dan Duwawunka fari,Dawowa yayi yace ba kyau fa batsa ki daina fadawa mutane kina zubar min da mutunci wajen masu Aiki tace oho,ta sake cewa me farar takashi.... AsmaBaffa [6/28, 1:46 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 6 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Rukayya Ummi H Roukayya Ruky Barin gidan yayi gaba Daya,gida ya koma Basma tana Palo tasha wasu arnayen kananan Kaya wani dan guntun wando da Yar ficikar Riga ta zuba kyau ko Ina Yana kamshi amma ko a jikinsa,tasowa tayi tare da rungume shi Murmushi yayi Kawai yace kinyi kyau,Sannu da zuwa Baby,Kiss ya manna Mata a kumatunta Kawai ya haura sama,Basma ta bishi da kallo tana lura da shi tun gaf da Hamida zata Haihu walwalarsa ta ragu sannan sam baya damuwa da ita irin da,Haka ta bishi sama,Abinci ya ci ya kwanta Yana hutawa,jikinsa ta Fado tana murza shi tana Masa wasanni Ina shi Indai ba maganin tada sha'awa yasha ba Sam ko me Basma zata masa baya ji baida feeling a kanta Kuma bata birge shi ko me zata Yi ya rasa dalili har gwara daya Basma din ma. Basma maganin Sha'awa ta dakko zata bashi yace bazan Sha ba so kike na cutu ki kyaleni,shagwaba ta fara please Baby kaji tsaki Yaja ya mike ya fito da wankin da me wanki Bai Zo ya dauka ba yace yau da kaina zanyi zanyi wanki,Basma tace ga washing machine ka bari me wanki zai zo ya mana, yace no ni da Kaina Kawai zanyi da Hannu na motsa jiki,dan Kar Basma ta dame shi sai sunyi sex shi yasa ya kirkiri wanki,Haushi Basma taji tace Allah yasa Aljanu su Karo maka nasu ka kwana kana Yi,Dariya ta bashi ya danyi Dariya ya kwashi wanki ya shiga toilet. Abinda bai taba Yi ba ya raba dare yaki dawowa bedroom har Basma ta gaji tayi bacci Yana can Yana facaka da ruwa. Washe gari Hamida taje gaisar da Affa ta durkusa yace no Ni ba sai an wani durkusa min ba ko a tsaye Zaki iya gaisar dani idan ta Kama ma Ni sai na gaisheki shine tsarin wayewa,Hamida ba hankali tace to Affa an gama Ina kwana yace kice an tashi lafiya Kawai Mene wani Ina kwana Bata da meaning ki kimin sallama itace me ma'ana ,Hamida Tace salamu'alaykummmmm....harda rerawa da Waka Affaa ya amsa ta kyalkyale da dariya tace Allah Affa tamu tazo daya,Affaa ya murmusa yace a gidan nan Ina da tsari Indai mutum ya wuce sati a gidana to dole sai na saka shi a makarantar boko da Islamiyya idan bazai Yi ba sai dai yaro ya koma gidan ubansa ko yabi duniya ba ruwana,Sabo da haka ke Kinga na Miki Uzuri kin warke sai na saki a makarantar kudi Zan dau nauyi in ma karshen boko Zaki gani Indai Ina raye Zan tsaya Miki,Nima da kike gani kwana Nan Zan koma Uk Karin karatu,Hamida tace to Affa kafin na Fara a kaini Kauye mu gaisa da dangi,A'a sai kin waye Zaki koma sabo da aga kinci gaba a rayuwa Kinga ba me kawo Miki shirme Hamida tace to Affa na gode amma su papa sun sani? yes of course sun sani da yardarsu Mimi ce ta shigo zata fita Office Affa yace Kinga wannan uwar taku nayi nayi taje tayi PHD taki Wai sai ta Shiga Islamiyya Karin ilimi shima dai ba laifi yafi Zama haka,Mimi tace kayi ka gama Ni na wuce Hamida ki kula da gida,Affaa yace tsaya Nima yau Ina da lecture da Zan dauki wasu muje ki saukeni in kin tashi ki biya ki dauke Ni, Haka Hamida ta rakasu har mota,da sauri ta Budewa Mimi ta shiga mazaunin driver itama ta zaga ta sake budewa Affa ya shiga tana musu a dawo lafiya ta rufe tace tunda na Haihu a dakko Fadila daga gidan kawu na ganta,Mimi tace uwar surutu ai ke kinfi Fadila surutu tunda kin gama tonawa kanki asiri. Hamida Kuwa hankalinta Yana kan fitilar mota ta zuba Mata Ido tana ta kallo,gaba daya bata jin me Mimi take fada har ta zaga wajen fitalar tare da sa yatsa ta laso ta dandana a bakinta,Tace ba Zaki a Haka kamar alawa,Affa da Mimi dariya ta kamasu suka ja mota Suka tafi suna fita ta kwashe da gudu tayi cikin gida tana uban gudu ita bata tafiya normal sai ta hada da gudu,Masu aikin gidan suyi ta dariya. Yayan Kanin Affa dana yayan Affaa ne Suka Zo mota guda Mata uku maza biyu samari kamar Nabeel,Wata arniyar mota ce ta shigo gidan wata budurwa ita take driving Ihsan Kenan Hamida tana Palo sanye da Abaya tun Wanda Mimi ta bata su basu San anzo da me cikin shege ba ko Nabeel yayiwa wata ciki sabo da Iyayen sun binne zancen,basu San ma Mimi da wata a gidanta ba tunda Allah baisa sunzo ba,sun San ma su Mimi basa gida Kawai dai zamansu zasuyi har su dawo,Suna shiga Suka ga Hamida tana kwance a kasan tiles tana wakokin Kauye su sun zaci ma sabuwar Yar aiki Mimi tayi,sallama sukayi kamshi Kawai ke tashi Hamida ta kallesu kyawawa suna yanayi da Nabeel da Affa amma Nabeel ya Fi kowa kyau da haduwa a family din kaf, Mikewa tayi tsaye ta washe baki tare da cewa Yan gayu sannunku da zuwa ku shigo ku zauna sannunmu sannunmu Yan gayu barkanku da zuwa marhabin lale...Marhabin...maharbin lale...lale. Basu ji komai ba sabo da sun Saba da Yan aiki daga kauye,suna Zama ba gaisuwa ba komai sabo da ita bata Saba ba da wannan a Kauye ba sangartacciya ce,Kitchen ta Shiga ta kawo musu lemo da ruwa harda kunu tace ku Sha nice na dama dazu da zafinsa akwai dadi, Murmushi sukayi Kawai suka Sha abinda zasu iya,Hamida tace da a Kauye kuke da yanzu Kuna gindin bishiya Kun baje sabo da zafi ko Kuma kun Zama kamar kadangaru kuyi ta bin bango Neman Ininuwa,Suka ce Hmm suna ta danna waya,ta sake cewa gaku Rida Rida Haka wasu zagada zagada duk kunyi zagadede ku Kuwa wanne laifi kuka yiwa Allah bakuyi aure ba? Baki Suka bude Ihsan tace ke daga Ina kike ne Wai? daga Kauye aka kawo Ni Nan na Haihu cikin shege nayi. Suka kalli juna Allah ya kaddara bata ambaci Nabeel ba,Anwar yace a kauyen? Da sauri tace ei daga birni yazo yayi min amma sau daya Muka Yi abin,baka ga yanda na haifi zallelen yaro ba sai jiya na daina kukan mutuwarsa Kun San ban haife shi da Rai b ...kafin ta rufe baki kamshin Nabeel ya mamaye palon,Shuru tayi sakamakon wata mugun kallo da ya Mata,Wayarta me kyau da Mimi ta siya Mata itace ta fara Kara dubawa tayi da kyar ta take hada sunan ta fara kokarin karantawa a fili da...ak....ta...Ah...Ah....Ahamad... shine ya rubuta Mata sunan da kansa tasan bazai wuce Dr Ahmad ba,mikewa tayi ta koma kitchen da sauri tana magana kasa kasa,Nabeel Wanda yaji wa ta ambata hankalinsa Yana Kai har ya gaisa da su Ihsan Kawai bai yarda da Wayar Hamida ba,kitchen din ya shiga ya iske tana cewa soyayya Kuma Ni ban iya b....Wayar Kawai taji an fisge ya bugata da bango ta tarwatse,Anwar ya zaci glass cup ne ya fashe,Wayar ya dauka a farfashe ya bude tare da zare layin ciki Yana huci,Tsoro ya Kama Hamida baki na rawar tace wallahi ka fasa min wayata sai ka biyani,wuyanta ya shake ta fara kakari idonta ya zazzaro cikin muryarsa me dadi yace wallahi Matukar na ganki ko najiki da wani a garin Nan sai na ballaki pieces,sakinta yayi ya tureta baya yace sai son mazan bala'i na gane so kike a sake Miki ko maza Zaki bi ko? to ko kinyi aure sakinki za ayi babu me aurenki a haka Yana sex dake zai San kina bin maza sai ya sakeki. Haka Zan zauna to bazan kula kowa ba bare nayi aure wallahi to ba a kaina aka fara ba karuwai ma suna Nan lafiyarsu kalau bare Ni akan nayi ciki bisa tsautsayi Kuma kaji in fada maka Affaa school zai sakani,Indai Ina garin Nan baki Isa kin fita karatu ba sabo da ki tafi wajen maza ko,Oho koma mene dai yau za a kawo form na waec da Neco na zana sannan ka sani a University can ta matse maka a matsematsin farar abarka ,Dariya ta bashi ya murmusa yace Affa ne yace zai saki da gaske? Kai ta daga masa tare da ficewa kitchen din ta barshi,fisgo rigarta yayi ya dawo da ita ciki ta fisge rigarta tace karka sake min wani cikin taja baya ta rakube a tsorace,Dariya ta bashi a ransa yace taji wahala Fita yayi abinsa ya zauna suna labarinsu na dangi,Nabeel yace muhseen din ne ya koma shaye shaye? sai Hamida ta fito tasa baki zaraf tace ai Kuwa bazai ga muhammada rasulillahi ba yayiwa Kansa wanne tambadadde ne wannan? yace baki da kunya fa ke, guduwa tayi dakinta,yace Yarinyar Nan ta rainani ya furta a ransa tare da ficewa gaba daya daga gidan,su Kuma Su Ihsan suna zamansu suna kallo da latsa waya har Nabeel ya dawo da Yamma,Ya gansu duk sun samu daki ko wanne ya kwanta Yana bacci. Hamida tana bedroom dinta,bedroom din ya Bude a hankali ya ganta kwance kasan tiles tana sheka bacci kofar ya rufe mata. Mimi sai 5pm ta dawo tare da Affa suka ga baki duk Fitowa sukayi Suka taru a Palo aka gaisa,Mimi tace abinci fa? Anwar yace ai wata yarinya da tace an Mata cikin shege ta Haihu itace ta dinga kawo Mana girki har sai da muka gaji da ci,Murmushi Mimi tayi tace Hamida kenan ba ciki aka Mata ba shirmenta ne ai cuta ce a cikinta wani Kari ne ya fito a cikinta aka kawota anan aka cire shine fa take cewa ciki ne,Dariya sukayi gaba daya,lokacin da Mimi ta fada Hamida ta tashi daga bacci ta fito kenan taji,sai ta fito Palo ta tsaya a kansu Mimi tace Bari na watsa ruwa nazo suka ce to dama Affa da Nabeel sunyi part dinsa. Tana gani sun tafi ta kalli su Anwar tace na rantse da Allah ba Haka bane ciki aka min wallahi Allah, Kai Naga fa har takashinsa ta fada da rada Kar Wai su Mimi suji,Anwar suka kwashe da dariya Hamida tace ei Yasin Al'quran duwawunsa ma fari ne,ba ruwansa da bakar takashi,Motsi taji taji kamshin Nabeel tasan shine tayi Shuru ta zauna a gabansu ta wayayence tace ai Sakina kawata Bata San an kawo Ni birni ba tana can kanta duk ya side da tallan Masara dafaffiya,Yaya Nabeel ne ya harareta ta sadda Kai kasa tana soshe soshe na rashin gaskiya tace jiya da zanyi wanka na fasa sanyin na'ura ma isheni Dan anan akwai abinci me kyau ne Ina ci Ina koshi Amma wannan raba ta gidan Nan idan ba abinci ai kasheka sanyin zaiyi. Nabeel ne ya harareta ba musu ta Mike ta koma karshen palon ta zauna tayi shuru,Basma ce ta shigo taji Yan uwanta sun Zo shine tazo su Sha Hira,tana sallama taga Hamida amma ko kallonta bata Yi ba,a gefen mijinta Nabeel ta zauna tana Masa wani fari da kwarkwasa. Hamida ganin haka ta Suri plate ta bugawa Basma a goshi Nan take ya fashe jini ya fara fita, Nabeel a fusace yace ubanki ta Miki baki da hankali,Baki ta turo tace kana gani tana maka karuwanci kai in baka gani ba ai mu mun gani,Ihsan ta rike Basma da goshi ke fitar da jini tace ke Baki da hankali fari fa tayiwa mijinta kwarkwasa da kisisina ce ta mata,Hamida ta langwabe Kai tace ohhh ai ban sani ba dama shine farin soyayya ai wallahi Naga abin karuwai ke Yi a bariki, Basma tace wallahi sai na rama ta Mike a fusace Nabeel sai ya riketa gam fafur yaki bari ma ta kwace bare tayi wani abu. A kunne yace kiyi Hakuri Zan rama miki Yana wani shafa bayan Basma har ta hakura, Hamida ta kallesu sai taji kishi sai ta tuna ita ciki ya Mata yake wulakantata,wannan matarsa ce sai lallabata yake a ranta tasan ya cuceta ita,a hankali ta Zo jikin Basma wuf tayi ta Mintsini Basma ta gudu dakinta,Basma ta sake kwalla ihu tana narkewa a jikin Nabeel tace wallahi Lele ka Rama min in ba haka ba sai na ji Mata ciwo ko ba yau ba,dressing raunin ya Mata sai dare suka tafi gida su Ihsan a gidan Suka kwana. Washe gari Affa ya kawo form na waec da Neco Mimi tace ka fara gwada ilimin Yarinyar Nan wallahi ko karatun hausa Bata wani iya ba,Affa ya kira Hamida yace maza ki rubuto min tatsuniya me Dadi a paper,Haka ta rubuta haukarta ta kawo ba abinda ya gane a ciki yace dole sai dai na dokko Miki malami ya dinga koya Miki a gidan kafin ki zana wa'ec da neco. A ranar ya Kira Malamin su Fadeela na IRK Wanda zai koya Mata Arabic da Boko,Shehu wanka aka dakko,Shehu badai iya wanka ba shi duk hirarsa ta Harkar wanka da gayu ce,Hamida tana wajensa yace a cikin darasina harda koya wanka yanda Zaki dinga kula da kanki wajen daukan wanka,Baki Hamida ta tabe duk abinda taga Nabeel yana yiwa Basma ya tsaya Mata ita sai dai hararara tsakaninsu duk sai tayi surrender. Shehu yace sai gobe zamu fara karatu Hamida tace Allah ya kaimu,Shehu Yana tafiya sai ga Basma wacce aka warware aurenta ta da Nabeel itama ta gama hadewa Hamida tabi motarta da kallo Kawai fitilun motar take kallo gani take kamar Alawa so take ta sake lasa taji,ga Basma ta tafi da imaninta,Basma ta cokalo shegen takalmi Tasha fariin lace white and silver Kawai sheki take da kamshi,Hamida tana bin jikin flowers na gidan a hankali har ta tsaya a kusa da motar Basma,Ita Basma ma bata kula da ita ba,a kasan motar Hamida ta tsuguna ta lallaba ta samu fitilar motar ta laso da harshenta tace aikin banza ba Zaki ma a Haka itama tata kamar alawa sai ta fito Bata San wannan Basman ba matar Nabeel ta sani,Basma tana kulle mota Hamida ta daga Mata hannu tana washe baki tace hey,Sai lokacin Basma ta juyo ta kalleta up and down ta yatsina fuska sannan tace Mimi sabuwar Yar aiki ta dakko kenan,irin wannan kyawawan ai sai ku kwace mata Affan Fadila da zata bani dama Dana Yi sama da yarinyar Nan nayi waje da ita Basma ta furta a ranta,a fili ta kalli Hamida tare da Mika Mata hand bag dinta me tsada nufinta Hamida ta Kai Mata ciki,ai sai Hamida ta durkusa ta fara zuba godiya tace na gode na gode Aunty Allah ya saka da Alkhairi wallahi kina da kirki jaka irin wannan taku ta Yan gayu Kika bani kyauta daga gani na Hamida ta furta tare da dagawa Basma gira tana murmurmushi tana Wal Wal da girarta. Basma tace ke shashashar Kauye baki ga tayi Kalar takalmi da kayana ba ke ba Yar aiki bace muje ki shigar min da jagata ciki nake nufi idiot...Hamida ta kankame jaka tace na rantse da Allah bazan Baki ba ai baki ce ciki Zan Kai Miki ba ce min Kika Yi kyauta Ni dama Ina so,ciki ta zuge taga kudi Yan dari biyar biyar tace harda tsintuwa nayi ta kwaso jambaki da powder ta mikawa Basma tace ungo Abinki Sabuwar Aunty ko na hada da su? Basma tayi galala tana kallon Hamida,Hamida ta maida cikin jakar tace na gode du Ina so zata fece motar Lele ta shigo da Matarsa Basma a gaban mota itama wannan Basman ta dau wanka kamar sun hada Baki ita ma material ta Sako fari tas komai fari,Lele Kuma ya sako shadda silver ya diga ruwan kyau, Hamida ta saki baki,Basma kishi ne ya mamaye mata zuciya Nan take ta kumbura ganin Lele da matarsa,sun jero sun fito daga mota sai ta juyo kamar zata Yi kuka tana kallonsu,Basma matar Lele itama ta gane Basma wacce tasa aka fasa Aurenta da farko,Hamida Kuma Lele take kallo kawai dake ita ba ruwanta da kowa Lele ta sani da shi take harka,Fuska ta kwabe zata Yi kuka ta taka a hankali kamar kwai ya fashe mata a ciki tana murza ido da hannaye ta tsaya cak a gabansa bata ce komai ba,Basma matarsa tace dalla matsa Mana daga gaba,do you want me to push you? Ko kulata Hamida bata Yi ba shima Lele Bai ce komai ba ta gefenta ya bi zai wuce ta dawo ta Kuma tare gabansa idan yayi Nan sai tayi Nan ta tare hanya ita kuma bata ce komai ba sai murza ido takeyi,cikin tsawa ya furta Zan kwada Miki Mari wlh in baki bani hanya ba,da sauri ta matsa gefe Yana wucewa ya juya baya ta riko rigarsa kadan a hankali yanda bazai ji ba tana binsu,Basma ta make hannun Hamida,Hamida tace ba ruwanki Dani ba ruwanki dani tam yanda kike gadara kina ganin duwawunsa kullum Ni na rigaki gani har tabo ne da shi a daya barin duwawunsa na bangaren dama, Yaya kyakyawa ko kurji kayi kana yaro? Maruru ne ya fito ma a wajen kana yaro? Naga tabon katoto ne,wani Takaici ya Kama Nabeel ya juyo a fusace zai mareta tayi baya da sauri tace wa yace ka hada harka da kwaila ai ka Shiga Uku wallahi baza ka shuma ruwa ba sai na dinga fadan sirrinka ai akwai wani ma dana gani na rantse da Allah har su Mimi sai sunji,Yasan da gaske take ba hankali ne da ita ba,juyowa yayi ya zaro chocolate masu tsada Guda biyar a Aljihunsa ya ce Zo ki karba,Tace zazzabi nake ji wlh yace Zo muji ya zafin jikin naki da sauri ta tafi ya sa Hannu a kumatunta kamar zai taba Kawai sai saukar Mari taji zata Yi kuka yace wallahi if you dear....kasa karasawa yayi ya tako inda take tana jiran taji duka sai taji alawowin ya watsa Mata a jikinta yace ki daina lasar danger mota,tayi mamaki taya ya sani tunda bata taba Yi a gabansa ba. Basma tuni tayi ciki,ita Kuma daya Basma ware Baiko Nan take ta gane Hamida ce wacce ya yiwa ciki wacce itace tayi sanadin da aka ware Aurenta da shi ya dawo ya auri daya Basman wacce itace sanadin rushe baikon waccen,Nan take tace nayi asarar Wanda na taba so a duniya wallahi duk wacce ta auri Nabeel baza ta zauna lafiya ba itama sai na kashe Mata aure,Dan wulakanci Nabeel ko kallonta baiyi ba sabo da Yana tare da matarsa. Wajen Hamida ta karaso wacce ta rataya Jakarta tana ta Shan alawarta,Basma tace bani handbag Dina,idan na baki in shiga wuta bal bal ai wallahi bazan baki ba kyauta Kika Miko min ta Zama tawa,kokawa Suka Fara Basma zata kwace jaka Hamida ta Hana karshe ficewa tayi daga gidan gaba Daya tayi zamanta a kofar gida wajen masu gadi su Inuwa da Sale wannan Karon alawa ta dauke Mata hankali bata musu surutu ko Daya ba. Inuwa ne yace Sale mu kiyayi Yarinyar Nan wallahi Oga ya shigo gidan Nan kasan Allah idan ya ganta a nan ba ruwanta mu zai ci uba,Hamida ta cika baki da Alawa gashi bata magana a hankali tace kuyi zamanku Yana da kirki bazai koreku ba Yaya kyakyawa Yana da kirki,Sale yace ke dai anyi shashasha wallahi Wai mutum ya lalata Miki rayuwa ya dinga wulakanta ki ya daukeki mahaukaciya Yar Kauye bagidajiya amma kullum sai ki dinga Kare shi kina yabonsa,Inuwa yace Ina ruwanka sale Yarinyar Nan Haka Muka tsince ta a gidan Nan Mene naka a ciki,Sale yace wallahi wallahi da zai yarda Ni sai na aureki a Haka duk da ana kallinki a Haka ba kowa ne yake da zuciya me kyau irin taki ba,yanzu da wata ce da yanzu ta Hana kanta sakewa,ta tsaneshi tana aibata shi ke Kuwa ko a jikinki kin karbi kaddara. Hamida tana side yatsunta kyawawa tace uncle Sale Ni na dauki kaddara na fahimci Yaya kyakyawa ba halinsa bane,sai yanzu dana Zo birni na waye na gane cewar Indai kaga anwa mace uhmmm...uhm...ya ma sunan sa? Sale yace Iskanci Zina,yawwa Dan gari Indai kaga ana yiwa mace Zina to laifinta yafi yawa,Ni Hamida kwarankwatsa dubu tana nuna kanta da yatsa duk ta hada zufa ta gigice duk akan zata ba da labari sabo da ita dama a hargitse take ba nutsuwa tace babu laifin Yaya kyakyawa nice naje da kaina, Kuma giya ita muka Sha,Sale yace wait wait dakikiyar Ina ce ke Baki San Shan giya ba kyau ba,Hamida tace Ina Zan sani Kar ka dame Ni Sale shi yasa nafi son Uncle Inuwa na daina fada maka uncle Hamida an waye har an San Uncle cewar Sale. Alawa ta bare ta sake jefawa a baki tace Sale kaja girmanka idan ban dura ma ashar ba shegiya uwata ta haife ni kasan halina,wallahi in Banda Ina tausayinka tuni Zan hada ma sharri a koreka daga aiki kabi duniya ka shiga Uku. Inuwa yace Sale ka bari karka zubar da girmanka Mana yarinya tana ganin girmanmu. Uncle Inuwa kazo kauyenmu ka nemi aure cikin sauki a baka budurwa zukekiya kyakyawa Fara a dubu hamsim komai da komai dubu hamsim zaka kashe a kawo ma Amarya har gida Ni Zan ma Hanya in ka tashi aure,Kawai ka samu gidan Zama da dubu hamsim na rantse da Allah budurwa zukekiya za a kawo mak....kafin ta rufe baki Nabeel ya leko ya ganta Shuru Shuru bata shigo ciki ba shi yasa ya leko,Sale da gudu ya fada Bayan gate ta waje ya manne a jikin katanga,Inuwa Yana zaune a bench din Hamida tana gefe,zumbur ta Mike itama ta kwashe da gudu tayi cikin layin shi Dariya ma Suka bashi,Inuwa Kuwa a wajen ya sankame . Basma da Basma suna palon Mimi suna kallo kowacce tana hararar Yar uwarta sai Tsaki da tsaki gashi Mimi Tace musu tana hanya ta kusa karasowa,Hamida tana waige tana gudu gudu sauri sauri ko mayafi babu a jikinta shine takaicin Nabeel,Yana ta faman daga mata Hannu ta dawo ita Kuma tunaninta dukanta zaiyi sai ta Kara sauri,Inuwa ya tasa yace ka tabbatar ka lallabo ta ta dawo gida mutanen banza Kawai ya juya ciki. Inuwa ne ya lallabo Hamida da kyar ta dawo gida da jakar Basma a rataye a kafadarta da ta kwace ta karfi,tana Shiga Palo ta iske Nabeel a 3seater Basma matarsa tana gefe itama Daya Basma ware baiko ta koma gefensa daya ta zauna tana muzurai sun sashi a tsakiya sun takura Masa,Hamida tace au abin gasa kuke kunji kunya, ta tugewa Basma matar Nabeel dankwali Hular gashin data kifa kanta sai ga Dan guntun gashin Basma da wani tsohon kitsonta goshi dum a gaba,Hamida tace ashe dama kina da goshi abinki Cass ,Nabeel ta kalla ya Naga idonka Yana wani blinki blinki mikewa yayi Fuska ba Rahma ya bar gidan gaba daya,sai lokacin Basma ta Mike ta rufe Hamida da duka,itama ware baiko haushin Hamida taji ta fisu kyau ta rufar Mata gaba Daya Suka nada Mata shegen duka harda ji Mata targade Suka fasa Mata gefen baki Hamida ta dinga kuka ta kasa tashi gashi ta Hana jaka ta boye, Basma tayi tayi ta dakko Mata jaka amma an nemi jakar an rasa ta boye ta tun kafin ta shigo palo. Mimi ce ta dawo ta iske Hamida tana ta kuka a tsakiyar Palo kuma taki tashi ta tafi,Mimi tace lafiya Matar Lele tace Iskanci da hauka zata Mana Muka Tarawa shegiya jini,Baku kyauta ba cewar Mimi itama ta share Kawai ta zauna suna gaisawa tasa aka kawo musu abinci iri iri Basma Ware Baiko tace dama zuwa nayi mu gaisa,Mimi ta dinga godiya ko kallon Hamida bata sake Yi ba itama Mimi Bata damu da wata Hamida ba sabo da in aka rainaka a waje ka gama yawo,Affa ne ya shigo yaga Hamida na kuka ba Wanda ya kulata a wajen,ya dinga fada kuwa ya Mika Mata leda katuwa shake da kayan makulashe Hamida ta dinga godiya tace Affa naji targade yace Sannu karki damu Zan Kira me gyara,da rarrafe ta koma gefe Mimi ta tabe baki suka hada Ido da Basma matar Lele suka wani Yi zinden Hamida suna tabe baki. Ware baiko ganin Mimi da Basma bakin su Daya sai ta Mike tace ni Zan wuce,Affa Kuwa ko kallonta baiyi ba sabo da yanda a gabansa taci kwalar dansa ta kifa Masa maruka ta yiwa Affa rashin kunya. Basma ware baiko tana tafiya Basman Lele da Mimi suka dasa gulmarta,Mimi tace tayi ta Gama ganin kwaf tazo Kuma Nabeel ya Mata nisa,Basma tace bar shegiya Ni kadai ma na isheta tunaninta zai koma ya aurota ta cuci kanta,Hamida tana jinsu bata ko bi ta kansu ba ice cream dinta take Sha. Sai gab da magrib Nabeel ya dawo gidan ya iske me gyaran targade ya saita kafar Hamida zai Kama kenan Lele yace Malam lfy? Yace gyaran targade aka kirani nayi,a'a dakata fada min karatun targaden Ni na Kama Mata,Me gyara yace gado Iyayennmu Suka bar mana akan me Zan baka sai dai in baka so na tafi,yace jeka mun gode,Mimi tace Lele Ina ruwanka Wai Kai me yake damunka ne baza ka kula da matarka ba sai shishishigi,Bai cewa Mimi komai ba ya fita,Chemist ya wuce sai da ya Nemo Mata cream na shafawa targade sannan ya kawo ya iske tana dakinta tayi bacci ma,Bai sani ba Yana fita Mimi tasa me gyaran targade ya gyarawa Hamida,tana kallo ya Shiga room din da Hamida take,bacci ya iske tana nan sanye da abayarta dama har yanzu kayanta kala Uku ne Mimi Taki ta siya Mata wasu itama Hamida bata Nema a siya Mata ba kullum ta cire sai ta wanke ta goge sai ta sa dayar Haka take rayuwa da Kaya kala Uku rak,bra dinta Guda daya ce duk ta tale ta lalace Haka take manage, panties dinta uku kacal Suma Kamar zasu Fado sabo da sun bude har sun fara yagewa ma, Mimi kuma tana kallo,Affa Bai sani ba tunda shi gani yayi Mimi farko tana son Hamida yasan zata kula da ita. Nabeel ne ya ware wasu kudade masu ciwo Nan gaba zai gwangwaje ta da Kaya. Cream din ya ajiye Mata a gefen bed din ya bar Mata short note ki dinga shafawa a rauninki kullum. Ko da ta farka ta gani bata iya karantawa ba gashi ta fuskanci kamar Mimi bata sonta yanzu sai tace bari na ajiye idan me lesson yazo ya karanta min. Sai washe gari da me lesson yazo tace Malam karanta min wannan takardar,karba yayi ya karanta Mata sannan tace na gode duk jikinta yayi sanyi sabo da yanda Mimi yanzu har harararta take Yi ta rasa dalili. Haka ta zauna dirshan Shehu ya koya Mata karatu da rubutu ta dawo ciki,Mimi ce ta kalleta ta harareta da sauri Hamida ta sadda Kai kasa ta koma Gaban Mimi ta durkusa tace Mimi ko na Miki wani laifi ne? Ki yafe min idan wani abin nayi miki ta kwabe fuska kamar zata Yi kuka,Mimi tace bana so ki dinga Shiga Harkar zuria ta tunda kece Kika bata min yaro har yaje Yana abinda bai dace ba kuma ya rasa da wacce zaiyi sai da ke watsatsiya wa ya sani ko iyayenki ne tun a sali suka Yi Haka ko ma ke ba Yar sunna bace Bamu sani ba ance Mana marainiya ce ke,daga gani biri yayi Kama da mutum rashin kamun kanki ya nuna da alama ke ba Yar sunna bace,Hamida gaba daya hawaye ya wanke mata fuska ranta bai taba baci ba irin yau,a duniya yauce rana ta farko da zata Fara tsinewa kanta,Mimi tace Allah ya gani dama can Ni dannewa nakeyi wa ya sani ma ko yawon bin maza kike ba cikin dana bane Kika lakaba Masa gashi Ni an jajibo min ke dama can yawon karuwancinki kikeyi Ni ban yarda cikin dana bane Allah ya rufa Mana asiri yaron baizo da Rai ba,can ke Kika San inda Kika samo cikin danki. Abinda Yan iskan leburori ne suke muku ciki,Ina yaro na Ina ke ki kalli Nabeel one in town muma munyi shirme da kuka fada ba bincike ba komai Muka dakko ki zuriyarmu Zaki yada Mana mugun iri,Kuma Ni gidana Zaki bar... tsawar Affa ce ta katse Mimi kukan Hamida ne kawai ke tashi,Affa yace karya kike wanne irin rashin adalci ne wannan da son Kai ai dazu duk naji zancen da kuke da matar Lele wato Kun hada baki to wallahi son zuciya shike cutarmu ita ba ya bace,ko Wanda aka haifo Dan shege lefinsa ne yazo a Haka? Gidana nane ba gidanki ba wallahi Hamida tana gidan Nan Inshaallah sai na tsaya Mata na bata ilimi Kuma Nan gaba Indai tace tana son Lele sai na aurarta ga shi ko Yana so ko baya so,yaro ya amsa shine da Kansa ya lalata yarinya sannan ki rufe Ido ki take gaskiya kiri kiri sabo son zuciya. Ki sani munyi da marikanta Hamida ta dawo hannuna nine Zan kula da ita na bata ilimi sannan na aurar da ita ga Wanda take so,duk waye ya jawo wannan in ba Kai ba tun yaushe Yaro yake so ka Masa aure kaki Kaine ka jawo,da naki Yi Masa aure sai nace yaje ya lalata Yar wani cewar Affa,to Ni Kuma wallahi Matukar kace zaka aurawa Lele ita sai na bar gidanka karshen zamana a gidanka kenan,to ki bari ta samu ilimi ta goge tasan fari da baki Inshaallah Ni Kuma in har tace Lele take so sai na aura Mata shi. Affa ne yace taso Hamida daina kuka,Hamida tana shesheka ta mike tace wallahi Allah Affa shine ya min ciki babu abinda Bai taba min ba duka dangerous part dina ko Ina ba inda ya bari na rantse da wallahi tallahi Affa sai da yayi Murmushi rantsuwa ta sake rantsewa da rantsuwa,a dakko Qurani Zan dafa Ni kuma shima Yaya kyakyawa yazo ya dafa. Duk abinda akeyi Nabeel Yana ji yazo gaida Iyayensa kenan yaji Mimi tana cin zarafin Hamida sai ta bashi tausayi,fasa Shiga yayi ya juya zai tafi abinsa sai ya fasa ya dawo ya sake tsayawa a bakin kofar palon Yana Jin komai ,ita kam Mimi Tsaki taja ta haura sama,Hamida tace a maida Ni kauyenmu nasan su baza su fada min haka ba suna kauna ta na fasa karatun a maida ni wajen Yaya Sulaiman dina,Affa yace karki sake ki bar gidan Nan kina tafiya za a San Kuma me za a sake lakaba Miki kinji ko, to tsakani da Allah na fada Affa bana so a dinga sani biyayyar dole alhalin Ina da gidan uba,Kar azo a dinga zagin iyayena nazo na gaza hakuri a sake ce min karuwa abinda yasa bana son Zama a gidan wani kenan duk tsiya gwara naka Yan Uwana sune dole na,babu yanda za ayi a zaunar dani Kuma azo kullum a zageni ba ni wallahi bana son wannan,idan dan su Basma ne zasu zageni ko a jikina amma Mimi fa haba Affa idan auren Lele nake duk tsiya Zan hakura ko me za a min biyayyar aure ce Kuma Kun Zama iyaye na amma haka Kawai bazai yuwu yazo ya dirkeni da ciki ba azo Kuma ace min karuwa, ba ai min adalci ba wallahi zan iya Kai Kara human right ta bi min hakki na,Affa yace kwantar da hankakinki nine human right dinki Hamida duk abinda aka Miki ba daidai ba ki fada min. Ai komai sai nayi adalci idan aka min ba daidai ba Zan fada ma idan aka faranta min Zan fada maka shine adalci ta sale yace anyi balancing kenan,Affa yayi dariya yace good,Hamida bata riko kamar ba ita ba ta kyalkyale dariya tace Ina da hankali fa Kawai kallon mutane nake ai inda tayi siriri Nan take tsinkewa ko ya kace Affa? Affa ya sake sakin Dariya yace ja'ira da iya hausa tace ai gaskiya ne Affa ai gwara in fadi gaskiya kaga yanzu na San nayi wai makaho ya taka kashinsa yace yanzu nasan nayi Nabeel Yana daga bakin kofa ya dinga dariya, Affa Yana ta janta haka suna Hira Nabeel yayi mamakin Hamida a ransa yace Ashe tana da hankali. Tace Affa muma fa Yan duniya ne wallahi Yasin kaji kwarankwatsa dubu duk iya shege ba Wanda bamu iya ba ni ko da waye Zan ja tun daga kauyenmu har zuwa majalisar dinkin duniya za aje dani akan rigima,Ni bana Jin kaina tana magana tana nuna kanta da yatsa tace duk in kaga anyi fada dani akan gaskiya ne Kuma har fadar shugaban kasa Zan ja da mutum,shima Lelen da kake gani Affa duk na gama tara shi Ina Nan da shi a cikin makokon makwallaton hanji na,badan ma Yaya kyakyawa bane Allah na tuba Nawa yake a wajena,in kaga an raina Ni to Ni na so amma Zan bada kala a gidan Nan Ina ma a Kano ne yau da a hukumar hisba Zan kwana bazan dawo ba sai an dauki mataki bawan Allah yazo hhar kauye wallahi ban taba sanin Yaya kyakyawa bai da Imani ba sai yanzu yanda muke da shi da yanda na bashi Amana a lokacin idan ya fada wuta Ina ganin Zan iya binsa amma ya min haka Affa ba kusan abinda Suka min da matarsa ba ne, lebe ta cije tace amma tunda Yaya Kyakyawa ne ba komai ya wuce na yafe masa a amma matarsa bazan taba yafe Mata ba,ta dukeni ta hantareni,ta nuna min kiyayya sannasannan watsa min ruwa ba abinda Bata min ba ta maida Ni Yar aikinta nasan me nake amma na hakura na maida kaina banza Kuma wallahi duk sabo da Yaya kyakyawa nayi amma baya gani Yana kallona a banz....kuka ne ya kwacewa Basma ta Mike Kawai ta Shige dakinta. Jikin Nabeel ne yayi sanyi Kamar baiji komai ba ya shigo da sallama,Affa ya kalle shi kawai ya mike ya haura sama,Nabeel Kuwa direct bedroom din Hamida ya nufa. Yana bude kofa ta dago Kai tana saman bed ta wani daure Fuska,Zama yayi a hankali gefen bed dinta Yana nuku nuku,gefe can ta matsa ta sake hade rai kamar ba ita ba shi kanshi yayi mamaki,ya tsura Mata Ido da masifa tace lafiya?yace ahm....Hamida....yayi Shuru tace Malam kayi magana ko ka fitar min a daki da sauri ya kalleta cike da mamaki,tana share hawaye tace ae duk da gidanku ne Nan dakina nane in baka da abin cewa fitar min a daki,Kansa ya nuna yace ni kike kora Hamida,nine fa Yaya kyakyawanki,Ni Kuwa nasan Kaine Nabeel ba wani Yaya kyakyawa fitar min a daki ,okay naji Zan fita amma ki saurareni dan Allah ya furta tare da marairaice Fuska tace ka matsa daga kusa dani,Matsawa yayi kusa da ita kafadarsu tana gugan juna tana cewa ka matsa wallahi ko na maka rashin mutunci gashi ba wajen da zata matsa ta manne da jikin banko hannunsa yasa tare da tallafe habarta ya matsa a hankali da Niyyar ya kissing nata,da karfi ta fisge ranta a bace tace ai kayi na farko har abada baza ka sake ba fitar min a daki bani ba Kai har abada karka sake ka sake nuna ka sanni, Dan Allah Hamida ki tsaya ki saurareni naji bazan tabaki ba amma ki tsaya ki saurareni Dan Allah ki yafe min abinda na miki,Tsaki taja ta jawo hand bag din da ta kwacewa Basma ta kwada masa a bayansa tace fita bazan yafe ba wallahi Zan fadawa Affa,yanda ta nuna bata sanshi ba shi ya bashi mamaki ba shiri ya fice daga dakin ya bar gidan gaba Daya. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 7 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Mum Khad Maman Maheer D-Gurl Da wannan takaicin ya koma gidansa ko gama parking driver baiyi ba ya fice daga motar Yana shiga Basma ta taso taci wanka tana oyoyo wani Takaici ne ya kamashi a ransa ji yake kamar ma ya Zane ta,Tsaki yaja yace matsa I'm so tired ya wuce tare da haurawa sama ya shige bedroom dinsa ya fada saman bed tare da yin ruf da ciki,Kawai tunanin Hamida yakeyi,Basma ce ta shigo bata kula da yanayinsa ba ta fada Kansa ta makaleshi,Hannu yasa ya yakiceta daga jikinsa yace dan Allah karki dameni bana son kowa kusa dani tashi ki fita,Shagwaba ta fara Baby..a fusace ya juyo ta Mike ba shiri ta bar room din. Ranar bai iya bacci ba,in Banda tunanin Hamida ba abinda yake da irin halaccin da ta Masa,sai bayan Sallar asuba sannan bacci ya kwashe shi,Yana tashi 11am Fitowa yayi yace Basma ki shirya a week din Nan Zaki tafi Umrah,Basma gani takeyi tsabar soyayya ce tasa ta dinga murna tana zuba Masa godiya duk da Makkah ba bakuwarta bace amma ace Nabeel da Kansa ya biya Mata ai ta musamman ce,da Yamma Yana gida abin duniya ya Masa zafi Basma tazo tare da kwanciya a jikinsa tace honey yau na kusa 1month baka min sex ba wallahi Hakuri nake,yace kiyi Hakuri ki min Uzuri ke kanki kin San bani da lafiya,Basma bata rai tayi tace amma ka iya yiwa karuwar kauye ciki Ni ka kasa na gano ma kafi sonta da ni,ko can kake zagawa ne naga alama,Dama a sama yake Nan ba jira ya huce a kanta ya hau zuba Mata mari ta ko Ina,sai guduwa tayi tana kuka. A daren tazo ta dinga bashi hakuri kamar me Yana cewa ya hakura tace to sex din fa dan Allah,Haka ya lallabata baida feeling a kanta Sam,washe gari da safe Haka sake hanashi sakewa,Yana Palo tazo ta fara cire Masa riga da sauri ya tashi yace masu share yanar nan basu iya ba bari nayi da kaina sun bar gida duk Yana ya mike yayi waje ya dauki abin sharar Yana ya fara Yi ba uwar da yake cirewa amma akan Basma ya bawa Kansa aiki da kunya yace bai da feeling a kanta,daga sharar Yana sai jin tashin mota tayi Kawai ya figa ya fice. Gidansu ya tafi direct Hamida ya fara hangowa Shehu wanka Yana ta koya Mata karatu ta maida hankalinta,tasan da zuwansa amma ko inda yake bata kalla ba bare yasa rai ta ganshi,har wajen shehu ya tako tana ganin haka taci gaba da rubutunta,tana ji suka gaisa da shehu,yazo ya tsaya a kanta yaga ko kallonsa bata Yi ba,fuskarta ya leka tasa pencil ta tsokane Masa ido,da sauri ya matsa baya Kuma bata kalle shi ba tace Malam ja muje mu gama English muyi Hausa karshe kayi min darasin daukan wanka sabo da sabon saurayina,Nabeel har ya juya ya tafi ya dawo ya kalli Shehu yace Kai karka sake naga wannan iskancin a gidannan Kaine ma zaka Mata darasin wanka waye ya saka? Kai har wani wanka ka iya kalleka fa,Shehu yace wallahi Oga idan na nuna Mata sa janbaki ko Rihanna uwar dabbara jambaki ta gani sai ta yaba bare Namiji kalleta kyakyawa ai maza layi zasu dinga Yi,Nabeel ya hade girar sama data kasa yace wallahi ka koya Mata cin abincinka yazo karshe,Hamida tace dan Allah Malam kayi sauri bako zanyi,Shehu yaci gaba aka bar Nabeel a tsaye yaja kwafa ya shiga ciki ya gaida Mimi ya tambayi Affa tace Affa baya gida. Tana gama karatu tazo ta wuce Nabeel Yana kwance yayi matashi da cinyar Mimi,Bata ce komai ba tace Sannu da hutawa Mimi ta wuce bedroom dinta ta fesa wanka sai gata ta fito Palo sanye da sabuwar Riga da skert na Atamfa sun kamata daf ta zuba uban kyau ba wata kwalliya tayi ba powder Kawai ta shafa sai eyeliner da maroon jambaki,gashinta ta gyara kawai ta Masa acuci ta yafa siririn mayafinta sky Kalar atamfar takalminta me dan tudu sabo Kalar kayan duk cikin darasin Shehu ne,tace Mimi nayi bako,Nabeel ya zaci da wasa take Mimi Kuma murna take tayi ta samu miji tayi aure can su huta,Baki Mimi ta washe tace Allah ya hada kanku yasa mijin aure ne,Hamida tace Ameen,Nabeel ya kalleta kamar zai kurma ihu, tana fita yace Mimi Zan wuce tace ka gaida matarka,Dan Allah ka rike ta amana yace Inshaallah tace ka biya Mata Umrah Allah hada kawunanku a ransa yace ba amin ba a fili yace Ameen ya fice. Duk compound har garden ya duba ba Hamida ba labarinta motarsa ya shiga ya tuka da Kansa yayi waje Yana fita ya ganta a jikin motar doctor suna ta hira tana dariya har wani nutsuwa tayi duk haukar Nan bata Yi,kasa hakuri yayi ya fito cike da bala'i yace Malam I'm warning you for the last time don't cross my line a gain... don't ever in your entire life cross my line again,ka daina zuwa gidanmu ka daina kula min Mata,Na maka warning leave my wife alone yanda ya rufe Ido Yana masifa yaba Hamida tsoro amma ta maze,yace ke Kuma ki tuna yanzu ba yarinya bace ki Zama uwa da badan yaron ya mutu ba da yanzu raino kike,koma gida wallahi ko na farfasa Miki jiki yanda ya yo kanta da bala'i da gudu ta shigo gida,ya karewa doctor Ahmad kallo yace ka kiyayi kanka da Shiga gonata Zan maka abinda baka zato na fada maka,Ahmad yace Ina sonta ai Kai ba mijinta bane sabo da haka tace tana so na dole naci gaba da neman aure kuma bazan fasa ba,mu zuba Ni da Kai cewar Nabeel ya fasa tafiya ya koma cikin gidan. A tsakar gidan yaga Hamida tana latsa sabuwar Wayarta kamar zai Mata kuka a nutse ba hayaniya yace Hamida me kike kika maida kanki why Zaki dinga haka? Me nayi? Yanzu ki duba yanda Kika fita ko kunya komai ana gani na surarki yanzu haka dai dai ne,da danmu Yana raye da yanzu fa ke uwa ce shayarwa kike yi,Ina sonsa Kuma aurena zaiyi Kai mene naka a ciki sabo da me kake so na daina kulashi? kasa cewa komai yayi haka ya sake hasala Hamida ta yarda baya sonta juyawa tayi ta tafi abinta. Yau Nabeel ma tunda ya koma gida bai iya baccin kirki ba sabo da tunanin Hamida,washe gari da sassafe jallabiya Kawai ya zura ya taho gidan Mimi,ya iske Affa da Mimi sun fita ma wurin aiki, dakin Hamida ya kwankwasa bata zaci shi bane ta bude ya Shiga ciki baki ya bude ganin kayan sawa sababbi na alfarma iri iri tana shiryawa wardrobe,ya kalli kayan ya kalleta yace Hamida Indai akan kaya kike sonsa ki maida Masa Dan Allah Ni zan siya Miki ko mene,Ko kallonshi bata Yi ba taci gaba da shirya kayanta,Hamida I'm sorry na rokeki ki yafe min,na dade da yafe maka ka rabu dani kaje kayi rayuwarka nayi tawa,dan Allah ni Jahila wacce ba class dinka ba kaje wajen dai dai da ajinka Bai kamata ka zauna Kamar ni Yar Kauye kana kulani ba kamarka kana bani hakuri. Fita yayi da sauri sabo da ji yake kamar zai mutu gaba daya ya rasa Jin dadin duniya tunda ya hadu da Hamida duniya ta daina masa dadi gaba Daya Kawai ya rasa me yasa yake jinta a ransa. Haka Nabeel ya kasance kullum sai yaje wajen Hamida Yana rokonta ta saurare shi ma taki ko saurararsa tsakaninta da shi bakar magana. Sati na cika Basma ta shilla kasa Mai tsarki Nabeel kamar an Masa bushara da Aljanna,so yake ya fito yanzu gadan gadan ya nemi auren Hamida shine Kawai kwanciyar hankalinsa,doctor Ahmad ba bata lokaci shi biyan kudi yayi ma aka zanawa Hamida waec da Neco,kuskuren Hamida ba Wanda ta fadawa a gidan ba ruwanta Harkar gabanta takeyi ita kuma Mimi dama ta daina shiga harkarta Affa ne Kawai ke kulawa shima Aiki duk ya musu yawa gashi Yana Shirin tafiya Uk Karo karatu. Wani eatery Nabeel da Ammar suka shiga Lele sanye yake cikin kana Nan Kaya yaje zai Yi take away shi da friend dinsa Ammar,Ammar yace Lele kalli can kamar Yarinyar gidan ku ce da wannan doctor din,da sauri Nabeel ya kalli wajen yaga Hamida an kashe dauri cikin wani shegen lace harda maka tafkeken glass na Yan gayu tayi Matukar haduwa sai kace daga kasar waje ta sauka,Shi Nabeel mamakin wayewarta yake lokaci daya,Bai San dama tana ta kallon me akeyi a birni ba,a fusace ya nufi wajen Ammar Yana rike shi Yana Lele banda fada yasan zuciyar Nabeel,da karaji yace ba nace karka sake kula min Mata ba Kai wanne dakiki ne,Ahmad ya mike tsaye yace kai kullum ba abinda ka iya sai masifa,ai Mata lallashinsu akeyi a haka zata aureka ko iya kyau Mata suke so?,me ka Mata a rayuwa in Banda kaje kauyensu ka Mata ciki,nine na taimaketa Ni na maida ta mutum kalli kayan jikinta komai Ni na siya mata Kai me kayi Mata na inganta rayuwarta,ka kalleta duk kayanta da take sawa ko iyayenka basu iya siya Mata ba komai nine na Mata Kuma Ina Kan Yi mata,komai Ni na Mata,Nabeel Takaici ya kamashi yace kin gani kinji Kuma ji gori yake miki wannan ya isheki ki gane mutumin kirki ne ko kuwa, Ahmad yace Kaine mutumin banza tunda Kai karuwa ka maidata,Hamida sai ta fashe da kuka tana nadamar surutunta da bata fada ba da ba Wanda ya sani,Nabeel yace wallahi ka sake ka Kara kiranta karuwa sai nayi maganinka,Ahmad yace oho ko karuwancin take haka Zan aureta Kai Kayi tunanin aurenta ne banza dabb.....kafin ya rufe baki Hamida ta kifa masa mari tace na daina sonka kazo ka kwashi tarkacenka,ta fige gyalenta ta jefa Masa da glass din tace ko wanne Dan iskan Namiji sai rashin mutunci duk na kirki sun Kare sai yan iska marasa mutunci,Nabeel Kamar ya taka rawar disco ya dauki mayafin yabi Hamida yace yi hakuri my love a rufe min jikin nawa ya yafa Mata ko kulashi shima bata yi ba ta Kara gaba tare da shigwewa taxi. Tana shiga cikin gida ta zauna a palon Mimi ita kadai Nabeel ya tsaya a jikin kofa ya wani labe Yana kallonta tace na tsinewa kaina kafin kowa ya tsine min Ni Hamida Kabir Tahir na tsinewa kaina sau Uku,Dan ubana Wai ni dabba ce bazan hankali ba,wannan tun ba ayi nisa ba ya Kama gori,shi wannan Dan iskan Nabeel din Ni ya zanyi da su,jakantata ce Ni na jawa kaina yanzu da na nutsu nayi hankali ban fada an min ciki ba ai da na zauna lafiya to da yake ni awon igiya ce sai na fada, dole na gyara kuskurena ba ruwana bazan sake cewa Naga duwawunsa ba ko wani farar takashinsa ya karata can da abarsa yaje uwar Basma ma tayi ta kalla karewa,amma tsakani da Allah banyi abin kirki ba haka Kawai na dinga ta'adin baki Ina fadawa duniya naga duwaiwai to dana gani sai akai me in banda haukata shima da halinsa dan duwaiwan burar .....ta narkawa Nabeel ashar Yana jinta yayi Dariya a cikinsa kamar me,mikewa tayi tsaye tace tashi Yar Iska gantalalliya tunda bani da me min fada na dinga yiwa kaina kowa ya huta,Kuma Nabeel alfarmar Annabi na barshi. Ido ya zaro waje ya Fado palon yace dan Allah Hamida karki min Haka,da wallahi kina so na kina girmamani yanzu me nayi Miki tunda dan iskan doctor din Nan ya shigo shike Nan ya canja kulaki,Harara ta watsa Masa tace sai kaga ana biki ma wallahi,gwiwowinsa ya zube a kasa ya kwantar da murya kamar zaiyi kuka yace Hamida please ya hade hannayensa biyu yace na gano sonki nake Hamida ban taba son wata ba a duniya sai ke,da ban gane ba sai yanzu na tabbatar Ina sonki Hamida fiye da kowa,kece farin cikina,bazan iya jure ganinki da wani ba,Tsaki taja ta Shige dakinta tare da rufe kofarta. Haka ya gaji da jira ya fita jiki a sanyaye,Wasa Wasa Nabeel ya kasa cin abinci sai dai Abu me ruwa,Mimi taga duk ya canja kullum sai taga ya zauna Yana ta tunani abinci baya ci,duk ya rame sosai,Tayi tunanin rashin Basma ne ta tafi Makkah,Bmbata San me akeyi ba,Ya samu kwangila me tsoka amma ya kasa zuwa ayi aikin kudi zai samu miliyoyi na kirki,daga lokacin idan yayi ya Zama hamshakin gaske amma tunanin Hamida yasa Office dinma ya daina zuwa,idan yaje gidan Mimi ta daina Fitowa yana ganinta Sam dakinta take kullewa idan har yaga Hamida to Doctor dinta ne yazo ta fita kofar gida tayi zance tun Yana masifa har ya dawo ya gaza,ya zaci abinda doctor ya Mata na gori zata daina kulashi amma sai yaga ya lallabata sun koma sun jone. Mimi ce ta tasa shi a gaba Nabeel Wai meke damunka mene ne ka fada min? Baka da lafiya kake boye min ko wata cutar ce ta kamaka,abinci ka daina ci nasan dai matarka Bata nan dole a nan zaka ci abinci me ya faru? Ya rasa inda zai sa Kansa in banda Ammar ba Wanda yasan zancen yasan Yana fadawa Mimi za a samu matsala,Affa Kuma yace sai in Nabeela ta yarda sannan zai aura Masa ita, ko me zaiyi Matukar Hamida bata sonsa bazai same ta ba,shi Kam rayuwa babu Hamida gwara ya mutu ma da yaga bakin ciki,Shuru yayiwa Mimi, Hamida tana jinsu tana kitchen kin Fitowa tayi,Mimi tace dan ubanka baza ka fada min meke damunka ba gashi Nan sai tunani kake Yi,Nabeel ya wayance tare da sakin murmushin yake yace ba komai fa Mimi a wajen aiki ne wata kwangila nayi asara,to ba Allah ne ke badawa ba Mene na damuwa haka,idan baka da jari ga gida na Nan na Kano nasan zai Kai Million hamsim yanzu tunda a g.r.a yake Kuma babban gidane sai ka siyar,wancan ma dana siya kwana nan duk ka siyar ka hada na bar maka,Ko a dawo da Fadila ta dinga tayaka Hira? Murmushin karfin hali yayi yace no ba sai an siyar ba,to kayi Hakuri ka fawwalawa Allah,Nabeel ya kalli Mimi yace hmm Kawai,rabon ma da yaga Hamida har ya manta sai dai ya hange ta a wajen Doctor,wucewa tayi da plate din Indomie tana waya da Saurayinta tace gashi na dafa Indomie zanci ka daina damuwa,Nabeel kamar ya kurma ihu haka yaji ta shige bedroom ta kulle,Mimi tana ta Murna tace Hamida doctor har ya siya Mata form din School of nursing yace kafin ayi biki zata Fara zuwa makaranta in anyi aurensu taci gaba a can kaga mun huta da Kaya,Affa Kuma ya amince ta nuna Masa komai da yardar sa akayi komai sun kusa kawo kudi ma,Bari naje na dakko ma form din ka gani Mimi ta tashi tana rawar kafa ta haura sama,Nabeel bai San Yana hawaye ba sai da yaji laima sannan ya shafa fuskarsa kafin Mimi ta dawo ya Shiga kitchen yayi sauri ya wanke fuskarsa ya dakko ruwan sanyi Yana Sha kamar bai damu ba. A hannun Mimi ya gani ko karbar form din bai iya Yi ba,hankalinsa ya tashi da yaji za a kawo kudi,yace Mimi Kuma iyayenta sun sani? Tace yaro har yaje kauyen ya gaishe su da danginsa da komai Kai abinfa ba na Wasa ba ne wallahi yaje can itama Hamidan ana kawo kudi zata tafi can, Nabeel mikewa yayi yace bari na karbi number dinsa ma dinga gaisawa Mimi tace ya kamata,ya nufi dakin Hamida, Yana knocking gabanta ya Fadi ta bude kofa tace mene ne? Yace magana za muyi,Fadi a Nan,Hamida Ni kike fadawa haka? Kallon tara Saura quarter ta Masa tace da kasan yanda na tsan....kasa karasawa tayi kallmar ta Mata nauyi, daurewa tayi tace Malam ka fita Ni ba Yar Iska ba ce irinka,mashayin giya mazinaci ka cuceni ta fashe da kuka,a zahiri Hamida fakewa take da kukan an cuceceta amma har ranta kukan son Nabeel takeyi ta kasa cire shi a ranta tayi tayi ta kasa kullum kaunarsa karuwa take a ranta Kuma kullum son ganinsa take tana son kasancewa da shi amma dole ta hakura ta tursasa zuciyarta. Durkusawa yayi har kasa a gabanta tana kuka,hawaye kamar ya zubowa Nabeel yace please Hamida kome kike so a duniya Zan Miki,matarka fa in ta dawo me zaka ce? Mufa musulmai ne Allah ya halatta min Mata Hudu,ya narkewa Hamida tace ka rike matarka Ni wallahi bazan.....bakinsa taji cikin nata Ido ta lumshe ta sa karfi ta ture shi tare da shigewa toilet ta kulle kofa barshi a Nan durkushe ya kifa Kansa a saman bed dinta,a toilet din ta durkeshi tana rusa uban kuka kasa kasa yanda bazai ji ba Kuma tayi ma kanta alkawari baza ta auri Nabeel ba duk son da take Masa, sai da Nabeel ya gaji da Zama sannan ya mike ya bar dakin ko Mimi baiwa sallama ba ya wuce gida direct. Shigarsa gida ke da wuya ya fada saman bed dinsa ya kifa cikinsa da kyar ya iya tashi yayi Sallar Isha ya kwanta bacci ya gagari idonsa,In banda Hamida ba abinda yake tunani,da komai nata shi yake tunawa,Mimi a cikin dare ta Kira Ammar akan yaje yaji abinda ke damun abokinsa,Ammar yasan komai amma Kawai yace to,Bai je wajen Nabeel ba sai da safe ya iske Nabeel Yana kwance zazzabi ya rufe shi ko motsi bai iyawa tsoro ne ya kamashi,Bargo ya lulluba Masa. Da sauri ya Kira doctor aka Masa gwaje gwaje hawan jini ya kamashi da karfi,an bashi magunguna da allurai an Masa Karin ruwa amma Nabeel babu sauki a abin nasa,Ammar duk iya kokarinsa yayi kasa hakura yayi yace mu tafi asibiti Kawai Nabeel yace bazai je ba,Lele so kake ka kashe kanka Kar ka manta Hamida yanzu Bata sonka gwara ka kyaleta ka fuskanci gaskiya ka rabu da ita sai kace Yar gwal,Nabeel baya iya Maganar kirki,Ammar yace to gaskiya Zan Kira Mimi,Nabeel ya girgiza Masa kai hawaye Kawai ya fara sakkowa Nabeel,tausayi ya bawa Ammar yace Kai Hamida kake so? Ya daga Masa Kai Wai ae,yace to tsaya naje na lallabota Allah yasa tazo ta kula da Kai,Ammar gidan Mimi yaje da sauri ya iske kamar kullum duk suna wayen Aiki sai Hamida,hankali tashe yace Hamida ga Nabeel can zai mutu sai abinda Hali yayi yace kije gidansa zai bar Miki wasiyya,Gaban Hamida ya fadi ta dora Hannu aka tace na shiga uku me ya sameshi yace ciwon zuciya,nayi nayi muje asibiti yaki yanzu ma kamar kakin jini ya fara Mimi ma ta tafi can kiyi sauri,Hamida tsalle tayi ta saki kuka ta fara tumami tana birgima Ammar ya saki baki Yana kallon ikon Allah yace ba kuka zakiyi ba kije ki bashi agaji idan Yana da sauran rayuwa to idan ya mutu duk munyi Rashi,Hamida ta daga hannaye sama tace bazai mutu ba...bazai mutu ba...in Allah ya yarda bazai mutu....bakin ka sari motar tantan ...bakinka ya sari tsohuwar tifa,tana kuka tace muje ka kaini,Ammar yace ni asibiti zanje karbo magani,mayafi ta figa ta Dora saman silk doguwar rigarta dark blue,ta fice da gudu takalman ma a Hannu ta eba,Tana Fitowa taga Doctor Ahmad dama sunyi zaizo ya fito da sauri ya ganta a hargitse. Yace Honey lafiya? Da bala'i tace karka isheni dan Allah zanyi rashi,Ya sake cewa Hamida...karka dameni Malam ka tafi sai na kiraka a waya,Ahmad yaji haushi ya figi motarsa a ransa yace ki gama wulakancin wallahi Kika shigo sai na Rama Zaki Gane kurenki baki San waye Ni ba dama kwadayi ne ya kawo ni in aura na gurjeki. Hamida Kuwa taxi ta shiga ta Masa kwatance kudi ta Mika Masa dubu Daya,yace Hajiya canjin tace na bar maka ta fyalla da gudu cikin gidan, dama tasan har room dinsa Kawai Shiga tayi lokacin ma duk ya jigata bai ma San me yake ba,Hamida tana hawaye kasa kasa ta ganshi cikin bargo,gefen fuskarsa dake waje ta taba taji mugun zafi Yana ta rawar sanyi,kumatunsa ta tallafe da Hannu biyu tace Yaya kyakyawa,tana fadan haka sai da yasan itace yaji wani sanyi a ransa duk da jikin da yake ji,yace sanyi nake ji kimin wani abin,Hamida tace ban San me Zan maka ba,Yana numfarfashi yace dumin jikinki dan Allah tace tab ba ruwana bamu da aure ai nayi hankali nida Namiji haihata haihata,wallahi... ba.. abinda Zan Miki kinji na rantse,Ya sake narkewa Kamar ransa zai fita harda tari, Hamida tsoro ya kamata,taji yace Hajiya Bilki me kosai tana bina bashin naira dari idan Allah yayi min rasuwa kije ki Bata,Ido ta zaro ta saki kuka,ya sake cewa sannan....Jamilu me dinki shima Yana bina dari hudu da hamsim ki bashi cikin abinda Allah ya hore min,...ya sake yin tari...muryarsa na rawa kamar zai sheka lahira yace Lawan kwalli me aski na shima Yana bina dari uku ,akwai wasu maza biyu ban San inda Zan same su ba amma idan na rasu a dauka cikin abinda Allah ya hore min ayi musu sadaka ta naira dari dari bazai wuce haka ba,Kimin Addua Allah ya min Rahma kinji.. Kafin ya rufe baki Hamida ta shide barkosa jikinta na rawa tana lallashinsa tana baza ka mutu ba Inshaallah baza ka mutu ka barni ba, Nabeel ya sake lumewa a jikin Hamida ya maida Kansa saman kirjinta yayi wani lamo Yana sake shigewa jikinta,gashinsa ta shafa da yake birgeta tace abinci Zan maka ai da sauri yace ban warke ba ya sake narkewa,yace Ammar ma Yana bina dubu uku nasan zai yafe min amma a bashi dai,,Hamida a ranta tace wannan shine final next week Ahmad zai kawo kudin aure dole ma ka hakura da ni,Nabeel a ransa murna yake Hamida ashe tana dan sonsa Allah yasa ta aure shi haka yake fata, ya wani makalkaleta Sharhi pls AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 8 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Yan albarka KHADIJA DEEY GIMBIYW DIYAR KATIBI HAUWA J MAMAN AHMAD OUM NU'AIMA M DEWU MRS NAZIR XARA UMMY MANGA HABEEBAH HIBBAT MMN SADEEQ MUMMY NEEMRAH Tunawa tayi da abinda ya mata a farko tuni ta fisge jikinta ta dirgo kasa tace bari na ma girki ka lallaba ka tashi kayi wanka,Ido ya zura mata kawai amma hakan ma yaji sauki sosai ya samu nutsuwa,da farko yace bazai iya tashi ba sai gashi ya mike ya shige toilet wanka yayi ya sake yin brush ya fito sanye da jallabiya blue mayen turare duk cuta yake amma komai nasa kamshi ko me ya taba sai yayi kamshinsa me sa nutsuwa. Kitchen ya bi Hamida ya tsaya tare da zura mata Ido kamar tsohon maye,juyowa tayi ta ganshi a tsaye a kofar kitchen ya harde hannaye a gaban kirjinsa bata ce komai ba kunya ma yake bata ta dan dafa Masa dankali da miyar kwai kamar ba shine ranga ranga ba,ba ruwanta tana gama Masa girkin ta ajiye a dining sannan ta hau gyara Masa gidan sai binta yake da kallo duk inda ta matsa idonsa Yana kanta,ko kallonsa Hamida bata Yi aikinta take Yi har bedroom dinsa sai data gyara ko Ina fes sannan ta gyara jikinta ta yafa mayafinta sosai ta fito. A Palo ta iske shi kwance a saman kujera duk ya Zama abin tausayi,nesa da shi ta durkusa a nutse tace abincin fa? Shi Kam mamaki take bashi kamar aljana har ta canja Masa gaba daya lokaci guda,idonsa ya lumshe tare da cije pink lips dinsa na kasa, hannunsa daya ya daura saman goshinsa ya dafe sabo da yanda Kansa ke Sara Masa,satar kallonsa takeyi Jin bai magana ba,ta mike jikinta a sanyaye ta zubo Masa abincin a plate ta ajiye a gabansa,komawa tayi kitchen ta dakko Masa fresh milk da ruwa ta tsiyaya Masa milk din a glass cup,tace abincin fa kaci dan Allah,Hannu ya daga mata da kyar yace dakko min magunguna sauri kaina,da sauri ta mike ta haura sama sai gata ta dawo da magungunan ta bude Masa ledar ya balla Wanda zai iya Sha ya Sha,ta tsura Masa Ido a tsorace. Wayarta ta zaro ta mike ta Shige kitchen,da kallo ya bita ji yake kamar zuciyarsa ta fashe,tunani yake ta wacce hanyar zai shawo Kan Hamida yasan ma Doctor Ahmad ne ya Kirata kishinsa Ahmad ma Yana da kudi Kuma gashi matashi duk da Nabeel yasan ya fishi komai amma yasan shima bashi da makusa. Hamida Kuwa number Ammar ta Kira wacce ta karba yace idan da matsala ta neme shi,Yana dagawa tace Hamida ce,yace ya ake ciki? kazo ka kwana da shi da dare gaskiya baiji sauki ba ya kamata ma a kaishi asibiti idan baza ka kaishi ba ni sai na kaishi da kaina,maralafiya haka an barshi a gida ta furta Kamar zata Yi kuka,Ammar yana sani yace aiki ya min yawa kuje asibitin zanzo anjima amma karki Kira su Mimi ya Mata kwatancen asibitin da zata kaishi yace amma karki biya kwandala za a biya,Hamida tace to ta kashe wayar, fitowa tayi Yana Palo tace na tafi Allah Kara sauki,Yana kiranta ko juyowa bata Yi ba ta wuce abinta tana Fitowa taga Doctor Ahmad Yana kallonta a tsaye jikin mota a ransa yace taje ya gama eban banza wannan Yarinyar sai na kure mata karshen malejin jarabarta ashe tana lallabawa,Hamida ta kalle shi ya kalleta. Ya kalleta shekeke yace me ya kaiki gidan Namiji bayan matarsa bata Nan? ran Hamida ya baci tace ka daina bin kwakwafi na kana zargina Kai din wani na kirki ne ko Kai baka wa Allah laifi zaka fada min magana,tana gama fadan haka tayi maza ta karasa mainroad idonta cike da hawaye tana tafiya tana magana ita kadai tace na cuci kaina dana tonawa kaina asiri yanzu wa zai yarda Dani?a zuciyarta tace Allah shi Yana gani tace hakane Allah shi yasan namijin hankaka.. Me taxi ta Nemo tunda Bata iya tuka mota ba sannan Kuma taga Nabeel baison a San baida lafiya,a gate me taxi ya tsaya ta shiga abin Mamaki Ahmad Yana cikin mota yayi parking daga baya yanda Hamida baza ta ganshi ba. Hamida tana shiga ta iske Nabeel idonsa yayi jajir Kamar Wanda yayi kuka,Hankalin Hamida idan yayi dubu to ya tashi ta kalle shi zata Yi kuka Fuska a kwabe ta riko hannunsa tace tashi mu tafi asibiti tunda baka so kowa ya sani,Kai ya girgiza mata shi bazai je ba,Hannunsa ta Kama ta dinga jijjiga shi tana rokonsa ka tashi muje dan Allah,ganin yaki tashi tasa karfinta wai zata daga shi kamar me Jan akuya,ganin baida niyya gashi ta kasa dagashi tace haba Leleluwa,Dan Leleluwan Mimi... Lelen gayu... Lelen kamshi...ko ba Lelen kamshi bane? Kallonta yayi ta bashi dariya ya girgiza Kai Wai ba Lelen kamshi bane shi,Tace to Lelen mene? Ko Lelen Kashi ne? Fuska ya daure tace ahhh shagwalliya to Lelen mene? da shagwaba kamar yaro yace naki, da sauri tace Lelen Pipi Hamida,kallonta yayi Jin sabon suna wai Pipi,tace Malam Shehu ne yace sunan gayu ne Nick name Pipi,Murmushi yayi tace taso to Hannu ya Mika Mata ta tallafa Masa ya mike hannunsa ta riko ta rufe ko Ina na gidan Suka fito,Ahmad Yana kallo takaici ya kamashi yace sai na dau mataki duk ya gama kwashe Mata albarkatu Ni Kuma sai dai na auri kankaren kanzo Yaja kwafa ya fisgi motarsa ya bar wajen. Hamida da sauri ta bude Masa mota ya Shiga baya itama ta shiga ta zauna gefensa,ta yiwa me taxi kwatacen asibitin suna zuwa Ammar yazo shima shi ya tsaya aka yiwa Nabeel duk abinda ya kamata sannan akace ba sai an bashi gado ba. A gidan Mimi Ammar ya sauke Hamida yaja shi da Nabeel Suka tafi tana shiga ciki ta iske Mimi da Affa suna dining ta gaida su,Affa yace Ina Kika je ne? tace wani shago naje Zan Nemo wani littafi da Malam yace na siyo ban samo ba amma na bawa Uncle Inuwa ya siyo min,Okay that's good cewar Affa, Mimi Murmushi Kawai tayi tace ai Hamida ta fara hankali Naga sai gogewa take kullum gashi ta Kara haske sosai tayi kyau da kiba,Hamida harda rufe Fuska taji kunya ta juya ta Shige bedroom dinta. Alwala tayi lokacin magriba tayi ta gabatar da Sallah a nutse Shehu duk Yana koya Mata yanzu ta iya abubuwa dai dai gwargwado. Bayan kwana Uku Nabeel yaji sauki sosai har ma yazo gaida Mimi amma bai samu ganin Hamida ba ta kulle ma kofarta da key suna ta waya da Doctor Ahmad akan maganar turo kudin aure sabo da Ahmad ya danne duk abinda ya gani sai Hamida ta shiga hannunsa sannan zata gane shayi ruwa ne,Lele har ya tafi bai ga Hamida ba yasan shine bata son gani haka ya shiga motarsa ya koma gida. Da dare bayan ya dawo daga masallaci Basma ce a harabar masallacin dakin ka'aba ta gaji yau satinta kusan uku kenan a Makkah idan tace zata dawo Lele yace ta Kara kwanaki ta Masa addua,Wayar Nabeel ta Kira Suka gaisa tace Honey gobe Zan dawo fa,Nabeel Yana kwance ya mike zaune yace no akwai adduoin da nake so ki min a dakin ka'abah dawafi bakwai sau bakwai kullum har kwana bakwai kice abinda Nabeel mijina ke so a ransa Allah ka bashi Allah ka cikawa Nabeel mijina burinsa haka Zaki dinga fada a dawafi kinji my wife. Basma tace wallahi bazan zauna ba na gaji haka kawai ka turoni Makkah Umrah ba watan Ramadan ba ba komai ba,Addua kana ta sani Ina maka kala kala kullum kace abinda kake so a ranka Allah ya baka Wai me kake so ne haka,Nabeel a ransa yace Hamida a fili yace calm down Ni da akwai Hali ma dan Allah ki zauna ki min aikin hajji,Wallahi bazan zauna ba kwana Nan fa aka Yi karamar Sallah ni ba takari ba ba komai ba Haka Kawai daga Nan Kawai na zauna nayi takarci mana to wallahi gobe i yanzu Ina gida kazo airport ka daukeni 5pm na gaji,Nabeel yace ke kullum idan zakiyi magana bakya taba cewa Inshaallah sai dai Kawai ki fada direct,Yo me zai hanani dawowa gobe bazan zauna ba wallahi,Wayarsa ya datse sabo da zai iya fusata. Nabeel ya fara murmurewa tunaninsa Hamida zata so shi tunda yaga ta damu Sanda baida lafiya,5pm ya manta ma Basma zata dawo sai Wayarta yaji tace Ina airport kazo ne? Yace au yau dama fa Zaki dawo na tuna,Basma tace bazan jiraka ba ni gani Nan na shigo airport car...kafin ta karasa ya datse Kiran sabo da ta fiye fadar magana yanda taga Dama sabo da ta taso cikin kudi,15mnt sai ga Basma ta dawo Yana kallon ball ta shigo kallonta Kawai yayi ya dauke Kai sabo da yaga tana ganin damarsa. Itama ganin haka ko kulashi bata Yi ba ta haura sama da kayanta. Key din mota ya dauka ya fice zuwa gidan su Ammar estate din su Ammar ba kowa haka yayi parking a bakin gate ya fito yasha kyau Yana taku dai dai kawai Yan daba ya gani sun zagayeshi da makamai,abin ya bashi mamaki dole mutum ya furgita,Nan take Suka ce koma cikin mota ba musu ya koma ba tare da ya nuna ya razana ba,mutum uku ne suka Shiga motar biyu a baya Daya a gaba sauran Yan daban ma suka shiga motarsu daya suka tafi da gudun tsiya,Daya daga ciki yace tuka muje,Nabeel ya fara driving suna zuwa inda ba gidaje ba ababen Hawa suka ce wait Nan take ya tsaya da mota yayi parking Yana ta karanta adduoi a ransa abinda suke nufinsa da shi Kar ya same shi,yana parking mazan biyu suka shake Nabeel ta baya ta yanda ba zai iya motsi ba,Wanda yake gaban motar Kawai Hajiya babbar Nabeel ya damka ya kafta Mata Sara da wuka Nan take jini ya balle ta gaban Nabeel,ya saki wata azababbiyar kara,su Kuwa da gudu Suka fice daga motar suka shiga tasu Suka bar layin a tsiyace. Nabeel kukan ma ya gagareshi sabo da tsananin bala'in da yake ciki, Affa Yana can tare da Papan Hamida sun karbi kudin auren Hamida,Ahmad ya Kai kudin aure Saura a sa rana ya rage,har ya shiga social media shafukansa ko Ina ya rubuta got Engaged ana ta Masa fatan Alkhairi,Hamida haka kawai ta fara nadama da tace a kawo kudi amma ya ta iya. Affa Yana zaune ya raka Papa ya hau mota kenan zai wa motarsa key yaga Kiran Nabeel,dagawa yayi kukan Nabeel yaji Kawai da Nishi Kamar ana zare Masa rai, Affa yace Lele lafiya Kai Lele,da kyar Nabeel yace Affa kazo Zan mutu,Affa mutuwa zanyi wallahi wasu Yan daba ne Suka yanke min Naja'atuta,Affa yace wacce Naja'atun? ta gidan su Muhseen? Yana Nishi jikinsa na rawa yace Affa..Affa...Ya Allah...Affa... Naja'atu fa Affa Naja ta,Affa duk ya rude yace kana Ina yanzu? Da kyar ya Masa kwatance nan Affa ya Kira Ammar da Mimi duk kafin kace me sunje wajen,Affa motar ya leka yaga gaban Nabeel jini yayi faca faca da farar rigarsa,Ido Affa ya rufe ya juya baya sai hawaye,Ammar Kuwa kuka wiwi take,Mimi zubewa tayi a kasa Kawai,Affa Yan Uwansa ya Kira Alhaji Ubaid da Alhaji Abbas,kafin kace me sojoji sun cika wajen su Alhaji Ubaid sun iso ba bata lokaci suka tafi katafaren hospital kafin su Isa asibitin Nabeel tuni ya sume tuni,Suna shiga hospital din taimakon gaggawa aka bashi likitoci sun dade suna aikinsu kafin babban likitan ya fito,Affa suka Yi Kansa yace Alhmdllh rabi Suka yanka Allah ya tsare basu raba jijijiyar jiki ba,yanzu zuwa gobe ku shirya komai Zan hada ku da likita a paris a kaishi can sun kware a wannan fannin idan ba Haka ba za a iya samun matsala ko ya warke yazo ya kasa haihuwa ko ya kasa biyawa matarsa bukata kuyi sauri kuje can amma gaskiya wallahi ko sun Masa Aiki sai ya dade Yana jinya zai kwashe watanni ko shekara ma dick dinsa bai dawo normal ba amma Inshaallah zai warke abin da sauki. Sai lokacin su Affa Suka danji dama dama,Sanata Alhaji Abbas ya Kira yaronsa yace a Fara musu Shirin tafiya paris,Hamida Bata San me ake ba tana kwance taga Affa ya shigo da sauri cikin tashin hankali ya fito da wasu takardu da international passport hankalinsa a tashe Hamida hijab dinta ta gyara ta fito har kasa ta durkusa tace Affa lafiya Kuwa? Affa yace Ina lafiya Hamida Nabeel wasu Yan daba sun yanke Masa Wai Naja'atunsa Affa shima bai San yanda zai fadawa Hamida ba kunyar fadar sunan abin yake a gaban yarinya,da Mamaki sai yaga Hamida ta gane Yana Fada ta dafe kirji tace Naja'atu? Affa yace ita,Hamida sai ta kwalla uban Kara sai kace wacce junnu Suka shigeta ta dinga wayyo Allah na Shiga Uku na lalace ta Fadi a kasa tayi birgima tayi burburwa Affa ba ta ita yake ba tuni ya bazama ya koma asibiti,Hamida ihu take da kururuwa kamar ance mutuwa yayi ta fito da gudu ta nufi wajen su Sale su dama sunji labari duk sunyi tsumu tsumu,Jama'a ku ceceni Ni yau Ina Zan sa kaina....ta wuce su Sale ta fice kofar gida,wani Almajiri yace Hajiya a taimaka min da sadakar yaji da Mai zanci kanzo mm,Hamida tana kuka ta cakumi Almajiri ta kifa Masa mari ya juya da sauri zai cika rigarsa da Iska ta tallafe Masa keya sai da ya kusa faduwa,ko me ta tuna oho gida ta shiga da gudu duk Yan aiki sunyi cirko cirko ta dakko waya ta Kira Ammar tana shesheka ta tambaya Kuna Ina? Ammar yace ba sai kinzo ba da Sauki,Ni ka fada min ta sake tambaya cikin kuka me ratsa zuciya,Kawai asibitin ya fada mata,ta fice ko wacce mota tarewa takeyi ba sai taxi ko napep ba,Wani me napep ya tsaya ta fada ciki Yana jinta tana ta zunduma kuka, kafin ta fita ma ta bashi kudinsa Yana kaita ta Shiga asibitin da gudu,Ammar ne ya hangota hijab dinta duk ya jike da hawaye,tana ganin Ammar ta sake rasgewa da kuka,yace kinyi sa'a doctors sunce za a iya Shiga a ganshi su Mimi suna ciki amma Indai kuka zakiyi baza su bari ki Shiga ba,tana shesheka hawaye Yana bulbula sabo dal tace na daina harda rufe bakinta da tafin hannunta. Ciki ta shiga a hankali,taga Mimi a gefe tayi tagumi idonta yayi jajir,Alhaji Abbas da Ubaid suna Nan a zaune,su basu San Hamida a Fuska ba har kasa ta tsuguna ta gaida su hawaye Yana bin kumatunta,Affa ya kalli yayansa Ubaid yace itace Hamidan fa Yaya,yace Allah sarki Sannu,Alhaji Abbas yayi dan Murmushi yace Kinga mutumin naki Yana numfashi,Hamida tana Jin kunyarsu sabo da sun Mata kwarjini,Sabon hawaye na bin kumatunta ta dan leka kirjin Nabeel da kyar muryarta ke fita sabo da kuka tace Mimi Yana numfashi Kuwa? Mimi tace yanayi Hamida zai tashi Inshaallah,Hamida so take ta taba kirjinsa taji amma tana kunyar mutanen wajen,likita ne ya shigo yace ku bamu waje za muyi Masa wani Aiki,dukka suka mike suka fita banda Hamida taki tashi tana ta hawaye ba ji ba gani. Doctor yace Madam zamuyi Masa aiki,Hamida tace bis..bis.. Bismillah kuyi abinku... ba abinda...zaku boye...boye min abinda bakwa so na gani na sanshi,likita yace matarsa ce ke kenan Hamida an Fara girma tace ae...yace to koma waje bama aiki a gaban kowa Hamida ta kwabe fuska tana hawaye ta fara doka kafafu a kasa,Likita yace to mijin naki baya ganin shagwabar taki ai,Mimi ce ta shigo ta jawo hannu Hamida suna tafiya amma fuskar Hamida tana baya tana kallon Nabeel. Likitoci tunda Suka Shiga sai dare Suka fito,Hamida, Affa,Mimi da Ammar duk a Nan Suka kwana wajen Nabeel kowannen su bai iya cin komai ba. Basma tun ranar aka sanar mata amma sai washe gari da Rana 2pm tazo itama tayi Dan kukanta,Hamida Sallah Kawai take iyayi ba abinda take iya ci sai malt ko milk shikenan,har fada Mimi take Mata taje gida tayi wanka ta dawo taki tafiya sai da Affa ya bata rai sannan ta Mike ta shiga Napep ta tafi gida,ko nisa Mai Napep baiyi ba ta bugowa Mimi waya Mimi ya me jikin? Yana da Sauki? Mimi tace ae ta kashe Wayar. Kafin me napep ya karasa gida Hamida ta sake Kiran Affa Yana dagawa tace Affa ya farka? Ya me jikin?har Murmushi tasa Affa yace da Sauki,tana zuwa gida zata Shiga wanka ta sake Kiran Ammar shima ya daga tace Yaya Ammar kana cikin dakin? Ya yake? Yayi ko dan motsi Ammar yace yanzu ya motsa yatsansa baki gani ba wallahi,wayyo Dadi kasheni dan Allah? Ammar Dariya ta bashi yace Allah tace bari nayi sauri na dawo ta kashe Wayar. Affa ne ya kalli Ammar yace Hamida ce ko? Mimi sai taji duk duniya bata da Kamar Hamida ta damu da danta matuka,Basma Kuwa karfe uku na Yi tace Mimi Naga an kawo abinci yunwa nake ji ta koma wajen kayan abinci ta ebi abinda ranta ke so taci ta shake cikinta,Mimi Kamar ta mareta haka taji,kafin magrib Hamida tuni ta dawo lokacin Kuma an gama komai na tafiya da Nabeel Paris,Affa,Mimi,Ammar da Alhaji Abbas sune zasu tafi,Hamida ganin an fito da Nabeel kamar an dauki gawa ta fashe da kuka tace wallahi mutum ba komai bane a wajen Allah dan Allah a tafi dani,Affa ya lallasheta yace ko sati baza muyi ba Inshaallah a gida zamuyi jinyarsa karki damu kije gida,Basma gidansu ma ta wuce abinta,Hamida ta koma gida ta tsaya a wajen su Inuwa suna jimami tace la'ila ha illallah Uncle Inuwa muji tsoron Allah mutum ba komai bane Hamida bata San Sanda tace Nabeel Dina sak gawa tana hawaye tayi cikin part dinsu ta fada bedroom dinta tare da fashewa da kuka ta kifa kanta a saman bed,su Affa Kuwa tuni sunbi jirgin Abuja daga can suka wuce kasar Paris AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 9 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Mom Aneesat Tajrah Ummeealgusawi Alhamdulillah J Jad kitchen Aysher kabara Asli Smasher Anty Nurse Zaria Real Maman Waleeda Suna zuwa hospital suka wuce direct dama an San da zuwansu babu bata lokaci likitoci Suka karbeshi,Suna gama komai su Affa Suka wuce hotel gaba dayansu,Mimi da Affa room daya,Alhaji Abbas da Ammar ko wanne dakinsa daban,wanka sukayi tare da cin abinci sannan suka gama komai Suka koma hospital din ba dadewa Suka yiwa Nabeel aikin gaggawa aka gama cikin kankanin lokaci Already sun sa Masa robar fitsari, Bayan sun gama Suka canja Masa Yar farar rigar hospital din sannan Suka maida shi dakin Hutu sannan likita ya nemi ganin su Affa a Office dinsa. Tsohon baturen tukuf su Affa ansha boko an koshi turanci Kawai ake watsowa ta ko Ina,Doctor din tsoho ne tukuf cikin harshen turanci yace Aiki yayi kyau ba wata matsala zuwa Nan da 14days za a sallameku amma sai yabi dokoki Indai baya so wata Matsalar ta faru,akwai wani liquid zamu baku kullum zai zuba a cikin ruwan dumi ya zauna a ciki kullum sau daya har tsawon 3mnths,banda sex sai After 5-6 mnths,ba fita sabo da ba a so yayi yawo ko driving ko motsa jiki daga kwanciya sai Zama sai ko Shiga toilet da ya Zama dole,bayan wannan ba wani abu da zaiyi,Kar abari yayi wani abu Wanda gabbansa zasu Sha wahala,Mimi har rubuta dokokin a jotter Kar ma a samu matsala,Bayan sun fito Suka Shiga inda Nabeel yake,aikin da aka Masa yasha wahala matuka duk ya fita a hayyacinsa kowa yaga Lele sai ya tausaya Masa,Alhaji Abbas ne ya kalli Mimi yace Fadila fa ta gaji kuka takeyi a kawota hutu wajen Mimi,kyaleta tukun sai Nabeel yaji sauki sai na maka waya a kawo min ita hutu,Alhaji Abbas yace ba matsala dama sabo da kullum ta ganni sai tace kawu Mimita a kaini wajen Yaya Nabeel,Murmushi Suka yi Kawai Jin Nabeel ya farka Yana kuka sabo da zafin da yake ji Yana Kiran Mimi dinsa,Mimi da sauri ta karasa Kansa tare da rike hannunsa tana cewa Nabeel dina gani,Ammar yana kansa shima ya rike hannunsa,Allurai Suka Masa ya koma bacci,Affa yace ah da Sauki ai in kaji mutum Yana iya kuka ma da Sauki,Sanda abin ya faru ai ko kukan bai iyawa,Alhaji Abbas yace duk Sanda aka Kama Wanda yayi abin Nan wallahi gidan sojoji za a fara kaishi duk azabar duniya sai an gana Masa kafin karshe a kaisu prison ko Yan Sanda bazan sa Yan Sanda ba a case din sabo da Kar su barsu a banza. Ammar yace duk Wanda Suka Masa wlh sai an musu abinda Suka ma Nabeel,suna ta tattaunawa,Hamida tana gida ta rasa sukuni gashi har yanzu basu Kira ba bare ta samu number ko Ammar ne,wanka tayi tare da gabatar da Sallar nafeela ta daga hannu sama tana yiwa Nabeel Adduar samun lfy,Ranar Shehu ma cewa tayi ya bari sai an dawo da Nabeel taga lafiyarsa sannan za a ci gaba da karatu,tunda Suka tafi Bata da aiki sai nafeela,karatun Qurani,tasbihi tana Addua Allah ya bawa Nabeel lafiya. Hamida Papa ta Kira Suka gaisa ta sanar musu halin da ake ciki,Yaya Sulaiman yace sai su Affa sun dawo zasu Zo dubiya.. Su Mimi kwanan su biyu a can Nabeel ya dawo hayaccinsa daga bacci ya farka Mimi ce kadai kusa da shi ya kalleta yace zanyi brush,da sauri ta kawo Masa wani bowl a ciki yayi sannan yace wanka,Mimi tace zasu zo su maka kasan Wanda ake maka daban Kuma nurses ke maka,kafin ta gama magana nurses maza sunzo Nan Suka saki wani labila suka masa wankan tare da canja Masa wata Yar Riga ta Hospital din fara dama simunce ba sa wando har watanni biyu haka,Alwala Mimi ta Masa a kwance yayi sallalolinsa sabo da ba damar tashi ko Zama bazai iya ba sai Nan da sati biyu lokacin da za a sallamesu,Abinci Mimi ta bashi yaci Kuwa da yawa yasha magungunansa sannan ya kalli Mimi yace Ina Pipi fa? Mene wani Pipi? Hamdy fa nace,Dariya ya bawa Mimi tace hmm Wai Hamidan ce Pipi Kuma? Wannan sunan Ina kuka samo shi? ko a Kira maka ita a waya? Kai ya daga Mata,Wayarta ta dauka ta Kira number Hamida,Lokacin Hamida tana kwance saman gadonta tana ta tunanin Nabeel,Ahmad sai kiranta yake taki dagawa,gajiya tayi da nacinsa ta daga da masifa yace dan wulakanci Ina Kira tun jiya kina shareni sabo da Farkan naki an yanke Masa abar,ai kamata yayi ma ku gane cewar Allah ne ya Nuna masa ishara,Tsaki Hamida taja tace Banda lokacinka ta kashe wayarta a ranta ta furta shi tunaninsa ai ya kawo kudi shike nan ya gama me wahalar zanyi maganinsa da kaina wannan ba mijin aure bane. Kiran Mimi ne ya shigo da number Paris,tana ganin number kasar waje da sauri ta daga Sallama tayi a nutse ta tsinci Muryar Mimi ce da ladabi ta gaisa ta sannan tace Mimi ya me jiki a sanyaye hawaye ya cika Mata Ido Nan take kuka ya kwacewa Hamida,ita Kam Mimi mamakin Hamida takeyi yanda ta fisu damuwa ma abin daure Mata Kai yakeyi,tun kafin a mikowa Nabeel waya tuni ya Miko Hannu a bashi ita Mimi tace Lele ne fa yace a bashi ku gaisa ta Mika Masa Wayar ta mike ta bar Masa room din sai shi kadai Hamida tana kuka tace Hello...Muryarsa taji tsab ba alamar Yana Jin jiki yace, Hamidatuwa Pipin Kyau,tana hawaye tayi dariya ba shiri tare da furta Ina Yini,Wai yaune Karon farko da Hamida ta gaida shi lallai an Fara hankali,tunaninsa ta katse Masa da cewa naji kayi Shuru ko jikin ne? Ya jikin da Sauki? Nabeel yace da Sauki sosai ba a taho da ke ba ga ranar ganin Duwawu a banza,ba shiri tayi dariya tace ba ruwana bazan sake kallo ba,Dan Allah ki ganta farar takashi gata a Nan ana barinta a banza,Baruwana ni dai dan Allah ka daina tuna min kunya nakeji ni,tunda kaji sauki Alhmdllh,Marairaicewa yayi yace me yasa Kika sa Ahmad ya kawo kudin aure? Mutumin da tun yanzu ya fara Miki gori shi kike so? Share zancen tayi tace yaushe za a sallameku? Nabeel yace Nan da 2weeks Inshaallah bakya son a Miki zancen Ahmad dinki ko? Yanzu kinfi son bakin duwawu akan Fari? Hamida tace ni dai dan Allah ka daina fadan harkar nan kunya kake bani,Jin tafi son Ahmad ya kashe Kiran kawai. Hamida Kuwa Jin Nabeel tar akwai sauki sosai sai Murna tayi tsalle ta fada saman gadonta tana wani farin ciki ta mike ta fito ta ebo abinci a kitchen da yawa ta zauna ta ci ta koshi tare da korawa da ruwa. Hijab dinta brown ta saka sannan ta fita wajen su Inuwa tace uncle Inuwa Lele yaji sauki sosai yanzu mukayi waya da shi har Wasa da Dariya muka yi,su Inuwa Suka dinka murna haka ta koma part din Mata Yan aiki ta iske su suna hutawa Hamida tace bayin Allah to ku tayamu godiya ga Allah Lele ya fara warkewa,gaba Daya Suka hada baki Alhmdllh,ficewa tayi ta koma bedroom dinta ta dauki Wayarta ta Kira su Papa ta fada musu Suma sunyi farin ciki, Doctor Ahmad ta Kira sabo da murna,ya zaci wani kudi ta samu yanda yaji tana Fara'a da murna Hadi da nishadi,yasan Kuma sunyi waya dazu sunyi fada,Hamida tace Yaya kyakyawa ya samu sauki sosai yanzu ya kirani har Wasa da Dariya mukayi,Nan take ran Ahmad ya baci Kamar zai cinyeta yace to shine abin murna haka ni na zaci ma wasu Kan kudi Kika danne tsaki Yaja tare da kashe wayarsa.. Tunda Hamida ta samu Number din Mimi kullum sai ta neme su an hada da Nabeel taji ya jikin har Suka kwashi 2weeks sai Shirin dawowa,Hamida ta zaci a gidan Mimi za a bar shi ta sa masu Aiki Suka gyara ko Ina na gidan neat,ranar Kuwa data kama zasu dawo bayan sun gama gyara gidan wanka tayi tasa sabuwar Abaya Arsh color tana jiran dawowarsu,Yamma likis sukaa sauka a Nigeria,a airport din Suka yi Sallah sannan Suka. Karaso gida Driver ya dakko su,Hamida tana Jin karar mota ta leka ta window na sama ta hango Nabeel shi ya fara Fitowa sanye da jallabiyya fara,Hamida ta Bude baki ganin yayi wani kiba ya Kara harske da kyau,Bedroom dinta ta koma ta boye a ciki,Sai da su Mimi suka Yi wanka ma tare da hutawa sannan suka zauna a dinning suna cin abincin da su Hamida sukayi me dadin gaske,Nabeel Yana ta zuba Ido Ina zai ganta sai kallon hanyar room dinta yake,sai ga Hamida an fesa kyau an fito,tunda yake bai taba sanin haka take da tsayi da kyau ba sai yau,Durkusawa tayi tana gaida Mimi da Affa suka amsa da fara'a Mimi tace Hamida wannan wanka Haka ko angon ne zai zo? Nan take annurin fuskar Nabeel ya dauke,Murmushi Kawai Hamida tayi tace Ina yini Yaya Kyakyawa da kyar ya amsa ya daure fuska,tace ya jikin da Sauki Kawai yace ya juya yaci gaba da cin abincinsa, bedroom ta koma abinta. Alhaji Abbas Kuwa Yana komawa Abuja Basma ya rufe da fada kamar zai duketa yace mijinki na can kin San halin da yake ciki ko ki Kira kiyi Masa Sannu mahaukaciyar Ina ce ke dan uwanki mijinki kowa Yana Kiran waya yaji ya me jiki amma banda ke, Maman Basma tace to wallah Alhaji Nan su Anwar Suka ganta da wani Namiji Wai tsohon saurayinta ne ya kaita shopping suna yawon shakatawa da Aurenta gata nan,Alhaji Abbas yace hada kayanki ki koma dakin mijinki yanzu maza kibi flight,ba shiri ta tattara ta taho Kaduna ta tare da tare taxi ta shiga tana shiga taga mutum wani murjejen kato baki wuluk kusa da ita ta firgita sosai sai dai ta fuske tana yiwa driver kwatance yayi parking a kofar gidan Affa,gabanta ne ya yanke ya fadi ganin wuka fyalleliya a hannunsa kafin tayi magana ya soka Mata wukar a kirji ya zare ya sake soka Mata har sau Uku sannan Suka bude mota Suka jefo ta kofar gidan da kayanta gaba Daya. Tana ta kakari bakinta kafin kace me ya cika da jini ihu tayi da karfi Sale ya jiyo ihun da sauri ya Bude kofa yaga Basma ce ihu ya kurma Yana Kiran mutane ya fada ciki da gudu su Affa,Hamida,Mimi da Nabeel duk Suka taho,Nabeel sai daga baya ya karaso sabo da an hanashi tafiya da sauri sai a hankalin idan ya warke,sabo da baya sa wando ma Sai jallabiya baya fita ko ina,kowa yaga Basma ce ai mata tuni sun rude da kuka Basma ta kalli Nabeel tace wasu ne a taxi ban San su waye ba....ka yafe min nayi ma abubuwa nice..nice..na sawa Hamida kwaya lokacin tana da ciki sabo da Kar...karrrrrrr....ta haifo yaron da rai kuci gaba da alaka,sa...sa..ta fara tari tace nice...nayi hayar Yan daba nasa su yanke maka gabanka sabo da na gane bani kake so ba baka sha'awata shine bana sooooooo.....wata ta samu itama....ka yafee....min...kishi ne yasa,Hamida kuka Nabeel Hawaye ya cika Masa Ido yace na yafe Hamida ma ta yafe,Hamida tana kuka tace a kaita asibiti waye marar Imani zai kasheta bata biyani dana ba,Ni ban yafe ba Dandana ta kashe min kowa yayi mamakin Hamida ba Imani haka,Hamida tace ni wallahi zuciya ce Allah Bai sa min ba amma ni idan nayi fushi bana sauka da wuri,sai da Kika Zo mutuwa Zaki ce a yafe miki Allah fa baya karbar tuban Wanda sai da mutuwa ta riske shi yaga mutuwa karara sannan zai ce zai tuba,sai kin tashi kin biyani dana da fadar dani da kika dinga yi Ina da ciki a kaita asibiti dan Allah karta mutu ta tashi a bi Mana hakkin mu,Kuma Yaya kyakyawa sai ya sakeki ko a lahira baza ki Zama matarsa ba Kar ma kizo Allah ya yafe Miki ki shiga Aljana a sake bashi ke a Aljanna munafuka wallahi walakiri sunfi karfin ki suna Nan taron dangi zasu Miki Matukar Kika je lahira hakkin Lele ma ya isheki. Hamida ta juya tana Basma kinji kunya yanzu Naja'atun ma Sai a hada da ita a wajen kishi me tayi miki ku kaita asibiti Dan Allah Kar ta mutu sai ta biya mu hakkinmu Yasin bazan yafe ba bazan ji wani tausayinki ba,Affa yarsa ce ba yanda zaiyi haka Suka sunkuci Basma zuwa asibiti Nabeel ba halin ya bisu jinya yake,Hamida ta ganshi ya kurawa motar su Affa Ido tace muje ciki ko binta zaka yi? Kai har abada baza ka Zama gwarzo ba,Nabeel shi kanshi ji yake bazai iya yafewa Basma ba. Suna komawa Palo Hamida ta zauna tare da zuba tagumi tace oh ina ganin duniya bala'i,Yaya Mu hada kanmu Kar mu yafe kaji ko ance mun yafe muce bamu yafe ba,Nabeel ya kalleta yace Yar uwata ce fa jinina,ban sanki da Haka ba Hamida yaushe kika Zama marar yafiya? Ni sanda kina Kauye kinfi birgeni kina so na sai abinda nace amma yanzu gaba daya kin canja sai dai ki tafi wajen Dan iskan bakin saurayinki zance Nima kin kasa yafe min kince ke sai me bakar takashi kike so me na Miki dan Allah? Hamida kwallace ta cika Mata Ido ta mike tare da shigewa dakinta saman bed ta fada ta fashe da kuka sosai bata son Dr Ahmad bata San ya zata yi ba gashi an karbi kudin auren sa. Basma Kuwa tana can Rai a hannun Allah,ko da Affa ya Kira Yan Uwansa Bai fada musu me Basma tayi ba amma gaba daya da Yamma maza da Mata sun cika asibitin,anyi kokarin ceto ran Basma amma abin yaki sai cewa take a Kira Mata Dady da Mummy,Nan aka basu dama Suka shiga ciki Basma tana kakarin mutuwa ta fadawa iyayenta abinda ta aikata karshe tace dan Allah ku yafe min ku rokar min Nabeel da Hamida kafin a sakani a makwanci su yafe min,Alhaji Abbas da Mummy sai hawaye suke suna cewa baza ki mutu ba Inshaallah,Basma ta fara salatin annabi kafin ma ta Kai karshe rai yayi halinsa,masu kuka da kuka na yi Ana ta sanarwa dangi janaza,ko su waye oho, tunda yamma tayi baza a bari ta kwana ba,Haka aka karbi gawa sukayi gidan Affa gaba Daya dangi suna ta sauka a gidan Affa maza da Mata sai mutananen unguwar. Sabo da Zaman tare Nabeel sai da yayi kuka amma Yana daki ba yanda za ayi ya iya fita,Yana kuka yace na yafe Miki Basma duniya da lahira,Mimi ce ta iske Hamida a Palo cikin Mata dangi tana ta kuka ita ma tana Allah sarki Basma Allah ka gafarta mata gata da kirki Wanda suke palo suna Allahu Akbar,Hamida tana shesheka tace munyi zaman mutunci Indai ba Ni na tsokaneta ba bata min komai,tsakanina da ita matar nan sai Alkhairi ,Bamu taba sa'insa ba da baiwar Allah nan,Muna zaune lafiya da ita baza ka taba Jin bakinta ba Wai Basma tace wani Abu a kanka Ina Sam badai Basma ba baza kaji ba,baiwar Allah ga hakuri, mace Yar gayu irin Basma,Dangi ana ta ai Basma ba ruwanta mutuniyar kirki ce duk gidansu ba me hankalinta basu San shegantakar data to afka ba,dama haka Mata suke Yi sai an Gama tsiya kala kala da mutum idan ya mutu sai ace ba a taba fada ba,ana yabon mutum,Ihsan ce ta shigo da katon Hijab da carbi,Hamida tace oh Yar uwa munyi Rashi Allah yaji Kan Basma mutuniyar arziki,Ihsan taji inda ake yabon Yar uwarta dama tasan Hamida sai ta fashe da kuka da fada jikin Hamida ta rungumeta,Hamida tana la'ilahaillahu kuyi hakuri Yar uwa munyi Rashi,Ihsan tana kuka tace Ina Yaya Nabeel? Wallahi shi nafi Jin tausayi wayyo Nabeel shine abin tausayi rasa matar aure ba karamin firgici bane ga Namiji cewar Hamida Yan dakin Suka ce Allah sarki Allah ya bashi ta kirki wacce zata maye Masa gurbi,Hamida Bayan kujera ta zura kanta a hankali tace Inshaallah nice, nice ma dani za ayi in ta kallon Lele me Kyau ga runtumemiyar Naja'at Cass abinmu sai ta fito da kanta tana goge ido,matar Yayan Affa tace Yar Nan ya akayi kikan San Basma haka ne da Alama Kun shaku? Hamida tana goge Ido da Jan majina tace Aiki aka dakko Ni daga Kauye a can gidanta na zauna da Affa yaga Ina da hankali shine ya 'yanta Ni na koma 'yarsa na dawo gidansa da Zama Ina karatu na,Ta kusa basu Dariya Wai aka 'yantata sai kace zamanin da ake bayi. Mimi ce ta Kira Hamida bedroom,tana zuwa tace zauna Mana,a kasa ta zauna da labadi,Mimi tace ki yafewa Basma dan Allah,Hamida tace haba Mimi sai kace nice kanwar fir'auna ai wallahi tun kafin a tafi da ita asibiti na yafe Mata komai Allah ya yafe Mana,Ni me tayi min ma Yar hantara ce da dan tsawa wannan ai ba wani Abu bane na yafe har ga Allah,Mimi tace Alhmdllh yanzu jeki dakin Lele ki kula da shi lallai yasha magani kinji,Hamida tayi dan damm sabo da gaba Daya yanzu tsoron kebewa take da namiji amma haka tace to bari naje,ki bashi abinci in yaci yasha magani,to Hamida ta sake cewa tace amma da kunya na ebo abinci a gaban mutane na wuce,akwai kitchen a sashensa kin manta ba abinda babu ki dafa Masa a can,Hamida ta sake cewa Mimi kukan mutuwar fa Kar a karasa Dani? Mimi tace Naga dai ranar da zaki hankali au dama duk uban kukan Nan da kike ba na Allah bane? Mimi ni fa Indai Kika ga nayi kuka to Allah akan yaya Nabeel ne ko wani abu da ya dameni a Rai na,amma zuciyata a bushe take ni kafin kiga abinda zai sani kuka sai ko In Lelenki ne. Sabo da ban taso da iyaye na ba ban sansu ba ma Ni ko kalarsu ban taba gani ba ko yayeni ance ba ayi ba iyayena Suka rasu,Mimi sai taji tausayinta tace sorry dole ki Shiga wani hali ki hada Masa ruwan dumi Wanda zai iya Zama a ciki kin San maganin da ake zubawa ai a ciki sai ya shiga ya zauna a ciki Hamida tace irin na me Jego? Mimi tace ae,tace to ficewa tayi ta nufi sashen Nabeel. Nabeel yayi zuru Yana tunani yaga Hamida ta shigo,sai data ga Lele Yana cikin damuwa sannan zuciyarta ta karye tayi kukan gaskiya da gaskiya ita aduniya in ana so aga Hamida a wani Hali to ace Lele ne ya samu matsala,a kasan bed din ta durkusa tana goge hawayenta ta kalli Nabeel tace Leluwan Kamshi...Nabeel ya harareta yace tunda bakya so na ki fitar min a room,Hamida tace mutuwa akayi Babba Addua zamuyi Mata,kin yafe Mata ne? Kai ta daga masa kawai,tace kasha maganin naka? Kai ya girgiza mata,Yana kallon Hamida sai yaji damuwarsa ta yaye wani farin ciki Yake tsintar Kansa in tana kusa da shi,sai da ta juya zata shiga kitchen tace Yaya Danyen jegon da Sauki? tana fada ta Shige kitchen bata jira amsarsa ba,tana Jin muryarsa yace a'a ai ba tambaya zakiyi ba kice a bude Miki ki gani,Hamida daga kitchen tace Kai Lele ko kunya. Hada Basma akayi tsaf aka kaita makwancinta gaba daya gidan Affa ba masaka tsinke,ba Wanda yasan me Basma tayi ko a dangi sai iya iyaye ne Suka sani Suka rufe zance tunda an yafe,sai dare Hamida ta gama Masa girkin tuwon danyar shinkafa tayi miyar danyar kubewa ta Sha kifi, ta hadawa Nabeel ruwan maganin a toilet tana ta zirga zirga Yana binta da Ido ta fito tace na hada ruwan zafin me jego,kallonta yayi ya murmusa Kawai ya wuce toilet,ganin Ana ta cin abinci a gidan ta zuba tuwon a flask ta kawowa Mimi har dakinta ta iske Yan Uwan Mimi Mata makil a dakin ta gaishe su sannan ta Kira Mimi gefe ta bata harda rada Mata tuwo nayi karki bari a cinye Miki suje suci shinkafa ta kullum kullum,Mimi tace to Kai dakin Affa,Hamida ta kai dakin Affa ba kowa duk suna kofar gida a Nan ta ajiye ta koma dakin Nabeel taga har ya shirya cikin brown jallabiyya ya dauki gajeren wando zai saka Wai sai yaje wajen zaman makoki , Hamida tasan a dokokin likita Banda sa wando,tace karka sa wallahi baza ka bi doka ba dan Allah karka sa,tsayawa yayi Yana kallonta ta Masa kyau bai ma San kyanta ya Kai haka ba,yace sai na sa tunda Ahmad kike so bata da amfani a wajena,Hamida cikin dakewa tace please Yaya karka karya doka ka Mata Addua a daki Dan Allah ba sai kaje ba,nasan zuwa zaka Yi,duk duniya ko Mimi bata gane abinda ke damunsa sai Hamida tun kafin ta fara hankali ko kallo ya Mata tasan me yake nufi Yana tunani ta kwace wandon ta maida ma'ajiya tace Jego fa kake zata Yi waje ta tsinci muryarsa yace abincin fa, dawowa tayi ta fara serving dinsa yace harda yin wani tuwo? Me jego ai sai da tuwo ta furta ba tare da ta kalle shi ba muryarsa taji yace dan Allah karki auri Ahmad,mikewa tayi ta fice abinta ya bita da kallo Kawai. Tana fita wanka taje tayi ta canja kaya tayi Sallar Isha sannan ta take cikinta da shinkafa da Miya harda salat ta sake sabon hijab ta fito cikin Yan makoki a palo,tayi jugum tana jan carbi, ana ta fadar halayen Basma na kirki Hamida tana cikin su Ihsan ka rantse dama a gidansu ta taso,Fatima kanwar Basma ce ta Dora hannunta a cinyar Hamida tace naji su Daddy suna cewa idan mutuwa ta lafa ranar arba'in din Basma za a daurawa Nabeel aure da Ihsan ko Ni wai,Hamida bata San Sanda tace Innalillahi wa inna ilayhirrajun ba,Mene ne Yar uwa? Hamida ta wayance tace Basma ce ke Fado min sai naji gabana ya yanke ya fadi,wata tsohuwa dake kusa da su tace Yar Nan haka mutuwa take mutum Yana Fado ma zaka ji gabanka ya Fadi sai hakuri duk mu na hakane kowa jiranta yakeyi,Hamida kuka ya kwace Mata za a aure Mata Lelenta kuka na sosai takeyi ana ta bata Hakuri ana yar Nan haka mutuwa take sai hakuri,Hamida Sam bata mutuwa take ba ta Lele takeyi tashi tayi ta koma bedroom dinta,Yan Uwan Basma dattijai Suka ce wannan Yarinya ta shaku da wannan baiwar Allah. Hamida saman bed dinta ta fada tana kuka sai ga Kiran Doctor Ahmad tsaki taja sannan ta daga yace ya Hakuri? Tace Alhmdllh,Allah yasa ba Murna kike ba ta mutu ta bar Miki mijinta,Takaici ya Kama Hamida dama kadan take jira tace na fasa aurenka kai zo ka karbi kudin aurenka wallahi bazan aureka ba ko sama da kasa zata hade ka turo a karbar ma kudinka,Hakuri ya fara bawa Hamida tace bazan hakura ba na gaji da zarginka kazo ka karbi kudinka wallahi ko na rotse ma kai banza Jaki,Dr yana gadara shi llikita ne yace da ilimi na da wayewata da kudina babu Yar da zata zageni na aureta ko wacece wallahi na barki har abada Ni da Zan rufa Miki asiri fa zaki zageni, gobe zanzo da kaina na karbi kudina,Hamida waya takashe tace maza zo ka karba dan me bakar takashi na huta da Kaya. Washe gari Ahmad ba mutunci ba kunya ana zaman makoki Affa ya zaci gaisuwa ma yazo amma ba Wanda ya gaisar Yana zuwa yace kudin aure na za a bani dana kawo na fasa yarinya bata da tarbiyya Wanda ya Mata cikin shege yaje ya aureta,su Papa da Sulaiman sunzo suna wajen,Ummi tana ciki wajen Mimi,Affa ya mike tare da rike hannun Ahmad yace muje gefe Ahmad ya fisge hannunsa ya fatalar da hannun Affa gefe yace dalla sakeni cikin dubban mutane yace kaje ka aurawa danka Wanda ya Mata cikin shege ta Haihu a bani kudina na fasa,mutane aka fara gunaguni,Alhaji Ubaid yayan Affa shi ya mike tare da kwashe Ahmad da mahaukacin mari Ahmad ya daga hannu zai rama Sulaiman ya tashi ya Masa wani mugun naushi a Fuska Nan take jini ta hanci ta bakin Ahmad,Su Anwar yayan Kanin Affa Dana yayan Affa Suka Mike zaratan maza sunkai su goma Suka yiwa Ahmad laga laga sai da kyar aka kwace shi,Muhseen shi ya zaro kudi masu yawa yace Nawa ne kudin Affa? Affa yace dubu hamsim ne,Muhseen yace kacal wannan ai kudin Yar budurwar akuya ce,Nan ya irgo kudi ya sawa Ahmad a Aljihu tare da tankada shi gaba gaba Daya family din tsabar hadin Kai Shuru sukayi Suka fuske Suka nuna Basu San ma zancen ba aka ci gaba da zaman makoki. A Haka sai da labari ya Isa wajen matan cikin gida Mata Basu San Kan zancen ba Suka dinga tsinewa Ahmad,Nabeel zai je dakin Affa kenan ya tsinci zance Nan take farin ciki da murna Suka cika Masa zuciya Kamar ba matarsa ce ta mutu ba,Wanda Suka ganshi ranar cewa sukayi yaron Nan da tawakali yake,yaro yayi tawakali. Anwar duk kwanakin da suke a hannun Hamida suke karbar Abinci duk sun santa ba Wanda bai santa ba,dama Anwar shi ya Santa yayi mamakin ganin wayewarta da hankalinta sai yaji kaunarta tana shigarsa shi Kam ya samu matar aure,Kowa in ya shigo sai dai kaji ana Ina Hamida bata Zama sai hidimar dangi takeyi dama gata ba kuya ai ta sata girke girke tayi suna ta Zama wata star Mata da maza Hamida Kawai,Muhseen ne shima fa yaji kaunar Hamida tana Neman kamashi birge shi take ga abin dariya,Ihsan ya Nemo yace Ina Hamida kice ta dafa min Indomie da kwai,Ihsan tace to ta Fara Neman Hamida,Yayinda Hamida ke dakin Nabeel tana hada Masa tea,Ihsan dakin tayi knocking, Nabeel yace come in, ta shiga tace Sannu Yaya Nabeel tace Hamida kizo inji Muhseen ki dafa Masa indomie,mugun tsoron Nabeel suke sabo da baya Wasa da kowa baya sabgar kowa,muryarsa taji yace get out baza ta dafa ba kowa Hamida, a girki zata Kare da aiki ku dama baku iya samun waje ba,Ihsan ta fice ba shiri,Hamida ta Mike zata fita yace wallahi kina fita zaki ga true color dina koma ki zauna yau ba inda Zaki,shike Nan kowa ya saki aiki ga masu aiki Nan,Shuru Hamida tayi ta dauki tea din ta Mika Masa ta koma gefe ta kwanta a kasan tiles,mikewa yayi ya koma saman resting chair yace hau bed din ki kwanta Kuma kiyi bacci,Fuska ta kwabe yace ba abinda Zan Miki Ni kin San Banda lafiya,tunawa tayi sai ta haura saman bed din ta kwanta ba Bata lokaci bacci ya kwashe ta,Shi Kuwa Yana gama Shan tea din ya fice tare da sa key ta waje ya kulleta gam ya koma dakin Affa ya kwanta a saman bed. Sharhi pls AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 10-15 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Yan kirki Safiyya Nabebe Ummulkhair Maman Alamin Habeebah Heebat Maryam T Baliya Maryam Ba Wanda bai nemi Hamida ba an rasa Ina take,dare har la'ar tayi Sallah Kawai tayi ta koma baccinta sai magrib ta tashi ta nufi kofa tare da murda handle taji gam gam,komawa tayi ciki tayi Alwala tare da yin Sallar magriba har Isha tayi ta mike tayi lokacin Anwar Yana so ya ganta su danyi Hira ya samu ya yada Manufa amma Nabeel ya boyeta, Muhseen ma ya nemeta Shuru ba a ganta ba har sai da sukayi bacci 11pm sannan Nabeel yasa key tare da Bude dakinsa tana gani ya bude tayi sauri zata fita ya riko hannunta ta fisge tare da karawa gaba. Washe gari sadakar Uku Allah yasa duk mutane sun watse sai iya dangi, matasa su Anwar suna zaune Kawai Sai ga Ahmad tare da kannensa su biyar matasa sun tsaya akan mutane yace zuwa nayi a bani dukkan kayan sawar da na siya Mata,Hamida sai ranar taji me ya faru tsaf ,wata ce ta shigo tace gashi can mutumin jiya ya dawo za ayi fada again, kofar gidan Hamida ta fito ta kalli Dr Ahmad, Mata sun fita suna ta kallo,Ahmad Yana ganin Hamida yace yawwa rigar ma dake jikinki tawa ce a hado min kayan Dana siya Miki akwai dubu biyar biyar dana baki sau hudu,Banda su ice cream da snacks duk Ina son kudina,Hamida ganin ba wasu mutane duk su Affa basa wajen ma Sai yaransu,tace zakkar Soyayya ka fitar nayi tunanin ma cikon kudin ka kawo min ai baka gama biyana ba Nike binka bashi ma,ba Kaine a zuciyata ba in ba kirana kayi ba ko tunawa da Kai banayi,kudi da Kaya Kuma Allah ne ya rubuta Kaine zaka siya min Kuma ka bani kudi Nasha Alawa,kudinka Alawa ma Nasha da su kaga basu da Albarka ya zaka Yi Allah ya rubuta. Ahmad yace tonon asiri ai ya Kare Miki ke da kikai cikin shege,Hamida tace danayi cikin ubanka ne ya min ta daga hannu biyu ta zageshi tace sharri zaka min sabo da zaka fasa aure kace nayi ciki Kuma tunda ka min kazafi sai na dakko ma Yan Sanda sai munyi Sharia da kai kayi min kazafin ciki, Hamida a ranta tace yo ko banza ai na kafa tarihi a dangina nice na Fara cikin shege Kuma banji kunya ba,? ke malama a hado min kayana,Hamida ta girgiza kai tace bani da lokacin ka dan tukunyar babarka kullum ka dakko bakar Fuska kazo duk a banza Zan fito. mu a jikin maza Allah ke fitar Mana da arzikinmu Kuma Allah ya baka har da kaso na a jikinka dole ka bani sabo ba yanda za kayi rabona na ci hakkina nane Allah ya baka ajiya,shawarmar ma na zaci wani dan faten yakuwa ne haka,da nasan ba fate bane Zan bika ba ai ni na zaci faten yakuwa ne, ficika baza a baka ba iya kudin aure ne an baka Kuma kayanka wallah akan na baka gwara na yayyafa musu fetir na kone su. wannan har wani kudi ka kashe,ni Murmushi million Nawa nayi har ce min kake na iya murmushi idan nayi sai kace Murmushi na Kai kosar da Kai yake kaji ba sai kaci abinci ba karka dauka ban San karya kake ba kana tafiya zaka narki abinci. Lele da ace ya warke da tuni ba sai buzunka ba,Kuma wallahi kana magana Zan sa ko wacce mace a gidan makokin Nan sai ta lakace ma tabilallen hancinka,Su Anwar suna ta dariya Hamida tayi Masa tas Kuma yayi shuru,kannensa matasan samari sunga Yan hutu masu kudi Shuru sukayi,Ahmad yace kuyi Mata dukan kudina suka ce mudai Yaya ba ruwanmu wallahi baza ka ja Mana ba daga Haka sukayi tafiyarsu,Muhseen ne ya mike ganin haka Ahmad ya fada motarsa yace akwai magana a gaba sai na hanaki zaman lafiya a duniya ai Zan ganki a hanya Watarana,Nabeel ne ya fito sanye da jallabiyarsa dark blue,ya kalli Ahmad yace Indai haka kace to ka tanadi likkafaninka,Muhseen kafin kyafta ido ya sace Masa tayar mota da wani karfe,Anwar da Zain Suka fisgo Ahmad daga mota sai ya Shiga basu Hakuri,Muhseen dama dan kwaya ne Kamar Allah ya aikoshi haka ya dinga jibgar Ahmad sai guduwa yayi a million ya Sha kwana Ya bar motar a Nan. Anwar yace wannan anyi jahili marar mutunci sai kace jahilin Kauye,Nabeel yace Wai doctor ne,please karku sake wani ambatar doctor jahili dai cewar Anwar. Nabeel ne ya nufi cikin dangi zai zauna a saman carpet din da suke,Hamida tasan ba short a ciki sabo da lalurar, tace Yaya Nabeel matsowa yayi da kunnensa saitin bakinta yace fadi a hankali ta rada masa Banda wawan Zama mutane na sintiri a layin Nan ato,Murmushi yayi yace tafi gida kinzo kinwa your love masifa Ahmad dinki, gida tayi tafiyarta,Anwar ya kalli Muhseen yace kai gaskiya sauri zanyi na fadawa Yarinyar Nan Ina sonta,Muhseen takaicin Anwar ya kamashi yace ku duk bakuwa idan kuka ganta sai kunce Kuna so to ance an Mata miji,Anwar yace ko kaima kana ciki ne? Zain yace gaskiya beb din ta hadu Kan bala'i komai Excellent gata social ba ruwanta da wani Jin kai,Anwar yace Ina kaunar hancinta da kalar lips dinta wow,gata doguwa skin dinta me Jan hankali tana da Fara fara amma me dan duhu duhu haka,Anwar yace sai kaga gashinta ma,Nabeel hade rai yayi Kamar yau ance Mimi ta mutu tunda yazo wajen yaki magana hirar duniya Bai ce musu kala ba karshe ma tashi yayi ya koma cikin gida. Bayan an sallami baki Saura iya family din su Affa Yan Mata da maza da dare sun cika palon damkam wasu a kasa wasu a saman kujera suna ta hira Hamida tana ciki amma bata sa musu baki a hirarsu sai dai duk Wanda yayi magana ta kalleshi,Nabeel Yana dining shi kadai Yana cin abinci,Mimi da Affa suna bedroom. Sale ne yayi sallama tare da neman izini ya shigo palon daga kofa yace ance ana sallama da Shakira,Kallon kallo aka fara wace Shakira Kuma a dangi ba wacce ta mike sai aka ga Hamida ta mike tace Uncle Sale kace Ina zuwa aka kwashe da dariya gaba daya palon har Nabeel ya dara yaushe ta koma Shakira basu da labari. Ita kanta Hamida sai data ji kunya,Anwar yace Shakira a Ina aka samo sunan? Hamida tace Nick name nayi sab...kafin ta rufe baki Nabeel yace sunan arniya ce fa mawakiya,Hamida tace ni Ina son abina Malam Shehu ne yace idan na waigo Zan kalle shi sai yaga kamar Shakira,su Ihsan dariya harda jefar da waya,Wanda yake kiranki fa? Nabeel ya tambaya tace me voters card ne Wanda Affa yace naje nayi tana da amfani shine yazo kawo min,tana fada ta fice ta tafi karbowa Yana kofar gida a Kan lifan Suna gaisawa ya bata voters card ta dawo gida,tana shigowa Nabeel yace mu gani,Mika Masa tayi yaga ansa Shakira Kabir Tahir,Kai ya dafe yace Hamida Oh my God yanzu dan kanki ya kwance Shakira Kika je Kika sa? Kowa ya fara dariya,Yace dole sai an canja wata,Hamida tace Ni Allah bana so ni na canja suna na tashi daga Hamida ta furta da shagwaba,Nabeel a ransa yace me hali baya fasawa dama yasan Hamida kafin ta dawo normal sai ta shiga school dole yace dole na kaita school a week din Nan. Hannunta ya rike ya jata palon sama ya bar su Anwar suna ta dariya,paper ya dauka ya Rubuta mata sunan bank U.B.A yace me ake cewa wannan a turanci yanda ake ABCD kin tuna? tace ae yace to fada naji karanta maza,Hamida ta karbi takardar ta gyara zamanta a kujera harda harde kafa tana karkada kafafu ta karanta abinta da Hausa tace Uba Kamar baban mutum Uba amma ba Ubana ba gaskiya wannan ai wayon ka zagi banana ne Yana kabari Kuma ta kwabe fuska,harara ya watsa mata yace bani school Zan kaiki shehu baya aikinsa Kuma wlh a primary Zan saki cikin yara,Hamida ta fashe da kuka yanda bata son makaranta za a maidata baya tace Allah Zan dage Shehu ne Ni kwalliya yake koya min,Nabeel yace ai dama wannan ba malami bane korarsa zanyi na kaiki school suyi ta zaneki a can. Hamida tace ai ya bani assignment na mathematics bari na kawo ka koya min Dan iskan maths din Nan ne me Find X wlh na gaji Ni bana iya nemota,Nabeel ma anyi rashin sa'a a duniya bai iya maths ba a school da kyar yake tsallakewa,sai yayiwa Hamida wayo yace tab Nemo x ai sai anje Taraba Hamida tace Allah dama acan take? Yace a school can ake kaimu a motar makaranta idan Muka ganta a cikin yayanta sai ta ba kowa daya shike Nan mun samo ta,Hamida tace dan Allah ka rakani,Ihsan tana da ita kije ta nemota ta miki assignment din dama yasan Ihsan ta bala'in iya maths, Hamida tace to gobe kafin su tafi zata min. Hamida ta bar zancen Assignment ta Mike zata tafi Yace ki zauna ki tayani hira tace a'a Ni dai bacci zanyi ,Kai ya jinjina yace Wai me yasa yanzu Kika tsaneni ne kin rainani fa? Hamida tace ka manta Sanda ka dinga wulakantani kana hantarata Kai da matarka ka mareni ka zageni duk sabo da kaga Kalar Dausayina bani da daraja sai yanzu gwara na auri Wanda banga Kalar tasa ba baiga tawa ba,ka je ka auri Virgin dinka ba ruwana,Nabeel yace haka Kika ce? tace ae ta juya tayi tafiyarta,tagumi yayi Kawai tare da furta ya Allah ka kawo min agaji Yarinyar Nan Bata San son da nake Mata ba tun farko Allah ka ganar da ita,Allah ka shiryi Pipi Fitowa yayi ya ganta zaune kusa da Anwar da wayarsa tana tura film Wai zata kalla,Nabeel yaja kwafa ya wuce ciki shi duk ya matsu su tafi Abujansu ya huta,Har ya kwanta ya sake Fitowa ya leko palon yace wai bakusan ku kwanta bane dare yayi,Muhseen yace Kai Lele duk Nan fa Zain ne da mata kannenka mun girmeka amma sai wani Raina Mana hankali kake yi,Tsaki Nabeel yaja ya koma bedroom Hamida bata ma San me yake ba hankalinta na Kan waya amma tana jinsa,room din Mimi ya shiga ya iske ta tana gyara Kaya yace Mimi kice Hamida taje ta kwanta tana can tana sakin layi wajen su Anwar,Allah sarki Hamida bata yi surutun komai ba ma, Mimi tace me Hali baya fasawa sai tayi tunanin gaske ne tace naga ta fara hankali fa Kai wannan Yarinya Mimi ta sauka da sauri tace Hamida zo. Hamida mikewa tayi tabi Mimi Sama,tana Shiga bedroom Mimi ta rufeta da fada Lele yana zaune Yana murna,Mimi tace Zaki je kiyi zancen Duwawun da kika Saba ne wallahi ki kiyaye Ni,Hamida tayi rau rau zata Yi kuka tace wallahi Allah bana fada tun yaushe na daina tun Sanda Kika ce na daina kula Yaya Nabeel na daina fadan komai Kuma Ina kiyayewa na gane gaskiya na gane ba mutunci na bane sai fa yau kadai Kuma daga Ni sai Nabeel na fada Kuma ban ambaci takashi ba wallahi Kawai dai nace Naga tasa yaga tawa Kuma ai shine Yace Yana s....Nabeel ne yayi sauri yace jeki Kawai duk ya hana aji karshen zancen Hamida sabo da Mimi Kar ta ji,tana Jin yayi Shuru taci gaba sai yace Yana so...da sauri ya dan bigi mudubin Mimi da Hannu ya saki Kara,Mimi tace maganinka kenan gashi Nan kayi famu,Hamida ta rufe bakinta da tafin Hannu sabo Dariya taci karfinta Wai yayi Famu kamar dan kaciya,Mimi ta kalleta tace fita ja'ira duk abin fitsara kina ciki kaima fita munafuki,Hamida tana sauka daga last steps ta juyo tana kallonsa shima Yana sakkowa a ranta tace sai na Rama,Tafi ta shiga Yi Masa tana wakar da akewa Yan kaciya a kauyensu Wai Lele takwa takwa....ah Lele takwa takwa...Yan Palo Suka kece da dariya kamar me,Nabeel shi kanshi da kyar ya shanye dariyar sabo da Kar ta Raina shi da yawa,fisgota yayi tare da murde hannunta ya kwace Wayarta ya wuce masallaci. Washe gari da wuri duk Suka shirya Suka tafi har Anwar sun ga alama kamar Nabeel son Hamida yake shi yasa Suka hakura Kawai,gidan ya dawo sai iya su ya su Yan gidan sai Fadeela da aka kawota hutu,bayan komai ya lafa Nabeel ya samu Affa a room dinsa yace Affa ka canjawa Hamida teacher wlh in Banda kwalliya ba abinda yake koya Mata bata iya komai ba,Affa yace naga hakan nima Inshaallah gobe Zan kawo Mata wata Zainab babbar mace ce me hankali in yaso sai a sata a Islamiyya bana so ta shiga secondary ss3 bata San komai ba rainata student zasu yi a dinga wulakantata Kai kasan Yan makaranta,yace hakane kam yace yawwa kaima ka dinga dan koya Mata abubuwa,Nabeel ya sake cewa to amma Affa Ina son Nabeela dan Allah ka aura min ita,Affa yayi Murmushi yace bayan ka gama wulakantata Lele,dama Ina sonta Affa lokacin ban gane sonta nake ba tun farko,bazan baka ita ba kaje sai Zama yayi Zama ka Fara Mata gori wani dan abokina Zan bawa ita. Nabeel sai yaji haushi yace Affa kafi son bare da ni? Affa yace kwarai tunda baka ganin darajarta ba ai gwara a bawa me hankali Kai ka hakura ka auri Yar uwarka Fatima ko Ihsan munyi magana da su Yaya mun yanke hukunci Hamida Wanda ta zaba zata aura,Nabeel yace Ni bana son su gaskiya da na auri Fatima ko wata gwara na Kare rayuwata a haka,Affa yace Kai ka sani kuma,Nabeel ya sake cewa please Affa,Affa yace karka dameni Lele tashi ka bani waje Hamida ko ta aure ka kana da tabbacin zaka Haihu sannan ma idan baka warke ba fa ya zakayi da Yar mutane wajen bukatar Aure? Nabeel yace Inshaallah ma Zan warke Nan da 5-6mnth Affa Ina da karfin jini,gwara Yar uwarka inda zaka samu rufin asiri,Nabeel yace ita Basma da aka aura min ita kalli fa abinda ta min Haba Affa,yace to dawo da daya Basma ka aura,Nabeel yace Ni duk me Suna Basma bana kaunarta yanzu, to tashi ka bani waje Allah ya hadaka da ta kirki amma ba Hamida ba. Mikewa Kawai Nabeel yayi ya fice cikin bacin rai,Hamida bata San me akeyi ba karatunta take Yi sosai wajen sabuwar malamarta Aunty Zainab ta fahimci Hamida a hankali take bi da ita tana koya Mata har abubuwan rayuwa sannan tana zuwa Islamiyya sosai,kwana biyu taga Nabeel Sam Bai da walwala,kullum baya fara'a da sauransu Kamar yanda aka Saba,Sabgarta ma ya daina shiga kwata kwata,hakan yana damun Hamida sosai tayi zaton ko wata cutar ce kuma,tana so ta tambaye shi amma ba fuska. Karatunta takeyi sosai ta nuna bata damu da shi ba amma a zahiri hankalinta na wajensa. Haka rayuwa taci gaba da tafiya zancen auren Nabeel ya kankama tabbas ranar arba'in din Basma za a aurawa Nabeel wata matar,Hamida sai ana gobe ta tsinci labarin,Kamar tayi hauka kasa daurewa Hamida tayi ta dauki biro da takarda ta Kira Shehu a waya tace mu hadu dan Allah a bayan gidan Affa,Shehu 5pm yace ta fito yazo,bayani tayiwa Shehu tace abinda yasa bazan rubuta wasikar da kaina ba nafi son rubutun kwari Wanda yafi Nawa kyau,Hamida ta shiga fadawa Shehu abinda zai rubuta a takardar har ya gama tace sa ayar tambaya a can,Shehu ya saka,Tace sa coma again,Shehu yace to ya saka ta karbi paper ta Masa godiya ta koma gida tana shigowa room dinta ta wuce ta saka a sabon envelope ta manne ta kaiwa Mimi tace gashi inji wani mutumi yace a bawa Affa,Mimi ta karba tace bai fada Miki sunansa ba tace ae yace shima aikoshi aka yi ya kawowa me gidan,Mimi tace to idan ya dawo Zan bashi Hamida tace to ta juya ta koma palo. Kwanciya tayi tare da yin rub da ciki tana rubutu da karatu Nabeel ya fito shi fa Ammar,dama sun gaisa Ammar ya kalleta yace Sannu da karatu tace yawwa ta dago ta kalli Nabeel,yaga tayi kyau taci kwalliya cikin wani material black me adon red Riga da skert shi kanshi Ammar sai da ya kafeta da Ido sabo da ta fita ba karya,Haka suka wuce suna barin palon Hamida ta ajiye biro ta dafe kanta tare da lulawa tunanin Nabeel,a hankali tace dole in shiga in fita Ina Zan bar wannan inyi ya da zuciyata wallahi Matukar ba a Mana aure ba sai na bar gidan Nan har abada. Zuwa dare Affa ya shigo bayan ya nutsu Mimi ta Mika Masa envelope ya bude tare da zaro takarda ya warware ya fara karantawa kamar Haka Kuyi Hakuri da wannan AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 16-20 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Ummu Abbah Maman Raiz Mrs Aleeyu Sadiya Muhammad Fatima Abubakar Ummu Shafa'at Maman Humaira mk Rabiatu Maharazu Ummu Ilham Roukayya Bello Ummisalehmuhd2 Najida Aliyu Bicca Dr Zainab Abdullahi Umma Khursum Zainab (Queen Hernah) Zainab Shehu Maman Humaira &ikhram Mk Hussein Maman Kadi Affa karatu ya fara Assalamu alaykum Bayan dubun gaisuwa me yawa tare da fatan Kana lafiya tare da iyalanka baki daya,Ya yaron wajenka da jiki? to Allah ya kashafe,na Kira wayarka bata shiga sakamakon Matsalar Network da muke Fama a Kauye. Ba wani abu ne yasa na rubuto maka wannan Sako ba sai wani arziki da muke nema a wajenku dan Allah idan babu damuwa me zai hana a bawa Nabeel danka auren Hamida sabo da mu rufawa juna asiri tunda yaron nan shine ya aikata Mana ba daidai ba,da farko Kuma kace shine zai aureta bayan ta haihu,Ina neman wannan Alfarmar ,nasan Kai mutum ne me adalci da sanin ya kamata Ina so kayi shawara da Yan uwanka idan Kun Amince ko a waya ku Neme Ni,ko Hamida ita bata cancanta ta Zama matar Nabeel ba? Indai akan halayenta ne Hamida Inshaallah zata canja Inshaallah kuma kaga alama ta fara canjawa,babban rufin asirin da zakuyi Mana mu iyayenta shine ku aurawa Nabeel ita da Kun gama mana komai a duniya. Dan Allah karku aurawa Nabeel wata face Hamida na rokeku ku rufa Mana asiri Kamar yanda Allah ya rufa muku,sai naji daga gareka bissalam Sako daga Alhaji Isah Tahir marikin Hamida Mimi tana ji tace Alhmdllh dama abinda ya kamata kenan dama Nima abinda na yanke dan naga Hamida Ashe tana da hankalinta rashin tsayayye ne ya jefata a wannan hali amma gashi yarinya sai hankali take Ina goyon baya Kuma Lele yana sonta gwara a musu aure su karata dama shima Lelen ai Watarana irin halinsu daya da Hamida,Affa ya kalleta yace Kika ce da akan ya auri Hamida Zaki bar gidan Nan,Mimi tace na janye ba gwara ni ba Kai da ya Mata ciki kace love ne,Affa yace Nima naji wa'azi na ajiye akidar Bokon Nan Naga aya a gidana ba ruwana yanzu sukayi dariya,yace yau Zan fada Miki abinda Baki sani ba Kinga abinda Nabeel yayi ko to Nima Sanda Ina matashi na aikata,Sanda naje karatu turai shekarata goma bana Sallah daina yin Sallah nayi Kuma giya Nasha sai dana aureki na daina Shan ta ruwa na koma Shan alawar giya,Mimi ta zaro Ido waje tace yanzu dama duk alawar nan da Naga kana Sha giya ce? Affa yace ei ai in baki manta ba Sanda nake zuwa zance ma Zaki ga na bare alawa na jefa a bakina har kike cewa na San Miki sai nace Miki sai naje shopping Zan siyo Miki taki daban ai wacce nake Sha giya ce Baki sani ba. Mimi tayi salati tace da nasan hakane ai bazan aureka ba wallahi,Affa yace aikin gama ya gama yanzu ko sakinki Kika ce nayi wa zai aureki a zamanin Nan da Mata Suka cika duniya yan matan ma ya Suka kare haka Zaki hakura mu karasa zuna,ke dai tunda Allah ya shiryeni ki godewa Allah amma Ni abinda nayi Nabeel baiyi ba,Mimi ta rufe baki da hannayenta yace shi yasa Kika ji nace love ne a zahiri ba haka nake nufi ba naji zafi dannewa Kawai nayi na tuna Nima nayi amma Ni bata samu ciki ba na tabbatar da fadar Allah duk abinda kayi sai an maka shi yasa ake so ka dinga hangen baya da gaba nayi nadama wallahi. Yarinyar nan Hamida Bata San tarihinmu ba Kuma ki duba Nabeel ya Mata ciki amma taci gaba da sonsa idan Nabeel ya rasa Hamida ai har abada bazai samu me kaunarsa haka ba, nan gaba zata san asalinmu Inshaallah itama ta Zama jininmu. A ranar Affa ya kira Yan Uwansa yace su taho jibi da Shirin daurin auren Nabeel da Hamida. Bangaren Hamida Kuwa Papa ta Kira tace idan Affa ya kiraka ko me yace kace ba matsala karka ce baka San zancen ba,papa yace wani abin Kika kulla Kuma ke Hamida ki kiyayeni,Dan Allah Papa Kawai ka amsa haka yace to Kawai. Sai 11pm Affa ya Kira Papa Bayan sun gaisa yace Naga sakonka Kuma nayiwa Yan Uwana magana sun amince jibi Inshaallah zamu Zo da Shirin daurin auren Hamida, Nabeel zai aureta Kuma mun dauki nauyi komai ba abinda zaku siya,Papa yaji dadi duk da bai San me Hamida tayi ba ya amsa da murna harda godiya. Yana Gama Wayar Nabeel ya Kira ya sameshi a bedroom Nan ma ya Kira Hamida tazo,Hamida gabanta Yana ta faduwa ta durkusa a gefe can ta rakube Kamar ta Allah,Affa yace Papa ya turo wasika gashi ku karanta ya mikawa Nabeel ya karba ya karanta tsaf sabo da farin ciki bai San Sanda ya washe baki ba,Hamida ya mikawa ta karba a nutse,Nabeel yace Zo a karanta Miki baki wani iya karatu ba Zaki bata Mana lokaci,Hamida ta taso sum sum ta dawo kusa da Nabeel ya fara karanta Mata rai rai Nabeel harda kari yace kinji yanda Papa ya yabeni yace Ni mutumin kirki ne na daban ne a cikin mazajen duniya,ya sake duba takardar ya dago ya kalli Hamida yace kinji yace gani da nutsuwa gentle man,Hamida tayi Murmushi tana sauraron zuki ta malle tace to Papa bai iya karatu da rubutu ba Kamar Ni haka yake, Affa yace to in ba shi ba wa zai rubuta,tunawa tayi zata tonawa kanta asiri tace Yaya Sulaiman ke Masa rubutun ai. Nabeel takardar ya kalla tare da kafe rubutun da Ido Yana karantawa a fili Yana cewa a bawa Nabeel auren Hamida badan komai ba sai sabo da hankalinsa da kamewarsa da nutsuwa,Alhaji Al-amin danka Nabeel ne kadai zai iya saita Hamida ya bata ingantacciyar rayuwa,Affa yace Miko min takarda dama yanzu uwarka tace kaima irinku daya da Hamida,Hamida an nutsu a dole ta kirki,Affa yace Hamida ya Kika gani kin Amince kina son Nabeel? Hamida tayi kasa da kanta tare da rufe Rabin fuskarta da hijab a hankali tace Affa ya tsaya nidai na Kara kallonsa idan ya min? Mimi tayi dariya tace duk kallon da kika Masa sabo Zaki sake yanzu,Hamida ta boye Fuska tace to abinda kuka ce yayi bani da zabi,Affa yace kin tabbatar? Hamida ta daga Kai wai ae Affa yace mashaallah za ayi komai Inshaallah,Kai Nabeel ka kawo kudin aure da za a bawa iyayenta,Nabeel murna ta isheshi yace million Nawa?Mimi Tace kaima fa Nabeel Zama da Hamida yasa ka zama wani iri tashi kuje,a tare Suka fice,suna fitowa a steps Nabeel ya rungume Hamida tare da sakinta yace wannan na Kai kudin aure ne,anjima kadan zanyi na Engage dana daurin aure da Kuma na Kai kayan lefe,Hamida tace duk a yau? a'a bada ni ba matsa dan Allah na wuce,Nabeel shi duk zatonsa bata sonsa ganin bata murna bai san itace ta Kai wasikar ba. Bayan Hamida ta shiga room dinta Papa ta Kira a waya,yace Hamida Wai wanne Sako ne Affan naku ne ke cewa yaga sakona mene? Hamida tace sai na Zo kauyen papa Zan fada maka, Papa yace to Hamida na yarda da ke,Shirin biki Kuma Affa yace za ayi a Nan kauyenmu gidana sai ki kokari gobe ki taho gida,Hamida tace to Papa,sunce su zasu Miki komai Hamida tace to Papa sai na Zo,Yace na sanarwa kawarki Sakina kin San tayi aure ta Haihu ma,Hamida tace ta fada min a waya,to shike Nan sai goben ki taho da wuri,Hamida tace to Inshaallah. Washe Gari da sassafe Hamida tayi shiri tsaf zata koma kauyensu,Mimi ta kawo Mata kaya duka English gown ne masu tsadar gaske kala biyu Wanda zata sa da biki sai wani arnen lace tace wannan da shi za a kawo ki dakin mijinki to Hamida tace tare da yin godiya duk tayi wani sululu haka bata da karsashi,shi Nabeel Yana kula da ita Kamar kaunarsa ce bata Yi haka yake gani,takalma da jaka masu tsada Mimi ta shirya Mata tsaf tace Nan gaba zamu hada lefe ko kina dakin mijinki Inshaallah,Affa ya hada Mata uban tsaraba iri iri yace taje ta rabawa Yan Uwa. Nabeel ne ya fito zai rakata mota driver ne zai kaita har can a zukekiyar motarsa,Cikin wata shadda purple ta fito tayi kyau masu Aiki Suka zuba Mata kayanta a mota komai,Hamida tana jikin mota ta kalli Nabeel shima ita yake kallo tace shike nan? Murmushi ya saki tare da gyara Mata mayafinta yace sai munzo jibin idan an gama Adduar arba'in,to ta furta Kawai sannan ya bude Mata ta Shiga mota ya zaro kudi masu yawa sun Kai dubu dari yace gashi kudin saloon,godiya tayi ta karba yace Zan turawa Yaya Sulaiman kudin girkin angwaye to Kawai tace, ya mayar ya rufe Mata da kofar ya zaga wajen driver yace ka tafi a hankali banda gudu da ganganci, ya sake lekawa ta window tayi dariya yace Yaya Sulaiman ya iya mota ne? Hamida tace ae ya iya dai sukuwa da jaki Sanda papa yana da jakin ebo ciyawa da harawa da Kuma kasa a kududdufi, Nabeel yayi dariya yace pipin shirme kenan mota kadai na tambayeki fa tace to gaskiya Ni iya jaki na taba gani Yaya Sulaiman Yana hawa har boris yake idan ya hau, yace to da ya iya mota sai na barmiki motar shi driver in ya kaiki ya dawo ya baki key din motar ki ajiye duk inda Zaki fita a ki bada key a kaiki. Hamida taji harka tace dama gashi Ina so naje siyayyar kayan robobi musamman pow na Yara Kar muyi Baki masu Yara su dinga bata min gida,Nabeel yace kinyi gaskiya amma bana son komai ko me kike so ki fada Zan siya Kalar na Yan gayu ban son tarkace,Hamida cikin sanyinta tace to ka siya min tandar waina da abin sinasir zan dai turo ma text a waya,yace to no prob ya daga Mata hannu tayi Murmushi Kawai. Ta window ta dan leka tace Yaya kyakyawa, juyowa yayi da sauri tace sai naji bana son tafiya,Murmushi yayi yace jibi Zaki dawo ai,Kai ta daga sannan ta Masa bye bye,har motar ta fita daga gidan suna kallon juna ta glass,Sai data bar gidan sannan ya Kira Ammar akan maganar abokai Wanda za a sanarwa daurin aure kawai ba wani shagalin dinner. Hamida Kuwa sai Yamma likis Suka Isa kauyen,sai bin motar ake da kallo har kofar gidansu sannan driver ya firfito Mata da kayanta kaf ya Kai cikin gidan ranar Karima da Yaya Sulaiman suna gidan Hamida tayi clean,tayi kyau an iya gayu duk Kuma ta wani nutsu tayi sanyi Sulaiman ya kalleta ta shigo ana gyara jaka dake kafada ana tafiya a nutse ba sauri ba gudu harda yanga,dariyar ma an daina ta hauka,Ummi anga Hamida taci gaba Tace Haba ko kefa yanzu za muyi alfahari da yarmu. Hamida tayi Murmushi Kai a kasa tace Ummi Ina yini ya gida,da fara'a Tace lfy Alhmdllh ai dama Hamida ba kece ba a so ba halinki ne ba a so gashi kin nutsu har kinfi Sanda mukaje ta'aziyya haduwa,Uhmm Kawai Hamida tace,Sulaiman ya kalli Hamida ta Zama mutum yace Hamidatuwanmu Dariya tayi ta bigi kafadar Sulaiman,Karima tace Kinga ni na saki baki sai kallon Hamida nake an Zama Yan gayu oh Allah me iko dariya sukayi gaba daya Sulaiman ya mike ya kaiwa driver abinci da ruwa,Bayan yaci yasha ya musu sallama ya tafi,Papa ma ya shigo Yana ta murna Hamida an nutsu sosai,Wayarta ta dakko tare da turawa Nabeel text mun Isa gida lafiya ka fadawa su Mimi. Tunda akaji Hamida ta dawo a dankareriyar mota mutane sai tururuwar ganinta akeyi Allah yasa ba Wanda yasan tayi wani ciki kowa ya yarda birni aka kaita wajen Yan uwa,Ummi sai rawar kafa takeyi akan Hamida tana bata magungunan gyaran jiki. Washe gari Hamida garin ta shiga ta Dan zaga gaida dangi da abokan arzuka,Samarin garin ana ta sonta a baya suna ganinta a banza ba Wanda yake saurarata ko da Wasa wasu ma mahaukaciya suke kiranta,wasu suce ko sadaka basu karbeta ba sai gashi Hamida Allah ya bata wanda ya fisu, yanzu da kyar ma suke gane ta sabo da yanda ta goge ta Kara kyau,dama ita rayuwa haka take Wanda ake rainawa ana Masa dariya ana kallonsa a banza to Allah baya hadawa mutum Inshaallah ta wani hanyar sai Allah ya Masa abinda zaizo ya Zama abin kwatance a rayuwa Gidan Sakina taje samari sai magana ake Mata ana Hamida ashe kinzo garin sai ta tsaya su gaisa ta wuce abinta tana taku dai dai da yanga tana wani takama,gidan Sakina taje ta samu Sakina ta auri wani teacher dan saurayi babansa ma Yana da Hali a kauyen bata da wata matsala,Sakina ta fito da gudu ta rungume Hamida tana ihun murna sai taga Hamida sai murmushin manyan Yara akeyi,Sakina tace gaskiya Hamida kin dade a birni Barka da zuwa wai Kinga yanda kike wani Gloshing,Hamida ta saki Dariya tace dalla banza Glowing ake cewa Kamar Baki school ba,Sakina tace iyye Allah ya yarda ai kin San makarantar kauye sai a slow, Hamida ta kalli Sakina tace Ina Dan namu? tace babansa ya fita dashi muje palon Suka shiga ciki,Sakina tace akwai labari fa,Suka balle da hira Hamida ta bata labarin birni amma batace cikin shege tayi ba kin fada tayi, Sakina tace ashe dama Kuna da Yan Uwa a Kaduna? Hamida tace baki San ikon Allah ba ashe Yan Uwan namu makwaftan su Yaya kyakyawa ne,Sakina ta saki shewa,Hamida tana wani kekebe baki ita Yar birni tace hmm mutumin Yana ganina Watarana na fito daga gidan da nake sai ya narke ya dawo ya dinga naci har da kuka,lokacin yaga bana ta tasa nayi Masa wani eban Karan mahaukaciya ko kallonsa ba nayi,a Hanya yake tare ni yana Hamida dan Allah ki yafe min I love you I waye waye Sakina tace shegiya kauna ta sheke da dariya to yaga kin goge. Hamida ta wani tandi Baki kamar tana side yatsunta Wai duk cikin birnanci ne an wani dora pillow a saman cinya hannayenta suna Kan pillow din tace baki gani ba harda durkusa min wai zai haukace a kaina tana fada ta rike haba da yatsu biyu ita ga wayayya tayi wani zaman daukan photo,Sakina tace bari na Mana girki ai nasan dole ki ja shi a kasa ko? ai yafi Gaban ja sai dana tuburbuda shi sannan a Haka ma bani nace ba Iyayensa ne Suka ce basu taba ganin yarinya me hankali a duniya sama dani ba ke Kinga kauna Miminsa komai My daughter, tasa a kawo min perfumes a kawo min snacks su lemuka chivita, Lacasera, ah lallai Kinga kauna cewar Sakina, Hamida tace ke harda su lemon kasar saudiyya su Sudeis Cola,Elsharawi aljamal nam, Sakina tace me ke nan wannan Yan gayu? Naman rakumi fa na kamfanin Elsharawi dake Qatar Kuna Nan kauyen baza kuji labarinsa ba,Sakina tace yo Ina zamu sani kaddarar mu tana Kauye. Sakina tace bari na aika a siyo Miki ko mirinda ce kiyi manage da kifi,ta leka ta aiki yaro sai ga yaro ya dawo yace babu kifi ba a soya ba sai anjima ya Miko lemo shima sai uban zafi na Rana,Hamida tace tirr da Kauye shi yasa akace arziki chasa'in da tara duk a birni aka saukar da shi Kauye guda daya ne tal nasu dole kusha masifar rayuwa Kuna cikin wani hali,Sakina tace dole ki zagemu tunda kin gama tsallakewa,Hamida tace Yi Mana jullof din taliya a birni abinci light ake ci ba me nauyi ba shi yasa kashin dan birni ma daban yake in Kika gani wani sawai sawai da shi,Sakina tace Hamida wallahi banda karya kin koyo karyar Yan birni,in kinje Zaki gani ai ki tabbatar ai. Sakina suna girki suna hira Hamida tana tayata duk ta damu Sakina tana zuba wannan soya wancan Wai ita tawaye har Suka gama,Bayan sunci sun koshi Suka Yi Sallah sannan Hamida tace Ina dan magungunan matan aure da uwar kudina ya kamata na Fara yiwa Dausayina polish na danyi polishing dinsa,Sakina ta dinga dariya tace kin shiga Uku wlh, Hamida bata ce Naja'atu bata da lafiya ba an boye sirrin Nabeel,Sakina tace ai jira nake ya dawo sai mu tafi hado kayan komai mu hada sai ki tafi da abinki can,Haka Suka dinga shirye shiryensu har Karima kwana tayi sai an gama biki,duk kauyen su Hamida Kamar Yan bariki suke har matan aure yawancinsu fitsararru ne abokan arzuka Suka ce sai anyi Dj ana gama daurin aure,Hamida tace gaskiya ayiwa su Affa Kara ranar da sadakar arba'in din yarsu fa, Ni rawa ma da Waka basu dameni ba so kuke duk Yar albarkar auren ta watse ku jawo Mana masifa,sukace su ba ruwansu basu Suka kashe ta ba Ummi tace ai Karima tuni ta dakko Dj a daga birni zasu Zo sai anyi shagali,Hamida tace ni dai gaskiya a ganina ba a musu Kara ba,Karima tace mu sai mun San anyi bikin Hamdy a garin Nan kawayena na birni duk na gayyace su da Yan school dinmu Kuma zasu zo,Baki Hamida ta tabe tace to nidai bana rawa Kuma bazanyi ba angon ma da kyar in zai samu zuwa. Su Ummi ana tashi aka fara girke girke Karima a birni inda take aure ta bawa kawayenta girkin manyan baki za a yo fried rice da Naman kaji,ga waina da Miya su drinks duk an siya da ruwan roba,Hamida Kuwa daga cikin birni aka Kira me lalle ta zana Mata hadadde Suka je saloon ta zuba kyau Dake daurin auren ya Kama ranar juma'a 2pm kenan duk abinda ya kamata sun hada komai cif dangin su Hamida duk sunzo sai shiryawa ake ana kwalliya,Yan birni Kuma gidan Sakina ake saukarsu,Me kida tuni sunzo suna jira a basu damar farawa. Nabeel sai wannan bikin ya gayyaci abokai sosai sai sauka suke wasu a motoci wasu a jirgi,Affa da Yan Uwa duk an taho har su Anwar kaf dinsu harda su Ihsan an dirga a kauyen su Hamida,gari ya cika,Hamida tana gidan wata kawar Karima dake kauyen acen take shiryawa kayan da zata sa ma suna can,kawar Karima tace karki shirya da wuri,Hamida tace kina ji fa Ango ya Kira yace sun sauka a jirgi yanzu zasu karaso kauyen,lekawa waje tayi ta dawo tace lallai nayi albarka ana ta min kallon mahaukaciya Allah kenan gashi na Zama me daraja sai ma anga ango za a San darajata ta wuce tunanin mutane. Kayan da Mimi ta zabar Mata na daurin aure wata gown ce me shegen tsada ko Ina walwali yake ta dan dame daga sama kasa ta bude amma ba irin da yawa ba Kalar ta amare ce,Me dauri cikin kawayen Karima itace tazo ta tsara Mata make up da kayan make up dinta tazo da kinkimemiyar jaka,sannan ta Mata hadadden dauri sai ga Hamida ta dawo wata Kamar Yar gomna, a mudubi ta kalli kanta ta rike Yar jakar amare ga takalminta wow Golden anda arsh ta sheka kyau na mamaki,Hamida tace yanzu nake Pipi ba da ba dole na nutsu na Kara hankali na waye na sake kilewa ya Zama Yar gayu dole na koma Queen,ta sake juyawa a mudubi tace inaga babana dan sadaka yalla ne ko Mamata ce ta hada alaka da larabawa kawayen kamira suka sheke da dariya,Kawayen Karima Yan birni ba kunya ce da su ba sun zaci Hamida irin Yan kauyen Nan masu kunya duk da sun ganta a waye take ba duhun Kai Suka ce ya kamata mu koma gidan Sakina tunda duk Yan matan suna can,Hamida tace mazane fa ko Ina Kar ace banda kunya domin dama Ni nayi kaurin suna ba karamin aikina bane inga Ango yayi kyau ya tafi da imanina kuga na dauke Hanya nayi wajensa da tsokana ta fada suna ta dariya Suka ce to ai baza ma mu bari kije ba a tsakiya zamu sa ki,Hamida tace uhm uhm zuciyata bata da Kashi ni zuciyata tafi karfina ban fi karfinta ba ku bari dai a daura sai mu fita, suna surutunsu sai Suka ji har ance an daura aure bayan idar da Sallah. Hamida tana Jin dahir an daura ta hau murna tana na cinye gasar na daga kofi,duk matan da suke ta wani son Yaya kyakyawa dukkansu karya suke na cinye gasa,Suka ce to mu fita muje can Kar angwaye su jira,Nabeel Yana cikin mutane da abokai suna tsokanarsa wani abokinsa ya bashi Hannu Suka gaisa yace congratulation Engineer, Kamar kasan sanadiyyar Aiki Muka hadu ba abinda zancewa aikin Nan Nawa ya gama min komai badan gudun abin kunya ba da guda zanyi Ammar yace sai kayi ma yanzu ai,Nabeel ansha wata farar shadda harda babbar riga ya diga ruwan kyau,yau haka yasa wadonsa Wai dole sai yazo daurin aurensa. Hamida a tsakiya kawayen Suka sata Suka fito,Nabeel ya hango ta Hamida tana ta Masa wani munafukin kallo tana cewa a ranta yau turare yaga ta kansa a wajen Ango,Zasu wuce gungun maza su Anwar Suka ce Amarya pics zamuyi fa Hamida dan Iyayi harda wani kuka Muhseen yace mene haka Kuma tace Yan birni na gani duk dalili na Suka Zo,Sukayi dariya tace bari a fito da kawayena ko ku ma zaku samu ku rabauta da partner,Suka Kara gaba sai koda kyan Amarya ake,tana shiga ciki Sakina suka lullube Hamida da ihu duk Yan kauyen nan masu tsokana na yi bata ce musu komai ba har Suka gama. Hamida taja hannun Sakina wani daki da ba kowa tace Sakina na lashe gasa,Nawa Kika ji Sadakin? Sakina tace Dan ubanki a banza Kika ga Muna murna dubu dari biyar da mota sabuwa dal,Hamida ta rasa inda zata sa kanta tayi kofa zata fita ta dawo ta juya ta sake juyowa tana ta diri diri wai duk murna ce ,Sakina tace ke dai ai zance ya cika gari,Karima ce ta shigo tace to an hada take away da komai na angwaye Hamida tace Ina na Ango da nace a ware min? Akace ga nasa jaraba za a baki tace kaza daya nace da farko to a Kara Masa guda daya su zama biyu tukwicin sadaki,Suna dariya Karima tace Ina zai Kai kaza guda kince a soya Masa tasa guda Kar a sake a yankata pieces ke duka a bankare za a bawa ango kince taki ma guda ta wa kike so a baki Kuma ai da Sai kice tun jiya a soya Miki uku,Hamida tace kazar ango ce taya za a bashi daya,okay fine ga Naman rago can da kika ce a soya sai a zuba Masa tace yawwa ta Miko wata ledar take away tace wannan na katuwar silver duka Zaki juye,Karima tace mu Kuma fa? Wa yake ta ku maci ko yanka dai dai ne,Baki Isa ba walh Hamida cewar Sakina Suka zubowa ango iya yanda za su iya Hamida ta dinga Fushi,ta koma tayi zamanta,aka kawo su peppe soup shima duka a mazubin take away ga lemuka su drinks komai dai. Sakina ce tace mun shirya komai namu kawaye, Karima tace ku dai kuka sani idan kuka kunyata kanku ba ruwana ,dukkan nau'ikan abincin waje aka fito da shi aka bawa dukkan manya nasu da matasa dana Dangin ango kowa sai ya zaba,Angwaye Kuwa a gindin wata bishiya aka jera musu fararen kujeru da Suka yo haya,Haka Yan Mata ma Suka zazzauna,masu kida suna ta cin abinci Suma,Angwaye basu Fara ci ba sai da sukayi hotuna da Amarya da kawaye sannan dangi ma kowa sai aka zauna ana cin abinci banda Nabeel da akace nasa daban,Yana zaune Suka ga ana ta girke Masa girki iri iri nama kala kala abokai Suka ce bai Isa ba Suka cinye nasu Suka dawo Kan nasa shi bai ci ma da yawa ba,Yana ganin Hamida ma bata da nutsuwa sabo da mutane ana ta kiranta ana hotuna. Bayan duk mutane sun tafi saura kawaye da Angwaye da Dangin ango Mata da maza,Dj ya saki Sauti Su Nabeel mamaki ya Kama su ganin matan aure ba kunya kowacce ta botso duwawu baya suna wani karkada harda masu yin goho suna rawar kwankwaso dattijai ,Yan Mata Kuwa inda kasan karuwai,Sanda Karima ta shiga Nabeel Nan ya tsinke da lamarin wakokin fitsara ake sa musu,Hamida Amarya tana gefe tana ta dariya tace Ni wallahi haushi ma suke bani a dinga barin takashi a gaban maza duwawu na tashi,Hamida ta jawo Karima tace ke Aunty idan mijinki ya gani sai ya tsine Miki wlh Duwawu haka ki ta zazzage shi a gaban mutane maza,Karima ta fisge ta koma abinta,idan sukayi wani abin Nabeel har rufe Ido yake sabo da kunya,Sakina ita Duwawun ma Kamar tsinke Hamida tace ke Sakina sunan naki duwai bai Kai darajar duwawu ba ki fito kayan takaici. Duk Yan birni kasa rawar sukayi sunga an fisu fitsara ma Nabeel yace ashe Hamida ba banza ba amma duk da Haka na Kauye suna fita na birni Suka shiga Kawayen Karima Suka fada ciki Suma na birni ne amma Ina rashin albarkar tayi yawa samari Kuwa abin nema ya samu sai barin kudi suke,Hamida tana daga gefe cikin Yan kallo kamar ba itace Amaryar ba,Tace wuhuhu Sannu Takashi sannu,Nabeel yace tazo ta karbi kudin liki ta makale kafada tace nidai bazan je ba Allah. Ihsan ganin Amarya taki ta musu liki tace a sa Mata tsohuwar wakar Shakira Shakira Dangin ango da Suka San da zance suna ta dariya Hamida ta gudu wajen Nabeel,Suka zo zasu jata ta karfi Nabeel yace baza tayi ba kuje ku kuyi,kudin liki Nabeel ya bata yace je ki musu liki shima ya mike ance Amarya da Ango ake bukata Suka shiga fili su kadai hannunsa cikin na Hamida sun Sha ruwan kudi ba Wanda ya kada ko kafa Kawai tsayawa sukayi aka dinga zuba musu ruwan kudi sannan Suka yiwa mutane liki sannan gaba Daya Angwaye Suka tafi sai Dangin ango mata iyaye da Yan Mata zasu taho da Amarya sabo da yawan Yan Kai Amarya kawai a tafi a motoci, basuyi booking flight ba Papa da Ummi suka ce su dai a Dangin Amarya ya zabi iya mutum biyar su zasu je Karima,Sakina kawa,sai dattijai guda uku,Dangin ango ma Yan Mata tuni sunyi gaba sai masu tafiya da Amarya su Uku kwata kwata mota biyu aka dauka sauran motocin empty Suka koma da ace sun San baza aje da yawa ba da flight zasu bi. Amarya kayan da abubuwan gyaran jikinta duk an zuba a mota komai tayi wanka tasa lace hadadde maroon mayafinta adon jikin lace blue takalmi da jaka blue,Hamida harda kuka,aka kaita gaban Ummi da Papa zasu Mata fada,Papa bai iya fada ba shi Sam tana gabansa tana kuka tana shesheka fuskarta a cikin mayafi tace Papa ayi Mana Addua Ina fargaba ban San wacce rayuwa zanyi ba,Papa yace ta alheri zakiyi Hamida Inshaallah Allah bamu sa'a sai Watarana,Allah ya bada sa'a ita Kawai papa yake maimaitawa Hamida,Hamida tace papa Kamar na dakko talla taci gaba da kuka, akayi dariya aka tafi da ita wajen Yaya Sulaiman shine yayi fadan yace rayuwar baya ta wuce sabuwa Zaki shiga me Dadi Inshaallah Hamida,ki nutsu kiyi hankali,ki kula da mijinki ki Masa biyayya duk abinda yace kiyi kinji,ki daure ki samu ilimin addini dana boko Banda shirme nasan kin samu nutsuwa ki Kara akan nada,ki koyi rike sirri banda bankada Hamida tace Inshaallah Sulenmu,Dariya yayi Wai Dan ta tsokaneshi. Wajen Ummi aka kaita Nan ma Ummi ba laifi tayi kokari ta gaya Mata gaskiya ta Mata Nasiha karshe tace aure sai anyi hakuri banda Raina Iyayen Miji da Yan Uwa a rage surutu marar ma'ana tace to,har zasu tafi tace tayi mantuwa wajen papa,ta koma ciki tace papa motar Sadakina na barmaka ita,kudin Kuma a bawa Yaya Sulaiman dubu dari uju yaja jari ya fara sana'a,a..papa ne ya dakatar da ita yace tunda kin bashi har dari uku ai ya isa,mota Kuma kice mijinki ya turo a daukar Miki,Hamida tace wlh tunda Ni ya bawa na bar maka ta dinga rokon Papa ya karba sai da ta hada da harda kuka da kyar ya karba mota ta million biyu da rabi,sauran dubu dari biyu Kuma a hannunta Papa ya bata ta zuba a jakar Karima sannan Suka tafi a motoci. Sun dau Hanya sun bar garin Adamawa sosai sun shiga daji ana tafiya Daya motar su Karima dama sunwa motar Amarya nisa Bama a hango su,sunzo wani gurin rami Kawai Suka ga manyan bishiya an datse Hanya da Yan daba dauke da makamai iri iri,Hamida kuka ta saki tayi maza ta zaro Wayarta jiki na bari ta Kira Nabeel Yana dauka yaji tana kuka tace Yan fashi sun tare mu,Innalillahi ya Shiga ja ta Wayar yaji ana durawa su Hamida ashar wani kato ya leko tare da karewa motar kallo Mata sai kuka jiki Yana Bari,wani cable Suka zaro Wanda ake shake mutane da shi,Nabeel Yana Jin kukansu sabo da Wayar ta fada kasan kafafunsu. Yana ta kwala Kiran Hamida,ai Kuwa suna zuwa Suka bude mota tare da fisgo Amarya waje ita kadai Suka dauka ku tafi ko mu hada da ku,Hamida ihu da tsalle. Take tana Kiran sunan Nabeel....driver jiki na bari yaja mota Suka daga musu hanya Suka wuce suna kuka suna kallon Hamida aka hankada keyarta cikin dajin. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 21-25 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM PAGE NAKU NE Hjr murja kankara Mk Hussein Ummu Zahyed Mrs Aminullah Khadijatul Kubrah Faiza Ummi H Ummul Ihsan Motar da aka sace Amarya sune suke ta buga waya dangin Amarya dana ango ana sanar da abinda ya faru duk sun firgice suna ta kuka,Driver me tuka motar sai Innalillahi yake furtawa Yana cewa da Mata kuyi Hakuri ku dowa Allah mun kubuta babu mu Allah ya taimakeni iyalaina Allah ya musu gyadar dogu da tuni Ina ciki shike nan su da cin taliya sai dai su gani a makwsta, sai da wata dattijuwa Maijidda ta zazzage shi tukun sannan yayi shuru Nabeel a haukace ya Kira jami'an tsaro ya sanar musu Nan take Suma Suka aikawa Wanda suke kusa da wajen har sojoji Su Affa sun sanarwa,Gaba daya su Affa sunyi jungum jungum a palo sabo suna karasowa gidan Affa aka wuce da su Kawai suna ta faman kuka sun rude,Affa yace ba kuka zamuyi ba gaba daya Addua za muke a tayata da shi itace mafita kawai kowa yaje yayi Alwala azo ayi saukar Qur'an ayi addua Allah ya kubutar da ita,Nabeel shi Kam kwata kwata ma ba a ganshi ba an Neme shi an rasa kwata kwata. Abinda basu sani ba Nabeel mutanen Unguwarsu duk ya bada sanarwa a tayasu da Addua sannan duk ya tattaro abokansa Suka shiga wani Palo kowa yayi Alwala sukayi Nafeela tare da mikawa kowannensu Qur'an da inda zai karanta da Niyyar Allah ya kubutar da matarsa,Affa bai San ma Su Ammar sun dauki mataki ba na gayawa Allah ya kirasu Yana Neman Nabeel ya fada musu abinda sukeyi Yace Alhmdllh kunyi dabara haka ake so muma gashi zamu dukufa duk abin ya samu bawa abu na farko ya tuna da Allah ya Kai kukansa wajen Allah ba wajen wani boka ba,ko mutum ya zauna ya dinga bakin ciki Yana kuka ya kasa bacci amma ya gagara tashi ya kaiwa Allah kukansa,duk abinda ya damu mutum to ya Kai kuka wajen Allah Suma can Su Yayan Affa sun bada a taya su da Addua a masallatai da Yan uwa,Ammar Yana ta karfafawa abokinsa gwiwa cewar Inshaallah ba abinda zai sameta. Bangaren su Papan Amarya ma haka suke ta kai kuka wajen Allah. Nabeel lokaci guda duk yayi wani iri duniyar ta Masa zafi,Kowa abokai da Yan Uwa da iyaye sai kwantar masa da hankali akeyi ana Masa addua,ko magana ma ba yayi sai ta zama dole sabo da tunaninsa kar su cutar masa da Hamida,duk Sanda akace an sace mace ana Shiga firgici sabo da raping da ake musu ko a aure su Kawai sun zama nasu musamman mace irin Hamida zukekiya. Bayan sun gama adduoi Nabeel part dinsa ya koma ya kwanta Yana ta tunani ko wanne Hali Hamida take oho,kwanciya yayi a saman bed ya kasa kwanciya ya Mike zaune ya zuba tagumi,Zama ne ya gagareshi ya mike tsaye sannan ya dakko Wayar Hamida data sullube a cikin mota ya kalli wallpaper dinta Wanda pic din Nabeel ta dora akai Yana Murmushi,tunano abubuwanta yake kawai bai Sanda hawaye ya taru a idonsa ba a fili yace kidnapping mutum da ciwo yake da ace mutuwa mutum yayi kasan Allah shi ya karbi abinsa amma Yana hannun wasu baka San a ya mutum yake ba Allah ka saka Mana ka kubutar da matata Ya Hayyu ya qayyum. Mimi ce ta shigo dauke da abinci tana kwantar Masa da hankali amma kasa cin abincin yayi ruwa Kawai ya iya Sha dole Mimi ta koma da abincin. Yayan Yan uwan Affa ma waya suke ta bugowa Nabeel suna kwantar Masa da hankali tare da karfafa Masa gwiwa zata fito Inshaallah shi dai Nabeel jinsu Kawai yakeyi. Bangaren Hamida Kuwa tafiya me nisa Suka dinga kwararawa da ita cikin dajin Wanda yaki karewa Hamida tun tana kuka har ta gaji ta daina ga yunwa ga kishirwa tafiya taki karewa,su Kuwa dukkansu da bindigunsu zafafa sun sa Hamida a tsakiya har dare yayi tafiya suke Hamida ta lullube jikinta da mayafinta sosai sabo da Kar ma su kalli surarta wani Abu ya darsu a ransu, Wasa wasa har akayi Sallar Isha,karfe goman dare ta hude suna ta zuba uban tafiya,12am tayi duk ana uban tafiya kafafun Hamida duk sun kumbura sosai da sosai sabo da bala'in tafiya,su Kuwa sai ihu suke suna wani irin yare Wanda bata gane wanne yare ne,sai wurin 2am taga wasu Yan daban a ciki yawansu ya baci da machine,tsawa Suka bugawa Hamida hau daya,Hamida bata ko uhum haka ta gyara skert din lace dinta ta hau Suka bi wata siririyar hanyar a dajin sukayi ciki gaba daya ana gudu ana ihu ana daga bindigu,Hamida ta fashe da kuka tana karanta duk abinda yazo bakinta tana rokon Allah ya kubutar da ita ana wuta ana fyalla uban gudu. Sai da Suka yi nisa sosai sannan Hamida taga mutane ta ko Ina duk gasu Nan a daure fululu da su kowa ya galabaita Yana cikin wani hali,ga Mata masu girki suna ta aikin girki da kantama kantaman tukane,suna tsayawa Hamida ta sakko,wasu Suka cafki hannayenta ta kwalla Kara tace zanyi fitsari cikin yaran wani ya Rakata can wani waje me uban nisa gaba daya kashin mutane ne da futsari Kamar zatayi amai ta dan yi yanda mutumin bazai ga tsaraicinta ba ta fara fitsari chaaaaaaa Yana tsaye a kanta da bindiga, mutumin sai da ya kusa Dariya bai taba Jin fitsari me karfin na Hamida ba kamar an kunna pampo da dan wani ruwa da Suka bata a jarka tayi tsarki ta fito da sauri daga bayan dutsen mutumin yana bayanta da bindiga,Tace zatayi Sallah wani ciki ya dura mata zagi sannan da kyar ya bari aka bata ruwan Alwala,ita dai bata ce komai ba bata kula kowa ba,har tayi Alwala ta fara gabatar da sallolinta tana sane da gayya ta dinga lankanji raka'a daya ma kafin tayi aikine ga dakaru suna jira tana ta kaiwa Allah kukanta ko adduar bata gama ba duka Suka tasa keyarta gaban Ogansu gaba daya A gabansa ta durkusa Yana zaune a Kan saman wani dutse Kato Yana bulbula wiwi ya kalleta sosai yace ke cikin tsawa ya furta ya sunanki? da Sauri Hamida tace Shakira wani mahaukacin Mari ya zuba mata ta fashe da kuka tace wallahi sunana Hamida na dawo Hamida ta,yace mu ba a raina Mana hankali a Nan yanzu Zan dauke kanki da bullet. Hamida tace kayi Hakuri bazan sake ba,yace ke nan Amarya ce ko? tace ae sunan mijina Nabeel Lele Kuma Yana so na sadaki na million Uku ya biya amma kuyi hakuri wallah bani da kudi na bayar kyauta dubu dari biyu ce ta rage Kuma yaranka sunyi shashanci basu ce a basu ba aka bar jakar a mota yanzu da sunce kudi tun a can ai da ka samu na siyen Sigarinka ko ta kwana Uku ce irin wannan bulubawar da Naga kunayi cikin nishadi yo ai sai dai ta dubu dari biyu a kwana Uku. Sai da ya gama Jin surutun Hamida tsaf yace ke daga wanne garin kike naga alama baki San a gaban wa kike ba,da sauri tace a gaban Uncle Me Imani nake,dariya ta bashi Wai shi zata wa wayo yace kalli wancan mutanen Hamida ta juya tana kallon wasu maza da Mata siraran gaske Kamar Kashi da rai yace to mutanen can Manyan alhazawa ne masu kiba da tumbi sosai cikin sati daya Suka koma kwarangwal,Hamida ta fashe da kuka tana magiya dan Allah Yaya ka min rai Kar na koma haka mijina ya tsaneni,Baki ya bude gani ba a taba kawo mutum gabansa Yana Magana shima yana magana ba sai Yarinyar na,da alama bata da tsoro sosai mutanensa ya bawa umarni Nan take Suka dinga Jan Hamida a kasa har suka daureta a jikin wata bishiya Kamar yanda sukewa kowa haka suka daure Hamida ta ko Ina,Hamida tace sai kace goro irin wannan dauro Jin abinda ta fada wani ya taho da Niyyar dukanta sai ga wani matashin wanda fuskarsa tasha nadi idonsa Kawai ake gani ya dakatar da mutumin tare da furta ka manta banda taba lafiyarta, yace sorry oga. Abincin da suke bawa sababbin zuwa shi aka sauki Hamida da shi wato tuwon dusar masara da miyar kuka wacce ba Maggi ba gishiri sabo da zalunci wai mutum ya barke da zawo komai kibarka ka rame ka dawo duk Kashi amma babu yanda mutum zaiyi haka Hamida ta lashe tuwo sabo da yunwa,idan baka ci bama ka Sha Mari da duka,Babban Oga Yana zaune da tarin wayoyin mutane a katon buhu a gabansa tunda aka kamo Hamida yake kallonta,matarsa itace shugabar masu girki na wajen.. Hamida taci tuwo cikinta Yana ta uban kugi da rugugi duk wajen Addua kowa ke yi har dare yayi gari ya waye Hamida kwana tayi tana zawo itama har gari ya waye,masu aikin abinci suna ta fama wata Mata dauke da goyon yaro a bayanta wace ance itace matar oga wacce ya aura ta karfi ya maidata matarsa. Yaron Yana bayanta ba dai muni ba Hamida tunda take bata taba ganin yaro me munin Dan gidan ogan kidnappers ba iya tsawon rayuwarta,wata mace dake kusa da Hamida tunda ta fahimci Kamar ogan ya fiye kaunar yaron da yawa sabo da duk auren da yayi dai akan wannan yaro ya samu haihuwa shi yasa yake tsananin kaunar yaron Kamar ransa. Hamida dan yaron ta kalla ta fara masa wasa Kai dan baba,Dan yaro kana goye,Allah sarki uwar yaro da fara'a ta juyo ta kalli Hamida tare da cewa kin ganshi sai rigima,dama duk bala'in mace kana yiwa danta magana sai kaga farin cikinta, Hamida tana yiwa yaron wasa daga nesa tace kai dan kyakyawa kamoshi nan kamoshi nan....kamoshi...yan Yan Yan...yaro da shegen muni y wani bangale baki Hamida harda cewa me sunan baba nane ko Salisu ne me Sunan kakana,Mahaifiyar yaron tana faman washe baki ta matso inda Hamida take daure da goyonta tace wannan sulaimam ne, ahhh ashe Yaya nane ma shi yasa kake kyakyawa da kai cewar Hamida a ranta Kuwa tace tab tunda uwata ta kawoni duniya ma na taba ganin yaro Haka Kamar aljani Aljani mutum mutum. Ogan Yan ta'addan ne ya kalli Hamida Yana murna Yana Jin dadi ta yabi dansa shi a duniya duk Wanda ya kula yaron Nan to ya gama masa komai a rayuwa Nan take yace Kai ku kwance wannan yarinyar nan take suka kwance Hamida,sauran mutanen wajen Kuwa wasu ma sun kusa mutuwa sabo da wahalar yunwa da kishi ga duka da azaba iriri kullum da ake musu, Allah ya rufawa Hamida asiri ance a daga Mata kafa zawon tuwon dusar masara ma ya isheta data kwana yinsa. Ogan ne ya kalli Hamida yace ke daga Ina kike, Hamida tace Yar asalin wani Kauye ne dake Adamawa shine anyi bikina za a kaini Kaduna gidan Lelen Pipina ko ka sanshi ne? Dariya ta ba mutumin shi Ina zai San wani Lele,yace da yau a dinga bata abincin da mukeci da ruwa albarkacin kaunar yarona da takeyi,Hamida farin ciki ya kamata ba shiri ta mikawa matarsa Hannu Miki min shi na tayaki Reno,Matar tana farin ciki ta mikawa Hamida yaro wanda ya fara tsaiwa ma,Hamida tana Masa rawa tana yaro dan kyakyawa Yana ta dariya,Hamida tsabar neman gindin Zama yaron a hannunta yake yini,duk Yan ta'addan kowa uncle take kiransa ogansu Kuma ya koma Abba shikenan ta samu yanci a cikin wajen sai abinda taga dama takeyi mutanen dake wajen ma taimakonsu takeyi Wanda taga Yana wani Hali sai dai Matsalar Daya ba wanka ko zaka shekara dari baza kayi wanka ba Hamida gaba daya duk sunyi futu futu tsoro takeyi Kar ta fara period brush ma Sai dai su balli abin bishiya suyi aswaki ga masu tsafta. Akwai Wanda ya nade fuskarsa sai dan iya idonsa Hamida tayi ta kallonsa kamar ta sanshi ta rasa waye har ta cika kwana biyar cif a cikin dajin. Nabeeel kam sai Addua ya rame damuwa ta Masa yawa a hakan ma Dan ko yaushe a Addua yake ne shine ma yake samun dan sauki sauki,kullum wayarsa tana kusa jira yake kawai a kirashi a nemi kudin fansa ko nawane zai biya Hamida ma kullum a Addua suke ba dare ba rana,Wanda fuskarsa take a nannade shine yasa azo wajen Hamida ta bada number mijinta za a sanar Masa ya bada kudin fansa Wanda dama shine dalilin kamota,Ogan yace a'a wannan sakinta za ayi baza mu karbi kudi ba tayi min abinda babu Wanda ya taba Yi wato Bata kyamaci dana ba me nadin fuska ya fara masifa ai ba haka mukayi da Kai ba mun riga munyi kasafi nawa zaka samu nima nawa Zan samu Oga fusata yayi ba a nuna Masa yatsa nan take ogan ya mike tare da bada umarni a ladabtar da shi,Nan yaran Suka kama shi shima aka daureshi suka fara jibgarsa kamar Allah ya Aiko su yace ku cire Masa nadin nan yarinyar ta san waye mun daina rufa ma asiri,Nan take Suka fisge Masa nadin fuskar Shehu teacher din Hamida ta bayyana. Hamida tace Malam Shehu kaine dama kasa a satoni ogan yace fada Mata gaskiya ko yanzu nasa a yanke min kanka,Nan take Shehu yace wlh ni dama sana'ata kenan tunda naga Nabeel Yana sonki nasa a sace ki idan ya aureki sabo da nasan zamu samu kudi amma ainihin sana'ata kenan na kashe mutane da dama,Hamida bata Yi mamaki ba sabo da yanda taga suna kashe mutane ba Imani ba tausayi,kafin kiftawar Ido Kawai karar bindiga taga bullet ta ko Ina duk a jikin Shehu aka juye bullet din nan take yace ga garinku nan,Ogan ya kalli Hamida yace tafi gida,Hamida ta kalli gabas da Yamma ta wacce Hanya zata bi Amma haka tayi ta kanta ta dinga uban gudu a dajin nan duk uban gajiyar dake tare da ita bata ji ko hutawa bata tsaya ba a dajin ma ko Ina tafiya take bata San inda ta nufa ba tun safe har dare yayi mayafinta da takalminta duk ta watsar da su,Wasa Wasa har gari ya waye bata hango titi ba ta fashe da kuka kafafunta duk sun kumbura taji rauni a kafafunta,faduwa tayi a gindin wata bishiya ba gida gaba ba gida baya ga yunwa da kishirwa kwanciya tayi tana kallon sama tayi flat tayi kuka tayi kuka tare da tsinewa Shehu ta daga hannu sama tace Ya Allah badan hali ba Allah ka nuna min hanyar da zan fita daga dajin Nan,Allah ka kawo min agaji yunwa da kishirwa zasu kashe ni ya Rahman ka ciyar dani Mikewa tayi da kyar take taka kafarta haka taci gaba da tafiya sai data sake yini Yamma likis tana tafiya a cikin dajin sannan ta sake Zama a wata bishiya tana hawaye tana Addua tare da Kiran sunan Allah ta koma Kiran Lele,Nabeel,Yaya kyakyawa tun tana Yi ta koma papa da Yaya Sulaiman yunwa taci karfinta baza ta iya tashi ba. Tana kwance taji wasu maganganu a kanta lokacin da kyar take gani dishi dishi taga wasu mafarauta su biyu da kayan harbinsu,a hankali tace ku taimaka min sace ni akayi daga wajen Yan kidnapping Allah ya kubutar dani,ruwa Zan Sha dan Allah,Wani a ciki ya tausaya Mata yace ai kin kusa bakin titi ma tashi ga ruwa hannunta na rawa ta karbi robar ruwan da ya Miko mata ta shanye tas,dayan ma ya bata tasa robar ta karbe ta shanye,wani a ciki ya zaro fura a cikin leda da yayi guzuri da ita ya mikawa Hamida ta karbe tunda ta kafa Kai a ledar sai da ta shanye tas duk yawanta bata rage ba tace bawan Allah bazan muku Kara ba ta jefar da ledar sannan ta koma ta kwanta sai data huta sosai taji karfi a jikinta ta mike tace ku nuna min Hanya naji garau yanzu na gode wayyo naga duniya Suka ce muje sai mu saki a motar garinku,Tace na gode Suka tafi gaba dayansu tace amma dan Allah idan akwai waya a wajenku Zan Kira mijina ince na kubuta,dayan yace ki bari mu Isa bakin titi sai a Kira shi tace to suna tafiya tana basu labarin komai Basu dade ba sai gasu a gefen babban titi Hamida murna Kamar zata yi me itace a gaba tana tafiya zungwi zungwi sannan Suka zaro waya ta karba tana Murmushi ta saka number Nabeel tayi dialing lokacin Nabeel Yana kwance Yana tunanin Hamida yaji wayarsa na Kara tunaninsa jami'an tsaro ne da sauri ya daga,Hamida tana Jin muryarsa yayi sallama ta kyalkyale da dariya Kamar yana ganinta tace Lele pipinka ce na fito Allah ya kubutar dani ka ganni za a sani a motar gidanmu ayyiriri Chaka lubaye chasss gani a bakin titi kaji karar motoci ta sake tuntsurewa da dariya tana murna,Nabeel ma har wani dan ihu ya saki yace yau yau zanzo garin zanbi flight gamu Nan zuwa. Su dai Hamida dariya take basu ba takalmi ba mayafi a haka Suka sata a mota Suka biya kudin motar,dankunnen Gold dinta me tsada da Lele ya siya Mata shi ta cire a kunnenta ta mikawa mafarautan tace gashi ku siyar na baku kyauta sabo da taimakon da kuka min,kin karba sukayi Hamida ta dirgo daga motar bus tana rokonsu da kyar Suka karba sabo da sunga passengers suna jira,Hamida Yan motar sai tayata murna suke ta dinga basu labari kuwa Ana ta mamakin tabarbarewar al'umma makwafci wani baka San sana'arsa ba sai addua Hamida tace na yarda da shi sosai har sirri nake da shi ashe shima sana'arsa kenan. Nabeel Kuwa sanar da mutanensa yake Kawai Yan Uwa suna ta tayashi murna,Ammar,Mimi,Affa da Nabeel Suka bi jirgi sai Adamawa,can Dangin Hamida ana ta murna ta bayyana,tana zuwa wanka ma botiki biyar ta Kai bayi kamar zata cire fatarta da gashin kanta sai da tayi fes fes dama Allah yasa ita bata Sha wahala a hannunsu ba wahalarta daya wannan tafiyar da tayi a daji gaba Daya kafafunta a kumbure suke,bata da kayan da zata a sa a gidan duk an tafi da su gidan mijinta sai t-shirt din Ummi ta zabi karama ta saka sannan ta daura zanin atamfar Ummi ta saka wata sabuwar Hula da Ummi ke siyarwa mutanen kauyen ba karamin Kyau tayiwa Hamida ba,sallolinta ta rama ana ta zuwa tayasu murna ko abinci bata samu ta ci ba sabo da mutanen dake turuwa Yan Uwa da abokan arzuka. 5pm su Nabeel Suka iso lokacin Hamida ta saka daron abinci a gaba shinkafa da Miya ga salat dinta a wani shegen plate an toza shi ka rantse mutum uku ne zasu ci,pure water a gabanta leda guda me sanyi,Papa ya siyo Mata wasu jelar kifi soyayye ta dora a saman abincinta hannayenta ta wanke ta zauna ta fara ci kenan taji muryar su Mimi da sauri ta wani ware murya ta amsa sallamarsu Wai Dan aji ta dawo fa da gaske,Har Affa sun shigo gaba dayansu palon Hamida ta bari da sauri ta fada tsohon room dinta Wai Kar aga Kalar abincinta da shegen yawa,mayafi ta yafa ta fito da farin ciki ta durkusa suka gaisa da su Affa,ta saci kallon Nabeel Suka hada Ido ita yake ta kallo zanin ya Mata kyau dake tana da hips ga duk jikinta luwai luwai ita ba me kiba ba Kuma ramamma ba,Signa ta Masa da Ido ya saki murmushi, Affa yace Hamida Kun Sha fama Hamida ta Basu labarin komai suka dinga mamaki wai Shehu ne ma,Affa ya kalli Nabeel yace kaga abinda nake fada maka shi yasa na hanaka Kama Doctor Ahmad da yanzu munji kunya Wanda baka zato shike aikata ma wani abin,kaga dai Shehu wa ya damu da shi an manta ma da shafinsa ashe Yana cikin Yan ta'adda ba a sani ba,Mimi tace mugu bai da Kama ai wlh ai gashi nan rayuwarsa ta Kare shima dama dubunsa ce ta cika ta sanadiyyar Kama Hamida Suna ta zancen da Ummi da Papa,Ummi yanda take bada labarin Kamar itace aka sace. Hamida bedroom ta koma ta fara cin abincinta sai Ummi tace jeka wajenta Man,ai dama kadan yake jira ya mike ya shige bedroom din Hamida ko Ina neat Yana kamshin turaren wuta,tana kasa a zaune tana hada kifinta da shikafa tana ci shi dariya ma ta bashi yanda take ci Kamar zata hada da hannunta, ba Bismillah Pipi? Hamida ta kalleshi tana Murmushi tace ban dawo hayyacina bane zo muci to idan mun cinye sai a Karo wani,rabon da yaci abincin kirki tunda aka sace Hamida,Sallaya ta shimfida Masa a kasan tiles din da Papa ya musu ba dadewa duk ya gyara gidansa sosai basu da makusa tun asali gidansu me kyau ne tiles ne Kawai yayi shi ba dadewa. Zama Nabeel yayi suna facin juna ya dauki spoon din data ajiye a gefe ita yake ta faman kallo ta masa kyau ne sosai,Hamida ta tsaya da cin abincin ta shiga tambayarsa mene? nayi muni ko? Ya za ayi sai hakuri dama abinda nake ta Jin tsoro kenan Kar dan haskena ya dishe dama yaya abin yake,mazan yanzu Kunfi son kuga mace ta kashe titi da haske to ni kaga dama ba Fara bace irin kal kal na Sha wahala dole na dan hasken ya ragu amma sai ni naga da haske na ma. Murmushi yayi ba shiri yace kyau Kika Yi wlh ban taba ganinki da single zani ba sai ya Miki kyau dake kina da shape rigar ma ta Miki cif cif masha'allah,Hamida tayi dan Murmushinta me kyau duk kunyarsa takeji ganin yanda ya kafe kirjinta da kallo ta sake kallonsa karo na biyu tace ya akayi da alama Naja'atu ta fara lafiya ko?ai kin san dokar sai Nan da 4months fa sannan Zan iya wani abu,Hamida tace ango ba harka ba shiri ya furta wlh karya kike kullum sai na latseki,Hamida ta rufe fuska ya fuske ya fara cin abincinsa yace ban son gulma kici abinci, Bude fuskarta tayi ta dankaleshi tace Lele me gemun gayu da saje,ke dai ki shafa idan zaki shafa da alama birgeki yake ki daina wani kinibibi cewar Nabeel Hamida tace to Miko fuskar ya matso Kuwa ba musu ta wani sa yatsa ta dan dangwala tace haduwa dariya ya saki yace zanga ranar da zaki daina shirme yazu da yatsa shine har kin shafa har kin san ya hadu.. Hamida tace Lele Nasha mari fa a wajen ogansu kin fadawa su Mimi nayi,Lele ya bata rai tare da furta Allah ya Isa,Hamida tace cewa yayi fa ya sunana ai dai kasan nace na canja suna ko? Nabeel yace yes,tace sai nace Shakira kafin na rufe baki kaji wani uban mari Kai Lele duk Adamawa nasan baza a samu me iya Marin wannan ogan ba,sai da jiri ya kwashe Ni ba shiri na dawo Hamidata,Nabeel yayi dariya yace maganinki kenan,kaga tuwon dusar masarar nan dana ci kwana nayi Ina zawo kaga Kuwa wajen da ake bahaya tab gashi ana tsaye a kanka da bindiga Ni dai da dabara nake ko fitsari ne,Nabeel yace Allah yasa dai baki bude...kafin ya karasa tace Duwawu ai da dabara nake dan satile pant na dan rufe da rigar,Naga duniya nidai Allah ya shiryeni gaskiya na koma ga Alla. Nabeel yana ta dariya,tace ai Kai kasan kanka Lele na shiryu pipinka ta nutsu da ace a baya ne ai da tuni a gaban su Affa Zan baje zancen duwaiwai amma kaga Kai kadai na fadawa Kai dinma dan na taba ganin naka ne shi yasa nake iya fada ma,Nabeel yace baki ganta ba sai nan gaba Zaki ganta,Hamida tace Fara ce na ganta tun yaushe Ina ta kallonta Sanda kana min abun nan,muci abinci ban son zancen abin Nan da mukayi Ina nadama,suna ta cin abinci itace ke cire Masa kayar kinfin tana sa Masa a gabansa Yana ci,idan salat ya Kare ta zuba masa suna dan hira sama sama,tace kalli kafata ya kalla ta tasa sosai yace sorry,tace Ni ban son Sorry din nan na bature sai naji Kamar ni ba a tausaya min, sannu to cewar Nabeel tace yawwa tana ta faman shagwaba tana kwabe fuska har Suka gama cinyewa tas taje ta Mike zata Karo yabi mazaunanta da kallo taje ta dawo kadan suka rage a abincin. Su Mimi suna tsakar gida kasan bishiya suna cin nasu abincin su Hamida Suka fito ta dakko musu sabulu Suka wanke hannayensu Suka koma ciki ya Mika Mata mint chewgum shima yasa daya a bakinsa ta kwanta a saman bed Yana gefen bed din a zaune tace marata ke ciwo sama sama, maybe period zakiyi cewar Lele Hamida tace haka ne ma,Hannunsa ya daura saman mararta Yana shafa Mata a hankali ta lumshe Ido tana Jin sauki sauki sai ya Shiga latsa cikin ta fara dariya tare da buge hannunsa tace bana so kana so a kamamu ace wani abu muke,yace Ni rabon dana tabaki tun Sanda tsautsayi ya faru sai ki ta min wayo,hannunsa ta kamo tace karasa kwashe dadinka ka huta tunda baka San adani ba. Dariya yayi ba shiri Albarkatun kirjinta dake tsone Masa Ido su ya fara shafawa Hamida ta mike zaune tace a gidan surukan naka ni bazan yarda ba yace to kizo mu tafi dake gida Kinga kin huta,idan Mimi ko Affa sunce sai na bik....bakinsa taji cikin nata Hamida ta fisge bakinta da kyar tace Naja'atu bata da lafiya zaka jawowa kanka ai yanzu dangerous ne a wajenka wannan wajejen ba abin ka kulasu bane,Nabeel yace Zaki sani ne yarinya lokacin nake jira sau biyar sai hudu kullum, fuskarta ta da danne da pillow yanda bazai ji ba tace Iskanci dadi Lele ya Zama nawa ahayye sai ma na sake zama wise a lokacin ne zan nunawa Lele ni din special ce. Nabeel yaji tana ta wani kuskus bai San me take cewa ba,pillow din ya fisge suka hada Ido tace ta Fara dariya tana wani kunya,me kike cewa? Ya tambaya, Tace ba komai cewa nayi alasittiri bukwi . Afwan jiya banyi posting ba. Masu Sharhi kullum Ina Miko gaisuwa AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 26-30 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Aimana Haruna Djamila Anty Nice Mamazee Princess khadija Mummy NEEMRAH Ummu Sharhabeel Ammin Samha Farida Yusuf Bashir Rahmat Saed WasilaIbrahim Maimuna Umar Heendu Hamida ce ta Mike tsaye ta gaji da halin Nabeel na tabe tabensa,Muryar papa Suka ji yace ke Hamida fito ku tafi dakin mijinki,Hamida ta zaro Ido tace papa a Hanya fa aka sace ni Yan Kai Amarya basu karasa dani gidan ba ai nayi tunanin sai an sake harhado Kan dangi a sake tafiya dani,Ummi tana ji tace ji sakarai Yan Kai Amaryar da sai da Suka karasa har Kaduna kwanansu daya Suka dawo sannan Zaki ce sai an sake kirasu sun tafi dake can din bakonki ne ko Nabeel bakon ki ne? Hamida ta turo lips tare da furta to azo a maidani dai dai inda aka saceni sai a daukeni a can ayi reverse a dawo baya, Papa yace ai ke Kam Naga Sanda zaki Zama mutum,Hamida kallon Nabeel tayi taga Yana lumshe Ido zaiyi bacci ta girgiza shi tace tashi Lele har kasa gabana ya Fadi yanda ake mutuwar Nan ta fuji'a haka Rannan wani daga kishingida ya wuce tashi gaskiya. Dariya ta ba Lele ya gaji shi Kam,Mimice ta shigo tace ku fito mu tafi Mana flight zai wuce mu,Hamida da sauri tace to amma dake su Papa ne ta raina su,Ummi tana mamakin canjin Hamida wai Hamida ke biyayyar suruka har a fada Mata taji ba tijara ba rashin kunya,Lele ya za ayi ban dau wanka ba Zan shiga jirki Kar a rainani mutane suyi zaton ma Yar aikice wasu masu kudin Suka zo da ita daga wani garin,Dariya Nabeel yayi yace sa hijab har kasa sai mu tafi, haka ta saka hijab din Karima data manta shi a gida me Hannu har kasa yake ja,Nabeel yace Kamar zamu tafi da'awa Suka fito Hamida ta musu sallama,Ammar ya fito daga wajen Sulaiman yau rana ta farko Pipi za a Shiga jirgi,motar airport data kawo su ita ta maidasu suna zuwa airport ba bata lokaci suka shiga jirgi Hamida tayi Shuru bayan tayi Addua... Nabeel fuskarta ya leka yaga bata kulashi ba duk surutunta yace madam lfy? Hannu ta taga Masa baza tayi magana ba sai idan sun sauka lafiya,Dariya taba su Mimi,Ammar dake bayansu yace Amarya? tayi shuru suna Dariya har su Mimi,Ammar yana tsokanarta Amarya ba magana a hankali tace da Nabeel ka amsa min Lele,Ammar ya sake cewa Amarya a kawo Miki juice? Nabeel ya makale murya yayi irin ta Hamida yace ae a kawo,Mimi tace Allah ya shirye ku,Affa yace manyan banza kun dami yarinya ku kuke Yi amma ni nake jiye muku kunya,Hamida dai bata ce kala ba har aka sauka daga jirgi sai data sakko sannan tace Alhmdllh Driver ne ya daukesu ya wuce gidan Affa a kofar gate ya sauke Affa da Mimi yaja Nabeel da Amaryarsa zuwa gidansa Wanda ya gaji da haduwa komai sabo aka canja masu tsada,Driver yayi parking ta hango motocin Nabeel harda wasu sababbi ta kalle shi kawai a ranta tace Wai ni da ba komai ba a garinmu ana min Dariya ana min kallon mahaukaciya babu saurayin da ya taba cewa Yana so na ko da Wasa yau gashi nice Allah ya daga martaba ta,Wanda Kuma Suka fini ilimi da farin jini Ana ganin sunfi kowa basu samu irin mijina ba ko a nan na godewa Allah,Nabeel ne ya fita a motar tare da Bude mata ta fito ya maida ya rufe driver yaja mota ya tafi dama motar Affa ce. A Palo ta zauna saman wata luntsumemiyar kujera ta harde kafa tana Shan ac,Nabeel ya haura sama yaje har yayi wanka ya shirya yaga baiga Hamida ta shigo ba sake fitowa yayi ya hangota tana maganganu ita kadai,kunne ya bude yaji tana cewa shike Nan ya Zama gidana yau sai kaji Ina bada address,inama za a dawo min da Sale me gadi da sai na kusa karasa shi da aiki ba irin Maganar da baice min ba ta wulakanci,gashi na koma Auntynsa dole bari na Kama kasa sai na mulki Sale Kizo kiyi wanka ko sai nazo na daukeki Hamida mikewa tayi ta wani fuske ta wuce shi yace Bari inje masallaci, okay ta furta tayi sama dama gidan ba bakonta bane,bedroom ta zaba dama ta rigada tasan na ogan duk da cewar an canja komai na gidan,Dakin data ciki ta karewa kallo ya gaji da tsaruwa mamaki tayi ganin akwatuna guda takwas da alama na lefe ne,tana mamaki yaushe aka siya mata,wanka ta Shiga ta Dade ciki kafin ta fito tayi Sallah,taga har mudubi an shirya mata ta tuna su Ihalsan sunce sun shirya Mata komai a bedroom kafin a sace ta,Body lotion ta kalla da gani kasan me tsada ne ga kamshi Zama tayi tare da shafe jikinta da man sannan ta zauna a gaban mirror daure da towel fari ta gyara dogon gashinta sosai sannan ta Mike tana bude akwatuna daya bayan daya kayan sawa ne iri iri ga kayan makeup,wata sabuwar Atamfa ta zabo brown and Golden dinkin Riga da skert ta saka abinta sun amsheta sosai ta zuba kyau matuka,ta coka dauri jelar gashin data tufke tana reto a bayanta tayi kyau sosai da sosai ta kalli kanta a mudubi tana wani juye juye ta furta gaskiya ban yarda ba zai wahala ba daga kasar Ethiopia Muka samo asali ba,ba Yar Nigeria bace Ni daga kasar waje iyayenmu suka zo aka haife mu a nan na sani ma,tana shafa turaruka Nabeel ya bude kofarta tare da shigowa bedroom din,yaga yanda ta dawo wata balarabiya yace sai kace a Ethiopia,Hamida ta juyo da sauri tace ya akayi kasan asalinmu ko Papa ne ya baka tarihinmu Ni Kuwa ce min yayi dukkan zuriyarmu yan kauyen Adamawa ne Wai Yan Fulani amma da yawan tsofaffin dangin namu sun rasu kasan yanzu duniya ba a dadewa duk dangin mu Papa ne Babba yanzu,ba a dade da haifata ba iyayena Suka rasu ance ma kamar da madara aka raineni so sad ace ni Yar Nigeria ce gashi kaima ka fada. Murmushi Lele ya saki yace ke Yar Nan ce muma Nigeria ai suna da masu kyau amma mu Kinga Yan asalin kasar Murtania ne a Nan Yankin Africa,Hamida tace wanne irin son Kaine haka ta Ina kuke Yan can ni taya za a kalleni a ajiyeni a Nigeria kai kace Yan kasar waje ne,Yanda ta dage da gaske shi ya bawa Lele mamaki, Rungumeta yayi tare da janta saman bed,Hamida ta zille tace bana son wasan Kan gado Ni dai Naja'atun nan kasan ba lafiya take ba so kake wani Abu ya faru ace nice bana kula da ita,kasan ni ba budurwa bace ko ya ka dan yo abu akwai damuwa. To yanzu Ni Zan kula da abata ko ke? Hamida tace tunda na Zama matarka ai ya Zama dole na dinga kula da shige da ficenta,Nabeel yasha dariya Kamar me shi Kam yaga ta kansa da Amarya,Kirjinta ya kalla yace to ko Nan Banda shi Hamida ta kalli kirjinta tace Wai gorar madara? Nabeel tana fada shi Kam kofa ya Bude yayi waje Yana ta dariya ya rasa inda take samo sunaye yanzu nonuwa ne Gora zai ga ranar da Hamida zata saitu da shegen surutu. Fitowa tayi tana sakkowa daga step Yana kokarin canja Chanel,Wuce shi tayi ta nufi kitchen ta duba komai akwai ta bude fridge lemuka iri iri ta dakko wata watermalone ta yanka abarta ta dau sanyi ta hada a wani juck ta zuba Madara a ciki Nan take ta shanye a barta,tana ciki tana ta hade haden tsuminta da kanta tana shanyewa daga ance tana yawan Sha sai da ta Gama ta fito dauke da ruwan roba da glass cup ta ajiye a gaban Lele tace kaga Sha irin naka,hadin da na Sha na manyan Yara ne,Lele yace to yanzu idan ba karamin yaron ta ya zakiyi kenan? Ki daina Sha fa harda wani shaye shayen kankana kinga dai ba lafiya ce da Ni ba idan kin birkice me Zan miki? Hamida tace Ina da juriya ai ka kyaleni lafiya nake karawa Ni ba maganin Mata na Sha ba kankana ce Kawai da Madara Kuma kowa Yana Sha,Nabeel yace to ai zamu gani ki dai sani ke ba virgin bace bare ki iya daurewa ba ruwana. Mikewa yayi da Niyyar fita dake yanzu babu kowa a gidan Hamida ta mike tare da kwabe Fuska zata Yi kuka tace Dan Allah kaje dani wlh tsoro nake ji yanzu Zan dawo abinci Zan siyo mana,kaje dani dan Allah,taya zan tafi da Amarya guda a kalle min ke tun ban kwashi harka ba,ki zauna ba abinda zai faru Inshaallah,yace Zo muje ki kulle ko Ina idan na dawo Zan kiraki sai ki bude min tace to. Hannunta ya rike Suka fito har compound ya Bude gate da Kansa sannan ya shiga wata bakar motarsa ya fita Hamida tana gefe tana kallonsa ta karasa da Niyyar kulle gate din ya fito da sauri Yana ce Mata no barshi Zan rufe karamar kofar Kawai Zaki kulle ta ciki,Hamida tace to ta kulle,ta jikin gate din yace kin kulle? tace ae,sosai? tace yes ya murmusa sannan ya Shiga mota ya tafi ita Kuma ciki ta koma tare da ci gaba da kallon tv ta kafe katuwar plasma da kallo ana ta labarai Israel suna ta harba makamin nuclear a BBC, Hamida tana ta kallo harda Karo Vulume bayan ba turancin da take ganewa sosai,taga an nuno wani dattijo ana ta fadan sunansa wani katon kafiri Lelgarz,Hamida bata ji sosai ba ta zaci Lele aka Kira,Zama ta gyara tare da cewa abin nayi ne harda takwaran Lelena a ciki ci ubansu me Sunan Lele ta manta ma da wani tsoro sai horn taji lokacin Kuma ta tuna da tsoronta ta fito da sauri ta tsaya a bakin gate tace waye? Nabeel Yana sani ya tsoratata yace Shehu ne daga lahira. Hamida ta kwalla ihu zata zura da gudu Nabeel ya saki Dariya ya dawo da muryarsa dai dai yace nine fa Lelen Pipi,Kofa ta bude da sauri ta saki fuska,Shigowa yayi tare da bude gate din ya shigo da motar ya fito da ledoji a hannunsa,Hamida tana tsaye a jikin motar ta karba ledojin ya fito tare da kulle motar tana gaba Yana bayanta Yana karewa duwawu kallo sunanta ya kira wai Duwas,Dariya ta kama Hamida tace Ni dai Duwai nace ba Duwas ba,Nabeel yace ai style nayi wannan irin Kaya haka ai sai da style,kunya ta Kama Hamida tace gaskiya wuce gaba tunda abin naka haka ne,gabansa ya dawo da ita har Suka shiga palo Suka fara bin steps ya rike hips dinta suna tafiya cas cas Yana sani yace na warke yau zamu sake Jin dadinmu,Hamida tace uhm Kaine zaka kasa haihuwa ka dai ji me doctor yace. Bedroom dinsa ya jata suka shiga ya baje mata su kaji,Hamida ta kalleshi tace me yasa ka siyo min kajin amare bayan ba fanshewa zakayi ba,Nabeel yace Zaki ga ta inda Zan fashe ne ai,Hamida ta kalleshi da idanunta masu kyau dara dara tace Indai zaka jawo Naja'atu ta Kara kwailaye to bazan kwana dakin Nan ba kasan dai ko a bed daya muka kwanta Naja zata ce bata San zance ba Kawai muyi hakuri har lokaci ya cika,Nabeel ya kalleta yace to gorar madarar fa? shike nan ai dai ko ruwa na Sha ko,Hamida tayi Shuru bata ce komai ba taji Lele ya fita fitsara Abincin ya fara ci Yana bata a baki itama tana ci Suka ci suka Sha sannan ta Mike tare da cewa Ina zuwa idan baki dawo ba ma zanzo da kaina na dakko ki cewar Nabeel. Brush tayi sannan tayi Shirin bacci cikin wata Nighty sky Yar Riga ce silk me hannun bra bata da ado a jiki tasa hula Kalar rigar me kyau tana kamshi ta tsaya jona Wayarta sai ga Ango har ya shigo sanye cikin wadu pjms arsh Riga karama da wandonta iya gwiwa ya sheka kyau Daukanta yayi cak yayi zaton baza ta yarda su kwana tare ba sai yaji bata ce komai ba,Saman bed ya kwantar da ita ta sakalo wuyansa da hanyenta tare da cewa Yaya Kara Yi min,kwanciya yayi a gefenta Yana Jan hancinta gwiwar hannunsa tana gugan Albarkatun kirjinta Hamida taji wani muguwar Sha'awa lokaci guda,Dan dannewa takeyi bata so ya gane,ya naji bakin ya fara mutuwa ya furta, wayancewa tayi tace bacci zanyi ,Samanta ya Haye a hankali ya Mata rufa ya Sata a tsakiya ya fara kissing dinta cikin salo,Hamida ta lumshe Ido tare da yin kasa da kanta gaba daya,tunawa tayi zai ganota sai ta sake fuskewa tana tureshi ko motsi baiyi ba yaci gaba da abinda yake ta fara shidewa tana dan kokorin fuskewa amma nema yake ya kure hakurinta,wuyanta ya gangaro ta daga kanta sama tana Mika Masa wuyan har ya gangaro kirjinta Nan Hamida abi ya gagareta tun tana Jin kunya Har ta fara ragewa a hankali yace ki bari kiji Dadi ki daina Jin kunya ta,Hamida tonawa kanta asiri tayi tace haka kawai kace bana Jin kunya Banda kunya Ni dama karfin hali nakeyi amma gwara nayi kunyar tunda Papa yace na dinga kunya Ina kawaici Ina danne abubuwa shi yasa nake yi amma ni dama kasan Watarana ba kunya gareni ba,Nabeel yayi dariya kamar me yace mamaki yake ace 21yrs Hamida take duk da cewar ana samun Wanda Suka girmeta ma wasu daban kafin su canja sai ansha fama,Baki Jin dadi ko kina Jin dadi ko na daina? Hamida tace eiiii to Allah dai ya gani bazan karya ba sai dai kayi hakuri Ina Jin dadi Naci gaba kenan ya tambaya?Yana tsokanarta tace ba a baki na ba,nidai baza aji mutuwar sarki a bakina ba idan kaci gaba to maraba idan ka fasa to wannan kuma,Nabeel yace Zaki kasheni da d Pipi ki daina Jin kunyata wlh Ni bana sonta,kafi son rashin kunyar tawa? Yace ae amma iya Ni dake Kamar yanda bakya boye min komai haka Ni nake so,Haka na ganki Ina so to Haka nake so ba kunya tsakaninmu iya Ni da ke amma a gari ko na saka ki a school ki Zama me kunya amma idan kin dawo gida ni da ke ba kunya, Hamida tace ko maganar komai ce nayi? Yace yes,idan naji Ina son wannan latse latsen fa? Yace shima ki fada min Ni dake ko a school Kika ji kina so kina dawowa ki fada min,Hamida ta rufe fuska tana jin Dadi tace tace ahhhh Freedom zalla,Nabeel Yana Dariya yace Allah yasa kije school kina cewa ahayee su rainaki,Hauka nake nafa waye,to aci gaba? Hamida shiga furta ae- a'a ae-a'a mene ae a'a bana ce banda kunya ba,da sauri tace to ae ta juya baya tare da kulle idonta ta Shige blancket tare da dukunkunewa a ciki sabo da kunya Fincike blanket din yayi yace jibi Zaki Fara zuwa school,sabo da Ina da aiki Zan Zama busy sosai driver zaina kaiki ya dakko ki,Tace to Allah ya kaimu,idan na dawo gida zan na Miki lesson,Da Yamma kullum sai kinje Islamiyya tace to girkinfa? Sai kin dawo Zaki dinga mana da rana Zan na ci a eatery tam ta furta,Zan mawo Miki me aiki, kwanciya yayi suna facing juna da wayo yake tattabeta tana jin abin a jikinta sosai tana kallo ya rabata da Yar rigar tata,Kirjinta da suke a cike bulbul Yan charas da su yace sai kace alkubus,Ganin tana ta Jin kunya ta kasa sukuni sai ya kashe light din taga duhu sosai duk da haka kasa sakin jiki tayi taki yarda. Ganin ta maida rigarta yaleta yayi Kawai ya rungumeta bata ko magana har bacci ya kwashe su Yau kadan akayi AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 31-35 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Hajjora Investment Oum Nu'aima Khadija Saleh Safiyya Nabebe Ummi Deejat Ummu Najwa Hamida bacci yayi Dadi duk ba a sani ba ta juyo ta manne a jikinsa Nabeel ya farka sai ya janye Blanket din a hankali ya jawo remote din ac ya Karo karfinta Hamida a hankali taji sanyi Yana shigarta ta koma jikin Nabeel inda take Jin dumi ta makalkale shi, tabarakallah Nabeel ya furta a hankali ya maida hannayensa saman Mazaunanta yana shafawa sai kace maye bazai bacci ba, Hamida bata San me ake mata ba,rigarta ya janye sama sosai gorar Madara suka fito yaci gaba da latsasu yanda baza ta farka ba,Hamida ta sake yin juyi ta baje Nabeel ya zura hannunsa ta kasan bayanta a hankali ya birkitota ta dawo samansa ya manneta a jikinsa yana shakar kamshin jikinta tsabar yanda yake shafa Mazaunanta Hamida sai data dan farka ta bude idonta kadan cikin magagin bacci tace Lele ana taba ma abinka,Nabeel ya wani sake kankameta tare da rada Mata me abun ne da kansa bata San ma yanayi ba haka ya raba dare yaki bacci,sai daga baya ya fara bacci ba tare daya shirya ba. Da asubar fari Hamida ta rigashi farkawa bata San me yayi ba tana bude Ido ta ganta sintir a jikinsa ta dinga mamaki it tasan da riga tayi bacci Nabeel ta kalla Wanda ke bacci hankali kwance,blanket din ta fisge ta ganshi ba Kaya tayi sauri ta rufe Masa jikinsa,wata dabara ce ta Fado mata a hankali ta leka da kanta cikin bargon tana kokawa ya zatayi taga Naja'atu ta Kare Mata kallo bai sani ba amma duhu yayi yawa alamun farkawa taji ta fito da kanta da sauri tana murza ido irin yanzu ta tashi, shi kuwa tun sanda ta farka ya farka shima Yana kallonta Dariya ma ta bashi. Ganin Kamar ya kamata tayi sauri ta gyara rigarta ta bar dakin zuwa nata bedroom din,brush ta farayi ta daura alwala ta fito tare da gabatar da Sallah tana saman Sallaya tana azkhar abinta shi Kuwa sabo da ba baiyi bacci da wuri ba ko masallaci kasa fita yayi yana idar da Sallah ya koma bacci,Hamida Kuwa gyaran gidan ta hau yi ko Ina duk da ba dirty haka ta maida shi Yana kyalli har toilet dinsa da bedroom ta gyara saman bed din ne Kawai Bata gyara ba sabo da bacci yake wanka tayi ta cakare cikin wani material red tayi kyau matuka dinkin doguwar Riga ta zamani kitchen ta shiga ta duba ba dankali,doya da kwai ta soya ta tafasa ruwan shayi lafiyayye Yana ta zuba kamshi,kazar jiya da suka rage tayi warming ta shirya dining tsaf sannan ta gyara kwalliyarta tana Fitowa Nabeel shima ya fito abinsa sanye cikin kana nan Kaya na Shan Iska sun Masa kyau matuka white and Silver. Murmushi Suka sakarwa juna yace bari na Kira Mimi a aiko Mana da breakfast,Hamida ta kalleshi ta koma gabansa ta tsaya tare da gyara Masa rigarsa da dan wajen wuyan ya nannade tace nayi ai no need a Kira mimi, Nabeel yace inye Wai duk a wajen Shehu Kika iya kalmomin Nan? Hamida tayi fari da Ido tace zauna ka gani Pipinka tayi nisa,daukanta yayi cak Suka nufi Dining ya zaunar da ita shima ya zauna ya zaro wayarsa Yana latsawa Hamida tana gama Serving a plate daya ta zuba tea din ma a cup daya ta hada yace bana Shan Madara kin manta? Hamida ta kalleshi fadar likita ce? Yace no bana son nayi kiba,Hamida tace Kai in zaka ci dadinda kaci kiba zuwa ce idan lokacinta yayi sai kayi sai kasha Madara so nake kafin Naja'atu ta warke ka tara kokon maza da yawa mu samu Baby, yldariya yayi yace gaskiya kin kaskantar damu Mene wani kokon maza ai gwara kice Madara muma, ance salty taste ne inji Karima ya baza ace koko ba,Allah ya kaimu yarinya wlh sai na dinke bakinki Naga karshen surutu,ganin da Sauran watanni ta dinga kuri suna cin abinci har Suka gama ya mike yace bari naje na gaida su Mimi daga Nan Zan karbo Uniform dinki da komai gobe sai school,Hamida zatayi kuka tace wallahi dan dai mutane sun damu da boko ne Indai baka yi ba Kai gara ne wallahi da bazanyi ba bana son makaranta a rayuwata,Hakuri zakiyi kinji Pipin Lele ni idan Kuma Kika sake wlh primary Zan saka ki cikin yara gwara ma kiyi karatu kafin wata hudu a Nemo Baby. Rakashi tayi zai Shiga mota ya hugging nata sosai tare da kissing lips dinta yace zan dawo yanzu a dawo lfy ta furta tare da bude Masa mota ya shiga ta bude Masa gate ya ja motar zai fita glass ya sauke tare da furta Shakira Zan wuce,Murmushi tayi fararen hakoranta suka bayyana hannunsa ya miko Mata ta window ta ta dan matsa tare da saka nata cikin nasa yace me Zan siyo Miki? Naman balbela murmushi ya saki ya wuce abinsa sannan ta rufe gate ta koma ciki,kwanikan ta kwashe tare da gyara inda ya baci ta zauna tana kallon wakokin Hausa kasa kasa take Jin maganganun mutane tsoro taji bayan tasan ta kulle ko ina,tv din ta kashe gaba daya sai ta tsinci karar tafiya tana Jin wasu sautukan maganganun garada a gidan suna cewa me gidan ya fita ta Ina ake Shiga ciki ne, yace ga kofar can naga wacce muke nema bai fita da matar tasa ba, Hamida a hankali ta ajiye remota tayi maza ta haura sama ta shiga wani bedroom ta Shige cikin toilet jiki na bari ta Kira Nabeel Yana dagawa yaji muryarta na rawa tana kuka kasa kasa tace kayi sauri Yan daba ne da safen Allah zasu kashe ni wlh gasu Nan da makamai na kulle kaina Ina toilet kayi sauri wayyo Allah. Yi Shuru gani nan Zan taho da Yan Sanda,ba shiri ya Kira police ya sanar musu sannan Suka taho gaba daya gidan da jiniyarsu,Yan daban suna kokarin bude Palo sai Suka ji jiniyar Yan Sanda da gudu suka haure katanga suka bar gidan ba tare da an Kama ko daya cikinsu ba,Hamida Allah yasa dakakkiya ce muryar Nabeel taji Yana kwala Mata Kira pipi fito sun gudu da sauri ta Bude kofa ta fito tare da fadawa jikinsa ta kankameshi ta saki sabon kuka jikinta na Bari tace shike Nan Ni Kuma sai ta Allah maybe Basma zanbi Kamar yanda aka kasheta, Inshaallah ba abinda zai sameki,Yan Sanda ne suke ta daukan report sannan yace su bashi securities masu kula da gidan suka gama komai sannan hankalin Hamida ya kwanta. Mimi ya yiwa waya a turo Masa me aiki mace daya wacce zata dinga taya Hamida zama a ranar Kuma aka turo wata Yar dattijuwa Habiba, Uniform dinta da duk wani kayan makaranta ya kawowa Hamida,girki ma yace Habiba ta dinga Yi tare da securities nasa Kuma Hamida ce zata na Masa. Da dare bayan sunyi Shirin bacci tea ta hado Masa ta kawo yana kwance Yana latsa waya,Wayar ta karba ta ajiye gefe tace ga tea ba lokacin waya bane yanzu Murmushi yayi yace yaushe Kika koyi kula da Miji Haka? Me ka maidani ba abinda ban iya ba Kawai sa kaina ne banyi ba Kuma bayan haka karka manta shekarar hankalina ce ta kama, kallo yake kare Mata na musamman anya zai iya bin dokar wani likita baya ga Naja'atunsa Yana jinta lafiya kalau Kawai mace take bukata,tunanin me kake yi Haka? Nabeel ya kalleta da sha'awa yace bazan iya jira har 4mnths ba wlh nifa lafiya nake ji na taba kiji,Hamida taji wata kunya tana daga zaune a gabansa ta jawo bargon duka ta kifawa kanta ta ciki ta Miko hannunta waje Wai to muji,Dariya ta bashi Yana kokarin janye bargon ta fada kirjinsa Wanda ba Riga a jikinsa sai dan short taji wani laushi sumul sumul sai kamshi yake,rada ta Masa a kunne bugawa likita waya kaji zaka iya dan rage zafi banda sex, da sauri yace ai yace Zan iya Yi ma yanzu,ba wani gaskiya baza a karya doka ba,Nabeel yace Wai da lafiyata a Raina min hankali ko so kike naci babu? Lele ka dinga alkinta abar nan Kar a samu matsala ka Kira doctor aji,Nabeel ya jawo wayarsa dama Yana da number likitan,Yana Kira bugu biyu ya daga cikin harshen turanci ya tambaya likita yace a'a sai Nan gaba lokaci baiyi ba,yace Romancing fa Likita yace wannan ba matsala amma Kar a zurfafa, duk da haka yayi mamaki da Nabeel ke sha'awa sabo da masu irin case dinsa wasu sai su kwashe shekaru ma basa sha'awar ya mace,Nabeel yace wai banda sex,Hamida ta furta Eyya ango ba harka tana kwance a kirjinsa tana shafa gemunsa ga yanda ya fuskanceta bukata take,zaunar da ita yayi a tsakiyar bed din tana sake like Masa a jiki,light ya kashe tana ta wani gulma Wai kunya Yana Fara kissing bakinta bata Sanda ta fara maida Masa martani ba. Hamida ta wani runtse idon kunya dan nishin ma dannewa takeyi bata yi,Nabeel yace ke bakya Jin dadi ne? ta ya Nabeel Guda Yana abu kamar bakya ji karki sa nacewa kaina ban hadu ba na daina to tunda bakya so,Hamida ta fara jin Dadi ya daina gashi sha'awarta ta motsa murya na rawa tace ai dai kace ko Mene nace Ina so Kar naji kunya ko? Nabeel yace ae ni bana son wannan kunyar na fada Miki zamuyi fada da wacce fitsara ce bakya cewa a haka na ganki Ina so sabo da kaso mutum a halin da yake shine so ba Wai sai kaga mutum da wayewarsa ba ko wata kwalliya ko wani Abu kaso mutum dan Allah shine so,da ace kyale kyale nake bi sai na Bari sai kin waye sai nace Ina sonki wannan Kuma ba shine so ba,a yanda na ganki haka nake sonki nace yanzu Ni kadai Zaki na na wa rashin kunyar ki fada ko Mene Indai daga ni sai Kaine,Hamida tace to ai Watarana ban San me yasa ba gashi Ina so Amma sai naji kunyarka,yace okay Nan gaba sai na auro wata wacce zata na min karuwanci a bedroom ke kiyi ta kunyarki,Hamida Kamar zatayi kuka tace Lele karuwa Kuma? Yes karuwa ko mene ko so kike na waje su dinga birgeni,Hamida tasa yatsa a baki tana tsotsa tare da cewa dama Karima tace na dinga tarairayarka,Tace ko ba daidai ka min ba Wai na saka ka a daki na rungumeka Wai Nawa kake a wajena Ni dai Naga gaka da girma amma ace nawa kake Wai na dinga tallafakarka na fada ma fari da baki,Nabeel yayi dariya ba shiri yace to naji a dinga min sai me? Sakina tace na dinga ma rada sai kace munafuka,to ai kin dade kina min radar duk abinda Suka fada kinyi sau nawa kece baki san kin iya ba,bangaren sex fa basu koya Miki ba?Hamida ta sani amma sai tace basu koya min ba a wajenka Zan koya,yace to naji last warning bana son kunya ko Mene ki fada, to now kin bata min rai na fasa jiyar dake dadin,Hamida ance ta dinga tallafe Miji tana Masa rada ta koma ta bayansa ta kwanto dashi jikinta tallafewa kenan rada ta masa tace fadan ya fara aiki tace aci gaba da dadi baka ji ba na fara jikewa,tsigar jikin Nabeel ta tashi yarrrrr yace nifa bazan iya bin dokar likita ba,Hamida tace to kaji shi yasa nake kin yin abu sabo da haka, to naji bazanyi ba karki daina,Gorar Madara yaji suna sukan gadon bayansa,Hamida ita kanta so takeyi janyota yayi ta dawo gabansa wuyanta ya Shiga kissing Yana shafa gashinta pipi ta jawo hannayensa dan munafunci ta dora a wuyanta alhalin ba Nan take so ya tsaya ba,Nabeel Yana sani yace Nan? Yaci gaba da shafe sambalin wuyanta Yana dariyar mugunta a ransa Wanda ita ba Nan take so ba,Kamar ta Masa masifa haka taji, kirjinta take turo Masa kamar bai gani ba,hannayensa ta jawo ta maida saman kirjinta tace idan anyi magana kuce ku kunyi nisa a wayewa alhalin ko kwanar shagari baku je ba. Yace ai ban San Nan kike so a taba ba Hamida tace kana sani fitsara kake so Kawai na fada, Dariya ta bashi yace sorry muy Shakira kece ai kike ta bani dariya ya tsaya da tabawa tace Wai kai Indai zakayi magana duk abinda kakeyi sai ka tsaya wlh da lalle kake zanawa bazan zo ba sabo da baza ka taba sauri ba sai kana cikin zanawa ana Hira ka tsaya da zanawa ka dinga magana,daina tsokanarta yayi yaga tayi nisa da yawa sosai ya bada amanna Yana shansu Hamida ta wani gantsare Kamar zata cinye masa baki ta huta tana ta wani nishin sweet sai da ya Mata sosai sannan ya bajeta ya koma dausayi wasanni yake Mata masu wahalar furtawa Hamida tana kukan dadi tana Kiran sunansa Lelen Kamshi..Lelen dadi....Zan. Mutu Hankalin Lele ya tashi yace Ina dole yau sai yayi xxx Hamida dake ta gama Jin dadinta sai ta gudu ta koma kasa,Nabeel ya bita ta zille ya haukace gaba daya sai toilet ta Shige ta kulle yayi lallashin duniya taki budewa haka ya kwanta Yana murkususu ya mike da kyar yasha maganinsa ya kwanta sai a hankali ya dawo normal bacci yayi gaba da shi sannan Hamida ta fito Sadaf Sadaf ta maida rigarta ta kwanta a can karshen gado ai tana kwanciya Nabeel ya farka sai kace wani robot har zata gudu yace ba abinda Zanyi matso komawa tayi ta Shige jikinsa ram ya riketa yace to ki tsaya ya fiye Miki mutunci kuka ta saki tace kana ji doctor yace baza mu iya haihuwa ba Indai ba abi doka ba,shine Allah dokar banza,kuka ta saki me karfi yace alright matse min cinya,akan cinya gwara kayi Kawai dan sai tafi illa dan Allah ka bari lokaci yayi yace to na hakura amma ki daina yarda Ina romancing naki tace to,ko nace zanyi ki hanani amma Indai Kika bari to dole sai nayi da sauri tace to,Hira sukeyi sama sama har bacci yayi gaba da su. Da Asuba ya tasheta bayan tayi Sallah ta hada musu breakfast sabo da makaranta zai kaita,sai da Suka karya sannan taje ta sake yin brush tayi wanka tana ta Jin haushin makaranta Nabeel wanka yayi a gurguje ya shirya cikin yard me tsada peach,kwata kwata yau bai sakar Mata Fuska ba ganin sai Fushi takeyi akan zata je school,room dinta ya shigo ya ganta a zaune ko uniform bata saka ba,tsawa ya Mata tashi ki sa uniform mu wuce Ina Wasa da ke,Hamida taji tsoro amma tace ae Mana jiya ma ai munyi wasanmu da dare,Tsaki ya ja cikin uniform din set biyar ya dakko daya tare da fisge towel din Saura kadan ya fadi kasa ta rike da sauri Zan sa da kaina ba shiri ta fara kokarin saka Riga yace Ina bra din ko haka Zaki tafi? Da sauri ta zabo Kalar kayan dark blue and sky ta saka sannan ta shirya a gabansa ya duba school baga din komai ta zuba,kokarin shafa powder take yace karki sake wlh ko bana nan so kike ai ta kallonki muje haka Yana juya baya sai data goga soson powder din ta gyara takalminta sandal me tsada ta bishi,Habiba tana ta aikin gyara gida Suka gaisa Suka fita. Mota ya bude mata ta Shiga Fuska a daure shima ya shiga motar yayiwa mota key ya dan kalleta yaga kamar tasa powder handkerchief ya Mika Mata goge fuskarki,ba shiri ta karba ta goge sannan yaja mota securities Suka bude masa gate bayan sun gaisa Suna hawa titi yace Saura ki ki yin karatu ki gane kurenki Shuru tayi har suka Isa katuwar makarantar tunda Hamida taga masu irin uniform dinta tasan ma itace ta dinga tsinewa makarantar tana yar iskar makaranta jahila Nabeel Yana jinta ya sake hade rai Suka shiga har ciki ana ta kallon motar da mutanen ciki,Yana parking ya fito tare da zagawa ya bude mata ta fito Suka jera zuwa staffroom hannunsa cikin nata. Ba bata lokaci pc ya Kira headgirl yace ta raka Hamida class Ss1,Hamida ta kalli Nabeel zatayi kuka ita da take Ss3 an Mata repeating kenan,bakin ciki ya kamata ta fashe da kuka Nabeel ya juya tana kallo ya shiga mota ya tafi, Headgirl baki ta tabe tace ke dalla lests go,Hamida ta mata up and down tace uban let's go tabi bayanta suna tafiya tana cewa wlh ba uban Wanda zanwa biyayya babu wata kidahumar shugabar dalibai da zata zare Mana Ido,duk na girmi Yan makarantar nan, Headgirl albarkacin new coma ce ta kyale Hamida ta rakata class,Hamida tace ni bance a rakoni ba ehe wallahi karatuna zanyi duk Wanda ya min sai na rama Ina katuwa ta da shekaruna Ss1 shima Lelen Zan koma gida ne zamu hadu. Yan daban da suke ta Neman Hamida wanted har school dinsu suka je a suffar mutanen kirki Suka tabbatar Nan aka kawota tunda gidan ya gagara ya zuba securities a waje zasu gama da ita,cikin Yan daban waya ya dauka ya Kira yace yawwa Basma hanya Mai sauki an sakat a school yanzu haka tana cikin aji,Basma tace yawwa so nake a Gama min da ita kafin bikina kasan bikina Yana matsowa idan nayi aure banda lokaci iya wuya Nabeel bazai samu farin ciki ba. Tana cikin waya kawar Basma wata Aliya ta shigo dakin tace Ware Baiko badai baki hakura ba har yanzu dan Allah ki kyale bawan Allah wannan ba rayuwa bace,Allah yayi ba mijinki bane ki kyaleshi haka,ki daina ja da ikon Allah,akan dan Adam Bai samu abububa shike Nan ba zaman lafiya bazai fawwalawa Allah ba,abinda Allah baibaka ba babu Wanda ya Isa ya baka sannan wallahi da hakuri kikayi ya fi Miki riba banga amfanin Wai mutum bazaiyi hakuri ya yafe abu ba sai ace lallai sai an dau fansa, ita Yarinyar Hamida karki manta ciki ya Mata fa karshe ya wulakantata amma ta yafe Masa Ana ganinta Kamar marar hankali bata da tarbiyya ashe wallahi tafi mutane da dama hankali da kyawun hali . ke bakya tuna samari nawa Kika yaudara Kika rabasu da matansu duk su basu dau fansa ba sai ke,hakkin Wanda Kika yaudara ne ya biki kina ganin dan Allah ya baki kyau kike amfani da hakan kina cutar da maza amma kin kasa ganewa,gaskiya Ni dai na baki shawara ki gyara ki kyale Yarinyar da bata ji ba bata gani ba,Tsaki Basma ta ja tace fita daga dakina karki sake zuwa gidanmu ko inda nake munafuka Ina ruwanki to bazan yafe ba yanda na soshi ban samu Jin dadi ba shima bazai samu ba na dauki alkawai sai naga bayan Hamida Matukar Ina raye,Aliya dai ficewa tayi abinta ta bar Basma da ciwon son Nabeel bata taba son wani kamar Nabeel ba a Kansa tasan soyayya. Hamida tana class sosai take saurarar abinda ake cewa,bata kula kowa ba haka ba Wanda ya kulata har aka musu break tana fitowa inda taga ana siyar da abubuwa ta tsaya wajen me kwakwa ta siya kamar ance ta daga kanta taga maza biyu suna lekowa ta saman katangar makarantar Hamida ta tsorata ita suke ta kallo ta kalle su itama ta zaro musu Ido tare da cewa dalla dalla can,taga Kamar suna magana tace kurwata kur nafi karfinku Pipin Lele sai ta Allah tayi,basu kulata ba, duk inda ta motsa ita kadai suke kallo a Yan school ma Hamida ce kadai ta kula da su,ta sake cewa to da a aurena sai a dinga kallon musulunci Yan Iska taci gaba da siyayayrta Daya hannunta a cikin aljihun wandonta tace idab baku koshi ba ai gwara ku fada min na siya muku gurasa,motar Lelenta ta hango yazo dubata yaji tana karatun kuwa da sauri ta tafi wajensa hannayenta cikin ajihun wandonta irin shegun Yan makarantar nan tana karasawa yayi Murmushi tace Sannu da zuwa tare da Mika Masa Kullin aya daya ya karba ta sake zaro kwakwa a leda tace ungo taka dama Kai na siyawa tsaraba. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 36-40 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Alhusna (Mrs Idris) Najida Aliyu Bicca 🥰H😘 Ummu Abba Nafisa Musa Hauwaumuhammadhamza Mommy Anas A A U Aymaan Haarun Maman Husna Mom Fuash Karba yayi tare da furta thanks Yana kallon fuskarta tayi maiko sai kyalli take ga biron har a gefen bakinta yasan data sani da tuni ta goge ga makarantarsu da maza dariya yayi yace kinyi kyau Yan boko,fuskarta ta shafo tare da kallon tafin hannunta Wanda duk ta zane shi da biro hijab din ma duk jikinsa biro Nabeel a ransa yace first day har anyi haka da biro,a fili yace kinyi note? tace ae,abinci fa?kwakwa ta isheni yace to gashi nan lokacin break ya kare koma class sai nazo daukanki tace to,yace bakiyi kawa ba? Duk school din Nan ba sa'ata nafi karfinsu 21yrs gashi da aurena wace zata yi gogayya dani me suka sani ma rayuwar duniya Ina Suka je ba mate dita duk ciki na wuce ajinsu ,Nabeel yace inye shi Kam murna yayi Bai son kawayen nan Watarana dadin surutu ya kwasheta ta Fadi zancen duwawu,Yace banda zancen duwawun nan please dariya tayi tace haba sai kace yarinya ko dan ka gani a secondary school ta juya ta wuce har tayi nisa ta dawo tace kazo da wuri daukana ana karkada bell a kunnenka Alright na wuce Office ya Shiga mota ta juya ta koma class. Malami bai shigo ba matan class sunyi wani group suna ta zancen samari da labarin me akeyi a aure suna ta Yi kasa kasa suna sheka dariya,Hamida ko kulasu bata yi ba tana jinsu,a ranta tace yara baku ga takashi da maiko ba mu muka ga yau muka ga jiya,Suna ta wani tafawa suna Jin Hamida tace Yara kenan,Kallonta sukayi Kawai tunda tazo take kallon kowa dai dai,wata a ciki tace Wai wannan Yar gidan uban waye ce ne kunga yanda take wani raina mana hankali,wata tace Hmmm baku ga wani kyakyawa da yazo wajenta ba dazu Kinga kyau subhannallahi ga motar daya zo ma abin kallo ce I think yayanta ne,wata tace ko karuwarsa ba,tana jinsu bata kulasu ba note ma da zata ara na wani Namiji ta karba taga Yana da kokari wani bayarabe Arne Ola, har wasu ya bata yace taje dasu gida in ta gama ta dawo masa da su,Hamida tace thanks alot dan na ololo masu kashi a leda, dan mutunci you know ni ba mate din Yara bace na wuce level din matan class din nan,Wata a ciki wacce take ta Jin haushin Hamida tace ke wallahi karya kike ki girmemu duk nan ba dan kasa 16yrs,Hamida tayi dariya tace to har yanzu ke yarinya ce karama tunda baki Isa ganin Naja'atu ba,Budurwar tace Indai Naja ce gata can a class din Nan itace monitor,Hamida tayi dariya sosai tace an taba drinking din gorar Madara a gabanki? Suka ja Tsaki to ba gora ake cewa ba yogurt gashi ma mun gama sha,what of Koko an taba tiltila Miki a baki? Wata a ciki tace Kai dalla muci gaba da hirar mu, basu gane me Hamida ke nufi ba, ta sake ce musu ko Naja'atu ta taba kawo burkutu a gabanku Suka Mata banza ba ganewa suke ba,Lele ta tuna tana note ta ajiye biro tayi tagumi tace Lelena Yan matan Suka juyo suna kallonta suna kallon Hamida, wacce ta tsani Hamida sai hararta takeyi wata Jamila,Hamida ko ta kansu bata bi ba ta dauki biro taci gaba da note har teacher ya shugo Hamida duk magana ko Abu zatace da hausa sai ta jefo ko kalma daya ce ta turanci Yan class Suka dinga gulma da gani wannan daga yanda take magana komai sai ta jefo turanci maybe tana da kokari nan Suka sallama Mata, nan kuwa basu San dan abu kadan ta rike ba Wanda ta tsinta a wajen Shehu,har wani kulata akeyi irin an kawo me kokari Pipi a ranta tana ta dariya tana Adduar Kar Allah ya kawo malamin da zai kureta. Sai da period ta Kare aka tashe su,Hamida ta tattara littanta ta gyara hijab dinta ta fice daga class tana fita Kuwa Lele yazo Fitowa yayi tare da bude Mata motar kawai ta shiga tana wakar I'm coming home..lele dai ya rufe sannan ya zaga ya Shiga sai kallonsa akeyi har Malaman gaba daya,Hamida an dakko yunwa da rana baki ya mutu tayi tsit tunda ta gama wakar murnar komawa gida har Suka karasa gida bata ce komai ba tana fitowa tayi cikin kitchen direct ta zubo abinci sai lokacin Nabeel ya shigo yayi Dariya yace sai da nace a kawo miki abinci Kika ce aya da kwakwa sun isheki,rabu dani banyi zaton haka nake ba ulcer ce ta kamani wannan shekarar maybe bazan iya azumin watan Ramadan ba idan ya zagayo Sama ya haura ya shiga wanka,Hamida tana gama ci ta cire uniform dinta ta bawa Habiba ta wanke su ta goge,Sallah ta gabatar sannan bedroom dinta dana Nabeel ta gyara neat har toilet sannan sauran Kuwa duk Habiba ta gama,Wanka tayi tasa Yar karamar gown iya cinya me gajeren hannu tayi kyau, kitchen ta Shiga ta danyiwa Nabeel girki me sauki sannan tayi Shirin Islamiyya dake kusa da gidan ne ba nisa sosai, nan ma sanye da uniform milk and dark brown ta fito ta iske Lele a dining,muji girkin naka ta danyi cokali daya sannan ya Mata kiss a kumatu yace a dawo lfy a kula da waya da Kinga ba daidai ba ki kirani tace to yace dan security zai rakaki kuje. Tana fitowa cikin securities din guda daya ne ya rakata har School ta Shiga sannan ya koma gida,Yan daban da suke ta bibiyar Hamida waya Suka sake bugawa Basma Suka ce yanzu fa Yarinyar Nan an bata tsaro sosai gaskiya,Basma ta dinga bala'i karfa ku min Wasa da kudi na,na biyaku kudi me yawa taya zaku dinga raina min hankali ku yanka Yar Iska Kun kasa,Dan daban yace idan aka Kama daya cikinmu wlh kema asirikin ya tonu kibi a hankali zamu sheketa ne duk inda take Muna kusa. Ana tashin su Hamida daga school Nabeel yaji hankalinsa bai kwanta ba da Kansa yaje ya dakko abarsa,zuwa dare ya koya Mata karatu sosai da sosai sannan Suka kwanta bacci,zai Fara tabe tabensa taki yarda Kar yace sai yayi haka ya hakuri sukayi bacci. Washe gari da safe ya sauketa a school ya wuce office,ana Fitowa break again ta sake ganin mazan Nan suna lekenta ta katanga wajensu ta matsa suna daga waje tace bayin Allah da aure na an siyar dani ni kayan wani ce,wata budurwa ta fisgo wacce ita bata kula da maza na lekowa ba Hamida ta juya bayanta sosai da yatsa ta nuna musu Duwawun budurwar tace ku kalli na wannan nawa an siyar da shi tuni akwai me shi ta Kara gaba,Budurwar kafin ta kalli katangar sunyi kasa basu sake lekowa ba. Nabeel Yana zuwa daukanta lokacin an tashe su suna Kan Hanya ta shagwabe tare da cewa Lele wasu ne kullum idan akayi break suke lekowa ta katanga Kuma ni kadai suke kallo ko duwawuna suke kallo oho nidai ban gane musu ba gaskiya,Nan take Nabeel hankalinsa ya tashi Yana tuki ya kalleta yace ba nan suke kallo ba,ki nutsu karki sake fitowa break ki dinga Zama a class Zan dau mataki kome kike so ki bayar a siyo Miki kinji,to ta furta jikinta yayi sanyi Islamiyya ma karki na Fitowa sai securities sunzo kinji ko? yanzu Ina da aiki da zanyi securities ne zasu dinga kaiki suna dakko ki,tun 7 Zan dinga fita sai dare,aikin kwangila ne? ta tambaya yes ya furta, Allah ya bada sa'a,Gefen fuskarta ya shafa a hankali sannan ya dauke hanyar layinsu har gida, abinci ta ci tayi Shirin Islamiyya yace muje na ajiyeki zanje gidan su Ammar muna Shirin bikinsa,Uhm kace shima ya kusa shiga layin ganin duwai,Dariya yayi yace sai kin girma kin koyawa yaranki fitsara naga alama,haba tarbiyya Zan musu zaka gani zagi yaro yayi sai dai kaji fas na kwade shi,a son yaranku Mata Allah ya kaimu Zan gani. Yana ajiyeta ya Mika Mata dari biyar,tace kana shagwaba Ni ta safe dubu ta Yamma dari biyar sai kace matar gomna a rayuwar Nan so kake ta Allah idan ta kasance babu Kai na Sha wahalar rayuwa ta window ta shigar da kanta ciki Kamar zata Yi kuka tace Lele Allah ya baka tsawon rai da lafiya Ina sonka wlh kayi lafiya kaji, Lele yau dadi kamar an Masa bushara da gidan Aljanna bai taba ji tace tana sonsa ba sai yau yasan dai tana sonsa ga yanda take nuna Masa,gemunsa taja kadan tace a kara bari yafi haka, Lele harda wani yin fari kamar mace shauki ya kwasheshi,Hamida ta kyalkyale da dariya ta sake tsura Masa Ido Kamar zata Shige Masa Fuska tace Lele kamshi Lelen kyau Lelen Pipi. Lele Yana ta dariyar Jin dadi sai ya fasa tafiya ma ya fito ya jingina da jikin motarsa ya wani harde kafa hannayensa rungume a kirjinsa yana dan Jan gemunsa yana karewa Hamidansa kallo. Sai Murmushi take zubawa tana dan kallon gefe gefe sabo da Lele ya kafeta da ido,Yace kin hanani tafiya you are so cute lips dinta ta wani gyara, ganin ba kowa a wajen ya dan zaro harshensa waje in a sexy way, Lele ji yake kamar ya dauketa su koma gida ,Ganin lokaci zai kure ya bude mota ya shige ciki tace sai na dawo ya daga Mata hannu tajuya ta wuce ta danje bakin gate ta juyo ta kalle shi bai tafi ba Yana ta faman kallonta alama ta Masa da Hannu Wai ya tuka mota ta Shige school sannan yaja mota ya wuce. Duk abinda sukeyi akan idon Basma wacce ke cikin mota tare da Yan dabanta,wani kishin Hamida ya sake ninkuwa a ranta suna baya sun buya a cikin mota suna kallo,Basma hawaye ya zubo mata,cikin Yan daban dayan yace gaskiya suna birgeni Yana son matarsa itama tana sonsa ni in ba a radio ba ban taba ganin so irin wannan ba,Ki daina kuka Basma karki ga wai Mata suna kuka a cikin film kice kema zakiyi akan Namiji karya ne wasan kwaikwayo ne Yi suke ana biyansu kudi,Kuma ba kukan gaskiya suke ba karki ga suna yi,su yi suke ana biyansu Kamar baki San me duniya take ciki ba ai su kudi ake biyansu Kuma ba hawaye suke ba ruwa ake zuba musu suyi bana gaske bane,Baku da aiki yanzu sai kwaikwayon Yan Film to Suma duk karya ce Kawai kudi suke samu ke gashi Zaki kwaikayesu ki bata hawayenk....tas kakeji Basma ta kwasheshi da Mari tace baka San so ba an fada ma kwaikayon wasu nakeyi na gaske nakeyi ni,dayan yace ah to ko mai yanzu ba su ake kwaikwaya ba daga anga Yan film sunyi abu sai a ara a yafa,Basma tace Baku San aikinku ba wlh kuje na fasa ni zanyi da kaina,Suka ce ah Indai kin bar Mana kudin ai shike Nan dama mu bamu taba kisa ba shaye shaye Muka iya ayi lafiya Kuma ki sani mun San kece Kika kashe matarsa ta farko Kika dakko Yan daba tun daga Lagos hausawan Lagos Kika yo haya Zaki sani,Basma taji tsoro amma ta fuske tunda tunaninta basu da hujja ko kotu aka je sabo da haka ko zata mutu itama sai ta kashe Hamida. A Nan Suka rabu da Yan daba Basma bindiga ta Nemo aka ce za a kawo mata ta biya kudin tana jira Kawai a kawo. Saurayin da zata aura Alhaji Sa'edu hamshakin me kudi ne Yana da Mata Daya da Yara biyar Basma gidanta daban ya kankara Mata shi a Abuja amma Sam ba shine a ranta ba Kawai ta gaji da rashin auren ta fiso tayi auren tunda me kudin gaske ne ko an gano tayi kisan Kai shi zai fita ya Shiga ya bada rashawa a saketa sabo da kasar haka take shi yasa ma take so Kawai ayi a daura auren ranar da za a kaita gidan miji ita Kuma ranar ta dauki alkawarin ranar zata gama da Hamida,Motarta ta ja ta koma hotel kafin gobe ta bi jirgi ta koma gidansu Wanda babu Wanda yasan me take kullawa duk anyi zaton Shirin auren takeyi,kudin ma idan an bata na gyaran jiki Yan daba take bawa. Ammar tare suke da Nabeel suna ta zuba hira da yanda za hada komai na auren Ammar, Nabeel agogon dake daure a hannunsa me tsada ya duba yace 5pm yanzu an tashi wifey zanje na dauki abata,Ammar yayi Dariya yace to wa yace tasa ce, Nabeel yace yaro tawa ba irin taka bace baza ka samu irin tawa ba,har mota Ammar ya rakashi Yana dariya sosai sannan ya wuce direct school din su Hamida ya wuce ya ganta a tsaye a ciki tana jiransa su da wasu Wanda suma suke jiran azo a dauke su, wata Khadija wacce ta damu sai tayi kawa da Hamida duk da ba ajinsu daya ba haka Kawai taji tana kaunar Hamida tace ya sunanki dan Allah? Hamida Kabir Nabeel,nice name sunana Khadija,Hamida harda cewa nice to meet you,itama tace nice to meet you too bye,Hamida tace bye itama ta nufi motar Nabeel Fitowa yayi tare da bude Mata yace Sannu Pipi yawwa Lelena ta Shiga ya rufe ya koma ya shiga mota yaja suka tafi Hamida tace Yar gata ni ba nisa amma sai an kaini an dakko Ni Allah ya daukakani thanks Lele. Hmm Kawai ya furta gobe za a fara kaiki ai,kafadarsa ta dafa tare da furta oh I will miss your driving,Dariya take bashi da mamaki Jin tana yawan kokarin yin turanci yace ashe dai Shehu yayi kokari Hamida tace hmm ai Shehu wlh Yana da baiwar koya karatu duk daskarewar brain dina sai da ya tasheta,Yana lailaya mota yace yayi dan abin kirki,hmm banji dadin da Shehu ya Zama haka ba ta wani bangaren Yana da Hali me kyau duk lalacewar mutum baya rasa wani halin kirki,Nabeel bata Rai yayi yace nifa? Why kike yabon wani? Murmushi ta saki tace sorry na manta mijina me kishi ne,Bmbai kulata ba ta girgiza kafadarsa I'm sorry Lelena ta wani kashe murya tare da kwanciya a saman kafadarsa,Ice cream ya tsaya ya siya Mata da kayan makulashe yace yau ba girki ki huta kinji my love. Wayarta ta jona ta kunna wakar hausa ta soyayya tana bi tace Sadaukarwa zuwa ga Lelena tana bin wakar tana kallonsa,yace zakisa nayi hatsari fa,Murmushi ta saki yaji wani baitin soyayya yace nine nace wannan zuwa ga ke,Hamida harda dafe kirji ta lumshe Ido ya shigeni tace,Hannu ya Mika Mata suka tafa,Yazo wajen danger suna tsaye sai ga Basma itama da motarta ta tsaya a saitinsu tana kallon Hamida ji take Kamar ta dauketa da bullet amma ba a kawo Mata bindigar ba,Nabeel ne ya dan leke fuskar Hamida Yana dariya, hannaye biyu tasa tare da rufe fuskarta,Yana kallon dayan hannun yayi Ido biyu da Basma,Kallonta yayi yanda ta kafe su da Ido,Hamida ma gefen ta kalla ganni ya kalli wajen sai taga Basma,Hamida taji haushin Nabeel ko tsohon so ne ya motsa shi yasa ya tsaya Yana kallonta,Glass ta sauke Kamar yanda Basma ta sauke nata,Hamida taga Basma ta Lula tunani ta Dan bigi mota ta dawo firgit ta kalleta taga ta rame sosai Hamida tace ga kwandalata a ajiyemin a cikin kashin wuyan, Baki da lafiya? ko Tamowa ce ta kamaki?Ana ba da gyadar Yara masu tamowa, danger ta bada hannu Nabeel yaja ya wuce itama Basma ta canja road inda zata koma Hotel,Hamida ta bata rai taki Masa magana,Maganar duniya taki kula Nabeel,Yana shiga gida kafin ya fito a mota ta riga shi ficewa da sauri ya gano kishi takeyi yace Pipi Ina magana Palo ta wuce tare da wucewa sama,a steps ya cimmata daukanta yayi tare da maidata bayansa ya goyata,Hamida sai ta daina fushin tace kaini dakinka ya kaita tace karka saukeni kaini dakina Nan ma ya kaita,ya dawo da ita ya dauketa suna facing juna sai ya Kai kanta kasa sai ya dagota sama sai Dariya takeyi,Sai da ya gaji yace to sakko,uhm uhm ni kar a saukeni Kamar Yarinyar yaye haka tayi,Saman bed ya kwantar da ita ya zare Mata katon Hijab din tare da Zama a gefen bed din ya cire mata rigar daga ita sai guntun pant da bra,kirjinta ya kifa a saman cinyoyinsa sannan ya balle Mata hook din bra din ya janye tare da jefar da ita,har ga Allah bada niyyar Mata wani abu yayi ba ganin boobs din nata da yake mugun kauna bazai iya kyalesu ba,Hamida Bata hanashi ba sosai ta bashi hadin Kai Suka fara murza juna suna sakin Nishi,ganin zai wuce gona da iri ta fara nokewa nan fa yace bai San zance ba Suka dinga kokawa,har ya samu nasarar danneta ta ko Ina Wayarsa tayi Kara Yana dubawa yaga Mimi,tana danne a kasansa ya daga wayar Mimi tace Ina Hamidan bani ita dama ita nake Nema yace ta shiga wanka idan ta fito Zan bata,Hamida tasan shirinsa da karfi tace gani Mimi na fito,Dariya yayi ya shake wuyanta da Wasa ta fara tari,Mimi tana ta hello hello Kawai tarin Hamida ta ji da dariyar Nabeel,Sai lokacin Hamida tace hello Mimi Ina yini ya gida ya...Dariya ta saki ta sake cewa sorry Mimi ya Affa na Kira bai daga ba,Mimi tace kowa lafiya Nima na jiki kwana biyu shuru bamu gaisa ba,Hamida tace uhm Mimi School ce wlh shi yasa. Yan makaranta ai naji Alama har sorry ake ce min dariya Kawai Hamida tayi sai Jin kunya takeyi tana wani ladabi ka rantse a gaban Mimi take,Nabeel sai Jin Dadi yake pipinsa tana ta hankali ko yaushe Kara canjawa take Yi,Mimi ce ta jaddada Mata karfa ta biyewa Nabeel ya karya dokar likita,Hamida harda rufe Fuska tare da cewa to Mimi,dama Kiran da na Miki kenan na tunatar dake,tace to a huta lafiya ta kashe wayar,Nabeel ya tallafe haba tare da zubawa Hamida Ido harda wani a huta lafiya,Wayo tayi Masa ta Shige toilet ta kulle Wai sai sunyi wankan tare shi yasa ta kulle da key, Bedroom dinsa ya koma ya zuba wanka sannan ya fito suka ciki kayan tande tandensu ya koya Mata karatu. Haka abin ya kasance har Hamida tayi sati biyu kullum baida lokaci yanzu securities ke kaita su dakkota daga Nan bai sani bama tace kumma zasu na koya Mata mota, a dan wannan lokacin take dan koya tana koya duk Nabeel bai sani ba,haka idan ba Islamiyya sai tace zata unguwa wajen mimi sai ta gama koyon motarta sai ta wuce can,har ta iya mota cikin kankanin lokaci sai dai hannunta bai gama fadawa ba. Lokacin Kuma bikin Basma Saura wata daya,Alhaji Sa'edu ne yaje zance ta hada Masa girki na alfarma suna hira yace My love ba abinda bazan Miki ba a rayuwa Matukar Zaki nuna min kauna,katon tumbinsa ta kalla ta dan tabe baki sannan tayi murmushin dole sabo da me kudine tace kome nake so zaka min? Yace kwarai kuwa tace ko kisan Kai nayi? Yace shi yafi komai sauki case nawa na kashe irin wannan yarona ma ya kashe wani na fita na Shiga nasa aka sakeshi ya kashe banza,Ni kaina mutane Nawa na kashe Kuma ba abinda aka iya Yi min ai yanzu in kinji hukuma ta kashe wani to talaka ne marar galibu,duk abinda kike so kiyi kanki tsaye ke idan ma so kike a kashe Miki a gabanki Ina da shahararrun Yan daba,Basma taji Dadi tace a gabana nake so ayi watace ta zalunceni taci amanata ranar da za a kaini gidanka ranar nake so a gabana a kasheta,Alhajin Sa'eedu yace karamin Aiki ne ma Ashe mace ce karki damu My love,Basma tace I love you ta fara bashi abincin a baki harda gyara Masa Karin hula Yana ta wani washe baki Yana murna ya samu budurwa zukekiya. Yau Saturday Nabeel Yana wajen da yaransa ke aiki Hamida tana gida sai ga wasu mata su Uku sun shigo da wata jaka katuwa da kayan Aiki Kamar Yan polio, Security ne ya sanar Mata tace ace su shigo,har Palo aka rakosu duk da Yan birni ne amma sunga hadadden gida yasha kudi sai kalle kalle sukeyi ko Ina kamshi na tashi Yana kyalli ga ac,Hamida Suka kalla ta zuba kyau cikin wata Riga Yan kanti marar nauyi me siririn Hannu Maroon da gani kasan me tsada ce,sunyi zaton irin Yan wulakancin matan birni ne,Hamida ta kallesu duk wasu a jigace sunsha Rana da ga yunwa suke ji,Hamida Murmushi tayi tace bayin Allah me kuke raba Mana ne gomnatince ta aiko maganinta kullum baza a rana abin arziki ba sai magani maganin ma bana kirki ba duk Kun jawo yaranmu sun kangare sabo da kwayar da ake Basu yaro ka zare Masa Ido ya zare maka,Dariya Suka dinga Yi Suka ce masu kananan ciki muke aunawa idan an tabbatar da cikin sai a bada maganin karin lafiya dake da jaririnki,Ahaf nasan bazai wuce wannan ba da wannan maganin da tallafe tallafe gwara a sakko Mana da Kaya mu daina Shan tsadar rayuwa. Tace Amarya ce ni banda ciki,dayar tace taya Kika sani Indai ba gwadaki ba,Ke karki min tambayar ya uwata ta haifeni bani da ciki amarci muke Sha Naga dai yunwa kuke ji bayin Allah ku zauna na zuba muku abinci kuci ku koshi gashi Nan duk Kun fita a hayyacinku,Dariya sukayi ta wuce kitchen suna ta yabon Hamida ta kinkimo musu wani hadadden flask da plate ga ruwa da lemo tace ku saki jikinku Gomnati tana ta wahalar daku wallahi kuyi aurenku Naga alama Yan Mata ne ku,Suka ce ai ance aure Rahma ne Allah ya bamu me son mu,Hamida tace Ameen Rahma kai ai Ni ban gane ba sai da na shigo daga ciki suna ta dariya tana ta basu dariya Kuma ita bata dariyar. Ta zuba musu Fried rice da soyayyar kaza Haba Malam baki dama yunwa ta ishesu Suka share girki,tace a kara muku Suka ce sun koshi tace don Allah Kar kuyi Kara yanzu an waye an daina wannan ta sake zuba musu Suka lashe kadan suka rage Suka Sha ruwa da lemo sannan suka dinga Mata godiya Suka ce zasu tafi tace ku gaida gida. Suna fita kofar gida Suka tsaya can nesa suna shawarwari,Daya a ciki tace wannan mutuncin data Mana ta ya zamu iya yaudararta a kasheta ki duba kwana Nawa bama samun abinci mu koshi haka sai yau a gidanta,gashi ta bamu shawara muje muyi aure muma mu samu farin ciki kullum muke Nan bara a Kan titi Muna neman abinda zamu sa a bakinmu yunwa ita tasa Muka karbi aikin nan sabo da mu samu kudin abinci,wallahi bazan iya ba iya abinda ta mana ya ishemu ishara,ki duba masu kudi gidajensu idan ka shiga Yanda ake wulakanta mutum kallo baka ishesu ba amma ita bata Sanmu ba ta karramamu har palonta ga abinci me dadi da nama ga ruwa da lemo haba ai wallahi mu samu miji ko talaka ne muyi aure Kuma Nan gaba muzo mu dinga gaisheta duk da cewa mun girmeta ita Kuma Basma mjn cinye kudin baza muyi aikin ba Suka kara gaba suna ta sawa Hamida Albarka. Lele sai magrib ya dawo lokacin tana kitchen ta Masa wani girkin na daban Wai bazai ci girk tazarce ba,kitchen ya shiga direct Jin motsin abar kaunarsa ta baya ya rungumeta Yana shakar kamshinta ta juyo a hankali tare da shigewa jikinsa ta kwanta a kirjinsa tana Masa Sannu da zuwa,Kanta ya dago da hannaye biyu ya hade bakinsa da nata ya fara tsotsa Yana cewa I love your lips, Hannunsa ta rike tace bari na karasa shirya dining kafin Nan kayi wanka,kafada ya makale yace yunwa nake ji,Lemon kwakwar data hada ta zuba Masa a glass cup ta Mika Masa ya shanye ya Masa dadi yace bari nayi sauri nazo naci girkin Amaryata me dadi yau wankan ma bazan iya na kirki ba sabo da girki me dadi zanyi ta tunani,Dariya ta dinga Yi tana lekensa ya wani haura sama da sauri,da dan karfi tace kayi a hankali Lelena,bazan iya ba kamshin girki ya cika min ciki,Yana shigewa daki Hamida harda tafin Jin Dadi ta ajiye abin juya girkin tace ahayye chass inji dan daudu,tayi wani takun yanga ta kalli kanta ta dan juyo ta kalli bayanta tace Lele zai Sha Dadi gaskiya Abu lunguna lunguna Dawas Kara taji girkin zai kone ta koma jikin gas da sauri ta sauke oh Zan bata rawata da tsalle Basma bindiga ta iso ta siyi abarta sabuwa an kawo Mata daga lagos ta boyeta tana jiran rana,gashi sunyi da Alhaji Sa'eedu tana kasheta Kawai zata bar kasar kafin lokacin zai musu visa da shi da Basma a ranar zasu bar kasar su wuce inda zasu kwashi love. Masu sharhi Wanda basa gajiya da min sharhi Ina Matukar godiya AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 41-45 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Nimcyluv Nanahkhadii Rayys Mom aneesa Fatima Umar Adams Madame Souley Aicha 🥰🥰🥰 Maman Sultan Ummu Jiddah Maman Murtalah MamaZee Ddm Maman Raiz Washe gari Sunday Bayan ta raka Nabeel mota ya fita Palo ta zauna tare da Kiran Karima bayan sun gaisa tace Aunty Karima ya za ayi ne?da me fa karima ta tambaya,Hamida tace Wai da Zan fara zuwa gyaran jiki kafin Lelena ya dawo normal sabo da time ya kusa,Karima tace ai ya kamata ki fara amma karki ta Shan magunguna Kar a samu matsala amma jikin Kam ki gyara sai maganin Infection kiyi kin San ba a rasa mata da shi kina da su duk an kawo Miki su suna Nan bedroom dinki,yes na gansu ai,to ai kowanne an rubuta yanda zaki amfani da shi ki fara amma banda siyen jike jike banza kina Sha Kar ya Haifar Miki da wani ciwo a internal organs ki kula in baki San Abu ba karki dinga shayen banza,okay ta furta Suka gama tattaunawa sannan ta ajiye Wayar tare da haurawa sama. Wankin Nabeel da aka kawo su Hamida ta zauna ta shirya Masa su tare da gyara komai ta tattara Inners ta wanke Masa a washing machine tayi drying dinsu bayan ta gama abinci ta goge su ta adana,nata ma da kanta take wankewa a machine sai ta bawa Habiba ta goge Mata,bata tara wanki ita,abincin ta zauna tana ci jollof din taliya tayi da doya taji kifi,su Kuwa masu aiki Habiba ke dafa musu abinda suke so a daya kitchen din,tana cin Abincin Nabeel ya Kira ta a waya,dagawa tayi tare da yin kasa da murya yanda taji Yan school dinsu suna gwadawa yanda akewa miji,itama haka tayi ya kike ya aikin gida? Hamida ta wani gyara zama tare da furta Alhmdllh ya aiki ya akaji da yaran nan naka marasa mutunci,dariya yayi yace kin tuna Sanda suke Jin haushi a kauyenku sabo da Ina baki 1k kullum,Hamida tayi dariya kasa kasa wani ta Yan gayu,ya naji muryar ta Kara zaki ne? Murmushi ta saki me sauti tace to kullum Ina Shan Madara da sugar ba dole ba ta Kara zaki,Kinci abinci ne? Kai nake jira ka dawo muci tare ni nafi Jin dadi idan muna ci tare kana min kallon nan naka sai kaga kafin kace me na tashi plate daya,Dariya Nabeel ya sake yi yaji wani dadi yace karki jirani kici abinci karki rame so nake ana ganinki asan na iya kiwo,Hamida harda shagwaba uhm...uhm...sai ka dawo gaskiya ta kallin uban abincin data dafa ta fara cinye abinta amma ta shirga karya Allah na gani baza ta iya jira sai ya dawo ba bata jure yunwa amma sabo da yaji dadi tace shi take jira. Yace kiyi girki kici abinci sai dare zan dawo yau,Hamida tace yau haka zan yini ban ganka ba? Nasan ma yau sai malaria ta tashi sabo da rashinka,Nabeel ya saki dariya yace anjima kadan Zamu yi video call amma kici abinci kinji tace to ya na iya tunda ka damu sai naci yanda kace haka za ayi bari naje na dafa,okay jeki I will call later,Love you cewar Hamida, love you much more Dear ya furta tare da datse Wayar, Hamida taci gaba da cin abincinta har ta gama tayi wanke wanke ta Shiga wanka tare da dauro alwala,Sallar azahar tayi sannan ta shirya ta cakare cikin wani tight arsh jeans da wata farar t-shirt me katon love red a jiki tayi kyau gashin ta gyara sosai tare da daura wani arsh siririn gyale me kyau gashin ya fito ta tsakiyar dankwalin goshinta kwantancen gashinta gashi nan a waje, kallo ta kunna kenan sai ga Kiran Nabeel video call Dagawa tayi Yana kallonta tana kallonsa yaga tayi kyau yace My Shakira,Murmushi tayi Mai sanyaya zuciyar masoyi,dan tashi na gani,taya zaka gani bayan wayace,da Wayar Zaki dinga hasko ko wanne part,haka ta fara hasko masa iya kanta sai kirjinta har zuwa kafafunta yace kin hadu Sarauniyata hasko gorar madarar ta haska masa Hamida har da wani karkada kirji,Nan take yace ganin nan yanzu zan dawo gida idan na ganki sai na koma Hamida har da wani iyayi hey take it easy Mana minti nawa ne ka dawo Kawai mu dai a samo Mana halak Banda haram mu da yaran mu masu zuwa nan gaba yace nifa kawai zuwa zanyi na ganki,ni zanzo sai ka ganni na koma yace kisa katon Hijab har kasa ki sa driver ya kawo ki,Hamida tace to gani Nan ta kashe wayar tana dariya bai San hannunta ya fada a driving ba,Hijab tasa me Hannu har kasa ta hada basket dinta na abinci ta dauki key din katuwar motarsa baka kowa ya ganka yasan ka hau mota Yar gaske,Gate tace a bude Mata ta bude baya ta saka basket ta shiga mota ta Mata key tare da bata wuta dama ta Sha wanki tana kyalli,a nutse ta bar gidan harda kunna dan kida kasa kasa Ya bata address da nisa ma wajen amma a wajen gari ne gefen Hanya,a nutse ta dinga driving har wajen aikin nasa tun kafin ta karasa ta hango shi a jikin motarsa Yana latsa waya masu aikinsa suna ta fama da motocinsu. Tunda yaga motar ta gangare tana tafiya daf da su ya kafe motar da kallo Yana tunanin wannan motar ai tasa ce tunani yayi ko Hamida ce ta bawa driver ya kawota amma sai ya hango Kamar mace a ciki,Hamida a saitinsa ta tsaya tare da sauke glass suuuuuuu kasa Kawai ya ganta a ciki,mamaki ya kamashi yaushe ta iya mota ko dama ta iya ne,Murmushi ya saki yace gyara parking hajiya Shakira ta wani gyara parking yana ta mamaki ta fito,ya kalleta sosai yace yaushe kika iya mota ban sani ba? Hamida tace driver ne ya koya min Kullum idan na taso daga school,amma me yasa baki sanar min ba? so nake na baka mamaki,yayi Murmushi yace to daga yau kina sanar min kinji to ta furta sannan ta Mika mishi basket din ya karba tare da furta thanks,tace na gaisa da yaran naka? Yeah ya daga musu Hannu lokacin sun dan tsaya da aikin suna hutawa sai gasu sun karaso da yawansu Hamida ta gaishesu da fara'a Suka amsa,Nabeel ya kallesu yace kun ganeta Kuwa? Wani aciki ya daura hannayensa a Kansa yace ahhh me dubu daya ce ikon Allah,Nabeel yace itace matata suka dinga mamakin ikon Allah da kyar Suka ganeta yanda ta Kara kyau da kiba ta Kara haske ta Zama Yar gayu sai kallonta suke Nabeel ya ajiye basket din yace gyara motar ta kalli wajen bishiyu inda ba me ganinmu duk da cewar akwai tint. Shiga tayi ta gyara parking din yanda ya dace yana ta mamakin Pipinsa ta iya mota wai daya side din ya bude ya shige tare da kulle motar juyowa yayi ya kalleta itama shi take kallo suna Jin wani nishadi da shaukin juna,Kullum kyau kike karawa my life, Hamida ta kalleshi da wani fari tace dan Allah ni life dinka ce? Kai ya daga Mata alamar kwarai kuwa,Hamida tace dan Allah fa? Allah ya furta,Ido ta Kura masa tace yanzu da Zan bar maka gidanka sai ka mutu?Nabeel yace ai tuni ma Sai dai aga nayi yuuff na wuce,Hamida tayi dariya tare da cewa shike nan na mallakeka ka shiga uku dani,hannunsa daya ya saka cikin nata Yana Wasa da yatsunta tare da dan janyota jikinsa suna shaka kamshin juna,lips dinta ta dan turo Masa su tare da nuna Masa da yatsa nan take ya hade bakinsu waje daya suna tsotsar bakin juna a hankali yace idan Ina gabanki sai naji komai yazo min da Sauki Pipina,Hamida ta danyi Murmushi tace da sonka nake kwana nake tashi Lelena Allah ya barmu tare,hijab dinta ya Dan daga yasa Kansa ciki ya kalli yanda kayan suka mata kyau, Yace baby kin zamemin aya,aya ce aka saukar yanzu so nake Kawai na warke na samu nayiwa soyayyata hidima na samu na kulle bakinki sai kinji Hidima a dausayi yarinya,Dariya Hamida tayi tace oh sex din ne Hidima yace yes ai Dausayi zanwa hidima Dariya ta saki tace Allah ya kaimu naga hidima,cikin hijab dinta ya dan sa hannunsa,hannunsa ta bige da sauri tare da furta Gorar Madara basu dauki sanyi ba tukun,sai ka dawo gida,shagwaba ya fara Mata kamar yaro haka yake mata,basket din ta bude Masa ya kalla har su dambun nama da pepper chicken da wani meat pie na gashi sai lemon data hada me dadi godiya yayi mata tace Zan koma gida Ina da Assignment sai ka dawo ma hadu,kallonta yayi yace kina bukatar kudi? No ai tunda ka soni me zanyi da kudade gwara ka so ni sai godiya ga Allah. Karki barni my Pipi mu rayu cikin amana kinji? Inshaallah ta furta Masa fita yayi a motar tare da cewa kiyi tukin a nutse a kular da pipina sosai ki Dan Kara hakuri Ina nan Zan yiwa dausayi hidima very soon,karfe Nawa zaka dawo? 8pm Inshaallah Fuska ta kwabe cike da shagwaba Gogar Madara zai huce fa gaskiya yayi nisa,a bar min abuna kin San Affa yace naje Yana son ganina idan nayi Sallar Isha sai na dawo Kawai ki min kwalliya kinji, Alright Allah ya dawo min da Kai lafiya I will miss you, me too my Pipi hannunsa yasa ta window tare da dan Jan hancinta kadan i love your nose,key tayiwa motar sannan ta fara tafiya tana kallonsa yanda mijinta ya hadu sosai kamar tayi ta kallonsa haka take ji, tace na manta Zan dan biya wajen Mimi kaji? Alright amma karki zauna, okay ta furta Jan motar ta fara tare da dage glass din window ta rufe sannan ta hau kwalta tare da yin you turn ta dauki hanyar gidan Mimi,Mimi da Affa dawowarsu kenan daga wajen aiki Suka ga motar Nabeel ta shigo gidan sunyi zaton Nabeel ne,sai suka ga Hamida suka dinga mamaki,wai Hamida ce haka Allah buyawi,Pipi Fitowa tayi tana dariya ganin irin kallon da su Mimi ke Mata na mamaki tace Hamida ce fa Affa. Mimi tace amma gaskiya karambaninki ya birgeni,palon Suka shiga gaba daya har kasa ta duka ta gaisa su da girmamawa,Mimi tace daga Ina? ai ta iya mota yanzu sai yawo cewar Affa Murmushi tayi tace abinci na Kai Masa dan kayan motsa baki ai Lelena Yana Shan wahala wlh halal yake Nemo Mana Neman halak da wuya yake har tausayi bawan Allah nan yake bani,Mimi tace a'a lallai dan halin yana nan dai akwai ragowa,Dariya pipi tayi,Affa yace ku ba dama a fadi gaskiya duk ba haka muke Shan wahalar Nemo Muku ba ku da yaranku,Hamida tace ai Affa maza bayin matane sai yanzu na yarda,uwaki ja'ira banda ni wannan ya nuna Mimi yace bata Isa na Zama bawanta ba,Mimi ta kalleshi tare da cewa na nawa kuma,mikewa Hamida tayi tace Zan tafi Ni,tun yanzu? ae Mimi zanyi girki ne shi yasa sai nan gaba zan dawo,to ki gaida gida Affa ya furta, Mimi tace Allah ya kaimu a dinga Hakuri da juna kinji,Hamida tace laaaaa Mimi baya min wani Abu Wanda za a ce sai hakuri ai mu hakuri ma bamu San inda yake ba,Murmushi Mimi tayi tace ai Kuwa Indai zaman tare ne Zaki ga hakurin da ake cewa kiyi sai gaba, Hamida tace to Allah bamu shi ni na tafi gida, Mimi ta dan rakata mota ta wuce. Lokacin Basma tana gidan Hamida ta Shiga cikin dabara bindigarta tana jikinta a soke,Hamida take son gani ruwa a jallo amma ta gama dubawa bata gani ba sai me aiki Habiba wacce Basma tace Yar uwar Hamida da ce zan jirata,karar mota taji tunaninta Nabeel ne zumbur ta Mike tabi ta kofar baya ta haure katanga ta bar unguwar gaba daya bata San Hamida bace ta dawo,Sai da Hamida ta shigo Habiba tace kinyi bakuwa tunda Kika fita tazo tace zata jiraki nace Mata ke kadai Kika fita amma Kuma tana Jin karar motarki ta fice ta gudu,Hamida tace Allah ya kyauta Allah ya tsareni daga Sharrin koma waye. Sallar la'asar tayi tare da yin assignment boko dana addini sannan ta shiga kitchen zata hadawa oga girki, tunani ta tsaya yi a kitchen din me zata dafa Masa ne, miyar jajjage tayi ta Sha kifi ta dafa farar shinkafa,Pepper chicken din da tayi ta zuba a wani hadadden mazubi Wanda kana gani kasan ba karya,hadin salat tayi tare da su cream salat ta ajiye a dining komai dai ta shirya abinta ga wani zobo me kauri Wanda ba Karin ruwa a ciki iya Wanda ta tafasa da bawon abarba da kayan kamshi yayi sanyi sosai ta barshi a fridge,Wanka taje tayi tare da yin Sallar magrib ta tsara gayu cikin wanu bum short me Kalar green,red and yellow an Masa layi layi da rigarsa Yar karama me hannun vest,Habiba tana dakinta,Pipi tana kamshi haka tayi Sallar Isha tare da shafa'i da wutir ta sake gyara kwalliyarta da gashinta,karar motarsa taji da alama ya dawo,a steps ta tsaya ba tare data sakko ba sai da taga ya shigo sannan ta karaso da sauri tare da fadawa jikinsa ya maida hannayensa ya rungumeta gaba daya a jikinsa cikin sigar rada ya furta you look good,Thanks ta furta itama da rada, hannayensa yasa tare da mikar da ita daga jikinsa ya rike hannayenta biyu Yana Kare Mata kallo ya Murmushi ya furta kin hadu, ledar da ya ajiye a kasa ta dauka yace abinki ne a ciki ta buda duk kayan tande tande ne ciki na gode tace tana murna tace muje kayi wanka,Sake rungumeta yayi yace ban gaji da kallonki ba, idan kayi wanka sai kaci gaba ta rike hannunsa suka haura sama. Sai da yayi wanka ya shirya cikin Kaya marasa nauyi Hamida ta fesa Masa turaruka sannan suka fito tana gaba Yana bayanta yace yau baki zancen duwawu ba? Dariya Suka Yi gaba daya tace ai Shuru na maka amma Allah yau na gani da zaka sa kaya,Dariya ta bashi yace kina da aiki ashe a dining ya zauna tayi serving nasa ya fara ci yace sai kace girkin fadar sarkin garin nan,Dariya tayi tana rufe fuska har ya gama ci Yana Santi kala kala, Yana gamawa ya nutsu yace ban fada miki ba dazu Doctor ya kirani ya tambayeni yanayin da nake ji a jikina na fada Masa yace na warke na Zan iya sex ba matsala,Hamida ganin baya karya tace da gaske ? Kwarai yace tace to shike nan,yanda yayi Maganar ba Wasa shi yasa ta gaskata,suna haka Kiran Ammar ya shigo wayarsa ya daga tare da sawa a handsfree suka gaisa yace ya amarya? Karfa ka bari sabo da Doctor ya baka dama kace Kuma zaka Yi ta abu kullum kabi a Sannu sai a angwance amma Kar a wuce gona da iri,Nabeel harda cewa Inshaallah Yana dariya a ransa,suna gama Wayar ya kasa rufe bakinsa sai dariya yake idan Hamida ta kalle shi sai yace Ammar da abin dariya yake wai nabi a hankali Kar nayi ta abu, ai doctor yace Kar ya wuce sau daya Kuma kullum a hankali a hankali zan na yi,Hamida Shuru tayi tana dan tuna wahalar data Sha ranar farko amma baza ta iya cewa a'a ba tunda doctor yace ayi Kar ta Shiga hakkinsa,Sabo da murna Nabeel baki yaki rufuwa cinyarta ya buga ya akayi ne Pipina da kallo ta bishi ya fara latsa cinyarta tare da cewa wannan laushin fa?hmm yanzu dausayin zaka yiwa hidima yau? Kwarai kuwa Inshaallah To ai ya kamata a tambayi Mimi in ta Amince cewar Hamida,sirrin namu za a fadawa Mimi?Ina school idan nayi ciki fa? a haka zakije sai kice dama kina da aure, shuru tayi yace ya Kika Yi Shuru Wai Ina surutun ne? Uhm Kawai tace,ke ai baza kiji wahalar komai ba,Ina da infection banyi magani ba zaka dauka,ba damuwa Zan dauka sai mu dinga Shan maganin tare,mikewa yayi tsaye ya kashe kayan wutar ya jawo hannunta ta mike Suka haura sama, wanka zanje nayi ta furta, bamu dade da yin wanka ba no need Nan take ya Mata wata zazzafar runguma tare da zame ribbon dinta kasa gashinta ya warware tare da bazuwa gadon bayanta kissing nata ya shiga Yi a hankali ya dinga tsotsar bakinta tun suna Yi a hankali Suka koma Yi cikin zafi zafi jikinsa rawa ya fara sosai Hamida tace rikeni bazan iya tsaiwa ba saman bed suka fada ya bita kamar maye ya cire kayansa sai jinsa tayi ba kaya ko daya a jikinsa,Yana wani kissing nata sai ji tayi Yana rabata da kayan jikinta kasa hanashi tayi duk ta Zama wet ta makalkaleshi tana goga Masa gorar madararta manya a jikinsa Yana wani lumshe Ido Yana furta Mata kalamai itama haka. Boobs dinta ya Kama ya fara tsotsa Yana Wasa da daya Hamida Nishi ta fara tana kara tura Masa harda cewa My love tunda Baby bai Sha ba ci gaba da Shan abinka,Nabeel yace shi yaga duhu Pipina gaba ta kaini gobarar titi a jos,jikinta yake lasa Yana tsotsa har ya gangaro kasanta Hamida ta wangale cinya yana Kai bakisa wajen ta dinga ihu tana hauka Kamar sabuwar kamu,Zaka haukatani Lelena I love you,Dadi...Zan mutu...Nabeel wani yabonta yake yana Kara gigitata,yace zo kiwa bakinki Exercise,Hamida Dadi ya kwasheta tace ko Mene Zan maka ka koya min, Naja'atu ya tura Mata a baki a hankali Yana koya Mata ta dinga Masa amma tana Jin wahala idan ya danna kanta har kakarin amai takeyi abinka da ba a taba Yi ba, shi Kam ya tafi garinsu wani gurnani yake da Nishi Yana yi da sauri da sauri Hamida baki ya gaji sai da yaji kamar zai kawo sannan ya cire naja'atun ya koma Yi Mata Wasa da ita a dausayinta Hamida an saki jiki sai ihu take tana Dadi..Dadi...ta kamo hannunsa tare da dora shi saman gorar madara tana cewa yawwa Lelena ci gaba, I miss you...I miss you yake furta mata kafin ta ankare garin wasa Hamida ta jike iya jikewa Kawai ji tayi ya fara kokarin shigarta a hankali jikinsa ya fara rawa tun kafin ya kai ciki muryarsa ma bata fita ya kasa magana Sam sai gurnani da nishin Dadi,Hamida ce ta danji zafi bada yawa ba sabo da yanda dama sau daya aka taba Yi,haihuwa Kuma operation aka mata Ihu tayi Jin zafi tace wallahi har yau da zafi wajen,yace murya na rawa am sorry, yana binta a hankali ihun dadi Kawai yake Yi yana cewa awesome, you are honey..sweet...oh...sweet....Zaki kasheni Pipina Hamida tace ya Isa haka wlh da zafi ba wani sweet da zaka rudeni da shi, ko ta kanta bai bi ba yaci gaba da gashi, ga Matsalar Kuma haka kawai yaje abokinsa ya bashi Men power yasha bai San men power haka yake ba kwata kwata masu aure ne yaga suna ta sha shima yace zai Sha, yaki gajiya Kuma yaki ya kawo shi Kam wannan abu ya Masa dadi Kawai dadinsa yake kwasa,Hamida tana ta wani cije lips a banza dan bai San tanayi ba,tun tana dannewa tace wlh wayyo dausayina Zan mutu,yaki kulata sai ma wani Kara dagewa da yayi Hamida taja kwafa yafi sau goma tace gobe ma rana ce Nabeel yace yess Zaki Kara min Zan Kara goben kullum ma rana ce Zan ta yi,kirjinsa Hamida ta fara duka tana tureshi tare da sakin kuka tace baza ka Kara ba shi Kam yaji dadin da bai taba ji ba yace Zan Kara dole,Hamida ta saki ihu ganin ma Wai style zai canja,tana ban Saba ba yace Ina ai jarumi Kika aura,Hamida tace magani ka Sha wallahi ba wani jarumi haka yayi ta abu yaki kawowa,Pipi tace wlh sai da magani ake irin haka sai kace Yan blue film,Nabeel baya hayyacinsa maganin ya Masa karfi. Juyata yayi ya fara Mata wani Kalar Hamida ta kurma ihu wayyo Zan mutu zai kasheni,am sorry Kawai yace yaci gaba da harka,kamar Yana daukan tsinke haka yake sarrafata tana ta kuka ko a jikinsa sai da ya dauki lokaci me tsawo sannan ya kawo ai Kuwa Hamida taji Abu da yawa ya kankameta kamar kashinta zasu rugurguje,sai da ya huta sannan yace kiyi Hakuri ba laifina bane wani magani na karba aka bani ban San haka yake ba,Hamida tana cikin bargo tana goge hawayenta tace ba komai ai kaji dadi ko? Murmushi ya saki marar misaltuwa yace sosai da sosai ban taba Jin dadi a duniya irin wannan ba kin hadu wlh Pipina,karka sake Shan magani sai na saba kaji Inshaallah yau ma tsautsayi ne, sai yau Hamida tasan anyi kwanciyar aure da ita Tasha wahalar da bata San da ita ba shi kuwa sai wani nishadi yake Yana murna da farin ciki,Hamida tace nafi Basma dadi? Yace wa yake zancen wannan Kuma kema ai Kinga sheda yanda na haukace Miki, Hamida Shuru tayi tana farin ciki a ranta tayi zarra, shi ya taimaka Mata ta gasa jikinta tayi wanka tare da tsarkake jikinta,shima haka sannan ya canja bedsheet wancan ya rigada ya baci ga jinin raunin da Hamida ta ji,da kansa ya wanke ya shanya,lokacin Hamida tuni ma tayi baccin wahala a gefen bed din ta kwanta can karshen gado,Dariya ta bashi ya jawota jikinsa ya makaleta a jikinsa shima bacci me dadi ya kwashe shi. Cikin dare Basma tasan yanda tayi ta shigo har bedroom kasancewar basu sawa kofa key ba da bindigarta ta saita Kan Hamida sannan ta bigi jikin gadon lokaci guda suka farka mamaki ya Kama su Nabeel ya kunna light Basma ya gani da bindiga tana kokarin harbe Hamida,Hamida ta kalleta tace me na miki kike kokarin kashe ni Muna tsaka da yiwa soyayya hidima? Murmushin takaici Basma tayi tace to kinyi na karshe yau sai dai kiyi a lahira,Nabeel kasa motsi yayi ya gama tsorata Kar ta harbe Masa Hamidansa yace akan ki kashe ta gwara ki harbe ni,Basma tace nice nake bibiyarki duk inda Kika ga Yan daba na binki nice nake sa su farautar rayuwarki,sannan har wasu Yan polio na turo suyi min aiki a kanki hakan bata samu ba yanzu da kaina zanyi aikin,Kuma ki sani nice wacce nasa aka kashe Basma matar Nabeel ta farko Kuma na dauki alkawarin ganin bayanki yau ba sai gobe ba sabo da kin aure min farin cikina Ni baya so na ke yake kauna,to ana yiwa Allah dole ne Allah baiyi da ke ba sai kice sai na aureki dole ki sani bana kaunarki duk abinda Zaki kiyi Allah ya fiki jahila wacce iliminta bai kara Mata komai ba Kuma abinda Kika shuka sai kin girba cewar Nabeel. Dariya tayi tace kana tunanin zaka iya daureni? to nafi karfin hukuma na gagaresu ka tambaya kaji wa Zan aura a kasar Nan,daga bidinga tayi tare da sa Hannu Kan mukunnin bullet a saitin Kan Hamida Ta bayanta taji Magana kamar muryar Alhaji Sa'eedu yace you are under arrest ajiye bindigar,a tsorace ta juyo ai arba tayi da Yan Sanda sun Kai su biyar ga Ammar ga Kuma Alhaji Sa'eedu,jikin Basma ne ya fara bari bata San Sanda ta saki bindigarta ba tasan ta shiga Hannu ihu ta kurma ta dira tsalle ta dirga a bed din su Hamida tare da shako Hamida,Mari Nabeel ya shiga kwasheta da shi ta ko Ina dama da hagu ta saki Hamida ta rusa kuka Hamida ta sake wanketa da Mari ta hankadota kasa,Basma tace ubanki yaci uwarki,da uwarki zai ci Hamida ta bata amsa,ai uwata zai c.....kafin ta karasa Nabeel ya rufe Mata baki yasan halin Hamida yanzu sai tayi loosing control tayi barin zance. Ammar Dariya ta cika Masa ciki ta Hamida da Nabeel, Alhaji Sa'eedu ne ya kalli Basma dake yashe a kasa yace mahaukaciya to bari in fada Miki barrister ne ni lauyan Alhaji Abbas ne baban Basma yarsa,dama Muna zarginki shi yasa na shigo rayuwarki da hadin gwiwar Yan Sanda wayarsa ya zaro yace komai da kikayi Yana cikin Nan hujja tana Nan Wanda da bakinki kike fada,sannan Ammar da Nabeel da sauran masu ruwa da tsaki duk sun San wannan binciken duk inda Kika sa kafa ko Kika tura Yan daba mun San da komai muma Muna bibiyarku,Kuma ki sani dukkan Wanda kikayi harkalla da su suna Hannu an kamasu har Yan taadda na lagos,da Wanda ya siyar miki bindiga ki sani kawarki Amal wacce ke baki shawara ita ta fara sanar Mana duk abinda kike ciki shi yasa Muka bullo miki ta haka yanda zamu kamaki a hannu Kuma kawar taki Amal itace wacce Ammar Zai aura,Hamida taji dadi sabo da ita bata San ana wannan Shirin ba,Hamida ta kalli Barrister tace Kuma idan an Shiga kotu a bi Mana hakkinmu Wanda Muna cikin yiwa soyayya hidima ta Fado mana daki a tabbatar an kasheta itama kamar yanda ta kashe dan Adam ku jata ku tafi da ita,Nan Yan Sanda Suka tasa keyar Basma gab da zasu bar dakin Hamida tace Yar Basmeme a gaida Yan gidan yari zanzo na muku rijiyar tuka tuka sadaka,Basma ta juyo ta harari Hamida, Pipi tace yo ya zakiyi dani kafin Allah ai ni sai ta Allah Pipi sai Lelenta haka Lele sai Pipinsa Kinga Lelen Pipi ko kice Pipin lele,gidan Lelen Pipi ko gidan Pipin Lele Shakiran Nigeria Suna fita Nabeel ya sawa kofa key yace sai gobe mun hadu a station na gode sosai ya koma wajen Pipinsa ta juya ta kankame shi harda kukan kisisina tana ta shagwaba da kuka tare da cewa da tuni na bakunci lahira a danna ni cikin kabari wata ta kwace min Naja'atuta ai wlh da fatalwa Zan dinga Yi muku duk wacce ta aureka taga ta kanta akan Naja'atu sai na dinga fatalwa kullum sai nazo cikin dare babu ita ba Naja ko Nima nayi maka ta Basma inzo a fatalwa na karasa girbe maka ita,Nabeel Yana ta dariya yace Kika dinga kuka Kika ce dazu dazu bakya sonta? ai ni na San zan so ta nan gaba zan karbeta Hannu bibiyu na dinga karramata,ka sake ma duk shekara sai na hada party na bikin karrama Naja'atu,yace yanzu kin san dole har shiga kotu sai munje har a gama case din,Allah ya kaimu cewar Hamida har alkali Zan fadawa ta kalli jar takashina Ina bacci,Nabeel yace no...hhhh Dariya tayi tace Wasa nake Kai dai, har bacci ya kwashe su Hamida ta daina kukan wahalar da ya bata sai dariya take bashi. Ayi Hakuri fans ban samu nutsuwa ba kwana biyu,bana so Kuma nayi typing ba nutsuwa za a samu matsala shi yasa Indai kuka ga banyi posting ba to akwai dalili a Kara hakuri Masu sharhi Ina kaunarku ko groups din da bana ciki wasu suna min screen shot Ina gani Ina Matukar godiya a ci gaba da gashi Idan ba a comment bama iya typing yanda ya kamata,Sharhinku shike samu a Hanya AUTA UMMI DEEJAT BESTYN BEELAT UMMI NAJWA kullum Ina godiya da kulawa AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 46-50 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Aynah Mum Islam Rufaidaahmuhammad Momyn Sultan Nafisa Musa Oum Bahiyya Ikeen Mama Safeeyah Bature Ummu Shurhabeel Nernah Sadiya H Nana F Mbello Jinjina gareku Queen🫅Meenat MHD Aynah Farida Yusuf Bashir Maman Samha Ummin Sadeeq Ummu Shafa'at Washe gari asubar fari ya dan fara tashin Hamida yin duniya tana jinsa taki tashi dan Kar yace taje makaranta bayan Kuma ya Mata illa a dausayi,tun Yana Yi ta lallama Pipina har ya gaji ya jijjigata tare da mikar da ita zaune Hamida ta fashe da kukan karya wayyo dausayina,wayyo ingallo na bazan iya tafiya ba,Nabeel yace in Zaki tashi ki tashi yau ko a baro ake turaki sai kinje school,haushin Lele ya kamata tace zaka dawo na rantse sai na rama,Yana dariya ya dauketa zuwa toilet tayi wanka da komai na bukata shima haka,Bayan ya ja su Sallah kitchen ya shiga ya soya musu kwai da dankali sai tea har bedroom dinsa ya kawo Mata a saman gadon taci ta koshi shima haka sai Fushi takeyi yace Kinga 7:30am tashi kisa uniform na ajiyeki a school,harararsa tayi tana kunkuni ta mike ta dakko uniform amma duk da Haka tafiyarta ta dan canja,da kyar tasa uniform ta fito,school bag din ya daukar Mata ya rigata fita Yana jiranta a jikin mota tana tafiya a hankali tana kumburi tafi ya mata Pipi takwa takwa,Dariya ta saki ba shiri ta tuna Wai ramawa yayi,Mota ya bude mata ta Shiga ya rufe sannan ya zaga ya Shiga ya bar gidan. Yana driving bata Yi magana ba sai ma gyangyandi da takeyi,Cinyarta ya dan latsa ta bude Ido ba shiri ta kalle shi ta sake rufe idonta,habarta ya taba tare da maida hankalinsa Kan driving dinsa,bata kulashi ba yace ba labarai ne yau? Yana gidan radio ta furta,har yayi parking a school din bata Yi magana ba yace ayi karatu da Kyau sannan a kular min da Yar bulbula me bulbulo ruwa Ina dawowa Zan kara,Murmushi tayi Kawai tace dausayin Kuma ka maida shi Yar bulbula ta juya ta wuce ciki sannan shima ya wuce,tana Shiga aji Yan ajin suke ta tambayar Hamida yayanta ne ko wa? Hamida tace mijina ne Ina da aure baku sani ba,Suka dinga mamaki matan Suka ce amma kina jinmu muna Maganar aure kika mana Shuru,ance muku ni yarinya ce irinku me kuka sani na rayuwar duniya,Yanzu kema Kuna buga harka ana Miki Dan Allah Wai da dadi? Hamida ta kallesu tace da tabewa ta gama samuna ace na zauna Ina maganar aure da ku yara ko manya basu Isa suji sirrin mijina ba,ga novels Nan kuci gaba da karanta abinku a Nan zaku ji,Kwanciya tayi ta kyalesu har teacher ya shigo,a ranar sai da Yan makaranta kaf Suka San Hamida tana da aure me kawota Kuma shine mijinta. Ana tashinsu yazo daukanta har da siya Masa tsamiyar biri da gyada dafaffiya kullum Nabeel sai an kawo Masa tsarabar school,tana Shiga motar ta Mika Masa tare da cewa ga vitamin c din bahaushe tsamiyar biri,Murmushi yayi Yana kallonta yace thanks da me Kuma? Gyda wanne zaka Fara ci? Yace a fara bani gyadar Yana driving tana barewa ta zuba Masa a baki sai taga sun nufi Police station, tace to jarabar report za a dauka,akwai wasu tambayoyi da za ayi Mana kafin a tura case din kotu,okay tace Kawai,suna Isa can suka shiga tare da basu wajen Zama,Dpo yasa aka fito da Basma wacce tun ba aje ko Ina ba taji jiki da duka,harara ta watsawa Hamida itafa baza ta taba saduda ba sai dai a kashe ta,Babban dan Sandan ya kalli Hamida yace madam Muna so ki fada Mana duk abinda Kika sani me dame Kika gani su waye Suka dinga bibiyarki?Hamida tace Bismillahi yanzu Oga in banda Basma shafin bayan rigace...wata Sha mu dora ce... nifa ba nice ta farko ba a wajensa,ita wannan me Ido Kamar matsefatar itace yarinyarsa ta farko Allah baiyi an aureta ba aka auri daya Basma wacce itace matarsa kaga Dan taji haushi ma ba laifi nice fa ta uku dorin dosano kunu bayan ludayi daga baya nazo nayi wuuf da shi tana ta hauka da bakin kishi,Ni da yayiwa babban laifi ma banji haushi ba sai ita . Basma tace ke da ya Miki cikin shege munafuka duk wacce miji ya Mata ciki baya taba Aurenta a kasar Nan,Wata Yar Sanda ce ta kwashe Basma da Mari tace ke aka tambaya,DPO yace naji Maganar ciki Nabeel ya fada min komai na gamsu amma a tsarinmu sai munji ta bakin kowa kafin muje kotu. Hamida ta kalli Nabeel yace fada komai ba matsala,tace to Oga ni dai farko aiki ne ya kaishi garinmu aikin kwalta,bana son maranta a rayuwata Kuma har yau wlh sabo da Lelena nake karatu badan ra'ayina ba in fada maka gaskiya,dpo yace waye Lele? mijina abin kaunata gashi nan duk duniya bani da sama da shi sabo da har dubu Daya daya yake bani kullum akan naje makaranta Yana lallabani,har Muka dan saba,ta dole na Masa sai naje masaukinsa yaki yarda na dinga kuka kuka haka ya kaini, bani da hankali a lokacin ga rashin ilimi ga kauyanci ga wawanci Ina ta zuwa ashe mutuminka yakan da kora abar ta kasar turai wato giya,Nabeel dariya yayi dpo ma haka, tace yo ba sai naga duniya zata kife ba kurba daya nayi,to karshen zance dai nan...Nan....Nan....Kuma...ahm....ae...kasa karasawa tayi ta rasa me zata ce dpo yace muna rubutawa fa duk wannan bayanin sai kinyi a kotu,Hamida tace dan darajar Allah dpo ka goge wlh ana sanin munyi Zina bulala tamanin zamu karba, ni gaskiya ba wani Zina da mukayi,dpo yace kwantar da hankakinki bamu da Hadi da kunyi Zina ko baku Yi ba Kawai iya saninki da shi ba wani Maganar abinda ya faru kinji ko idan ma ta fada a kotu kunyi abinda ya faru ya rigada ya faru shi yasa duk abinda Allah ya hana to karka aikata to gashi tunda ita ta sani sai ta fada a can amma wannan baya cikin shariar da za a gabatar a kotu abinda ake tuhuma akai akan abin kadai za ayi magana ba Maganar wani ciki ko wani abu, in ance ki fadi saninki da shi karki kawo Maganar ciki kin gane ko? Hamida tace ae,Basma tace ai wallahi sai na fada Ni ai har farin duwawunsa tace Mana ta gani,Hamida tace yo dana gani sai akai me yanzu ba gata Ina gani a cikin kwanciyar hankali ba ranar ma ba ita na gani ba ruwan sama akeyi aka Yi walkiya hasken walkiya ne Ashe dpo ya dinga dariya yace to yanzu ci gaba da bayani an wuce wajen hotel Hamida ta bada labari Karshe ta nuna Nabeel tace bawan Allah nan ba ci min mutuncin da baiyi ba,ai dai kema Kinga ba a son raina ba Kuma na gyara cewar Nabeel,Haka aka Kira yayar Basma da mijinta sunyi kuka Jin abinda ta aikata,Yayar Basma tace wlh kinwa kanki kin cuce mu kije duk abinda hukunci ya yanke a miki,mutane iri iri Wanda Suka shafi case din sai Suma Suka bada nasu report daga Nan aka Mika Basma kotu tare da kwararan hujjoji. Hamida suna dawowa gida yace ta shirya Islamiyya haka taje Islamiyya ta dawo,tana dawowa ta duba ko ina bata ga lele ba tana ta kwala masa kira Lelena...Leles...lelewas lelewan Pipi shuru ba Lele, Bedroom ta duba ta ganshi a kwance kamar bacci yake,ko uniform bata cireba ta haura saman bed din tace Lelena....Shuru sai baccinsa yake a nutse,tashi tayi da niyyar sauka taji ya riketa Kam Yana dariya tace kaci abinci? ke nake jira ki dafa mana amma Nasha fresh milk yanzu dan Allah ki taimaka ki bani dausayi na danyi Hidima,Hamida kwabe Fuska tayi tace wlh zafi ban warke ba,yace Milk na Sha bazan iya hakuri ba, wayo tayi zata gudu ya cafkota ya Mata mugun riko,ihu ta saki da kuka na Shiga Uku zai kasheni,duk yanda yaso ta bashi hadin Kai taki, yayi lallaba har ya gaji taki yarda,ta karfi ya Shiga cire Mata uniform din,Hamida kuka wiwi tana wayyo ka taimaki Yar makaranta,Yar makaranta ce ni Nabeel shima yace ki taimaki Engineer dan Allah,wayyo mugu mugu mugu.....sai kace za a yankata ta yo kasa ya rike hannunta ta rike jikin bed tana so ta kwace hannunta amma ta kasa sai da ya gajiyar da ita hawaye ke zubar mata kawai,yace haba Pipina ke da kika ce har fatalwa Zaki dinga Yi a kanta,Hamida da sauri tace bazanyi ba idan na mutu du Zan mutu a binne ni gaba daya bazan dawo ba,yace to party fa da Zaki dinga hada Mata nasha juice kala kala,Ruwan madaci Zan baka wlh bana so da zafi Hamida kuka take Kamar ba gobe amma ko tausayi,Hamida sai lokacin ta kula dama ita Kawai yake jira Ashe ba kwayar Kaya a jikinsa a haka ya kwanta cikin bargo, Naja'atu ta gani ta mike ta saki sabon kuka wayyo Allahna naga ta kaina ni Hamida ya zanyi Adamawa Zan koma Nabeel bai San inda hankalinsa yake ba tunda yayi arba da surar Hamida kamar ya dauki tsinke haka ya dawo da ita saman bed,tana ta kuka ya hade bakinsa da nata yana Sha Kamar zai cinyeta haka yake bin sassan jikinta,ya tsotsi Nan ya lashi nan ya murza can ko Ina aiki yake a jikin Hamida Wanda tashin Hankalin da take ciki yasa bata karbar sakon,Gorar Madara yabi da wani irin salo na musamman Nan Hamida ta danyi Shuru ta fara karban sakon,tuni ta fara jikewa tana dan maida Masa martani,a Haka ya shammaceta ya shigeta,zafi take ji sabo da bata warke ba Sam ya sake dole taji azaba,kuka wiwi take tana rokonsa ya daina amma nabeel ko a jikinsa gurzarta yake sosai, Hamida bata San tun asali Lelenta jarababbe bane shi yasa ya damu sai an Masa aure,Yana yi Yana ce Mata in na kyaleki raguwa Zaki Zama gwara ki Saba a haka,Hamida da masifa tace idan lokacin sabon yayi sai ka fada min karka isheni Malam,duk ka gallabeni jiya kayi yau ka sake sai kwashe ni kake Yi ni wlh baza....ihu ta saki tare da sakin kuka Zaka kasheni wlh Lele,Lele Ina yana can ya lula bai san Ina yake ba sai da ya samu nutsuwa sannan ya koma gefen Hamida ya kankameta Yana Jin wani kaunarta ashe mirgayya Basma Kawai wahalar banza yake Sha,sai yanzu yasan Yana da Mata,Cikinta ta kifa ta kwanta tana ta kuka. Nabeel ya rasa me zai ce gaskiya bai kyauta ba mazaunanta da yake ta kallo manya su ya shafa yace so Sorry my Pipi dadinki ne yayi yawa bana iya hakura idan na ganki,Hamida bata kulashi ba,Mazaunan ya dan latsa yace ga jar abar a nan,Murmushi tayi a boye ya bata kunya ita ta manta ba bata rufe ba,tana shesheka tace rufe min abata Nabeel Yana ta nishadi yace Nima ga tawa farar ki rama,kin kulashi tayi Kamar Yana kwaben fulawa hake yake ta lagude Mazaunan Hamida ba shiri ta juyo ta saka hijab dinta har kasa ta sauka a saman bed din cikin Fushi cafko ta yayi da karfi yace second round,wani ihu ta saki da karaji ta Fadi ta fara birgima tana kururwa da sauri yace Wasa nake Wasa nake Yana dariya ba shiri ta mike ta fice da sauri ta bar dakin. Ranar Habiba yasa ta musu abinci har lokacin Hamida tsoro take yana Shiga bedroom dinta sai ta mike ta tada Sallah sai ya fita zata sallame,da dare ma Yana Shiga ya iske tayi Shirin bacci cikin wasu kayan bacci masu Jan hankali,a ransa yace da zata yarda ai da na Kara da Kansa yaba Kansa amsa bari dai Kar na cutar da ita na hakura,Sakina ce ta kirata a waya,Hamida ta dauka ganin haka sai Nabeel ya bar room din ko da wani sirri da zasuyi abu na kawaye,Sakina tace kawas ya najiki haka haka? Hamida tayi Murmushi tace ba komai Sakina ya kike ya yaronmu? Duk lafiya kowa, kin gwada maganin Kuwa da nace ki Sha shekaran jiya? Hamida tace nasha wallahi Sakina Kuma sai na sha a sa'a,heeee Sakina tayi shewa tace kice kinji wuta,kina gani Zan mutu Ni wlh bazan sake Sha ba,ke banza ce yanzu idan Kika Kara Maggi ai shine babban abin farantawa me gida rai wlh ki dage karma kiyi Sanya da gyara wajen nan shine mutuncinki a idonsa,ai yanzu ya zame Miki gum tunda kin Kara Maggi,Hamida ta saki kuka tace dole ashe Mata idan ba abinci su ragargaje su lalace, ashe shi yasa ki duba su Alawiyya ta Bayan gidanmu yarinya sa'ar mu amma ta tsufa sai hakora sababbi da suka yo tsiri gaba sunyi cakoko a gaba yarinya me kyau da bata da hakora amma irin wannan abu ba dole mace tayi hokoran gaba ba,ga haihuwa ga ciki ga goyo ace baka samun cima me kyau Sakina ka gama yawo Allah ya rabani da hakoran gaba,Sakina ta dinga dariya tace yanzu Kika San abin kenan Zaki Saba ne kiyi Hakuri karki dinga Fushi da shi,kina hauka Hamida wannan Yara ke yi mu ai mun girma,idan kina Fushi zai dan samu damuwa daurewa akeyi,Hamida tace inda kisan zan yage fa ni Kam na saduda,Sakina abin bana Wasa bane wlh,Sakina tace ai kamar doki haka suke komawa Astagafirilla ba kyau fada dai Hamida tace ai Bayan doki ma Sai an Kara da bijimin sa,Sakina tace ai yanzu zaki San farar takashi,farin sani ma ashe da ba abinda na gani ni ki daina tuna min Hamida harda kuka sabo,Sakina tana ta dariya tace a daure kowa da Haka ya Saba ki karbi abarki Hannu bibiyu, bana so bazan karbeta ba cewar Hamida,Sakina dai tace ah mu kaunar tamu muke ni yanzu in ba ita ai ba rayuwa,sai ki ta yi jarababba mayya cewar Pipi. Hamida haka Suka gama waya yanda Sakina ta sake dan koya Mata yanda zata kula da kanta haka tayi harda Kira likitar da Nabeel ya hada su ta kawo Mata magunguna ta fada Mata Matsalar, ta Sha abinta tayi wanka ta sake gasa jikinta da ruwan ganyen magariya tana fitowa daure da towel tace gwara nayi na samu sauki kafin ya dawo yace zai Kara naga baida hakuri. Fitowa tayi sanye cikin kayan baccinta komai ana gani,Nabeel Yana Palo ganinta haka hankalinsa ya tashi sosai ji yake kamar ya cinyeta,tsayawa Hamida tayi daga nesa taki karasawa tace Mene? yace kari,Pipi tace zance kake haba Lele Wai me ya sameka ne ko so kake hakorana na gaba su yo waje ? Dariya ta bashi sosai, taci gaba da cewa nice fa Pipinka kamar baka Sanni ba Kai Lelena dan Allah kayi Hakuri sai na Sha maka da baki please kullum mudinga Mouth xxx ko Mene Zan maka ka bari Yar bulbula ta warke,Murmushi ya saki yace ba matsala Pipina karki damu zanyi Hakuri Inshaallah kece kin fiye dadi da yawa. Jikinsa ta koma ta kwanta ya fara shashafata Yana murzata bata hanashi ba tasan halinsa sai yace zaiyi. Yau lafiya suka yi bacci me dadi bai ce zai Kara ba,amma Yana dawowa daga sallar asuba tana Kan Sallaya yace da wuri zanje wurin aiki yau akwai aikin da Zan nunawa yarana sai ki driving kanki to school kinji,to tace tana kallonsa yanda yake ta kallon kirjinta da bata sa bra ba,tace Lelena yaya ayi na bakin ne? Dariya ta bashi Wai da sauri zata tareshi tun kafin yace zaije dausayi,kafin yayi magana ma ta fara shafa Masa gemu tare da furta I Love you Lelena,Sai kace tsohon zaki haka jikinsa ya fara rawa ya fara goge Mata hadda da salonsa,Gorar Madara ya Shiga yamutsawa Yana lailaya su Suka fada saman bed,Hamida anyi abin Kai tsora yasa ana ta nunawa Lele kauna Yana ta Mata sambatu,Gorar Madara ya Kai bakinsa Yana lalube Hamida tace tsaya ni ungo ta sa Masa a baki ka ishi mutum yaro baya gajiya da tsotso Lele ba shiri ya tsaya Yana ta dariya, Murmushi Kawai tayi bata kauna yace zaiyi xxx yanzu babu lafiya a wajen,Ita kanta da ta bada hadin Kai sai taji tana Jin dadin abin sosai tana kwanciya a jikinsa duk yaji laimarta,Nabeel yaji kwadayin wajen yace gajimare sarkin ruwa ana dan abu sai ki saki girgije, kiyi sauri ki Saba please,Haka Suka kasance cikin farantawa juna rai ta tsaya sosai ta Masa da bakinta Kuma ya samu gamsuwa matuka. Breakfast ta hada musu bayan sunyi wanka tare Suka ci abinci ya fita da sauri ya sake dawowa ya Mata kiss ya fita ya hau daya jar motar tasa,ita Kuma a gurguje ta gyara dakinta da nasa har toilet tayi Shirin school har ta makara ma, Habiba tayiwa sallama ta Shiga farar motarsa ta tuka kanta zuwa school,yau Yan makaranta sai Suka ga Hamida da kanta ta lailayo mota tazo school har malamai sai wani girmamata akeyi. Hamida bayan sun tashi a school har gida ta samu Affa bayan sun gaisa tace Affa dan Allah ka min Hanya a wajen Kawu senator na kawo takardun Yaya Sulaiman da ya gama karatu da takardun Karima yayata ko teaching ne a sama musu a Adamawa idan da hali, Affa yace kinyi hankali Hamida amma Yaya Ubaidu shike da babbar hanya a State dinku kice a kawo takardun wanne mataki suke? Hamida tace degree sukayi,yace mashaallah ki kawo sai na yiwa Yaya magana,godiya tayi ta yiwa Mimi sallama ta tuka mota sai gida dama ta fadawa Lele ya sani. Bayan kwana Uku Sulaiman ya Aiko da takardunsa dana Karima,aka bawa Affa shima ya turawa Yaya Ubaidu. Kwana Uku tsakani Nabeel ya bar Hamida ta huta sosai da sosai,da dare suna kwance ya fara murzata tace na baki ko? ae yace Mata ta saki jiki suna ta buga love suna sarrafa juna Kawai ya shammaceta ya shiga,a tare Suka saki ihu bata ji zafi ba sai kadan Yana yi tana dan Jin dadi kasancewar an taba Yi Mata da dadewa Wanda shine sanadin samun cikinta, ...sai Nishi suke suna kukan dadi,Hamida tana Lele zafi ci gaba da zafi wayyo dadi...Lele Kamar zai kacalcalata haka ya Mata wannan Karon Kam yace Pipina cikin Diary zan rubuta wannan rana duk shekara sai nayi murnar zagayowarta,Hamida tana kwalla tace ansha fama maza rubutata yau ranar farko dana Fara Enjoying,Hamida harda kallo Naja'atu tace ke ashe haka kike,no wonder ko wacce matar aure ana zancen Naja'atu sai ta saki shewa bata bakin ciki ba dama a zageta sai Matan aure ko wacce munafuka za a Saba ne ayi ta wani kareta ba a son laifinta,Nabeel shi murnarsa daya yau ya birge Hamida taji dadinsa wow abin yau ya Masa dadi. Da asuba ma da Nabeel ya nema Hamida bata hana ba. Haka Hamida da Nabeel suke kwasar amarci kullum sai soyayya da kaunar juna,Affa ne ya Kirata ya bata Offer din Karima a ministry of Land and Housing a cikin garin Adamawa inda take aure,Hamida ta dinga Murna,ya bata ta Sulaiman lecturing a wata college of education,Hamida ta dinga godiya Mimi tace to Kinga Ashe kece silar samun aikinsu,sunyi karatu tuni amma ke da kika ki yi ake dukanki yau kece Kika samo musu aikinyi ikon Allah kenan,Hamida tace wlh Mimi sai gashi ko ta Nan na godewa Allah ko banyi karatu ba zasu iya rikeni kowa da baiwarsa,Mimi tace Inshaallah ma zakiyi Hamida ba a San me Zaki Zama ba,ai ni nafi so na karanci Harkar Kashi gyaran Kashi bone,Mimi Ina gama secondary Zan karanci Bonology, Bone Kashi kenan Kinga Bonology,Mimi tayi dariya tace ke dai Hamida naga Sanda Zaki canja,Hamida tace haba ai na gama canjawa na gama hankali yanzu da ace da ne ai da tuni na tonawa Lele asiri amma Kinga bana fadan komai,Mimi tace me kike nufi ba dai ya karya dokar likita ba? Baras ma Kuwa Mimi ya rukurkusheta ma ai yace doctor ne yace Hamida ana fada harda rufe Ido da gyalen Abaya Wai kunya,Mimi ranta ya baci Nan take ta kwalawa Affa Kira taje har dakinsa ta fada masa,Affa yace sai ki rabu da shi Wai likitan Allah ne,ki kyale yaro ya sakata ya wala kina ga abinda ya faru a baya naki Masa aure karshe ya dakko Mana abin kunya Ni Ina son ganin jikokina Hamida Zan dakko ta dawo Nan,Hamida tana Jin duk abinda suke cewa da sauri ta fice ta shiga mota ta tuka ta bar gidan tana cewa haka Kawai muna soyayyarmu a rabani da Naja bazai yuwu ba ai Ni yanzu bazan iya kwana Ni kadai ba,Lelena kullum ya zuba min Kokonsa ace wani baza ayi ba baza ta sabu ba. Mimi sai Jin tashin motar Hamida sukayi Affa yace to kinji dai ko kunya bakya ji Maganar Naja'atu a Gaban suruka,Dariya Mimi tayi tace wato kaima ka samu inkiyar su Nabeel ko ka koya,Affa yace ai mune manyan kwari kema fa tsohuwa dake sonta kike bare matasa,Mimi tayi shuru dai bata ce kamai ba. Yau monday yau ne za a fara Zama a kotu sauraren Karar Basma da Alhaji Abbas ya shigar akan kashe Masa yarinya da tayi,Su Hamida da duk wani me ruwa da tsaki sun hallara. Masu Sharhi kunyi sanyi fa Zan iya tafiya hutu🤣 AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 51-55 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Mom Abdallah Teemas collection Khadija Ismail Khadija Saleh Innah Habee Murjanatou UomuFarhan Umma Halliru Umma Zahrau Sani Bilkisu Tabari Nafeesa Nuhu Mamie Imam Umma Musaa (Queen Hernah) Hamida zaune take gefen Nabeel kana gani kaga masoyan asali idan suka kalli juna sai su sakarwa juna murmushi,Basma kawota akayi tayi baki ta wani rame ta lalace,Hamida ta radawa Lele da badan ta nuna min bindiga ba da na tausaya Mata da yanzu sai naji tausayinta amma yanzu naki harda makale kafada,Nabeel yace ba a magana fa za ayi waje damu,Shuru sukayi Hamida ta sake Yi Masa rada kana missing Dina Kuwa yi sauri ka fada min kafin a tarfa mu,Lele shima ya karkato da rada yace sai a nan Zaki tambayeni ba a surutu fa,I miss you shike nan,Hamida ta dan kalleshi tare da cewa me too to muyi Shuru cikin rada duk ta fada. Sharia aka gabatar da hujjoji komai a gaban Alkali, Alkali yace kinji duk hujjojin da aka gabatar kin gamsu ke Kika aikata Basma tace kwarai kuwa nice na aikata Kuma har yanzu Ina Kan bakana,Haka su Nabeel kowa sai da ya bada sheda Yan daba da komai sun tabbatar Basma ce,Hamida a kotu tayi hankali ta bada shedar iya abinda ta sani,duk da haka Alkali yace sai Nan da sati biyu za a dawo bayan an sake bincike Kuma za a Kai Basma gwajin kwakwalwa,Suna fitowa Nabeel ya dauki kanwarsa Fadila wacce ya dade rabonsa da ya ganta sai dai waya tana can Abuja gidan Senator,Dariya takeyi tace Yaya an kawoni Hutu munyi Hutu gidanka Zan zauna,yace to ga me gidan Nan ai,Hamida dake yin magana da su Anwar suna ta surutu ta juyo tace ga Fadilanmu ga Fadilanmu,Fadila ta dinga dariya taje wajenta tare da rike Hannun Hamida,Mimi ce ta Mika musu jakar kayanta da aka kawota da su tace kuje da ita can dama ai tafi son Yayanta,Anwar yace sai munzo gidan kafin mu wuce tace Ina jira,Fadila tana zaune a cinyar Nabeel,Hamida itace ke driving,Anwar yace ashe mutuniyar an goge,Dariya Hamida tayi tare da danna musu mahaukacin horn sai da Mimi ta Mata dakuwa sannan taja mota Suka nufi gida. Bayan sun koma gida wanka ta yiwa Fadila ta canja Mata Kaya marasa nauyi Yan kanti,itama wanka tayi ta hade cikin Atamfa Riga da skert ta Sha kyau,Me zakici Fadila? Fadila tace koma Mene Aunty Ina ci ai,taliya da Miya ta zuba Mata Tasha nama ga lemo da ruwa su Fadila an Kara girma da kanta taci bata bata jikinta ba,suna kallo tana cin abinci,Nabeel ya fito Yana baza kamshi cikin jallabiyya arsh,Zama yayi gefen Hamida lokacin Fadila tana kasa ta kwanta tana kallo,Nabeel sai ya faki idon Fadila sannan yake wani shafa Gorar Madarar Hamida,Hamida tana kwance a cinyarsa,Harda wani cewa Fadilata Kai cartoon chanel mu kalla,to ta furta da sauri ta kamo Channel hankalinta ya tafi gaba daya kallon cartoon. Har dare Hamida sannan ta musu girki Suka ci ta yiwa Fadila Shirin bacci itama ta shirya cikin kayan baccinta masu kyau,Fadila ta kwantar a bed dinta amma ta saka fitina ita a wajen Yaya Nabeel dinta zata kwana,Hamida tace a ranta yanzu ya Zama nawa yarinya,hannunta ta rike muje to na kaiki dakinsa,Lokacin Yana danna laptop suka shigo yasan dama haka zata faru, Fadila tace Yaya a wajenka Zan dinga kwana yace to Fadila hau bed,Kawo min tea yace da Hamida Hamida taje ta hado Masa tea lokacin Fadila ta dawo jikin Nabeel ta kwanta sai surutu takeyi Taki bacci,har ya gama abinda yake tana surutu Hamida tana gefen bed tana latsa waya,Fadila ya daura a saman bed Yana mata Wasa tana ta dariya kamar me, Hamida tana jinsu har 12am Fadila taki bacci Nabeel yace maza kiyi bacci,Fadila tace Aunty ke baza ki kwanta ba,Murmushi Hamida tayi tace yanzu Kuwa ta koma gefe ta kwanta itama,Nabeel Yana gefe ansa Fadila a tsakiya ta makalkale Nabeel sai gani sukayi tayi bacci,Nabeel yace Yi Mata shimfida a kasa,Hamida tace akwai sanyi ka sata a bayanka Kawai Aka tura Fadila can karshen gado Hamida ta koma jikinsa ta shige Yana shafa kanta Yana lumshe Ido zaiyi bacci yau an gaji bacci za ayi Hamida tace bata San zance ba, bacci ya fara daukansa ta fara kissing dinsa sai kace mayya,idonsa ya bude a hankali ya kalleta Kawai jaraba ke addabarta,kayi min Hidima Lelena Ido ya zaro bata taba tambaya ba sai yau yace to an gama ni dama Hakurin dole nayi, Suka Fara sarrafa juna Nabeel ya rude ya zauce sabo da irin sakonnin da take aika Masa bazai iya hakura ba,Pipi kullum gogewa takeyi da Harkar yau Kam itace me riding dinsa itace a samansa kullum sai anyi sabon style,ihu take sun manta Fadila na dakin, sai da sukaji mutsu mutsunta Kamar zata farka Nabeel ya maza ya toshewa Hamida baki da tafin hannunsa har Suka samu gamsuwa bai bar bakinta a bude ba bare tayi ihu,suna kwance Fadila ta tashi zumbur tana ruwa Zan Sha,Hamida suka fada cikin bargo ba shiri suka Yi Kamar suna bacci. Fadila ta tsallako tsakiyarsu ta fashe da kuka tana tashin Hamida wai Auntyn Lele ruwa,Nabeel yace dan ubanki Aunty na ce? nine Yayanta dai kanwar Lele ce,Hamida ta rada masa Miko min kayana na saka cikin duhu ya jawo Riga da wondon baccinsa ya Miko Haka ta zurma su Kawai ta Mike tare da kunna haske,Fadila ta bude Ido ta tashi zaune ta kyalkyale da dariya Aunty kayan Yaya ne fa kin manta,Nabeel yace ke zanci ubanki Kuma kina Shan ruwa kiyi bacci ko na ballaki,Fadila ta cuno baki gaba Wai tayi fushi tace tunda ka samu sabuwar kanwarka ni ka tsaneni wlh sai na fadawa Mimi Ni in nace ka bani nasa kayanka sai kaki yarda ga Aunty ka bata sai na fadawa Mimi Kuma shine ka jefar dani ka koma wajenta,Dariya Nabeel yayi a ransa yace kaga yaran yanzu da wayo,a fili yace Sorry sis karki fada kinji na daina,Fadila ta fada jikinsa can wajen cinyoyinsa da sauri ya riketa kafin ta kwanta a jikinsa zata iya jinsa ba Kaya,yace bani da lafiya fa, Shagwaba ta fara ta fashe da kuka ta kwala uban ihu, ihu take zundumawa Kamar wacce aka sokawa Allura. Hamida ta shigo da sauri dauke da ruwa tace Zaki tara Mana mutane Fadila Yi hakuri,yarinya ta makale kafada naki ta fashewa da sabon kuka, Nabeel ya bata rai yace Zaki ci ubanki gobe kije can wajen Mimi na daina kulaki tunda baki da kunya dukanki akayi,Shuru tayi Jin ance za a kaita wurin Mimi ita tafi son Nabeel ruwa aka bata tace ni ba shi ba tea nake nufi,Nabeel kamar ya mareta haka yaji ya kalli Hamida yace gidan su Anwar ne wlh suka batata Wai da dare yaro in ya farka Nanny sai ta hada musu tea haka sukeyi,Hamida tace ga ruwan zafin dana tafasa ba kayan Hadi na juyeshi nayi tsarki dazu,baki ta rufe da sauri ta manta,Fadila tace Aunty Sannu baki kone ba tab,Nabeel ya kalli Fadila Kawai yace to ba tea kinji,Bari na Mata wani ya na iya da jarabar dangin miji cewar Hamida. Dariya Nabeel yayi yace dangin nawa ne jaraba,to kaki yi a tsaneka ba dole kayi biyayyar dole ba,au ta Dole kike? ae Mana idan a gidan mu ne ba sai nayi ball da yarinya ba,Fadila ta kyalkyale da dariya ance za ayi ball da yarinya,tashi ki dakko min towel a toilet,ta Saba dama can Watarana Yana aikenta toilet dinsa ta dakko Masa towel bata gane komai ba ,yace to jeki wajen Aunty zanyi wanka,da gudu ta Bude kofa ta fice,da sauri ya fito ya daura towel ya kwashe tissue da wives din da sukayi amfani da su ya zuba a dustbin,ya gyara bed din tare da duba lafiyar bedsheet yaga baza a gane ba sai Yar alamar laima kadan a wani wajen,wanka yayi tare da tsarkake jikinsa ya saka jallabiya Yana cikin Sallar nafeela suka dawo da tea,Hamida tace ai kin iya Sha ko? a'a Ni a baki ake bani,haka ta zauna ta dinga bata a baki tace biscuits fa Yana Ina mu da shi muke Sha,Hamida ta bude fridge ta dakko wani kala tace gashi,mu ba irin wannan ba butter milky shi muke ci,Nabeel ne ya sallame Sallah yace to Kisha haka gobe Aunty zata kaiki Shopping mall,Murna ta fara kafin kace me ta shanye taje tayi fitsari ta dawo ta kwanta,Hamida ma wanka ta shiga tare da tsarkake jikinta ta fito ta busar da gashinta ta gyara kanta sosai tana kamshi ta haura saman bed,Fadila tuni ta koma bacci Suka sake maida ta karshe. Washe gari suna zaune a Palo bayan Hamida ta dawo daga school Exam Suma sukeyi an kusa musu hutu,Bayan Sallar Isha suna kallo Fadila tana wajen Habiba,Wayar Hamida ce ta Shiga ruri Nabeel ya Mika Mata yace Sakinanki ce dagawa tayi Suka gaisa Sakina tace ke an sani School fa zanyi NCE, Wow na miki murna cewar Hamida,Iya fa aure zata yi jibi za a daura da wani,Hamida ta bude baki tace Iyanki duk tsufanta bata hakura ba,Wai ta gaji da tallan Masara cewar Sakina,Hamida tace wani tsohon ne amma Allah kiyaye Kawai jinya ta tafi yi Wanda Iya zata iya aura ai karewar tsufa ya kusa mutuwa,Sakina tace Wai tace da Dan kwari kwarinsa,ahh kice Kawai zuba ruwa a buta zata je tayi Sakina tana dariya tace aikuwa shi zataje tayi ya samu me zuba Masa ruwa a buta,Wai matarsa ce ta mutu wani tsohon bafulatani ne,Allah Sanya Alkhairi ko banza taci kajin kiwo,Nabeel ta bawa Suka gaisa tace Ango kasha kamshi ya mutuniyar tawa,Nabeel yace gata tayi bulbul ta kumbura kumatu subu subu,Sakina tayi dariya tace ai na ganta a Online ta turo min pics ta Whatsapp ka iya kiwo,na gode ya furta Sakina tace ka tayani godiya fa ta tura min dubu hamsim Wai Naja jari,Nabeel yace an gode Mata to ta kyauta ya mikawa Hamida wayar,Sakina tace Su Sulaiman Ashe an samu Offer shi da Karima nayi murna wlh Yar uwa,Bayan sun gama waya Hamida ta Kira Papa Yana ta yiwa Hamida godiyar aikin data samowa yaransa yace ai Ummi harda kukan murna haka suka gama wayar. Nabeel yace a Ina Kika samu kudin bawa Sakina? Kudin break da kake bani nake Tarawa da Wanda kake bani idan Zan siyi Abu na hada na bata, yace amma baza ki tambayeni ba Mene amfanina? Nan gaba zaka Yi ne karka damu Bayan Sati biyu anyiwa Basma duk wani gwaji kwakwalwarta fes take sannan hujjoji sun tabbatar ita ta kashe Basma sannan ta Kara tabbatarwa itace ta kashe Alkali hukuncin daurin Rai da Rai ya yanke mata, Yayarta ta rushe da kuka da danginsu amma Basma mirsisi tayi ta kalli Hamida tace sai naci Uwarki Allah ya tsine Miki,Hamida ta Mata gwalo yayin da matakan tsaro Suka fita da Basma tana ta durawa Hamida ashar Hamida ta kwantar da kanta a jikin Nabeel tana ta faman yiwa Basma gwalo,Alkali ya nuna Hamida yace ke Zan yanke Miki hukunci bulala dari akan gwalon da Kike ta yi kullum ina kallonki indai an shiga kotu kin dinga yiwa Basma gwalo kenan,Dariya akayi Alkali ya mike kowa ya fito ana murna dangin Basma ne kadai ke kuka. Yau Mimi ta karbi Fadila ta koma wajenta. Hamida tana dawowa daga Islamiyya ta damu Nabeel sai ya bata labarinsa da rayuwarsa, suna kwance bayan sunyi Shirin bacci tana jikinsa Yana Wasa da gashinta yace Kamar Yanda Kika sani sunana Nabeel Al'amin Lele,asalin fulanin bakwalo ne masu jajayen shanu,mu kaf zuriyarmu basa kiwon fararen Shanu sai jajaye wasu ma Jajaye ake cewa irin wannan fulanin,Fulanin Cameroon ne mu Wai inji manya amma asalinmu dai baki ne har Cameroon zuwa kakanni Suka yi,Hamida tace lallai to da ganinku kunyi Kalar larabawa,Nabeel yace oho dai, Nigeria kuma Wai ance asalalin zuwan kakannin mu to kakannin kakannine wata a ciki Wai tayi kambun baka sunyi fada da wata tace Zaki gani shike Nan Wai washe gari aka ga matar ta kwanta cuta shine a kauyen Suka hadu zasu kasheta tana ta kuka tace wlh taka San barawo tayi,Hamida kirji ta dafe Kar dai ace Dangin mayu na shigo Naga ta kaina gwara ka auri barawo akan maye,Nabeel ya tintsire da dariya yace ke Kika sani ita dai data ce zata gani ance ba abinda ta Mata Kawai ta fada a akasi ne, ganin haka Dangin da yawa Suka gudo Suka dawo Nigeria Wai Suka zauna a tudun wada Kano,Suka dinga hayayyafa wasu Kuma suna mutuwa har aka haifi kakanninmu Sara da Malam Adamu suma auren dangi aka hada suka haifi Iyayenmu Kawu Ubaidu Suka fara Haifa Sai Al Amin Affa sai Kawu Senator Abbas su Uku kenan rak, su kawu sun taso Suma kakanninsu duk sun mutu iyayensu suna son boko suka tsaya musu har Suka gama secondary da Diploma sannan aka zaba musu Mata a dangi aka hadasu auren Zumunci,Affa ne kadai yake da budurwa a Dangin Mimi Kawai aka bashi ita,aka musu auren gata kowanne aka gina Masa gida a cikin garin Kaduna sunce can suke son rayuwa kowanne da gidansa. Kawu Ubaidu sai da ya haifi Yara uku,Kawu Senator ya haifi Yara biyu sannan Mimi ta Samu Ciki ta Haifeni shi yasa dangi suka sa Min Lele,aka Haifeni santalele nafi kowa kyau a zuriyar mu sabo da tsananin kyawun Mimi ga Affa ma me kyau shi yasa yasa nazo a a zizana Nima,Hamida tayi dariya,a shekarar Kuma Iyayen su Affa Suka rasu motace ta bigesu sunje unguwa wajen tsallaka titi mota tayi gaba da su. Lokacin da aka sakani a primary lokacin Affa Suka siyar da gadonsu me uban yawa Suka tafi turai Karo karatu,har Suka gama degree lokacin na kusa Gama primary,Suka koma Masters lokacin Kuma na shiga Secondary,suna dawowa Ubaidu ya Zama babban likita ya gina katon asibiti a Abuja ya tashi da iyalansa ya koma can,Alhaji Abbas tuni ya shiga siyasa amma duk da haka da sun samu dama suke komawa school su Karo karatu komai nasu boko,Indai Kai ba dan Boko bane baka birgesu,rayuwar turawa sukeyi,Amma akwai zumunci sun Zama tsintsiya madaurinki Daya,sun tarbiyyartar da iyalansu akan haka,damuwar Dan Uwa ta Dan Uwa ce Kuma kowa baya abu Kai tsaye sai yayi shawara da Dan Uwansa. Ga rike sirri basa fadawa ko matansu suji wani sirrinsu bare 'ya'ya su Haka su binne Kuma haka Suka koya Mana Muna kaunar juna,babu kyamar talaka ko wani,ba wulakanci nine ma na Dan fita daban ban son surutu,Alhaji Abbas ya fito takarar chairman yaci lokacin Affa tuni Yana lecturing a university, bayan chairman lokacin ya fito takarar dan majalisar tarayya Allah yasa yaci ai Kuwa da shi da Kawu Doctor sune Suka daukewa Affa nauyin komai ganin sun fishi samu,karshe ma Kawu Abbas a gidansa na girma a Nan ya hadamu da yaransa ya turamu kasar waje karatu akan Ni nayi Medicine sabo da na fisu kwakwalwa amma da naje can Ni nafi son Engineering,na karanta shi,mahaukatan kudi suke tura Mana Kawai saving muke. Lokacin Mimi ta haifo min kanwa Fadila,Ina Uk Nasha murna,tun kafin mu gama karatu Allah ya hadani da wani company na Yan China masu aikin titin kwalta,muna Hira Haka Suka ga Ina da basira sukace nazo company dinsu zasu gwada kwazona,naje Allah ya bani Nasara,Suka bani aikace aikace na dinga nunawa yaransu suna aiki Kuma abin yayi daidai na samu kudi a wajensu na hada na zuba shares dina daga Nan Muka fara Ina dawowa kasar Nan na mallaki wasu motocin aikin wasu Kuma su suke bani haya da komai dai da Kika sani nazo kasata Ina samun Kwangila har Allah ya hadani da ke Hamida tace gaskiya ne Alhmdllh Yanzu gashi Kawu Senator yayi Senator har sau biyu ga kawu Ubaidu shima ya bunkasa asibitoci ne da shi kala kala Allah ya baku, suna Hira har bacci yayi gaba da su. Lokaci na ja Hamida har ta kwashe wata biyar a gidan Nabeel suna zuba love ta goge sosai ta Kare wani irin wayewa in kaga Hamida sai ka rantse ba ita bace,ta Zama me aji lokacin ne Kuma ya maidata Ss3 ta zana waec da Neco ganin yanzu tana kokari ta iya karatu da rubutu,turancin ma tana Dan tabawa sai dai ba irin me yawa sosai ba wannan sai a hankali, Islamiyya ma kanta ya bude matuka Yau final Exam Suka zana tana ta faman Murna ta shigo gida shima bai dade da dawo ba congratulations my wife washe baki ta furta thanks yau nayi candy sai hutu da Hidima wa Naja'atu cikinta ta shafa ta kalli Nabeel dake zaune Yana kallon News Yaya Kyakyawa wlh cikina sai kumbura yake Yana tauri kullum har motsi nake ji,Nabeel ya murmusa nace Miki tun Rannan ciki ne da ke kince ke Allah ya kiyaye baki da komai yanzu Kika Fara harkalla da Naja'atu kina ta cin abinci kullum Kamar hauka gashi Nan cikinki ya fara Fitowa,Hamida da sauri tace a'a kiba ce teba ce har yaushe aka fara Amarcin za ace ciki Ni wlh Indai Muka je asibiti akace cikine to idan na haihi tsarin iyali zanyi gaskiya bazan iya ba,Harkalla da Naja'atu ta yanzu na fara kullum a zandamo min abata Kallonta Nabeel yayi yace to Sannu Mijina,Dariya tayi ta fada jikinsa yace maza ki zubar da cikin shima garin tsalle tsallenki, Naja'atun Nabeel ta kalla dake wando tace Najancy ana ta hutawa? Dariya ta bawa Nabeel yace Naja'atu dadi kenan?inama ana ajiyeta a gida idan zaka tafi unguwa,Allah ya shiryeki Pipi amma farko Kika dinga kuka, yace Yunwa nake ji kinga tafi kitchen Kawai Madam,kitchen ta shiga ta kyalkyale da dariya Yana jiyota ta Palo,Bread ta dakko da lemo Cock tana girki tana ci,Nabeel ne ya shigo ya ganta yace Kinga ta kanki,tana cinyewa ta hada cornflakes ta shanye sannan taci gaba da girkinta Nabeel Yana ciki Yana tayata suka Gama da wuri. Nabeel washe gari 10am Bayan sun karya kowa ya zuba gayu ya fito Yana daura agogo yace muje asibiti dakko mayafi,Ni bana so naje ba ciki bane wani kallo ya mata ta mike zunbur ta dakko mayafi yace koma kisa hijab kina gani duk hips a waje muje ana ta kallonki Hijab ta saka me kyau da jaka sai yaga tafi kyau ma haka yace Kai baki da nikaf ne? Hamida tace ae yace muje haka ya rike hannunta suka Shiga mota Yana driving private hospital suka je,Suna zuwa Nabeel yaga Doctor Ahmad a can a nan ma aiki yakeyi,Nabeel Suka shiga dai Yana Fitowa ya gansu Ahmad sai bin Hamida yake da mayen kallo ganin tayi uban kyau ta wani goge gwanin sha'awa,a ransa yace a haka ma a hijab kenan,Nabeel tsaki yaja,Hamida tace bari na gaisheshi,wlh kina gaisar da shi sai Kinga abinda Zan Miki wanne irin Iskanci ne wannan Zaki gaida da shi mene hadinki da shi dalla tashi mu bar asibitin wlh ko a Hanya kuka hadu Kika kulashi ban sani ba ban yafe Miki ba na fada Miki tashi ya fisgi hannunta Suka fice tare da Shiga mota Suka koma wani Hospital din daban. Hamida cikinta wata hudu ma da aka gwada,murna Nabeel yake sosai itama haka,tace dan Daddy ya dawo ahayye dadi Zan samu dan aike idan aurensa yazo ni Zan hada Masa Lefe,Idan macece ni Zan Mata kayan kitchen in gyara yata mijinta yajita zakwai,Dariya ta ba Nabeel tun ba a Haifa ba har an kawo zancen auren da ko 'ya Gidan Mimi Suka wuce suna shiga Mimi tace Naga Kuna ta fara'a yau lafiya? Nabeel yace jika Kika samu fa shine,Hamida tace 4mnths harda kunya Wai ta Shige kitchen,Mimi Tace gwara ma ki fito min a kitchen ke dai in kin Haihu Naga yaro tsakanin ke da dan naki Tuwo ta gani anyi ta ebo ta fito,Mimi tace tuwon Affa ne fa,in yazo kice surukarsa taci cewar Nabeel , Affane ya shigo yace naji ana gulmata,Dariya sukayi tace tuwanka dai Saura kadan rumbu ta kwashe tana ci,Affa yace Shakira Alu takwashe,Dariya sukayi Mimi tace sunan ya dace da ita Alu takwashe girki,Hamida ta kalli Nabeel tace Lele na fada? Nabeel yace a'a, Affa yace me zata fada?Hamida ta kwabe Fuska yace Kar na fada Kuma Ina so na fada,Affa yace Fadi,Nabeel yace no Mimi zata fada ma,to ku bar min gida na karku takura min cewar Affa,Hamida sai da ta cinye tuwo Mimi ta zuba Mata a flask Kato da yawa miyar kubewa danya Suka dauka sai gida. Mimi Affa ta fadawa Maganar ciki ce fa Hamida ta samu,Murmushi yayi yace shine ake ta yayatawa Kai Yara da shiririta in ya girma ma kowa zai gani ai,Mimi Tace naji dadi wlh inaso a Tara min jikoki tunda Ni Allah Bai bani da yawa ba Affa yace Allah yasa. Akwai wata marainiya Dana gani lokacin da Muka Kai ziyara da Yan Uwana Suka taimaka musu yarinya ce me Hakuri ga hankali 16yrs take Zan dakko Miki ita ki riketa Kawai a Nan a bata ilimi ai taimako ne abin,in kin ganta Zaki so ta kyakyawa ce kamar Hamidan Lele Ni suna min Kama sosai wlh. Mimi Tace Ina so a kawo min ai taimako ne dama an kwace min Fadila tana can ya na iya,Dariya sukayi Kawai. Su Anwar da su Ihsan duk sun fitar da matan da zasu aura matan ma sun kawo mazajensu wasu a dangi wasu Kuma a wani wajen Suka samu,shirye shiryen biki akeyi za a tafi Abuja asha bikin yaran Yaya Ubaidu Dana Senator Abbas. Hamida sai Murna takeyi zasu tafi da Lele dama ba school jiran Exam suke yi,Maza hudu Mata Hudu za a aurar sauran masu tasowa ne sai Nan gaba. Nabeel ya musu dinkuna na Alfarma,biki Saura sati daya Mimi tuni ta tafi can ita,Affa Kuwa Saura kwana Uku a fara ya tafi can Su Hamida ana gobe za a fara Event Suka sauka a Abuja ita da Nabeel dinta. Hamida ta kalli gidan senator Wanda har family din Ubaidu can Suka koma gaba Daya a gidan za ayi shagalin sabo da girmansa, Hamida an dau wanka ansha takalmi me tsini,Nabeel ta gani ya karbi key a hannun wani me aiki a gidan,masu Aiki sun daukar musu Jakar kayansu sunbi bayansu wani part da ba kowa Nabeel ya bude hadadden part yasha gyara sai kamshi da sanyi ke tashi Kawai,yace Pipina a Nan na zauna Sanda Ina gidan Nan,Gashi Allah yayi Zan shiga Nima ta furta,Kasancewar a jirgi Suka Zo ba gajiya Kawai kayan suka ajiye Suka fito zuwa wani part inda manyan suke iyaye kenan har Affa Yana can da matansu a Nan Suka kwashi gaisuwa sannan Suka tafi inda dangi suke suna Shiga katon Palo Hamida taga su Anwar maza da Mata ana ta labarin duniya ana Dariya harda dattijai dangi suna tsokanarsu,Hamida tana shiga suka hau ihu ga Shakira ga Shakiran Lele, Dariya Hamida ta saki ba shiri ta shiga ciki suna ta kallon dan cikinta. Fatima tace Pipin Lele ashe an hadu da abin Hamida tace wlh Allah ya nufa suka dinga dariya,Lele ne ya shigo Suka Yi tsit ana Masa Sannu da zuwa Suka gaisa yace ana ta surutun shirmen ne,wajen Hamida ya karasa tare da Mata rada zanje wajen wasu friends Dina sai dare Zan dawo,a dawo lfy tace ficewa yayi abinsa mota ya hau,Suka Dora surutunsu ana ta abin dariya Hamida tace bayin Allah Zan zirarawa cikina abinci yanzu Ni bana jurewa a nuna min kitchen,ai Kuwa aka nuna Mata ta Shiga abinci iri iri gashi Nan abinda take so ta eba. Akwai wani yaro Dan gidan Senator ne Fauzan baya son magana bai wuce 24yrs ba, duk gidansu yafi kowa kyau in ka cire Nabeel Wanda shi na daban ne amma Fauzan ya hadu sai girman Kai duk Family yafi su nuna Isa da mulki Yana Jin kansa,tasu tafi zuwa Daya da Nabeel,Nabeel sai yace ai yafi kowa hankali Sai bayan an gama biki Suka dawo gida anji Dadi anyi zumunci biki ya kayatar an kashe Naira. Bayan watanni Hamida cikinta ya tsufa sosai ga maitar Nabeel baya bari ta huta,tana kwance ta ya fara rabata da kayan jikinta wani dadi take karawa Yana ta buga harka Hamida tace marata ciwo take wlh tun safe Kamar Zan haihu,Nabeel bai ma ji ta ba sai da ya gamsu sannan yace ya shiga wata tara ne? Hamida ta fashe da kuka tace nace ma Banda lafiya kaki kulani wayyo Allah cikina ta dawo kasan bed,Nabeel ya rude ko wanka baiyi ba ya saka kayan baccinsa dogon wando da Riga ya sa Mata doguwar rigar Atamfa ya dauketa da tarkacen kayan haihuwarta da tace ta hada cikin Daren 12am ya tafi da ita asibiti ya Kira Mimi ya fada Mata ta taho itama asibitin. Hamida tana ta faman kuka bata San inda hankalinta yake ba taga asibiti mutane duk gasu Nan ana hada hada tace ku tafi masallaci kuyi Sallah,duk inda aka wuce da ita sai tace su tafi masallaci suyi Sallah labour room aka shiga Hamida kuka takeyi tana zanyi Sallah Zanyi Sallah Kuma kuje kuyi Sallah. Dama ita bata da juriya a ciwo ta cika asibitin da kuka Lelene ya jawo min Nakuda wlh Dana baiyi niiyar zuwa yau ba Lelene ya jawo shi,Mimi Tace ke ki rufe Mana baki ke baki da Hakurin ciwo,Kowa ya San haihuwa bazan iya ba Lelene mumnafuki bakin kwarto Nishi ta fara masu karbar haihuwa suna kanta, Ni bazan Haihu a gaban surukata ba,Mimi tace ai ke sai gyaran Allah duk haihuwa sai kinyi abin kunya,Hamida tunda wuya tayi wuya magana ma dainawa tayi har sai 1am Allah yasa ta haifo danta Namiji katon gaske me Kama da Nabeel,Mimi sai Murna,sai ga Hamida an dawo normal tun kafin ma a gyarata da kanta tace zatayi wanka,Mimi ruwan zafi taji akwai a toilet din tace,gashi dake private ne sai kamshi ke tashi kawai,Wanka tayi da ruwan zafi ta shirya kanta,Mimi ta bata wata Abaya baka ta shirya kanta ta fito Kamar ba ita ba,sai kunyar Mimi take ji tace Dan Allah Mimi Kiyi Hakuri,Dariya Mimi tayi tace ai ke Kam kinji kunya Hamida haihuwarki ta farko ma Haka Kika Yi Allah yasa ma operation aka Miki waccan. Dakin hutu aka canja mata sannan Mimi ta hada mata tea me kauri ta sha,Nabeel Wanda yake rungume da dansa ya Gama Masa Addua Mimi Tace ya shigo ya shigo Yana Mata Sannu Hamida Suka balle da hira,Nabeel ne ya kalli bed din da Hamida take kwance ya zaro Ido tare da furta Mimi na Shiga Uku Matata zata mutu king jini ita kanta Hamida ana ta Hira bata San jini ya balle Mata ba Yana ta malala,sai ta fashe da kuka Jini Kamar an balle pampo Nabeel ya rude zai jefar da Baby Mimi ta karbe shi tace sauri ka Kira likita, Nabeel ya fita ya dawo da wasu matan likitoci tace amma an Bata tea ko?mimi tace ae Tace Watarana ba a bawa wacce ta Haihu ruwan zafi ta Sha sabo da idan me zubar da jini ce Yana Jin zafi zai balle Mata dama kadan yake jira. Nabeel cikin karaji yace dalla malama ki daina Mana surutun Iska ki kula da matata wlh na rasata sai na daure ku,Kun San yanda nake sonta zaku min ganganci,Hamida tuni ta fara kokarin sumewa jininta Kawai malala yake Ummi tana dagata sai bul bul,Nabeel Hannu ya Dora a Kai ya fara kuka. Saura na dare Inshaallah AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 56-60 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Herwwerhy Ummu Lateepha Ma'esha Mrs Sadauki Mrs Mukhtar ~• ~🥰 Hamida idonta Yana wani juyewa cikin kasalalliyar murya tace a Kira min Papa....kafin ta rufe baki tuni ta sume,Nabeel bai San Haihuwa ba sai yau sai kace mace ya dinga girgiza Hamida Yana kuka Hamida idan ta dan farfado sai tace Nabeel mutuwa zanyi,Lele ya rungumeta Yana kuka wiwi baza ki mutu ba,Hamida baza ki mutu ba anyi anyi ya fita yaki sai da babban likitan yazo yace ayi maza a kawo Wanda za a ebi jininta yanzu zamu bada Aron wani a asibin Nan in an eba Zaki biya mu namu,Mimi tace Dan Allah kuyi sauri yarinya zata mutu Kuna kallo Kamar ba private ba,Nabeel ya Mike ya Bude kofa ya fita fakal fakal ya dawo Yana ta Neman wayarsa alhalin Wayar ma tana hannunsa. Su Ammar ya Kira da su Sale yace su taho asibiti jini ake so dama sunji labarin tana asibiti,Allah sarki Inuwa da Sale wasu Wanda suke mutunci Suka tattaro a daren Suka je asibitin,cikin gaggawa aka gwada mutum biyar duk lafiya suke Kuma yazo daya dana Hamida aka eba,already dama an Mata Allurori an sa Leda Daya na asibiti, Masu gyara dakin sun gyara shi neat har jikin Hamida Mimi ta cire kayan jikinta an goge Mata jiki tsaf da wives me shegen kamshi da nurses Suka kawo Suka taimaka aka gyarata suka kawo rigar asibiti wata bue doguwa aka saka Mata,Sannan aka ce Nabeel ya shigo lokacin ya daga hannu sama ba ruwansa da mutane Addua yake a fili duk su Sale suna ji. Yana Allah ka bawa matata lafiya Hamida,Allah Ina sonta ya Allah ka barmu tare har tsufanmu Allah ka bata lafiya da tsawon rai,Yana ta Yi wani abin ma bai San me yake cewa ba,Mimi ta tattara kayan da Suka baci gaba Daya ta kaisu wani katon Rami a asibitin Wanda kullum wuta ci take a ciki a Nan suke kone duk wata najasa ta zuba a Nan sabo da kafin ace sun wanku za a Sha fama. Nabeel ta samu a ciki ya zuba tagumi ya kafe Hamida da Ido,Har tausayi ya ba Mimi tace kaje gida kayi wanka ka dawo kaga yanzu wajen 3am ma Sai ka dawo da asuba Nabeel yace bazan iya ba wlh,Ina jaririn? Nabeel yace Ni na manta Wanda na mikawa ma shi wlh ohhh Inuwa na bawa sun tafi dashi gida nace a kaiwa Goggo Sara me aikinki sai ta Masa wanka ta gyara shi,Mimi tayi Murmushi tace Ashe akwai sauran dan Hankalin bai gushe ba,a Daren Suka Daura Mata jini Leda na biyu sabo da abin na gaggawa ne, ana Fara sa Leda ta biyu ga Allurai ta Sha sai ga Hamida ta dan motsa tana jujjuya Kai,Nabeel murna ta kamashi yace la'ilahaillahu Yana wani Murmushi Mimi tace kaji kunya dai Da asuba jini na biyu ya Kare Hamida harda bude Ido wannan Karon tace Ina Lelena yace gani Nan Pipina ya rike hannunta ta damke hannun sosai tace ashe Zan sake ganinka,Murmushi yayi sai ga likita ya shigo yace Alhmdllh Yanzu idan zata ci wani abu a bata sai da anjima kadan Zamu Kara Mata wani,Lele yace Mimi a gida akwai farfesun da tayi ma ko ci bata yi ba,Hamida tace da zan samu nama da madara ta ruwa su zanci tana kwance duk da haka ba kwari a jikinta tunda jinin Bai wadaceta ba,a hankali tace da maltina,Nabeel jiki na rawa rigarsa ma ta bacci duk ta shafi jinin Hamida,Waya ya yiwa Habiba ta hado komai driver ya kawo ta,shi Kuma ya fita yaga inda ake siyar da abubuwa a asibitin Nan yaje ya lodo Mata su fresh milk,Madara peak,maltina,fresh yo,gasu Nan dai,ya dawo da sauri ya kawo,da Kansa ya hada Mata Madara da malt ya dagata Mimi ta Mikasa Masa ya bata tunda ta kafa Kai sai data shanye tas,ta dan kalli Lele idonta na lumshewa tace Naman fa? Yace yanzu za a kawo,ba a dade ba Habiba ta kawo ya zuba a plate ya fara Bata a baki tana ta cinyewa tana Shan Madara sai gata ta dan Kara karfi tace cikin sanyin murya Mimi kinji Ina iya daga hannuna,Sannu ana Kara Miki wasu Zaki iya mikewa ma ai jini haka yake,tace zata Yi fitsari Lele ya kamawa Mimi ta kaita tayi ta,tace Nabeel ya jiramu a dakin ba sai ka shiga toilet ba,Yace Mimi na fa San komai jinin Hamida ai jini nane mene in na gani,kofa Mimi ta kulle bata kulashi ba, wata kujera ta zaunar da ita duk ta wanke Mata jikinta da sabulu me kamshi sabo da ba Dadi ka zauna da me jinya da kazanta babu amfanin jinya,Nabeel karbo min wata rigar a wajen nurse sabuwa a sa Mata Yaje ya karbo a ledarta Mimi ta shiryata tsaf Suka fito Nabeel ya taimaka Mata Suka kwantar da ita,Hamida a slow tace har na danji Dadi,Masu gyara ta Kira Suka sake gyara ko Ina Yana kamshi har toilet sannan Suka sake sa mata wani jinin,Mimi tayi Alwala tare da sallah,tana idarwa Nabeel yace zaije shima yayi wanka zai dawo Tace kasa habeeba tayi breakfast a kawo sannan ka taho da kayan bukata Dana sawarta yace to ya fita ya shiga motarsa zuciyarsa da sukuni,Yana zuwa gida gari ya fara haske ya fadawa Habiba abinda zata dafa sannan ya haura sama ya gyara bedroom din da Suka bari a hargitse da Kaya,Ya tube kayan jikinsa ya zuba a washing machine ya wanke su Kal ya shanya sannan yayi wanka tare da tsarkake jikinsa yazo yayi Sallah da azkhar Hamidansa ta Sha Addua,Kwanciya yayi ya huta amma bai iya bacci ba,Habiba tana gamawa ya kwashi komai ya koma asibiti Hamida tana ta sheka bacci jini na shigarta,Mimi ta eba abinda zata ci taci tace Nabeel yaci yace Mimi bazan iya ba sai naga abinda hali yayi ya sake Zama. 11am jinin ya Kare tana ta bacci su Ammar da Yan gidansu har sunzo dubiya sun tafi,su Sale sun dawo dubiya,sai da tayi bacci ta koshi sannan ta farka tana Bude Ido taji wani Dadi a jikinta sai gashi ta mike ta zauna da kanta,Nabeel sun shigo da likita sai Murna ya tafi wajen abarsa yace a kaiki fitsari ne?Zan iya zuwa da kaina fa, ta mike a hankali ta sakko Mimi Tace banda ruwa me zafi da yawa,Brush ta karba tayi tayi wanka sosai da sosai ta gasa dausayinta duk a hankali take komai sabo da bata gama dawowa normal ba,shirya kanta tayi ta fito tace an kawo min Kaya? Mimi tace ae a ciki ta Mika Mata doguwar riga Yar kanti marar nauyi me gajeren hannu ta saka ta zauna a bakin gadon ta kalli Lele da ya zuba Mata Ido tace ka Kira min su Karima a fada musu,Nabeel yace na fada musu dazu Ummi tana Hanya ma amma bance musu ga halin da kike ba gudun Kar hankalinsu ya tashi. Mimi abinci ta zuba Mata taci da yawa sosai dankalin turawa da kwai Tasha tea taci nama ga Madara me kwakwa da malt,Taji karfi sosai tace bani wayarka,Nabeel ya Mika Mata ta Kira Sakina bugu Daya ta daga tace me jego ya jikin naji haihuwa,Tace Alhmdllh ku fitar da Ankon,ba Mimi ba har Nabeel sai da suka kalli Hamida tana fama da kanta a fitar da anko,Nabeel yace ke da ya kamata ki huta wanne bikin suna za ayi Kuma, Inshaallah Zan warke ne kafin lokacin Ina so zanyi,Mimi tace tunda tana so ka barta sai ayi a gidana tunda dama tafiya zanyi da ke,Lele yace ah tab a turo dai tsohuwa,Mimi tace ai dama ba riketa zanyi ba ta zauna da mu har na sati biyu sai ta dawo tare da Goggo ta kula da ita da yaron,to Nabeel yace badan ya so ba. Sai dare Suka sa Mata na hudu suka ce daga shi an gama ya isheta dama sun gwada sunga kadan ya rage ya koma normal lokacin tuni Ummi ta iso sai lokacin Mimi ta Bata labari,Nabeel Yana wani corridor na hospital din su da wasu mazan Suma an kawo matansu,Nabeel yace Kuna ruwa suna ta dariya,wani yace ai Ni jini aka karawa tawa,Nabeel yace kaima? mutumin yace Naga tashin hankali,Nabeel yace Ni mamakin da nakeyi ka duba wannan Yar kafa ta Mata Yar bular kofa karama amma yanda jini dunkule dunkule yake fadowa,dayan yace Kai wani fa yayi dan botiki tari guda zaka ga ya Fado faf, Wanda Bai bi uwarsa ba ya shiga Uku dole mutum ya Shiga wuta cewar Nabeel,yace na Kara ganin darajar uwata Ni Kam,wannan yaron idan Naga ya batawa momynsa rai sai na karya shi Nabeel ya furta,suna ta dariya dayan yace Ina jaririn naka? Nabeel yace Yana can gida wajen me aiki ko ya suke ciki oho shi ya sani akan na rasa matata gwara shi ya koma dama ban Saba da shi ba. Mimice tasa aka kawo jariri ance Yana ta kuka nono yake so duk da Haka an bashi madara,an Masa wanka yasha fararen Kaya sai kamshi yake kyakyawa da shi,Mimi ta mikawa Hamida tashi ki daure a bashi nono mu gani dama nonuwan sun cika sunyi bake bake har zafi suke Mata,Hamida tace a tambayi Lele na bashi? Ummi tace wacce irin Yar iskar yarinya ce kene Wai nononma sai an tambayi miji Ummi ta mike da kanta ta zuge zip din riga,Hamida ta saka hijab sannan ta shigar da yaron ciki Wai Kar a kalli nononta,Boyo ya Kare yarinya Ummi ta cire hijab din tace ki bashi Muna gani in da gyara a gyara miki,Duk da Haka Saida ta sa mayafi ta Kare sannan tayi Bismillah ta fara bashi Yana zuka ta fara mutsu mutsu da kafafu Wai zafi. Ido ta rufe tare da daga Kai sama tana Jin azaba,Lele ne ya shigo room din ya sake sabon wankan shadda Fara Yana kamshi ya kalli Pipinsa yace zafi Wai? Kuka ta saki Kawai tana ba yaron tana hawaye Wai zafi,Lele yace to ba sai a bashi madara ba a huta,Mimi tace Naga uban da zai bashi madara kowa a haka ya koya in zata daure ta daure ai ganinka ne ya Sata sakin kukan shagwabar. Nabeel zai zauna Yana Sannu zai daina,Mimi Tace fita wlh ko naci ubanka a dakin Nan yanzu zaka Zo ka damemu da fitsara,to ai yaron nake jira ta gama bashi na daukeshi,ba inda zaka da shi tashi ka fita,ba a sonsa ba ya fita. Washe gari kwana biyu Hamida tayi waras sai dan abinda ba a rasa ba a ranar aka sallamesu Suka koma gidan Mimi gaba Daya,Yan Uwa da abokan arziki ana ta tururuwar zuwa Ummi ta tafi su Karima da Asiya suna nan,suna saman bed har me jego ana zuba Hira yaro ya ishesu da kuka an rasa dalili,Nabeel ne yazo gidan tare da Shiga dakin yaro Yana ta kuka an rasa ya za ayi da shi yace ko zafi yake ji naji Kamar zazzabi a jikinsa,Daukansa Hamida tayi ta mike tsaye tana jijjigashi yaki Shuru,Nabeel ya dauki dankwalin Hamida ya fara Masa fifiti sai yayi shuru idan aka tsaya ya saki kuka,yace ga ac nayi fa,da Alama Ac baza ta Masa ba ci gaba da Masa fifitar,Nabeel yaci gaba da fifita Masa dankwalin Hamida tana continue continue ac baza ta Masa ba,Sakina da Karima sun saki baki suna kallo Nabeel ya dage Hamida tana ci gaba suna tsaye,sai leka fuskar yaron yake Yana Yi tana jijjiga yace I miss you Yana fifita Dan kwalin,Hamida tace miss you more continue ci gaba,Yana fifita Yana kallon fuskar Hamida yace I Love you,Love you too ci gaba ya fara bacci,Murmushi suka sakarma juna Yana ta faman fifita har yaro yayi bacci tace Alhmdllh yayi bacci a hankali ta kwantar da shi tace kaci abinci kuwa? Yace yanzu dai Mimi tace yana dining kizo kiyi Serving Dina,ta bishi Suka fita Mimi tana ganinta tace koma ciki Kar Naga kafarki a Nan in bazai ci ba ya barshi,Hamida ta juya ta shiga daki tana leken Nabeel ta kofa ta Masa alama da Hannu Wai ya zuba ya ci,Murmushi yayi sai da ya fara ci sannan ta koma wajen su Karima,Sakina tace soyayya Dadi lallai Hamida Yana kaunarki ba karya Na gaji gaskiya sai gobe Ayi Hakuri da kadan AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 61-65 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Karima tace Hamida har yau wlh rashin kunyarki da ragowa kina ganin suruka gaki a gidan ki dinga dannewa,Hamida tace me nayi duk irin Hankalin da nayi Baku gani ba a baya Sanda Ina Kauye babu maraba ta da Yar Kamar Tinkiya,Sakina ta sheke da dariya ai a lokacin in an fada Miki bakya ji komai Yaya kyakyawa Yaya kyakyawa karshe ya dirka Miki ciki munafuka Wai Ni Hamida ta boyewa sirrinta ai to Karima ta bani labari,Hamida tace Aunty Karima baki da sirri wlh shine Kika fada ko sai na fadawa Papa ance a rufe zance shine Kika kwayewa Yar uwarki baya,Sakina tace ai wlh abinda wani Dan uwan naki zai Miki Ni bazan Miki ba Hamida kin sani ko mijina da Iyata ban fada ba na rike sirri Kuma Ni dake kin San akwai Amana,na sani ai cewar Hamida. Sakina tace wlh Hamida ki rage uban gayun nan naki kin Haihu ma kullum wanka kike dauka kina gani Nabeel yanda yake ta kallonki a dai Yi a hankali Kar kafin arba'in a samu wani,Dan girman Allah ku daina zancen Haihuwar nan wallahi bana kaunarta ko kadan na gaji bazan iya ba tsarin iyali zanyi wlh wannan bala'i haka. Ke yarinya ana komawa harka kina Jin Naja'atunki Zaki manta,wa zai manta Allah kiyaye Naja'atun banza yama maida abarsa ba ruwana ta Dana nake wannan wahalar da Nasha ba dole na kula da dana ba kunga abin kaunata yanzu ba wata Naja'atu ba,Affa lokacin da aka Haihu ya tafi Lagos sai da ya dawo ya shigo har dakin da Hamida take su Karima Suka gaisa da shi ,Hamida ma Haka an duka har kasa yace Hamida haka Mimi ta sanar min anyi haihuwa Ashe haihuwa Kika yi,Hamida ana Jin kunya ya dauki dan yace sai a sa Masa Shakiri tunda ga Shakira,Suka dinga dariya Affa da tsokana,plates ya kalla yaga anci tuwo yace ya Naga tuwo Ni da zanga nama ko Ina Me jego sai da nama ai ko mage tasan ta kamowa danta bera ko kadangare ko tsuntsu suci,Mimi ce ta shigo tace to ga flasks can ka duba su duk nama ne tuwo Suka ce suna so aka musu,yayi kyau cewar Affa ya Mika musu dan yace wannan abokin Nawa irinsu Daya da Lele,Mimi ya kalla ba Lele na gani a gidan Nan bane? tace shine Mana kice yazo Ina son ganinsa tace to ya fita ya wuce part dinsa. Yaro yaga gata siyayya ake dankarowa harda ta hauka Haka Hamida ma an Mata dinkuna ko Papa kala biyar ya Mata,Ummi kala Uku,Karima Kala biyu,Sakina kala Daya da kayan jiriri,Nabeel Kuwa kamar hauka Haka ya narko Kaya da nata Dana yaro,Mimi da Affa Haka,Dangin Nabeel kaf sabo da kirkin Hamida ba abinda Basu Mata ba,Senator ne ya Aiko da raguna biyu manya manya,Yayan Affa Sa yasa aka kawo,Papa da Sulaiman sunzo sunga jariri Suma,sai ana gobe Suna Ummi ta dawo har take fadawa Hamida Sulaiman ya kusa aure a cikin garin Adamawa shima zai zauna kusa da wajen aikinsa,Hamida Tace wace matar? Watace a wajen aikinsu Suka hadu an kusa bikinta da wani aka samu matsala aka fasa sai Nabeel yace Yana sonta shine fa za ayi biki Saura wata Uku,Hamida tace mashaallah Allah ya nuna Mana. Waje Nabeel ya Kama musu Yan suna Jin har Kama Event center akayi dangi Suka dungumo suna,Yan School ma ta gayyaci Wanda suke mutunci,Ranar Suna yaro yaci sunan Baban Hamida Kabeer ana ce Masa Annoor. Sai da Yamma aka dauki wanka Kamar za aje Dinner Hamida tace tunda ba amin shagalin biki ba wannan ne biki na,sunsha suna ansha kida anyi liki anci an Sha sai cikin dare Suka Gama,har su Mimi duk sunje wajen. Washe Gari kowa na nesa Suka tafi gida ya Zama ba kowa a gidan sai iya su. Mimi tana da Goggo Sara kwanan Hamida goma a gidan Mimi tace Lele yazo ya dauketa su koma gidansu taga ya damu kansa,da wuri yazo driver duk ya kaiwa Hamida kayanta gida Lele Yana zuwa ya iske ta cakare cikin lace sabo dal tana kamshi ya dauki jaririnsa ta rataya Jakarta tare da yiwa Mimi sallama Suka tafi. Suna zuwa gidan Hamida taga an Kara gyara gidan an canja sababbin kofofi na musamman har gate ciki ma komai an canja furniture ya Kara kyau,garden da flowers na gidan an Kara saka sababbi sun Fara tasawa,tana ta santin gidan Suka Shiga bedroom Nan ma duk an canja. Kayanta ya tayata suka shirya Aslam ne ya farka a bacci Yana tsala kuka ta daukeshi ta fito da nono tana bashi,Nan take Nabeel hankalinsa ya tashi ganin Gorar Madara sun Kara girma a waje,Baki Fara Sallah bane? Hamida tace ban Fara ba,yace to ya za ayi Dani Ni? Hamida Ido ya ciki da kwalla tace duka duka yaushe na Haihu yau fa kwana goma jiya na Fara Sallah nayi mamakin da jini ya tsaya da wuri haka,Mimi tace dama Haka wasu suke Yi,Nabeel farin ciki ya manayeshi yace amma shine da Zaki min karya wlh Allah zai konaki,Hamida tace Wai Yi za kayi? Kallonki Zan tsaya Yi da,ka Bari a fara min Allurar tsarin iyali wlh Ni tsoron haihuwa nake ji Nufinki daga haifo Daya jal Zaki hakura wlh baki Isa ba Ina laifin ma ki haifo min Uku sannan ki fara planning din,tuni kuka yaci karfin Hamida Tace Uku fa....bazan iya ba mahaifata bata da kwari,Yaro ya karbe ya kaiwa Goggo Sara ya dawo sai kace maye ya fara aikin cire Mata Kaya tana kuka ya fara murzata, bakinta yake tsotsa Kamar yau ya taba ya shiga lasar jikinta ko Ina har zuwa kirjinta Yana zuwa Nan daga Wasa ya dinga shanyewa yaro milk,Hamida kuka Kawai take ita haihuwa take hangowa shi kuwa ko a jikinsa yayi yayi ta tayashi taki ai Kuwa shi kadai yayi abinsa Yana shigarta yaji ta fara matsewa sosai har zafi zafi taji karshe ta fara Enjoying Niimarce ta fallasata ya gano tana Jin dadi ihun kuka takeyi Ashe munafukar harda da na Dadi ta hade abinta waji Daya,sai wayyo zanyi ciki take fada tausaya Mata yayi yayi Niyyar yayi releasing waje amma ya kasa a ciki ya juye mata,Sai ga Hamida ita dalilin kin bada hadin Kai bata samu gamsuwa ba,Nabeel zai zare Naja'atu sai ta matse jikinta gam tace Allah baka Isa ba ai Ni ban Gama ba,Dariya yayi yace to ai kinsan baza tayi Aiki ba sai ta huta,Hamida ta fashe da kuka Allah sai tayi a haka,bankareta yayi ya zare jikinsa ya kwanta a gefe ta koma jikinsa ta kwanta tana ta faman mammatse cinya sai maganganun Iskanci take Masa har toshe kunnensa yake Yana dariya, Abinci yaci ya Sha Madara sannan ya koma wajen Hamida tana kwance sai ta matse cinya ta wangale Haka take ta yi,Nabeel yace har yau baki hakura ba? Harararsa tayi taci gaba da abinda take. Dariya yake ta Mata ta tashi ta Shiga toilet Wai tayi zuciya binta toilet din yayi tana Niyyar sakin shower ya jawota jikinsa dama kadan take jira yace ba a Fushi da Naja'atu Pipi baza ki iya ba, Sarrafa juna Suka shiga Yi a toilet din ya fara mata suna ta ihu da Nishi Kalamai harda na hauka,yanda Pipi ke birgeshi ta iya Masa yanda yake so,gata duk Kalar da za ayi tana bada himma komai ta iya in ta koya tana Masa ji yake kamar zai bar duniya sabo da dadi,shi yasa baya gajiya da ita kullum Kuma cikin gyara take,sai da ya gamsar da ita sosai da sosai sannan Suka Fara wanka kafin a Gama wankan ma an sake komawa harka garin Jin Dadi duk ya Sha nonon jariri Bai shirya ba Sai da Suka gama Wanka suna fitowa Pipin Lele ta rushe da kuka tana shike Nan nayi ciki na sani, Lele lallashinta yake amma kuka take kwasa ya riketa Yana cewa lafiya my love? Hannunta ta fisge tana kuka wiwi tace shike Nan nasan nayi ciki ma,karfin jini ne da Kai Yi kadan sai na samu ciki wlh bazan taba yafe maka ba har kabarinka yana ci da wuta ta tsuguna a wajen tana ta kuka,baki bude yake kallonta tace Kuma gidanka Zan bar maka bazan taba Zama a Nan ba gidan Mimi Zan koma ta mike a fusace tana kuka ta jawo Jakarta data jariri ta figi kayanta ta maida jikinta ta Suri mukullin motarsa shidai Yana tsaye mamaki ya kashe shi yace ko dai Aljanu gareta? Aslam ta karbo su dai masu aiki sunga tana ta kuka ta fice da kayanta Dana jariri ta hau mota ta bar gidan,Nabeel ransa ya baci yace tab za ayita sabuwa ashe Ni Kuma kinyi da dan halak bazan je biko ba kada Allah yasa ta dawo,gashinsa ya shafa ya juya Yana huci yace ga masifar Ina sonta sai kace Wanda aka yiwa asiri Ni zata rainawa hankali,gashi na daina Shan giya bare na kora,ruwa ya dauka ya tiltilawa cikinsa yace Zaki sani yarinya,Zama yayi a bakin bed din ya sake mikewa yace Mata ba Yan goyo bane Yarinyar Nan fa ta rainani Ni to na zauna Ni Daya a gidan nayi uban me Hamida Kuwa a gidan Mimi tayi parking ta fice jaririnta na hannunta tana kuka ta shiga sai taga wata yarinya gidan Yar kyakyawa da ita ta rakube a gefe ta hade rai kamar an aiko Mata da mutuwa,ita Yarinyar Bata da fara'a ko miskala zarratin kafin ma tayi dariya Aiki ne itace wacce Affa ya dakko daga gidan marayu 17yrs take,Mimi da Affa Suka Mike tsaye suna tambaya Hamida lafiya,Bata ce komai ba tana ta faman share hawaye,Baza ki magana ba wani abin ne ya faru? Hamida Tace Yaya Kyakyawa ne Ni gaskiya garinmu Zan koma,Affa yace Mene yayi miki to? Tace Mimi banfa Dade da haihuwa ba Nasha wahala gaskiya Ni gida Zan koma. Nan take su Mimi suka Gane har Mimi ta bude baki Affa ya Mata alama da tayi Shuru,da Kansa yace a'a ke da kike da gata Hamida ai ke Yar gata ce ki zamanki karki koma zauna a nan,da sauri ta kalli Affa tunaninta zaice a Kira Nabeel a Masa fada ta koma gidanta sai yace ta zauna ai ita ba Zama tazo Yi ba me zata Yi a Nan ba Nabeel a kusa. Sarkin Fushi ce tayi magana ba wani alamar fara'a ko Wasa tace mu Muna layi Muna jira idan wata ta saki nata zamu damke mu,Hamida ta kalleta Tace ke nayi Miki saurayi akwai irinki family din Nan wlh idan Kika kalli Lelena Sai na koma gidan mijina,Mimi suka Kama dariyar Hamida sun zaci wani mataki zata dauka suna Haka sai ga Fauzan yazo gidan an shigo da akwatinansa bautar kasa yazo a Nan zai zauna Dan gidan Senator. Sarkin Fushi ta zaci shine mijin Hanifa a ranta tace dole a kirashi da Yaya Kyakyawa sai ta tafi waje Fauzan ta tari gabansa Kamar zata shiga jikinsa ta kwalalo Masa Ido sai da yaji tsoro ma shi,gata ba Fara'a ko digo a fuskarta, fari ta Masa farrrrrr farrrr Wai duk Dan ta bawa Hamida haushi ta tashi ta koma gidan mijinta, Bata iya Dariya ba ta yake hakora kamar me tallan toothpaste,Fauzan ma sarkin Fushi ne ga saurin Fushi ga rashin magana,Hamida ta kyalkyale da dariya tace algunguma to ba Nabeel bane wannan Fauzan ne,Fauzan Hannu yasa ya hankadeta gefe ya kalli Affa yace Can you Imagine wannan yarinyar tana kwalalomin ido, sai fa na fasa Zama a gidan Nan daga Ina aka kawota? Affa yace daga gidan marayu Allah sarki marainiya ce sunanta Jannat,Mimi tace kace me hankali ce Ina hankali a nan? To gwara ita dai akan Hamida da farko,Hamida tace Kai Mimi nafa Yi hankali,Ina hankali kinyi yaji,Affa sama ya haura sai ga Nabeel ya Fado dakin. Lokacin sarkin Fushi sai da taji tsoron kyansa da kwarjini da haibarsa,wajen Hamida ya nufa yace Ina key din motata tace oho,Mimi tashi tayi itama ta barsu Yana ganin ba kowa ya fara lagude kirjinta da wayo Wai neman key yake, sarkin Fushi tuni ta bar wajen ta Shige dakinta jikinta na rawa, Nabeel baiga key ba ya karbe Baby ya ajiyeshi gefe ta cikin kafafu ya zura hannu ta kasan skert ya bige da shafa cinya duk neman key yakeyi,Hamida taji kamar tana son Hidima tace mu je gida na fasa yajin yace karki sake ki dawo gidana kiyi zamanki Kuma bai fasa mutstsika Gorar Madara ba Wai key yake Nema har yanzu Hamida taji tsoro Kar a fito a gansu ta dakko a jaka tace ga abinka Kiri Kiri yasan shine Yace ba shi bane wannan ai key din kofa ne yaci gaba Dama zuwa yayi ya kunyatata yanda da kanta zata bar gidan,na shiga Uku Kar a kamamu da yarinya a gidan Nan yace muje bedroom nayi searching ko na Miki tsirara a Nan,tashi tayi ba shiri ta shiga wani daki harda da sa key,Suka bar yaro Yana ta kuka a palo. Dakikantar Hamida ta motsa tana kallo ya cire Mata Kaya Yana ta Murzata ta biyewa Jin Dadi sai da Suka sake Yi a dakin sannan Suka maida kayansu,ta fashe da kuka shike Nan ciki,Kinga wallahi ki bini mu tafi gida ko na Miki abinda Baki zato ba,suna fitowa Suka ga Mimi tana jijjiga yaro Hamida tayi sauri tace banga key din ba mun duba dakin ma babu muje gida mu gani kunya ta kamata ko Dan Bata iya karba ba ta figi kayanta ta fice,Nabeel ne yayi karfin halin karbar yaro Mimi ta Mika Masa ta dada Masa duka a baya ku tafi marar kunya,Nabeel dai ya fice Sarkin Fushi tana ta lekensu ta kofa Nabeel ya tafi da imaninta,Nabeel take kauna gaskiya tana so ko a ta biyu ya Kara da ita. Jannat Jin sun tafi sai ta fito tana Fitowa Fauzan ya sakko shima da sauri,Jannat ta kalleshi da sauri tare da dauke kanta tace ko wannan Zan aura ne? Wa Zan aura duk gasu masu kyau Kai wancan yafi gwara wancan wannan bashi da mutunci,a ranta ta sake cewa Kai gwara wannan amma ban sani ba ko shima Yana da Mata bari naji,Fauzan ya zauna cin abinci a dining ya kashe gayu cikin kana Nan Kaya Jannat ta karasa inda yake tare da durkusawa har kasa a gabansa ta sadda Kai kasa tace dan Allah Ina da tambaya babu fara'a ko digo shima haka,tace dama wata magana nayi a cikin zuciyata Kawai Dan babu damar da zaka ji ne amma Zan dai Yi tambayar please kana da Mata kaima? Baki Fauzan ya bude spoon a hannu ya kasa cin abincin tace karka Yi Fushi tambaya ce ance matambayi baya bata wani Abu nake so na tantance,are you normal? Fauzan ya tambaya tace yes I'm normal please yace Ina da Mata what's your problem? tell me ya furta da karaji,Jannat ta Sosa gashinta ta fara masifa itama Kamar sa'anta Wai ku Mene Haka ne ae wannan da Mata wannan da Mata shima duk Yara daku baku taru kunyi mutum Daya daya kwakwara ba,ae Haka akeyi a rayuwa, Fauzan ya fusata ya mike zai mareta Affa ya fito Yana tsawa Kai Kai lafiya? Me tayi maka Dan Iska dama Kai duk yaran Nan Kaine ba mutumin kirki ba kullum sai zafin zuciya Kai da Lele baku da kunya yarinya me hankali,Affa yanzu wannan abin ce me hankali wallahi bata da hankali ka kaita asibitin kwakwalwa,Mimi tace sai da na fada ga masifar Fushi yarinya ba faraga a Haka Kuma baza ta taba magana akan abin kirki ba sai shashanci zaka ji tayi magana ga bala'in kyuya wannan ba irin Hamida bace gwara Hamida tana Aiki gata tana da ilimi na banza,Affa yace Kai ku daina Haka wlh a gidan marayu na dakkota, Mimi tace Hmmm ai sai kayi ta koma daki tana cewa yaje ya kwaso Mana Yar shege wa ya sani ko cikin shegece aka jefarta aka kaita gidan marayu bazan iya ba a kaita wajen Alhaji Abbas baban Fauzan shine sarkin dakko marayu ya Raine su idan sun girma ya musu aure ya musu gida da komai Kawai a kaita can ta hadu da halin Maman Fauzan Bata kaunar marasa asali Nan gaba can Zan kaita taci ubanta a gidan bazan iya ba Ni ban iya zalunci ba Jannat Jin irin masifar Fauzan ta yanke a ranta Nabeel zata aura Kawai,Amma Kuma taji ance suna da yawa, washe gari a Palo ta shimfida Sallaya tayi Sallar azahar tana idarwa lokacin Fauzan Yana kwance a palon yaji ta sallame Sallah maimaikon yaji Addua sai Jin tafi yayi tana rera kasidar manzo Ya manzon Allah Sayyadil wara yaaaaaaa.......Manzona manzon Allah Sayyadil wara.. ta rera harda da Kara volum,Fauzan ya juyo a fusace tana sani zata kashe Masa dodon kunne,tayi mugun tsorata Amma Bata tashi ba tunaninta kasidarce baya so sai ta fara Na kusa Na kusa in Mari soja... sai Dan Sanda ya Kare Kai Dan Sand Yi a uwarka Ubanka tana nuna Fauzan da Hannu ai Kuwa Yana tashi yaga shi take nunawa Ni kike Zaki dan ubanki a gidan marayu ba manya ta kwashe da gudu,Affa ne ya fito yace Kai ka kiyaye ni Yarinyar Nan wlh ba a agidan marayu ta girma ba da girmanta aka kaita can Zan baku labarinta nan gaba,ko wata Bata Yi ba a gidan marayu Kuma da iyayenta ku daina Mata wulakanci karku zo Kuna Jin kunya. Waya Fauzan ya Kira Nabeel yace matarka tana gida? Yace ae Mana yace bari naje can wannan jarabar Yarinyar da Affa ya kawo daga gidan marayu ta dameni,Nabeel yace au wata aka kawo Kuma gidan? Kai baka ganta ba da kazo daukan matarka,Allah me iko ban kula da ita ba ma ni matata nake hangowa Kawai. Fauzan tashi yayi ya tafi gidan Hamida,Hamida tana ganinsa tace yau a gari,yace uhm Kawai tare da daukan kyakyawan Annur dinta Yana Masa rawa Hamida tace karka tsinke Masa hanjin ciki baka San wahalar haihuwa ba kwata kwata kwanansa Sha biyu a duniya wannan wacce rawa za a Masa bani Dana gaskiya Hamida ta karbe danta,Aunty Hamida Wannan son Dan fa ai gaskiya ne,me zaka ci? Allah kiyaye naci girkin me jego cewar Fauzan ai daga juice na kwali sai lemon da Zan balle da kaina sai ruwa su Zan iya ci Hamida tayi Murmushi tace na Jannat dama kana labari Haka,Shuru yayi Mata Yana canja channel,Nabeel ne ya fito an zuba wata gezna arsh kamar ango yace na tafi,Hamida tace a gaida Amaryar Ammar kafin naje yace zata ji ai ya Miki afwa tunda kina jego. Sai ka dawo ta mike ta rakashi yace ki shirya dausayi kafin na dawo a Kansa Zan huce gajiya Nima angwanci make,Dariya tayi tace to Kawai ya tafi ta dawo Suna Dan magana da Fauzan Jefi jefi ta kawo Masa lemo da ruwa. Affa ne ya Kira Nabeel yace idan ka Gama kazo Ina nemanka,Bayan Nabeel ya Gama abinda yake ya wuce gidansu Bayan sun gaisa da Mimi yaga Jannat ta zauna Fuska ba Rahma Tace Ina yini daga Haka bata Kara ba ko kulata Nabeel baiyi ba ya haura sama Yana zuwa Suka gaisa da Affa,Affa yace kasan me yasa nace kazo? Yace a'a Alfarma nake Nema me zai Hana ka auri Jannat yarinya baiwar Allah in kayi Haka kayi taimako zaka samu Lada Ina maka kwadayin wannan ladan Nabeel,yarinya Yar sunna ce Nan gaba Zan baka labarinta Mai ban tausayi,Nabeel Nan take ya bata rai yace Affa ba Wai bazan ma biyayya ba Amma Ni gaskiya bana sonta Haba Affa Hamida fa,Affa yace Allah ne yace a Kara ai Kuma Hamida nasan bata da matsala zata Amince Ni da kaina Zan Mata Maganar, Nabeel murmushin bacin rai yayi yace Hamidan ce zata hakura? Kamar baka santa ba to wallahi ko ta yarda a gabanka Ni na fada maka sai ta bar min gidana,Ni Kuma Ina son matata wlh bana son bacin ranta farin cikin Hamida shine Nawa, in ba Hamida babu rayuwata,ko wace bazan iya sonta ba,Ni za'a sa na dinga aure aure ko wacce ace Ni bags dangi Nan ba a jona su Mana sai Ni za a ruguza min farin ciki wlh bana sonta ko an daura sai na saketa Ni tun yanzu ma na saketa saki Uku Kuma wallahi idan aka fadawa matata ta tafi ta barni Nima baza ku sake ganina ba. Mari Mimi ta kifawa Nabeel wacce shigowa tayi ta tsinci zancen,Bata so itama ayiwa Hamida kishiya sam,Tace baka da hankali kasan a gaban Wanda kake mahaifi ya wuce Wasa so hauka ne bai Isa ya baka umarni kabi ba Ashe yanda yace Haka za ayi,ko dan kaga Kai kadai ne damu sai Fadila tashi ka tafi karka sa na maka baki, Nabeel mikewa yayi yace Kuma wallahi bana sonta wallahi ko an daura sai na saketa na rantse da Allah gwara ma ku bawa wani ita,Kofa ya bude ya sake juyowa yace bana sonta ai Allah yace sai kana so zaka auri mutum ya fice abinsa ya koma gida,lokacin Fauzan ya bar gidan,Hankalin Nabeel a tashi ya shiga palonsa,Hamida taci uban kyau cikin Nighty dinta tana kamshi,Annur Yana wurin Nanny,ganinsa Haka sai jikinta yayi Sanyi Tace lafiya? jikinsa ya jawota tare da rungumeta Kam bakinsa ya daura a kunnenta yace kishiya za a miki,Affa Yarinyar daya kawo Wai ita zai sake aura min nace bana so wlh da alamu baza su yarda ba,abin Mamaki sai yaga Hamida tayi Murmushi tace to menene ba Allah ne yace Ayi ba,lokaci ne Allah ya kaddara ba yanda za ayi. Ka daina damuwa Indai dan nice tunda iyayenka ne Suka ce,Kuma ba a Wasa da iyaye kullum kokari ake a musu biyayya sabo da a Gama lafiya da su,Aljanna kake Nema fa haba Lelena ya za ayi kace baza ka musu biyayya ba taya Ina kallo Zan bar mijina ya nufi wutar jahannama Ni da nake so mu dawwama a Aljanna. Duniyar kanta Nawa take yanzu zakaji ance babu mutum amma a kanta a zauna ana bata lokaci gaskiya baka kyauta ba,yanzu ka Kira su Affa kace ka Amince Nima na Amince mu basu hakuri Saura kadan kuka ya kwacewa Hamida za ayi Mata kishiya amma dai ta danne abinta su Hamida anyi hankali bai zaci haka daga gareta ba yanda take Yar daru. Gefen bed ya jata suka zauna yana karewa fuskarta kallo tana murmushin karfin hali fuskarta ya shafa yace kin San dalilin da yasa nake kaunarki? Hamida tace sai ka fada? Yace sabo da Kawai kece Hamida Pipin lele duk a yanda kike Ina kaunarki,Kamar bakya kishina ke Why? Me yasa bakya min son da nake Miki? baki cancanci Haka ba a wajen iyayena,Wacce mace ce a duniya ta gagari a Mata kishiya duk wacce ta sa Rai zata zauna ita Daya ta yaudari kanta,Fiyayyen halitta ma ya auri mataye sannan matansa da Suka fimu daraja sunyi zaman kishi to mu su waye Wayarsa ta dauka ta Kira Affa Saura kadan tayi kuka ta sake dannewa tana murmushin dole Yana dagawa yace Lele me ka kirani ka min bayan ka nuna bani na haifeka ba,Hamida tayi magana Affa kayi Hakuri Dan Allah Hamida ce,Oh Hamida sai Affa yaji wani kunyarta Kamar me,Tace Ya tuba Affa kayi Hakuri ka yafe masa ka bawa Mimi ma Hakuri ya amince Nima Haka na Amince Allah ya bamu zaman lafiya ya bashi ikon Yi Mana adalci,Mimi tana gefe tana ji tace yanzu abinda kayi ka kyauta kenan? Yau da Lelene yaga wata yace Yana so ba ruwanmu a Haka Kuma ku maza kullum kuce kunfi Mata hankali,Affa yayi Murmushi yace da kinji tarihin Yarinyar Nan da kin San da Lele ta dace,bani da shakku da Lele wlh zai riketa Amana ko da baya sonta,to yanzu Mene ribar ashi wacce baya so Kai wa ya maka dole? akidarka ta boko ma ku ai ba a Baku shawara kuji sai kayi wlh ba hannuna a ciki,Kuma Ni Hamida nake so sai dai kayi Kai kadai. Ni kuma Zan nuna muku Ina da iko,Iko sai Allah shine me Iko Kuma idan Allah baiyi ba baka Isa ka daura auren ba ta fice fuuuu. Bangaren Hamida Kuwa Lele ta taimakawa ya cire kayansa Yana ta faman tunani,toilet ta kaishi sannan ta kulle Masa ta fito,tana fitowa dakinta ta wuce ta kulle tare da fadawa saman bed ta fashe da kuka Hamida harda jiniya Idan tayi tayi karshe tace Lelenaaa...ta sake ci gaba,Har ya shirya Yana jiranta yaji Shuru Shuru dakinta ya nufa,Jin kamar ta fiya ta mike tare da fadawa toilet ta rufe kofa ta shafawa fuskarta sabulu tana wankewa tana daura alwala ya shigo toilet din direct yace I thought wanka kike,Kasa magana tayi sabo da tana bude baki kuka ne zai kwace Mata. Tashi tayi kanta a kasa sabo da Kar yaga alamar kuka,kiranta yayi Pipi...uhm Kawai ta amsa,yace Hamida ajiyar zuciya tayi tace na..na"am...hannunta ya riko Suka fito room din,fuskarta ya leka yace kuka kikayi? A'a ta furta tana girza Kai sai hawaye ratatata tafin hannunta tasa tare da rufe bakinta da fuskarta kuka ya kwace Mata me karfin,Amma Kika amsawa Affa?ban taba saninki da boye boye ba bakya boye abu me yasa kika lallaba Affa,Ni nasan wlh ba haka bane a ranki,ba...baf...bafa komai Kawai iyayena na tuna,Ina Kika sansu har da Zaki tunasu Pipi. Saman bed din ya jata suka kwanta Yana ta lallashinta har ya dan samu tayi Shuru. Bacci ya fara daukansa sai kukanta yaji ya tashi da sauri ya hangota a saman Sallaya ta daga hannu sama ana addua shine kuka ya kwace da Alama Nafeela tayi,Shuru yayi Yana kallonta ranar a haka ta kusa kwana sai da ya gaji yazo ya dauketa Yana ta lallashi bakin ciki ya isheshi suna zaune lafiya da matarsa anzo an ruguza musu farin ciki. Nan na kawo karshen Part 1 Saura part 2 Idan na huta kwana Uku ko sati daya zanci gaba Ina godiya fans da masu godiya da masu sharhi,Wanda ban bawa page ba suyi hakuri abin sai a hankali Zan Basu a part2 Inshaallah Ayi Hakuri banyi editing ba yau. WARE BAIKO GROUP page naku ne AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 (JANNAT) Part 2. 66-70 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne mutanena BESTYNBEELAT AUTA UMMI DEEJAT AUNTY NICE MAMAN SAMHA UMMIN SADEEQ UMMIN NAJWA QUEEN MEENAT MHD Washe gari Jannat da asuba ta tashi tayi Brush da Alwala ta fito Sallah ta gabatar ta zauna tana ta azkhar Allah ya hore Mata Addini har rana ta fito sannan ta Mike tayi wanka ta shirya cikin wata kodaddiyar atamfarta ja Riga da zani,Hijab ta saka baki fuskar Nan a daure ta fito ,tana fitowa Fauzan ya Sha wanka cikin kayansa na NYSC zai fita,Mimi da Affa suna dining dake da wuri suke fita aiki,har kasa ta tsuguna ta gaida Affa ya amsa da fara'a ta gaida Mimi itama ta amsa,Fauzan ta dan kalla tace barka da asuba ko jiran amsawarsa bata yi ba ta mike zata bar wajen Garin sauri ta dan bigeshi bata kula ba,Mari ya kwada mata Yana masifa naki da hankali Zaki bata min Kaya,a fusace ta kalleshi dafe da kumatu Shuru tayi ta juya ta tafi Kawai a ranta tace wlh sai na rama. Affa ne ya lullube shi da fada ya kamata kusan darajar dan Adam sabo da yanda Allah ya karrama dan Adam,bana son irin wannan ka kiyayeni tam,Mimi tace Fauzan bai kamata ba gaskiya ka gyara,Shuru yayi ya zauna Yana cin abinci,Bacci ta koma sai 11am ta tashi ta fito taga ba kowa duk sun tafi wajen aiki sai masu Aiki, tace ana yiwa boko baurta a gidan Nan,abinci taci itama ta koshi sannan ta koma dakinta ta dakko Qurani tana tilawa,tana gamawa ta koma sauran littafan addini tana bita sai data gama sannan ta fito bakin gate Har kasa ta tsuguna gaban su Sale tace Ina yininku suka amsa da fara'a tace Wai a gidan Nan ba cinnaka Kuwa nemansa nakeyi zan hada maganin Ulcer,Inuwa da Sale suka kalli juna cike da mamaki,Inuwa yace tab ai sai dai kije Garden jikin fulawoyi da bishiyu maybe ki samu,na gode tace ta nufi garden tun 2pm take neman cinnaka a garden din bata samu ba har Allah yasa ta ga wasu birda birda a kasan bishiyar mangoro harda masu tashi, farar Leda ta dakko tayi ta zubawa sai da ta tara da yawa sannan ta daure ledar ta koma ciki A dakinta ta ajiye tazo taci abinci tayi sallah. Sai da asuba tana Jin fitar Affa da Fauzan masallaci tun kafin tayi Sallah ta fito sannan ta haura sama a hankali Kamar barauniya da sauri ta Bude dakin da taga Fauzan Yana shiga,Bedroom dinsa ta shiga ta hango takalmansa guda biyu na nysc sai ta cire dankwalinta ta goge Masa shi tas ta zuba cinnaku a ciki da yawa,ta koma wajen dayan ma ta goge ta zuba cinnaku incase of duk Wanda ya saka akwai cinnaka ciki,gashi sun Sha wahala a leda kasa fita sukayi daga takalmi,ficewa tayi tayi Sallah tare da wanka Sannan ta fito ta iske Mimi,Fauzan da Mimi suna breakfast duk sunyi Shirin fita,Fauzan yasha kayansa na nysc yau ma akwai abinda suke Wanda dole sai sun sa kayan shi yasa ganin takalmisa fes fes bai ko goge ba ya saka abinsa Tun Yana cin abinci yaji Kamar abu na bin kafafunsa haka dai ya fita compound da key din mota a hannunsa,Yana bude motar yaji abu ta cikin wandonsa ya galla Masa cizo a jere, tsalle ya buga cizo suke bashi ta ko Ina a cinyoyinsa,Su Inuwa suna kallo,Dan fuskewa yayi ya tafi zai shiga mota ya saki Kara tare da dawowa baya ya fara cire takalman Ina cinnaka har cikin duwawunsa suke ta gallawa cizo da sauri ya shiga zare belt din wandon ya zuge zip tare da yin kasa da wandon Boxers dinsa suka bayyana azaba ta isheshi gashi wandon wani tight na daukan wanka sai an nutsu ake cirewa, wandon ya sutale kasa iya dunduniya gashi yaki cirewa ga azaba ta isheshi Yana ta Sosa cinyoyinsa da Suka yi rudu rudu abinka da me haske. Su Inuwa ne Suka Zo Alhaji lafiya? Fauzan ya daura hannunsa a bayan duwawunsa Yana ta Sosa wajen ga cinnaka a ciki Kara cizonsa yake,duk ya hada zufa Ya dafa sale yace Inuwa karasa tsige min wandon Nan Inuwa da sauri yace Alhaji ai cinnaka ne ga wasu Nan suna yawo a jikin takalminka,dan Allah ka cire min Ni cewar Fauzan,Inuwa ya fara kici kicin cire wando ya kasa Fauzan ganin haka yace matsa dalla ya zauna a kasan Interluck dirshan cinyoyi duk a waje ga dan guntun boxers Sale sai kunshe dariyarsa yake ya tabbatar sabuwar bakuwa ce me kunci itace take neman cinnaka jiya,idan ba haka ba Ina za a samu kwari a gidan Nan,Shidai Fauzan da kyar ya samu ya zare wando sannan ya mike Yana zazzage boxers dinsa Kamar zaiyi tsirara,Sale ya karbi wandon ya karkade sai ga cinnaku sun zubo kasa,da sauri Fauzan yace jefar da shi ya koma ciki da sauri,Mimi da Affa suna zaune Jannat tana gefe tana karyawa ya shigo da Yar Riga sai boxers,Mimi Tace lfy Kai Kuma? Cinnaku ya iya furtawa ya haura sama,Suka dinga dariya Cinnaka ne ya shiga wandonsa,Affa yace sai dai idan a can wajen da suka je jiya ya kwaso cinnaka amma ai Naga ya bada kayan ma wanki,Fauzan ne zai maimaita maka Kaya ba a wanke ba,Dariyar Jannat Suka ji Kamar mahaukaciya hhhhhhhhhh Yi take harda rike ciki,tunda suke basu taba ganin dariyarta ba sai yau Kuma da yawa Haka. Mimi ta kalleta tace ke sai a mugunta kike Dariya abinki, Fauzan wanka yayi ya fito daure da towel da kayan Nysc duka ya kwaso da takalman Nysc ya watsowa su Inuwa waje yace ku duba lafiyarsu a sake wanke komai a washing machine ku tabbatar Engine ya markade Yan iskan cinnaku,Affa Dariya yake sosai ya kalli Fauzan yace Gaye how far, Fauzan da har yanzu susa yake,Dariya ta sake Kama Jannat ta kyakyala abarta,Fauzan shima sai yau yaga dariyarta kallonta yayi yanda duka dimples dinta suka loba tayi wani kyau,wani dan garin maganinta ta dakko a leda Fara a kulle ta bude ta zuba Dan Rabin cokali a ruwan lipton ta shanye. Lokacin Affa ya fita Mimi tace ke Kuma wannan maganin fa?Jannat yau nishadi take ji tace maganin sanyi ne a gidanmu gidan marayu wata tsohuwa take raba ma Yan Mata tana koya Mana in ya Kare ma Zan koma na karbo wani sabo da tsaro ta hanamu ma tsarki da ruwan sanyi Dana zafi mukeyi mu,Mimi tace ta muku gata ta kyauta,Baki Fauzan ya tabe tare da barin palon,Yau Mimi sunyi hira ta hankali da Jannat Kamar ba ita ba. Hamida ce tayi Sallama ta shigo palon Aslam yana kafadarta Mimi tace daga ina Haka da safen Nan? Asibiti na Kai Aslam aka karasa Masa rigakafinsa shine na biyo mu gaisa Ina Affa fa? Mimi ta karbi Aslam tace yanzu ya fita sabani kuka yi,ya banji karar motar ba? Lele ne ya kaini ya ajiyeni ya wuce wurin aiki sai ya dawo zamu tafi gida,Mimi tace kice yau yini zan sha,Jannat ce ta kalli Hamida wacce ke zaune ta dau uban wanka cikin wata abaya me tsadar gaske,wani kamshi Hamida takeyi me arnen dadi Wanda jikinta ne ya rigada ya Kama sabo da gyara, tace Ina kwana? Da fara'a Hamida ta amsa tace wlh ban kula dake ba surutu ya dauke min hankali,ba damuwa ta furta,Jannat son Yara ne da ita sabanin Hamida ita da Harkar gabanta takeyi Kawai. Daukan yaron tayi,tunanin Hamida ko Dan Jannat zata auri mijinta ne shi yasa ta canja take wani daukan danta,Jannat ta samu yaro me kyau ta makale ta hana kowa,Fauzan ne ya fito cikin Shadda sky Yana kamshi,Yace Aunty Shakira,Dariya Jannat ta sake Yi Karo na biyu ta kalli Fauzan ta manta basa mutunci tace au nick name dinta ne Shakira,Hamida tace don't mind them tsokanata suke Fauzan ya gallawa Jannat hara yaja tsaki,itama Shuru tayi taci gaba da kuncinta ita da Fauzan kowa Fuska ba Rahma,Goya Aslam tayi tana ta reno abinta har Sallah Yana bayanta taje tayi Hamida tuni ma tayi bacci ita. Sai Yamma Nabeel yazo ya dauki Hamida ko gidan bai shigo ba Jannat tana rike da Aslam ta raka Hamida har mota,tun kafin Hamida ta karasa Lele ya fito tare da budewa Pipinsa mota ta shiga ko kallon Jannat baiyi ba,Sai da tace Ina yini sannan ya kalleta kadan tare da furta Alhmdllh ya Shiga mota Yana Magana da Pipinsa,Jannata ta mikawa Hamida danta ta juya tayi tafiyarta,Hamida tace na gode,Lele ne ya kalli Hamida yace muje gida ko Ina? Ranta a bace tace gida,driving ya fara ya canja zai kaita shopping taki magana Sam sai lokacin tace gida fa nace ko na shiga Napep ne,Nabeel ransa ne ya baci gaba daya Hamida ta canja Masa,yace look bazai yuwu a gabansu kije normal baki nuna komai ba kizo ni kina tayar min da hankali ba,Ni nace kicewa Affa kin amince a gabansu ki nuna ba matsala ni kizo kina azabtar dani,a hankali yayi parking a gefen titi ya sassauta murya yace why Hamida why the sudden change? da me zanji ya kike so nayi bayan ke Kika ce kin yarda tun daga ranar bakya kwana a dakina sai dai nazo naki in ban Zo ba you don't care,you don't care about me anymore,kanta na kasa ta fara cewa ni...ni... gidanmu Zan koma dan All....hawayen da suke Neman hanya suka gangaro sai kuka sosai take yi,yace Allah ya shiryeki Pipi yaja mota ya dauki hanyar gida. Yana parking a gida ta fito shima Haka tana shesheka yace bani dana karki jefar min ya karbi Aslam ya Kara gaba Yana cewa Allah ya yaye Miki a haka kike nuna ke ta Allah ce akan yarinya 17yrs kina wannan shirmen yanzu da ace da gaske kuma ni nace Ina sonta ya kenan? Sai ki kashe kanki ko me, bayansa tabi tana cewa dan Allah ni gida zan tafi ka sake n...kafin ta karasa ya kwasheta da Mari are you stupid...are you mad?ki kiyaye ni na fada Miki duk abinda zakiyi kiyi amma wlh duk ranar da kika Kara furta min na sakeki what I will do to you ehm you will no like it, so you better change this your stupid attitude Yana gama fadar haka ya bata Aslam yayi gaba abinsa. Bedroom dinta ta wuce tayi lakwas ganin ransa ya baci amma Shuru tayi,har ta mikawa Nanny Annur da kayan da zata sa Masa tayi wanka itama tare da Shan tsuminta kala kala,wani turare ta dakko shima na matan aure ne da wani hadi tayi amfani da su ta tsuma kanta,duk rikicin Nan bata fasa gyara kanta ba,ta gama abubuwanta ta Shafa wani turare kala kala a jikinta tana Shirin fita ta karbo Aslam sai ga Nabeel ya shigo sanye cikin kayan baccinsa masu kyau brown,ita data Masa laifi bata tunanin zata iya ganinsa a bedroom dinta ba yau,gefen bed dinta ya zauna tare da tallafe fuskarsa da hannayensa,light ta kashe ganin Aslam yayi bacci Kuma baya tashi sai asuba shi yasa Watarana Yana kwana wajen Nanny ma,saman cinyarsa tazo ta zauna ya tureta dariya tayi tare da furta Baby I'm sorry bazan sake ba ta koma ta sake zama a cinyarsa tana shafa gemunsa da sajensa Leluwan kamshi please forgive me, kaji ta furta da shagwaba Wanda sai da tsigar jikinsa ta tashi,kafadarsa ta dan girgiza Lelen Kyau.. Lelen Pipi..Lelena ta wani saki kukan shagwaba. Bayan kin daina so na sai tayar min da hankali kike yanzu yaushe rabon Dana muyi Hidima bana Jin dadinki kwata kwata to kayi hakuri na daina haka kike cewa daga ganin yarinya yau Kika birkice ko da me ta fiki oho,to muyi bacci kayi hakuri,Kinga kin jawo na mareki,dama Mari Kam ai ba yau ka fara ba,sorry ya furta tare da kwanciya a saman bed din ya daurata a saman sa ta kwanto hannayesa suna saman mazaunanta suna shakar kamshin juna,lokaci guda ya birkice ya fara aika Mata da sakonni Masu zafi suna tsotsar baki kamar ba gobe,rudewa yayi ya fara zaucewa itama Pipi haka,a rude ta fara cire Masa kayansa yayin da tuni ya fige rigarta ya jefota kasa itama ta watso nasa,Gorar madara ya cafka Yana murza Mata su yanda yake so yana tsotsarsu Kamar jaririnta kirjinsa take shafawa da nipples dinsa tana ta sambatu,Lelena ta furta tare da kamo hannunsa ta Kai shi dausayi tace ji da Nan, Naja'atunsa ya Mika Mata ta cafketa Su Pipi an Saba da Naja'atu,Lele ya gigice in Banda Nishi da gurnani ba abinda yake,ji yake kamar zai sume sabo da dadi,Hamida ta tayi tana hango dadinta itama cewa take nima...Nima...lelena nima....sai data ba Lele dariya,yace sai kace nace bazan miki ba. Jawota yayi tare da daura kafafunta a kafadunsa ya fara Sha Mata dausayi Hamida Kamar wata Yar bori haka ta haukace masa tana ta faman cewa Lelena na gode...na....gooo....yes...Lele a nutse ya shigeta yaji ta Kara wani dadi na musamman ta sake matsewa ya fara baje harka,Yana ta sambatu itama haka...Yana Yi tana hardcore Lele fuck....ai ko Lele shi haka yake so suna gamsuwa ko baccin kirki bai Bari tayi ba ya dawo,a iya dare sau uku yayi,asubar fari suka sake sai da Hamida ta gudu da kanta sabo da Dausayin yasha wahalar gaske . Washe gari gidan Mimi ba kowa har masu Aiki sun tafi kasuwa Inuwa ne Kawai a bakin gate,Affa da Mimi ma suna wajen aiki,Jiya Jannat cikinta a rikice ya kwana sabo da ciye ciye da tayi,tasan ma ba kowa a gidan ta maida kwanika ta fito Palo tayi wata doguwar Mika tare da gantsarewa tace Masha Allah yau ba kowa dole na tuna gidan marayu yanda idan Yan daki sun fita muke sakata mu wala dama cikina a rikice yake yanzu zan samu in sace iskar cikina,Ni kadai a gida ba me ji ina banka tusa ta son rai na,mika ta sake Yi ji kake bottt....ta saki tusa da karfi Fauzan dake ta sama ya rike karfen steps har maganarta Yana ji tsab a kunnensa tusa na tashi ya danne hancinsa sai ji yayi ta sake sakinta burrrrrrrr....barrrrrrrrrrr saman kujera ta fada tayi wani bododo da duwawu gaba sai bur...bur.....Fauzan ya toshe hanci da Hannu daya dayan Kuma ya nuna ta tare da furta ke jahila bude kofa ki fitar mana a palo dakinsa ya fada da gudu tare da banke kofarsa yasa key sai lokaci ya janye hannunsa da ya toshe hancinsa. Kunya ta Kama Jannat ta mike tsaye tare da Dora hannaye akai yau na Shiga Uku ya zanyi da kunyarsa,ban San Yana gidan ba,ya akayi ban kula da shi ba wayyoo bazan sake hada Ido da shi ba wayyo na cuci kaina tana yarfe hannaye ai daki ta fada tare da kulle kofarta itama ta fashe da kukan kunya da takaicin kanta. Zuwa dare Affa ya dawo ya Kira Lele yazo Yana son ganinsa,lokacin suna dinner da Hamida tana bashi abinci a baki tunda taji muryar Affa gabanta ya fadi tasan bazai wuce akan maganar auren ba,kuka take Neman saki Nabeel ya girgiza Mata tare da furta don't start bana son ganin hawayenki Pipi dan baki San me nake ji bane,Zan bika to muje sai na zauna a Palo ni kaje ka fito mu dawo gida,fine tunda kin bukata mu gama muje,Suna gama cin abinci Suka shirya Hamida ta matsu taji mene ne ake Kiran,ita kadai take tunanin ko kudin aurensa za a Kai oho, Aslam Yana hannunta ta Mika Masa ta karbi key din ita ke driving yau,Suna zuwa ba kowa a Palo sai Fauzan da Mimi,Fauzan ba surutu yake ba shi yasa sai karar tv Kawai kake ji,Jannat Sam ta kasa Fitowa sabo da kunyar Fauzan abinda tayi a gabansa tana Jin muryar Hamida tasan anzo Mata da dan jaririn da take kauna amma ba damar Fitowa,Nabeel Mimi ya gaisar tace Yana sama muje Suka wuce sama tare da Mimi,Fauzan sama sama suke dan Hira da Hamida yace ya kusa komawa Abuja bazai iya ba shi can yafi Masa dadi Daddy ma ya Masa Hanya an maida shi Abuja acan zai karasa Service dinsa. Jannat ta kwalawa Kira yau baza kizo mu gaisa ba ga Baby Aslam na kawo miki,Jannat Kamar ta fashe da kuka haka taji ga Fauzan Yana wajen,Hijab dinta ta saka Kato ta fito tana bin bango tana rabe rabe,Hamida tace kullum Jannat sai kin tsiro da sabon Hali first ganina dake ba Haka kike ba,last ganina dake kin koma mutuniyar kirki and now kin fito kina kunya kina rabe rabe kina bin bango kamar daga Kauye common relax Nan kamar gidanku ne fa,Jannat kanta a kasa tace ai Ni kuli kuli ce ba a gane gabana,Allah daya zance Miki ki yarda Aunty ta duka tare da cewa Ina yini Aunty Hamida,Hamida tace lafiya Lau ta dauki Aslam tana Masa wasa. Suna kallon wani Indian Film Jarumin ciki Yana ta rawar kafa a Kan budurwar har Fauzan Yana kallo,Zaraf Jannat tace kyaci ubanki Indai Namiji ne Yana aurenki Watarana ma Sai kin Masa magana yaki amsawa ke Kinga Yana washe baki ya haukace a kanki Zaki gane kurenki ki dai shiga daga ciki maza ba mutunci ne da su wani Mari sai ya kwada Miki Mari Aunty kune masu aure ko ba Haka abin yake ba? Hamida tayi dariya tace ke bar Yan Iska ai idan kika yi iska ma ta fishi mutunci sai kiga an daidaita, Jannat harda Dariya yau tace ashe dai kin gane Kuma Yana lallabowa kice uhm uhm Basu da aiki sai dai su zuke Miki juice su wuce karki sake cewar Jannat,Fauzan Yana Jin Haka sai da ya kalli Jannat ya sake kallonta anya Yarinyar nan ba Yar tasha bace Kuwa ko ta taba aure,Hamida yanzu anyi hankali Ido ta kyaftawa Jannat Wai Fauzan Yana wajen,Jannat tace yo yaro ne shi duk haka suke shima hakan take mene bai sani ba Inama zaiyi aure ki Zama dan kuda ki fada dakin ki gani ya ake ciki ai mune muke ganinsa a mutum banda matarsa,Hamida Kunya ta lullubeta,Fauzan abin yasha Kansa tashi yayi ya Kama gabansa,Yana tafiya Hamida ta dinga mata bai kamata ba,Mimi ce ta leko tare da Kiran Hamida Nabeel Yana zaune ransa a bace Hamida tana ganin Haka tasan karshen zancen,Affa yace Hamida hakika kin birgeni Kuma Allah ya Miki Albarka nasan ke ta daban ce,Ni nace Zan karawa mijinki aure amma baki tashi hankalinki ba Kuma Baki nuna Mana ko a Fuska ba,Baki fasa mutuntamu ba ba shakka nasan munyi dacen suraka da ace Mata zasuyi koyi da halinki da an zauna lafiya dama abinda ake so ko wacce uwa mace ta Zama ta gari inda zata tarbiyyantar da yayanta,ta koya musu Susan waye Allah,soyayyar Annabi muhammadan (saw),su San addini,su koyi daraja Dan Adam,mu'amula da sanin rayuwar duniya inda duniya zata Yi alfahari da shi yanda idan mutum Allah ya karbi rayuwarsa al'ummar dake yankin zasu Yi kukan rabuwa da shi ana ganin an rasa wani jigo a rayuwa ku iyaye Mata kune nauyin wannan yafi karkata a kanku Kuma ba a samun Haka sai uwa ta kasance ta gari. Kamar Yanda kuka ga kudancin kasa na yi mace zata haifi da ta dinga kosan siyarwa a Haka zata tura danta kasar waje karatu wata gasa Masara take amma danta Yana karatu a waje wani ya Zama doctor wani ya Zama lawyer gasu Nan da dama,Amma mu arewa Miji shi zai bata kudin makarantar Yara,littafa komai da komai har zuwa kudin cefane Amma sai kaga uwa Watarana tallafi idan tayi kadan ta dinga fallasa kenan ita an barta da komai ita kadai ga wasu can suna gina Al'ummarsu da Addininsu Kuma in ka duba dan abinda suke samu na sana'a bai taka Kara ya karya ba,Ilmi shine jigon rayuwa Kuma ko a kanki Hamida munga ranar Ilimi da ake tilasta Miki sai kinyi ilimi,sannan rashin ilimi a baya da rashin kulawa ta iyaye da baki samu ba lokacin baki San fari ba baki San baki ba har takai ga an samu wannan Matsalar a baya yanzu gashi kin Zama abar koyi abar Alfahari Ilimin addini Dana zamani shine jigon rayuwa idan mutum yayi amfani da shi,yanzu babu wacce nake Alfahari da ita irinki Alhmdllh Hamida dai tana ji,Lele a ransa yace Nasiha ko lallashi sabo da za a Mata kishiya ba,Amma kazo gidana kaga kukan Hamida da tsiyar da take tata min akan auren da baka yabeta Haka ba harda bada shawarwari a fili Kuma shidai baki ya gyara kawai. Hamida tace tun farko da ace Ina da uwa da ban kasance haka ba a baya Asalin Baffa na fulanin kauyen Adamawa ne Kamar yanda Papa yace su Iyayen su sunyi haihuwa da yawa amma duk Allah bai bar musu ba sai iya Baffa na Kabiru sai Hamza Papa kenan sun taso da son junansu da kaunar junansu,lokacin shi Papa Yana shekara goma shi Kuma Baffa na yana Shekara ashirin iyayensu Suka rasu sabo da tsakanin Baffana da Papa sai da aka haifi wasu da yawa suna rasuwa kafin a haifi Papa,Tun asali iyayensu talakawa ne shanun Basu da su ma duk sun Kare sai Noma a haka suke ci da kansu shima din da kyar ake kaiwa Har Baffana ya girma Noma yake a haka yake daukan Nauyin Papa ya sashi a makarantar boko data Allo sabo da shi Baffa iya ta Allo yayi kuma Yana so kaninsa yayi karatun boko a haka Kuma gaba daya dan abinda yake samu bai da yawa duk akan kaninsa suke karewa,Lokacin Baffa ya Isa aure amma baida abin yin auren amma Yana da budurwarsa Khadija Mahaifiyata kenan wacce ita kadai iyayenta suka haifa,suna soyayya Abu yayi nisa Iyayen Khadija na wancan lokacin masu arzikin shanu ne shi yasa suka ce baza ta auri talaka ba gashi Kuma suna son juna,Karshe Har Baffa take bi dakinsa tunda lokacin iyaye sun mutu gidan ma ya rushe sai dakinsa daya tal da suke kwana da Papa kaninsa. Khadija tana zuwa Yana hanata ta daina zuwa sabo da shedan ita Kuma kauna tayi nisa ta kasa fin karfin zuciyarta a Haka Watarana taje kaddara ta afku ta Kai ga sun sadu da juna a wannan rana, data koma gida iyayenta sun gane babarta ta kaita daki ta karfi ta duba taga ai an rigada an lalata musu yarinya,sun tabbatar Kuma Kabiru ne sabo da shi kadai take bibiya sabo da haka suka jira har wata biyar Allah bai sa ta samu ciki ba sabo da a lokacin yarinya ce ta gaske Kun San mutanen da, to bayan haka Suka ce Kawai a daura musu aure tunda abin yazo da Haka,Babanta shi ya ginawa Baffa gida ya aura Masa yarsa Khadija,Bayan aure kullum suna kaiwa da kyar cikin talaucin ga nauyin Papa shi yake dauka har ta kwashe shekara takwas bata samu ciki ba sai a shekara ta goma ta samu ciki,watan cikin uku ya zube har Papa ya Gama secondary Yana diploma har ya gama ya samu aikin gomnati bata samu ciki ba Papa a haka Baffa ya Masa gini ya Masa aure da Ummi wacce itama tare Suka Yi secondary da Papa said dai ya fita da aji uku,Bata karasa ba aka musu aure har Suka haifi Yaya Sulaiman bayan shekara uku Suka haifi Aunty Karima,sai da Aunty Karima tayi shekara biyu sannan aka samu ciki na aka Haifeni,a wannan shekarar Iyayen Khadija ita Suka rasu. Ina da shekara uku a duniya Watarana Mamata da Baffana sunje Kano Siyayya lokacin a gidan Papa Suka barni ba a tafi dani ba sun dawo gida an saukesu a gefen titi sunzo tsallaka titi mota katuwa ta bigesu Nan take Suka mutu gaba daya dan Naman su ma pieces yayi,Daga nan na taso a hannun Ummi. Bata takura min,ba rashin ci ko na Sha sutura ko yaushe Papa Yana min sai abinda nake so,Papa da Baffa basu da zafi,basa fada sai dai Nasiha zasu maka sai dai mutum yaki dauka Wanda Papa bai da hakki na sabo da duk wani gata da kulawa ya bani abunda na rasa training na uwa ba abinda Ummi zata sa nayi ko tace na bari ba ruwanta tunda ba ita ta haifeni ba,yaranta take nunawa komai na duniya shi Kuma namiji ba a gida yake ba bazai yuwa ace shine zai nunawa 'ya mace komai ba musamman ya mace dole sai mace,sai dai Allah ya sawa Yaya Sulaiman da Karima kaunata suna so na wani abin ma sune suke nuna min,sannan Karima bata gari a bauchi tayi University da service,Kuma secondary school Boarding tayi,Yaya Sulaiman ma haka sai ni sai Umma sai Papa a haka na taso,sai da Yaya Sulaiman ya dawo gida da Zama yaga halin da nake ciki shine yake zaneni a lokacin bai San duka kangarar da yaro yake ba. Thank God na hadu da Lele duk da an samu matsala amma shine silar komai nawa a rayuwa,kullum mutum ya baka dubu daya akan naje makaranta har Mai afkuwa ta afku Kuma Alhmdllh komai ya wuce. Sannan Affa ka yafe min takarda da aka kawo maka akan Papa ne ya rubuto a aura min Lele ba Papa bane wlh Ni na sa Shehu ya rubuta maka,Dariya ta kama Mimi har Nabeel da Affa yace ja'ira dama kece da kanki ba Papa ba? Hamida tace nice wlh na tsara Kalamai Kuma nayi wuf da shi suna ta dariya Papa yace lallai kin wanani,yanzu tarihin iyayenki waye ya fada Miki komai? Tace Papa ne Sanda yaga nayi hankali ya fada min Yace shi yasa lokacin da aka tabbatar Ina da cikin shege basu damu ba ta tabbata zina tana bin dangi zai wahala abinda kayi ba ayi maka ba,wannan izina ce a garesu, sai dai Allah Yana fitar da matacce daga rayayye haka rayayye daga matacce,Wannan haka yake Allah ya tsaremu Affa yace shima Nabeel ba banza ba a bar dai kaza cikin gashinta Affa yayi wayo dan Kar aji yayi shima. Yace magana ta karshe Hamida Hakuri Zan sake baki amma kafin Nan Kira min Jannat Hamida ta fita sai gasu sun dawo da Jannat da Fauzan,Affa yace yawwa Fauzan zauna ka zama sheda bari ayi a gabanki Jannat ya nuna Nabeel yace kiyi hakuri na zaba Miki miji a matsayina na uba a wajenki ko shakka babu nasan Zaki min biyayya wannan itace abokiyar zamanki, Nabeel na yarda da nagartarsa zai rike ki Amana ku zauna lafiya na Kai kudin aure inda na daukoki sun Kuma nada ni waliyinki,ga Nabeel Nan Inshaallah Nan da sati biyu zan daura muku aure. Kallon Nabeel yayi yaga Nabeel ya fara Hawaye,yace amma anyi lusarin da mijin tace anan, Nabeel yace ai kishiya kace zaka min,Mimi ta fashe da dariya tace ikon Allah Nabeel Kaine za a yiwa kishiyar ma? Ba kunya yace ae ai Ni pipi ne pipi ma lelece. Affa yace Yarinyar Nan Jannat da kake ganinta Marainiya ce a hannun kishiyar uwa ta taso aka turata karuwanci Abuja an gama gogar da ita a gidan karuwai tayi wata Uku ana koya Mata kwalliya da yanda zata dinga amfani da maza Yar asalin Katsina ce bata da kowa tasha wahalar rayuwa a yanda aka bamu tarihinta a gidan Marayu ranar farko data fito gefen titi layin ashawo a nan Allah yasa ta hadu da wani ma'aikaci a gidan marayu Nan ya ganta yarinya karama ya tambayeta tarihinta ta fada Masa to bashi da aure sai yace bari ya kaita can gidan marayu ta zauna kafin ya samo Mata Iyayen da zata zauna a hannunsu har su aurar da ita,tun daga Labarin Nabeel Bai yarda ba amma gata da iliminta da komai Kawai dai Allah sarki Suka ce. Affa yace abin da ban tausayi Allah ya baku zaman lafiya kuje aci gaba da shirye shirye. Baki Mimi ta tabe ta tashi ta fice ita bata goyon baya. Fauzan yace a ransa Nabeel ka hadu da karuwa za a kasheka da tusa cikin dare ni Kam Nan da kwana Uku Zan koma Abuja ba ruwana Nima Kar a dakko wata a lika min. Jannat Kuwa a dakinta ta kwanta tace baza ta sabu ba ni da nake Neman inda Zan samu kudi dama Ni burina a fitar da ni daga gidan Marayu dama,wata Daya Kamar Ina prison gashi Ina so can nasan me ake ciki dole na gudu na bar gidan nan tunda Naga sunfi karkata a ilimi ba kudi ba to bada ni ba Wanda na samu Alhmdllh secondary private me kyau dana Yi ta isheni yau cikin dare Zan gudu in koma Neman kudi na Kawai duk abinda na samu naje na Kai can. Hamida ta koma gida tana ta rusa uban kuka tun Nabeel Yana lallashi har ya gaji a saman Sallaya ta kwana tana Nafeela Allah ya rage Mata kishi ya Basu zaman lafiya ya bata Hakuri,Kuma Allah Kar ya bari Lele ya juya Mata baya. Cikin dare Mimi itama masifa take ta yiwa Affa tace wlh baka da adalci Sam bakayi ba Al'amin baka Yi ba,Affa ya juya baya sai bacci ko a jikinsa. Cikin dare Jannat ta tattara nata ya nata ta sadada ta bi ta wata karamar kofa ta bayan garden dake sadaka da wajen gidan ta bude a hankali ta sadada ta bar gidan tana Isa titi da kyar ta samu Napep sai ta Sha karfe dayan dare ranar sai a tasha ta kwana motar Asuba tabi sai birnin tarayya Abuja. Fauzan shirye shiryen tafiya yake Kar Affa ya samo wata nan gaba ya lika Masa shima duk basu san Jannat ta fece ba tuni. Sharhi dan Allah fans Ina godiya. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 (JANNAT) Part 2. 71-75 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Mrs Aboubacar Maryam Umar M Bash Suleiman Murja Ummu Annur Nabilancy Mrs Muhammad jmsy Mmn Sudeis Rouqayya Bello Murjanatou Mrs Aminullah Maman Dr Godiya ta musamman Ummu Shafa'at Mummyn Sultan Maryam T Baliya Cool lfe Hauwancy S.y.Sagagi Umma Halliru Jibril Maman Raiz Khadija Dandume Hauwaumuhammadhamza Asmausaad Ummu Ilham Washe gari saturday ba aiki da safe su Mimi har Suka gama breakfast basu ji motsin Jannat ba Wanda a ka'ida ana breakfast take fitowa gaida kowa amma Shuru,har 11am Affa yace Wai Ina Jannat ne je ki dubata,tashi Mimi tayi ta Shiga dakinta ba kowa wayam ba ko handkerchief nata babu ko Yar letter, tace to ta gudu ba ita ba kayanta ta kwashe komai,salati Affa ya saki tare da dubawa dakin da Kansa komai nata babu yace tab na gama yawo wlh idan gidan marayu Suka Zo duba yarsu naga ta kaina wlh akan guduwar da tayi Gomnati sai ta daureni Kuma duk duniya ba Wanda ya Isa ya karbo ni,Mimi tace Innalillahi wa inna ilayhirrajun kaga abinda ake fada maka gashi nan garin Iyayinka da kwashe kwashe ka jangwalo Mana bala'i da hannunka,Affa yace Allahu Akbar Allah ya sani niyyar taimako nayi fisabilillah Allah zai kubutar dani Allah ya bayyanata in maidata gidan marayu inda na daukota, Mimi ta tambaya ko an ganta ka fasa aurawa Nabeel din? yace Ina fa Zan aura Masa ita ai na daina har a bada ba ruwana,Mimi tace maganinka kenan ai Wai Kai na Allah,to da na shedan kike so na Zama cewar Affa. Fauzan ne ya fito yaji ana cece kuce Jannat ta gudu ya dinga yiwa Affa Dariya yace yarinyar dama ba Yar arziki bace daga gani anyway Ni dama gobe Zan tafi Affa yace kafi ruwa gudu dariya sukayi gaba daya,sai wurin magriba Mimi ta Kira Hamida tare da fada Mata halin da ake ciki,ko ta dawo Affa yace ya fasa aurawa Nabeel,lokacin Hamida tana kitchen Lele Yana Palo Aslam Yana hannunsa Hamida ta fito da gudu sai data bawa Lele tsoro ta fara tika rawa ba kida abinda Lele bai taba gani tayi ba sai yau tana haki tace Jannat ta gudu jiya cikin dare Affa yace ko ta dawo baza a aura maka ita ba ai sai ta fara waka ahayye nanaye Yan matan duniya Duwaiwai Abu na sama na kasa, sai ki haka ki haka Duwaiwai tana murgudawa Lele gaba daya ta zare Lele yana ta dariya yace Kinga fa Aslam Yana gani,me ya sani Kai koma ya sani ya sani yau murna ce ta tashi taci gaba,Lele yace na gani akwai Duwai zauna Yana dariya ya dauki remote ya Kai Mata channel na wakar Nija Lele ya mike ya wani zaro kudi Yana ta Mata liki Yan dubu dubu Hamida ta nanawa Nabeel Mazaunai a Naja'atu tana ta haukar murgude murgude Yana Mata liki, sai da yaji ya fara feeling Kamar yayi sex sannan yace to girkinmu zai kone Sai yanzu ta tuna ta duka tare da kwashe kayan kudin Nan tas ta soke a jikinta yace bani kudina daga Wasa sai ki kwashe Allah bazan bayar ba ai lika min kayi tace tare da Masa gwalo ta wucewa kitchen tana wata tafiya tana nishadi. Lele yace yau akwai Hidima ta kirki ba bacci,Hamida tana daga kitchen tace tunin ma wani ma ya ji. Waya ya dauka tare da Kiran Affa yace bayan sun gaisa Affa ashe Kuma Allah baiyi za a min kishiya ba,Lele uwaka Affa ya furta tare da kashe wayarsa. Jannat Kuwa da wuri ta Isa Abuja Nyaya unguwar ta masu karamin karfi ce da Yan Tasha Yan bariki duk Nan suke tarewa wasu Wanda basu da wani kudi sosai,wani gida aka sauketa dan madaidaici me kyau da shi ta Shiga,tana shiga wasu Yan Mata ne girda girda su shida ne duk kusan yare ne amma suna Jin hausa sai wata bahaushiya guda daya katuwa itama duk sun Sha kwayoyin hips da kiba sunyi wani fresh da gani kasan Yan bariki ne suna kashewa jikinsu kudi,da mamaki suke Kallon Jannat suka ce Jannat Ina Kika shiga mun Sha kuka munyi zaton ma saceki akayi ranar farko Zaki Fara business bamu sake ganinki ba daga fita Kuma kalleki da wasu Kaya lalatattu Ina Kika samo su? Jannat tace hmm ta zauna ta basu labarin komai tace wani dan iskan ma'aikacin gidan marayu ne a Kaduna ya daukeni Wai bazan Yi karuwanci ba,tana basu labarin su Affa Zee musulma ce itama tace me yasa Kika dawo ke da baki taba sex ba ranar farko Allah ya tsareki aka kaiki gidan mutunci masu arziki wlh da kinyi Hakuri kudin da kike Nema Zaki samu Kuma da kin fada musu matsalarki da tuni sun magance Miki ita,Jannat tace Boko suka sa a gaba Zee ki barni kawai ba a taimakeni da komai ba sai aure,mutumin Yana zamansa da matarsa lafiya dan cin Fuska na aure Mata miji duk da ba haramun bane amma wlh mutuncin matarsa da yanda suke soyayya yasa na kasa zama. Kawai yanzu Ina kayana na gayu da kuka shirya min na dawo kudina Zan Nema da Kaina a hankali sai na dinga tura kudin,Kun San yanzu rayuwa ce ba taimako a ciki kafin ka samu me taimakonka sai an tona,sai irin su Affa shi Kuma abinda zaiyi ne Sam Naga bai kamata ba,wallahi da wani ne daban ko marar Mata sai na aureshi tunda har ga Allah bana son bata rayuwa ta bana son nayi sex da wani face mijina,ki duba shekaru na Jannat hawaye ya zubo Mata tace ba yanda zanyi wallahi da Affa bai Sako da zancen auren Nabeel ba da sai na fada Masa matsalata nasan za a min maganinta amma sai ya kawo zancen aure a ciki Kuma mijin Hamida suna soyayya matar Nan bata taba min ko kallon banza ba Kuma tasan an bawa mijinta ni zai aura,Kawai Zan fara neman kudin da jikina is better. Yanzu abinda nake so kudin hayata Nawa ne? dubu Hamsim kudin abinci da zamuyi contribution mu zuba dubu talatin Zaki kawo naki, sabo da Kinga 3rooms ne mu Uku Uku ne a daki daya,naki room din kince ke kadai kike so a baki 1room to a Haka ma ganin baki da kudi wallahi Muka rage Miki mun biya Miki Rabin kudinki na shekara yanzu wannan Kawai Zaki kawo. Jannat tayi godiya ta irgo kudi cas ta basu,peace ta kunna Sigari tana Sha tace a Ina Kika samo kudin Nan? Jannat tace Affa ne ya bani na siyo kayan sawa,karba sukayi suka ce sauran ki adana tsansport tace ae ai dama,kayanki da komai Yana room dinki,tashi tayi ta Shiga daga ciki,har me aiki ce da su ita ke girka musu abinda suke so ita ke musu duk wani aikin gida har wanki da komai sabo da su sun Dade a Harkar suna samun kudi sosai,ana musu hanyar Alhazawa da masu kudi arna etc,Watarana ma basa fita titi Good evening sai ta kacame. Kwana biyu tsakani Jannat tayi wani kyau ansha saloon gata da gashi Kamar me,Yar Fulani Fara me kyau da ita ga kyan diri wata Yar chamaimai da ita,ta gama damewa cikin wani dogon wando da Riga,wandon me Fadi ne daga kasa sama ya matse da Yar rigarsa me siririn Hannu peach gashinta yaci gyara ta daura silk dankwali ta dan daure shi ta wuyanta surar Nan ta fito Kamar me ta zuba uban kyau kamar a saceta,su kansu data fito sai da suka koka dama sun santa tunda su Suka gogar da ita duk wani fitsara a bakinsu take ji. Mutum hudu suna da wajen zuwa akwai Wanda zasu taya kwana mutum uku har Jannat good Evening zasu fita titi,me taxi dinsu ne ya dauke su tare da kaisu can kusa da maitama inda suke tsaiwa duk da Watarana ana zuwa kame suna da hanyoyi inda suke guduwa su haure katanga. A gefen titin Mata ne gasu Nan kala kala da yawan gaske ana ta tsayawa ana dauka,Fauzan ne ke driving yazo wani Eatery kusa da wajen matan yayi parking Yana dago Kai yaga kamar Jannat, mamaki ya kamashi kamar ita kamar ba ita ba sai da ya dade a mota Yana kallonta kafin ya tabbatar da itace hakan ma Sai data Yi Dariya da Kuma digon bakin dake Kan hancinta da haka ya gano itace Gata da addini amma ta fada wannan harka yace dole ta gudu amma bari Yarinyar nan sai na bibiyeta dole sai nasan rayuwarta mene a ciki,Mata Kamar zasu cinye Fauzan sai zuwa jikin motarsa sukeyi suna juya Masa jiki komai a waje duk da haka Jannat itace kadai me shigar Kamala,Kuma ta tsaya can gefe sai tsoro take ji taki zuwa,duk motar data tsaya a gabanta sai ta gudu daga wajen ta koma baya Kar ma a zabe ta gashi Kuma kowa wajenta yake zuwa sai tace akwai Wanda take jira. Wani hamshakin me kudi ne ya tsaya matan sukayi wajensa ya nuna Jannat tazo ita yake bukata sai tayi tsalle ta gudu ta koma baya kamar zata Yi kuka tace ita akwai Wanda take jira zai dauketa shi zata taya kwana,shi kuwa yace to Zee ta shigo su tafi ta Shige mota da sauri,itama dayar ta samu nata sai Jannat tana ta wasi wasi a ranta tace Kai koma waye yazo tafiya zanyi na bishi I have to survive. Fauzan face mask ya saka a fuskarsa da farin glass ya fito ya Shiga yayi take away ya dawo Yana Shiga mota ya sa pcap ya kusa rufe fuskarsa ga glass ga face mask. A Gaban Jannat yayi parking yace ta shigo lokacin ta gama deciding zata bi koma waye ai Kuwa ta Shiga gaban mota Yan matan suka dauki sowa irin tayi dace ta samu Handsome. Tunda ta Shiga mota taga bai kulata ba itama Bata kulashi ba,wani katafaren gida ya kaita sai kalle kalle takeyi a ranta tana cewa karfa ya sace ni irin wannan gida haka ko dan mafia ne ban sani ba,Maimakon ya kaini Hotel sai gidansa. Yana gaba tana binsa ya canja murya tare da furta ga daki nan ga toilet ciki ki Zama ready kafin na zo ya fita tare da ajiye Mata ledar abinci daya ya dauki nasa daya ya fita zuwa Palo,Jannat ta zauna a gefen bed tsoro ya kamata haka ta dan ci abincin ba laifi ta mike ta tsaya tana magana ita kadai anya daya fita Kuwa ba kartan maza zai kawo su yankani ba Kuwa na Shiga Uku Mummy ta. Shuru tayi Jin ya shigo sanye cikin wasu kayan bacci masu kyau,har yau da face mask dinsa da glass Yana kamshi Yace baki da hankali ne dalla sauri bacci nake so zanyi sai kace ba biyanki zanyi ba,kiyi wanka nace to ta furta Kamar zatayi kuka ta shiga toilet da Jakarta gaba daya,a ciki tayi wanka sosai a tsorace ta shafa lotion dinta ta sa turaruka masu shegen kamshi ta saka rigar baccinta ta dan wuce gwiwa kadan me gajeren hannu ta fito tana rabewa tana bin bango, mamaki Fauzan yake Kamar ba ita ba a waye take sai dai tsoro ko munafunci ne shima ta Saba dama,da bata Saba ba taje Kan titi Neman maza. Saman bed din ta haura ta kwanta tare da lullube jikinta cikin bargo ta dan kalleshi Yana gefen bed din a zaune tace baka son Yi ne? kazo kayi karka bata min lokaci gari ya waye kace baza ka biyani kudina ba,Fauzan yace karki damu Zan biyaki kudinki Amma gaskiyar magana na fasa bana sex da karuwa sai matar aurena ta sunna idan na aura,Jannat ta Kura Masa Ido a ranta tace da gani ya hadu ko a jikinsa kaga surarsa kasan ya gama hadewa Yana yanayi da Nabeel din Hamida a fili tace tace amma dai zaka biyani kudina ko? Yace kwarai kuwa,to ta furta tace to ka kwanta mana a gefe can ko ba a nan zaka kwana ba? Wani Abu ya tuna Kuma yace bari na tabbatar sai ya haura saman bed din yace can gefen kike so ni na kwanta a can tace fine duk yanda kace,tsallakawa yayi tare da kwanciya shima,jikinta Kawai ya hau bari tana makyarkyata ita kadai ta sake Matsawa Kamar zata fada,yace a haka kike sana'ar taki tsoro kike ko munafunci yau ce ranar ki ta farko karuwa dake Zaki raina min hankali kudi fa kike so dalla matso Nan ki kwanta a kirjina,Jannat gabanta ya fadi ta matsa a hankali ta juya baya ta dora keyarta a gefen cikinsa, yace haka nace Zan fasa biyanki kuka take son Yi tace wallahi idan na juyo nono na zai taba ka ni Kuma bana so,Amma Kika fito da sura Kika tsaya a gefen kwalta kin San Kuwa irin wannan karuwancin shine mafi kaskantar karuwanci gefen kwalta kuma a haka kice musulma ce ke dauke kazamar keyarki daga jikina munafuka,kuka ta saki Masa tace Ina ruwanka dani ai dai Allah ya gani nace kayi sex ka kace baka so,Ni kaga karuwa ce ni ba ruwana yaro idan zaka ji dadinka kaji ga Condom karka bari Kuma ya fashe tam,Yace bana Sex da karuwa ni ba kalata bace karuwa tace oho maka Niace to bari naji kina da juice din,Laaaaa kaima kasan juice? kawayena ke fada,karuwan kawayenki? tace ae yace rufe min baki ko na Miki duka a gidan nan,dama haka akace ana yiwa karuwai duka,Baya ya juya Mata Yana mamaki a ransa a gidan Affa bata magana sai fushi,a Nan gata da surutu ga fara'a Kamar ba ita ba, Kayi bacci ne? ae yace ya fara baccinsa. A gida Maman Fauzan taga Shuru Fauzan bai dawo ba tace to ko Yana gidan kawu Ubaidu sabo da Watarana suna zuwa can su kwana shi yasa ba Wanda ya damu, sai d Jannat tayi bacci Fauzan ya tashi ya koma wani room din a can ya kwana da asuba tare da me gadi Suka je masallaci Suka dawo ya koma bacci abinsa a dakinsa,Fauzan karatun Qur'an yaji Yana tashi yasan itace tana Yi dama breakfast yasa Mai gadi ya siyo ya kawo Mata taji ana knocking ta zaci shine sai taga me gadi ya Mika Mata ledar abinci,na gode ta furta kawai ta rufe kofa sai da ta gama Addua sannan taci abincinta sosai ta mike ta gyara room din fes tayi wanka ta fito ta shirya tsaf tare da maida kayan jikinta ta zauna a gefen bed Jakarta tana saman cinyarta shi Kawai take jira zata tafi gida,shigowa yayi dakin sai da ya fesa wanka ya Sha wani yard brown me tsada Yana kamshi,face mask dinma brown ya sa glass baki babu yanda za ayi in baka yiwa mutum farin sani ba ka gane shi,itama ba irin sosai ta sanshi ba tunda basa shiri kuma bata dade a gidan Affa ba,bata taba sanin ma yana da alaka a Abuja ba bare ta sa rai shine tafi ganin kamarsa da dirinsa irin Nabeel Hey Beautiful ya furta,Murmushi tayi tace ka tashi lfy,ta ya zaka kirani da Beautiful bayan har bed daya mun kwanta ko hannuna baka rike ba bare ka tabani kaga Kuwa ai ban cika me kyau ba,yace kyakyawa ce Mana Kawai Ni bana neman Mata shi yasa,tace to Zan tafi kudin nawa,Nan take ya bata bundle na 1k yace gashi bani number dinki Sanda nake bukatar ki Zan kiraki,sai yaushe Kuma zaki sake fita business din? Jannat ta kalli kudin da mamaki tace wow a hundred thousand Naira fa,wani ma baya biyansu dubu biyar amma you don't even touch me ka bani haka thank you dan Allah ka Zama Farkana, yace ba damuwa yaushe Zaki sake fita? tace sai Nan da 3days gobe Zan danyi wanki da gyare gyare jibi Zan karasa wata tilawa na kusa sauka ta haddar Al'qurani,Yace awesome sai karuwanci kuma hadda bata da amfani bakya amfani da iliminki,Jannat tace ba ruwanka dai da rayuwata a karuwa ka ganni ka barni a haka ta mike yace muje na saukeki. Mamaki yake yanda ya ganta ta iya zuba wanka ga class ba irin a gidan Affa ba,Yana driving tace kana min yanayi da wani a kaduna, yace ban hada alaka da Kaduna ba ni ban ma taba zuwa ba,okay ta furta tana nuna Masa har yazo Nyanya tace ajiyeni a Nan Zan karasa da kafa ba nisa,yace oh bakya so Naga gidanku? ba haka ne ba babu nisa daga nan don't worry Zan karasa,Okay ba damuwa ya furta tare da Shiga mota ita Kuma ta tsallaka titi tayi gaba ya juya ya nufi gida. Taxi ta sake Shiga ta karasa da ita gida ta iske Yan matan dukansu su shida sun saki kida suna taka rawa ga sigari ga syrup ga giya a table suna ta sha,Jannat ta shugo Suka saki ihu tana dariya,Zee tace yau da alama anyi disvirgin peace tace Naga alama Naga tana tafiya slowly,Jannat Murmushi tayi tare da shigewa dakinta,wanka tayi ta canja Kaya wata Riga da skert na Atamfa tasa me aiki ta kawo Mata lemo ta fito tana Sha tana kallon rawa da shaye shayen da suke yi. Dakinta ta koma ta kwanta saman katifarta tana tunanin ko dai Yana da wata manufa a kanta har zai bata dubu dari gaskiya zata dauki dubu ashirin ta mayar Masa da sauran kudinsa ta fara tsoron mutumin nan tana wannan tunanin azahar tayi ta mike tare da dauro Alwala ta gabatar da Sallah sannan ta fita Palo suna hira sai zancen Iskanci sukeyi ko wacce tana bada labarin irin namijin data kwana da shi daren jiya. Peace tace Kai na jiya young Me kudi na samu ya Iya Sex yanda ya bani service a bin ba a cewa komai,Zee tace tirr da nawa wani Alhaji ne kazami wlh sai toshe hanci na nakeyi warin Kashi yake gaba daya,Wai kunji Iskanci shi bama Ashira za a Sha Masa ba golaye za a Sha Kawai wlh Kamar nayi amai amma na samu kudi dubu talatin ya bani,peace tace ni Kuwa dubu goma,wata Ramcy tace uhm ni Kuwa 5k,daya Mery tace ita dubu hamsim ta samo ko,Jannat tace dubu ashirin Suka ce ai kin samu,ko wacce ta kawo dubu biyu za ajiye a accnt sabo da biyan light Bill,gas da ruwa,sannan a haka kafin shekara ta zagayo sun tara kudin hayar gida ko wacce ta Sha sha'ani da sauran kudinta. Fauzan Yana komawa gida Mama ta haushi da fada karka sake tafiya ka kwana a wani waje baka fada Mana mun San Ina kake ba,Haka Kawai irin wannan sakakin na iyaye ganin mazane yaransu sun girma sai su daina sa Ido a kansu a Haka yaro zai tare wajen abokai idan na banza ne daga can zai koyo shaye shayen,Neman Mata,luwadi,damfara etc bana son irin wannan karka sake ban hanaka zuwa gidan Kawu ka kwana ba amma ka sanar Mana Ni da mahaifinka,Kiyi hakuri Mama Inshaallah wani Aiki nakeyi ma aka bamu a can dole sai na dinga kwana Watarana a estate dinmu na Nysc sabo da group project ne,kasan haka ai sai ka fada Mana yanzu kaga idan zaka tafi ka sanar mu sani hankalinmu zai kwanta yace to ayi hakuri ya wuce bedroom dinsa washe gari aikinta tayi ta gyara room dinta tare da shirya komai neat tana cikin karatun Qur'an Wayarta karama tayi Kara ta duba taga number Fauzan ce daya bata number yace sunansa Abbakati dagawa tayi tare da yin sallama ya amsa tace Abbakati ya aiki, Alhmdllh me kike yi yanzu? Karatu nake yi alright gobe kina nan baza ki fita Business ba? Jannat tace ae dama Ina son ganinka akwai wata magana da zamuyi okay ba matsala gobe 5pm yayi maka? Ae yayi a Ina Zan dauke ki? No karka damu I will find my way to your House Zan gane, okay ya furta tare da datse Wayar. Jannat ta ajiye waya jiki a sanyaye tace tabbas mutumin nan da akwai wata a kasa ba banza yake damuna ba anya ba Dan mafiya bane kuwa bari dai Zan gani ai. Washe gari 5pm Jannat ta Sha wanka cikin kana Nan kayanta rigarta t-shirt baka me zanen fari sai Jean dinta tight sosai fari kal kal gashinta ta gyara tare da saka wata pcap fara gashinta har tsakiyar bayanta ka rantse sawa tayi,ta rataya jaka da takalminta duk bakake ta diga kyau,Me gadi ne ya rakata har Palo,tayi knocking ya taso ya bude sai da zuciyarsa ta buga sabo da yanda ta zuba kyau. Shima cikin kana Nan kayan yake ya sheka kyau Jannat sai kallonsa takeyi yau ma da face mask da glass gashi Yana canja murya yanda yake Mata magana daban,a palon ta zauna a saman 3seater ya zauna shima kusa da ita sannan ya tambaya Me Zaki sha? Tace ba komai kafin na fito naci abinci,no bazai yuwu ba in na bada abu ba a cewa a'a Yana Magana Yana binta da mayen kallo ta masa kyau har kunya ya bata sabo da kallo ta sadda kanta kasa tana wasa da yatsunta tace a kawo min ruwa Kawai,okay yace ya tashi ya kawo Mata ruwa tare da tsiyaya Mata a glass cup tana ta bin zobon yatsansa da kallo ta rasa Ina ta San zoben bayan tasha ruwan ta zaro kudin da ya bata a jaka tace Kudinka ne na dauki dubu ashirin na dawo maka da sauran gaskiya sunyi yawa ace ko Nono na baka taba ba Kuma ka bani har dubu dari amma idan kace na rike du yau sai na maka aikinka na sauran kudinka kaga Ni aikina na yiwa Namiji service,Fauzan ya kalleta yace bafa kiranki nayi inyi sex da ke ba bana bukata ni Kawai so nake in dan rage kadaici don't worry Zan sake biyanki yau ki maida wannan kudin na jiya ne,na yau daban ne and I will double you again. Jannat tace na gode yace so any news? Murmushi ta saki yace ya kuka ji da kartan maza kwana da su Kuna kokari fa Business dinku akwai wahala,Murmushi ta saki ta kalle shi kadan tace uhm gashi Nan dai wani kazami wani me tsafta,wani mummuna wani me kyau gashi Nan dai kawai,Yace na taba soyayya budurwar ta yaudareni ashe tana kula wani ban sani ba sai labarin aurenta naji,Jannat tace dama bata sonka amfani tayi da Kai taga kana da kyau da kudi,Ni Ina da kyau ne kin taba ganin fuskata gaba daya? Dariya tayi tace common kowa ya ganka yaga me kyau ko ta jikinka,Kika sani ko hakora ne dani shi yasa nake rufe bakina da hancina ko tsinin baki gareni,Jannat tana dariya tace matarka ta huta da Mika Fuska sosai idan za ta maka kiss to baki yana kusa dariya Suka dinga Yi Yana kallonta kamar me yace me yasa bakwa jin kunyar fadar magana? ka tambayi karuwa kunya a gidan karuwai fa nake ni. Mikewa tayi tace Zan wuce na gaji da surutu baki gama aikin ba ai,Zo muyi game wacce nifa whot Kawai na iya yace Ina da ita ya dakko sabuwa suka koma kasan center table suna facing juna. Masu sharhi Ina godiya AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 (JANNAT) Part 2. 76-80 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne OUM AMATULLAH MAMAN HANEEF CHANNEL Ga masu karanta Audio ku gargazawa DANDALIN HAUSA NOVELS Wanda Maman Haneef ke karantawa. Kadawa yayi tare da raba musu yace Nawa Nawa? bakwai bakwai zaka raba tunda ba mutane da yawa cewar ta,Haka ya raba Suka Fara sun wani bararraje a palon suna ta yi tana cinye shi,dariya ta dinga masa yace alright a sake yanzu zan rama ta karba ta kada ta raba Suka ci gaba da buga Whot tana ta dariya tana zuba Masa pick 2,pick 3 ya cika hannunsa da cards yace gaskiya ban yarda dake ba taya kike samun pick pick da yawa ni bani da su,gwalo ta Masa tare da matso da fuskarta saitin tasa tare da turo Masa dan Jan lips dinta tace ci gaba malam and last card ta nuna masa Kati daya tana dariya yace why are you always laughing? tana kebe baki tace nothing ci gaba Yana sawa ta jefa dayarta tace check up. Ban yarda ba gaskiya ko boyewa kike Yi tashi tsaye na gani,ta mike ya kalli surarta Malam ya hadiye mugun yawu yace zauna let's do it again ni Zan gama dake dama kyaleki nakeyi ae naji muje Suka sake wannan Karon shine zai Check up tana gani ta hade tata a cikin market cards din tace a sake tana Masa dariya tare da kwashe sauran gaba daya a hannu, yace no.. no ki dawo da shi kema kin San na cinyeki Kawai,ai ba ayi ba ta furta,Hannu ya Kai zai kwace cards din ta mike tsaye zata gudu,ya bita suna dariya ta zaga bayan kujera Suka fara tsere a palon har ya samu ya kamata ta fisge hannunta kafa yasa mata ta fadi a kasa Wannan ai mugunta ce ta furta tana kwance a kasa tasa hannaye tare da kwashe kafafunsa Saura kadan ya fada kanta dake Namiji ne ya ya dan kwanta a gefenta Yana maida numfashi ya kalli sama,gangarawa tayi zata haye Masa jiki yace ke ba kyau ni ba dan Iska ba ne,Jannat tace haba Abbakati sai kudi kake bani kyauta ai yau sai ka latsa kudinka maza ta kamo hannunsa yasa karfi ta kasa Jan hannayen iya karfinta,Kansa ta koma ta haye masa ciki yace ba kyau fa ba ruwana Allah Yana gani,Karuwa ka dauko fa tana dariya yace wait,Yi tayi Kamar zata cire rigarta da sauri ya rufe idonsa yace bazan gani ba wayyo Mama zan kalli abu,yace kiyi hakuri Ni rabona da Nono tun kafin Mama ta Yaye ni Matsoraci ta sauka ta dauki handbag dinta tace Zan wuce Ina da wajen zuwa miko kudi na tafi,Kallonta yayi yace Ina Zaki je ki kwana a nan tace no Ina da abinda zanyi,amma ba Business yau? tace na gama maka aikinka zuwa dare Zan iya yiwa wani nasa,yanzu unguwa zanje,yanzu Zan biyaki double ba sai kinje wajen wani ba please, ba ruwanka da rayuwata a titi ka Sanni,yanzu haka kike yawo kowa Yana kallon tsaraicinki? Fuska ta bata ba ruwanka Kuma ni na gaji da kudi da kake bani haka Kawai daga yau in ba Sex zaka Yi ba karka sake kirana,Ido ya lumshe yace gashi ya bata dubu dari again,sai da ta jujjuya kudin tace na gode Allah ya buda ta juya ta fita abinta yace ki tsaya na kaiki,tace bana bukata ta bar gidan. Me gadi Yana kallo yace tab wato Oga Mata yake bi ya dakko karuwa kullum tana nan idan na gaji gidansu zanje na Kai kararsa ai bazai yuwu ba ana Zama na Amana kana kallo mutum Yana aikata ba daidai ba amma kayi Shuru idan baza ka iya fada Masa gaskiya ba to ka sanarwa Wanda Suka Isa da shi a tsawatar Masa shine ka fita hakkin mutum,Nabeel Alwala ya daura ya shiga mota shima ya bar gidan. Jannat taxi ta shiga tare da dauko Wayarta ta Kira bugu daya aka daga tace Ina Zan ganka? Yace yanzu na bar Office amma kina Ina yanzu? Ina kusa da wuse market,yawwa jirani a nan kin kawo ne? ae ta furta yace ga driver Nan zai karba, Nawa Zaki bayar? tace dubu dari da hamsim,yace okay tsaya to Kawai na baki accnt dinsu sai ki biya a nan Kawai sai ki rike shedar biyan ta bank a hannunki na gode ta furta,minti Daya ya tura Mata ta shiga bank zata tura kudin sai ga Fauzan ya shigo da wasu kayan daban a jikinsa wannan Karon ba glass bare face mask a fuskarsa, ya tsaya a bayanta ma'ana yabi bayanta,ta juyo bata San da mutum a Bayan ta ba,ta bige shi,da sauri tace I'm sorry,Kamar an aiko Masa da mutuwa yaja tsaki tare da Mata kallon banza,Jannat tana kallonsa ta gane Fauzan ne. A ranta tana cewa to me ya kawo shi Abuja, gaskiya suna Kama da Abbakati na,amma wancan Yana da mutunci sannan ban San ainihin ya fuskarsa take ba, wannan Kuwa na sanshi masifaffe ne,zoben hannunsa ta kalla sai taga ba iri daya bane dana Abbakati wannan da babanci,Kunyarsa taji sosai da ya tsinceta da wannan shigar ta karuwai,da tasan zata ganshi da baza ta shigo wajen ba,tusarta ta tuna wata kunya ta lullubeta da sauri ta karbi tailer ta Kara gaba tana uban sauri sabo da kunya har tayi nisa ta dawo ta tsaya jiransa taga wasu kudi ya saka masu yawan gaske. Ya fito shima zai fita ta tare gabansa tace Dan darajar Allah karka cewa su Affa ka ganni a Nan garin,Ashe karuwa ce ma ya furta da raini,Ni dai Dan Allah karka fada musu ka ganni a Nan,Tsaki ya ja ya fice abinsa Yana juya Mata baya ya saki dariya ya Shiga wata Kalar motar daban ya bar layin,itama taxi ta Shiga ta koma gida. Tana komawa gida lokacin ma anyi Sallar Isha,da sauri taje tayi wanka tare da daura Alwala ta gabatar da Sallah sannan ta zuba tagumi a gefen bed dinta bata kauna Sam Affa ya nemeta, kiranta yayi ta daga da sauri ganin Abbakati ne yace kinje gida lfy? Lfy Alhmdllh me ki kike Yi yanzu? a kwance nake on my bed that's Good baza a dade ba Zan tafi aikin Hajji Daddy ne yace muje a gidanmu duk sunce su sai dai Umrah sun gaji da aikin Hajji,Ni Kuma nace Zan je,Murmushi tayi tace wow ayi Mana Addua,Murmushi ya saki yace ko zaki je mu tafi? Haba wasa kake yi dai,no da gaske nake ba karya ba,hmm ni dai ban yarda da zancenka ba. I'm serious Indai Zaki je ki shirya Zan biya Miki next week sai mu tafi a international kin San dai ba sex nake dake ba bare kice kudin haramun ne aikin Hajji bazai karbu ba,me yasa kake min abubuwa haka ne?ba komai iliminki yasa kike birgeni,karuwa irinki da ilimi haka, uhm tunaninka karuwa bata da ilimi? Akwai masu degree ma,okay Zaki je? gaskiya akwai kudin da nake so na hada zanyi wani abu da su da ace na gama hadawa sai na je amma Kawai kaje Zan Nemo kudin da business dinmu. Nawa ne kudin name your price, wata daya da Yan kwanaki ya kamata a cikin wata daya na hada dubu dari uku, idan na huta like one week sai na koma harka na ci gaba da neman kudin,Me kike yi da kudi ne haka?ba ruwanka, Alright tura min accnt na Miki transfer,tace Wai Dan Allah da gaske kake Yi? Yeah of course ki tura min ki gani amma Ina biyanki kudin ki shirya mu tafi Saudiyya Kinga kema sai kiyi Addua dama gaki sarkin addini duk da cewa baida amfani a wajenki,Yana da amfani ni Kuwa nasan amfaninsa anyway thanks alot Zan tura ma accnt yace Ina jira. Yana waya Mamansa ta fito tace hmm ko dai Suruka na samu ne Fauzan? Naji ana ta waya da alama da mace kake yi,Murmushi Kawai yayi yace Mama yau naje Office dina fa dan iskan yaron nan Hameed yaje Wai ya kwashi kudade Wai na kirashi Yana Fada min ya tafi kd shi wajen Affa,Rabu da shi Kaine kake barin kudi a office dinka kasan dai ka karya jalin company dinka wallahi Daddynku bazai doraka ba dama da ya ma ya yarda ka Fara wannan business din ka sani you have to be very careful yaushe zaka tafi aikin hajjin? Yace next week Inshaallah Nima zanje sai mu tafi tare,Ni fa ta Lagos Zan bi bata Nan ba,a dawo lfy cewar Mama taga baya son ya tafi da ita. Affa zaune yake cikin tsakiyar dare ya kasa bacci ya zuba tagumi Kawai tunani yake Ina zai ga Jannat,Mimi ce ta farka ta ganshi ya zuba tagumi tace so kake dai Ka jefawa kanka hawan jini akan yarinyar da ita ta manta ma da gidan nan,baza ki gane ba ana Miki Maganar yaran Gomnati,wannan fa yaran under Gomnati suke wa zai iya fada da gomnati,Mimi tace Allah zai fitar da kai abinda za ayi aje a duba ko wacce tasha aji ko za a samu motar data hau sai aji wanne gari ta tafi,Affa ya furta ehem now you're talking Allah ya kaimu ya kwanta da kyar ya iya runtsawa. Fadila tana gidan Nabeel an kawota hutu yau gidan su Nabeel zata kwana a can ma zata kwashe rabin hutun nata,tunda Nabeel ya ganta bayan ya dawo daga Office yace sis amma kwana daya Zaki mana ko? kuka ta saki tace ai dai Mimi tace a nan zanyi hutu na shine zaka koreni, Hamida tana dariya tace haka Kawai ka takurawa yarinya ka kyaleta muna tare ko? ga danta Aslam ma yau tare zasu kwanta,Fadila ta washe baki tace Allah Dana ne? Hamida tace ae Mana dan Lele ai naki ne ko baki sani ba? Yeeeee ta fara tsalle da ihu tace wallah yau sai na bashi nonona ya sha,su Hamida suka dinga dariya,tace sai da dare Zan bashi ko? Lele yace ke Wasa ake Miki fa,ya kalli Hamida so kike yaro ya tsotsi fata ta girma ta lalace ta saba ana Sha mata abu,Nabeel ya kalli Fadila yace Indai Kika bashi nono sai na zaneki a gidan nan baki da kunya ko,kaji yaya Lelen nan ni sai na bashi ba ku kuka ce dana bane,to ki bashi ki gani yanda zanyi dake Aslam ya karba yace ke Kuma fake bakya sonsa so kike ta jefar da shi wata Fadila ce zata iya raino,Fadila ta saki ihu ita sai an bata danta,haka ya bata yaron yace in dai Kika jefar da shi sai na zaneki zauna na dora Miki shi a cinyarki,tana dariya ta zaune tare da mike Yan kafafunta aka daura Mata shi a cinya ta jefar da Teddy dinta tare da rungume Aslam tace Aunty dora Masa teddy din yayi Wasa yaron da bai dade a duniya ba Wanda sai yanzu ma ta kusa yin arba'in. Bedroom Suka wuce Nabeel hankalinsa Yana Kan Aslam dinsa yace Sam ban yarda da Yaron nan ya zauna a hannun Fadila ba koma wajenta ku zauna idan na gama Zan fito na same ku,haka ta koma ta zauna a Palo suna ta surutu da Fadila. Fadila harda nutsuwa dan a yarda da ita tace dan Allah Aunty na bashi Nonon? Dariya ta bawa Pipi,ta sake cewa please pipin Lele,Hamida dariya ta kamata wato ta rike sunan,Lele fa zai siyo Miki chocolate da ice cream ki sha abinki karki San min, to na bashi? Hamida tace no ya hana,zan siya Miki mota fa idan na girma cewar Fadila,Hamida tace sai da dare yanzu ya koshi,Fadila ta girgiza Kai Wai taji haushi tace Lele sai ya Miki kishiya in ta haihu ta dinga bani danta ke Kuwa bazan dauki naki ba Kuma wallahi idan nayi nono na danta zan bawa ya Sha, ai zasu girma ne nima kuma danki ko kallon Nawa ba zaiyi ba na saka abina a bra, Hamida dariya ta kamata da mamaki Zama cikin gidan da Yan Mata suke yasa Fadila duk tasan wannan. Lele ya fito tayi Shuru tasan ubanta zai ci,Hamida tace kaga Yarinyar ta lalace,mikewa tayi zata jefar da dan yace kin gani ko da gudu ya cafe Aslam dinsa za a jefar da shi,bakin Hamida ta rufe da tafin hannunta dan mitsil, dan Allah karki fada Aunty alawa ta dakko tare da mikawa Hamida tace shanye du karki fada kinji,Hamida tana dariya har Lele ta karba tace to na fasa fada. Ai Mimi ta kusa dawo da ita gida tunda bata da kunya fitsara take koyowa a kanta,sabo da Zama da Yan Mata a gidan Kawu,in zasu magana basa korar Yara a gabansu sukeyi Kinga dole ta koyo fitsara,Fadila tayi Shuru Kamar ba ita ba. Zuwa dare tace yanzu ma a wajen Nabeel zata kwanta,Nabeel ya rasa ya zaiyi da ita ga yau Yana so ya kwashi harka jiya baiyi ba ya dawo a gajiye,Aslam ya karba yace daki daya zaku kwana da danki fa,ta fara murna tace na bashi nono idan yayi kuka? Yace ae ki bashi ya koshi karki sakko daga bed din,ko yayi kuka karki zo wajenmu ki Kira Nanny tace to a Kira Nanny Mana mu kwana tare,yace yawwa Kanwata muje wajen Nanny ya rakasu yace Fadila su kwanta da danta Aslam idan yayi ta bashi nono a kula sosai ya juya ya tafi,Fadila tana ta Murna Suka kwanta a bed daya harda rungume Aslam, tunda tayi bacci bata ko farka ba har Rana ta fito Aslam dinma tun dare yake tsala kuka sai da kyar aka lallashe ya koma bacci amma duk Fadila bata sani ba bare ta bashi Nonon Tunda ta tashi aka Mata wanka tare da shiryata ta nufi bedroom din su Hamida lokacin sun koma Karo na biyu suna ta hidima suna Jin Fadila tana ta Sallama tana kwankwasa kofa Shuru tace har yanzu bacci suke ta koma kasa taci abincinta. Nabeel da Hamida Suka fito sun Sha wanka fadila ta kallesu tace Yaya ko kaima Pipin nono take baka ne? Irin Aunty Ihsan Muka je gidanta zamu kwana na rantse mun ganta tana bawa mijinta nononta har tabawa yayi kuma bata San mun gani ba lallabawa Muka yi da su Yasmin kofar bedroom Muka leka mu Kuwa Muka gani na rantse,mijinta me katon kai. Nabeel kamota yayi ya dauki wayar Charger ya kaita bedroom tana ihu tana bashi hakuri ya dinga tsula Mata Wayar nan ba tausayi sai kuka take tana dan Allah Yaya kayi Hakuri bazan sake ba, shafda mata waya yake sai da Hamida tazo tace haba dan Allah yarinya ce me ta sani wannan,a Haka yaro yake tasowa a lalace ana ai yaro ne yaro ne kafin ayi aune yaro ya lalace wannan ai Iskanci ne su dinga leka mutum a daki wannan yaran na yanzu da kike ganinsu basu da kunya wayon tsiya ne da su. Hamida daukanta tayi Suka fita tana lallashinta tace aunty nifa nemanta muke Yi muka ji Shuru shine muka shiga dakin Kuma ba Kaya a jikinta Allah duwawun Aunty Ihsan Kamar na Tom,Kuma No....Nabeel ta gani tace nooooooooo karka oo ta wayance,Hamida tace kina sake fada wlh Zan kirashi ya zaneki, kyaleta ta dawo gaban Mimi da Zama zata ci ubanta Indai Mimi ce cewar Nabeel. Fauzan ne ya Kira Jannat a waya yace fito mu wuce Ina inda Kika ce ba a dade ba sai gata ta fito daga taxi taci wata gown Yar kanti doguwa har kasa amma me siririn hannu ta dan Dora siririn mayafi a kanta duk damatsanta a waje. Kallonta yayi Kamar maye da face mask da glass baki yace me yasa Kika fito haka? Ina ruwanka Wai mantawa kakeyi wace ni ne? bari na tuna maka prostitute ce kake tare da in Kuma kana so na sa hijab ka siyo su sannan nawa zaka biya? aikin kudi nake ni, ko Zaki iya bani tarihinki? Kai waye a wajena? to bazan fada ba ta furta tace kana tunanin Ina son abinda nake ne? hawaye ne ya zubo Mata tana gogewa,kallonta yayi a nutse ya furta I'm sorry. motar ya ja sanin wace ita ya sa Mata kida Waka tana ta shi tana sheshekar kuka da kyar dai ta danni zuciyarta tayi Shuru ta kalleshi da guntun hawayenta Murmushi ya sakar mata,Murmushin ta Masa itama tace thank you tana Jin wakar me shegen duka,sai yaji ta iya tana bi Kamar ita ta rera bai San dai dai wakar da bata sani ba both ta turanci data hausa har ta Yan kudu sabo da gidansu kullum kida ke tashi ba dare ba rana sai in ba kowa a gidan. Gani yayi har rawa take da Hannu da kanta,kin iya rawa ashe? tace ai sai dai in banga dama ba amma mu rawa ai ko mazari haka ya ganmu ya bari,Zaki min Ashe wata rana ko? Nawa zaka biya kasan mu komai kudi yace za a biya tace to. Passport ya mata ya hada ya Kai Embassy next week zasu karbi visa dinsu. Gidansa ya wuce da ita suna shiga ya dakko ball yace tazo suyi can garden suka koma suka Fara ya fita iyawa Kawai yanka yake zuba Mata suna ta dariya,Me gadi lallabowa yayi yana kallonsu a boye ya labe yana daukansu a waya yace na samu sheda Nan da sati biyu Inshaallah sai gidanku zanje sai na hada hujjoji na masu karfi,Ya kafa waya Yana ta daukansu,Fauzan ya sakawa Jannat ball ta Osinta ya juya zai tafi da ball din a kafarsa ta rike karamar t-shirt din dake jikinsa ta jawo shi Yana dariya yace sai na Kara Miki kwallo ta goma, kugunsa ta riko da hannayenta tana dariya Yana Jan jikinsa ta rungume kugunsa ta zuro hannayenta ta cikinsa sai faman dariya suke, juyowa yayi gaba daya har zai rungumeta sai ruwan sama ya tsuge dake garin akwai hadari,a Sai ya fasa tana kallonsa ta Mika hannunta da Niyyar cire Masa face mask ya goce ya matsa baya yace karki cire min Corona virus bana so a samu matsala na dauka,da karfi suke magana sabo da karar ruwa ,ruwa Yana dukansu tace ai ni ban taba Yi ba,ae sabo da iska Kar ta dakko ta gari na shaka,Dariya tayi tare da bugar kafadarsa da tata Juyawa yayi suna kallon juna Karshe tace mura fa sanyi,Matsawa yayi Suka koma Palo suna hutawa yace bari na Mana order abinci Kamar kasan yunwa nake ji,Waya ya Kira tare da yin order ba a dauki lokaci ba ruwan Yana zagaitawa me gadi ya shigo yace oga ga sako an kawo yace ajiye a Nan,Jannat tace Wai ya sunanka ne? Yace Murtala,okay ta furta me gadi ya fita Yana Jin haushin Jannat Yana kunkuni shi kadai zata lalata min oga sai nasa an raba ku algunguma karuwa,in banda ma oga ya lalace sai ya fara kula karuwa duk matan Nan na duniya ko da yake tana da kyau. Sai da suka ci abinci yaje Sallar magriba a gidan tayi Sallar Isha ya dawo ya maidata gida amma bata bari yasan gidansu ba a bayan layin ya sauketa kamar yanda suka saba. Wasa Wasa kullum Fauzan sai sun hadu da Jannat a gidansa suyi kallo tare suyi game etc har sati ya cika ya karbo musu Visa,Yau da murna ta shiga gidansu ta iske matan duk suna Palo suna Shan kida, tace farko dai ku Karo min kida suka ware kida tun basu ji mene ba Suka mike Suka Fara cashewa Banda Jannat passport ta dakko tare da bude musu visa dinta tace gobe zamu tafi Makkah aikin Hajji da Guy na,Ihu Suka saki ko wacce ta karba tana kallo tabbas ba karya,tace Kuma ya biya wasu kudin da nake bukata na next month har muje mu dawo bana bukatar kudi. Ramcy ce itama ta zaro nata passport din tace ga nawa Ni Kuma Dubai zamu tafi hutu da Alhajina yace muna dawowa zai canja Mana katon gida sannan zai siya min mota,Suka Fara murna dama su sun Saba zuwa Dubai Alhazawa suna tafiya da su,wasu su Zee ma Makkah duk sunje da kudin Haram,Jannat ce ba inda ta taba zuwa. Zee tace Allah ya shirye mu wlh Makkah dinmu ba lada sai tarin zunubi Mace baki sana'a baki da hanyar samu,iyayenki suna gida ba ko kwandala amma sai a ganta a Dubai gobe Makkah wacce ba lada sai dai ki dawo da zunubi,ko a ganta da jibgegiyar mota kullum tana yawo kasa kasa abin haushin ma Makkah kasa me tsarki da kudin haramun an tafi da dadiro ana Iskanci a can. Jannat kije kinji amma ki taimaka karki Yi sex da shi kiyi addininki cewar Ramcy,Jannat kallonsu Kawai take in ta fada musu basu taba sex ba baza su yarda ba shi yasa tace to Kawai. Har ga Allah Fauzan zai tafi da itane Kawai dan Kar ya tafi bai sani ba wasu su dauketa suyi ta sex da ita suna bata kudi tunda kudin take nema shi yasa Kawai yace zai tafi da ita badan wata manufa ba. Washe da wuri ta wuce gidansa tana zuwa ta iske haraminta Abaya baka ce marar ado ko daya yace wannan kala biyun sune haraminki daya Umrah Daya aikin hajji tace Ni da ka sani Riga da wando ka dinka min da hijab sai sunfi min dadi da ka siya min farin yard plane an dinka min yanda Yan Nigeria sukeyi amma tunda an siyi wannan it's okay,anjima zamu tafi ba time ne,hijabai masu Hannu masu kyau kala Uku sai wasu Abaya masu kyau kala Uku yace in munje can a siyi wasu tace to,a Nan ta shirya yar akwatinta komai cif tayi wanka ta shirya cikin Abaya arsh me tsada da kyau ta fito kamar balarabiya, jallabiya yasa Fara da farin glass sai face mask fari,kallonsa ta dinga Yi yace lafiya? tace wlh Kamar wani Nabeel kai kana Kama da Nabeel,Dariya yayi a ransa yace muje Suka fito da akwatina,abokinsa Hammad shine yazo ya kaisu airport,shi tunanin Hammad ma Yar uwarsa ce sabo da yanda suke da Yan Uwa ratatata. Kamar Yanda yace jirgin Lagos ya shiga,Yau shine karon farko da Jannat zata Shiga jirgi,Allah sarki Hamida ita har yanzu ba a sauke farali ba ciki da haihuwa ya ja Mata. Jannat tana gefen Fauzan sai washe baki take an hau jirgi,tana jikin window ta zuba Ido tana kallo ko kula Fauzan bata yi har Suka Isa Lagos sannan Suka Yi transit aka musu screening suka shiga jirgin Jiddah suka sake keta hazo,Basu dade ba aka kawo musu abinci Suka ci 4hrs Suka Isa Jiddah,a Nan Suka yi wankan harami Suka dauki niyya shi da hirami fari daya ya yafa,Ita Kuma tasa Abaya marar ado ko digo,ta fito zasu Shiga mota dama tana period,kallonsa tayi zasu shiga mota tace Abbakati period nake fa ba pad yace tab kin shiga Uku wlh kafin kiyi Umrah sai kin samu tsarki Kuma ba cire harami haka Zaki ta wanka kina maida abinki,kinji dai me nace Banda turare karki bari ki karce fatarki jini ya fita ko garin brush kin karanta hukunce a littafin dana baki ,tace Allah yasa kwana biyu nake yi nake Yi yace kin shiga Uku bake ba ganin kaaba sai anyi sati sai dai mu dinga zuwa wajen darul tauheed kina Shan ice cream Dariya tayi. Siyo Mata pad yayi ta koma toilet ta shirya kanta tsaf sannan ta Shiga mota suka tafi Garin Makkah,Suna zuwa hotel yayi ta dubawa da kyar ya samu Wanda yake kusa da harami,ya Kama Mata daki shima nasa daban,yace tazo su tafi ta rakashi Umrah amma ita a waje zata jira shi,Haka Suka fito ko mota basu samu ba sabo da yawan mutane a kafa Suka taka har can. Wajen wani katon agogo yace zauna a Nan idan na fito zanzo mu wuce,Jannat ta zauna ga Mata Nan Yan Pakistan da larabawa Suka ta Yi Mata magana harda yin kawa Yar Pakistan tace tazo suje taga masaukinta Jannat ta bi kawa,tafiya me uban nisa Suka Sha,taga daki Daya a hotel din nasu gado sun Kai biyar a ciki,cikin harshen turanci Jannat ta tambayeta me yasa a hotel guda da wannan beds Haka,Tace ai su haka sukeyi ta nuna Mata gadajen tace Daya na surukarta da danta a Nan suke bacci,Daya nata da mijinta,Daya na Kanin mijinta da matarsa Daya na yarta da mijinta Daya Kuma Babar mijinta da baban mijinta,Jannat tace uhm sai da Suka Sha Hira sannan ta rakata inda ta dakkota kasancewar Jannat bata san gari ba sannan sukayi sallama. Bata dade ba Fauzan ya gama Umrah ya fito Mamansa ma tana garin amma basu hadu ba. Jannat ya gani tana jiransa tana ganinsa ta mike tace ice ko ka mana Addua yace na Miki Allah yasa ki daina sana'arki Dariya tayi Suka jera suna tafiya,Wurin aski ta raka shi aka rage Masa sumarsa tare da sajensa da gemunsa aka gyara su sosai sannan Suka wuce gida. Suna tafiya suna hira cikin nishadi Kawai ya hango Mamansa Ashe tazo tuni ita sai yanzu zata sauke Umrah,ai da sauri yace da Jannat mu tsallaka titi mu bi ta saman gada canja hanya yayi Jannat bata San Mene dalili ba ita dai shine jagoranta. Affa ne ya Kira Lele lokacin Hamida tana kwance a jikinsa Yana shafa Gorar Madara Yana Wasa dasu ya daga,Affa ko gaisawa basu yi ba yace ka tayani Neman Jannat please Zan fara zuwa tasha ma gobe naji,Nabeel a ransa yace bazan nemo jaraba a aura min ba bazai yuwu ba,ai Kawai sai yace Affa kayi zamanka mene amfanin haihuwata bari Ni Zan fita dubata da kaina,bari na tafi tashar ma dama Ina wajen aiki Bari na dauki hanya ko wacce tasha zanyi kwakwaran bincike idan ta Kama ma wani garin ne zanje sai a dubata kayi zamanka Inshaallah zaka ji sakamako me kyau,Affa yace Allah ya maka Albarka maza kaje kasan dole baza a fadawa hukuma ba sai asirina ya tonu,Nabeel yace ba abinda zai faru Inshaallah. Suna gama Wayar ya koma saman Hamida ya gyara musu bargo ya fara Hidima yace haka Kawai a dawo da ita a aura min ita,Hamida tace Ina Jin dadin Najancy ta ni kadai haka kawai aje a dangwalawa wata a dausayinta a dawo Nima ayi ciki da shi Allah ya tsare ni Fauzan Wanka yayi ya shirya cikin kana Nan Kaya sannan ya fito ya leka room dinta yace ta fito suje suci abinci haka Suka je Suka ci abinda suke so yace ba time idan Zaki siyayya mu Fara jibi in kinyi Umrah tace to. Bayan kwana biyu kullum tare suke zuwa masallaci ta jira shi a waje har ta Zama Yar gari ma da kanta take siyan kayan ciye ciye da duk abinda ya birgeta har itama ta samu tsarki ta tafi sauke Umrah ,ganin ka'aba ta fashe da kuka tana Abbakati kaini na shafa ka'aba mutane sunyi yawa, ya ja hannunta ya kutsa da ita ya kaita har jikin ka'aba ta rungumeta tana cewa Abbakati Kamshi wow mutane sunyi yawa akayi tafiyar ruwa da Jannat da kyar ta samu tasa karfi ta dafe jikin ka'aba ta fara adduoi tana fadar bukatunta,tuni an rabata da Fauzan mutane sunyi yawa sai baya ya koma ko hangota bayayi,Haka tayi dawafinta ta gama sannan ta fito kaf ta gama Umrah dinta tana tambayar wurare ana nuna Mata tunda ga mutane Nan suna Yi,tana gamawa ta lalubo Fauzan shima ita yake Nema sai ganinta yayi tazo inda yake,yace Yar gari an waye tace Saura yanke gashi ya rakata toilet din Mata inda suke yanke gashi yace ki bawa wata ta yanke miki tace to. Ai Jannat gaba dayan Nan ta auna aka yanke mata sannan suka tafi,a ranar ta fara fita siyayya har tayi kawaye hausawa kudi yake bata suje siyayya tayi dai dai gwargwado shima Haka,kwanansu goma Sha biyar a Makkah daga Nan Madina suka wuce Nan kwana takwas sukayi sannan suka dawo gida Nigeria,ko Daya Fauzan Mamansa Bata ganshi ba sau daya yaje hotel dinta Suka gaisa yaki fada Mata masaukinsa. Tunda Jannat ta dawo take fama da tunanin Abbakati,kullum cikin tunaninsa take,me gadi jira yake a nutsu yaje har gida ya fadawa Maman Fauzan komai yanda Fauzan yake bin Mata wata karuwa ta rike shi har Makkah da ita ya tafi Bayan Sati taya tunda Suka dawo Jannat bata ji Abbakati ya Kirata ba gashi bata da burin daya wuce taji muryarsa ko ta ganshi duk ta kasa sukuni. Da kanta ta gaji ta kirashi,ya daga da fara'a yace na zaci baza ki neme Ni ba, Murmushi tayi tace ya gajiya ya su Mama?lfy suke yaushe Zaki fita business? tunda na dawo ban fita ba ai zamu hadu ne? yace uhm sai jibi Inshaallah tace yayi nisa,kin matsu ki ganni?tace ae so nake mu hadu na baka tarihina na yarda da Kai na aminta da Kai bani da kowa a duniya sama da Kai,Ina ji Zan iya sharing rayuwata da kai,yayi murna sosai yace thanks gobe mu hadu a gidana tace karfe Nawa? Ai tare zamu yini 11am kizo zuwa dare mu rabu in ta Kama sai mu kwana gida daya ma karki damu Zan biyaki okay ta furta Suka gama waya.. Ranar yana Office Murtala me gadi ya dauki wayarsa ya tafi gidan su Fauzan zai fadawa Iyayensa su dauki mataki Masu sharhi godiya nake Aci gaba Dan Allah. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 Part 2 81-85 Official By AsmaBaffa WARE BAIKO Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Ga masu karanta Audio ku garzaya DANDALIN HAUSA NOVELS Wanda Maman Haneef ke karantawa. Page naku ne Gimbiya Diyar Katibiti Maman Baby Hajjora Investment Fauxeey Mmn Ihsan Mrs Usman Xerkiyyatou Rukey Muaz Oum Affan Kankara Ummu Faruq Mrs Lawan Bara'atu Ahmad Buhari Fatima Yahaya Ali Mmn Muh Mama ce ta fito cikin shiga ta Alfarma ta zauna a kujera tare da harde kafafu,Murtala ya kwashi gaisuwa sannan tace ya akayi ne Murtala ko gidan Fauzan ne ya samu matsala meke faruwa? Murtala yace matsala ma Kuwa Babba Hajiya shine na taso kafa da kafa nazo na sanar muku domin ku dauki mataki,bata kamata ace Muna Zama na Amana ba Kuma naga barna ta shigo na bari ba,tunda Kinga ni bazan iya yiwa Oga magana akan abinda yake aikatawa ba dai dai ba naga ya kamata nazo na fadawa inda aka Isa da shi inda za a tsawatar. Hajiya wata karuwace ta rike Fauzan ta gama shake Masa makoshi wallahi kusancinsu yayi yawa duk inda mace da Namiji zasu kebe to shedan shine na ukunsu amma inda kisan arna haka suke rayuwa kwana sukeyi tare su yini tare,ta maida gidan nan gidanta kudi yake kashe Mata na fitar hankali mu da muke mabukata ko dubu goma ya Kara min akan albashina ai na rage matsalata,Amma kawai ya Zama Atm,to in karkare miki aikin Hajji bana da ita yaje wallahi,suyi Wasa tare harfa kwallon kafa suke bugawa suyi wasan buya buya,da langa harda goyo goyo,ball Kuwa yanda suke yinta inda kisan Messi da Ronaldo gaskiya Fauzan ya bata wayonshi,Mene hujjarka? Mama ta tambaya Wayarsa ya zaro wata vivo ya kunnawa Hajiya ball dinsu ta gani tabbas ga mace ta rike Masa kugu suna kokawa,ya danno Mata inda take bedroom ya kawo Mata abinci ta matse cikin kana nan Kaya,har whot da suke bugawa da inda ta zauna a Kansa, sai tafiya Makkah dinsu inda Suka fito da akwatina Hammad ya dauke su a mota,har hawansu jirgin lagos ko da ya yaje ya dakko oho yace har airport na bisu a taxi na tabbatar Mama tana gama kallo tace na gode Murtala irinku ake so idan kunga barna zata faru kuyi Hani da ita,ai da ace Ina da dama har Makkah Zan bisu na dakko miki to ba Hali,Mama ranta a mugun bace tace hakan ma yayi,Yana zaune a gabanta ta Kira Fauzan tace zo gida yanzu Ina nemanka. Fauzan Jin muryar Mama cikin Fushi sai da yaji tsoro,yace gani nan,motarsa ya shiga zuwa gida,Yana shigowa Palo ya iske Daddynsa da Kawu Ubaidu Mama har ta kirasu ta nuna musu komai,da ace Affa Yana kusa harda shi za a Kira to yayi nisa shi amma an fada Masa a waya,Murtala Yana zaune tunda Fauzan ya ganshi yasan tabbas ya tona Masa asiri a ransa yace zaka ci ubanka Murtala, Murtala Kuwa sai da yaji tsoron Fauzan matuka tunda yayi kasa da Kansa bai dago ba,Fauzan ya zauna a kasa yace Daddy gani,Kawu Ina kwana Yana gidan ubanka dan Iska marar mutunci tarbiyyar da Muka maka kenan ashe Mata kake bi,karuwai to munga komai, me nayi? Karka raina Mana hankali Murtala mika Masa waya ya gani da Kansa,Murtala jiki na rawa ya dannowa Fauzan komai da ya faru sai ga Fauzan Yana kallo ya manta ma fada ake Masa Yana wani Murmushi ya kafe waya da Ido lokacin suna ball ruwa ya zuge yace wow a fili,Kai Murtala ka dauka ashe amma ai da Sai ka tura min irin wannan amazing tarihi da Muka kafa,wayarsa ya zaro me tsada ya tura duka videos din tare da goge na Murtala duka ya Mika Masa Wayar sannan ya juyo. Yana juyowa Daddy ya kashe shi da mari ya Sosa wajen yace to ai Ina jinku ayi min fadan cewar Fauzan, Mama harda kuka yau na shiga Uku karuwa ta Masa asiri wacce tsinanniyace wannan Zan maka baki wlh idan ka sake Fauzan,Dr Ubaidu yace ba Maganar baki a nan Kai Fauzan sonta kake ko me? a'a Ni ba sonta nake ba,to ubanka me kakeyi da ita? taimakonta zanyi tana da ilimi bai kamata ace tana wannan harkar da maza ba shi yasa nace gwara tayi dani,baki Suka bude gaba dayansu,Daddy yace da gaske kaje Makkah da ita? Sosai ma ai shi yasa naki bari mu tafi da Mama,Mama ta sake fashewa da kuka shi dariya ma suke bashi,yace to kuyi Hakuri na daina baza a sake ba,idan sonta kake ka kawota a daura muku aure cewar Yaya Ubaidu Mama tace wlh bazan yarda Dana ya auro Mana karuwa ba,bazan yarda ba sai dai duk abinda zaiyi yayi,Ni ba Aurenta zanyi ba ma Fauzan yace. Daddy yace Kar na sake ganinka da ita, Zan saka CID Matukar Suka ce sun ganka da ita wlh sai na tsine maka,Mama tace Nima haka,yace akan an ganni da ita zaku tsine min? ai dai baku tsine min yanzu ba? Kawu yace ana sake ganinta da Kai akace yace to baza ma a ganni ba Inshaallah kuyi Hakuri na daina. Affa ne ya Kira waya yace kuci ubansa ku mammareshi yaro marar tarbiyya a haka sumi sumi kullum yace shi me aji ne gashi ya Kare a gindin karuwa,Fauzan yayi dariya Kawai a ransa ,har Suka Masa Nasiha sosai karshe suka ce ya tashi ya tafi... Yana mikewa ya hankade Murtala tare da take Masa Hannu ya murje,Murtala ihu ya saki Mama tace Yi hakuri harda bashi dubu goma Murtala ana ta murna. Murtala gida ya koma tare da fesa wanka ya Sha shaddarsa wata red ya fesa turarensa ya dora hularsa ya fice ya Shiga taxi sai gashi a kofar gidan su Jannat,gidan ya kwankwansa me aiki ta fito ta bude Masa gate yace dan Allah Jannat zakiwa magana kice me gadin saurayinta ne Abbakati sabo da yaji Abba take ce Masa tunaninsa duk soyayyace tasa ya koma Abbanta, kice shine ya aiko ni. Me aiki tana zuwa ta sanar wa Jannat Sako,Jannat mamaki ya kamata taya yasan gidansu amma tace kice ya shigo. Me gadi ya shigo tun daga waje yaji kida kamar zai fasa gidan har Palo aka shigo da shi yaga Yan Mata zagada zagada gaba daya jikinsu a waje kusan tumbur,Jannant ce ta fito sanye da Hijab da fara'a Suka gaisa. Ta kalli su Zee tace me gadin Guy dina ne,Suka gaisa da shi yace Maganar ta sirri ce, Jannat tace shugo to ta kaishi dakinta ya zauna a saman wata kujera ta kawo Masa lemo da ruwa,Yana ta kallonta yace ashe kikan sa hijab,ae mana me ya aiko ka Ina jinka? Yace magana ta Allah Ni na Aiko kaina gaskiya nazo na fada Miki,Kinga saurayinki to Maganar gaskiya Mata yake kawowa iri iri dabam dabam ba ke kadai bace,yanda kike kyakyawa bai kamata ki biye Masa ba,Jannat tace to Ni mene hadina da matansa ni baka San karuwa bace ni ko ance maka shi kadai nake kulawa. Murtala ya washe baki yace Alhmdllh shi yasa nayi tattaki nima Maganar gaskiya tunda na ganki nake sha'awarki, gaki da duwawu masu birgewa musamman idan na kalli kirjinki nan take sai inji na kawo,babu Wanda zai ganki baiji wani abu ba sai in baida lafiya,da kaina na kwakwulo gidan Nan ba abinda bazan kashe Miki ba,ke Ni nayi Miki alkawarin salary na duk wata,Haba kalli Yar katifarki me kyau sai naji Inama yanzu Muna kwance akai tare da kinji Dadi, gashi Allah ya hore min katuwar mazakuta babu inda baza ta Kai Miki ba,kudi ya zaro dubu talatin ya ajiye a Kan katifar Jannat da ta sume a zaune yace ga wannan burina naji Ni a jikinki nasan zaki ruwa Yana wani zaro Mata harshe Kamar Kare. Jannat ta kwashe kudin ta zuge Jakarta ta zuba ta karaso daf da shi Yana yawwa Yi min kiss,saukar Mari yaji ta ko Ina tass tass,takalminta me tsini ta Zara ta kwada masa a goshinsa wajen ya fashe Yana jini,ya fito da gudu su peace dama sunyi ready sun San ba lafiya ai basu ji labari ba Suka rike shi Suka rufar Masa da duka Kamar Allah ya Aiko su jibgarsa suke Kawai tare da yayyaga Masa riga da wando zasu Masa tsirara Allah yasa ya fita a dari daga shi sai gajeren wando Yana dawowa gida ya iske Fauzan ransa a bace ya kalle shi yace kwashe naka ya naka ka bar min gida na koreka daga aiki dama da irinku ake hada baki a kashe me gida to bar min gida ko da kudin ubanka a ciki,kuma wallahi ka koma gidanmu kace na koreka sai nasa an batar da Kai,Murtala ya fashe da kuka ya Fadi a kasa Yana bada hakuri Wai Sharrin shedan ne yace kwashe kayanka kafin na irga Uku,da gudu ya fada dakin ya tattara kayansa gashi baida sisi ya fito zai tafi Fauzan ya Mika Masa dubu ashirin yace to Kara gaba na sallameka babu Kai ba ni,ya tafi Yana dana sani. Jannat ya Kira ta daga yace kina Ina gashi Ina shiryawa Zan fita,Ina Zaki kuma? Unguwa ki jirani a gidan naku bani address ko har yau baki yarda dani ba? Jannat bata so ya kalli matan Nan tsaraici a waje amma ya zata Yi haka ta bashi Address, Fitowa tayi ta iske su suna ta zuba shaye shaye tace saurayina zaizo fa kusa hijab dariya ta basu peace tace ko sonsa kike? Ina ruwanki,to ba inda zamu wlh Kuma baza mu canja Shiga ba in zaizo yazo, yanzu haka ma wani gara ne duk Yan barikin ba mun sansu ba,Bata rai Jannat tayi tana kallonsu harda tashi su Fara rawar fitsara wiwi duk gasu nan a table,Zee ta Mike tana rawa tace yazo wallahi yaga Kaya idan Kuma ya canja ki shike Nan, Yar Kauye ance kizo aje gidan wani malami dake yanda Kika hadu da me kudi haka ki daki Kansa kinki,Allah ya rabani da shirka akan Namiji ban zuwa gaban malam ko ma ince boka,bedroom ta koma ta sake gyara shi Yana kamshi ta Kara gyara kwalliyarta sai gashi yace yazo,da kanta ta saka katon Hijab dinta me Hannu saman Riga da guntun wandonta iya karsa rabin cinya. Yana mota Yana kallon gate dinsu yaga ta fito tana Murmushi tun daga waje yake jiyo kida ta gidan nasu,shigo tace tare da bude masa mota,ya fito tace ko zaka shiga da ita ciki? Yace no sauri nakeyi, Yana Kare Mata kallo yace yau a gari kece da Hijab? Dariya tayi tace hmm dama Ina sawa idan Aljanunsa sun zo Wai baza ka cire face mask ba da glass kullum a haka nake ganinka suna magana tana gaba har Suka Shiga Palo yasha kallon badala a ransa yace dole taki yarda na gani,Ramcy ta daga kwalabar giya ta Mike tana rawa,Zee wiwi take bulbulawa,Peace Kuwa codeine take bulbula,Mery da Chima Kuwa daga su sai bra da pant sun wani baje dukkansu kyawawa Yan gayu sai dai kana gani kaga Yan duniya ne,Jannat ce kadai baza ka taba cewa ta hada harka da su ba sai zee itama da dama dama. Sai binsa suke da mayen kallo ko wacce ta Miko Masa Hannu Wai su gaisa Jannat ta bige hannayensu tana harararsu tace muje ciki,Jannat Service him well well cewar Peace,shi dai Fauzan ya shige ciki Jannat ta fita tare da kawo Masa lemo da ruwa itama sai data tsaya ta dan cashe na murnar ganinsa sannan ta dakko ta kawo masa, yace labarin naki fa? Shuru tayi tace na fasa sai Watarana,ki kwaso kayanki ki koma gidana da Zama Mana wannan gidan bai da amfanin Zama a cikinsa,na gode ta furta yace to muje na kaiki inda Zaki je,Sha lemon first ta tsiyaya Masa a glass cup ya Sha yace let's go, akwatunanta ta shiga budewa yaga Kaya na alfarma ga kanana da gani duk Yan kasar waje ne,wando ta zabo,yace maida su baki da aiki sai kananan kaya,Fuska ta kwabe tace dan Allah na sa? no ya furta,na saka din dai ko? ta furta tana kallonsa,Dariya ma ta bashi. Yace Atamfa zaki saka,skert din Atamfa ta jawo ta shiga toilet ta saka a saman wandonta ba tare da ta cire hijab ba ta fito baiga tsaraicinta ba ya kalleta yace haka kuke adon tsoka a gidan naku Ashe? ai duk ganin da kake min cikin shigar mutunci kake ganina,a musulmata nake fitowa Hijab dinta ta gyara ta riko hannunsa tare da cewa muje,hannunsa ta saki da sauri tace hannunka ya min Kama da wani,Nan take yaji haushi yace wani dan iskan ne? Wani a Kd ana ce Masa Fauzan yana da class sosai kaga yanga da gadara shegen akwai iyayi,ni a lokacin dana zauna a gidansu ina cikin damuwa bana fara'a bana magana Kawai kudi nake hangowa,idan na hango alhazawan Abuja sai naji na tsani Yan gidan,duk tunaninsu banda mutunci, amma magana ta Allah ba a taba namijin da yake birgeni ba irinsa komai nasa me kyau da mijin Aunty Hamida wow,Fauzan sunansa idan kaga lips dinsa pink gashi fari ne irinka,har na dawo garin nan da haushin lips dinsa na dawo sabo da ban musu mmmuahhh tayiwa iska wani kiss da bakinta ita a dole Wai karuwa,Fauzan yaji Kamar ya taka rawa. Tace Abba karka ji haushi darling kana min yanayi da shi sosai da sosai fuskarka ce Kawai da ban sani ba,Kai Nifa dalilin birgeni da yake naga Kuna yanayi shi yasa nake ta kulaka amma yanzu ka fishi a wajena da za a kawo shi a hadaku Kai Zan zaba sabo da kafi shi mutunci shi baida mutunci sai masifar jaraba kunyarsa nake ji sabo da na tafka abin kunya a gabansa ban San Yana Nan ba,ban taba Jin kunya a duniya ba irin ta ranar ba daga ranar har abada bazan sake maimaita kurena ba. Key din ta karba tace kawo nayi driving na iya,yace a Ina Kika iya ko Fauzan ne ya koya miki,Ramcy ce ta koya min lokacin tana da mota kafin ta siyar motarta muke yawo,Alright gaba ya Shiga ta Shiga mazaunin driver ta fara driving a nutse suna zuwa wata Danger Daddyn Fauzan driver Yana jansa Yana bayan mota,Kamar Motar Fauzan ya gani ya sake kallo amma shi Yana daya hannun titin kuma mace ya gani na tuka motar da Namiji a gefenta sai dai ya Sha face mask da glass brown ya kasa tantancewa haka Jannat taja mota ta Kara gaba. Fauzan yace me mota ya ba a kwanto ba a layiii a saman kwalta da ni idan ba layii a bani kudina,Dariya tayi ta fara yanka tsakiyar motoci ko ka kauce ko ta buga ma wani tukin ganganci takeyi tana ta over taking,Fauzan ya tafa Mata yace to ya Isa karki aika mu lahira,tana dariya tace wlh da ace fili ne ba titi ba sai na zana maka kwabo ka gani to sai Watarana ya furta Yana kallonta. Lele ne ya kawowa Hamida Admission tun ranar da ya kawo Yana nuna Mata ta fashe da kuka ita baza tayi ba,tagumi Lele yayi ya saka Pipi a gaba Yana kallon ikon Allah,Tace ba na iya karatun da rubutu ba na iya turancina daidai gwargwado me Kuma zanyi,lallabata yayi yace yanzu rayuwa fa sai da ilimi,Ni ya isheni ga Islamiyya ina ta zuwa ya isheni da me zanji,kullum kazo kayi ta hidima duk ka haka min rami a jikina,ga rainon yaro ga girki da aikin gida sannan ka kace karatu again da me zanji yanzu anjima nayi zaka Zo Hidima Ni gaskiya bana so bazanyi ba. Yanzu Pipina kina ganin wasu da kudi suke Neman Admission Basu samu ba,wani Wanda zai dauki nauyinsa ma yayi ko Secondary yake Nema ya rasa,wani ma Yar Diploma yake Nema ko ita yayi a kasar Nan amma ba hali,ke gashi Private na Nemo Miki me tsada sabo da kiyi karatu a saukake amma baki gode min ba,Yan aiki gasu Nan,in banda nono me kike bawa Aslam? Yaushe Zaki girma yaushe Zaki Fara son karatu Pipina. Rungumeta yayi yace haba Pipina gata nake Miki ga wasu can matan mazajensu suna da kudin biya musu karatu amma sunki yarda su biya musu,Yanzu ki yarda zakiyi Ni kuma na biya Miki Makkah,sai lokacin ta dago da kanta Fuska duk hawaye ta furta da gaske? yace yes tare zamu tafi har wata kasar ma,Kuma Muna dawowa Zan siya Miki mota,gashinta ta Sosa ta fara Murmushi tace zanyi to har masters ma in kana so, Lele yasan ta Kan pipinsa,yace but Indai na cika Miki alkawari Kika ce zaki Wasa da karatu to karshe na fatattakeki gidanku. Dariya tayi tace wlh baka Isa ba,ai ko Sakina kayi ba fata nake ba babu inda zanje Zama daram, ai na sanka sai Kawai naje garden inda kake hutawa nayi irin daurin zanin tsofaffin Kauye na daura shi kasan gorar Madara sai nazo na Fara shanya Ina girgiza su kafin kifta Ido kace na dawo dake,dariya yake sosai yace ko kallonsa bazan Yi ba yarinya,sai dai in ba na Pipi bane,ai kishiya Zan Miki ki daina min kuri, duk unguwar Kuwa da sai sun San zaka yiwa Pipi kishiya,Sanda Affa ya kawo Jannat in banda kuka me Kika iya?kukan ma Ni kadai kike wa,baki ta murguda masa,yace Zaki yaye Aslam ne zanga yanda nono zai dawo dan tamilo daga lokacin na daina tabawa shike nan taki ta kusa karewa shike Nan. Hamida tsayawa tayi cak ta Lula tunani tabbas duk wacce tayi yaye sai nononta ya dawo sai fata, Tace baza ta sabu ba mikewa tayi tace wayyo gora zata koma faifai, Wayarta ta dakko,Nabeel ya jawo hannunta Yana dariya yace Wasa nake Ina so haka,Hamida tace bazai yuwu ba Muna da hulba da kayan Hadi Allah ya Mana sakaki ne irin namu Allah maka Albarka daka tuna min ta fisge da hannunta tayi dakinta. Affa ne ya Kira Nabeel sai yau ma ya tuna da Neman Jannat da sauri yace Affa yanzu nake Shirin kiranka ae to ya Maganar take? Yace ai ba tashar da banje ba Allah yasa Ina zuwa tashar da ake zuwa Lagos na Basu bayaninta sosai ai shugaban tashar ma har littafi ya dakko ya dubo min sunanta amma number Wayar da ta saka wrong number ce an Kira an Kira sai muji wani yare ya daga Yana ta gwalalgwalan,Kasan yanzu anci gaba duk tasha Indai tafiyar nesa ce dole sai an dauki sunanka da number Wayar sabo da rayuwa ko hatsari da sauransu. Affa yace tsarin ai me kyau ne yanzu a Lagos Ina za a ga mutum Kawai mu duka Addua Allah ya bayyanata bazan kashe kaina akanta ba Yar iskar yarinyar da bata San arziki ba algunguma,dama da gani kaga munafuka Affa haka ya dinga ta masifa,Lele ya dinga kyalkyala dariya,ai Affa sai ya juyo da masifar kan Lele yace kaima ubanka zaka ci wlh duk ba a kanka ta gudu ba me bakin jini in banda Hamida ma wace ta so ka duk matan ba ubanka Suka ci ba,daya ta yanke Maka Safara'u take ko Naja,daya ta Shiga Neman ranku me zaka ce sai iyayin da girman kan jaraba Kai da Fauzan ba fus duk mata ke juya irinku ai zamuga Fauzan ma gashi can ya Kare a karuwa zata cinye masa jari, Allah yasa ta karya jarin kamfaninsa muga shegen da zai Kara Masa jari ya kashe wayarsa,Lele dariya Kamar ta kashe shi,Affa Yana shiga bedroom Mimi tace kai Kuma lafiya Kai da wa kake hayaniya Haka? to azukwi uwar son Jin gulma karki dameni dan Allah in ba so kike na koraki kauyenku ba ki min Shuru karki shiga harkata yaja tsaki, kafar Mimi ya fatalar ya wuce ta jikin bed din,ta bishi da kallo Kawai fadansa ya motsa yau. Jannat wani hospital Babba amma na Gomnati ne under federal akwai kwararrun doctors ciki,me zamuyi a nan Kai dai ka biyo Ni muje,Yana binta Suka Shiga asibitin,office din wani Suka karasa tayi knocking yace yes,kofar ta bude suka shiga yace Jannat ya kwana biyu,Fauzan ya Mika Masa Hannu Suka gaisa,yace Jannat ya na ganki yau ba itace ranar zuwanku ba fa amma sai kizo yau? Murmushi tayi tace ko zaka min hanyar Shiga? Yace no ba ranarku bace yau jibi ne ai baiyi nisa ba ko da damuwa ne?ba damuwa Allah ya kaimu jibin tace ta mike Suka Masa sallama Suka fito yace Ina zakije baki da lafiya ne? Kalau nake ta furta tana murmushin take,Ina so ka Fara sanin tushen labarin da Zan bak....kafin ta karasa kuka ya kwace mata tana kokarin tsaida kukan wani hawayen sabo Yana zubowa. Jikin Fauzan ne yayi sanyi yace sorry kiyi hakuri,Hawayenta take sharewa tana cewa to nayi Shuru ta kirkiri Murmushi amma sai kuka ya sake kwace mata,key din motar ya karba ta shiga shi yayi driving Suka bar asibitin lokacin ta dan tsaida hawayen ta daina kukan,ya kalleta yace be strong okay Kai ta daga masa,yace Zan aureki idan kin yarda,da sauri ta kalleshi tayi dariya tace karuwar? ae Zan aureki Haka ko nasan wani labarinki ko ban sani ba Ina sonki a haka a shirye nake da na aureki idan kin amince. Babu mutumin da baya so yayi aure amma kayi Hakuri yanzu ba aure ne a gabana ba,duk abinda ke gabanki bai wuce na kudi ba ni Kuma ki Nawa ne Zan na baki ko yaushe, Rally? Yace shured, alright na amince. A wani katafaren gida tayi parking a kofar gidan Wanda securities ne ko Ina,ta kalleshi tace kaga gidan nan to nan ne gidanmu,ya kalleta da sauri tace yes,suna haka sai ga katon Alhaji ya fito daga gidan securities suna take Masa baya da alama masallaci zai je harda carbi a hannunsa tace shine Mahaifina,bari ka gani sai ta bude mota ta fita daga Nesa tace Abba,a fusace ya juyo Jin muryarta ya kalli securities dinsa tare da furta ku Mata rugu rugu shegiyar yarinya mayya,nace ba ubata bane ni,cikin mota ta koma da sauri tace ja mota mu wuce,Fauzan ya figi mota suka Kara gaba ta kalle shi tace labarin ne bazai yuwu ba sai ka gani da idonka sai jibi zamuje Inshaallah ranar Zan fada maka komai amma dogo ne labarin tana magana tana hawaye Yana parking a wani eatery ta fito shima ya fito har yanzu kuka take yace Ina zamuje a haka kina kuka, kanta ta daura a kafadarsa tana goge hawayenta tana cewa bari na gama. Ki Gama ubanki Suka ji muryar Mama,suna juyowa Ashe tare suke da Daddy da Kansa sunyi parking motarsu a gefe basu kula ba,Jannat ta tsuguna tace Ina yini Mama ta kifa Mata Mari,Fauzan zaiyi magana tace kana magana Allah ya Isa shine kake boye kamanninka,Fauzan Yana ta Addua karsu Kira sunansa Mama ta tankada keyarsa shiga mota mu tafi bakin lalatacce,Daddy yace yau sai ka yabawa aya zakinta,karuwar banza karuwar wofi kin lalata min dana cewar Mama,Daddy yace kin San waye ni idan na sake ganinki da Dana sai na daureki wlh duk kwaratan naki babu me iya karboki,tuka mota muje dan iskan yaro. Fauzan zai Shiga motarsa yace ki jirani zanzo karki kula kowa please,karki ma sa wannan abu a ranki,ko a hijabi na ma cewar Jannat,Mama kuka ta fashe dashi tana na Shiga Uku anyiwa dana asiri shike nan,Daddy yace rabu da shi Zan dau mataki Kai shiga mota,Fauzan ya shiga mota ya sauke glass Sai da ya juya zai wuce ya zubowa Jannat bundle na 1k har biyu yace ban San ya zata kasance ba ki jira dai ko kinji Shuru nasan yanzu za a sa min takunkumi,Jannat ta kwashe kudi tayi cikin hijab dasu tana Masa bye bye tana daga Masa Hannu Yana Murmushi,tace nan gaba zaka bude min fuskarka ya Mata alama da Hannu tayi Shuru,gaf yaji ya daki motar su Daddy,ai Jannat na ganin Haka ta tare taxi ta wuce,Fauzan Kuwa Daddy ne ya fito ya leka ta window dinsa sabo da ya tsaya da driving din dama a hankali suke tafiya shi yasa har suke magana da Jannat. Daddy Hannu ya zura ta window ya Fara dukan Fauzan Yana gocewa,face mask din ya fincike ya jefar ya zare glass din ya ballashi ya zubawa Fauzan rankwashi,Fauzan yace I'm sorry haba Daddy saurayi kamata na wuce duka kana kunyatani kalli mutane suna ta kallonmu ana Mana dariya please Daddy,Daddy yace kana Wasa dani ko ja mota Bari muje gida naga Wanda ya haifi wani Ni da da Kai. Mota Daddy ya koma Suka jera Suka tafi suna hanya,Fauzan ya Kira Affa bayan sun gaisa yace Affa kaga na samo matar aure nace ayi min aure anki Wai sunce karuwa ce baza ayi min ba Allah Nima zanyi ta Nabeel idan aka ga yarinya da ciki ba ruwana ,Affa sarkin kulla aure gashi Nabeel yayi abin Nan basu ji dadi ba azo ace an sake Yi a family ai da kunya,yace shi Abbas din ne yace baza a baka ba? Yace ae da Mama ma, rannan ma itace akace karuwa nake bi Allah sai na bita ma,Affa yace a'a dan nan karka sake bari za baka ita Ni Zan tsaya maka,ka kirashi ka Masa fada tunda Kaine yayansa watakila Kai yaji maganarka,yace dama Ina so in baka labari ma na ga Jannat din da kake nema Affa yace Kai bana son karya yace wallahi har gidan da take kayiwa Daddy magana su kyaleni kaima Zan fada maka inda Jannat take ko na kawo maka ita har gida wallahi,Affa yace an gama ba abinda zasu maka shi yasa nace duk yaranmu kafi kowa hankali,gaka babban yaro ba abinda za a maka yanzu zanyi magana. Ai Affa Wayar Kaninsa sanata ya Kira ya zazzageshi yamusu warning su kyale yaro aure zaiyi ba karuwa bace,Daddy yace shike Nan Yaya tunda ya hadani da Kai,ba zancen hadi wlh karka sake ka shiga safgarsa ka kyaleshi Yana da hankali yaro aure zaiyi ka jawa matarka kunne,Mama tana ji tana gani Mijinta yace Yaya ya hana zata Yi magana yaci mutuncinta yace ta raina Yan Uwansa haka tayi Shuru... Affa yau sabo da murna Haka ya hakimce a gaban tv ya Kira Mimi yace Aisha Kamo min tashar da suke sa michiel Jackson da Bob Merly. Masu sharhi Ina godiya AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 Part 2 86-90 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM page naku ne Ummu Haidar Mom Abdallah Ma'esha Inner Habee Habeebah Heebat Ummu Lateepha Fauzan suna komawa gida Daddy yace sai ka fada Mata yaushe zamu Kai kudin aure bazai dauki lokaci ba wlh aura maka ita za ayi ka karata,Mama ta fashe da kuka tace wlh gidan Nan za a kawota ko anyi a nan zamu zauna da ita sai Naga halayenta da idona bai Isa yayi rayuwa shi da ita ba tazo ta mallake min yaro a kawota nan gidan Ina kallo a gaba na,Fauzan ya kalli Mama yanda ta damu kanta dariya ma take bashi yace Daddy jibi Zan fada maka tsare tsaren bikin namu nawa ba irin nasu bane sosai za ayi sha'ani kawaye ne da ita na gagara, Allah yasa ya Zama Alkhairi cewar Daddy yace Ameen ya haura sama aka bar Mama tana kuka. Wanka Fauzan yayi ya canja cikin kana Nan Kaya ya wuce masallaci yayin da Jannat ta koma gida ta samu su zee da zancen aurenta,Murna suka dingayi tare da furta haka Allah yake ikonsa na kirki suna gida kullum cikin hijab ana tafiya Islamiyya amma ga Yan bariki suna ta aure na kirkin su suna gida a zaune,ai wlh kawaye zamu gayyata sai munyi bikin da ba'a taba Yi ba a kusa damu, dama lokacin Ramcy ta canja Mana katon gida,Jannat tace matsalata daya dangina,ke karki damu ga Maman zee ga Babanta sannan ga Yan uwanmu duk su zamu kawo su Zama iyayenki tunda dai Kinga Indai aka tabbatar da karuwanci mukeyi Iyayensa baza su yarda ba wlh gwara ma ko za a fada to ace babu me hujja Kawai fada akeyi babu Wanda ya taba gani,kin San duk wannan dogon binciken yanzu ba wani Yi ake sosai ba musamman Abuja Jannat tace Kawai ku Fara tunanin anko da alama baza a dauki lokaci ba gwara a fara shiri,Peace tace gyaran Amarya fa shi Zaki Fara dole a fito da a susun mu da shi za ayi Miki abinda ya kamata,Jannat tace na gode bani da Yan Uwa kamarku wlh Kun rufa min asiri Kun daukeni kanwarku,muma so muke mu daina Indai mun samu miji na gari an gama,Allah yasa cewar Merry,Littafi suka dakko aka fara rubuta abinda ake bukata,Kudi karku damu Abbakati nasan zaiyi komai zai bada cewar Jannat. Bedroom ta shiga tayi wanka tare da gabatar da Sallah sannan ta Kira Fauzan tace ya kaje gida hope basu maka komai ba,Yana zaune a dining shi da Mama suna dinner yace no ba abinda ya faru gani ma ga Mama ya kalli Mama yace na baki ku gaisa? Jannat tana ji Mama tace Allah ya kiyaye wlh bana kaunarta Wayar ya kashe da sauri amma ta Riga taji,Jannat a ranta tace ke Kika jiyo tunda ogan Yana so na angama ba abinda zai dameni mu rayuwa wacce ce bamu gani ba. Sai 11pm ya sake Kiran Jannat bata nuna Masa taji me Mama tace ba yace baki bacci ba? ae ni bana bacci da wuri,me kikeyi a kwance Kawai nake Ina tunanin duniya,hmm bama tunani na ba? kaima kasan Indai za a tuna rayuwata ta duniya ai kana ciki,Fauzan harda wani lumshe Ido a ransa yace shege zama da karuwa ba karya ba,Yarinyar ta gama dani lokaci daya,Wai ya haka ne Abba? ya naji kayi Shuru ta furta Masa tana wani Kasa da murya ta katse Masa tunaninsa,yace na dan gaji ne eyya Sannu dama munyi aure da na maka massage sorry bana kusa, Fauzan ya zaro Ido yace a ransa Allah ya datar dani ni Kam Wanda baiyi love da Jannat ba an cuce shi ji yake Kamar ya fisgota ta cikin wayar ta sake katse Masa tunani da tambaya kayi Shirin bacci kenan uhm yace sabo da yanda tayi Maganar sai da tsigar jikinsa ta tashi,tana magana sai ya lula tunani har tace ko dai bacci kake ji ne?sabo da Kar ta gano shi sai yace yes gobe Zan kiraki back ya kashe wayar ya juya tare da jawo pilow ya rungume Yana tuna Jannat. Bangaren Jannat ma ta Dade bata Yi bacci ba sabo da yanda take tunanin Abbakati har kashinta take Jin kaunarsa. Washe gari zata fita lokacin Yana office da safe text dinta ya gani ya shigo wayarsa ya duba tace zanje Saloon sai 2 ko 3pm Zan koma gida,reply ya Mata adawo lfy take care of yourself for me,love you. Yana tura Mata ya kirata yace wanne saloon zakije? ta fada Masa yace okay sai gobe zamu hadu,ba damuwa ta furta. Tana taxi gaf take da karasawa saloon din taga wata shegiyar mota ta gani ta fada tana Mata horn,mamaki takeyi ko waye wannan oho,Me taxi yace da alama wancan mutumin ke yake bi tace ban San motar ba ni karka tsaya. Sai da yayi parking ta bashi kudi ta fito kenan shima me motar ya fito sai taga Fauzan Dan uwan Nabeel a duniya ba Wanda take Jin kunya irinsa hijab dinta ta ja tare da rufe fuskarta tana boye Fuska,shi kuwa Kamar yanda ta sanshi tun farko ba Fara'a Haka yau ma,a kunyace tace Ina yini Sannu,Yace Wai mene kike Jin kunyata? Murmushi tayi ta sake gyara hijab dinta tare da rufe fuskarta kusan gaba daya,yace Jannat tsakaninki da Allah baza ki fadawa Affa inda kike ba ko zai samu ya maidaki inda ya dakko ki kin San irin damuwar da yake ciki? Kanta ta sadda kasa tana kallon yatsun kafarta hawaye ya dan Fara sakko Mata tace nasan ban kyauta ba Zan Koma ne.. Wata magana ce ta kawoni wajenki Jannat ta kalleshi kadan tare da maida kanta kasa tace to Ina ji,yace Ina sonki Jannat wlh tunda na ganki a Abuja naji Ina kaunarki in ba damuwa mu koma ni na yarda Affa ya daura min aure da ke,Zan rike ki Amana Jannat,Ina Matukar kaunarki,kullum da tunaninki nake kwana nake tashi,duk abinda kike so a duniya Zan Miki ko million Nawa ne Zan baki tunda Naga Kamar Neman kudi kike da jikinki. Kallonsa tayi ya gyada Mata Kai yace wallahi ko Mene Zan kashe a kanki in ma ba a kasar Nan kike son Zama ba Zan tafi dake London muyi rayuwa a can,Jannat tayi Murmushi Kawai kanta har yau Yana kasa sabo da kunyarsa da take ji,yace ya Kika ce? a hankali tace kayi Hakuri Ina da Wanda nake so shine rayuwata,duk abinda nake nema a duniya ya gama Yi min,Ko Nawa ya kashe ya fada ni zan biya shi burina ki aureni Jannat kece rayuwata haba me dadin suna. Jannat tace nidai kayi Hakuri wallahi ko duniya zaka bani bazan iya rabuwa da Abba ba,au sunansa Abba? Jannat tace ae,yace Allah wadaran Abba Kuwa ya cuceni Kika sani ma ko Dan Iska ne kike bata lokacin ki,ba Dan Iska bane Jannat ta hayayyakowa Fauzan da masifa ya zagi Abbakatinta, sorry ya furta Bazan miki dole ba Allah ya bada zaman lafiya idan biki yazo kije kiga Affa dan Allah, Inshaallah ta furta,ya sake cewa Allah ya bani me so na Nima irin yanda kike son Abba,tace Ameen tana ta Jin kunyarsa,Kudi ya zaro Wanda bai San Nawa bane ya Mika Mata fafur taki karba tace na fada maka ni Abbana yana min komai,yace ai a madadin Affa na baki,karba tayi tace na gode ya Mata sallama ya tafi Yana ta dariya a mota harda cewa woo shege ni Yana driving dinsa. Kullum suna wayarsu suna soyewa da Fauzan Wanda bata San shine Abbakati ba,har ranar da zasu koma hospital tazo,su Zee Suka ce zasu gaisa da shi idan yazo kofar gidan,Jannat tace ku bari zaizo musamman,Suka ce ba damuwa,Yana zuwa gate dinsu ta fito sanye cikin lace milk and Golden takalminta,mayafinta da jaka Golden,tunda ta fito yake kallonta ta cikin glass dinsa, ya dauketa Suka je ba bata lokaci aka ce su shiga,duk ga mutane nan suna zuwa da alama ziyara ake Shiga, ita dama tasan Hanya itace ke nuna masa Hanya dake katon asibiti ne sai da Suka Yi tafiya me nisa kafin su Isa wani bangare Wanda ka rantse a daji wajen yake wani katon daki Suka shiga,farkon shigarsu sai da Fauzan ya tsorata da irin marasa lafiyar da ya gani har idonsa yake rufewa bai taba zaton a duniya da marasa lafiya irin wannan ba. Gaba daya wata irin halitta ce da su ta daban,wani me Kalar wani ciwon ma bai taba ganin irin ciwon ba,baza ka taba cewa mutanene ba,sai ka rantse Aljanu ne abin ba kyan gani ko kadan tsoro ne ya kamashi Addua Kawai yake a bakinsa. Wata nurse tace Jannat an Zo ne ai ku Kuna layin masu sauki sauki kuje,wani daki Suka sake shiga wani gadon ruwa Jannat ta nufa Wanda Sam ba a gane wacce halittace macece ko Namiji sabo da gaba daya in banda Kashi sai fata a jiki,Kamar kwarangwal,gashin kanta babu ko daya,sai a wani gadon ruwa ake kwantar da irinsu in ba haka ba zagwanyewa zasuyi su rube a hakan ma wani wajen duk ba fatar ma Sai Kashi gashi nan ana gani an nade da bandage da auduka kowa sai wayyo wayyo Kawai ake ji,Jannat a gaban gadon ruwan ta tsuguna tace Mummy matar nan duk wayyo wayyo da takeyi sai data gane muryar yarta,bata iya magana sosa amma da kyar ta hada kalmar Jan..Jan...sai da ta huta tana numfarfashi ta sake cewa ki roka min Allah ya dauki raina na huta,Allah...Allah...ya Miki Albarka...Allah ya baki miji na gari...Allah ya tsareki da Sharrin duniya....Ni Kam nasan bazan tashi ba...shi...shi....shi...yasa nake so naji kinyi aure.... Jannat tuni zuciyarta ta karye ta fashe da kuka me tsuma zuciya,jin Haka matar tace Zan warke Inshaallah...ki daina kuka bani hannunki naji....Jannat tana kuka ta kamo hannun Mummy ta damke suna ta kuka a Haka. Shi dai Fauzan tausayin Mummy ya kamashi kamar zaiyi kuka ga marasa lafiyar dake wajen ba me iya zuwa wajensu sai Mai juriyar gaske,Jannat tace Mummy ga mijin da Zan aura na kawo Miki shi yazo duba ki,Matar nan tace Alhmdllh daga yau na daina kuka ko yanzu na mutu Allah ya Gama min komai,Jannat ta kamo Hannun Fauzan ta hada Dana Mummy ta damke hannunsa tana sa Masa Albarka Wanda shi baya gane me take fada ko daya ma Jannat ke fada Masa abinda take cewa. Mummy ta sake yin Mimimi da baki a haka magana take Yi Jannat ta fassara masa tace Allah ya maka Albarka,Fauzan yace Ameen Ameen Allah ya baki lafiya. Masu kora ne Suka Zo suna cewa lokaci yayi kowa ya fita aka Kori kowa aka rufe wajen. Wajen Doctor Jannat Suka koma yace Jannat I'm sorry to say mahaifiyarki ta cike iya kwanakinta Wanda aka gama kayyadewa in mutum bai warke ba zuwa wannan lokacin to an daina kawo Masa ziyara,Kawai kudin kula da ita Zaki ci gaba da turawa duk wata,amma bazan boye Miki ba,dakin da za a kaita sai me nisan kwana ke Fitowa daga ciki za a barsu a Nan ana dan basu treatment idan Allah yayi tana da nisan kwana ta warke idan kuma kwananta ya Kare to za a kiraki ku dauki gawa Kuma kin San komai tunda an fada Miki. Jannat duk iya dauriyarta ta kasawa tayi hawaye ne ya balle Mata tace ba komai zanci gaba da Mata Addua da ace Ina raye Ina kallo uwata ta mutu gwara ta mutu a asibiti ko banza idan na tuna zan San nayi kokari Allah ne baiyi ba, Allah yasa ta warke yace Ameen,Fauzan Yana kallo yace Nawa ake biya duk wata? Yace dubu dari biyu,Nan take ya karbi accnt din asibitin,suna barin asibitin ya tsaya a bank ya biya na wata biyar,yace Zan tura wasu bayan biki ya Mika Mata tailer. Godiya ta dinga Yi Kamar zata goya shi,kafin ya tashi motar Hannu yasa tare da goge mata hawayenta yace cry no more Inshaallah zata warke ai cuta ba mutuwa ba sai kiga me lafiya ya mutu marar lafiya ya mike karki damu Allah na Nan. Tana ajiyar zuciya tace In...Inshaallah. Kayan ciye ciye dana Sha ya siya musu yace sai Ina? tace muje Queens Garden sai na baka labarin a can I think is better, ba gidana ba?shedan Yana kusa Kuma ma gidan da za a kaini Zan gama kalle shi,yace farko Mama tace a gidamu za a ware Miki part ki zauna kafin mu koma gidanmu,ba damuwa cewar Jannat. Wurin shakatawar Suka je ba mutane a ciki sai dai dai,Katuwar Sallaya ya shimfida musu suka zauna suna cin Shawarma da Ice cream tace Kamar yanda ka sanni Hannu ya daga Mata yace bari Mana mu gama ci,okay tace sai da suka gama sannan yace Ina jinki to Alhmdllh Yanzu naci na Sha sai ayi ta yi Ina ji start Labari Jannat tayi dariya tace Babana dan asalin Bauchi ne shi kadai Iyayensa Suka haifa suna da arzikin dabbobi ya taso cikin gata su Suka daure Masa gindi yayi ilimin boko dana addini,bayan ya gama Diploma Iyayensa suka zabo Masa Mata a cikin dangin sabo da Babarsa Hajiya Saudatu da suke cewa Anne itace ta zabo Masa matarsa Talatu Yar yayarta ya aureta,bayan ya aureta Allah bai taba sawa sun Haihu ba har yaje matakin degree ya samu babban Aiki a NNPC lokacin Kuma mahaifinsa Yakubu ya rasu Haka arzikinsaYana ta bunkasa Babana Alhaji Usman Yakub mutumin kirki ne sosai da sosai akwai kyauta da taimako ga addini amma akan abinda mahaifiyarsa ke so ko yake so to fa idonsa rufewa yake Yi,danginsa kaf shi yake musu komai sai abinda yace daga nan ma da arziki yayi arziki sai ya tattara ya dawo da matarsa Hajiya Talatu da Mahaifiyarsa data rage Masa wato Anne,Anne sabo da tana son Talatu bata damu da rashin haihuwarta ba sai ma hanawa tayi tace baza a Mata kishiya ba,har Abbana ya koma England Karo karatu da iyalansa kaf yake tafiya Kuma suzo hutu Watarana ya gama Phd ya dawo an Masa Karin girma arziki yayi gaba ya Zama kusa a kasar nan,Watarana da watan Ramadan yaje masallaci Jin tafsir da Yamma a Nan Abuja sai ga Yan agaji sun kawo wata budurwa amma ba yarinya bace zata Kai shekara 32 Suka ce wani yare ce a Nigeria can kauyen Ogun state suke Yan ta'adda sun kashe musu kowa a kauyensu sun kone Kauye Suma da kyar wasu Suka tsira ciki har da ita. Ta shiga zaga gari gari Neman taimako tayi aikin wanke wanke da shara a gidajen masu kudi daban daban amma wahala da wulakanci ke korarta har Allah yasa ta samu aiki a Nan Abuja a gidan wani me kudi Nan ma wulakanci kala kala,ita Kuma babu abinda yake birgeta irin musulunci tunda yanzu ba dangi ne da ita da zasu hanata ba tana dai da Yan Uwa a Lagos Suma ba zumunci suke ba amma sun San dai juna ana gaisawa watarana. Kawai sai tace zuwa tayi a musuluntar da ita Kuma a taimaka Mata da wajen kwana,Mummy Kyakyawa ce matuka fara babu Wanda bazai so ta ba,Nan take ta Musulunta a masallacin ta zabi suna Asiya Abba yace shi Kuma Yana sonta idan ta Amince zai aure ta. Kowa yayi farin ciki ana ta yabonsa a Nan malamin ya nada Mata waliyyai Abba ma ya bada nasa lokacin ma Yan Uwansa maza sun Zo Watarana a Nan suke azumi sune shedu Nan take ya bada sadaki dubu hamsim aka daura Masa aure da ita. Sai a ranar Anne taji da ita da uwar gidansa Talatu ai Kamar Abuja zata Kama da wuta haka suka dinga bala'i,Abba yayi ta bawa Anne Hakuri da matarsa yace kaddara ce, Bayan nan Suka Yi kamar sun hakura da komai, ya bawa Mummy part dinta daban. Daga ranar Kuma Anne ta fara kishi da Mummy tare da Hajiya Talatu Suka hade kai basu da aiki sai zagin Mummy da wulakanci kala kala bata da katabus a gidan nan duk aikin gidan nan itace takeyi shekara daya ta samu ciki,Hajiya Talatu tana Jin labari taci kwalar Abba tace munafuki kaje kayi Mata ciki ni kaki kayi min wallahi bata Isa ba Nima sai na samu ciki,Fauzan yace tab hauka sai Mata Jannat tace Anne tace kayi mata Kamar yanda ka yiwa Amarya ciki itama Talatu ai itace uwar gida itace ya Dace ka Fara yiwa yawwa yanzu sai kayiwa Talatu ciki itama,Abba yace ciki ai Allah ke badawa ya kuke abu Kamar jahilar,Anne ta fashe da kuka tace yau akan Amaryarka banza Asiya kake kirana da Jahila,Abba yace kiyi hakuri ba haka nake nufi ba,da kyar ya lallaba Anne ta hakura,watan cikin Asiya biyar Talatu ma ta samu ciki,Anne tace dan jakar uba yaji wuya da ace ban Masa kaca kaca ba ai dai bai Miki cikin ba,Talatu tace ai duk da haka bai birge ba tunda daga zuwanta zata rigani haihuwa. Ana zaune masifar yau daban ta gobe daban har cikin Mummy ya shiga wata tara tunda suka ji labarin watan haihuwa ya Kama Anne ta saka Talatu a gaba Suka tafi Kauye Wai zasu je zaga dangi dan Kar ma su taimaki Mummy,gashi Mummy bata da kowa sauran a Lagos suke ba wani ma mutunci ne da su ba suna ganin su Yan birni ne basa harka da Mummy,cikin ikon Allah ranar da Mummy zata Haihu Abba Yana gida ya kaita asibiti tare da wata dattijuya me aikin talatu,ana zuwa ta Haihu lafiya kalau ba wata matsala har akayi suna Basu dawo ba,har Mummy tayi sati biyu sannan Suka dawo Suna dawowa Suka ga Namiji ne ashe sabo da a garin da sukaji ana zancen Amarya ta Haihu ko saurarar zancen basuyi ba,Anne ko yaushe a karbowa Talatu maganin gargajiya take Wai duk dan ta Haihu lafiya sabo da Talatu Yar gidan Yayarta ce,sai ga ikon Allah lokacin da Talatu ta zo haihuwa sai aiki aka Mata aka Ciro jaririya mace. Tunda taji sauki aka sallamota ta dawo sai tace bata San zance ba me yasa Abba ita bai Mata cikin Namiji ba,Kuma ta ya za ayi Amarya ta riga ta haihuwa bayan daga baya aka aurota,suna ta wannan, rayuwa tayiwa Mummy tsanani kullum sai kuka sai Addua Allah yasa ma tana zuwa makarantar Islamiyya sabo da ta kula da addininta. Watarana Anne tace Mummy taje ta dama Mata kunu a kitchen tana shiga kitchen Talatu ta Shiga ta durawa jaririn Fiya fiya a bakinsa,sai da Mummy ta fito taga gawar yaronta bakinsa Yana ta warin fiya fiya,Mummy tayi kuka,Abba Yana zuwa ya tara Yan aiki ana bincike wata a ciki tace Hajiya Talatu ce ta ganta da idonta,Anne ta fashe da kuka tace idan yayi magana sai ta tsine Masa Abba Yana gani ya hakura Kuma shima bai damu ba sabo da yafi son Talatu tun asali duk abinda tayi bata laifi a wajensa Watarana ma yasan gaskiya amma sai ya take. Cikin ikon Allah bayan wata biyar sai Yar Talatu ta kama cuta a ranar da aka kaita asibiti ranar ta mutu,Suka ce Mummy ce ta kashe Mata 'ya sabo da taga danta ya mutu a lokacin sai da Abba ya farfasawa Mummy jiki,Kaf Dangin Abba sun tsani Mummy arniya ma suke kiranta da shi, sabo da mutuwae yarsa ya saketa,bata San inda zata je ba sai Anne tace a bata boys quarters ta zauna ciki sai ta dinga musu wanke wanke da shara da aikin gida,Mummy ashe tana da ciki bata sani ba sai da ya saketa da sati daya ta fada Masa Abba yasan gaskiya sai yace shi wallahi ba cikinsa bane Sam,Anne da Hajiya Talatu suna zuga shi. Tafiya tayi nisa kullum Mummy itace ke aikin gidan komai da komai ga duka ga zagi ga hantara ita Kuma sanadin cikin da take da shi na Abba shi yasa taki tafiya ta bar gidan,a haka cikinta ya shiga wata tara,lokacin Talatu ta sake samun ciki ya zube amma,Suka sake cewa Mummy ce mayya. Daga nan Mummy ta Haihu da kanta a daki ta gyara kanta da jaririyarta Ni kenan nice,Allah yasa Abba duk wata Yana biyan Mummy kudin aikinta su take tarawa da kudin tayiwa kanta komai da me haihuwa ke yi har Tinkiya ta siya da kudinta aka yanka naci suna Jannat. A haka na taso Mummy na raino na tana tara kudin aikinta har Talatu ta samu wani cikin yaron data haifa bai zo da rai ba har na shekara biyar lokacin nasan yanda Talatu da Anne suke dukana sun tsaneni sosai ko bangarensu bana zuwa amma duk da haka har bangarenmu suke zuwa su min duka,tace in munyi aure zaka ga inda Talatu ta yanka min duwawu da wuka,Haka Mummy ta samu makaranta me tsada ta sakani primary da Islamiyya me kyau,tun Ina Yar karama take koya min karatun addini amma bata Yi boko ba nice idan na koyo karatun boko sai na koya Mata,Muna haka har na shiga Secondary,a lokacin duk aikin gidan Nan tare mukeyi da Mummy duk sun sallami Yan aikin Mata,Abba Kuwa baya kaunata,baya kaunar ganina,Mummy har Kara ta kaishi wajen Yan Sanda amma abinka da me kudi ko fada basu Masa ba sai Suka ce Kawai ya barmu a gidansa muci gaba da Zama a matsayin yan aiki,lokacin Kuma Talatu ta Haifi danta Namiji,Mummy in kaga yanda ta lalace duk ta rame amma a haka ban rasa komai ba komai tana min Kaya masu kyau nake sawa makaranta me tsada. Talatu da Anne suna ta Jin haushinmu har na gama Secondary Abba baya kaunar ganina karshe ma suka hanashi ya dinga biyanmu kudin aiki sukace kyauta zamuyi kudin aikinmu shine Zama a gidansa ,ranar da bazan manta da ita ba itace ranar da munyi girki da Mummy mun gama zamu ebi abinci dake dama abincin sai taga dama take bamu Watarana sai dai muci a boye,tana hanamu iba Muka tafi sai da Yamma bayan na gaji na tafi Islamiyya sai ta kawowa Mummy abincin ranar Mummy tayi mamakin ganin abincin da yawa,Haka taci ta koshi ta ajiye min nawa,na dawo daga makaranta Kawai na iske Mummy kwance tana murkususu,na fashe da kuka na fito na Kira masu gadi su taimaka min amma Anne ta fito tace duk Wanda ya ko kulani a bakacin aikinsa. Da gudu na tafi na kirawo Abba,Ina kiransa da Abba ya kwada min Mari ya kore ni yace shi ba ubana bane, na fito Ina kuka na rasa wa zai taimaka min na fita na kirawo me taxi shi ya taimaka min na kwaso kudin da Mummy take Tarawa Muka tafi asibiti Labarin Nan yanzu aka fara sai gobe Zan ci gaba kaga yanzu dare yayi yace no muje gidana ki karasa min a can,tace hadari fa yace alright muje to na ajiyeki a gida Allah ya kaimu goben,tace ameen ya Mata take away tare da kawayenta na kayan makulashe ya ajiyeta gida. Masu sharhi kunfi kowa birgeni Ina kaunarku AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 Part 2 91-95 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naki ne GIMBIYA DIYAR KATIBI Washe gari da wuri ya nemi Jannat wannan Karon a gidansa Suka hadu basu bata lokaci ba yace Ina jinki Ci gaba tayi da Muna zuwa asibiti aka Mata wasu gwaje gwaje Nan aka tabbatar min guba aka bata kuma kayan cikinta duka sun tabu babu Wanda bai tabu ba,lokacin munga tashin hakali lokaci kadan idan zatayi Kaki sai dai na jini Kashi ma Sai kashin jini a haka kudin data tara ya Kare na siyar da abubuwanmu duk Suka Kare a magani Kai har katifarmu sai da na siyar sutura masu kyau duk na siyar da su a araha sabo da kudin magani Duk abin nan Abba ko lekomu asibiti bai taba Yi ba haka danginsa kaf bare su Anne ko kulamu basu Yi,watanmu uku a asibiti Mummy taji sauki tana tafiya da kafarta amma bata warke ba,abinci baza taci na kirki ba ko ya taci da yawa sai kashin jini ciwo ya tashi,daga wannan muka rasa Mai taimaka Mana karshe Abba ya koremu daga gidansa gaba daya,ba yanda zamuyi haka Muka Fara Neman aikatau duk Wanda ya ganni da me jinya sai yace baya so,kullum Mummy ciwonta Kara karfi yake ba kudin asibiti. Nayi kuka na godewa Allah gashi kuma a kasan gada muke kwana ruwa iska kanmu zai Kare karshe wani bawan Allah dan cirani ne yazo daga Kano ya Mana hanyar wani kango kafin a karasa gini mu zauna,abincin ci ya gagaremu na samu na lallaba mummy Muka Fara fita yawon bara da maula gidajen Yan siyasa,idan muka samo sai asibiti ya cinye kudin ga jini da ake yawan karawa Mummy sabo da bai Zama a jikinta,muna wannan hali me ginin kangon yazo ya kore mu yace gini zai karasa muka fita muna ta yawon bara da maula tun Mummy tana karfin hali har ta gaza ruwa iska sanyi duk akan mu ke karewa kullum dare sai dai mu je bankin wani shago mu kwana kowa yaki taimaka mana. Yan siyasa ma karshen taimakonsu a bamu dubu goma shima idan Muka je sau biyu baza a Kara bamu ba,a haka Watarana shagon da muke kwana a bakinsa masu shagon mace ce wata dattijuwa suka Zo Suka ganmu tausayinmu ya kamata ta tambayeni labarinmu na fada Mata shine ta hada Ni da yarta Zainab wacce ake cewa Zee kawata kenan ta gidanmu. Zainab itace tazo tare da kawayenta su peace a motar Ramcy lokacin Ramcy tana da mota suka rungume mu hannu biyu,karuwai sun taimaka Mana masu mutunci basu taimakemu ba,wlh da su muka dinga Jinyar Mummy a cikin gidansu suna kashe Mana kudi,sune suka tsaya min Muka kaita asibitin daka ganta suna kashe Mana kudi lokacin ma sunfi samun kudi a karuwanci,har tsawon shekara guda suna dawainiya da mu,ci Sha da sutura,mummy Kuwa abin Kara gaba yake,suka tura mu asibitin Aminu Kano watanmu uku ba sauki,muka koma asibitin shika tsawon wata biyu,karshe Muka sake dawowa Abuja da Mummy lokacin kamannin Mummy ma ya fara canjawa,daga nan asibiti suka gaji aka kaita inda ba a zaman jinya sai dai aje ziyara,kudi Kawai Zan ta turawa,lokacin su Zee sun gaji har kunyarsu nakeyi idan na kalli irin sana'ar da sukeyi suna biya min kudin asibiti,gida,ci Sha da sutura basu taba gajiyawa ba. Wani Yana wannan sana'ar Yana taimaka min ni me zai hana bazan Yi ba ga inda Zan dinga samun kudi a Kan lokaci,duk da Haka Kuma Ina zuwa gaisar da Affa na amma baya ko kallona har na gaji na daina kulashi nima na Shiga harkata,bani da Yan Uwa sai su zee,Haka na nuna musu Ina so Nima nayi irin sana'arsu har shawara suka bani Kar na shiga Suma so sukeyi Allah ya shiryesu,nace ni zanyi ai Kuwa Suka tara min surutu masu tsada da kyau ba abinda basu siya min ba. Suka dinga gogar dani suna koya min abubuwa Wanda ya shafi bin maza da yanda zanyi sex,da sauransu amma rule dinsu daya babu wacce zata kawo musu kwarto gida suyi Iskanci a cikin gida,sai dai bako ko yazo a gaisa ko wani abu ana Haka ranar farko da zamu fita gefen titi Good Evening Ina bakin titi duk su zee Suka samu aka daukesu banda ni,Fauzan yace ai baza ki samu me daukanki ba Jannat ni Allah ya ajiyewa ni akewa tanadi, Jannat tayi dariya taci gaba Sai dana dade sannan Allah ya kawo wani matashi ya daukeni a motarsa,bamu karasa hotel ba yayi parking yace na bashi labarina dan Allah yarinya dani na fito irin wannan sana'a shine na bashi labarin karya Kamar yanda Affa ya fada muku shima haka yaji,shine ya daukeni yace gidan marayu zai kaini ajiya kafin nan gaba ya nemo min gida na mutunci su rikeni,ban San abinda zaiyi kenan ba da gaskiya Zan fada Masa watakil yasa a taimaka min. Amma na rigada na Fadi karya idan na canja baza su yarda dani ba daga shi har Affa,kaga ba me yarda ya tallafa min,a lokacin da Affa yace aure zai min ba haka naso ba banyi Niyyar barin gidan ba naso ya barni mun dan Saba daga nan sai na fada Masa gaskiya ya taimaka min to amma Ina canja labari ba Wanda zai yarda dani,gashi sai yace mijin Hamida Zai bani Lele,ba wacce baza taso auren Lele ba amma me zuciyarsa tana Kan Shakiransa,gashi Ina tsananin kunyar wannan Fauzan bana son hada Ido da shi Ga tunanin Yan Uwana su Zee duk halaccin da Suka min sai suyi tunanin guduwa nayi ma,sannan basu San Ina nake ba ai bai kamata ba,shi yasa a gidan Sam bani da walwala bani da fara'a har sai dana samu hanya na gudo sannan na samu Jin dadi. Mummy ta Kuma shike Nan bazan je mata ziyara ba taya Zan iya Zama a gidan Affa dole na gudu. Amma shi Fauzan mun hadu sau biyu da shi a nan garin ma Kuma mun gaisa,Fauzan ya gama jin labarin kaf zuciyarsa ta tsumu sosai badan namiji bane sai ya sharbi kuka to amma ga Jannat na hawaye shi idan yayi wa zai lallashi wani,ya maze yace kiyi hakuri Inshaallah wahalarki tazo karshe in Allah ya yarda bake ba bakin ciki,Jannat ta kalleshi tace taya zanyi farin ciki Bayan Mummyta na daina ganina Inshaallah zata warke ai cuta ba mutuwa ba. Lallashinta yayi sosai har ta daina kukan yace yau Zan nuna Miki fuskata gaba daya,Nan take ya cire bakin glass dinsa tare da face mask taga Fauzan da gudu ta koma bayan kujera ta buya dariya ta bashi Yana ta dariya ta buya da rarrafe ta dauki Jakarta Haka da rarrafenta tayi waje tana zuwa bakin kofa ta fice da gudu,gashinsa me Matukar yawa da laushi ya shafa Yana kiranta amma da gudu ta bar gidan, kyaleta yayi sai da dare ya Kirata a waya a hakan ma sai da yayi bugu hudu kafin ta daga cike da kunya tayi sallama ya amsa Ina yini ta furta kamar tana ganinsa haka take nuna Jin kunya a fili,ya furta my Jannat kasa magana tayi sai da ya kirata sau Uku sannan ta iya amsawa a hankali na'am,yace tawan tayi mukus a ranta tana Jin wani irin farin ciki tace oumm,yace ko ba mine bace? dariya ta kyalkyale da ita tace ka raina min hankali da yawa na daina kulaka,Ido ya waro waje Lokacin Mama ta shigo palonsa bai sani ba tayi Shuru ta labe Wai dan taji da wa yake magana,taji yace wannan kunya haka sai kace yaune zan kalla Duwawun,ai Mama baki ta rufe tare da juya baya ta juyo tare da toshe kunnuwanta ta karaso ta Bayan Fauzan tare da fisge Wayar tace to Yar Iska karuwa kin lalata min yaro kinibabba Allah ya Isa Zaki aure min Dana ki cuce shi mayya Dangin tsiy....da sauri Fauzan yace haba Mama ya Kai Hannu zai karbi wayarsa da take ciwa Jannat mutunci,Mama Wayar ta jefar ta rufe Fauzan da duka ta gadon bayansa mahaukaci ka zare ka susuce a Kan karuwa ta fashe da kuka tace wallahi bazan taba yafe Mata ba Fauzan tsayawa yayi Kawai Yana kallon ikon Allah tace ka Zama dan Iska Ashe zancen Iskanci kukeyi,yace wlh Mama ba haka bane ba abinda kike tunani bane yanzu nifa Duwaiwan da nace nufina idan anyi aure zanga wani tabon rauni,Mama ta sake fashewa da kuka tana na shiga Uku ni Mariya sai tayi part din Daddy,Fauzan kansa ya dafe shi kadai yace Mama bata gane ba Sam yanzu duwawu shine zancen Iskanci tashi yayi ya bita part din Daddy. Can ya isketa tana fadawa Daddy tace to danka ya lalace ni ban taba haifo da irin Fauzan ba yaro baya Jin magana ga taurin kai, ga miskilanci ayi Masa fada bazai ji ba to wlh na gaji yayyensa Zan fawa su Anwar,Daddy yace Anwar Ina zai iya da Fauzan ai duk duniya Nabeel ne kadai zai fada Masa yaji ki fadawa Nabeel ni Fauzan yanzu Addua nake Masa karuwa ta gama da shi,Mama tace zancen Iskanci fa na iskeshi yanayi Wai zaiga Duwaiwakanta abin ba dadin ji,Fauzan da Yana shigowa yaji me Mama ke Fadi juyawa Kawai ya koma part dinsa. Sai wurin 2hrs ta kawo Masa wayarsa tace gashi nan tana Kira sai ka daga in kayi da kyau kanka ta juya ta fice,Jannat ce ke kiransa kashewa yayi ya Kirata back,tana dagawa yayi zaton tayi fushi ko bakaken magana zata fada Masa sai yaji akasin haka tace kayi Hakuri ana ta maka fada a kaina zai wuce ne karka damu fatan ranka bai baci ba,Fauzan yaji wata sabuwar kaunarta ta kamashi lokacin Mama ta kasa zaune ta kasa tsaye ta sake lallabowa ta shigo dakin Fauzan bai sani ba lokaci yace wow shi yasa nake Kara kaunarki da ace Ina kusa yau da sai nayi hugging naki so tight,Kukan Mama ya sake ji tana rafka salati,Fauzan yace na shiga Uku yace Zan kiraki ya kashe wayar Mama tace ta tabbata abinda kake kenan ka rungumeta daga Nan sai me? sai aikata masha'a daga ji dama Kun saba marar mutunci ta sake durmawa Fauzan duka a baya,ya gantsare tare da cewa da zafi fa Mama,duka ta sake Kai Masa ya tashi ya fada bedroom ya kulle Kawai ya kwanta. Tana fitowa ta Kira Nabeel,Dawowar Nabeel daga Office kenan Hamida ta kawo Masa abinci yaga Kiran Mama Aslam Yana hannunsa ya daga Suka gaisa,Mama tace karar Fauzan na kawo maka Kai kadai kake fada Masa yaji yaron Nan ya lalace karuwa ya samo ta gama da shi Wai ita zai aura nayi magana su Affa sun nuna ban Isa ba,to yanzu na hakura ya aureta ya koma kalaman banza da ita yanzu Kamar Fauzan ace baida Aiki sai waya da mace Kuma kalaman batsa kullum batsa da maganganu marasa dacewa shi suke kwana Yi da yarinyar nan, shine na bugo waya na sanar maka dan Allah kayi Masa fada tunda taku tazo daya Lele ya bawa mama Hakuri yace yaron ai gani yake ya girmi kowa yanzu bayan Lele kwata kwata shekara daya da rabi ya bawa Fauzan,Indai haka ne Fauzan zai gane kurensa ya kalli Hamida Suka hada Ido Suka tafa a hankali yace Zan Masa fada karki damu Mama zai hadu dani,Fauzan bai kyauta ba ya bata wayonsa Yana Magana ya daura hannunsa daya a wuyan Hamida Yana ta matsa wuyanta Yana ta wani jijjiga Mata kai,Mama tace to Alhmdllh Yanzu hankali ya kwanta,a Kara hakuri Yara sai hakuri Mama cewar Lele,to ba komai a gaida Hamida da Aslam zasu ji Inshaallah ya kashe wayar. Yana kashewa ya dakawa Pipi duka a kafadarta daga wajen tsakiya ji kake dassss,Wurin ta Sosa tace Kai Kai wlh sai na rama ko ba yau ba,Hamida tace ko Fauzan wa ya samu oho yace ke rabu da su Mama yanzu matasa da Yan Mata Watarana a soyayya akan dan kauce wannan ai zunubin soyayya,Hamida ta Fara dariya zunubin Soyayya, Aslam ya Mika Mata ungo danki ki kaiwa Nanny na gaji,au dana ne ma? ae Mana,Pipi tace Yaro in Yana jariri na mamanshi duk wahalar duniya Uwa,idan ya girma na Babansa sabo da zai na tayashi aiki ko gona ce da shi za a tafi,idan yayi aure na matarsa ya koma wajen matarsa komai matarsa da yaransa,shi yasa nake son mace me tausayi da Imani ko Ina take iyayenta na ranta cewar Nabeel, to Allah dai ya bamu masu Albarka cewar Hamida. Tace to Abincin fa tunda ai dai kayi wanka,na koshi yau gidan Ammar naje matarsa ta takura min sai naci abinci,Fuska Pipi ta bata tace amma kasan Zan maka abinci me yasa baka fada min ba ka Bari na wahalar da kaina? Sorry ya furta Yana gyara kwanciyarsa Nanny ta kira ta karbi Aslam sannan ta dawo ta kwashe abincin ta Bawa masu gadi duka Lele ya fara bacci bai sani ba tace in Kun koshi ku bawa Almajirai ai suka lashe abincin oga sun San yafi nasu,Idonsa ya dan bude a saman Sofa yace na gaji ne Pipina,Tausa ta fara masa Yana Jin dadi ta furta dan Allah karka Yi bacci yanzu da dare ka hanamu yin bacci. Jawota yayi jikinsa ta fada tana kwance a jikinsa ya maida hannayensa ya rungumeta sai bacci,sai magriba ta tashe shi yayi Alwala ya wuce masallaci bai dawo ba sai bayan Sallar Isha Yana dawowa yace Yunwa nake ji Ina abincin Nawa? Na bawa masu gadi ai Kai kace ka koshi an cika maka ciki a gidan wani shi yasa na bayar sai kasha tea. Kallonta yayi yace bana son Wasa haka nace bazan ci ba? ae Mana haka kace ka koshi yaushe Zan ta ajiyar abinci ya lalace,kallonta ya sakeyi ya fara fada to nufinki me zanci yanzu? Sai kasha tea ko ka siyo Mana muci,na gaji yanzu bazan iya fita ba,kawo kudi na siyo, kin San Allah ki tashi ki dafa min abinci wallahi idan baki dafa ba ke Zan cinye Kuma na rantse sai na baki kuka sai kin kwana kina kuka gwara ma ki tashi. Je ki dafa karki bari na siyo abinci,Hamida tace yo wa zaka tsorata mutane ne suke wani maka kallon wani na kwarai suna ganinka da Riga da wando su zaka zarewa ido,kwafa Lele yaja yace in na saki abu bakya min musu baki taba ince kiyi kice a'a ba sai yau kin fara rainani Pipi,ya zanyi na takarkare na maka abinci kace min ka koshi ai da Sai kace min na koshi amma ki bar min sai anjima, zaka ce min wani na koshi an cika min ciki a gidan Ammar yan.ya..yan...ni bacci zanyi ta furta tana cuno dan bakinta. Yace baza ki ba kenan tace gaskiya dai cikin kalami me dadi aeee, Alright ya furta ya figi key din mota ya fita Yana cewa bari na siyo kaza me nononuwa Zaki gane kurenki yau,Hamida ta harde kafafu tana wani karkada kafafu Yana fita bai dade ba ya dawo duk ruwan sama ya fara jika Masa Kaya sabo da dan Fitowa da yayi a mota,mura har ta fara kamashi,Yana dawowa taga Leda daya ya siyo komai guda daya kazar ma quarter tana ta kamshi taji hadi, kwadayi ya kamata,ta koma kusa dashi ta zauna Lelena ta kwantar da kanta a kafadarsa yaki kulata cin abincinsa yake kawai taga alama zai cinye bai bata ba. Hannu tasa ta zari cinya daya ta gutsira Lele ya kwace zata gudu ya jawota ya danneta sosai ya kwakwulo ta bakinta gaba daya, Tasha wahala tana faman nishi ta sake dawowa zata dauka ta sunkuci Fruits salat ta fara kurba yace wallahi kina hadiyewa ban yafe ba,Tissue ta dauka ta juye ta bakinta ta kuskure da ruwa ta zubar tace to dai ban hadiyi komai ba yace ya fiye Miki ya bata rai Kamar ba shi ba. Yana gama cinye komai, yaga tayi zuciya ta Shige dakinta tayi wanka tayi Shirin bacci tana zuba kamshi a ranta tace Wai Lelene zai tsine min akan fruits ba komai,tana Shirin kwanciya ya shigo bedroom dinta cikin Shirin bacci amma ko Riga bai Sa ba daga shi sai boxers yana ta kamshi ta ko Ina,Kuma ransa a bace sai da Hamida ta tsorata Ko magana bai Mata ba ya haura saman bed ya jawota ta kwalla yace ihu wayyo na shiga Uku,yace gwara ma ki tsaya na rantse yau Banci abinci ba fa,yace ni na hanaki ya hau cire Mata Kaya gaba daya tana nokewa yace ki tsaya ko na yaga su wlh,tana gani ya ciresu du ya jefar yace naso na Miki wani abu na masifa amma kece karki damu bazan iya Miki ba,ya damki Pipi tun daga kiss ta gane babu lafiya,Kamar zai cire Mata baki tace da zafi wayyo lebe na,Dan muguntar Lele ma harda cizo yake hadawa haka Yana zuwa Kan gorar Madara sai ga Hamida tana kwarara kuka komai baya Mata da sauki,Lele yace in saki abu kice baza kiyi ba sa'anki ne ni sabo da Ina kyaleki,Wallahi bazan Kara ba dama ban taba musu ba muje sakwara Zan daka maka,Lele yayi Dariya a ransa a fili yace a'a sai dai ke na daka Miki sakwarar yanzu ta Fara Neman guduwa ya damkota ya dadddanneta sosai yace yanzu Zan Miki dakan sakwarar ya shigeta da karfi, Ya fara jajjage Hamida da wani salon mugunta yake mata ta fara daurewa amma ta kasa sai ta fashe da kuka wallahi bazan sake ba,dan Allah kayi hakuri,Yana Hidima yace Ina saki abu.... kice baza...baza.. kiyi ba...sabo...sabo da Ina Wasa dake...bai San wanne hukunci zai Mata ba bata Jin magana Hamida kuka wiwi tana bada hakuri,kayi hakuri wallahi na tuba bazan sake ba wayyo Allah Lele zafi,nice fa ta sake fashewa da kuka,Lele bai kulataba sai da ya tattabatar ta ladaftu ta Sha wahala matuka,taji jiki ko motsin kirki bata Yi sabo da dausayi radadi yake da azaba kawai Hamida tana ta kuka yace tashi to sai kinyi girkin ta fashe da kuka yace ko baza kiyi ba ne? zanyi zanyi zanyi wlh ta furta ta sauka daga bed din tana tafiya wani iri ta fada kitchen tana kuka tana girki ta gama Masa jullof din spaghetti ta kawo Masa bedroom dinsa lokacin ya fito a wanka Yana goge jikinsa da towel Yana wani nishadi sabo da shi dai Kam ya kwashi dadi sosai sai dai Yana Jin bai kyauta ba da yayiwa Pipinsa haka. gefen bed ya zauna sanye da rigar wanka,ta ajiye Masa abincin a gabansa yace zauna ki cinye hawaye yaki tsayawa haka ta zauna ta cinye dama yunwa take ji,Aslam ya karbo mata yace gashi ki bashi nono ya Sha,kuka ta saki ta kalli yaron tare da cewa ubanka ya cinye nonon babu,baza ki bashi ba Nabeel yace tace to da sauri ta janye rigar baccinta data maida Kan nonon yayi jajir sabo da wahala,tace au ashe Kan bai gutsire ba,ai na zaci ya cire, ta bawa yaro tana ta hawaye ya koshi ta canja Masa kayan bacci sannan ta kwantar dashi a bed dinsa karami ta Shiga wanka. Ta gasa jikinta yau Kamar hauka sannan tayi wanka tare da tsarkake jikinta ta fito,tana fitowa tana ta Fushi idonta duk ya kumbura ta canja kayan bacci ta shirya sosai ta haura saman bed ta kwanta can karshen gado,Murmushi ya saki yace Pipina,My love come to me Baby,kin kulashi tayi ya jawota jikinsa Yana Pipina I love you, ya saki dariya Yana ta faman Yi mata dariya yace my lollipop ya kwantar da ita a kirjinsa zata tashi yace kina tashi Zan Kara,kwanciya ta koma tayi ya daketa ya hanata kuka,Yana so ya nuna mata ba komai yayi ba,rungumeta yayi Yana shafa bayanta yace I'm sorry,Kuka ta fashe da shi Yana ta lallashi taki Shuru tace bazan je makarantar ba na fasa yin karatun ma,Lele Yana dariya a ransa yana dan lallashinta bata hakura ba har bacci ya kwasheta. Bayan kwana biyu Affa da Kansa ya isa Abuja tare da Mimi sabo da a nuna Masa Jannat ya gani da idonsa,Mimi tace munzo hankalinka ya kwanta yace ah ai gwara na gani Ido da Ido yaran Nan Fauzan da Nabeel ba kirki ne da su ba sai su sani a kwana na gama chashewa da kida a banza,Fauzan da Lele ai kananan mutane ne abin kunya gaba suka bashi, baya kuwa sai dai aga bayansu idan sun tada Sallah,Mimi da Mama suna ta dariya gidan Yaya Ubaidu Suka sauka har Daddy can yaje Suka hadu suna ta hirar zumunci,Fauzan kuwa Jannat ya dakko suka zo tare gidan Kawu Ubaidu inda manya Suka taru,a kasa Suka zauna Jannat ta gaishe su,Affa ya kalleta yace haka kike Yar gayu? Dariya sukayi duka Fauzan yace ki basu labarinki Jannat kowa yaji,Jannat ta nutsu ta Basu labarinta kaf har haduwarsu da Fauzan,Affa ya tausaya yace Yar Nan bar fada sai nayi kuka saurin kuka ne dani,Mimi tace Kinga rayuwa Jannat Allah yasa karshenta yazo,Daddy har da kwalla yace mutane ba Imani,Kawu Ubaidu ya gyara glass dinsa yace tab ikon Allah yarinya Sannu kinji Mamanki Kuma Inshaallah Zan tsaya Mata ki bar komai a hannuna Ni likita ne Babba zanyi iya kokarina,Jannat sai godiya take Fauzan Yana ta murna Affa yace yo ai nine ubanta dama na Kai kudin Aurenta gidan marayu shike Nan Kawai sai a daura da Kai Fauzan dama tsoron hukuma nakeyi na warware auren da Nabeel ya dawo kanka nine waliyin Jannat,duk wani Abu Ni Zan dauki nauyi,Jannat tana ta godiya tace amma Affa a barni a gidanmu anan za ayi bikin yace ai kowa naki Yana Abuja Nan zamuzo gaba daya a daura aure ayi biki,Mama ce ta fashe da kuka tace wallahi karya take ban yarda da labarinta ba karuwa ce. Gashi Nan a gidan karuwai take,Affa yace da Allah saurara karki Mana hauka a nan anji a gidan karuwai take yarinya ta shiryu danmu Yana so zai auri abarsa Haka shike nan, kince a gabanki zata Fara Zama mun baki girmanki a matsayinki na uwar yaro to me Kuma za ayi,Daddy yace dan Allah Yaya ku rabu da ita kada Allah yasa ta hakura,tashi Mama tayi ta bar palon ta shiga mota ta koma gidan mijinta. A lokacin aka yanke biki wata daya,an fadawa Lele da Hamida komai suna ta mamaki. Tun daga ranar aka fara Shirin biki ba Kama kafar yaro,harka da Yan duniya ba karya Jannat Tasha wani irin gyara in and out sai kace wata Yar Gomna ta Kara wani uban kyau da haske,skin dinta wani glowing take duk inda ta wuce kamshi ke tashi,Ramcy tace to Banda Wasa da gyara ko kinyi aure ki dinga samun lokaci kina gyaran jiki tunda mijinki Yana da hali Sex da komai mun karanta miki yanda zaki nunawa mijinki so da kauna duk an gama da Nan girke girke kin iya. Ana ta Shirin biki har ya rage Saura sati biyu duk sun gayyaci Kawaye na gaske tsageru sunyi anko sosai,komai Fauzan Yana bada kudi yanda ya kamata,sun hana ma yaga Amaryar Sam. Tunda Mama ta fadawa Nabeel ya yiwa Fauzan fada ko Fauzan bai Kira ba yace zunubin soyayya ne,Hamida kam tuni ta hakura ta daina Fushi da Lelenta ta shiga taitayinta Biki Saura kwana hudu Maman Zee Hajiya Bilki ta dawo gidan su Zee da Zama har sai an gama biki,duk su zee sun daina fita business sun canja shiga ta mutunci sukeyi sabo da biki,Maman Ramcy ma gidan ta dawo sun Zama Iyayen Jannat da su aka ci gaba da shirya komai. Ranar Kuma aka kawo lefe akwati ashirin cif Kaya na Alfarma Fauzan ya zuba,sannan Jannat har gida ta aikawa da Babanta IV Yana gani sai da yaji haushi a ransa Taya zata Yi aure sai dai Kawai a aiko Masa da Iv,yasan Jannat a gidan karuwai take Zama bai damu ba sai yaronsa da ya aiko lallai karta sake tayi auren nan. Jannat zancen Kawai taji Kamar Iska ta share aka ci gaba da shiri komai sun shirya,dinner ma Mama da kyar ta yarda ayi kala daya bazai kamawa karuwai waje a banza ba,Yan biki na nesa a bangaren Fauzan duk sun zo har Hamida da Lele su Affa dasu Mimi,bangaren Amarya ne dai ba kowa sai Maman Zee da Maman Ramcy sai su Yan matan,Dangin uban Jannat duk sunki zuwa Kuma har katin gayyata ta Kai musu. Tunda su Hajiya Talatu suka ga Iv Jannat zata Yi aure hankalinsu ya tashi ita da Anne,Talatu garin masifa harda jefar da yaronta karami Wanda shine na biyu yanzu Anne tace rabu da ita baza mu bari ta zauna lafiya ba har gidan da take auren zamu Shiga sai mun watsa komai munafuka Mai halin uwarta Talatu tace bana kaunar ci gaban Yarinyar Nan tambadaddiya Haka suka dinga Yi. Ana gobe dinner Mimi tace Hamida ta koma gidan su Jannat ta zauna a can har a gama biki,Lele nai sani ba ta tafi bayan sabo da ita ya samu part huda nasu su kadai ne ba Wanda zai shigo musu tare zasu zauna a Nan har a gama biki gashi bata Nan bai ma sani ba sai labari yaji Wai sun koma can ita da Ihsan. Yan matan Amarya Yan duniya kawayensu na nesa sun Zo duk Yan duniya ne sun cika gidan Nan shafta Kawai ake Sha gashi sun hadu da Shakira. Ina godiya masu sharhi AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 Part 2 96-100 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Rukayyatu Mom Aneesa Anfare Nanacool Ayi Hakuri ba Editing sabo da masu jira na bayar Hamida sakin baki tayi tana kallon ikon Allah yanda suke iya shege baki ba sakata ba koma,i komai ya Kama fada sukeyi, Jannat ma tana ji iya kaci tayi dariya,Ihsan ta kalli Hamida tace Pipi ta Lele ba Kya magana Ina bakin,Murmushi Hamida tayi tace Ina fa zanyi baki Ina gaban Iyayen gidana,peace tace dan Allah kuyi Hakuri zan dan Sha sigari yau tun safe ban Sha ba suka kunna wiwi suna ta bulbulawa Zee ita Shisha ta dakko ta kunna ta zauna a gefe ta fara bulbulo hayaki sai kace salansa,Ramcy idan zata huro hayaki har wani karkace baki take gefe,Jannat tana kallonsu ba ruwanta ita, Ihsan suka hada Ido da Hamida suna ta uban mamaki ga uban kida duk an bulbule su Hamida da hayaki kamar su suke Sha har kawayen su duk Sha suke wasu su basa Harkar hayaki sai Syrup zancen Iskanci Kuwa sai ka toshe kunnenka,Jannat an Sha kyau,motar Hamida da tazo da ita suke ta ara suna yawon shirye shiryen biki,Jannat bata ko daukan tsinke komai sune suke mata ka rantse Yan uwanta ne A cikin kawayen Merry akwai me make up na gaske da me gyaran Amarya da tsara wajen wedding Event,komai suna da me sana'ar a cikinsu sabo da sun hada da kabila a cikinsu sun kware wajen Neman na kansu kumai,Kawar Merry wajen Make up ne da ita ma a Lagos gashi tazo biki da kanta da kayan aikinta ba inda Jannat zata je wani abu kayan gyaran gashi ma akwai me saloon a kawayen peace,sunga Aslam din Hamida me kyau Yana Shan gayu sai daukansa suke yi Hamida taji dadin Zama da su,sai karuwa takeyi,Hamida ta kalli Jannat ta wani Kara kyau tace Amarya ke bakya Dan zukawa ne? ba shi nazo Yi duniya ba cewar Jannat,peace tace to Oga Fauzan dai da gani zaiyi zalama Yana sonka da yawa ki dage dariya suka yi suka tafa. Mama taki sakewa da bikin ko Murna bata Yi,kannenta sunzo suna dakinta suna hira,Daya a ciki tace wai ni wace Fauzan ya makalewa haka naji a cikin Yan biki ance ya haukace a kanta so har dana hauka,Mama baki ta tabe tace wata low life prostitute ce kin San badan me gadinsa Murtala yazo ya fada Mana ba da baza mu Gane ba,bana farin ciki da wannan aure sam,kin San halin Iyayensa su ba ruwansu duk abinda yaro ke so bashi suke,Kanwar Mama tace dan Allah Aunty karki wa auren nan baki wannan rashin farin cikin da kike fada ba Kya so zai iya kawo tangarda a auren nan,danki ne kiyi hakuri kisa albarka tunda abin Allah yayi,Yayar Mama dake zaune saman sallaya tace barta wallahi mariya bata da hankali Sam banga ranar da zata girma ba suna ta yiwa Mama fada tace Ina bafa Zan so Yarinyar Nan ba na tsaneta ni ,sai kiyi ai Suka rabu da ita. Affa ne ya Kira Mimi yace ya wajen 'yata Jannat ba matsala ba abinda suke bukata? Mimi tace ae na kirata a waya ba wata matsala,Nabeel kayan da zai saka a dinner da ranar daurin aure ya kwaso Yana neman Hamida ta goge Masa su aka ce tana gidan su Jannat can zata zauna har biki,a waya ya Kirata tana dagawa yace wa Kika tambaya Pipi? Mimi da Affa ne Suka ce naje ba yin kaina bane Kuma na kiraka Wayar taki shiga kin San Ina tare da su Anwar anyway Allah kaimu ma hadu I miss you,Miss you more,Ina Babyna? Ka ganshi yayi bacci yaro me Hakuri Dan Albarka,to Allah dai ya Masa Albarka cewar,Murmushi Nabeel yayi tare da furta to Ameen Su Anwar da Hammad abokin ango ana ta shirye shirye Fauzan sai wani nishadi yake,ana cewa ango sai ya washe baki,Palo ya shigo ya iske Mata Yan Uwa da dattijai sai tsokanarsa akeyi ana ga Ango sai wani fara'a Wanda ma baya saurara a biki Yana ganinsu sunzo sai gaisuwa da karramasu,Wata tsohuwa tace ango kasha kamshi harda Masa guda Fauzan hannunsa a Aljihu sai siyat ya zaro du uku ya Mikawa tsohuwa aka dinga dariya da sowa Sai da ya fito Fatima kanwarsa da aka Mata aure tace gyara kintsi da kyau angon Jannat muna murna ya saki Murmushi yace ai ke dama ta kowa ce ga hankali duk matan gidan Nan ke ta daban ce ,tace kudin make up Yaya ya zaro ya bata Nan take,Yana fita kofar gida zai fita wajen Amarya sai ga danginsu na Kauye mota guda Bus an kawo su duk mazan gidan suna kofar gida ana ta hada hada,Fauzan da in Banda gaisuwa baya kulasu in sun Zo Harkar gabansa yake Yi amma yau dake bikinsa suka zo har cewa sannunku da zuwa,Yan Yara sun dirgowa daga mota bus ya tsaya kamar conductor ya dinga fito dasu daya Bayan daya, su Muhseen suna ta kallon ikon Allah suna gulmar Fauzan Kamar ba shi ba. Ya dakko wata Yar yarinya harda cewa yawwa Yar kyakyawa fito ya ajiye a kasa manyan Kuwa duk wacce ta fito sai yace barka da zuwa,suna ta mamakinsa sai Murna suke an karrama su wajen driver ya zaga yace Nawa ne kudinsu ya fada masa yayi ai kuwa biya kudin yace ka dawo ka maida su gida idan an Gama biki,wata tsohuwa tace yaro Allah ya maka Albarka jibi zamu tafi,Fauzan ya bawa Tsohuwar kudin motar komawarsu dukansu yace in ya dawo ku bashi har da karawa me Mota dubu daya yace gashi kasha ruwa a Hanya sai godiya me Mota keyi yace sai na dawo jibin,tsaya a kawo maka abinci in kaci sai ka tafi cewar Fauzan Driver yace Allah mutumina to godiya nake ,Me aiki ya fadawa ta kawowa Me motar abinci harda ruwa da lemo su Kuma Yan biki Suka shige cikin gida. Anwar dariya suke ta Yi suna kallon Fauzan kamar ya zare,Muhseen ya durawa Fauzan ashar yace shege indai matane sai ka gaji ka ture mun San abinda kake yiwa wannan munnar, Fauzan yace ku dai dinga Jan girmanku ato ya Shiga mota Yana zuwa gidan Amarya Hamida ya gani ta fito zata siyo abu yace yawwa Kanwata,Hamida ta juyo taga Fauzan tace wlh karya kake yaro matar yayanka ai nice yayarka Amma kin San dai na girmeki da shekaru wajen biyar kanwata kike,hmm haka dai kace amma kayi kadan nice Aunty,yace Amaryar taki daga waya ki Kira min ita,Hamida tace ai Kuwa sun fita yanzu da motar da na Zo da ita zasu Nemo abu, Envelope ya bawa Hamida yace gashi ki bata kudin likinta ne gobe ta karba ya ja mota yayi gaba abinsa. Shi rabon ma da yaga Jannat an dade Washe gari Dinner da Yamma Mata da maza ta bangaren kowa shiri akeyi Kamar me,kowa kure adaka yakeyi,kawayen Amarya gaba daya sun wani hade cikin Kalar ankonsu daban,bangaren Dangin Ango ma haka, Hamida ankon kawayen Amarya tasa Ihsan ma haka,Iyayen Amarya Babar su Zee har Mimi a layin Iyayen Amarya suke da dattijai kawayen Maman Zee,Hajiya Talatu da Anne ba Wanda ya gayyace su Amma sai da Suka kurda suka samo Kalar ankon Amarya Suka Yi Suma suka saka Wai zasu je ganin kwaf me kudin Jannat ta aura ko talaka Kuma anan zasu kulla alaka da Iyayen Ango su samu shiga. Motocin abokai ne Suka Zo daukan kawayen Amarya lokacin Amarya make ake tsara Mata,Ango harda tafiya wajen aski na musamman da wankin kafa,ya Sha wata arniyar shadda Yar gaske wow in kaga ango abin kallo ne da Yar babbar riga dai dai shi Yar dagwas ya zuba kyau wata Kalar silver,Amarya Kuwa kayanta gown ce dark pink ta Sha uban dauri me shegen kyau Kalar Silver gogoron, make up din yayi kyau matuka da gani kasan kwararriya ce tayi,Takalmi,Jaka sai tasa Silver Kalar kayan ango, ta diga kyau kamar a sace ta,Hamida da iyayi wajen make up ta tafi aka tsarata sai kace Amarya a can Nabeel ya dauketa ko Aslam Mimi ta bawa shi take ta fama.. Yan matan Amarya ba a magana sabo da Yan duniya ne dole aga wanka,suna can suna jiran Amarya tazo a shiga,kida Yana ta tashi mutane suna ciki ana zuba Idon ganin Amarya,dangi kaf anci gayu ana can,Mama da kawayenta harda make up Suma,Fauzan Hammad ne ya dakko shi a mota ta musamman Suka je zee itama a karshe ta fito taja motar Hamida ta tafi Bayan ta saka Amarya a mota,Fauzan ji yake Kamar ya sume yanda yaga yaga Amaryarsa ta hadu,wani kamshinta ya cika motar,shima ga nasa kamshin Yana tashi. Juyowa yayi ya kalleta tare da sakin murmushinsa me tsada,kunya ta kamata ta lumshe Ido yace wow beautiful,dariyar kunya tayi,yace yaushe rabon duniya da ayyaraye Yana rike hannunta,a hankali tace bafa a daura auren ba,pink lips dinsa na kasa ya dan cije yace ai gobe ne, tana ji Yana ta kallonta Yana kallon lallenta yace Mashaallah My Heart har suka Isa wajen Yana yabon kyawunta. Yan matan ne Suka taho jikin motar har Hamida Amarya aka fito ango ya fito,Yan matan Zee da peace sune a gaba su biyu sun jere, sai Merry da Ramcy a bayansu mc ya bada sanarwa masu rawa ku koma ku zauna Amarya da Ango Zasu shigi. Gurin an kayatashi wajen da Amarya da Ango Zasu shigo an Masa wani ado na musamman ga wani golden buzer Yana zubowa ta sama, aka saki kida Zee da Peace ne Suka Fara shugowa da rawa suna rawa me Kayatarwa,Merry da Ramcy suka biyo baya,Hamida da Ihsan suka taho Hamida ba'a rawa Ihsan Kuwa ana yi sama sama Suka wuce Suma ta wuce inda Lele yake Yana dariya yace kin rufawa kanki asiri da kin sake ki yatsanki ya mota da yau kinji jiki fari tayi yace kinyi kyau Pipina. Amarya da Ango ne suka shigo da taku na takama sai waya kake gani ta ko Ina ana dauka,sai sauran kawaye da abokan ango Suka biyo baya masu shigowa da rawa suna ta fama,Amma kowa kallon kawayen Amarya akeyi sabo da abu suke na musamman da birgewa Bayan an zauna mutane an cika sosai anci gayu bikine na Yan gayu da masu kudi,Mc yace abokin ango ya fito ya dan bada tarihin ango Hammad ya fito ya bada a takaice da turanci aka tafa masa,aka ce kawar Amarya ta fito sai suka tura Peace sabo da ita har masters ne da ita ta iya turanci na gaske Sanda ta fara magana sai da kowa yasan me ilimi ce Haka ta danyi a takaice, sai ga su Talatu sun shigo karya kake kace basuyi kyau ba sun kashe Naira a jikinsu Talatu harda saka gwalagwalai,ba Wanda ya santa a wajen sai Jannat sai su Zee,suna wani takama suna gadara Suka Yi gaba gaba suka zauna suna tabe Baki,Anne ta tsufa tukuf amma har wani iyayi take Dariya ta dinga bawa mutane ma. Jannat ce ta radawa Fauzan a kunne tace kaga su Talatu can ki waye ya gayyace su oho mc yace Amarya da Ango su shigo fili suna Fitowa Hajiya Talatu da Anne ne suka Fara shiga ciki Anne Yan dubu dubu take likawa Talatu Kuwa Doller take karantawa sabo da tsabar son ace su shegu ne suka dinga zuba kudi shi kuwa Dj ya dinga ragargaza kida,Fauzan ya rike hannayen Jannat suna kallon juna Yana ta cewa I love you suna ji Talatu ta dinga harararsa mutane sai liki ake yiwa Amarya da ango bayan sun fita kawayen Amarya suke shiga rawa suke ta gaske duk sun kware sai kallo ya koma kansu ga wanka iya wanka,Su Zee kamar Mazaunai zasu fado wasu matan kasa Zama sukayi suka mike sun baza Ido suna Shan kallo,Hamida ta sake komawa zata yi liki Lele yace banda rawa amma tana gama tayi girgiza a haka har sau Uku ta yo waje su Anwar sai dariya suke Yi sabo da idan ta girgiza kafada sau daya sai ta huta sai ta sake yin daya tana yin sau Uku ta fito. Haka ance anci an sha an chashe kuma abin ya kayatar bayan sun dawo gida kawayen Amarya suka Yi wanka Suka Fara hira har Suka Yi bacci. Washe gari daurin aure 11am,duk sunyi wanka ana ta shiri ko wanne Bangare wani masallaci kusa da gidan su Jannat anan aka taru an cika sosai,Ango ansha farar shadda kal kal Yana wani sheki,Amarya ma taci gayu cikin wani lace me kyau da tsada dark blue an Mata dauri duk sun Gama hadewa 11pm aka daura auren Jannat da Fauzan akan sadaki dubu dari,bayan an daura ango suka Zo aka Yi pics sannan Suka wuce inda za aci abinci gidan su Nabeel dama iya dinner din da akayi shine shagalin bikin gaba daya an gama shi yasa wasu duk a ranar Suka tafi sai tsirari Wanda suka Zama dole sune Suka rage ranar da Yamma likis Amarya taci wanka cikin wani material me kyau dark green and black Mimi tazo tayiwa Amarya Nasiha Haka su Maman Zee sun Mata Nasiha sosai,Jannat ta danyi hawaye kadan aka dauki Amarya a motoci zuwa gidan su ango part din Mama aka kaita Yan Uwan Mama ne suka karbesu hannu bibiyu tare da yiwa Jannat Nasiha sannan aka musu jagora zuwa part din da aka gyarawa Fauzan yasha furniture kowa sai yabawa yake,dangi aka din zuwa ganinta,Jannat ta kalli su Zee Kamar zata narke tace dan Allah karku tafi yau,wayo Suka mata Suka tafi bata sani ba,Hamida da Ihsan sune a wajen amarya har 9pm sannan Suka Mata sallama Jannat tace Ina su Zee ne wai? Hamida tace Zaki hakura ma yarinya ki hakura sun Miki wayo sun tafi tuni,Jannat Jin haka ta fashe da kuka,Fatima tace kai muje ayi dai Hakuri suka tafi. Mama ce ta damu kanta tasa aka Kira Mata Fauzan lokacin ya gama shiri zai je wajen amarya a wani room da ba kowa ya iske ta tace bani wayoyinka ya Mika mata su duka tace Ina zuwa ta fice tana fita tasa key ta kulle Fauzan ta baya,Fauzan kasa magana yayi sabo da tsananin mamakin Mama,tun Yana zaune har ya gaji ya kwanta a saman bed din. Bangaren Amarya tana jiran ango Shuru Shuru,tun 10pm tayi har 12am bai Zo ba,mikewa tayi tare da Shiga toilet tayi wanka ta fito taare da gabatar da sallar Isha tayi adduoi sannan tayi shirin bacci ta haura saman bed kwanta tana tunanin ko lafiya,wayarsa ta Kira taji a kashe bata San Mama ta karbe wayar ba tana hannunta ta kashe ta haka ta kwanta bacci barawo ya Kara gaba da ita. Bangaren Affa kuwa Wayar Mimi ya karba Yana kallon videos na dinner,Alhaji Abbas da Ubaidu suna kallo su ma,Affa ya nuna screen din yace ga surukata ta wuce,Alhaji Abbas Yana kalla yace oumm itace hamidar? Affa yace Kai daina fadar sunanta Lele akan wannan sai yayi yaki ba kunya gare shi ba Dariya sukayi suka koma hirarsu ya duniya,Affa ya sake danno wani video Sanata yaga Yan Mata su hade yace mufa zamaninmu ya wuce ko ba dama ka so daya? Ubaidu yace Sannu me budurwar zuciya Allah ya shiryeku,Affa yace Ameen muna Shan wahala duk Mata daya ne da mu sai kace fitilar machine suyi ta shuka Mana rashin mutunci Washe gari gaba Daya bakin sun tafi har Hamida Amarya tana ta mamaki Bata San Ina angon yake ba,Bata San Mama abinci ma Sai dai ta Mike Masa ta jikin kofa tayi maza ta sake kullewa Fauzan ya rasa yanda zaiyi so yake ma Kawai Jannat tasan a inda yake Jannat tana ta gwada Kiran wayarsa tun safe har Yamma gashi Ko Yan aiki Mama ta hana su Shiga bangaren Jannat bare ta tambaya haka yansu duk Yan makaranta sun koma su Hamida sun tafi gida. Gajiya tayi ta gyara gidanta tare da dagawa kanta abinci taci ta koshi sabo da komai akwai an zuba,tana gamawa ta Kira su Zee Suka Sha Hira bata ce musu Bata ga angon ba tace suna zaune lfy Allah sarki ango Yana can an kulle shi. Murtala ne ya gaji talauci kamar zai kasheshi a Kauye ya taso har gida ya samu Mama Bayan sun gaisa ya furta gaisuwa nazo da rokon iri ki taimaka min wallahi Fauzan akan na Fadi gaskiya ya koreni da jimawa,ki taimaka ki bani Aiki ko a gidan Nan ne,Mama tace au korarka yayi baka fada min ba,yace in na fada sai ya min rashin mutunci Mama tace kwantar da hankalinka na daukeka Aiki a gidan Nan ka diga gyara flowers Zan dinga biyanka Murtala ya dinga godiya Mama ta mike tare da juyawa tace bari nazo ta fara tafiya lace ne a jikinta Riga da zani dake tana da kiba tana tafiya Murtala ya zaro harshe Yana wani kallon Mama yace kaga abinda Sanata ke Eating,Kaiiiiiiiiiii sai kace turmi ya kure Duwawun Mama da kallo Yana lashe lips harda Shan yaji shiiiiiuuii.....Mama bata San me yake Yi ba sakamakon a hankali yake Maganar yanda babu me jinsa. Jannat kwana daya bata ga angio ba kwana biyu shuru,ranar shiri tayi sosai ta zuba kyau cikin Atamfa maroon ta wuce part din Mama,palon ta Shiga Mama tana kallo a tv ta amsa sallama harda fara'a sabo da ta hada mugunta,Jannat baza ta iya tambayar Ina Fauzan ba babu kowa da zata tambaya,Mama tun daga gaisuwa bata Kara magana ba Jannat sallam tayi Mata ta fita,a boye ta tambayi Yan aiki suka ce su basu ganshi ba haka ta hakura ta koma part dinta. Mama shiri tayi zata fita,Murtala ya buya a jikin bango ya leko da Kansa mama tana tafiya Yana wayyo Ina Sha'awarki Mama kalli kaya,, Kaya Kaya,Haka ya leko Yana Shan yaji tare da kwance tazugensa a hankali yanda baza taji ba Ya furta Mama gata riketa kisha dadi,Haka yake ta iskanci Bangaren Fauzan kuwa Yana kulle a daki sai dai yayi wanka ya canja sutura ga abinci Ana kawo Masa zai ci gashi kuna,ya rasa ta inda Zai sa Kansa,tunanin Amaryarsa yake Mama ta shigo Yana ganinta ya fara rokonta Yana magiya dan Alla Mama ki Bude Ni dan Allah,ko ki fadawa Jannat gaskiya. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 Part 2 101-105 Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne UMMU ABBA HASSY SOJA LEEMAT SADIYA Maida key tayi ta datse kofar, idonsa ya rintse Yana Jin wani bakin ciki a ransa,toilet ya shiga ya leka ta window ya hango Murtala Yana aikin bawa Flower ruwa,Kira ya dinga Masa a hankali Kar wani yaji gashi ya Masa nisa Yana kasa shi Yana sama,amma Murtala yaji Kiran Yana dago Kansa yayi Ido biyu da Fauzan,har yaji tsoro Kar ko kara korarsa zai yi Karo na biyu,Fauzan yace Ina nan Mama ta kulle ni a daki kasan yanda zaka Yi ka bude ni idan ba haka ba wlh sai na sake korarka,Murtala ya tsorata yace a wanne daki ne? yace idan ka hauro sama to bedroom na karshe tana barin key a jiki Kawai kasan ya zaka yi,Murtala yace angama. Yana ta jira Mama ta fita unguwa dama gata da yawo amma Shuru bata fito ba,sai Yamma Mama ta fito driver zai kaita Shopping,Murtala Yana ganin Mama ta dau wanka yace shegu kudi badan da kudi ba wannan in a Kauye ne wallahi baza ta ganu ba fuska kamar ta Kura,ko matata Lawisa ta linkata kyau sau goma,tana Shiga mota ta bar gidan Murtala sai ya fada cikin part din Mama ya haura sama da sauri Yana duba room din sai ya hango na karshe da key a jiki sabo da Kar Fauzan ya bude ta ciki shi yasa ta wani bar key a jiki,Murtala Yana zuwa ya murda key ya bude Fauzan wani kamshi ya biki murtala Fauzan an Sha wanka sanye da wata jallabiyya sky, yayi kyau ana bude shi ya fito waje da sauri ya rufe kofar ya kalli Murtala yace muje,Suka fito Fauzan sai uban sauri yake zubawa kamar zai tashi sama,Murtala yace Alhaji kaga na maka rana dan Allah ka maidani gidanka aiki kudin albashi na yafi yawa,yace sai munyi shawara da Jannat,Jikin Murtala yayi wani sanyi yasan Jannat baza ta bari ba shi tsoro ma take bashi irin dukan da ya Sha a hannunsu. Kallon Fauzan yake yanda yake uban sauri Murtala ya saki dariya yace Kinga ta kanki Jannatu ga zaki nan na Sako shi,ya sake tuntsirewa da dariya yace sai kace an saki Zaki Yana Jin yunwa Amarya ba Wasa ba yau tsuliya zata ci ubanta ya juya ya koma wajen aikinsa Yana cewa badan Fauzan yayi wuf da yarinyar nan ba da tuni na samu garabasa amma shu'umi ya rigani ba komai rayuwa ce sai na kulla Masa tsiya Jannat tana kitchen tana girka abincin dare kamshi ya ciki part din gashi ya Sha gyara,Door Bell taji tayi Kara fitowa tayi ba tare da ta leka ba ta bude kofar Kawai taga Fauzan bata ko kawo a ka ba. Ihun murna ta saki kadan cike da salo Murmushi ya saki ya tsaya Yana Kare Mata kallo karshen kyau ta zuba Shi,fari tayi da idanuwanta tare da lumshesu,I'm sorry ya furta tare da karasawa inda take tsaye ya rungumeta habarsa ya daura a kafadarta Yana shakar kamshinta ya furta kiyi hakuri wifey,karka damu amma meke faruwa ne ko Mama ce? Kai ya daga Mata tare da rike hips dinta da hannaye biyu,kunyarsa ta hanata sukuni wai Fauzan ta aura ikon Allah tunaninta ya katse mata yanda taji bakinta cikin nasa Yana tsotsa gani tayi duk ya rude idonsa ya canja kala girkina zai kone ta furta a hankali muryarta na rawa tare da jikinta gaba daya Kissing nata yaci gaba da yi a nutse cike da wayewa A wani yanayi ta tsinci kanta me dadi muryarta tana rawa tace Zan duba girkin hannayensa ya sarkafo ta cikinta ya koma ta bayanta Suka shiga kitchen din a haka sauri takeyi gashi ya manne da jikinta tana juya miyar jajjagen da take yi ya Miko tafin hannunsa ta kasan hannayenta yace dandana min,Dariya tayi tace dan Allah ka tsaya nayi sauri na gama,Kinga Allah ne ya kubutar dani daga hannun Mama tayi kidnapping dina,au Kidnapping dinka tayi ya furta kwarai kuwa ai kulleni tayi a wani room sai dai ta kawo min abinci naci nasha nayi wanka sai Sallah shike nan,Ina tunanin ko Ina kayi ganin Mama ko damuwa bata Yi ba shi yasa nasan kana lafiya hankali na ya kwanta. Kawu fa ya dauke Mummy a wancan Hospital din shima dai yace ba zuwa ziyara ganinta,Allah ya bawa Mummy na lafiya ta furta tana Shirin sakin kuka,yace karki kuka please Inshaallah zata warke,to ta furta idonta ya kawo ruwa Girkin ta gama tare da dawowa Palo yace karki kai min Dining ni cin abinci a dining bai dameni ba,a Palo ta jera komai Suka zauna a Saman center carpet,abinci a baki ya shiga bata a nutse suna labari sai faman kunya take ji yace har yanzu kin kasa sakewa dani, cike da shagwaba tace ba Kaine ka fito min a Abbakati ba,Dariya yayi yace ko dadi sunan baiyi ba,Jannat tace wlh kaima sai kace wani Murtala,yace shine fa na gani Nima,ai shine ya bude ni a dakin da Mama ta kulleni Tsohon munafukin kenan kasan fa lokacin da ya Kai kararka wajen su Mama Wai kana kula karuwa sai gashi har gidanmu yazo tsabar munafunci har gidanmu ya sani Wanda ko Kai baka sani ba Jannat ta bawa Fauzan labarin Murtala yazo yace Yana sonta har gida,Jannat tace ai naso bai gudu ba wallahi a ranar da sai mun Masa fidiyar Danakuya,sabuwar kaciya zamuyi Masa da reza,Fauzan yace gwara da baku Masa ba ai azabar da yawa take haba....Wayar Jannat ce me tsada da Fauzan ya siya Mata tayi Kara tana dubawa taga Zee Da sauri ta daga Murmushi,Zee tace ranki ya dade Amarya ya muka ji Shuru ba a kiramu gashi ba,Jannat ta murmusa tare da furta to jaraba ba abinda ya faru,Zee da mamaki ta furta Jannat to wallahi ya kamata ki motsa fa,bayan motsin da nake Yi yanzu karewar Motsi har girki nayi wanne motsi Kuma kike so nayi,Dariya Zee tayi tace karki raina min hankali kin San fa me nake nufi,Jannat yi tayi kamar bata da gane ba,Ramcy ta karbi Wayar ta zagi Jannat tace to tunda baza ki gane ba bari muyi gwari gwari,Na gane na motsa ma cewar Jannat,Fauzan Wayar ya kwace tare da kashewa yace tashi muje bedroom kafin Mama ta shigo Jannat taji tsoro amma bata da zabi mikewa tayi hannaye ta daga sama tayi Mika kafin ma ta sauke hannayenta Fauzan yasa hannaye biyu tare da daura su saman gorar Madara ya wani dumbula,ba shiri Jannat bata gama hamma ba ta katse tare da sauke hannayenta kasa tana nokewa yace ai mu ba a Mika a kusa damu ba tare da munkai Hannu ba,Jannat ta fara shagwaba kamar zata narke duk ya wani zauce,rungumeta yayi Yana Jin kafafunsa baza su daukesa fadawa sukayi saman Sofa yaci gaba da kissing nata Yana laguda dukiyar Fulaninta duk ya zauce itama ta Fara karbar sakon sosai. Mama ce ta dawo daga shopping tana sauri ta koma ta kaiwa Fauzan abinci Kar ta shiga hakkinsa ta fito tana takawa dai dai Murtala ya leko da Kansa ta cikin dakinsa yace a hankali yanda ba me jinsa ya furta Oyoyo Oyoyo Kai Sanata kana rakarkashewa wlh wannan irin masakai haka kabaki guda,ya sake cewa Hajiyata zo Nan ga Murtala dan Almajiri azo a bani kabaki,Hajiya bata San me ake ba tana tafiyarta,Tazugensa ya kwance tuni Naja'atu ta mike Sai Kiran Mama yake a hankali Yana Hajiyata Mariya...Mariya...Mariya kizo agajin gaggawa ni irinku nake so Yan gayu,ganin wata me aiki tayo wajen ya maida Kansa dakinsa yayi mukus tana wucewa ya sake lekowa Yana cewa cikin rada Mariya ga tawa cable din Zan jona chaji fa bayan ta sanata a Kara da tawa a cikin adafton ki, sai da ya bari tayi nisa sosai ya fara Yi Mata dan Kira siiii....siii...Mariya ga Murtala naki a gefe idan Zaki bi Shortcut ki kirani da Tale babban gaye,Mama dai tuni ta Shige ciki bata dade ba ta fito a fusace tana huci tana kwalawa Murtala Kira Ya fito da gudu kamar mutumin arziki Yace Maman kowa gani ranki ya dade,Tsaki Mama taja tace Kai karka kawo min hauka Ina kaga Fauzan? Murtala dama gulma yake so yayi ya nuna part din Amarya Jannat yace kina fita ya dinga kwala min Kira ta window yace nazo na budesa ni ban San ke Kika rufe shi ba na bude Masa kofa sannan yace kece Kika Yi kidnapping dinsa Ni kaina naga rashin da cewa ka fadawa mahaifiyarka haka Wai ke Yar Kidnapping ce shine Yace shi a gaskiya a shekarar nan yake so matarsa ta haihu dan Allah na bude shi ya tafi can ai Kuwa ya tafi Ni dai nace Oga Allah ya raya ai zai wahala wata tara cif kiga ta Haihu sabo da yau da zafinsa ya tafi can Kinga kuwa sai ta Allah. Mama ce ta kwashe Murtala da Mari har sau biyu tace munafuki Dan ubanka ba Kai ka bude shi ba zaka Zo kana munafuncin dana Kai ka Isa ka hadani da Dan dana haifa Kuma wallahi last warning idan ka Kara furta min Maganar banza makamanciyar wannan wallahi sai na sallameka mutumin banza Kuma ka fito da mata ayi maka aure Naga Alamar shi kake bukata,Murtala yace Ni Hajiya Ina da matata da dana daya a Kauye yanzu me kudi nake Nema a birni wacce zata Yi wuff Dani komai tsufanta Matukar tana da kudi ba ruwana biyayya Zan Mata ta dinga ci dani, zuciyata ta mutu tuni Indai da kudi to Zan Zama mijin Hajiya tayi ta aikena Ina Hawa motocinta,Dariya ya bawa Mama tace Allah ya shiryeka ta wuce part din Fauzan a fusace,kofar palon ta Shiga knocking lokacin Fauzan yayi nisa Yana murza Jannat duk ta tsorata,Muryar Mama yaji tana cewa Fauzan fito ko na tsine maka,da Sauri Jannat ta janye jikinta tace dan Allah jeka karka ja min zagi,Kara kamo Jannat yayi ta fisge tace jeka dan Allah bana so ta zagar min iyayena gwara kaje please,Fauzan yace wlh sai na fadawa Affa yau ba gobe ba yaushe Zan zauna haka kofa ya Bude ya fito idonsa jajir daga shi sai 3qurt ko Riga babu yace gani ransa a bace,Mama a Nan taji tausayin danta ita bata son a haifo Mata irin tsiya da ta hakura tunda dan nata Yana son matarsa tace muje ko ya? Na barka a nan karka kusanceta ko na tafi da Kai? Yace yanda Kika gani duk yayi,muje to yace to ya koma ciki Jannat taji tausayinsa kayi Hakuri ta furta yace ba komai rigarsa ta dauka tare da Mika Masa ya zura ya fita. Murtala baki ya bude yace Kinga matar nan ta iya tasoshi a gaba ba tausayi wayyo Amarya an kasa Shan manta ya tintsire da dariya yace har da wani Shan gyara ana walwali an tara ruwa ana jiran oga ya zunduma cikin tafki to gashi an hana ya kece da dariyar mugunta harda gwada Maganar Jannat tana wani My Husband. Jannat Zama tayi ta zuba tagumi ta rasa wanne tunani ma zatayi akan abin,Fauzan kuwa Yana Shiga yaga Daddy ya dawo a ransa yace Alhmdllh ya dawo daga Lagos din zan Kai Kara,Sannu da zuwa ya Masa ya zauna suna ta Hira Mama tana zaune ta kasa ta tsare bata so Fauzan ya fadawa Daddy abinda take Masa Shi Kuma bai da niyyar fada ma Hajiya Talatu ce ta shiga part din Anne tace Anne ya kamata muje muga kwaf fa,Anne tana ballar goro tace yo ai ya Zama dole muje yarinya ta samu daula a banza,ai kece idan nace muje sai ki canja rana,Anne tana tauna goro an Sha gogoro tace ai ni Allah Daya zance Miki ki yarda karamar magana gaba na bata yanzu mu tafi da yamma dan ubanta ita kadai take son aure Nima da Zan samu matashi wallahi kudi Zan kashe Masa sosai na aureshi,ai ba wuce aure nayi ba,Talatu a ranta tace ai gwara ma kiyi auren ki bar min gida na shana,a fili tace ai yanzu matasa irinku suke nema Ido rufe Kuma ke ai da kwarinki wa zai ce ke Kika haifi baban Umar,Anne tace Allah Yar Nan? da gaske baki kalli kanki bane ai karki damu za a samo miji shirya anjima mu tafi,Anne tace an gama. Yamma nayi Suka ci uban wanka Anne baka Isa kace itace kakar Jannat ba sabo da Allah ya bata tsufa me kyau ga kudi ga abinci me kyau ga gyara sabo da ita bata yarda ta tsufa ba har jambaki sawa take ta zana gira duk abin zamani tana yinsa. Suna Isa gidan da wata arniyar Mota Driver ya kaisu har ciki ya shiga da su,Murtala anga masu kudi har rawar jiki yake ya tafi da sauri,Anne ta kalli Murtala tace yanzu Dan Allah Kamar wannan idan na kashe Masa kudi ai nayi dace kalleshi matashi dan Fulani gashi Dan gajere me kyan sura faffada dashi sak Kamarsu daya da Baban Kabiru tsohon mijina uban dana Sanda Yana yaro,Yana min Kama da Malam Adamu tsohon mijina Talatu tace to ko da shi za ayi? Hajiya Anne tace idan zai yarda me zai hana, kece me kuruciya ki San ya zakiyi ki jawo min shi ko Mene Zan kashe masa,sai da Suka gama maganganunsu, Talatu so take Anne ta bar Mata gida a ranta. Fitowa sukayi suna gadara,Mama ta leko ta window taga sune Fitowa tayi har waje amma ko iskar data kawota basu kalla ba Suka ce da Murtala Kai nuna Mana bangaren Yar mu,Murtala jiki na rawa ya kaisu har can Yana kallon Talatu Yana zare Ido ta birge shi Fara da ita ga gayu,Talatu Tsaki taja tace Kai mene kake kallona haka? Murtala yace a'a ni Iya nake kallo tayi kyau Kamar ba tsohuwa ba,Talatu a ranta tace mun samu dama,sai tace ko kana sonta ne? Murtala ya zaro Ido yace anya Kuwa akwai tafkin da Zan Yi iyo da ninkaya? Anne tace Kai irinmu munfi Yara mun San ta Kan duniya Karrr muke,Murtala a ransa sai mamaki yake wannan mutanen ba kananan Yan Iska bane har biye Masa sukeyi dole Jannat ta Zama karuwa ashe har Iyayen nata haka suke, a fili yace duk abinda Kika ce ai shi za ayi,Anne ta zaro kati ta mikawa Murtala yace gashi in kaga nayi maka kazo gidana Zan aureka,Murtala jiki na rawa ya karbi Kati yace Iya ke Zaki aureni ma ba nine Zan aureki ba? to waye me kudin? ai kaga Ni Zan aureka, Murtala Shuru yayi Yana Maganar zuci yace wannan sun Sha kaina, har bangaren Jannat ya rakasu yace ku shiga Nan ne Anne tace Kai Dan wanne gari ne? Yace ai sadaka Yalla ne Ni daga Yankin Libiya muke, Kai karka raina Mana hankali,to kawai Murtala ya furta nan ya koma bakin aiki,Mama ta koma ciki tana Fushi tace wallahi Ni da gidana ba wata shegiya da za a kawo danginta su Raina min hankali sai na koreta gidansu,Fauzan Yana ji ta hanashi fita yace ko na ce ta koma gidansu to? Dariya ya bawa Mama tasan Sarai me yake nufi wato ya dauketa ya kaita gidansa suyi ta Shan love abinsu Tasa keyar Fauzan tayi gaba tace muje ga iyayenta can sunzo zasu Mana wulakanci bari muje na gama da su,Fauzan ya kalli Mama Kawai Suka tafi yace bafa iyayenta bane Mama baza ki gane ba wallahi Jannat mutuniyar kirki ce Mama,Mama tace sai ka bari wani time na gani da kaina tukun Ni Kuma nayi Alkawari Zan baka matarka ka kyale na gani tukun har na gamsu,Fauzan a hankali yace to tunda dai zaki bani ita ba matsala tace yawwa ka kyaleni Fauzan bafa kaunarka ne bana Yi ba ka bari kaji kaci gaba da Zama a part Dina Ni Kuma Ina gama tantancewa Zan baka abarka,to ya furta Yana murna harda cewa Mama Kin San dai Ina sonta,uhmm na sani ai shi yasa ma nake daga Mata kafa,a hakan kin daga Mata kafa kenan? Ae mana ko na sake matse lamba? a'a dan Allah Mama,tace to karka sake ka tsallake dokata to Kawai yace Suka karasa ciki. Su Talatu kuwa suna shiga ciki Jannat taga sune ko kallonsu bata Yi ba tashi tayi tare da haurawa sama ta barsu a nan suna mamakin irin kallon wulakancin da Jannat ta musu taja Tsaki tayi sama,Anne tace lallai Jannat ta shigo gidan daula Ashe masu kudi ne zata ci ubanta sai mun dauki mataki,Talatu tace zamu kulla Mata tuggu Kuwa, Mamace ta shigo tare da Fauzan Anne ta tabe baki,Talatu ta kalli Mama tare da dauke Kai can gefe taja uban tsaki tace ya akayi ne tsohuwar Banza yarinya ma baza ki bari ta zauna a gidanta ita kadai ba sai kin kawota gidanki tayi Miki bauta ai ta fada Mana komai zaluntarta kike Yi,sabo da su Kullawa Jannat sharri sabo da Mama ta yarda Jannat ce ta fada musu,Mama ta kallesu tace to Sannu Iyayen banza ai mun San komai ku ba iyayenta bane,sabo da bakin hali har jikanki Kika kashe tsohuwar banza,Uwarta kune kuka sata a halin rashin lafiya munafukai,Talatu ta mike tace ke wallahi ki kiyaye mu Kuma mu aure bada yawunmu akayi ba sabo da haka kisa danki ya sakar Mana yarmu. Mama tace idan ku Jahilai ne mu ba Jahilai bane,Fauzan ganin haka sai ya sulale ya haura sama wajen Jannat ya barsu da Mama suna ta cacar baki,Yana shiga ya sawa kofa key yace suna can suna ta yi, Jannat tana tsoro tace karfa su daki Mama yace Maman ce zata daku ai Kuwa yau da sun tafi da karaya gida,Anne ce tace tashi mu wuce Suka fita,Mama sabo da masifa ta manta tare da Fauzan suke ta fice itama,Talatu kuwa mota suka Shige abinsu sai gida. Fauzan kallon Jannat yakeyi a nutse wacce zata Shiga wanka daure da guntun towel jikinta fari kal sai sheki takeyi tana walwali mulmul da ita,tana kusa da bed takowa yayi har gabanta gashinta ya gyara Mata duk tsayinta sai ta dawo Yar gujil a kansa,kwarjininsa da kunyarsa ta rufe ta duk ta rasa inda zata sa kanta hannunsa yasa ta bayan wuyanta tare da matso da ita gabansa,towel din ta ta dafe da sauri gudun Kar ya Fadi dama gashi guntu,kissing dinta ya fara a hankali yana shafa wuyanta da kafadunta a hankali,Ido ta lumshe sabo da dadin da take ji har kwakwalwarta bata san sanda ta rungume shi a jikinta sosai tana maida Masa da martani har da dage kafafu,a hankali Yana bin wuyanta hannunsa yake sawa a hankali Kamar zai kwance towel din sai ya fasa,har ta matsu ma ya warware towel din amma yaki sake haukace masa tayi Yana murzata kamar me Hannayensa ya maida saman Mazaunanta Yana laguda su sai kara zauce masa take a hankali ya janye towel din ya Fadi kasa hannayensa ya daura saman na shanunta Wanda suke manya mulmul a tsaye,bakinsa ya Kai Yana lasarsu Yana murzasu a hankali,Jannat ta manta Ina take har ya samu ya turata saman bed suka fada ya haye samanta shi Kam Yana furta nothing compares to you ko ta Ina lasar Mata jiki yake, jikinsa yana wani uban rawa da kyar muryarsa ke fita Wani lokacin ma hakura yake da magana da kyar ya furta,My wife kisa naji dadi kafin Mama tazo relax ba yau zamuyi ba nafiso nayi Muna cikin nutsuwa, Jannat tace okay ta kwantar da hankalinta,ya sake furta ki min please,Jannat ta tuno hudubar su Ramcy ta fara lasar kirjin Fauzan tana Masa abubuwa masu wuyar fassarawa Fauzan ya sake susucewa sai kace wani Zaki,a hankali ya gangara dausayi Jannat wani shidewa tayi,niima sosai ta sake bude Masa cinyoyi Wanda ya dauki Hankalin Fauzan sosai ba tare da ya shirya ba yace Uhm...uhm...uhm....Rashana...Kunya ta Kama Jannat ta Kama dariya sama sama yace Allah ai kece Rashanatu wannan irin rashasha haka,ya kurawa Dausayi Ido yace ahh lallai na dace fari kwal harda tawadar Allah,Jannat kasa kallonsa tayi sai da ta kulle idonta sannan tace Mama fa ka kafe abu da Ido haka, ci gaba yayi da abinda yake Mata ta Zama kwarkwar gaba Daya sai ihun sweet take Masa ta tana bankaro Masa kirji,a hankali ya fara Neman hanya bazai iya jira ba,Jannat ta San me zaiyi bata hana ba,zafi ta fara ji da wani uban radadi ya kasa shiga sai da kyar ba karamin wahala yasha ba,sai yau ya tabbatar Virgin ce da gaske ba karya ba,wani farin ciki da kaunarta ta sake Kama shi kamar ya cinyeta haka yake ji,Jannat iya dauriya tayi dan hawaye tayi kadan,Dake sabo ne yau ya fara bai dade da yawa ba ya samu gamsuwa sosai bakinta yaci gaba da tsotsa kafin ya kwanta a gefenta Yana hucewa. Lallashinta yayi sannan ya dauketa Suka shiga bayi tace nidai ka fita zanyi Ni kadai,fita yayi sannan ta samu ta gasa kanta sosai da ruwan zafi me gishiri a ciki sannan tayi wanka tare da tsarkake jikinta ta dauro Alwalar sabo da magrib tayi. Daya Room din shima ya Shiga yaje yayi wanka ya tsarkake jikinsa ya dawo room din lokacin tana goge gashinta da towel a gabanta ya tsaya daga shi sai towel daure a kugunsa ya karbi towel din ya fara goge Mata gashi Yana karewa fuskarta kallo Pink lips dinta ya tsurawa Ido ya matso da fuskarsa da Niyyar kissing din dan towel din taja tare da rufe fuskarta tana dariya baya ta juya masa,jikinsa ya manna da nata tare da rungumeta da Hannu daya yabi ta kirjinta ya harda dora shi a gorar Madara ya kwantar da Kansa a dokin wuyanta knocking Suka ji Mama tana kwala masa kira cike da masifa tace Allah yasa bata Kama mu ba,Fauzan yace ai wannan ibada ce sunna ce Allah da Kansa ke tsare masu aure ba a kamasu amma kwarto Kam tuni za a Kama shi,Jallabiyarsa ta dakko wacce cikin kayansa da aka kawo ta Mika Masa tare da taimaka Masa ya saka,har 3qurt kyale Wanda ka cire Zan wanke jeka Kawai Har zai tafi Jannat ta riko hannunsa tace tsaya doguwar Riga Yar kanti me kyau ta saka ta shirya sosai ba tare data daura dankwali ba gashin a jike da gani yasha ruwa,da kyar take iya tafiya Amma tace zauna Ina zuwa Fauzan yace Alright,fita tayi tana tafiya tana yatsina fuska tana dingishi har da Kari tana wash....sai ta tsaya ta yarfe Hannu sannan ta karaso gaban Mama,Mama baki bude take kallon Jannat,Mama ranta yayi bakikirin da gani kasan me akayi dama ita Jannat burinta kenan,a kasa ta durkusa tana cije lebe tare da furta Ina yini Mama,Yana gidan biki Yar arna dalla tashi ki bani waje,Mikewa Jannat tayi tace wanka yake yanzu zai fito kiyi hakuri wankan ne ya Kama,Mama ji tayi kamar zuciyarta ta buga sabo da bacin rai yanzu Fauzan sai da ya hada jininsa da karuwa,Jannat ciki ta koma tace kaje yanzu to Tashi yayi ya fita Mama ta ganshi da sabon kaya ta tabbata wankan yayi Yana wani nishadi Jinsa yake Kamar ya tashi sama sabo farin ciki cikin murna Yana zuba Murmushi ya rungume Mama,tureshi Mama tayi yace I'm sorry muje ki sake kulle ni Mama zanyi Biyayya bazan sake fitowa ba,duk abinda Kika ce shi zanyi,Tsaki Mama taja ta furta sai kaje can ka karata na kulleka nayi me ta juya ta bar sashen tana masifa nidai Allah kiyaye na karbeta a surukata,Fauzan ya dinga dariya ya koma sama ya iske Jannat tana gyara bedroom din hanata yayi yace ki bari na dawo daga masallaci zanyi komai My Wife . Sallaya ta shimfida ya Mata kiss yace yau Zan kwana da matata naji dumin jikinta ya fice,a dawo lafiya Jannat ta furta. Hamida Kuwa Lele ya cika Alkawari ya biya musu aikin Hajji tare zasu tafi ,tana ta rokon Lele ya barta taje ganin gida yaki yarda Yau ma ya dawo daga Office yayi wanka yaci abinci ya huta ta fuskanci a cikin nishadi yake bai da damuwa yanzu ya kamata ta sake rokonsa ko zai barta,amma da a cikin wani bacin rai ta ganshi to Sam baza tayi Maganar ba Amma Yana cikin yanayin nishadi yau,Kallon ball yake tayi matashi tayi da cinyarsa Aslam Yana wurin Nanny gemunsa take shafawa tana Wasa da shi ta lankwashe murya cike da salo ta fara yabon Lele,Lelen Pipi ba tare da ya kalleta ba yace Ina jinki, I love you,you are such a nice person,Allah ya Kara buda maka yanda kake kula damu duk yanayin aikinka bai hanaka bamu time dinka ba ni da Aslam,Kai na daban ne,nafi ko wacce mace sa'ar dacen Miji,gashi bangaren Hidima haka ake ta min ita baji ba gani banda damuwar komai,Nabeel yaji yabo har wani Jin dadi yake ya gyara Mata kwanciyarta a jikinsa Yana shafa gashinta ya Mata wata rada Wai I need you badly tace me too gama kallon sai muje mu chaskale, dariya ya saki kadan,tace yaushe zanje Adamawan ne? Nan take yace ki shirya weekend sai kije amma two days Kawai ba Maganar 1week hakan ma na gode Allah ya Kara maka lafiya da tsawon rai. Kallon ya kashe ya dauki Pipi Kamar wata jaririya Suka wuce bedroom. Murtala tsabar naci washe gari ya tafi gidan Anne,shi murna yake Anne zata aure shi,yace lallai Murtala kwana Nan zaka kalli tsuliyar tsohuwa yanzu nasan wajen duk yayi yaushi ya zanyi haka Zan jona Chaji a cikin adafton Iya,dama wata Iya Ina zata Yi maiko,Haka Nan zata bude min Adaftor gayau da gani wani dan muyot ne,wannan idan Ina sex din ma wani ihun Dadi zata iya Ihun Iya sai dai kaji Kamar kukan mage tana rashin lafiya Yana ta maganganunsa Kamar Yana kunkuni har me Taxi ya sauke shi kofar gidan Iya. A bakin gate ya tsaya tare da sa handkerchief ya goge shaddarsa wata koriya fatau da ita,ta goge katon takalminsa yace yawwa Iya tayi wuf dani cikin sauri Karin hularsa ya gyara sannan ya kwankwasa gate,Cikin Securities daya ya leko,Murtala yace Hey please ka fadawa Hajiya Anne kace Tale Babban Gaye ne yazo na gidan su Jannat ya Mika Masa card,Yana gani yace shigo Kawai ai wannan shine shedarka ta shiga,Murtala ya shiga gidan Yana yiwa Yan aiki kallon banza yace kwana nan abincinku ya kusa karewa a gidan Nan Zan kore ku a aiki a gidan nan,kina zare min Ido ya fadawa wata me wanki,har palon Anne lafiyayye aka yiwa Murtala iso Yana shiga ya zauna a saman kujera ta Alfarma tare da harde kafa Yana karkada kafa Yana kallon kowa dai dai. Tun kafin Anne ta fito ya dakawa wata Yar aiki tsawa yace dalla kawo min chivita ki hado da Lacasera me sanyi,jikar Anne ce ta shigo da gudu Tasha kana Nan Kaya kana ganinta kasan Yar Madara ce yarinya ce bata wuce 6yrs,tsawa Murtala ya buga Mata Dan ubanki baki iya gaisuwa ba kina ganin kakanki,Yarinyar bata da kunya tace uwarka shege ai Murtala fusata yayi ya cafko ta tare da tsinketa da Mari kamar ya Kama gardi,yarinya ta saki ihu ta fita a guje sai wajen babarta Talatu. Anne ce ta fito da gudu taji kukan jikarta tana uban waye ya dakar min jika Masu Sharhi ban San da me Zan gode muku ba, Allah ya saka da Alkhairi aci gaba da min sharhi AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 JANNAT Part 2. 106-110 Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page nawa ne ASMABAFFA🤣 Tana Fitowa taga Murtala ko kulashi bata Yi ba ta fara tambaya ya naji kukan Rumaisa waye ya taba ta,Murtala yace faduwa tayi ita daya,Anne Zama tayi suka gaisa sannan ta kalli Murtala suka hada Ido Murtala ya Mata fari da Ido,Anne tace sai kace mace,ai ke Kika ce kece Zaki aureni ya furta tare da danyin tafi Wanda ba shiri Anne ta Fara dariya,a ka'ida bai kamata ma na biyoki gida ba kece Zaki dinga zuwa zance wajena sabo da gudun shedan Kar ya Shiga tsakani wani abin ya afku Anne tace to yaushe za a sa ranar auren? Ki bari sai Nan da wata uku sabo da zanyi shirye shirye dan gyaran na amare nima nayi shi Anne tace ba matsala Tasa aka cikawa Murtala gabansa da kayan ciye ciye ya cire hularsa tare da ajiye ta gefe ya kwashi girki lafiyayye harda Santi yace da alama tsohon Hannu ne yayi girkin nan kece ko? Anne ta furta nice, Ni na sani haba dadin yayi yawa nasan sai ke Sai da ya gama Yana wanke hannunsa yace Zan tafi ni bani number ki,Anne ta karbi Number Murtala tare da kiransa Nan take yayi saving a wayarsa da Iyalle Kudi ta bashi dubu hamsim a envelope Murtala ya karba yace harda kudin zance to na gode Anne har da rakoshi compound sai ga danta Abban Jannat ya shugo dama Anne tace baza su fada masa zasu Yi shuru sai an daura zai sani Kar ya hana auren. Murtala bai San zancen ba Anne tace ga Babban dana shi kadai gareni, Murtala yace duk da ya Haifeni dole ya gaisar dani tunda kwana nan Zan Zama Babansa Anne tace ka rufamin asiri sai an daura zai sani in ba haka ba hanawa zaiyi Yana kashin ubansa,Tale yaji zai rasa kudi sai yace kice Kawai jikan kawarki ne ni,da sauri ya karasa suka gaisa da baban Jannat suna Kama Jannat sosai,Anne ce tace jikan kawata ce ta Kauye yazo Abuja Cirani shine ya kawo min ziyara zai dinga zuwa muna gaisawa,Abban Jannat yace Allah sarki to Allah ya taimaka ya zaro kudade masu yawa ya bawa Murtala yayi godiya ,Yana ganin Abba ya juya baya ya danyi nisa yanda bazai ji ba ya juyo ya kalli Anne tare furta kawo bakin Kinga mmmmuah Wai yayi kissing nata ta nesa,Anne harda Jin kunya. Fauzan bayan Mama ta juya ta tafi wajen Jannat dinsa ya koma cike da murna, Already ma ta fara gyara dakin ta canja bedsheet Yana shigowa ya yace a tsaya haka muyi Sallar Magriba, Hijab ta saka ta bi bayansa ya jasu Sallah sannan yace karki Yi girki bari na karbo wajen Mama, daukanta cak yayi tare da kwantar da ita a saman bed sannan ya fita,mikewa tayi tare dan shafa powder tare da lipgloss ta dawo Palo ta kunna tv tana kallon film Palo ya Shiga ya iske Mama tana kitchen tana shiryawa Daddy abinci a tray, yace Mama na'am ta ba tare da ta kalle shi ba,yace Abinci zaki...kafin ya karasa tace gashi nan ta nuna Masa wani basket hadadde ta shirya abinci a ciki tace dauki ga naku nan Yar Gold din taka ta nuna min na gani dauki ka tafi Kar isheni ,Fauzan ya rungume Mama yana mun gode Mama Ashe kin Fara sonta,dauki ka tafi kana sonta ya na iya jeka karka isheni dan Allah,Yana dariyar farin ciki ya dauka ya fita. Yana haurawa sama ya isketa a palo ya shigo da abincin shi yayi serving nasu ya zauna Yana bata a baki tana ci shima haka,tambayarta yayi Wai dazu me Kika cewa Mama ne? Labari ta bashi yace gashi Kuwa kin kwato Mana yanci ta fara hakura,dan Allah? Yace Zaki gani da idonki idan lokaci yayi,kirjinta yake kallo Wanda ba bra ko ya ta motsa sai na shanunta sun motsa,ya ebo abinci zai bata bai sani ba ya dora spoon din a saman hancinta,Dariya tayi hade da kunya spoon din ya ajiye a saman plate din ya kalleta itama haka suna kallon Zama cike da shauki da kauna,yace na taba? ba abinda Zan miki Kawai na dan latso su ko na dubu Daya ne a cikin Sadakina,ai dazu ka cinye sadakin naka Hannu yasa ya fara shafasu Yana lailayasu yanda yake so Jannat zafi ma suke Mata sabo da yanda dazu suka Sha wahala a hannunsa sai dan dan Shan yaji take tana wash hakan wani birgeshi takeyi Yana Kara Jin wani dadi na musamman, ganin zai shiga wani hali ya hakura ya ci gaba da bata abincin bai Gama bata ba ya koma yaci gaba laduga gorar Madara sai da ya gaji yaci gaba da bata abincin har Suka gama a haka,Alwala yayi ya Zo inda take a zaune ya duka yayi ruku'u a gabanta tare da zura Mata idonsa me Matukar kyau cikin sigar rada ya furta ranki ya dade a bani a izini Zan tafi masallaci Dariya ta saki tare da shafa gashinsa tace a dawo lfy to,Allah yasa ya furta ya sumbaceta a kumatunta sannan ya fita ,a gida tayi Sallah ta canja wanka tare da yin Shirin bacci cikin wata Riga ta Jan hankali,tana shafa turaruka ya shigo ta baya ya rungumeta Yana suna kallonsu ta mudubi hannayensa ya maida kirjinta Yana shafawa tana kallonsa taci gaba da abinda takeyi ribbon zata dauka ta juyo suna facing juna duk haka hannayensa ya zagaye cikinta a haka ta juyo tace zan dauka abu My Prince Ya murmusa tare da an min suna na Zama Dan gata ya fara kissing din lips dinta hannayensa suna cikin gashinta Yana shafawa a hankali,Jannat ta kwace bakinta tare da furta ribbon Zan dauka,bana so bar min Abuna haka,saman bed ya daura ta shima ya haura Suka shige bargo abinsu tana cewa wait wait Banda gaggawa ya haye kanta ba tare da ya sakar Mata nauyinsa ba sai da ya Gama murzata son ransa sannan ya tuna baiyi wanka ba ya mike ya shiga toilet ya dawo tare da fesa wanka ya saka boxers dinsa ya kwanta sannan ya janyota jikinsa ta rungumeshi suna facing juna Yana Wasa da gashinta suna hirar soyayyarsu har ya Fara Jin bacci yace muyi Adduar bacci sukayi sannan bacci ya kwashe su makale da juna. Pipin Lele ce ta tasa littafin aikin Hajji gaba tana karantawa ta kalli Lele dake zaune a saman Sofa ya dauki kafa daya ya dora Mata a kafada,mene haka ta dauke kafar ta fatalar da ita,a gadon bayanta ya sa kafar harda danna bayanta juyowa tayi suna kallon juna taci gaba da karatunta,kafarsa yasa a saman kirjinta Yana danna gorar Madara Yana murmushi,hararar Wasa ta aika Masa ta Saba da tsokanar Lele,Amma aikin hajjin tamattu'i zamuyi ko? Yes ya furta yafi sauki,Ina tafiya Ina labbakalla humma labbayk, Lele kaga ta kanka ai har a ka'aba sai na rokarwa dausayi Karin Dadi da lafiya,yawwa Indai wannan ne ki roko min Nima Zan tayaki dausayin matata Allah ya Kara Masa dadi,Nima Yar Naja'atu ta Allah ya Kara Mata lafiyar Hidima,tashi ki kawo min tea Zan Sha daga Nan mu Shiga daga ciki duk da period kike yi sai na rage zafi. Murtala tunda ya karbo kudin Anne yazo yayiwa Mama Sallama tace me aka Yi maka zaka ajiye aikinka? Murtala yace kawai ni da Kaina na Kori kaina da kaina Allah yayi min arziki naci gaba nafi karfin gadi,Mama ta tabe baki tare da cewa Ina abin yake Nawa ka tara? Kudi ai sirri ne naki na fada nawa ne,dama kin isheni da aikata zunubi kullum baza kisa hijab ba ko katon mayafi sai kuyi dinki damamme Kuna yawo cikin garadan ma'aikata ku a dole masu kudi da boko,babbar mace ta wani yada dan mayafi ta fice ko Kuma a cikin gida ga Yan aiki maza amma ko mayafi babu kuke yawo a cikin gida ku da yaranku,Ya ilahi ai sai ku jefa mu a wani Hali Yara kanana a samu wani ya musu fyade ya gudu sabo da kana Nan Kaya suke sawa suna abinda Suka ga dama musamman ma'aikatan gomnati gani suke wayewa ce, wata ma a cikin gidan bata sa dankwali ta rufe gashinta,gashi Nan dai Abu iri iri Ni bazan iya ba na sallami kaina Mama tayi Shuru tabbas magarnar Murtala haka ne Kuma ya kamata su gyara ga Jannata ita Indai zata fito to Inshaallah da hijab take fitowa compound ita da ake ganinta a karuwa ,Murtala sallama yayi Mata Mama ta Kara Masa kudin sallama ya fice da kayansa sai kauyensu. Yana zuwa can ya siyawa Lawisa kayan abinci iri iri ba karya Yana son Lawisa ko yaya ne Yana son matarsa baya barinta da yunwa,matarsa tace kudi ka samo haka? Kwarai kuwa bari na dawo ya sake fita a kauyen ya siyo zabi guda uku manya yace gashi ki gyara kiyi yanda Kika ga dama Ni gobe Zan wuce,Murtala akwai iya ciyar da iyali,Haka danginsa ya bisu ya gaisar dasu Yana Basu dari biyu wasu dari biyar iya samunsa washe gari ya tafi Abuja sai gidan Anne direct sabo da ta Masa alkawin bashi gidan Zame a can Bangaren Mama Kuwa har part din Jannat taje ta samu Fauzan da Jannat ta musu Nasiha sosai sannan tace anjima ka dauki matark ku koma gidankku ai komai ya Zama ready,ke Jannata ki hada komai naki driver zo ya kai,Allah ya bawa mahaifiyarki lafiya sannan Dan Allah a yafi juna na tabbatar ke ba yanda na zata bane na zauna nayi tunani da kaina ban kyauta ba komai Mama Jannat ta furta tana murna,Fauzan kuwa Kamar zaiyi tsalle haka yake ji harda godiya Yau bazan iya da yawa ba ga guntu nan AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 JANNAT Part 2 111-115 Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Masu Sharhi ayi Hakuri network ne yake bani matsala tun jiya Gashi tun 9pm zanyi posting amma maybe bazai Zo da wuri ba sabo da network. Page naku ne Ummi Manga 🥰 Hauwa Kasim Mk Hussein Firdausi Mrs Shugaba Maimuna Umar Hajiya Abou Maman Murtala Zakiyya Bello Sadiya Muhammad ~• A ranar Fauzan da Kansa ya tattara kayan Jannat duka komai nasu a gidan,Jannat waya ta Kira su Ramcy suje gidan su Kara gyara shi, a can Suka Iske Fauzan Yana jiransu ya bude musu gidan kasancewa ko me gadi babu,kayan ciki komai an canja an sake sababbi ya linka da haduwa lokacin da Jannat take zuwa komai sai da suka gyara shi yanda ya dace Suka sake kalkale gidan Yana wani daukan Ido,Fauzan fita yayi ya musu take away na abinci da kayan Sha,sai da Suka ci suka koshi sannan Suka ci gaba da gyara kitchen ma Suka shirya komai kayan abinci na store suka gyara,Fridge duk abinda ya dace sun zuba a ciki suka kunna turaren kamshi da su room freshner lungu da sako sannan Suka tafi Fauzan ya musu godiya harda kudade ya basu Yana cewa sai yaushe zaku Zo wajen Aminiyar taku? Merry tace weekend Inshaallah,yayi nisa gaskiya har yanzu baku zo ba fa baku kyauta Mata ba ai ba Amana sam dariya Suka yi suka ce zamu Zo ne,Allah ya kawo ku lafiya ya furta,yace dan Allah kuyi kokari ku daina sana'ar Nan ku tuba kuyi sure Kuma Yana ta musu Nasiha dai har suna godiya Suka wuce. Burin Fauzan su dinga zuwa wajen Jannat ya samu yayi ta Jan ra'ayinsu ko Allah zai sa su daina Jannat Kuwa Yana fita wanka tayi tare da cakarewa cikin gown ta atamfa me tsada lemon green ta yafa mayafi ta Shiga part din Mama,a Palo ta isketa tana zaune da mazan yaranta su Anwar da sallama ta shiga a kunyace sabo da yanda Suka amsa tare da zuba Mata idanuwa,a kasa ta durkusa tare da gaisar da Mama da sakin Fuska ta amsa Wanda yasa Jannat taji dadi a ranta,ta juya tare da gaida su Anwar Suma da fara'a cike da mutuntuwa Suka amsa,Mama tace zauna mana Jannat,kujera ta samu ta zauna tare da yin kasa da kanta,Anwar yace Amarya ba magana wannan Shuru haka bafa bakunta an Zama Daya kin shigo family ki saki jikinki Kinga da Hamida ce tazo da yanzu Muna ta zuba hira Muna Shan Dariya,Mama tayi dariya tace ai Pipin Lele gwana ce wajen surutu da abin dariya , Pipi ake ce Mata ko? Wannan Dan iskan suna Ina ta samo shi haka Wai Pipi Mama ta furta suna dariya har Jannat,tace ai akwai wani ma dana ji Shakira,ai da Hamida ce tazo to da tuni Kinga dangi ana ta zuwa har yaran kawu Ubaidu,Jannat ta murmusa,Jannat irin Fauzan ce magana Bata dameku ba ko?Mujaheed ya furta Jannat Murmushi tayi tace Nima Ina Yi ai, da mijinki ba da zaku ga Fauzan da matarsa da Kun San Yana sani yake kin magana cewar Mama dariya sukayi Fauzan ne ya shigo ya iske suna maganarsa ana Dariya Yana zuwa Jannat ya kalla yace Ina wayarki Ina ta kira na dawo bakya wajen,Wayar ta nuna Masa a hannunta ta Masa inkiya da Ido Wai Mama tana wajen,a fili yace to sabo da Mama sai ki fasa daga min waya sabo kunya ko bakuwa ce ke ki saki jiki, Madam tashi mu tafi an gama komai Mama tace Kai ka kiyayeni da fitsara yanzu da Rana zaka tafi da yarinya sai dare to, Fauzan Yana lallaba Mama yace Alright Allah ya kaimu yasan da yaya ma ta hakura Lele ne yace Pipi je ki shirya zamuje test inda akewa Masu tafiya aikin Hajji test in mace tana da ciki baza taje ba sabo da gudun samun matsala,Hamida ita tasan bata period take ba kwana biyu tsoro take ji Kar a Kara gano Mata ciki a hanata tafiya,shiryawa tayi cikin Abaya peach color, Yar kwalaba ta samo karama tace da Lele muje kayi min fitsarinka a ciki Dariya ya dinga Yi yace Hajajju na gane me zakiyi kawo,Karba yayi ta bishi toilet din ya mata fitsari a ciki ta rufe sannan ta wanke kwalabar suka fito cikin gashinta ta tura kwalaba Suka tafi. Suna zuwa aka dauki jininta tare da bata Yar kwalaba akace tayi fitsari ta karba ta shiga toilet din da aka tanada kwalabar su ta bude tare da juye Fitsarin Lele a ciki ta rufe ta jefa kwalabar a cikin shara ta kawo musu tasu ta bada,Nan take aka gwada mintuna kadan me gwaji tace kin tsallake rijiya da baya baki da komai,Bayan 1hr aka kawo result din gwajin jini duk lafiya ita da Lele sai Malaria da Typhoid da Hamida take da su,tace tun Ina Kauye Ina da typhoid dama sabo da Shan ruwan rijiya to ya Muka iya ai dole baza a rasa wani da cuta ba,Lele dai ance ba wata matsala, Hamida tace karya ne shima bazai rasa wata Yar matsala a makale da shi ba,Dariya suka Yi yace to ya zakiyi dani Allah ya bani,Likita yasa ya rubutawa Hamida magunguna sannan suka tafi,tsinken pt test ta siya a gida ta gwada ko tana da ciki taga bata da cikin komai sannan ta fara Shan magungunan da Lele ya siyo Mata. Tunda Yayan Affa ya dauki Mummyn Jannat daga asibiti ya maidata nasa ba wani Abu ma aka mata ba har yanzu gwaje gwaje akeyi kala kala amma komai na jikinta Normal,Yana ta tunanin a fitar da ita kasar waje ko a Mata na hausa sai suka ga haka kawai kullum ta samu lafiya,kullum aka je Sai aga tafi jiya lafiya,tun Bata iya tashi har tazo tana iya tashi da kanta ta zauna ga abinci tana ci sosai ba magani ba komai,sai ta fara Kumari,ganin haka likita sai ya bata wasu magungunan masu Kara lafiya da sa cin abinci sannan ya bata maganin da tsokar jikinta zata ciko da wuri tayi mulmul,ko sati bata yi tana Sha ba ta fara kiba ga cin abinci lafiyayye ga bacci,sai ta fara mikewa tsaye har tayi tafiya da kanta ana ta mamaki ana tayata murna,Kawu Ubaidu yayi ta mamakin ikon Allah in Allah yaso ka warke ko ba magani zaka warke Ana haka har tayi dan jiki mulmul gashi ba aikin wahala sai ci da sha da bacci, tayi Sallah tayi wanka,Kawu Ubaidu da Kansa ya siyo Mata dogayem riguna masu kyau kala biyar da duk kayan bukata har abinci ba irin na asibitin take ci ba shi yake siyo mata,in ya Shiga dubata sai su Dade suna Hira ya bata labarin Jannat dinta da Wanda ta aura Mummy sai Murna hankalinta ya kwanta bata da burin da ya wuce taga Jannat amma ta hana a gaya Mata sai ta warke sosai zata ganta,Ubaidu har matarsa da yaransa ya kawo Suka duba ta,Umma Hajiya Amatallah mace ce me Hakuri da tausayi kullum sai ta duba Mummyn Jannat sosai take kaunarta,tausayi take bata kullum tana hanyar dubata tana Kai Mata abinci,har kayan kwalliya body lotion turaruka da abubuwa na Mata duk ita ke Kai Mata kamar a gida haka take da akwatinta da kayanta komai a ciki Kawu Ubaidu da dare suna kwance tare da matarsa Umma yace Amatullah da ace zaki Amince nayi Niyyar auren Mummyn Jannat wato Asiya idan ta warware amma idan Kinga da matsala to a hakura, Amatullah ga addini da Ilimi tace haba abinda Allah ya halatta na Isa na Hana,Dan Allah karka Bari Allah yayi Fushi dani haka Kawai ma Kuna Kara aure bare ka ganta tayi maka Kuma ma ai taimako ne lada zaka samu tunda bata da kowa sauran dangin nata ma Arna ne baza suyi mu'amula da ita ba,mu musulmai idan bamu rungumi Yan uwanmu ba to me zamuyi ai bamu da amfani ma kenan. Ka duba halin data shiga a hannun tsohon mijinta ai ta cancanci a taimaka Mata wallahi na amince,nasan ba matar da zata so ayi Mata kishiya sai dole amma ni nayi tawakali Allah ne yace bare Asiya mace me hankali ka aureta,Alfarma daya nake nema,Ubaidu likita yace ta me? Umma tace ka raba Mana gida Ni ka barni a gidana itama ka bata wani gidan cikin gidajenka in ka min wannan ka gama min komai,Farin ciki ya Kama Doctor Ubaidu yace dama haka nayi niyya Allah ya Miki Albarka tace Ameen Allah ya baka ikon Yi Mana adalci yanda ka bata Naja'atu Nima a bani haka,Dariya ya dinga yi yace Nabeel dai wato duk ya baku Sara kowa yasan da Zaman Naja'atu,Nabeel anyi Dan banzan yaro ko a Ina ya samo sunan oho, Umma tace a mutuwar matarsa ta farko Muka ji labarin Washe gari Alhaji Ubaidu ya sanarwa da Affa Maganar aurensa dama sun San ta samu sauki,Affa yace yayi kyau gaskiya kayi taimako dama fa mune Muka cuci kanmu da akidar turawa Muka zauna da mata daya amma ba komai Allah ya sadamu Dana gidan Aljanna Ni dai bazan Kara ba tsohuwata ta isheni,tunda taimako ne Kuma kana sonta kayi,Ubaidu yace yo ai dama so ne ya jawo tausayin in ba so ba mu da likitoci zuciyar ta Gama kangarewa ba cutar da bamu gani ba sannan mutuwa har mun gaji da gani Ina son kayata har yanzu bata wuce 45yrs ba,Affa yace da sauranta aureta ka karasa da ita,Ubaidu yace ai uwargida fakewa nayi da taimako zanyi dama ita akwai Hakuri ba zafi amma gidan kowa daban Hakan yayi Allah ya Sanya Alkhairi amma idan Dan kishin ya motsa kace itace take sonka ga halin da take ciki zaka taimaka Mata fa sai ka Zama makaryaci a wani abun kafin a zauna lafiya cewar Affa Ubaidu yace ai gidan Nan dana gina a Kaduna uwar gida zan bawa kyauta sannan na bata abubuwa na Kara sanyaya Mata rai,ai wlh sai ta gane ka da can baka bata ba sai yanzu,yace to dai ai kyautatawa ce, hakane ai Amatullah tana da Hakuri Suna gama waya ya Kira Daddy shima ya fada Masa Suka Gama shawarwarinsu Kamar kullum Alhaji Ubaidu dakin da aka canjawa Asiya Mummy ya Shiga tana Zaune tayi kwalliya tayi wani kyau dama ita gata Fara Kamar Jannat ta ciko kibarta tana ta dawowa abinta,Abayace dark blue a jikinta ta yafa mayafin tana ganin likita ya shigo ta gyara mayafinta tare da gaisar da shi cike da kunya,Kwarjini yake mata tana Jin kunyarsa ita mamakinsa takeyi gashi dai a haka Babba amma kullum kashe kala yake sakamakon duk family dinsu haka suke kamar ba Yan kasar nan ba Kyakyawan dattijo ne dogo ga daukan wanka ba a barinsu a baya akwai wankan shadda masu tsada da yadika na Alfarma ga kamshi kullum a cikinsa yake,kallonta Alhaji Ubaidu yayi tayi Murmushi yace jiki kullum Yana ta kyau,tace hmm ko za a sallameni haka a gida sai na karasa warwarewa,a gidan wa Zaki zauna? Ya tambaya,tace Wajen 'yata Ina da kamarta a duniya ne,Ni sabo da na ganta ma nake so a sallameni,Yace da kin bari kin fi haka Muna komawa ki bata mamaki tayi murna sosai,baza ta iya Masa musu ba haka tace to Allah ya kaimu,a hankali tace ya sunanka Wai likita? Alhaji Ubaidu harda gyara sunan yace Ubaid mashaallah,ya kalleta yace zuwa nayi muyi wata magana,Ina jinka ta furta kanta a kasa ya zauna a wata kujera suna facing juna ya bata labarinsu kaf da asalinsu sannan yace idan ba damuwa Ina sonki kuma da gaske nakeyi aurenki zanyi idan kin amince,Mummy da sauri ta kalle shi tana mamaki duk irin kudinsu da yanda yake dattijon arziki yace zai aureta yanzu da me kudi sai me kudi basa auren talakawa,duk kyawun Yar talaka wasu masu kudin basa Aurenta sai dai dai su nemi Yar masu kudi duk muninta da rashin kyan halinta haka zasu aura Kuma ga dukkan alamu yafi baban Jannat hali na kirki,Mummy tace ba Wai bana sonka ba amma gaskiya Ina kunyar matarka yanda ta daukeni kamar Yar uwarta ko yau tazo dubani ba abinda bata kawo min karshe taji Zan auri mijinta ai ban kyauta ba gaskiya kayi hakuri bazan iya ba. Alhaji Ubaidu ya kalleta yace ai matar tawa da ita mukayi shawara ban fada Miki ba sai da yardarta da amincewarta sannan nazo Kuma duk Yan Uwana munyi shawara sun San komai bari na Kira Amatulla kiji daga bakinta,ya danno number Umma ya Kira tare da sawa a handsfree yace uwar gida gani ga Amarya tace sabo dake baza ta iya kishi dake ba Umma tayi Murmushi me sauti duk da cewar tana Jin kishi amma ta daure tace bata Wayar,Asiya ya mikawa Wayar ta amsa Suka gaisa Umma ta dinga kwantar Mata da hankali akan ta amince ba matsala,Bayan sun gama wayar yace to ya Kika ce? Tace Saura Jannat idan ta yarda,Yace haba zata yarda mana Jannat ai sai tafi kowa murna ganinki a dakin mijinki hankalinki kwance,duk wata kulawa zan baki Inshaallah yanzu Zaki San kinyi aure Allah ne ya hada mu Haka ya dinga tsara Mummy har ta amince amma sai ta karasa murmurewa an sallameta sannan zata tare,tunda Abu na manya ne daura aure ma Nan da Yan kwanaki za a daura ba wani jira. Murtala Kuwa Bayan ya sallami Kansa daga aiki gidan su Anne ya koma aka bashi part guda lafiyayye,an Masa dinkuna na Alfarma motoci Wanda yaga dama yake hawa sabo da Isa ma baya tuki Bai iya ba dama Kuma yace bazai koya ba yafi karfin tuki da Kansa duk inda zaije driver ke Kai shi Gashi yaki yarda a daura Masa aure da Anne kullum sai yace sai Nan da wata daya,Anne ta takurawa danta duk abinda Murtala yake so sai an masa,Murtala Yana samun kudi ya siyi katon fili a cikin Kano ya fara gini a birni gida yake na kirki Anne ganinta kudin shi zai sa Murtala ya aureta,matarsa ita yake wa bajinta Lawisa tayi kiba ta Kara kyau Kaya take sawa masu tsada abinci me Dadi suke ci sabo da duk iskancin Murtala nai da burin da ya wuce ya kyautatawa iyalinsa da Iyayensa da Yan Uwa,duk kauyen suna cin arzikin Murtala bare mahaifiyarsa yanda zai siyawa matarsa Kaya me tsada haka Mamansa ma zata sa ba ruwansa data tsufa a siya Mata me araha, Lawisa tace yanzu Inna ma me tsadar zaka siya Mata ta tsufa wa zata birge a duniya wa zai San ma ta saka,yanzu Abbunka ma haka ka dinka Masa shada masu tsada har kala biyar me suke nema a duniya,Murtala yace ke wlh akan wannan sai na kore ki gidanku duk yaro Yana jariri bai da hankali bai San ma kowa ba uwa komai tsadar Kaya bata kyashi ta siyawa danta tasan Kuma lalata su zaiyi da Wasa amma haka zata dinga kashe kudi a kansa, sai ita dan ta tsufa ace za a siya Mata me araha matarsa Kuma tasa me tsada matar taci Uwarta sai da Suka gama wahala dani Kika ganni na aureki sannan ko iyayenki ai Ina musu alheri daidai gwargwado me yasa baki ce su sun tsufa na daina ba sai iyayena. Lawisa tace kayi hakuri,karki sake min zancen Yan Uwa da iyayena Matukar ba shawara me kyau Zaki kawo ba,duk kudin da nake kawowa kin taba tambaya wacce sana'a nake Ina samu? halak ko Haram ba ruwanki burinki a kawo Miki Kawai in ma mafia nake ba asararki kinibabba da kunnenki Kamar na Tinkiya, Rannan na siyo kaji nace kiyi farfesun biyu namu na gida,Guda Uku ki soya ki kaiwa uwata shine Kika soya guda daya Kika Kai musu sauran Kika kaiwa uwarki,,Iyayen naki fin nawa sukayi ai nasan komai kyaleki nayi wallahi idan baki gyara ba sai na Miki kishiya ko na koreki duk sabo daku nake wannan wahalar Amma bakya gani Lawisa tasan ta aikata sai hakuri take bashi. Talatu ta matsu Murtala ya auri Anne su bar gidan a huta amma yaki sai yawo yake musu da hankali,Hajiya Talatu sai kudi makudai take dannawa Murtala itama akan ya amince ayi auren Yana ta hanya hanya,gajiya yayi yaga shifa ba da gaske yake ba Kar yazo ya dauki zunubi shi yanzu Haka Kawai shiriya tazo Masa yanda yaga duniya Yanzu ta rikice mutuwa Kawai ake tunda babban abokinsa da Suka taso tun suna Yara a Kauye daga idar da Sallah ya kwanta Yana jira a kawo Masa abinci sai gawarsa aka gani ashe ya mutu,wannan mutuwar ta girgiza Murtala har tasa yaga gwara ya gyara halayensa bai San a ya tasa mutuwar zata Zo ba. Abban Jannat ya samu ya fada Masa komai Anne tace lallai sai ya aureta,Abba yace Annen tawa ta auri kamarka? Murtala yace ae sai kudi suke ta bani Kai Naga abin yayi yawa shine nace bari na fada maka gaskiya Ni bazan iya ba sai kace Wanda aka tsine masa na auri Anne ai sai ace na zare,Ni dai gaskiya ka shiga Maganar sun bani kudi da yawa ma Zan fara kasuwanci ko na kawo maka?Abba ya furta ai Ni fada min da kayi ba karamin faranta min kayi ba wannan kudi ka rike an bar maka kyauta ka tafi abinka,Murtala dama karya yayi ba dawo da kudin zaiyi ba so yake kawai a bar Masa ai da sauri ya hada kayansa akwati uku duk masu tsada ya fito zai tafi Anne ta fito kenan taga Murtala tace Kai Ina zaka dan kundun ubanka ai ni da Kai mutu ka raba auren zobe zamuyi taci kwalar Murtala ta fara dirka Masa duka a gadon baya,Talatu ma data fito taji itama takaicin bai auri Anne sun bar Mata gida ba ta dakko wata muciya ta dinga timawa Murtala a ko Ina a jikinsa harda fasa Masa goshi Abba ne yazo ya fara fada yace sai Kun kashe shi mene haka? Duk ba akan Auren Anne ne da shi ba? Talatu tana huci tace Anne tace tana sonsa,Abba yace ahhh tunda Anne ta amince shike Nan duk abinda Anne take so Ina so Kai Murtala kayi Hakuri kwadayinka ya ja maka ko Nawa ne Zan baka ka aure ta,Ni duk abinda uwata ke so Ina so,Murtala yace Nima uwata haka take ko taka tafi tawa ne? Abba yace Kai taka danta talaka ne Ni tawa me kudi ne danta sabo da haka wallahi kwadayi da butulcin daka yiwa gidan da Suka baka Aiki Suka mutuntaka ba ruwana a maganarku,tabbas banso auren ba dan babu mutumin da zai yarda dattijuwa kamar Anne ta auri kamarka amma yanzu duniya ta canja tsofaffi ke aure irinku sabo da son kudi ba aka Anne aka fara ba tsofaffi da yawa sun auri Yara matasa masu lafiya sabo da kudi Ina so na rabu da uwata lafiya,Anne tace ai wallahi kana hana auren Nan Allah ya Isa nono na gwara ka kyalemu,Nan Abba baya son auren amma yace kayi hakuri Murtala Zan baka million biyar kaja jari,Nan take Murtala yace na yarda danmu,Allah maka Albarka Inshaallah Zan maye maka gurbin mahaifinka daka rasa Zan Zama uba na gari a wajenka,Talatu ta kyalkyale da dariya a duniya bata taba ganin Dan Iska irin Murtala ba,mutumim da baifi shekara talatin ba Abba da yake babban dattijo amma Wai Dansa,Anne tasa masu aiki Suka maida kaya,Murtala yace a bani million biyar dina a ciki a dauki dubu biyar sadakin Anne,nasan farashinta bazai wuce haka ba na biya da tsada Abba dai ba a son ransa ba Haka ya turawa Murtala kudi a accnt yayi tafiyarsa,Anne Sai washe baki take duk goro,Murtala ya kalleta ya fara wakar India Hangama Hangama hangaaaamaaa Wai bakin Anne. Abba Sam baya son auren sabo da Haka cikin dare ya Nemo manya a cikin Yan aikin gidansa shima Murtala yace auren sirri zaiyi bai son kowa nasa ya sani a cikin gidan aka dan hada mutane basu fi mutum goma ba a iya ma'aikata Murtala ya bada sadaki dubu ashirin da budurwar akuya,Masu Aiki suna ta boye dariyarsu ko su basu San Anne aka aura ba tunda iya sunanta na gaskiya Suka ji an fada Murtala ma sunansa na gaskiya,da dare aka daura aure sannan Murtala ya koma part dinsa Yana jiran Amarya Kamar ya fashe da kuka haka yake ji. Abba Kuwa bayan daura aure harda kukan bakin ciki akan abinda mahaifiyarsa ke Yi,Talatu ita murna take harda bashi shawara ya canjawa Anne gida yanda bazai dinga ganin Anne da yaro Yana Jin haushi ba,Kuma ya amince da hakan yace Nan da sati biyu zai maida Anne sabon gida ta zauna tare da mijinta Murtala. Anne Kuwa wanka tayi ta cakare cikin lace me tsada Kamar ba ita ba tayi kyau dai irin nasu na tsofaffi turare ta fesa tace yau Zan tuna da Malam ta fashe da kuka ta tuno tsohon mijinta tace Malam duk da kana kabari kayi hakuri nafi son Murtala da Kai dama auren Zumunci aka Mana ba wani sonka nakeyi ba Anne tayi sallama a hankali ita a dole me miji,Tace na iya shugowa? Murtala yace ke da Allah in Zaki shigo ki shigo Ni ba gane kusisinarki nakeyi ba,Anne tace Karka damu komai kayi kudi za a baka Murtala ya saki ransa yaji kudi ya mike tsaye Yana Murmushi ya daga Anne sama tare da yin Hajijiya da ita yaji ba nauyi ko kadan yace bargo duk ya zagwanye sai kace buhun auduga tace Kai dan ubanka ajiyeni Dan iskan yaro zaka karya ni,Murtala yace ki dai bi a hankali Aljannarki tana karkashin kafata dole ki min biyayya,jallabiyya ya saka yace ki bini muyi Sallah,Anne ta maka hijab tabi bayansa sukayi raka'a biyu da adduoi . Murtala Yana tashi ya fige Hijab din Anne Yana ta dariya a ransa,Shi Kansa kunyar Kansa yake ji,yasan Anne ko kyau batayi ba amma yace Wow wannan irin kyau Haka Darling sa'adatu, ta juyo da masifa baza ka dinga girmamani ba,danki ne ni matata fa kike,fatar hannun iya ya gani tayi yaushi damtsenta tsokar daban tayo kasa kashin daba fatar tana lage lage,Hannu yasa ya dinga lila fatar tana wani lage lage Riga zai cirewa Iya tace Kai Dan jakar ubanka da girmana zaka cire min riga,Murtala yace Dan me Kika aureni? Iya tace Kawai dan mu dinga hira ne wallahi ba wannan yasa ba,Murtala yace dake uwata ta tsine min ai billahillazi ko a baro ake turaki sai nayi dake dole ne,ki min zigidir Ina kallo Kuma yau sai kin min rawar Zanku nayi nishadi,Anne ta zaro Ido tace haba yaro Ina laifin ma Zigidir din ma,Murtala yace Ina son matata ta dinga min rawa yau har makossa dance sai kin min,Kuma sex na zamani har Sucking Kuma karki sake ki shafa min goro a jikin 'Yar baiwata kal kal Kika ganta,Yana fadin haka Murtala ya zare guntun wandonsa, Anne tace Subhannallahi ko ta Adamu bata Yi rabin taka ba,Murtala yace ai shi yasa take 'yar baiwa sabo da ita Lawisa bata iya tafiyar kwana Matukar Ina gari Masu sharhi akan Murtala Kuna sani nishadi🤣🤣 Aynah thanks AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 JANNAT Part 2 116-120 Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Mmn Meenat Ummi Manga Mrs Uwais Fulani Gal Didi Alhusna (mrs Udris) Mufeeda Murtala yace Anne karki damu ba akaina aka fara ba,ga samari nan tsofaffi suna ta aure su ki daina wani Jin kunya,Anne har ga Allah ita tace bata wuce Aure ba tana so, Murtala ya kalli Nonon Anne yace sai kace Harshe wannan Abu haka yayi yaushi yayi lakaf Kuma dan ziriri kucul da shi Allah kamar harshe,Anne ce ta furta ragowar Adamu ne,Murtala harda bata rai yace karki sake ambaton tsohon mijinki a gabana Ina kishinki in ba so kike kiga ranki ya baci ba, Anne farin ciki ya kamata tayi wani fari, Murtala ya kalli idanuwan Iya tana fari yace haduwa,Wayar Anne ce tayi Kara kirrrr ta daga jiki na rawa bata bari Murtala yaji Wayar ba sai ji yayi tace yanzu Kuwa ta kashe wayar,Kawai Murtala sai yaji hankalinsa bai kwanta da Wayar da Anne tayi ba,sai tace kwanta Mana a saman gadon,a tsorace ya kwanta ba komai a jikinsa Anne ma haka ko kunya ta kwanta a gefen Murtala tare da juyowa suna facing juna Murtala yace Dan Allah Yi can haka da bakin cin goron nan naki ni na fasa yau ba abinda Zanyi,Anne tace Kai yanzu da Saura na karka raina min hankali,ya kalli Dausayin Anne bakikirin duk ya bushe,Murtala ya kece da dariya yace wlh bada ni ba Ina ji Ina gani da hankali na bazan shiga nan ba, Anne ta koma jikin Murtala ta mamuke shi tace akwai ni Onga, yace Ongar Miya dama ai baza ki rasa ba ki matsa in Banda yaushi ba abinda nake ji bana sha'awarki Iya,yanzu wannan kabiru yasha ya girma to wlh bada ni ba Anne tace ka bani hakkina ko Kuma bazan yafe ba ai Allah Yana ganinka tunda Ni matarkace,to Abu bai Mike ba da me zanyi aikin Sahibar Lawisa bata yinki yanzu da Lawisa ta samu da tuni bata Mike ba,ke Kuwa gaki ma ba Kaya tace akai kasuwa bata sonki Anne tace sai ka cika min burina,bari na rera Miki Waka Murtala ya mike yana Waka da tafi Yar Iyalluwa Ina Zaki Zani kan tudu na Kai Gari daga Nan na kurgumo kabewa ta...Anne ta washe Baki,yace a bakacin hakkinki ya koma ya kwanta,gefe daya Kuma Anne tana ta faman nunawa Murtala dausayi,ta jawoshi da karfi,Murtala ya kwala ihu yaji tsohon Kashi. Lallaba Anne yayi ya kwanta shima,ta shammaceshi ta jawo Naja'atu ta Kai Dausayinta ihu Murtala ya kwala ya dirga kasa Yana birgima da ihu tare da kururuwar kuka,gaba Daya Naja'atu ta kone kamar an jonata a ruwan zafi. Alhaji Kabir baban Jannat Yana cikin wani dakinsa na sirri sai kudi wani gunki yake Fitowa da su ta baki bundle na dubu dubu farrrr,Dariya ya kece da ita tare da Kiran Anne a waya yace yaya? Yace Aiki yayi kyau ya mutu ne? Anne tace shegen nisan kwana gare shi gashi Yana ta murkususu. Murtala Naja'atunsa ta satile ta kone kamar an sata a cikin tafashashen ruwa,ihu yake da kururuwar neman agaji,Anne tace to ya kace uban kwadayi?ance a banza Zan aureka dukkan mu Film Muka makaTalatu ce Kawai Bata san me muke ba,amma kudi mukeyi da ku,ka godewa Allah wallah da ka sake ka sadu dani sai dai gawarka,sake ni Kuma,Murtala Yana kuka yace na sake ki saki Daya,na sake ki saki biyu Allah ya tsine muku na cikashe saki Ukun,Anne ta sheka dariya tace kuma Matukar ka fadawa wani sai dai gawarka,yace girmanki ya zube naga tsuliyarki da gashi, kudin da kaci kaje an baka da komai kyauta,Murtala yace Ni kuma sai Naga bayanku wayyo Lawisa an Miki asara,Anne ta Kira masu aiki tasa aka kwashi Murtala shi da akwatinansa a mota aka kaishi can wata unguwa me nisa wacce ba kowa suka jefar da shi tare da kayansa. Fauzan Yana Isa gidan Suka fito harda sakin ihun murna,Jannat tayi wata Hajijiya tace na shaki iskar Yanci Hannu ya ware ta Shiga ya rungumeta a hankali ta dago tare da zuba Masa kyawawan idanuwanta kissing dinta ya fara a hankali kamar me a compound ganin ba kowa,goyata yayi a bayansa tana dariya har Palo sannan ya ajiyeta saman 3seater yace anjima za a min Rashana?Dariya tayi tare da rufe fuskarta da tafin hannunta,muje Na kalli ko Ina gidan yayi kyau haka aka canja komai,Yace Affa ne yayi Miki,tace wow Zan Kira shi na Masa godiya,ya kamata. Yau Fauzan bai Bari tayi girki da kanta ba siyo musu yayi,Bayan sunyi Sallar Isha yace tare zasu Yi wanka,kamar Jannat zatayi kuka haka ya jata toilet tare da cire Mata kaya idonta ta rufe da hannayenta ji tayi Kawai Yana murza gorar madararta Yana wani Jin dadi. A hankali tace da Allah karka min me zafin sex din nan tana zubar da hawaye,yace I'm sorry Baby bazan iya hakura ba ni dai,na siyo Miki magunguna yanda raunin zai warke idan kina Sha Amma batun na hakura bai taso ba kin San yanda nake jinki a raina anki yin wankan sai murzata yake Yi son ransa Kuma tana karbar sakon sai dai tsoro,daukanta yayi tare da dawo da ita bedroom ya jata saman bed ya fara murzata yanda yaga dama,Dausayi ya fara tsotsar Mata tana Nishi tana cewa dama wannan akeyi kawai yafi dadi tana shafa sumarsa me yawa sosai yake Mata abubuwa masu wuyar fassarawa sai Nishi takeyi a haka ya samu ya shigeta a hankali yake bi da ita amma duk da Haka sai data Yi kukan zafi, sai da ya samu nutsuwa sannan Suka Yi wankan ya gasata sosai ta Sha magunguna sannan suka kwanta bacci makale da juna. Hamida anyi sallama da mutane Basu dade ba Jirginsu ya daga kasa me tsarki,Suna Umrah tazo dawafi ita da Lele Hannu cikin Hannu suna tafiya tayi Addua sosai ta roki abubuwa tazo Kan Lele tace Ya Allah ga Lelena harda daga hannun Lele Sama Allah ka gafarta Masa zunubansa ya rabashi wutar jahannama ka sashi a Aljanna firdausi etc tana ta yiwa Lelenta Addua ta duniya da lahira,bayan sun gama sun dawo masaukinsu sunyi wanka abinci Suka ci lafiyayye sannan Suka kwana a room din dake hotel din,Aslam a gida aka barshi da Madara da duk wani abinda ya kamata a bawa yaro Fara shafata yayi a hankali Yana bin sassan jikinta yana murzawa a hankali,Ido ta lumshe tana Jin dadin abin,ko da ya jo Kan Gorar Madara yaji sun Kara cukowa sosai Yana sani ya tsokaneta Kai Kai Yar gullisuwa haka suka dawo Yan mitsil,Dariya Hamida tayi tare da Dan dukansa a kirji tace komai abinka kasan har sunfi da ma,suna ta kashe juna da love ya shiga Yana faman hidima duk ya fita a hayyacinsa itama haka Yana zuba sambatu Kamar me,Hamida in banda dadi ba abinda take ji dadin ya Mata yawa,Lele ya furta Allah yasa mu samo Madina muna kiranta da munawwara,Hamida tace Makkah zamu sa mata sunan wayyo lelena.....Kar mu koma Nigeria...da Nan dacan duk daya ne ya furta Yana wani nishi pipi tace Lele yaga ni gida biyu,Mu samu ladanmu da yawa cewar Pipi, Haka suka kasance cikin nishadi bayan sun samu nutsuwa wanka Suka sheka sannan Hamida tace zanje gidan Alhazan Kaduna Ihsan tana can ita ta can ta biya,yace to karki dade ki jawo min bacci ni daya a dawo lafiya ki dawo da wuri ban koshi da ke ba,tace to ta fita sanye da abaya baka Dakin su Ihsan taje Yan Mata Mata irin su Hamida suka cika room din suna ta zuba hira harda masu siyar da abubuwa sosai,Hamida tace Kai kuyi can da wani man shafawa na Nigeria bayin Allah babu me kayan harka ne?aka nunawa Hamida kala kala ta siya ingantattu Yan saudiyya,tun a dakin tasha wasu,suna ta hirar duniya,Lele ya gaji da jira sai kiranta a waya yake Taki dagawa sai wurin 1am ta koma Hotel tana Shiga ya lullubeta da fada sai hakuri take bashi tayi Shirin bacci ta kwanta tare da furta to gani ya Isa haka,Tsaki yaja ya kwanta can gefe ga dan gado kwukwuf da shi,a jikinsa ta male Suka Fara farantawa juna Murtala tunda aka jefar dashi wayarsa ya jawo tare da Kiran matarsa Lawisa ya saki sabon kuka yace ku taho Abuja sahibarki ta kone,Kirji Lawisa ta dafe ta saki salati tace Sahibar? Garin yaya? Murtala Yana kuka yace idan kinzo kyaji wayyo...Yana kashe wayar abokansa ya Kira na Abuja Nan take suka Yi asibiti da shi,Akace dubu dari biyar zai biya,yace akwai a accnt ko million Nawa ne,Bank aka je yin duniya kudin suki cirewa,banki Suka Shiga aka duba accnt din fake Alert aka yiwa Murtala ba ko kwandala a ciki sai dubu biyar dinsa,Jin wannan zance Murtala ya fashe da kukan tausayin Kansa karshe sai filinsa da yake takama da shi aka siyar aka fara kashe Masa a kudin a asibiti,Murtala dana sani da nadama suka lullube shi in Banda kuka da Istigifari ba abinda yake yi. Washe Gari Lawisa tazo da komai nata na zaman jinya,tana dubawa taga su Sahiba an nadeta da bandage ta kumbura suntum,Lawisa ta fashe da kuka tace haka akayi maka da ita? Ashe haka abu ya faru,Murtala yace karki damu ai ta cikowa tsokar jikinta ta fara dawowa normal,Lawisa ta zauna tana jinyar Murtala, shegiyar Tsohuwa me bushashiyar tsuliya cewar Murtala. Fauzan soyayya suke bugawa sosai komai tare sukeyi,Jannat ta Saba da shi sosai,tun tana boyewa har ta dawo ta Saba,Fauzan Yana ji da ita yanda ya kamata. Fauzan Yana shafa gashin Jannat me santsi ya tambayeta Wai kawayenki mene labarinsu? Jannat tace Zan fada maka in mun samu time gobe,Allah ya nuna Mana ya furta tare da shigewa jikinta sosai Kawayen Jannat suna yawan zuwa suna ganin irin soyayayyar da Jannat suke bugawa suna sha'awar hakan,kowaccensu marmari takeyi tayi aure itama. Watan su Hamida daya Suka dawo Nigeria lokacin Murtala ya warke sumul kamar baiyi ba ana sallamarsa Kauye ya koma sai ya huta zai dawo Neman aikinsa sai labari yake bayarwa Yau ma Yana majalisa wani abokinsa yazo suna zaune yace Murtala ya jikin? Murtala yace haba ai na warke tuni amma kaga farko yanda ta suntume tayi suntumtum ,aka nadeta bandage,ta fara warkewa wallahi Ina fada muku sai kaikayi kaiyi ba dama na Sosa sai ta sake kumbura suntum,Lawisa Allah ya Mata Albarka Kai Yarinyar nan Yar mutunci na auro itace ke hanani sosawa,Allah ya Kara Mata tsawon rai suna ta dariya,Murtala yace tsohuwar Nan sai na Mata abinda baza ta manta ba a aduniya na gama tarasu zasu San sun taba Murtala Mummyn Jannat ce aka daura Aurenta da doctor ubaid Wanda ko Jannat bata sani ba amma Fauzan ya sani da dukkanin dangi,wajen Maman Fauzan aka kaita ta zauna anan har ta murmure kafin Nan ta tare a dakin mijinta. Bayan Sati biyu Murtala ya dawo Abuja direct gidan su Fauzan har part din Mama Yana zare Ido AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 JANNAT Part 2 121-125 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_ _*infection*_ _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_ Official By AsmaBaffa Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naku ne Ummuzahyed Bahijja2017 Mmn Wahida No Name Alhamdulillah A.H.H.N Kunderhamza Halimatussaadiyya Aisha Sa'adatu Tijjani Rukayya Attahiru Maman Arfat Mom aneesat Khadeey A kala Maman Kadi Maman Khalifa Princess Khadija Bilkisu Tambari Momcy Ummi Mrs Mukhtar Hadeeza Mukhtar Fatima Zarah Amina Adamu Usman Ummihauwa Hammads treats and spice. Murtala Yana shiga part din Mama ya hangota ta cakare ta dan fito tana Shan Iska ga Yan aiki suna ta sintiri maza baligai,Yana ganinta yayi sauri ya ritse idon Yana cewa babu ruwanki da ita Sahibar Lawisa ki dinga Jin tsoron Allah ki tsaya a iya kogon Lawisa,har ya karasa inda Mama take taga Murtala mamaki tayi,a gabanta ya zube ya fara gaisheta ta amsa tana cewa lafiya dai? Kasa yayi da murya kiwa Allah dan darajar Allah ki dawo dani bakin aikina na tuba,Kai da kace ka bar aiki har da cewa Muna sawa kana sha'awa muna yin shigar da Muka ga dama ta ya zan saurareka Murtala, Mama ba a son rai na ba asiri aka min,Aljani aka turo ya Shiga jikina nasha wahala a asibiti,Hajiya tace dama a asibiti ana maganin Aljanu? Murtana ya hada zufa yace ai likitan ne maye,maita gareshi magani kala biyu yake Yi Dana bature dana gargajiya shi yasa,to gashi ni dai na sa wani aikinka baka da guri amma ka koma gidan Fauzan ko zai baka,Murtala tsoro ya kamashi amma ya zaiyi haka ya tafi gidan Fauzan Yana zuwa gidan ya fara knocking Ango da Amarya suna ciki su kadai suna cin soyayya,girki takeyi Yana tayata aikin basu ji ba sam,Jannat tana juyowa ta shafa Masa flower a fuska tana dariya, goge min ko na shafa miki ruwan wanke Naman nan, kafada ta makale lokacin Murtala ya gaji da buga kofa ya zauna a bakin gate din ya zuba uban tagumi ga yunwa da kishirwa ta addabe shi tagumi ya zuba tare da furta Ina ganin ta duniya ni kam,Sannu Murtala Murtala kana ganin ta duniya ya furta tare da mikewa ya dauki dutse ya dan bubbuga nan ma Shuru lokacin ma abinci suke ci,Jannat tana saman cinyarsa suna kwasar girki ana kashe soyayya,Fauzan harda cewa gidan dadi duniya,Jannat tsoro take ji tasan zai wahala in ba ayi hidima ba bayan sun gama cin abinci,narai narai tayi zata Yi kuka,suna gama cin abinci tace zazzabi nake ji tana mikar karya da rawar sanyi,ya zaci da gaske takeyi duk ya rude har da dafe kirji babu lafiya garin Nan ko mutanen layin nan yau sai sun ba mutunci Amarya guda,Jannat dariyarta ta kunshe yace duk Wanda bai matsa ba ta kansa Zan bi da mota in yaso na shekara Ina azumi a gaban kujerar da take kwance ya durkusa tare da cewa ko ciki ne? Jannat tace haba jiya fa kayi sai yau shine har zanyi ciki To ni Ina Zan sani Mahaifa a jikinki bari na kawo Miki magunguna ya fice,gate ya bude zai je chemist yaga mutum a kwance sai da ya duba sosai yaga ai murtala ne, Fauzan yace kai me ya kawo ka Nan?ko matar tawa ka sake biyowa, Murtala durkusawa yayi yace dan Allah Oga kayi min rai Ulcer chronic ta kamani,haka na bar gidan nan ko kwallon shinkafa babu Lawisa ma Sai Hakuri na bata,Indai ka ajiye mace to fa dole ka dinga bada hakuri,Allah shike rike da mu dan girman Allah ka taimakeni ka maida Ni bakin aiki na ni wallahi na shiryu Zan gyara Haka Kawai ka dinga kallar min mata bada ni ba,Kai da ka sallami kanka kwarton banza,kafar Fauzan ya rike Yana rokonsa wlh na gyara abar ma yanzu a gimtse Mata kaifi sai da ta sutale ta kwailaye lawisan ma yanzu bata isarta bare har wasu su birgeni dan Allah Alhaji Fauzan wlh matar ma bazan kalleta ba babu ruwana kayi min rai,Murmushi Fauzan ya saki yace in ka sake wlh bazan sake ma Uzuri ba,Murtala harda bawa Fauzan Labarin Anne yace kwadayina ya kaini tambadaddiyar tsohuwa tsuliyarta ma dana gani Allah ya isa,Fauzan yace ka koma Kauye sai Nan da wata daya zaka dawo ka Fara aiki yanzu bama bukatar kowa Amarya gareni,idan zaka dawo ka taho da matarka ku zauna a boy's quarter ka daina kallon matan mutane, Yace to Alhaji a bani dan Abinci,dubu ashirin Fauzan ya bashi yace kaje ka siya kaci daga nan ka wuce Kauye,Murtala Yana ta godiya yace Kuma Anne ta shiga Uku taga ta kanta da Ni, Fauzan ya wuce ya bar Murtala na cewa wannan nonon nata me Kama da kunnen balama sai naje na tatse shege sai nayi sanadin tafiya dasu gidan yari Murtala wayarsa ya dakko tare da Kiran matarsa Lawisa tace hello Darling Tales,na'am ya amsa da sauri tare da cewa an dace an maida Ni bakin aikina amma yace tare zamu taho dake mu zauna a boy's quarter amma sai bayan wata daya tsaiwar darenki tayi amfani Lawisata me Sunan Laushi,ai daga Jin sunanki an San kin hadu,Lawisa tayi murmushin Jin Dadi cike da shagwaba ta furta Darling dama ni bana son kana tafiya kana barina ni kadai kishi nake Kar wata ta kwace min Kai,Murtala murna ta isheshi yace wayyo ni Ina kaunarki masoyiya,Lawisa tace Nima haka karka min kishiya kaji,Murtala yace nayi ma Mana dan ubana da me Zan riketa ke kadai kin isheni,Lawisa tayi dariya tare da cewa Ina Sahibata? Oh wire ?uwar shocking tana nan sumul yanzu Zan dauki hanya na dawo na jona miki ita ta Miki shocking kiyi ta vibration ke kadai,Allah ya kawo min Kai lafiya yace Ameen,harda Mata kiss ta waya,Ina gudan jinina?tace Saifullahi gashi Yana wasansa, mashaallah daga yau na maida shi Saif muma baza a dinga barinmu a baya ba Saif yawwa,Lawisa tace yafi dadi ma. Bayan ya kashe waya yayi wata dariya yace oh wai ni dan murtalan nan ace ni ake nunawa soyayya haka,ana min kallon banza a birni a wajen matata Kuwa Ni sarki ne Allah mun gode maka maza Muna da rabo,shi Kansa Fauzan watakil ma Lawisa tafi tasa iya love duk ya haukace akan mace sabun shiga an shiga sabuwar Fadama ya juya ya tafi,Abinci ya siya yaci ya koshi harda nama sannan ya hau motar Kano, da yamma ya sauka a birnin kano ya shiga Oasis yayiwa Lawisa siyayyar kayan makulashe da yawa sannan ya hau motar kauyensu. Jannat tana kwance a dole zazzabi takeyi tana ta rawar sanyin karya,Fauzan ya kawo Mata paracetamol yace Sha idan baki warke ba gobe sai mu tafi asibiti,dake paracetamol ne sai ta shanye biyu a ranta tace na Nigeria ba abin arziki yake ba maybe ma da flour ake yinshi,Fauzan Yana ta jinya amma shi Sam bai ga alamar zazzabi ba,wayo ya Mata yace ko dai sex ne ya jawo miki,Indai shine bazan sake Yi ba sai Next week Inshaallah Allah Nan take tace shine ma ai,yace to an daina sai Nan gaba ya dauki bargo me nauyi ya lullubeta,ba a dade ba ta hada uban zufa,tace zazzabin ya sauka,yace ko 10mnt ba ayi dashan magani ba kice ya sauka? Wannan maganin me kyau ne dama Kuma Ina da karfin jini Fauzan yayi dariya a ransa yace bari naje gida wajen Mama yanzu Zan dawo tace to harda wani nishi,Yana fita ta mike tare da kunna tv harda yin rawa a zaune,ba fita yayi ba ashe yana jikin window Yana kallonta,Kofar ya taba da sauri ta kashe tv din ta kwanta taci gaba da nishinta irin ta fara farfadowa,shigowa yayi yace mantuwa nayi ya haura sama ya fito ya wuce ta. Sai dare ya dawo lokacin yayi Sallar Isha ya isketa a bedroom taci wanka ta sa kayan bacci ta kwanta ta wani dafe Kai,Fauzan yace duk zazzabin ne? tace dazu ya sake dawowa Ina jinsa sama sama,Yana ai gani na dawo ni zanyi kasa kasan,kuka ta saki yace mene tace ba Kaine kace zaka Yi kasa ba,ya Zama farilla ai my wife ai yanzu ni naga guri kuma ba sauki ciwon arne Kuka ta saki Masa na shagwaba amma hakan bai sa ya kyaleta ba a kanta ya fara huce gajiya Yana binta da wani salo na musamman tana hawaye a haka ya samu shigarta ya fara hidimarsa kamar ba gobe,taci kuka ta godewa Allah tace har sau biyu fa kayi yau ta fashe da sabon kuka Jannat akwai raki Yana ta lallashi da kyar ya samu ta daina kukan yace na daina sai cikin dare lokacin kin murmure,ta barke da sabon kuka tana haba Dan Allah da dare fa kawai baka hakura ba,to gobe ai nayi Hakuri dai har gobe,Allah kashe ni zakayi ma Kawai Ni wajen su Zee Zan koma,har abada my life Muna tare Yana shafa jikinta taji Naja'atu ta sake mikewa tayi zumbur ta tashi tayi baya bata San tazo karshen gadon ba Kawai tayi baya ta fada tare da bige goshi da jikin gado kum,Saura kadan Fauzan yayi dariya,yace yanzu Yar wannan abar kike tsoro haka Wifey har da fasa goshi a kanta,tana mulmula goshin tace ai Kaine ka jawo,Hannu ya kawo zai mikar da ita tsaye tace karka tabani tana hawaye dole haka ya kyaleta ta mike da kanta ta Shige toilet,sai da taje bakin kofa ta Masa gwalo ta fada toilet dariya ya saki yace zamu hadu bashi Kika ci. Mummy tana gidan Mama tayi wata kiba haskenta ya dawo har yafi na baya ta zuba kyau abinta,gashi Mama ta tsaya Mata tana ta gyaran jiki abinka na manya a sirri akeyi Kamar basa Yi. Yau Alhaji Ubaidu zance zaizo wajen matarsa Yana zuwa ya Sha wanka n shadda komai fari,Mummy kuwa taci shadda me kyau cikin kayan lefenta da aka Mata akwati Takwas kamar budurwa,a palon Dan Uwansa ya zauna,Mummy da kanta ta shiryawa mijinta girki na musamman an cika gabansa da kayan ciye ciye,a nutse ta shigo tayi kyau shaddar Sky,Ido ya zuba Mata a ransa yace anyi kyau a nan Kam,sallama tayi Masa a kunyace ta zaune a kujerar dake facing dinsa ,gaisar dashi tayi cikin Ladabi ya amsa tare da cewa kinyi kyau,tace na gode tana Jin kunya,Murmushi ya saki tare da cewa wannan kunya Kam har yanzu taki karewa Murmushi tayi ta rasa me zata ce ma,yace shikenan idan kin tare ai Kya daina kunyar tawa dan Allah dawo Nan kusa da ni an daina wannan nifa mijinki ne yanzu,Mummy komawa tayi 2seater da yake zaune ta zauna tana kasa kasa da kai hannunta ya riko a hankali Yana kallon yatsunta masu kyau Yana Jin shauki hannunta ta zame a hankali,Ido ya tsura Mata Yana kallonta ta dago Suka hada Ido yace I love you,Fuskarta ta rufe da tafukan hannayenta tana Murmushi tare da Jin sabuwar kaunar Angon nata,Kiss ya mannawa hannunta,a hankali tace Jannat fa yaushe Zan ganta? gidan zamuje yau ai shi ya kawoni Mummy cike da farin cike ta mike tare da gyara mayafinta rungumeta yayi ba tare da shiri ba suna shakar kamshin juna. Jannat tana dining ta gama shirya Dinner Fauzan yasan da zuwansu,sanye take cikin Atamfa super brown and milk tayi kyau matuka,gidan ko Ina ya dauki kamshi ga na turare ga kamshin girkinta, mota taji Fauzan ya mike yace ga fa kawu Doctor da Amaryarsa ai na fada Miki dama yayi aure,Jannat tace Masha Allah gaskiya Family dinku sunyi a rayuwa Haka ake son masu ilimi amma wasu ga ilimin basa amfani da shi,Door bell Suka ji Fauzan ya mike tare da budewa Yana musu sannu da zuwa,Mummy tana ganinsa tasan 'yarta tayi dace,shiga sukayi tare da Zama,Jannat ce ta fito har ta durkusa a gaban Kawu bata gane Mummynta bace sai da ta amsa gaisuwar sannan ta gane ta dago kanta da sauri Jin irin muryar Mummy,kafeta tayi da Ido,Mummy ta saki Murmushi tace Jannat Mummy ce ta warke,Ihu Jannat ta saki sai da Suka tsorata jikin Mummy ta fada tare da rukunkumeta tana murna da kuka,Mummy ma Haka harda kukan farin ciki Fauzan da Doctor Kawai kallonsu sukeyi da sha'awa ba Wanda zai ce Mummy ce ta Haifi Jannat sai dai ace Yayar Jannat ce,sai da Suka gama Murnar Jannant tace Mummy ikon Allah tana bin Mummy da kallo tace kece Mummy how? Duk Jannat ta rude sai Fauzan ne ya kawo musu abinci da kayan sha, Doctor da Kansa ya bawa Jannat labarin komai har auren su,Jannat tana ta Murna tace Mummy Amarya ce ashe ni Zan kaiki dakin Miji,Kawu suna ta dariya mummy tace baki da hankali Jannat sa'arki ce ni ko dan kinga munyi Kai daya, Dariya sukayi Jannat tayi Serving nasu sai kallon Mummy takeyi,Mummy tace dan Allah ki daina kallona haka,kinyi kyau ne Mummy to naji,Fauzan shima da tsantsan Ladabi ya gaida su,Mummy tace mashaallah Ina godiya sosai,yace ba komai Mummy. Jannat plate daya ta zuba musu ita da Mummy Wai suci tare,Fauzan yace mene haka duk kin hanata sakat,Kawu yace kyaleta sun dade basu ga juna ba,sai da Mummy ta ci abinda zata iya sannan ta Mike Suka haura sama bedroom din Jannat,Jannat tace Mummy nasha wahala tace na sani tambaya nazo yi a Ina Kika dinga samun kudin da kike biya min a asibiti? Jannat bata boye ba ta fadawa Mummy komai,Mummy tace yanzu wannan kawayen naki Inshaallah bayan na tare zamu je nayi musu godiya sannan Zaki bamu labarinsu ko akwai wacce zamu iya tallafawa a ciki suyi aure su daina wannan sana'ar Addua tayi Aiki Allah ya tsare min ke Yanzu dai ke da mijin naki ba wata matsala? Jannat tace babu matsala sai...sa...sai...dai...Mummy....gashinta ta Sosa tace Ina Jin kunya.....amma...ni na kasa sabawa da shi Mummy kullum zafi,to ai baki dade ba Zaki Saba ne,ki daina Jin tsoro wannan tsoron shi zai sa kifi Shan wahala,Jakarta ta bude ta bata wasu magungunan matan tare da Mata bayaninsu tace karki min Wasa da magani da tsada na siye su in kin San baza ki Sha ba ki bani abu na, Murmushi Jannat tayi tana Jin kunya tace Ina so,Saura ki bari ya gani kuma nasan shirmenki,to ai bazan bari ba cewar Jannat,idan na nutsu zamu je gidan friends din naki,Jannat tace Allah ya kaimu tace sai kinzo mu wucewa zamuyi,tare Suka fito tana bata shawarwari yanda zata kula da kanta da mijinta. Suka fito Fauzan da Jannat har mota suka Raka Kawu likita da Mummy,baya driving da Kansa amma sabo da Amarya da Kansa ya tuka mota Amaryarsa na gefe, Shopping mall ya wuce da ita suna Shiga sai ga Uwar gida Amatullah tazo itama,ta hango mijinta da wata,ita Kuwa Sam baya fita unguwa da ita komai sai driver, ita Kuwa gashi ga Amarya suna nishadi sai kace saurayi da budurwa,gashi Asiya ta Kara uban kyau sai kishi ya motsa,mota ta koma fuuuu ta Shiga sai gida tace wlh na fasa a kawota gidan da nake a hadamu mu zauna Ina kallo duk abinda ya Mata Nima sai an min Bayan ya gama da Mummy a gidan Mama ya sauketa a haka ma da kyar ya iya tafiya gidansa,Yana komawa ya iske Uwar gida ta cika ta batse tana Fushi,lafiya ya tambaya tace ban sani ba wallahi bazan yarda ba ka dauketa ka kaita shopping Kuna wani rangaji Kuna soyewa tsofai tsofai da Kai ko kunya baka ji,yanzu idan yaranka Suka ganka fa,Ni wato na tsufa baka ta tawa sai wulakantani kakeyi to wallahi bazan yarda ba a kawo Nan gidan itama Kuma wallahi idan ka zalunceni bazan taba yafe maka ba. Hannunta ya rike zai lallasheta ta fisge hannunta tace ai naji har lefe kayi Mata akwatu takwas Ni Kuma ga tsinanniya ka bani wani gida a Kaduna,baki bude yake kallon Amatullah duk dadewarsu tare basu taba sa in sa haka ba,yace yanzu gidan dana baki kin San Nawa ne,lefe kwata kwata Nawa na kashe,Haba Uwar gida sarautar mata daga zanyi aure duk kin canja bayan da shawararki nayi,ai ban San haka zaka Fara nuna banbanci ba Kuma dama kwanaki ai kace na bawa Yafendo dubu dari ta rabawa Yan Uwa a Kauye dama bance ka bani ba to yanzu ka biyani kudi na Yace bani accnt dama bance ki bani kyauta ba Kuma bazan hadaku ba kowacce gidanta daban duk abinda zakiyi kiyi,Kuka Amatullah ta fashe da shi sosai tace dama ni nasan ka gaji dani ai a hannunka na tsufa munafuki, Ubaid yasan kishi ne bai damu ba ko kadan sai lallashinta ma da ya dinga Yi tana botsewa,ranar bata bari sun runtsa ba Sam Washe gari ma ko abinci bata bashi ba sai da Kansa yasa me aiki ta kawo Masa Wasa Wasa har aka kwashe kwana Uku Uwar gida ta hana sakewa Yana fita zata ce ya tafi wajen Asiya rashin mutunci kala kala take Masa tun Yana hakuri har ya gaza ya sanar da iyayenta a waya,Suka kirata Suka Mata tatas sannan ta dan rage,tana jin ance gobe Mummy zata tare kwana tayi tana uban kuka, Doctor Ubaid yana jinta tun Yana lallashinta har ya hakura ya rabu da ita. Gidan da ya tsara dan madaidaici me kyau yasha furniture Mama da kawayenta su biyu Suka Kai Mummy dakin mijinta da Yamma likis komai sun Mata 9pm Suka tafi gida aka bar Amarya ita daya,Jannat ce ta Kira Mummy tace Mummy Congratulations Allah ya bada zaman lafiya,Aure dai sai hakuri komai indai akace Ibadana to fa sai anyi hakuri,Mummy Yi nayi bari na bari banda....Mummy ce tace yaushe na Fara Wasa dake Jannat Sannu uwata ke Zaki min fada ki kiyaye ni fa na fada Miki Mummy ta kashe wayarta tana dariyar Jannat Wai ita zata ma fada ai tasan wasan Jannat ma dama Watarana suna Wasa da juna. Karar mota taji tasan angon ne,shi kadai ya shigo dauke da uban leda me kayan tande tande,Sannu da zuwa ta Masa sannan yace kiyi Alwala,tace Ina da Alwala Sallah ya ja su Nafeela yanda sunna ta koyar sannan ya bude Mata kayan kwalama kaji dakwa dakwa da su abinka da manya ci Suka yi sosai,Sannan Mummy ta shiga toilet tayi wanka tare da tsaftace bakinta again ta fito,sannan ya Shiga Yana binta da mayen kallo,wanka yayi shima da brush ya fito ya Iske Mummy har tayi shiri cikin wasu kayan bacci gown guntuwa purple surarta a bayyane,turare Kawai ya iya shafawa jikinsa ya kasa hakura ya rungume Mummy Yana daure da towel,Mummy an dade ba a hadu ba ai Yana Fara murzata ta susuce ta Shiga amsar sakon yanda ya kamata bata San ma Sanda take tayashi ba, Doctor sai sakin nufashi yake suna nishi abinka da tsohon Hannu an San Kan harka sai da yasa Mummy ta Zama wata zararriya ba abinda bata Masa na Jin Dadi ba shima haka sannan a hankali ya nemi Hanya yaji mashaallah a matse gam sai niima ke kwaranya Yana Shiga ta saki ihu na dadi da Dan zafi zafi sabo da an Dade sannan ga Kuma gyara,Shi kanshi ya tsinci Kansa a wata duniya ta musamman sosai suke kwasar Amarcin yau,Ubaidu yace haka kike da maiko ban sani ba wannan irin kogin Hamada haka,Mummy Ido ta rufe tana Jin kunya sai yabonta yake. Jannat shawarar Mummynta ta bi tana farantawa Fauzan rai sosai ta kwantar da hankalinta. Pipi an dawo daga kasa me tsarki harda saka hakorin Makkah Gold Guda daya ba karamin kyau ya Mata ba dama Lele ne yace Yana so ta saka,ana ta zuwa Mata Sannu da zuwa harda Yan school dinsu,Duk Wanda yaje Yana Shan labari wajen Hamida ana magana zata ce da a Saufiyya ne Yan school dinsu wasu su biyu Hanna da Hafeeza Suka je Mata bayan sunci sun Sha Suka zauna suna hira Hamida suna kallon wata channel sun saka labarawa Yan darika suna rawa ana yabon manzo,tace a Makkah ka Isa kaje musu da bidi'a ai sai dai kaji Yalla...yalla...Haba ai duniya anci gaba an Mana nisa Kawai muci gaba da Sallah Allah ya bamu a can amma an Mana nisa. Hafeeza tace Allah ya kaimu muma, Hamida tace wayyo Ameen ga aikin Hajji ga Umrah ga sunnna Ni da Lele kullum muna samun lada,Dariya da shewa sukayi Hamida tace haba Jin Dadi Yana Madina garin manzo ba bakin ciki su Papa ma mantawa nayi da su sabo nishadi gani ga Lele na a gefe muna Kai ziyara,inyi Addua sannan na juya gefena na kalli Lelena abin kaunata naji sanyi Lele Yana sama Hamida tace ai har dutsen badar muka je ziyara abin ba a cewa komai na manta sunan daya wajen ta Shiga kwalawa Lele Kira Lelena....shuru...Leluwan kamshi....Shuru ...Lelen pipi...yafito kenan daga wanka yaji Kiran Pipi yace Menene da karfi sabo da nisan dake tsakaninsu.. Kazo ka dauki Aslam ya isheni sannan dan Allah ya ma sunan makabarta da Muka je ziyara ka fada min sunanta,daga ciki yace Baqiya? Yawwa mutanen kwarai suna kwance a can Sai mu Yan iskan gari muka rage,Hanna dake itama masu kudi ne taje ai Kawai labarin suke da Hamida sabuwar Hajiya,Lele ya dau wanka Yana kamshi cikin wani yadi me tsada Hamida tace karka karaso gani Nan please komawa yayi Bedroom ta hauro da sauri tace haba Lele wannan buga wanka haka nifa ban yarda da Kai ba,duk Yamma sai ka cakare kace wurin masu aikinka zaka je,Kuma ga Mata a palo,Hijab dinta kato ta dakko tace saka wannan ai ba Mata kadai ya dace mu da hijab ba harda ku,Lele yayi Dariya Kawai yace na zaci wani abin ne Ina Aslam din? Yayi kasa suka gaisa da kawayen,Aslam dai Hamida ta Mika Masa yaro fari tas kyakyawan gaske ko askinsa na Yan gayu yasha Kaya masu tsada Yana kamshi gashi dama ya fara rarrafe. Har mota Hamida ta rakashi ya Shiga Bayan mota tare da Aslam sannan Driver yaja suka fita. Wajen Mimi Suka Fara zuwa ya Kai Mata Aslam dake ya Saba da ita Sanda zasu tafi Saudiyya Mimi aka kawowa shi,Yana ganin Mimi ya fara Zullo Yana kuka sai Mika Mata hannaye yake,Lele ya bata shi ya Mata sallama ya wuce abinsa Sai cikin dare ya koma gida Aslam wajen Mimi ya barshi 11pm ya dawo ya iske Hamida ta shirya Masa abinci dama yunwa yake ji yaci sosai yayi wanka tana ta bacci abinta sai da ya kwanta sannan ta farka cikin muryar bacci ta furta Sannu da zuwa Lelena, rungumeta yayi Yana shafa Mazaunanta tare da furta Mata I love you,tana Mika tace me too tana kankameshi har bacci ya kwashe su gaba daya. Bangaren Jannat Kuwa soyayya suke zubawa ita da Fauzan tun bata Saba ba har ta Saba sosai Watarana ma itace ke nema Bayan wata daya Murtala ya hado kayansa da shi da Lawisa tare da danta suka zo,Jannat ta kalli Fauzan au har da Mata? Yace ae mene rayuwa su ci su Sha dai sannan dan Adam ai Rahma ne Kinga kin samu kawa ga bangarensu can,matarsa ita zata na tayaki aikace aikace ana biyanta shi ma mijin ya kula da compound Kinga har lada sai ka samu tunda dole dai sai an kawo masu tayaki aikin sai ayi hakuri da su,ya canja halayensa,Jannat tace hakan yayi ai,Lawisa tana ta kallon gida,itama Lawisa kyakyawa ce bafulatana wankan tarwada kayan jikinta masu kyau kana ganinta kasan ba a wahala take ba,Kuma ta iya kwalliyarta dai dai talaka babu me rainata Murtala Yana kula da iyalinsa Dan nasu ma tsaf,Bayan sun gaisa,Murtala fafur kin kallon Jannat yayi Kar ma ya batawa Fauzan rai ya sake korarsa shi yasa ya dauke Kansa Yana Wasa da dansa,Jannat tace ya sunansa? Saif cewar Lawisa Jannat tace mashaallah Allah ya raya Miko shi,ai murtala Lawisa ya bawa ita Kuma ta bawa Jannat Dan Kar ma a samu matsala ya kalle ta, Fauzan Yana hankalce da Murtala sai dariya yake a ransa. Wani part aka basu wanda yake da two rooms da kitchen da komai har kayan abinci an zuba musu komai nasu tsab katifa katuwa Babba da karama ga bedsheet kala biyu,daya room din kuma kujeru ne masu kyau harda tv plasma karama dama sabo da Yan aikin aka yi wajen Fauzan ne ya zuba musu komai,Murtala yace oh da Zan cuci kaina tsuliyar tsohuwa ta rinjayeni,Lawisa tace Allah ya Kara maka ai da nasan abinda kayi kenan ko jinyarka bazan Yi ba gidan ubana Zan gudu,Murtala yace yo ai shi yasa naki fada Miki dalili nace Yan ta'adda ne Suka zuba Mata ruwan zafi,Lawisa ta galla Masa harara,Murtala yace kiyi hakuri wallahi ko Daya tsuliyarta bata birgeni ba kwayar haske babu duhu dundum ciyawa ta rufe komai ga abu bakikirin Kamar takashin Dan Iska,Sai da Lawisa tayi dariya. Kayansu ta shirya Murtala yayi tsalle ya fada saman katifa yace kizo mu Fara nuna murnar mu a saman wannan katifar zo Yar Albarka ki bude min fadama uwar ruwa,Murtala ya tube zigidir aba ta mike yace zo Nan ga wire in jona Miki shocking Lawisa me dadin suna ta Murtala Taleluwa me dadin harka,Lawisa ya jawo ganin saif yayi bacci ma,ya rabata da kayan jikinta yace bari na kwashi tagomashin soyayya,Lawisata me tantakwashin Virgina,ta bature yace Virgina shege bature ya iya sa suna bajaina Haka Kuwa yake a baje Malam,karya yake satar hausa yayi daga bajewa aka samo Bajaina shine ya canja rubutu yace Virgina. Yaya iceko an Miki Allurar Nan ta family planning bana so a dinga yawan haife haife ana rabani da Virgina,Lawisa tace anyi ai tun shekaran jiya date ya cika yace to a Nan garin zamu ci gaba da Yi, maza baje min fadama dama rashinki a kusa ya jawo na Fara Zama kwarto Anne ce ta Nemo labarin Mummy ta warke har ta auri me kudi Dan uwan mijin Jannat,bakin ciki ya Kama Anne ta fesawa Talatu labarin,Talatu tace ai ni haka nake so ta bar mijina na huta Yar tsiya taje can ta auri shugaban kasa ma,Anne tace Ni nafi so naji ta a cikin wahala tana fama,a sirri ta nemo baban Jannat ta bashi labari tace Kar kaga yanda ta Kara kyau Kamar balarabiya,Kishi ya Kama baban Jannat yace ai Kuwa ba a Isa ba sai an bani matata,Anne tace har gidanta na sani da ace zaka iya da kaje ka kashe Mata auren ka kulla Mata sharri,Yace ai Ni nasan me zanyi kiyi Shuru Kawai. Anne burinta taga Mummy a mugun wani hali,Talatu tafi so tayi nisa da mijinta,burin Talatu ta raba Anne da danta ta mallake mijinta,Shi Kuma Baban Jannat da gaske kaunar Mummy yaji sabuwa ta Shige shi so yake ya dawo da ita gidansa ko ta halin Yaya ne, sabo da haka takanas ya shirya escort dinsa Suka ajiye shi a kofar gidan Asiya Mummy ranar Kuma Miji Yana gidanta. Masu Sharhi Ina Miko gaisuwa Kuna birgeni Allah ya biya muku bukatunku. AsmaBaffa [6/28, 1:47 PM] Sis Asma: 🔮🔮WARE BAIKO🔮🔮 JANNAT Part 2 126-130 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah. Please don Allah duk wacce ta san ba siyan maganin za tayi ba kada ta dauki number ko ta kira waya, kada mu 'batawa kai lokaci🙏🏻_ _*infection*_ _Muna da magungunan sanyi sadidan! wanda yake kassara kowane irin sanyi na fili da boye! infection yana karya garkuwar jikin dan Adam yana dakusar da kowace irin mu'amula mussaman ga ma'aurata, sanyi ko wane iri kike/kake fama dashi da izinin Allah idan anyi amfanin da irin maganinmu za'a dace_ _*SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI*_ Ware Baiko Sadaukarwa ne ga AIDA MAMAN TASNIM Page naki ne UMMI DEEJAT Yana zuwa gidan ganinsa babban mutum yazo da motoci na Alfarma sai me gadi ya bude Masa kofa ya shiga ciki sanye cikin wata shadda harda Babbar Riga dinkin hannu,Kofar Palo ya Shiga bugawa kamar zai balleta,Mummy tana zaune Kawu Ubaidu yayi matashi da cinyarta Yana kwance suna hira,dukan kofar yayi yawa Kawu ya mike tare da bude kofa Yana Jan tsaki,baki bude yake kallon bakuwar fuskar Abbann Jannat yace Malam lafiya da girmanka? ba cecekuce ne ya kawo ni ba zuwa nayi ka sakar min Matata ta dawo gidana,Mummy lekowa tayi bayan tasa hijab Abba ya ganta tafi da komai da komai tace me naji kana cewa Baban Jannat? Ki koma gidana ai ni na Fara aurenki,haka ka haukace ko shaye shaye kake yi? wallahi kizo mu tafi ai Ina sonki gaba Daya ke da 'yata Kun tare a gindin wannan mutanen Kai ka sakar min Matata ko wlh na dauki mataki a kanka sai na batar da Kai,Mummy tace yaushe Jannat ta Zama yarka? ai dama nasan 'yata ce kuma Ina son abata Allah ya Mata Albarka Kuma kema Ina sonki Dan Allah ki taimaka min mu koma gida na wallahi Ina kaunarki Asiya Dan Allah,to bana sonka ni karka sake zuwa gidan mijina ka manta wulakancin da ka min Abban Jannat yace wallahi Sharrin shedan ne Amma Ina kaunarki Mahaifiyata itace silar faruwar komai Kawu Ubaidu yace Kai dalla fitar min a gida ko wallahi nasa a wulakanta ka yanzu, Kabir yace ba inda zanje Ina kaunar matata a shirye nake dana aikata komai a kanta,banki a kaini gidan yari ba a kanta,Murtala ne ya shigo da Yan Sanda zuga guda harda jiniya wiwiwiwi yace yawwa gashi,a fara Kama wannan kafin uwarsa,Abba ko kula Yan Sandan baiyi ba ya Mika Hannu ya kaiwa Mummy cafka ihu ta saki tare da komawa bayan mijinta ta buya. Abba wata kururuwa ya saki yace wallahi Anne ce ta jawo min Ni na yarda ki dawo wajena na zauna bani da ko sisi ma dama kudin tsafi ne da ni da farko kasuwancina ya fara bunkasa na halak Anne ce ta hadani da wani boka a Imo state nake yin kudin tsafi itace take taimaka min ana hada tsafin da ita,Murtala yace yawwa Officer kaji uwarsa ce ta soye min Gilala ta,Officer yace Mene Gilala?Murtala yace mazakuta ai sakayawa nayi a kauyenmu Gilala ake cewa,Murtala yace gata Nan har yau bata dawo dai dai ba tunda Anne ta soyeta Al'quran wuta ce a tsuliyar Anne har wani hayaki ke Fitowa ta ciki,Yan Sanda Suka kyalkyale da dariya,DPO yace ka dai tsorata ne Murtala azaba ce tayi ma yawa,Murtala yace Allah koriyar wuta ce irin ta Gas a bajainar Anne tana jonawa sai tiriri wani cuuuuuu gilalata ta fara tafarfasa sai da ya bawa su Mummy dariya 'yan Sanda ne Suka Kama Abban Jannat Suka datse Masa hannaye da Ankwa aka sashi a mota Suka Kara gaba,Murtala yace Sannu Kawu ku koma ciki ni Murtala shugaban Yan sa Ido Ina da hujjoji wannan mutumin bazai tsira ba sai ya shiga gidan yari,Mummy tace mun gode mugun bawa ne wlh, Murtala yace karki gode min da kin San bala'in da na Sha a hannun gyatimarsa da kin jinjina min,Lawisa sai da ta bani sarauta ta masu juriya,Dariya Kawu yayi yace to sai mu hadu a police station,Murtala ya juya ya tafi gida Yana komawa ya Kira Fauzan ya Masa bayani,Fauzan yace karka bari Jannat taji Babanta ne duk masifa Uba uba ne tana son abinta akan haka sai ta tsane mu Kawai muyi case din ba tare da ta sani ba,Murtala yace ko Lawisa baza taji ba kasan Mata da tsegumi bare naga Lawisa ta Shige jikin Jannat tana Neman fada,har fada nake Mata a wajena ya kamata ta samu fada yanda Zan kasa yi Mata kishiya amma bata ji ba sai a wajen Jannat, ranar da Zan Mata kishiya na gani idan Jannat zata iya hanawa,Fauzan yace matar tawa bata Isa ba kake nufi? Murtala yace a'a ya wayance yace Jannat baiwar Allah mace Yar Aljanna irinta,Fauzan yace daina yabar min Mata ni kadai ya kamata na yabi abata ni jeka dan Allah ka isheni,Murtala ya wuce sum sum part dinsu. Yana zuwa bedroom ya samu Lawisa daure da towel tana kwalliya,Murta yace Loviiina zo ki kwance min tazuge na,Lawisa tana zizara eyeliner tace Kaine sai a dinga maka tazuge zurere ka canja tela ka dinga bawa kwararru,Murtala yace to Zaki fara ne ai Neman kudi ne ya kawo Haka,yanzu ke kanki da bana kula dake baza ki dinga min soyayya ba,hararata Zaki dinga Yi,ko kanwarka sai da kudinka take kaunarka, yanzu maganin da kika Sha jiya Nawa Kika ce na bayar amma ko ba komai naji canji na musamman idan ya Kare ki sanar min na Karo Miki a siyo sannan yanzu ki sa a kawo Miki Zan biya kudin ki bawa Jannat tunda Naga Kuna mutunci shima oga yaji Karin dadi a dalilin wannan sai ya Kara Mana Albashi,Lawisa tana dariya tace to zan siyo Nima wajen wata na siya kusa da gidan Nan inda ake siyar da awara,Murtala yace to ki Zama kawarta Kawai ki dinga samo mana kayan harka Yana fadar haka ya shige toilet yayi wanka ya koma bakin gate wajen aikinsa,Lawisa Kuwa ta gama komai na aikin Jannat. Anne tana gida taji an Kama danta Nan take ta fadi kasa gaba daya ta samu paralyse aka kwasheta zuwa asibiti Wanda ko yatsanta bata iya dagawa,Talatu tana Jin labarin haka ta tattara duk wasu takardu na kadarorin Abba ta shirya tare da bin jirgin Dubai da yaranta gaba Daya Bayan ta sallami duka Yan aikin gidan da securities ta biya su hakkinsu gidan Kansa a kasuwa ta saka shi ta dauke ATM cards din Abba ta tsere da su Abba kwanansa biyu sannan aka bashi damar Kiran wani nasa Yana ta Kiran Wayar Anne akan a kawo Masa kudi amma bata shiga,Talatu ya Kira itama Bata shiga,wani babban yaronsa ya Kira sannan ya samu aka daga shine ya bawa Abba labarin komai,Abba yace ya akayi a Rana Daya zata kwashe komai nawa? Yaron yace dama ta Dade da target dinta komai ta hada naka Kaine kake ganinta kamar kaunarka takeyi amma abubuwa dama dama suna hannunta,Abba salati ya saki Nan take zuciyarsa ta buga ya fadi a wajen Yana Kiran sunan Jannat ki yafe min ke da mahaifiyarki kafin a kaishi asibiti yace ga garinku nan,sai Mummunan labari su Fauzan suka samu. Rasa yanda za a fadawa Jannat akayi sai Fauzan ne ya sameta a daki tana gyara Masa kayansa ya kalleta ya furta zo ki zauna muyi magana Babyna,tana Murmushi tazo ta zauna Fauzan ya kalleta tare rike hannunta ya fara Bata labarin Abbanta da yaje gidan Mummy da duk abinda ya faru sannan yace kiyi hakuri Abba Allah ya karbi abinsa lokacin da yaji matarsa ta kwashe komai nasa zuciyarsa ta buga,Jannat duk da bata ji dadin mahaifinta ba sai ta fashe da kuka,Fauzan yace ba kuka zakiyi ba Addua Zaki Masa sannan ki yafe Masa,Mummy ma tace ta yafe Masa,Jannat tace Ni dama ban rike a Raina ba na yafe Masa tuni Allah yaji Kan Abbana ta fashe da kuka tare da mikewa ta dakko Hijab tace Zan tafi gida,yace ai kauyenku aka tafi dashi Hajiya Talatu ashe tuntuni ta siyar da komai nasa bai sani ba, ta gudu Kuma ba a San Ina take ba. Dukkan Yan Uwa da abokan arziki Kauye suka tafi a can akayi masa sutura tare da kaishi makwancinsa ana ta labarin Talatu ta yashe kudi ana tsine mata,shi yasa ake so ka shuka Alkhairi baka San yaushe zaka koma ga mahaliccinka ba,Jannat ba wani kukan kirki tayi ba kasancewar basu shaku da shi ba,sai bayan sadakar uku sannan Jannat ta dawo gidan mijinta,su Fauzan da danginsa ma sunje gaisuwa har garin,Anne Sam babu me kula da ita sai labari taji danta ya mutu,ta koma abar tausayi sai kuka,Haka dangi Suka dauki Anne tare da tafiya da ita kauye Babu me jinyarta sai wata kawar Anne wacce taci kudin Anne ta more itace take Dan zuwa jefi jefi tana dan gyarata,abinci kuwa Watarana ma ba a bawa Anne,cikin wani dakin kasa aka sata Wanda a baya kitchen ne ma duk jikin ginin bakin hayaki,Kullum Anne Sai tayi kuka ta godewa Allah,sai neman Mummy da Jannat takeyi amma Basu je ba. Bayan wata biyar Anne yanzu ba a gane ta Sam dakin da take in Banda doyi ba abinda takeyi babu me kulata kawar tata ma ta daina zuwa,ga rashin abinci a haka ma Sai Jannat ce ta samu wata dattijuwa a kauyen duk wata tana biyanta kudin Jinyar Anne,ana jinyarta Amma ba wani na kirki ba,Anne Sai Jannat take sawa Albarka da Mummy ko Omo da sabulu duk sune suke kawowa a haka ma Yan gidan sacewa sukeyi,Anne har mutuwa take rokawa kanta tana tuba ga Allah amma taki mutuwa ta dawo Kamar tsinke sabo da Rama,komai a kwance takeyi fitsari da Kashi a kwance takeyin abinta sai surutun tsiya bakinta bai mutu ba kullum sai ta sawa Jannat da Mummy Albarka sannan tace Talatu Allah ya kwashe Miki Albarka Hamida tana zuwa school abinta ta samu ciki Bayan ta yaye danta Aslam,Lele sai Murna yake za a haifo Masa second Baby, Pipinsa kullum kyau take karawa da wayewa abin ba a cewa komai wani sabuwar soyayya suke Kara dasawa,Bangaren su Papa mashaallah suna cikin rufin asiri,Yaya Sulaiman ya auri matarsa suna zaune lfy har ta samu ciki yayin da Karima ta haifo yarta ta biyu ita da Sakina Kawar Hamida. Jannat ce take bawa Fauzan Labarin kawayenta tace Zee asalinsu Yan Jigawa state ne Babanta ne ya Mata auren dole ita Bata son mijin,ganin taki Zama Babanta ya Kori mamata daga gidansa sabo da Zainab taki Zama a dakin mijinta,dukka Dangin miji suka tsaneta hakan yasa ta dawo Abuja gidan Yar uwar Mamansu itama ta Gaza rike su mijinta me kudi amma basu da yanci,wannan yasa Zee da mamanta suka Fara sana'ar siyar da abinci a cikin tasha har Zee ta fetsare ta Fara sanin maza,ita Kuma Maman Zee ganin lokaci guda Yarta ta sama musu babban jari da wajen Zama shike Nan ba ruwanta tasan me yarta ke Yi amma ko a jikinta tunda ta samu kudi ta Bude katafaren shago Daga baya tazo tana nadama tana yiwa Zee fada ta daina karuwanci ta samu miji tayi aure ita kuma Zee ta Saba da rike kudi shi yasa taki dainawa tun tana mata fad har ta kyaleta tana kallo amma tafi karfinta,Kuma ta kyaleta dama ba damuwa tayi ba tunda ana bata kudi. Ramcy yare ce Yan ogun state ne Musulma ce akwai wani saurayinta da take mutuwar kauna ya Mata wayo ta bashi kanta Yana sex da ita sai da ya gaji sannan ya wulakantata wannan bakin cikin yasa ta koma karuwanci iyayenta sun mutu sai uwar daki itace tazo ta zauna tare da Maman Zee lokacin bikina,su peace Kuwa gaba daya su Uku Ra'ayinsu ne da son karya dole sai sun sa suturar da Yar Gomna zata saka,Kawai su dai karya suyi kudi shine ya kawo su Abuja Wanda karya Suka yiwa Iyayensu cewar Aiki suka samu a Abuja sakamakon duk sunyi Degree sun bar iyayensu sun dawo Nan Fauzan yace tab dama can lalatattu ne a kansu aka fara talauci ki shirya gobe muje da Mummy,washe gari haka suka tafi gidan su Zee suna zuwa suka iske su suna Shan kida ana rawa ganin Mummy da Fauzan suka kashe tare da Basu wajen Zama harda ruwa da abinci,Bayan sun gaisa Ramcy tace Jannat murna muke Zee ta samu mijin aure Nima Haka,Jannat ta dinga murna,Zee ta kalli Mummy tana kunya tace Yana da Mata Daya da yaransa biyu custom ne a Kano gidana daban bikin bazai dade ba Inshaallah za ayi,Ramcy Kuma wani dan uwan Mamansu ne a Nan Abuja,Sannan Peace da Merry sun Musulunta shekaran jiya,Kuma a masallacin Suka samu wasu musulmai zasu aure su mun tuba gaba dayan mu rana daya muka tsara bikinmu,Mummy tace Mashaallah Muna tayaku murna,Fauzan ya kalli peace harda hijab yace Kun Musulunta duk abinda kuka Yi na zunubi babu yanzu gobe kowacce zata koma wajen Iyayenta,Fauzan yace Alhmdllh mu Kuma Inshaallah zamu dauki nauyin komai naku,Mummy tayi ta musu godiya sun dade suna hira kafin su musu sallama su tafi. Bayan Sati Uku Jannat ta fara laulayin ciki sosai lokacin bikin su peace Yana matsowa,Anne Kuwa tana nan rai a hannun Allah babu Wanda yake lekata,har ta mutu ba a San ta rasu ba sai da Me kula da ita tazo ta iske Anne ta mutu gawarta har ta kumbura, mutane aka dan tattara tare da Kai Anne makwancinta kusa da danta,Jannat suna can akayi janaza kowa ya guji Anne,Jannat tana zaune Hamida ta shigo da Dan karamin cikinta Lele Yana kofar gida tare da su Fauzan,Hamida waje ta samu ta zauna anci shadda me tsadar gaske ta gaisa da mutane tayi musu gaisuwa ta kalli Jannat tayi Narai narai da Ido zata Yi kuka tace oh Jannat kina ganin Iftila'in rayuwa sai ta fashe da kuka,a ranta tace karya nake kukan karya nake ai mu duk gidan mutuwa sai mun taya Wanda aka yiwa mutuwa kuka,Jannat ko ita bata Yi kuka ba sai Pipi,Murtala Kuwa da yazo gaisu tabarma Guda ya dauka ya ware can gefe daya azo a dinga Masa gaisuwar tsohuwar matarsa Anne,Fauzan bai gane nufin Murtala ba yaje ya zauna a tabarmar Murtala yace Anne baiwar Allah ga iya tuwo da Miya,Sanda hakoranta na karshe turmi zai fice tace Murtala sa kibiya ka banbro min shi,Amma matar Nan Haka ta soye min Gilala ta,ba komai Allah yaji kanki amma tooooo na dai Yi shuru amma da kyar ne idan ba a fara Jibgar Anne a kabari ba,watakil tana can an Mata butar Malam,Fauzan yace ka Fadi Alkhairi ko kayi Shuru,Murtala yace an gama Oga amma gaskiya Anne zai wahala ta tsallake siradi,Jannat ce ta fito ta rako wasu Murtala ya Mata gaisuwa,Fauzan kuwa suna hada Ido ya kashe Mata Ido daya saura kadan tayi dariya. Da rana ana ta kawo abinci kala kala Hamida ta tashi ta koma wajen Abinci duk wani abinci me dan dadi sai ta juye a wuri na daban,a kitchen take buya taci ta cika cikinta sai ta fito ta zauna idan ance abinci tace sai anjima,Kunu aka kawo na daka lafiyayye Hamida ta mike ta karba tayi can wajen wata Amarya a gidan dake gidan yawa ne,a can tayi Sallah ta Sha kunu ta koshi ta dawo kusa da su Jannat tayi malaho harda sadda Kai,Jannat tace Aunty tun safe baki ci komai ba ga aikin juye abinci da rabawa kina ta Yi ki samu ki sa wani Abu a cikinki,Pipi tace hmm wa zai baka cin abinci a babbar mutuwa irin wannan,Ni kaina iyayena nake tunowa sai tsusayin Anne ya Kama Ni,idan aka yi mutuwa dole sai kaji ba dadi bazan iya cin komai ba kyale abincin Nan jannat. Tana zaune taga makwafta sun kawo Dambu me rai da lafiya Yana tiriri tace bari a juye sai a hada da na dazu a sallami bayin Allah,Jannat tace Sannu Pipi Muna godiya tace ai an zama daya,tana karba tayi kitchen da dambu plate Guda ta zuba taci ta koshi ta rage ta dawo ta rabawa wasu da Yamma gaf da zasu tafi sai data Kara cin dawake sabo da Hamida ita laulayinta cin abinci da yawa take yi, da su Fauzan suka tattara suka tafi Abuja,Jannat sai da akayi Uku ta dawo,Fauzan ya dakko abarsa a airport Yana ta zumudi kwana Uku baiyi komai ba,Bayan Yan kwanaki suka Shiga bikin su Zee dukkansu sun shiryu,anyi biki na gagara ko wacce an kaita dakin mijinta. Hajiya Amatullah tun tana damuwa har ta hakura da auren Mummy suna zaune lafiya sai dan abinda ba a rasa ba,Mama Kuwa shiri suke sosai da Jannat. Itama Jannat ta shiga University. Bayan wata shida Hamida ta haifo yarta mace kyakyawar gaske taci suna ummussalama kyakyawar gaske Kamarsu daya da Lele wata biyu tsakani Jannat ta haifo twince dukkansu Mata zuka zuka,Fauzan sai Murna duk ya rasa inda zai da kansa ranar suna aka sa musu Fuad da Fudhal. Bayan shekara biyu Mummy cikinta ya tsufa sosai ba a dade ba ta haifo 'yan biyu itama duk maza,Jannat sai Murna take tayi kannai,ba Wanda bai taya Mummy murna ba,lokacin Pipi ta gama degree abinta,Jannat ma tayi nisa,Arzikin Nabeel ya Kara bunkasa,ga Affa yayi retire Lele shike komai na gidan,Fadila ta girma ta shiga primary 5,Fauzan lokacin Jannat ta samu wani cikin shima arziki sosai ya bunkasa,kowa Yana cikin Jin Dadi da kwanciyar hankali sai abinda ba a rasa ba kasancewar dan Adam baya rabuwa da jarabawa kala kala ta rayuwa. Aslam Yana yawonsa ko Ina sai rigima,yau Sunday Nabeel Yana gida babu inda yaje,Pipi tana kitchen tana tsantsarawa me gida girki kamshi ya cika gida,Aslam ya shigo da gudu su Fuas sunzo Mum Yana Jan rigar Pipi,to je ka fadawa Dad,da gudu ya fita har da faduwa Lele yace sai ka Fadi baza ka taho a hankali ba sai kace mamanka a Kauye,Aslam yace cikin gwarancinsa Fu'as ne ya Jo,sai ga su Jannat sun shigo tare da Fauzan da yaransu abin sha'awa,Hamida tace Alhmdllh sai ku tafi min da Aslam,da gudu ya fada bayan Nabeel yace Daddy ni wajen Mimi zanje,Fauzan yace wa zai dauke ka dama ka damemu da kuka. Zama sukayi suna ta hira anci an koshi a gidan Suka yini. Suna kallon news suka ji an Kama wata Mata Yar asalin Niger tana safarar miyagun kwayoyi,ana hasko matar suka ga Hajiya Talatu ce ashe ,an yanke Mata hukuncin daurin Rai da Rai a kasar China. Hajiya Talatu duk abinda ta kwashe na Abba ya Kare ta kashe su wasu sun damfareta millions of Naira karshe shine ta koma safarar kwayoyi da ragowar kudin Abba. Yaranta biyu mace da Namiji Kuma aka dawo da su Nigeria. Su Nabeel na gama ji Suka dunguma hukuma aka shigar da komai sai da aka tabbatar kannen Jannat ne sannan aka Basu yaran,Mimi ce ta karba zata rike su,Affa sai Murna ya masu Yara zai rike ya samu Lada. Ita Kuwa Talatu sai kuka sai nadama gashi abinda ta tara cikin kankanin shekaru sun Kare, karshe anyi gidan yari da ita,dama China su akan harkar kwaya basa dagawa kowa kafa kisa suke yi,Talatu tun tana kuka har ta daina,ta fita a hayyacinta gaba daya. Basma ware Baiko Kuwa ta hada kungiya guda ta mata itace shugabar Mata ta gidan yari sai abinda tace da Mata ga zalunci,duk ta addabi Yan prison kowa ya tsaneta a ciki. Wata tantiriya aka kawo gidan yari wacce ta gagara ita Yar daba ce ta gagari ware Baiko a Iskanci tana zuwa Basma ta mata wani kallon banza,ai Kuwa matar ta Kama Basma Ware Baiko ta lakada mata dukan tsiya ta farfasa mata jiki,sai Murna akeyi ana Allah ya kara. Yan matan Basma ne Kawai suka ji haushin dukan Basma da akayi sabo da gaba dayansu Yan matan sunfi su ashirin Lesbian sukeyi,Basma duk amfani take da su a boye a prison din. tunda ma'aikatan suka gano sai aka dauketa aka maida ta prison din Lagos acan ake cin ubanta gaba daya wahala tasa tayi ladab Kamar ba ita ba,tana zaune sai kace an tonota daga cikin toka kanta ko dankwali babu ta rakube a jikin wani karfe ga aikin wahala,a wajen ta tsuguna tare da fashewa da Kuka abin gwanin tausayi tana na cuci kaina sai ta sake rushewa da kuka,Wata Igbo me karfin tsiya tazo ta sharara mata Mari ta bata aiki taki yi ta zauna tana uban kuka,Kafa Igbo tasa tare da yin ball da ware Baiko ta sake rushewa da kuka ta rarumi cuttlas ta tafi aikin sassake ciyawa tana bawa Igbo hakuri ba shiri ta fara aikin tare da wasu yaran matan Suma. Pipin Lele ce ta dau wanka ta fito tana jiran mijinta a jikin galleliyar mota,Daya Yar tana kafadarta, Lele ya fito tare da Aslam rike a hannunsa sun zuba gayu wata dalleliyar mota Suka shiga driver yaja su tare da tafiya yawon shakatawa. Jannat Kuwa da Fauzan suna Bedroom suna zuba Hidima Kamar zasu kashe kansu. (END) karshe Nan na kawo karshen Ware Baiko Allah yasa muyi amfani da darasin Dake cikin wannan Novel Kuskuren da muka Yi Allah ya yafe Mana. Masu sharhi Ina Matukar godiya da jinjina Wanda ban bawa page ba ayi min afwa na gode Sai Allah ya kai mu mun hadu a sabon Novel 🥰💕🥰🥰zanyi missing naku fans Copy By Zainab Butalawa AsmaBaffa