BISSIMILLAHI RAHAMANIN RAHIM GODIYA YA TABBATA GA ALLAH DA YA BANI IKON FARA WANAN NOVEL DIN A CIKIN KOSHIN LAFIYA YADDA MUKA FARA SHI LAFIYA UBANGIJI YA BAMU IKON GAMAWA LAFIYA. DA FATAN SAKON DAKE CIKINSA ZAI ISA GA INDA YA KE BUKATAN ZUWA GURIN MATA YAN UWANA ALLAH UBANGIJI YASA MU ANFANA DASHI WANAN PAGE DIN FREE PAGE NE DAGA SHIMFIDAR LABARIN MAI SO ZATA IYA TUNTUBANA DON YIN REGISTER SHIGA GROUP DIN NAGODE TAKU HAR KULLUN ZAINABUN KU Hasken farin watan daya haski taurarin da suka zagaye shi masu fitar da kyalli daga ganin su, Wanda hakan yasa sun kayata gari matuka hadi da sanya zukatan bayin Allah a nishadi Wanda mafi yawan zukata mutane musan man na kauye inda babu wutan lantarki a garesu cikin jin dadi da walwala. Ga iska mai dadi da yake dan kadawa lokaci lokaci gami da kamshin kasa dake tashi gwanin dadin shaka. Ga yara dake jin dadin yanayi duk da dare yayi amma suna waje suna wasan su don babu duhu da zai sa ashige gida a lokacin Tafe take da sauri iskana dan kada ta hannuta rike da farar roba mai marfi da ta dauko nikan awara da zasu soya da safe kafin ta tafi makarantan boko. Tafe take cike da nishadi a zuciyar ta wanda yanayin yake saka ta jin dadi har tana lumshe idunuwan ta. Tana tafe cikin sauri bata da wani guri daya wuce taga ta isa gida ta tatace markaden wanken da ta dauko daga gurin nika. Wasu mutane ne zaune wanda magidanta ne dabian su shine duk dare a shimfida katon tabar kofan wani gida su dinga yan ciye ciye kafin su shiga gida gurin iyalinsu da aka bari da tuwo da miyar kuka bakifi ko nama a cikin sa haka mace zata rufe idon ta taci har sun saba. Basu da wani aiki idan idan sun zauna sai tsirko da sa ido idan mace tafito zuwa unguwan dare zasu fara cewa wance ce matar wani ko diyar gidan wani ne waccan. Idan akwai abin da naki jini a rayuwana shine na wuce wanan bakin daban na yan gulman shiyan mu. Don duk mutuncin da kai masu baka taba tsira a gurin su sai sunyi gulmanka idan kaba da baya. Ina kawo gurin kamar na wuce na share su amma hakan baiyuyuwa don hasken farin watan dake akwai a lokacin. Ina kawowa gurin su na dan duka ina fadin ina aunin ku suka amsa kusan a tare da lafiya kalau. Nasa kai na wuce su nasan cewa ba tsira zanyi ba nima daga kaidin su lokacin. Sauri nakeyi ba abinda ke raina kamar naga nashiga gida na idar da abinda ke gabana lokacin. Ina shiga gida da sallama na samu su Inna zaune tare da yan uwayena suna cin abincin dare mahaifina shima ya dawo gida a lokacin. Gaishe su nayi inna ke cewa dani kin karbo nikan ne nace da ita eh inna. Ban tsaya bana na tube zanin jikina kada ya baci na daura wani kodaden zani nawa duk dashima wanda na cire din kodadde ne sosai amma wanda na daura yafi kodewa sosai. Nafara tatsan kullun wanke dake cike fam ga roba ina jin suna hiran su na manya har nagama abinda nakeyi sai a lokacin na samu saidan kaina. Kwanon tuwo na najawo na tasa a gabana don naci amma ina kallon tuwon naji banajin cin sa sai kallon tuwon masaran kawai nake yadda yai sanyi kalau a kwano har ya fara bushewa daga sama. Muryan mahaifiya na naji tana fadi wai Rahama bazaki ci abincin nan ki tashi ba ? Kin saka tuwo a gaba haka kina kallo yanzu zaki iyacewa yai sanyi bazaki ci ba ki kwana da yunwa. Jin maganan ta yasa na dan kai hannu ga kwanon na fara tsakura a hankali nasan cewa idan naci sai ya tayar min da zuciya na don haka nake tuwo mai sanyi baya bani lafiya. Gashi kuma Allah ya hallice ni a gidan tallakawa tallakan ma na kwarai don ko a kauyen mu mahaifana basu dashi ko kadan. Hakane yasa muke cikin wahalan rayuwa sai nayi dan talla zamu samu abinda mukai lalurar rayuwan mu dashi. Duk da hankan da muke zance Alhamdullahi don munajin dadin rayuwan da muka tsinci kan mu a hakan. Idan na dawo boko zan dauki tallan abubuwa iri daban daban nayau daban na gobe daban. Tun daga kan awara da safe idan na sayar na wuce boko idan kuma na dawo na dauki shimkafa da wake dafafa zuwa yamma wani lokaci na dan je islamiya wani sain kuma na kara fita da tallan gujiya ko rogo ko marau, marau wani lokaci har kwai dafafe nake dauka ina yawata dashi. Duk wani abinda za, a dora min sai Allah yaban sa, a na sayar na dawo a cikin lokaci. Da haka muke samun dan abin rufin asirin mu bamu zama da yunwa a gidan mu. Akan ce talla yana bata yarinya ni dai zance sai dama an tarar da halin baci ga yarinyar don bana tsayawa wasa da maza balle har akai ga min maganan banza. Ko hannu namiji ya rike min zan tsaya nai mai cin mutunci da gobe bazai kara ba ma. Ganin yadda Allah yake ban sa, a ga sana, ata har wasu iyayyen sukan min kazafi wai kila loko ake tsayawa dani aimin juye abani kudi ko suce akwai wanda na lakanta da ke bani kudi na cas. Abin basu san daga Allah bane sa, a yake na saka a raina nema wa mahaifiyata zaman lafiya a dakin ta. Kishiyar Inna ta takan ta faman sake magana da diyan ta don su basu da irin hazakana ta ko ina. Duk da ba wani issashen karatu nake samun yi ba amma kuma Allah yabani kokari ga karatuna na boko da na mahammadiya din. Don ba, a taba mayar dani baya ba ga karatuna shiyasa ko yaya ne nake dagewa naga naje kowani don na dan samu. Duk da mahaifin mu baison tallan mu dole ne yasa yake bari don idan yai magana yasan amsan da zai samu gun uwayen mu akan tallah. Wata rana an kawo mai kara hafsat diyar kishiryar innata yashigo gida rai a bace yana fada sai cewa Mama tayi. Yo idan basuyi tallaba kan mu zamuci mayye amfanin diya mace a gare mu idan ba tallaba damay zamu tara masu kauan aure ga lalurorin da baka iya tsare muna. Ka kwaso mu ka cika a gida kamar zaka kai kurmi sai diya muke zubawa ba wani tallafi a gurin ka. Baba yace amma saboda Allah ko ban iya tsare maku komai ai baikamata ace har an kawo karan yaran nan ba gareni kan talla. Mama tace idan baka son suyi talla sai mu gani a kasa kaga sun huta muma mun huta. Su yan gulman da sukazo fada maka ga aibun su ina duk karkaran nan ba gidan da yaran su basu talla. Murmushi yayi kawai yace lauratu wata rana zaki gane magana ta gaskiya ne, idan yaro yayi ba daidai ba har kasamu mai fada maka gaskiya kamata yayi ka tsaya ka duba baka hau fada ba. Tace ai dole na hau fada tunda anzugaka kashigo zakai mun tujara a tsakar gida haka. Ba lawisa ce kawai ke tallaba a gidan nan amma don ana hassada da ita andauki tsana an sakawa yarinya ita kadai. Fita yayi daga gidan don baida tacewa don mama ba wani power yake dashi ba agurin ta. Mahaifiyana ma haka take zaman hakkuri da ita tana binta don azauna lafiya kawai. ****** ********* ****** Na dawo daga makaranta ke nan ina kokarin cire uniform dina naji murya sanusi dan gidan mama Altine makwabciyar mu yana sallama. Tsarabane ya kawo gidan mu yana fadin gashi inji maman shi tace yakawo muna wai anty Sa,ade tazo daga birni. Sabulun wanki ne clean da biscuits a cikin wani roba aka sako mai kunsan halin yan kauye da kara ko yaya abu yake sai makwabci ya san ma makwabcin shi idan yana da dan yawa. Da sauri na daga labulen dakin jin sunan wace akace tazo daga birni yar gayu ce ta karshe don ko maganan ta abin sha, awane gata da son mutane bata kyaman yan kauyen mu ko kadan. A yadda naji wai diya take ga mama altine yar kaunata ce ta birni da ta rasu su biyu ne a gurin iyayyen su shine da mahaifiyan ta ta rasu ta mayar da mama Altine kamar uwar cikin ta. Da sauri na daga labule ina cewa anty Fara tazo sanusi ? Yace tazo har ta haihu da yar ta maikyau da sauri na juya na jawo tsohon hijjab dina na saka na suri yan tsufin takalmana da duk sun sude gurin yawon talla ba asai min wasu ba nafice daga gidan mu. Ina jin Inna ta kwada min kira da ke ke don bata kiran sunana saboda ina yar fari gurin ta. Ban tsaya ba don nasan kiran akan dafafan gyadan da aka dafa min ne nazo na fita dashi. Ina shiga gidan na samu ta dauko buta zatai alwala sai naja na tsaya don kunya. Saboda ina matukar jin kunyan ta haka kawai tun ina karama idan tazo ina like da ita kafinta tashi zaka gane don ina shan kwalliya da kitso irin na yan birni kalakala akaina. Don Allah ya yalwantani da yawan gashi mai santsi da tsawo gashi baki amma bai samun gyara don ba lokacin yin hakan gare ni saboda busy akan talla tun ina yar ficiciya ta. Idon ta yakai gareni tace cikin murmushi a, a wa nake gani haka kamar yar Rama rama na ? Nabi bango ina karasowa inda take duke zata fara alwala a lokacin mama altine tafito daga dakin ta na bunu take cewa itace mana. Ba ta girma ba yanzun kuma kunyar ki take ji tagama maki fitsari a kwance nace kai haba mama ai dane wannan. Ida mama take tsaye rike da yarta na karasa nace mama diyar anty ne wanan ? Ina mika hannuna ina kokarin karban yarinyar dake dauke a hannuta nace mama yar anti ne wanan mai kyau haka ? Yarinyar sai kamshi takeyi kamar kamfanin turare a jikin ta nace kukan kunji dadin ku komai naku na birni ji yar nan mama kamar baturiya. Dariya magana ta yaba anty dake alwala batai magana ba sai da ta gama alwala tana mikewa take cewa ni dai Rama baki gaishe niba fushi nake dake ai. Nace don Allah anty kiyi hakkuri idan kinyi fushi dani ai na bani. Dariya ta karayi har hakoran ta na makka ya dan baiyya na a fili tace kai Rama har yanzun dai kina nan da shirmay ki ashe . Yanzu Rama na kece kiga girma haks idan wani guri na ganki ai bazan ce kece ba haka. Kunyan maganan ta naji mama ce tace ga ta saura aure ta girma abinta fa bakiga har ta wuce kidan dangiba komai acan acan da ita. Don ma Asiya tana azama mata talla ba hutu gareta ko kadan ta samu yarinyar ta mayar kamar injin. Mama bata rufe baki ba sai ga kani na Nura yashigo yana cewa Rahama Inna tace kizo wai gyadan da kika bari wa zai fita mata dashi ? Mama tace bakaji ba maganan da nake fada maki ni nasan ba, a rasa abin fitarwa ai yanzun haka. Nace kace gani tafe zan ga antyna ne tukun kafin nazo yaron ya juya yana fadin wallahi zanje nace kince bazaki zo ba. Ban damu da zancen shi ba nabi bayan anty zuwa cikin dakin mama dauke da yarta a hannu na. Na zauna nan na shantake gurin kallon yarinyar ina mamaki irin kyaun da Allah yai mata haka. Har ta idar da sallah ina zaune mama tana waje tana dan aiyukan ta na tsakar gida. Tana idarwa ta juyo gareni bayan ta shafa tana cewa Rama ke nan kinga yadda kika girma kuwa ? Na kara jin kunya ina sune kaina ajikin yarta wace nake jin dadin kamshin ta sosai har cikin raina. Tace ina fatan dai kina karatun ki ko har yanzu baki daina ba ? Nace lah anty banayi maki alkawarin zanyi karatu ba kince fa idan nai karatu watarana zan kai ki nima. Tace kwarai kuwa Rama kilama har kifini haka muke fata insha Allahu nace cikin dago kaina ina mamakin abinda tace. Anty wane ni, ni dake kauye kullun talla bani da hutu idan ba dare yayi ba na kwanta. Tace to kin san abin Allah ne ? Nace kamar wata babba cikin girgiza kaina da a, a amma gaskiya da wuya hakan ya kasan ce. Tausayin yadda yanayina ya kasance da nake maganan taji har a cikin ranta ga yarinya har yarinya amma babu wadata ga kauyanci zai illanta ni. Gafara dai masu gida muryan mama Laure ne kishiyar inna ta tayafo tabiyo ni da cin mutunci har gidan mama altine. Sun gaisa sama sama da mama Altine take cewa halan mutumiyar taki tana ciki ko ? Da hannu tai mata nuni da dakin take cewa tana ciki kuma kun san tunda Sa,ade ta sauka garin nan kuda samun hankalin Rahama kuma sai baba yagani sai saade tabar garin nan. To in ba shedana irin na Rahama ba ace uwarta ta dafa mata sana,a amma tanajin ance saade tazo ko minti daya bata kara ba ta suri takalman ta tayo nan. Daga cikin daki ina jin ta na balai akaina akan an aiko nazo naki zuwa na lake a nan, na dan turo bakina nace ni ba inda zan tafi ina nan yau da Anty ina zan tafi nabar wanan yar mama altine dama ko goyo bata iya ba tabarta a kasa. Kai Rama yanzu mama din ne bata iya goyo ba ni waya goyani har nakai haka yanzu ? Lokacin mama altine da mama suka shigo dakin mama tace wai mai take fadi ne ? Dariya ya kama anty sai kyalkyala takeyi nan dai suka gausa da mama laure ta hauni kuma da fada. Muryan anty ne ya katse fadan ta tana cewa wai gyadan har na nawa ne mama ? Tace kai yana da yawa fa kin san sherin Rahama yawa gare shi idan ta tashi amma ta yaya uwarki tayi sana, a zaki zo nan kiyi zaman ki. Maimakon na tashi ga mamakin mama ko har tai min zan bar duk abinda nakeyi na kama wanda ta sani amma yau sai gani zaune ko gezau ban yi ba. Rahama wai ba dake nake magana bane mama ta kara nanatawa cikin hasala. Anty Saade tace gyadan na nawane mama ? Tace zaikai na jakka biyu fa idan taso sayarwa ko da dan kai sama. Mikewa tayi zuwa inda hand bag dinta yake ta dauko kudi a ciki dubu daya mikakan ta tana cewa ina gashi da na yau da gobe don Allah abar min Rama na ta huta mama. Harara mama laure ta watso min daga gurin da nake tana cewa dama haka kike so ai. Ji fa mama ita da ko yaushe take cikin kyashewa tallana shine wai take fadin haka don taga kudi. Ta juya tafice daga gidan tana zuba magana tana fita nace lah Anty aida baki bata ba baki san halin mama laure ba ko ? Yanzu bai wuce tabawa mamana jakka daya tace ai shi kika bada, daga inda mama altine take tace karamin aikin Laure ne hakan. Tace to bari idan zaki wuce nabiki a boye sai kikai wa inna ta rike a hannun ta bashi ke nan ba. Aiko kamar na sani hakan tayi don tana shiga gida dakin ta ta fada ta dauko jakka daya da rabi tabawa Inna na wai inji anty Sa,ade tace arabawa yara gyadan ta saye sana,ata na kwana biyu. Inna tace kai ita bata gajiya da dawainiya ne da yarinyar nan idan tazo gari ko yaushe cikin dawainiya take. Allah ubangiji ya bar zumunci baki mama ta tabe tace kwadayi dai madudin wahala ne karamar yarinya tasan ta lakewa masu hannu da shuni tun tana kara ma idan ta gan su gashi har girma abin yabita Allah dai ya kyauta kawai. Ban shigo gida ba sai da magariba koshi don nasan baba idan ya dawo ban gida zai min fada ne shiyasa. Don mu kadai yake da ikon yaima fada a zauna lafiya a gidan batare da anyi tada jijiyan wuya ba. Nashigo ina dan rabe rabe na samu suna sallah don haka nima suri buta na wuce zuwa alwala. Na idar da sallah Inna tana zaune tana addua nace Inna nawa mama ta kawo maki dazun. Tace ina ruwan ki ai a gaban ki aka bata takawo min ko don naji nai saurin cewa eh jakka biyar ba sabuwar ta fil a mike. Humm din da naji Inna tace yasa nagane anyi cuta ke nan kai mama dai ba, a girma wallahi na fadi a raina. Kudin da anty taba sabbi fil ban ko tsaya kidayawa na fitar daga haban zani na dana kulle nace ma inna ta Inna gashi inji anty tace na kawo maki. Don na fada mata mama bazata baki su duka ba dazun shine tabani wanan nakawo maki. Bakina Inna takaiwa duka tana cewa kika aibanta uwarki agaban bakuwa aiko yaya take dai uwarki ce ita din. Bakin nawa da Inna ta daka na dafe cikin jin zafi amma hakan bai hanani kokarin mika mata kudin ba da nakeyi. Takarba da mamaki tare da kirgawa ta dago da sauri tana cewa ke yar nan har jakka hamsi ne fa tabaki ? Nace ban kirga ba ta daice na kawo maki kiyi amfani dasu kafin ta wuce na fara talla. Take cewa ikon Allah ita din aikin may takeyi haka har ta samu wanan kudin masu yawa take kyauta dasu ? Nace Inna ba, a birni take ba ance kudi abirni banza ne duk wanda yaje fa sai yai kudi a can. Tace ke rufa min baki da maganan wautar ki can a ina kika samu wanan labarin karyan haka ? Idan da banza ne may zaisa wasu suje su dawo tsula yadda suka tafi ? Mahaifinku sau nawa yake zuwa birni bai samo ba da zaki fadi hakan. Nace to inna kin sani ko baiso ne shi yafi son zaman mu haka ? Kallon takaici tai min tace ke kan ban san ranan da zakiyi wayau ba wallahi. Nace killa sai na girma ko Inna ? Wani irin takaici na kara bata tace to ai sai ki tsaya har ki girma din sai kiyi wayon. Sai dan shiru da ya biyo baya a dakin can tace ki saurare ni da kyau kiji abinda zan fada maki. Na gyara zama ina fuskantar Inna na tace banda kwadai banda roko don yafi komai zubar da mutuncin mutum da sauri. Ki kawar da idon ki ga abin duniya sai ki zauna da kowa lafiya a duniyan nan. Allah ne ya hada ki da ita jinin ku ya hadu haka don haka ni bazan hanaki hurda da ita ba don ban taba jin wani abin assha daga gare ta ba banda alherin ta da nake ji a gurin uwarta ko yaushe. Don haka ki kama mutuncin kan ki don Allah ki rufa min asiri ni da mahaifin ki. Inda sabo na saba jin nasiha irin haka ko yaushe a bakin Inna ta don haka wanan ba bakona bane sai ma cewan da nayi. Ai ina dazun da mama altine ta dafa mata kaza tace nazo naci nace da ita na koshi. Tace kin daiji na fada maki don ke har yanzu naga ba wayo ne dake ba. Haka ya kasance tsakanina da Inna ta har mahaigin mu ya dawo daga kasuwan kauye da yake zuwa tallan buhun shi na saka kayan masarufi aciki. Lokacin Inna ta fita don itace da girki ranan idan tana girki dakin mama laure nake kwana haka ma idan mama laure ce da girki dasu Lawisa muke kwana a dakin Inna ta. Ba zancen awara da safe don haka na fito daga dakin Inna ina gaida baba da dawowa. Yace a, a Rahama yau ba atafi kai nikan bane nace baba ai bazan yi tallah ba har kwana biyu. Yace ikon Allah damay ya faru kuma sarkin tallah ? Nace baba Anty Sa,ade ta zo na gidan mama altine itace ma tace na zauna gida har sai ta koma. Yace a, a kice min uwar dakinnki ko uwar goyon ki har yanzu ashe ana tare ke nan ? Mama na zama take cewa kai kwadai bayi ba wallahi yanzu kaida kan ka kake koya mata harkan kwadayi ? Ashe bari nabar ganin laifin uwarta ita kadai abin ruwan dare ne ashe Allah ya kyauta. Muna nan maji magani wai an bizzine tsohuwa da ranta. Yanzu may ye abin kwadai a furin nan ina dai jinin sune ya hadu da yarinyar nan tun tana karama suke tare ? So kike nace ta daina kulata ko may kike son nayi Allah ne fa ya hada jinin su. Yara nawa ke garin nan wakikaga ta mama idan ba ita ba da Allah ya hada jinin su. Yanzu dai ni may nace kuma wanan ai koyawa yaro kwadaiyin abin duniya ne ba akidar alheri bane . Baba bai kara mata magana ba yajawo turen abincin shi kawai ya soma ci ranshi a bace Da dare na shiga kwanciya har na kwanta a saman dan keson tabar da nake zuwa kwana dashi naji mama laure tana tashina tace ke Rahama tashi muyi magana. Wallahi idan naji kin fadawa sokuwar uwarki ko nawa aka bani gidan Altine sai rayuwan ki ya baci a gidan nan kin dai san halina wallahi ko. Nace ni mama ai ban san ma ko nawa tabaki ba balle na fadi tace munafuka kece baki san kudi ba ? Kin dai ji abinda na fada maki saina lahira yafiki jin dadi wallahi ko. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU MARICCIN KAN DUTSE, , , WANAN LITTAFIN NA KUDI NE CIGABAN SHI SAI DAI ZAKI FARA KARANTA FREE PAGE DINA A KYAUTA YAR UWA IDAN KINA DA RAAYIN HAKAN. 2⃣ Yau da sauri na shirya zuwa makaranta tunda ba tallan safe gareni ban tafi ba sai da na leka gidan mama Altine tukun. Ita kadai ce a tsakar gida tana yan aikace aikacen ta muka gaisa nace ina baki tace wai ke ma kin san ai basu tashi da wuri haka. Tace yau da wuri haka za, a bokon ? Nace mama kin manta anty ta saye tallen nawa sai hutu yanzu tace humm hakane fa na shafa sam. Duk da ance suna barci bai hanani lekawa ba dakin nasu suna kwance saman gadon mama da yasha shimfidan sabon zanin gado. Barci suke hankalinsu a kwance na dan dade tsaye a kan su ina kallon su cikin sha, awa komai nasu gwanin ban sha, awa dashi. Najuya nafito mukaci karo da mama zata shigo dakin tace ai har ina batun shiga na samay ki kada ki tayar dasu da ga barci. Nace kai haba mama, may zai sa na tayar dasu suna hutun gaji tare da su. Nace zan tafi mama sai na dawo muryan ta ne naji tana cewa yaki Rahama. Najuyo zuwa inda take tsaye tana kokarin kwance haban zanin ta data kulle kudi a cikin sa . Naira ashirin ta miko min tana cewa karbi wanan kyaci tara dashi indan kin tafi can. Take fuska na ya sauya nace cikin marairaicewa mama da kibar shi wallahi yau ai Inna ta tabani Naira biyar zai isheni na sha ruwa a can. Tace ruwa kawai Rahama bayan nasan ko karyawa bakiyi ba kika fito daga gida? Nace dimamay mama laure tace baida yawa don haka su dake gida zasu ci abinsu wai idan naje can ban rasa abinda zanci. Mama Altine tace shine kuma ita Inna ki ta baki Naira biyar kacal ki sai mai da naira biyar din. Muryana na tausa kada wani yaji ni nace mama kin san idan tabani da yawa mama fada take mata wai tana lalatani da yawa shiyasa mama ta kafa doka wai Naira biyar kawai za, a dinga bani ya isheni . Kai amma dai laure takai muguwa wallahi nace mama barin tafi kada na makara yau ina son naga assymbly don na manta yaushe rabo da ayi shi dani. Najuya ba tare da na karbi ashirin din hannun nata ba nafice daga gidan da sauri tana kirana amma bai sa na tsaya ba . Koda na isa makaran ta nayi dace da abinda nake son gani ina shiga ana kada kararawan assymbly yau ba duka gare ni zan kuma ga assymbly din mu. Kowa ya ganni sai mamaki daga dalibai har malamai suna cewa, sarkin late yau lafiya kuwa ? Sai dai nayi masu murmushi kawai na wuce haka muka zauna nai matukar jin dadin samun darasin safen da nayi yau. Allah Allah nakeyi a tashi daga makaranta na koma gida na samu anty na yar birni don ni gaskiya ban gajiya da kallon ta ita da yarta mai kyawo. Har zuwa lokacin tashi ranan saurin da nayi har yafi wanda nakeyi zuwa daukan talla na a kullun. Na shigo gidan mu da hakki alaman nayi gudu ko sauri a lokacin sai dai may na samu a gidan mu mama lauratu na sana,an fadan ta da ta saba yi idan fitinan ya motso mata. Duk da har taci ta sude babu mai biye mata indon ta inna tace zata iya kwana tanayi bata tanka mata ko uffan. Sai dai idan baba yana gida ne wani lokacin zaibi ta kanta suyi ta tonon asiri a junan su. Wanan haushin da naji tayi yayi dalilin da na fasa shiga cikin gidan namu na dan daka ta ina sauraren ta don naji akan may take fada kuma. Daga inda nake sauraren fadan nata na fahinci fitina take da Inna na wai akan kudin da aka bani inna bata nuna mata ba taba babana ya dan kara jarin shi. Sai zuwa can naji muryan Inna tana cewa yaya kiyi hakkuri dan Allah ni bawai na nuna bakece kika haifi Yarinyar nan ba . Naga kin san da zancen ne tunda boyar Allah nan a gaban ki ta furta cewa ta dauke ma yarinyar nan yin sana,an ta. Ai fa yanzu sai kiyi kwana nawa ne idan bakin ciki kikeyi dani akan ki zai kare Asiya don wucewa yar gidan Altine mai kuli zatayi. Kuma kowa komawa zaiyi ga turken shi mai cabo ai har kudin nawa ne da suka rufe maki ido haka ? Maimakon na shiga yadda nai niyar yi da farko sai kawai naja na juya zuwa gidan mama altine mai kuli. Tafiya nake kamar banda lakka a jiki Allah ya taimake ni naga kanina zai shiga gida na mika mai jakkar makaranta na nace ya kai min dakin mu. Da sallama na shiga gidan suna zaune su biyu ga kwanon dan wake da mai da yaji tana ci cikin irin cin abincin su na yan gayu. Mama altine ne tace a, a yar gidan anty har andawo bokon ke nan nace eh mama cikin kada kaina. Zama nayi tare da gaishe su naci gaba da tunane a cikin raina wai yaushe ne Inna ta zata samu saukin rayuwa ne agidan mu? Duk abinda tayi batayi daidai ba gurin mama, damu da ita duk bamu da wani yancin kan mu sai abinda mama laure tace. Na sauke ajiyan zuciya ina fadi a raina yaushe ne wai muma zamukai ga namu yancin kan ne agidan mu , ? Jin ajiyan zuciyar dana sauke karama dani yasa hankalin su ya dawo gare ni mama altine da anty sa,ade har suna hada baki ita mama na cewa may kuma ya faru yar gidan anty ita kuma nacewa Rama na duk gajiyan ce haka wai ? Nace a hankali mama ni halin mama laure ne yake min ciwo ace kullun duk abinda Inna tayi ita a gurin ta ba daidai bane ? May kuma ya faru yanzu? Nace mama bakiji haushinta bane har nan gidan wai akan kudin da anty ta bani shi ne Inna nasan tabawa baba kudin ne ga Mama can ta saka inna a gaba da masifa akan may tabashi kufin bata bata ba. Ikon Allah waiko laure na da hankali kuwa mama altine ne ta fadi hakan. Nace mama akullun wanan halin na mama ya damu na inna sam bata da sukuni a gidan mu. Wanda kinga abin har muma ya shafe mu muda ita bamu da incin kan mu ko kadan. Nan kata tunanen yaushe ne wai muma zamu zauna kamar kowa agidan. Nace mama fa har ikirari takanyi da cewa sai dai mu zauna a haka mu da uwar mu don bazata zauna tana ganin ita da mijin ta ba wasu banza can suzo su shige mata gaba. Duk da Inna tana hakkuri da ita kalamanta badu damunta nake gani amma baisa mama ta watsar da wanan halin nata ba har zuwa wanan lokacin. Wai mama kin kuwa san duk saba, an da nakeyi kudin mama laure ce ke karbe su a gurin Inna da sunan wai zatai min tari ko kuma tace wai ta ara. Kuma bawai zata biya bane sannan ni har yau banga wani tari da ake min ba agidan. Wani lokaci idan tace abata kudin na hana don sai yakai ma bamu da jarin da zamu juya awataran. Data gane ina hanawa yanzu shine take cewa idan ina ganin nai wayo ne na kama kaina don dagani har uwana da uban nawa bamu fi karfin ta ba don haka in ina shiga hankalina mu zauna da ita lafiya nayi . Idan bazan iya ba wallahi ko yaushe kofa a bude yake mina dagani har Inna muyi gaba. Anty ce tace kai ashe haka take ina ganin ta a hakan ? Mama tace wa laure da kike gani bata da dama komu makwabta sai munkai zuciyar mu nisa da ita ake zaunawa lafiya. Nace muma hakan muke zaman takura da tsangwama a tare da ita kullun sai ta kirkiri sabon jidalin da ta dora akan Inna don dai ayi fitina kawai. Anty tace kuma shi mahaifin naku duk yasan da haka Rama ? Nace cikin kada kai kamar wata babba dani yasani mana anty may zaice tunda baya iyayin musu kullun da ita baya kuma jayayya da ita sai abinda tace don azauna lafiya. Sai idan abin ya ishe shine yake magana kuma maganan ba amfani zaiyi ba ai. Balle ma yanzu nagane baba yana matukar gudun bacin ran mama sosai sai abinda takeso akeyi agidan mu. Don kinga kan tallah mu ba yadda baba baiso mu bari mu kama boko da islamiya ba amma mama ta hana. Don dai kawaiba zauna lafiya a gidan da ita ko kwanaki an kawo karan Lawisa amma mama ra hana yayi magana dole yai shiru ya kyale ta hakana. Anty tace Allah ya kyauta ni dama zai ban ke mu tafi birni muyi zaman can ki shiga bokon ki yadda kike so daya kyauta min. Nace wai anty idan na tafi birni na zauna waye zai kulla min da Inna ta ko kudin sayen sabulu kawai ya isheta ai. Mama tace balle ma laure bazats bari ba dakike ganin ta na tunda ba yayan tane zaki dauka ba. Ai duk wanan fitinan da kikaji tanayi da ace tare da yarta kike da baza, a ji shi ba sam. Halin Laure sai ita dubi yadda Asiya ta koma kamar ba ita bace ta tashi a garin nan abin sha, awa ga kowa. Amma mahaifinta ya hana ta zabi yacs sai malam Abubakar zaiba don zumuncin dake tsakanin shi da mahaifan ta. Yarinya da gatan ta amma dubi yadda duk ta zuke takoma kamar ba Asiya ba, lokacin da tai yan matancin ta babu wanda zai ganta bai kyasa mata ba. Yanzu gashi tun auren ts gidan nan dubi duk yadda ta tsiyaye babu komai gajikin ta sai tarin hakkuri da zaman sunnu kawai. Anty tace mama ashe mahaifiyan ta takwaso gurin kyau ke nan ? Kai wane ita da kyaun Asiya wanan da bata gyara kai zaikai wata biyu ba kitso kafa ba lalle kamar ba matashiyar budurwa ba da ita ? Nace kai mama duk wanan gyaran da nakeyi zakice haka ina wanka fa sau uku ko biyu a sati 😆 Dariya ne sosai ya kumshe anty tace kai Rama na wankan ma har sai an kidaya kwanakin yin shi kuma ? Nace anty ai nayi kokari bakiji har ana yaba tsabtana ba don fa ina da tsabata wasu ke sayen sana, ata sosai. Dukan su dariya suke min akan maganata niko ko ajikina ban damu ba sai mama ce tace nidai bari na zubo maki abinci kici da wanan bakin surutun naki haka ? Na gyara zama ina ta kawo min dan wake ranan har da ruwan goran da anty ke sha nasha azatona yana da zaki amma sai naji shi salaf kamar ruwan rijiya. Ina gamawa na gyatse dama nasan ko naje gida tuwo ne zai tare ni don haka ban rage komai ba harda sude kwanon nayi. Anty tana ganin haka tace dani ko a karo maki ne idan baki koshi ba nace sai zuwa anjima Anty yanzun kan Alhamdullahi. Tace oya zo na banye maki kanki nai maki kitson shi duk da take na manta ko yaushe rabona da yin kitso a duniya. Ina bude kaina saida tai wani irin ihu tace Rama subbahanallahi kanki ne haka nace shine anty yayi yawa ko ? Tsuki naji taja tace haba Rama kamarki kuma kinkai har secondary ace baki gyara jikin ki sai yaushe zaki koyi gyaran jiki kuma ? Haka zaki dingayi agidan mijin ki idan kinyi aure ki dinga zama da kazanta yace kina wari. Kunya maganan ta yabani na tsune kaina akafa nace aure Anty ina nai aure wazai zauna da inna ta yana taimaka mata da diban ruwa da tallah kuma ? Kinaji na idan kina son mu shirya dake daga yau duk sati ki dinga kitso da kunshin da mama tace idan ba haka ba wallahi wanan kazantan zai sa mu bata dake. Nace insha Allahu anty zan dinga kitso bani son mu bata dake ko kadan a rayuwana. Tace dakin kyautawa kanki haka taci gaba da sance kan har wani gari ke zuba a cikin don dankarewan dayayi. Dama asalin haduwan mu da ita shine yawan gashin da nake dashi. Watarana tazo garin inna takaini an min kitso ya sauko har bayana taga mun shigo gidan mama Altine sayen mangyada take cewa kai wake wanan fine girl din a kauyen ga kyawon yarinyar na ace a birni kika fito da kinsha gyara yarinya. Tace zo nan ban mata kiuya ba nazo ta rugumay tana cewa kina so na na kada mata kai alaman eh. Tun rana muka shaku da ita da zan koma ta saya min biscuit da sweet naje dashi gida amma mama tana gani ta kwace ta rabawa yayan ta lokacin ni kadai ne a gurin inna ta ban da kanne baya na. Wassh nace don jin zafin kan da anty taja min da karfi tace yaya akayi kuma nace babu komai idanuwa na sun ciko da hawaye da zata gani kila zata barni don akwaita da tausayi sosai. Tana gamawa ta sa asayo mata clean ta wanke min kan tas dashi sai da naji wani iska yana shiga na sosai acikin kaina. Mun zauna tafara min kitso ke nan sai ga Rakiya diyar mama tashigo babu ko gaisawa tace to akwadaita mama tana kiran ki. Nace cikin daure jin zafin kitso kice kitso ake min gani nan zuwa idan angama min. Tace mama tace tana kiran ki shine zakice wai ana maki kisto ne barin je na fada mata kince bazaki zo ba. Anty tace bari na sake maki idan kin dawo sai mu karasa ko ? Nace taci gaba don nasha zafi daya yanzu idan na tafi bazata bari nadawo maza ba. Ban tafi ba Rakiyan ma bata dawo ba daga sakon har aka gama min kitsona nai wanka wasu kaya daga cikin tufafin ta sun min yawa sosai amma haka tasa na saka su na fito wata shar dani. Sai da na gama komai na kama hanya na nufi gidan mu nan na tar da balain dake jirana na mama. Ina sallama tako haukaina da balainta tana fadin mai kwadai baji dadi ba wallahi yanzu don kina isar sa ke kinga gurinci shine na aika kizo kikace ace min bazaki zo ba sai kin gama kwadayin ki ko. Bari mahaifin naki ya dawo gida yau ai ayita akare don wanan abin baku kadai da uwarki za, a zaga ba harni sai an hada dani an muna suna indai kauyen gane. Kuma ki tafi ga diban ruwa can yana jiran ki tunda babu bawan ubanki da kika aje da zai debo maki ruwa ai aiki dashi. Ban tanka mata ba don nasan ko na fada mata yadda mukayi da Rakiya ba yarda zatayi ba. Kayan jiki na na cire na daura tsuman zanina na fara diban ruwan don nasan idan banyi har inna ranan sai ta yabawa ayya zaki. Saida na cika mata randunan ta na fara cika na Inna na don ban isa na fara zuba a namu ba naja bala,i kuma. Ban koyi rabin randan mu ba sai ga Lawisa tafito da roba tana diban ruwan rabi a cikin roba rabi a kasa . Kasa daurewa nayi nace haba lawisa wanan ai hainci ne idan ma zaki dibane ai ki tara roban dakyau mana amma kina diba kina zubarwa akasa don baki san wahalan diban ruwan ba ko ? An zubar din ko zaki hanani amfani da ruwan ne kuma tunda wuyanki yai kwari yanzu ya isa yanka don kina ganin kina hurda da yar birni ana hure maki kunne kiwa mutane rashin kunya. Nace ashe hurda da yan birni isa ne ai ban san kina hassada da hakan ba sai da kikai magana yanzu? Kafin tabani amsa sai ga mama tafito daga dakinta tsagal tace eyye Rahama lalai kuwa ashe wuyan ki ya isa yanka yanzu yarki kikewa shamaki akan ruwa don ta diba. Saboda kina kurin kece kika debo ko may ai kafinki fara diban ruwa su suka fara kuma akai amfani dashi. Kamar ince bako ga Inna ta ba don da wayo na akai fadan ruwa agidan mu wai don may babana yake debowa innata ruwa. Kuma alhalin ita bata bari yaranta su diban ma Inna ruwa anata randan haka inna zatai ta zama ba ruwa koda kuwa girkin gida ne zatayi. Tun ranan baba bai sake diban wa inna ta ruwa ba sai dai ta dinga tarataran yaran mutane suna dibo mata. Tun ban kai munzalin iya jan ruwa arijiya ba dole haka na fara zuwa bakin rijiya wanda yaga Allah ya taimaka ya zuba min har na samu Inna ta dan samu na aikin ta. Muryan mama ne ya katse min tunane na tana fadan ta da cewa yanzu don kinga kin girma kin iya hassada da kyashi irin na uwarki shine zaki hana ai amfani da ruwan ko ? Ni dai ban kara magana ba na fita raina bace daga gidan sai magariba na gama diban ruwan a gurguje na shiga naiwa anty sai da safe. Tana ganina a jiki cikin tsuma babu dadin gani tace yaya haka kuma Rama na ? Na turo baki gaba nace ba mama bace saida tasa na cika duk kayan ruwan dake gidan mu kuma ban gama ba Lawisa tana diba tana zubarwa nai magana kuma ta hauni da zagi wai don naga ina hurda dake ne nake wa mutane rashin mutunci. Kai ikon Allah yanzu har nima na samu shiga cikin ran mama daga zuwa na ko ? Nace ai har yaranta bakin ciki suke da ke wai don naga kin fito daga birni nake lake maki ina kwadayi. Allah sarki ni may nake baki da zasu ce haka Allah dai ya rufa asiri wallahi shaf na manta da zancen ki da sun ga aikin gaiyya kuwa. Nafita da sauri na koma gida kada aga na dade inna tai min fada don ni ko tallah naje bani kai magariba koda kuwa ban sayar ba ne. Sai bayan sallah ishai baba ya dawo daga kasuwan kauye yana jaye da wani dan karamin rago da yasayo daga can kauyen da yatafi. Baya ya daure ragon wanda ya cika muna gida da kuka irin na dabbobi kowa yasan an shigo da dabba. Mama tafito daga dakinta tai mashi shimfida inda yake zama yaci abinci ya huta idan ba zai fita ba hiran dare wanda shi ba kasafai yake fita ba don yafi fita ne idan suna siyasa ko wani abu mai muhinmanci a garin. Bayan ya zauna muka dinga fitowa muna mashi sannu da zuwa wanda zance kusan mu yan dakin mu ne keda wanan halin. Sai nice nafito karshe don ina sallah koda ya dawo lokacin na gaishe shi na juya zan wuce ne naji Mama tana fadin dama kai nake jira ka dawo tun dazun. Yace to ai gani kuwa Allah ya dawo dani lafiya cikin ku tace dama akan Rahama ce . Don dakai da uwarta kun daure mata gindi akan bakuwar birni da tazo don kunga kudi idanuwan ku sun rufe . Shine take ganin kowa tana iya takawa ta zauna lafiya yanzu wai har na aika don ta samu daurin gindi daga uwar ta tace min wai bata zuwa tana kitsone. Ni zata gwadawa kitso tunda tun uwarta bata san duniya ba nakeyi a kaina. Yanzu dai may tayi baba ya katse dogon sharhin data fara cikin tambayan ta ba, asi don baison suyi jidali daita gashi ranan itace da girki a gidan. Yasan idan yaja zance cikin shi tayi don daren shi ke nan zai kashe a ranan. Tace ruwa fa zata debo bayan tasan cewa itace da alhakin diban ruwan gidan nan akanta amma uwarta najin amsan da ta aiko min bai sa ta dauki mata ki ba jifa ? Yanzu ita Asiya da taji abinda tace bata dauki mataki ba akai ? Tace ta dauka ran yar gwal din ta ya baci ita ma nata ya baci, yanzu ta debi ruwan ko bata debo yar kwal uba ?. Tace ta debo amma kuma sai rashin mutunci yabiyo baya nan tai muna tas nida Lawisa wai don may tana wahala ana zubarwa jifa wai aikin gidan ubanta ne wahala ? Ina daga daki daga ni har Inna ta muna sauraren maganan da mama keyi karya da gaskiya . Cikin bacin rai ya kwala muna kira ni da Inna ta bamu dauki lokaci ba muka fito inda yake zaune. Tambayan dalilin dayasa Inna tanajin sakon rashin kunyan da na aikowa mama dashi taki daukan mataki a lokacin. Cikin murya mai sanyi Inna ke magana tana cewa haba malam yanzu don ban da kunya zan saka baki ga maganan yarinyar nan da maman ta ? Aikuma sai ace nayi rashin kunya kuma baba yace ke nan kina nufin karya Lauratu tai mata ba amsan banza ta aiko mata dashi ba ke nan? Inna tace ni bance karya yaya tayi ba dakai da ita sai ku dauki hukuncin daya dace akanta basai kun fada min ba. Au to haka ma zakice ke nan ko ? Inna tace idan ba haka zance ba ni may kake so nace yar tace tana iya daukan matakin daya dace akan ta duk sanda taso. Mama tai karaf tace wace ni na dauki mataki abi gari dani ana nazalunci uwa da yar ta don cin amanan dana iya Sai ranan naji Inna ta ba da amsa mai ingaci da tace uhumm zalunci kan ai sai dai kada a kara don kullun a cikin sa muke raye, sai ranan da mai ramawa zai rama muna idan ba yafewa mukayi ba. Ai Inna ta na fadin haka da ga baba har mama sukoyo cikin ta da masifa kamar zasu cinye ta danya a ranan. Wai tayi masu Allah ya isa shi da mama ke nan take nufi akan yar ta na suka sakata gaba da wullakanci kowa yana fadin albarkacin bakin sa. A take naji jikina yahau tsumi ina ta dan karkarawa daga inda nake a tsugune kamar na tsoma masu baki ga zancen su wata zuciya ta haneni da hakan. Na rasa yadda zanyi a inda nake yadda ake ciwa uwata mutunci yau akaina gaba daya kwanakin nan baba ya karkare birkicewa akan mama a gidan. Duk abinda ta fada ya zauna ke nan daram ba canji cikin sa . Nasan idan na saka bakina ga zancen abin zai kara muni gashi yau alama ya nuna inna ta fara gajiya da halinsu har takai ga fara bada amsa da bakin ta . Don haka na mike tsam na juya zan tafi daki muryan mamace ke cewa dani ina zaki rasa kunya an sallamay ki ne ? Bari ta nuna min ta isa mana tunda uwarta ta daure mata gindi inji baba yake fadin haka. Ke maza shiga daki kada ki dawo gurin nan kinji na fada maki so kuke da ni da ita ku turke mu kuyi muna wankin babban bargo don bamu dagata kuke gani ko? To bari kuji gatan muni dayara na Allah a gidan nan da duniyan nan kai nagaji da wanan halin cin amana kullun mune dai masu laifi a gidan nan ku bakwa yi. Idan wani laifi ne ai babu dan da baya laifi ni dan wa nataba kawowa kara duk da urin kuncin rayuwan da ake min a gidan nan ina sa kafa ina takewa daga haka ta juya tabi bayana zuwa daki. Ranan daga ni har Inna babu wanda yaci abincin dare ba, a ma taya muna balle muci. Shekaruna da kurciya na bai hanani fahintan ranan Inna tana cikin kunci da bakin ciki akan dalilina. Daga inda nake zaune takure bakin gadon karfen ta na mike zuwa inda take zaune saman tabarman sallah ta na tsunguna nace. Nace Inna don Allah kiyi hakkuri duk nice na jawo maki wanan bacin haka da ba don ni ba bazaki shiga wanan bacin ran ba yau. Batai magana ba sai na kara cewa don Allah Innan mu kiyi hakkuri ki yafe min. Tace ke nagaji ne da irin cin kanshin da ake min a gidan nan don may har in suna ganin kinyi laifi ne bazasu hukuntaki ba sai sunkirani don raini sun hada dani. Saboda yana son gyarawa matar raine zai dinga min wullkanci a duk lokacin da ya bushi iskan shi ko may ? Nagajine wallahi ni may ye yaran yaya basuyi min a gidan nan waya taba jin nayi magana balle nace itace ke daure masu gidin sai ni da aka raina za aiwa cin fuska yadda akaso. Shiru shiru aiba tsoro bane don sunga ina basu girman su shine zasu dinga takani yadda sukaso. Inna na kaiwa nan sai ga baba ya daga labulen dakin mu yana fadin ke Rahama daga yau sai yau kada na kara ji ko ganin kin kara hurda da bakuwar birnin nan don ba yar uwarki bace ban san dalilin ki na manne mata ba to na hana wanan hurdan daga yau. Yana fadi haka a cikin daga murya nasan yana fadi ne don mama taji ya yanke alakata da Anty. Abinda take muradin gani daji don tasan zamana da ita babban alheri ne ga rayuwan mu idan bata hana ba. Zama guda ta kashe min kudi haka har jakka sittin ba gaira ba dalili akaina. Yana gama fadin haka ya juya ya cuce a cikin hasala babu wanda ya tanka mashi yabar dakin dama yayi ne kawai don dadin ran mama takuma ji dadin. Sai bayan tafiyan shi Inna ke ce wa an daiji kunya wallahi mutum har mutum amma baida ta cewa a cikin iyalin shi sai yadda akace mai. Hakkuri na kara ba Inna don nasan yau kan ancin ma rashin hakkurin ta a gidan. Duk da karancin shekaru na ina iya fahintar wasu al, amuran da akeyi a gidan mu wanda ko kadan bai dace ace anyi shiba a tsakanin iyali. Amma gashi da karancin shekaruna yakai har na fahinci hakan a gidan mu, kai bani kadai ba duk yaron dake gidan mu yasan irin zaman rayuwan da akeyi a gidan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, 3 IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA, , , Shiru mukayi dakin akan hukucin da mahaifi na ya yanke ta alakata da anty birni, yanzu baba akan su mama ya rufe idon shi ya yanke wanan hukunci haka duk da yasan mutunci ne ya hada ni da ita ba wai kwadayin da suke ikirari bane. Muryan Inna ce take ce min kin dai ji may ya fada don haka sai ki san yadda zakiyi da shiga gidan mai kuli. Waahegari ban tafi makaranta ba sai da na faki idon mutane na leka gidan mama Altine muka gaisa dasu na wuce. Haka ma da na dawo ban shiga gida ba sai da na fara shiga gidan gurin su . Hakana wuni ina fakin idon mutanen gidan namu ina fita zuwa gurin anty sama sama. Ganin haka yasa suka fahinci akwai matsala na fito zan tafi diban ruwa na shiga gudu gudu gidan. Nan ne mama take tambaya na ko may ke faru ne yau na kasa tsayawa kamar kullun. Ban boye ba na fada masu komai da ya faru a gidan mu har baba ya hana ni shigowa gidan su. Mama ce tace to babu laifi ki natsu ki zauna gidan ku kada kuma ta sa aiwa Innan ki wani abin. Kin san ance mai hakkuri dama bai iya kai karshe ba sun kai ta karshe ne tunda ta fara basu amsa yanzu. Allah ya taimake ni aahe mama ta saka ido sosai a kaina kozan tafi gidan mama altine a wunin nan. Ganin ban fitaba yasa ta fara sakin magana a tsakar gida tana cewa ai na dauka ko ba abin dokar mune inwa uwa da diya dukan tsiya yau a gidan nan. Idan shi ya kafa doka ba,abi ba ni dole na kafawa mutum ko baiwa Allah dole ko abi. Ke a dole wai ga yar gwal ba, a tabaki uwar ki ta shigan maki ba kunya ba tsoron Allah. Inda ma mutum nada wani asalin kwarai ne har zai muna yanga da kyau yo ina kyaun ma yake don dai haske fatan da ake kuri dashi kawai bayan shi din sai may kuma ? Inna dai bata tanka taba sai ci gaba take da masifan ta tana cewa ni za, a gwadawa rashin mutunci ni da mutunci ya ganni ya gudu. Idan kace zaka shiga tsabgata wallahi sai inda karfi na ya kare a kan mutum duk da haka kana doso ni da rashi mutunci in kama mutum in mashi dukan tsiya a gidan nan inga uban da zai ramawa mutum. Mu dai muna daki abin mu muna jin ta tana faman haushi tana neman mai tanka mata ta sauke mai. Da babu wanda ya tanka mata sai ga lawisa ta dawo da kayan sana, an da mama ta dora mata batai ciniki ba. Nan mama ta juye fadan kan yar ta tace shiyasa ake ganin daman ku ana maku yadda rai yaso harda sheri. Ko da yake kubaku iya shiga lungu ai maku juye ai abinda akeso da ku ba a baku kudi. Mama tana nugin nice mai shiga lungu da maza da sana, ata ana min juye idan anyi lalata dani. Ban san lokacin da na ce Allah ka isar min ban yafe ba sai Allah ya , , , Marin da Inna takaiwa bakinane yasa naja nai shiru ban karasa fadin maganan da nake fadi ba. Tana cewa kul na sake jin kina jawa babba Allah ya isa sai na fasa bakin nan naki. Duk wajawo min wanan bake da ban isa na tsayar dake inda naso ba da kin dauki sana,an ki kin tafi wa zai ganki a gida yai maki maganan banza haka. Kamar nace Inna aiko bani gida mama zata fadi hakan ne a kaina don bayau ta fara fadin hakan ba. Da dai tagaji da fadan naji tana cewa ai tunda abin haka ne wallahi mu zuba da mutum a gani. Inna tafito yin alwalan la, asar ne mama take cewa kada ta dibi ruwan randan ta don dashi take son yin wanka don randan ta ba ruwa a cikin sa. Inna bata saurare ta ba ta duka tana diban ruwa ne ta ji saukan duka a bayan ta daga gurin mama din. Yaya abin yakai harda duka tace na doke ki ko zaki rama ne mara mutunci kawai. Ta sake daga hannu zata kai wa Inna duka ina tai cikin ta Allah ya bata sa, a ta kwashe kafan mama tai kasa tim, ta bita ta haye taita dukan ta. Ga mama babu ko dan buje a jikin ta sai tsiraicin ta da ya baiyana a fili lokacin. Jin haya niyar sau yasa mukayo waje gaba dayan mu muka shiga ihu don bamu taba gani ba. Ganin haka su Lawisa suma suka far wa Inna da duka ina ganin haka nai kan lawisa sauran suka biyo ni suna duka Allah yaban sa, a na jefa ta a randan ruwan su saida ya fashe. Ta samu targade ta yanka wani irin ihu kamar ranta zai fita a lokacin ganin haka Isa ya dauko tabarya yai kan Inna dashi bai kai ga buga mata ba ni rike shi yai baya yafadi kasa shima sai da yaga wani wuta ya gifta mai. Wani ihu suke kurma wa na neman taimako mama tace shigiya mai karfin doki wace ta san ma diyan ta mugun abu. Su mama altine da wasu makwabtane suka shigo don jin kururuwan da yai yawa a gidan. Da kyat aka banbare Inna ajikin mama sai zagi da ashar mama ke faman sakewa aka bata zanin ta, ta daura. Inna tace sakariya kawai wawiya wacd bata riki darajan ta ba balle na uwargidancin da bai amfana mata komai sai zalunci an fada maki shirushiru tsoro ne dama. Mutane sai fadi suke asha Lauratu mai yakai wanan taasan haka bayan karfi ba daya ba ? Gaskiya wanan abin dai kan baiyi dadi ba wallahi yarinyar nan tana maki biyayya yadda ya kamata karami yai wa babba amma sai da yau kika kaita bango. Makwabta kowa na fadin albarkancin bakin shi abindai kan baiyi dadi ba wallahi don babu wanda bai san halin da gidan mu ke ciki acikin su. Har da anty Sa,ade sai da tashigo gidan dauke da yarta a hannun ta tajani gefe tana min nasiha yadda ya dace. Jinya sosai mama tayi a ranan har dare suna daki ita da yaran ta da sukai tangarde tana jiran dawowan baba. Tun a hanya yan unguwa suka tare baba suka fada mai tare da bashi shawaran ya saka ido ga halin da iyalin shi suke ciki don babh inda akejin wai kishiya don samun guri ta daki kishiyar ta koma wacece bazata kyale ba . Haka yasa koda baba ya dawo gida bai dauki wani matakin da mama taso ya dauka ba. Ganin baba bai dauki matakin da taso ba na farwa inna ta da duka ya rama mata ba ita da diyan ta. Wanan zance yasa har saida Iyayen mama suka ziyarci gidan mu nan suka zauna kowa ya mayar mai da bayanin kan maganan. Nan dai suka taru suka bawa mama rashin gaskiya yadda ya dace akai masu nasiha da suci gaba da zaman lafiya. Tun daga wanan ranan mama ta kwashe kayan ta na aiki dake a tsakar gida ta boye kuma wasu ma da kudin sana, ata aka saye su. Nice nake labartawa anty da mama take anty tabani kudi tace kada na koma gida naje na sayo wa mama duk abinda bata dashi komai da yakamata na aikin mu saida na hado shi kamar wata babba can dani. Aiko mama tana ganin haka hankalin ts kuma ya tashi ta fara sabon habaici tana fadi sai dai haka dama an samu kayan banza ana amfani dasu. Take cewa wai na dauki kaina na saka a cikin kishin su ai tasan magani na indai itace. Wanan kalamin na mama da takance wai tasan magani na kullun na rasa wani maganin me zatai min wai ? Mu dai bamu biye mata ba haka zaman ya koma na doya da manja a gidan na mu. Naji dadin zuwan anty Sa, ade a wanan lokacin don ko ba komai ta fitar min da uwata a kunya. ****** ********* ****** Ban san da zancen tafiyan anty ba sai dana dawo daga school nashiga don nagan su. Sai mama ce kawai na samu a gidan cikin karaji nace mama ina antyna ? Idona yana gurin da kayan ta suke a dakin mama, murmushi mama tai min tace yar gidan anty ai yau anty ki tai muna na baki. Dazun mijinta yazo ya dauke ta suka tafi sun koma birni inda suka fi wayo in ma ba don Saade yarinyar kirki bace ina zata iya zaman garin nan har tsawo sati daya haka? Inda kinga irin daulan gidan iyayyen ta da na mijin ta ai bakyace zata iya ko zama ba anan din. Duk wanan maganan da mama take bana jin ta don nayi nisa ga tunane ina fadin yanzu shike nan anty ta tafi tabarni zan koma ga turke na mai cabo ke nan na talla. Gashi dan kwana biyun da nayi bana talla har na dan yi kyau na koma wata wayayiya dani. Ashe anty tasan zata fi a yau shiyasa jiya tasa na sance kaina tai min wani sabon kitso a kaina duk da wancan na farkon da tai min bai tsufa ba? Muryan mama ne ya katse ni tana cewa ga sakon nan ta bayar abaki tace kiyi hakkuri idan ta samu hannu na gari zakiga sakon ta. Dakin ta shiga ta dauki min wasu kaya tufafi ne na anty da na santa dasu na jikin ta, ta bani. Sai sauran tarkace irin su sarka takalma da gyale da sauran su ta bani nai amfani dasu. Haka na karbi kayan jikina duk a sabule na juya jiki ba lakka zuwa gidan mu inajin kamar na kurma ihu a lokacin. Mama tabi bayana da kallon tausayi tana mamakin wanan irin shakuwa dake tsakanina da yarta tun ina karama. Don itama antyn ta tafi dani a baki tana fadin Allah sarki wallahi mama da mahaifin Rama zai yarda dana wuce da ita kano taje can tayi karatun ta . Mama tace raba kan ki da zancen yarinyar nan Sa,ade iyayyen ta basu da mutunci don basu san haka ba. Wanan dalilin yasa taja bakin ta tai shiru ba don ranta yaso ba ta kyale zancen. Nan na dawo kan sana, ata ban ko tsaya Inna tai min umurni ba na dauki wake na wanke nakai nika da sauran abinda ya dace inyi. Ganin ina wanke wake yasa mama take cewa yau kuma karya ta kare wa buddari ne za, a koma inda akafi wayo. Ban dai kulata ba naci gaba da abinda nakeyi don na nasa a raina washe gari bazan shiga makaranta zan zage naiwa Innata sana, a ne don nagane shine kawai rufin asirin mu a gidan. Na dade a zaune ina kwalliya irin ta mu na yan kauye idan zamu fita nacewa inna na dauki kayan da anty tabani ne na saka. Tace ba naki bane idan zaki saka sai kin tambaye ni na jawo ledan kayan da tunda nashigo dasu ban bude ba tun jiya sai a lokacin nan. Na fara budewa naga emvlove a ciki a mike a hankali na bude kudine yan duba a cikin har dubu ashirin sai yar guntuwar takardan da ke ciki. Da mamaki na dauki kudin na kiraga duba ashirne cif din su sai na dago kai na kalli Innata data kura min ido. Takardan na bude na fara karantawa ga abinda tace a cikin takardan kamar haka. Rama na nasan lokacin da zaki samu takardan nan nakai kano kiyi hakkuri ban fada maki yau zan tafi ba don kada ki fasa zuwa makaranta da fatan zakiyi hakkuri ki kula min da kanki. Ga kudi nan daga ciki nakine kibawa Inna bana son kina wanan tallan a rayuwa na idan sun kare insha Allahu zakiga sakona. Kada kiyi wasa da karatun ki kidage sosai don watarana ki samu ki taimakawa Innan ki don tana bukatan taimakon ki sosai saboda halin da kuke ciki a gidan ku. Dafatan zaki fahinci abinda nake nufi naki antyn ki Saade sa, adu rano. Kifewa nayi ina kuka a gurin wanda ban san dalilin yin kukan nawa ba a lokacin ko na may nenw? Sai da nayi mai isata na fita na wanke fuskana na dawo na shirya na fice daga gidan dauke da roban tallan wara na. Ina fitowa mutane suka fara tambayana ko nayi tafiya ne kwana biyu sun daina ganina a garin. Ba wani cikakken amsa da nake basu sai kawai ina nan boko nake zuwa shiyasa. Saura kadan ya rage min a roba don haka nai haraman komawa gida don nasan yanzu diban ruwa yana can yana jirana ko karfe nawa zan kai a wajen tallan. Ina tafe bugujan buganjan dani a cikin sauri naji muryan dattawan nan dake zama a gindin cidiyar uguwar mu suna fadin ke mai wara kawo wara mu dan taba. Ban ja ba na juya zuwa gurin su inda suke a zaune tare da durkusawa na fara gaida su tare da aje roban a wara a gaban su. Nawa nawa ne dayan ya tambaya nace mai biyar ashirin yake yace to kiba kowa na ashirin anan. Na shiga saka masu na ashirin a leda ina mika masu daya bayan daya suke karba. Don ina gurin bai sa su fasa hiran da sukeyi ba na matan su sai faman dariya suke a tsakanin su. Muryan dayan naji yana cewa ka samu daidai wanan ka saka a gida ai damana da sanyin bana lafiya ga mutum. Sai suka fashe da wani irin dariya fuska na a daure daidai lokacin da na gama mika masu a sanyaye nake cewa na gama zan tafi. Dari biyu ya miko min ina kokarin banye kudi na bashi canji naji yana cewa a, a ki bar canji kawai ki tafi dashi ai gobe ma ma hadu ko ? Cikin sanyin murya nake cewa Inna ta ta hanani rike kudin maza a guri na don haka ga canjin ka na aje mai a gaban shi ashirin uku na mike tare da daukan roban tallah na bar gurin cike da jin takaicin su. Ina ba da baya naji daya na fadin ga yar gutsun uwa arziki na binki kina ki dan shashanci kawai. Daya ce bata san arziki bane in bashi ba aiko yaro mara hakori yasan sa, a a yanzu balle ita da tafito cikin rana nema. Mai kudin yace ku kyale ta in kunga haka tarbiyan da uwarta tai matane take bi dagani danya ce shatab. Sai duk suka sa dariya a lokaci daya dayan yace yaya dai mutumina sai naga kamar fa ka kyasa Allah ? Yace ko na kyasa may wanan yar shilar zatayi dani da hurhura na har a mugun guri. Cab di ai sai dai idan ka tsuke aljihunka ne za, ace ba, ayi dakai zamanin nan amma ina wani hurhura can kawai watarana sai ka nema ka rasa kana kwasan kurciya gurin yar yarinya ka huta da wa yan nan tsufin kwaman kwana biyu. Ayi haka ga yara ina zan kai wanan yar shilan cikin wanan dabin iyalin nawa ai sai su farwa yar mutane tun dai ban ce ma kaciya ba ? Aff ina ruwan ka da wanan mace ce ma fa ita kada kaji mamakin ka shigo gida wataran kasamu ta zage tana masifa a kan ka. Dariya sosai suka kwashe dashii har nai nisa ina jin sautin dariyan su na shige gidan mu abina tafe nake a cikiin sa, a na akoda yaushe haka Allah yai min baiwa ni. Abinci na dan tsakura na kwabe kaya na tafi diban ruwa marance da nakeyi. Sabbin robobin da na sayowa inna ta saida na cika su taf da ruwa na kawo marafan su na rufe su akofan mu. Shine yaba mama haushi sosai tace wai karama dani na iya bakin makirci kamar wata tsohuwar mace. Da baba ya dawo ina ta tare shi da zance wai bata san inda muke samun kudi ba da inna na yanzu ya duba yaga irin kayan da muka saye ? Idan ba dai maza na fara bi ba ina kawowa Inna ta kudi muna shagalin mu a daki ba wanda yasani.? Ita ba don komai tai magana ba don zama tare ne kada wani abu yazo ya samay ni ace tana gidan ta sa ido. Baba ya hasala da zancen sai gashi ya daga labulen dakin yana cewa ke Asiya kki fada min gaskiya gidan uban wa kuke samun kudin da kuuke wanan bushashan haka agidan nan keda yar ki ? Shiru inna tayi har saida ya kara maimaita tambayan shi gareta ba dake nake magana ba ne wai ko bakiji may nace bane ? Iinna tace bada amsa baida amfani don ko na fada ba yarda zakayi ba tun da an fada ma sheri. Ni dai nasan kulba dade kulba jima Allah yana tare da mai gaskiya komai dadewa kuwa. Yace to yayi kyau ya juya ya fita da daren nan Inna ta shiga gidan mama altine da kudin da anty tabani na karatuna. Bayan sun gaisa tai mata godiya take cewa mai kuli nazo gurin ki ne don ki bani shawara akan kudin nan. Kinga kudi bazasu aju ba don haka nazo neman shawaran ki da na aje kudin nan a guri na sai naga kamar na baki su ki sayowa yarinyar nan kayan tari ki barsu anan gurin ki kamar zaifi. Don ko na barsu ban san ranan da zan sake samun irin su ba haka sai ma mu dinga zara da guda da guda har mu kashe su ga banza. Idan kuma yaya ta gane karshe ma rance su zatayi tace zata juya muna don ni ko malam ban son yasan da zancen kudin nan yanzu. Mama Altine tace kin kawo shawara mai kyau Asiya nima sai da nai tunanen haka tun farko. Amma sai na bari naga hankalinki da fun tunii kike wanan dabara da tallan yar nan da yanzu ansan abinda aka aje mata ai. Amma kin bari ana maki wayo kullun ana karbewa baku aje komai ba sai bakin wahala ke a wahalce ita yarinyar a wahalce. Inna tace to ita yarinyar takice indan anyi maganan haka sai tace ita karatun boko zatayi mai zurfi irin na anty ta. To ke kyabi tana ta ballantana a kauyen nan yaushe karatun bokon ya mace ke zurfi suma ainaga sun jima suna karatun don tana son abin. Yanzu da miji yazo zakiga afitar da ita karatun ya tsaya ke nan cak ba ci gaba sai wahalan aure ya biyo baya. Ai mai kulli mukan kauye ana kwarar mu wallahi kai wahalaa dan ka a wahala shine rayuwan mu kawai. Tun wanan lokacin Inna take daukan dan riban da muka samu ga tallah bayan ta cire na amfanin mu take kaiwa mama altine ba tare da sanin kowa ba. Zancen da mama tayi na zuga baba ina samo kudi ba asan inda nake fitowa dashi bane yasa aka kafa min doka akan talla sau daya a wuni. Haka yasa har na mayar da hankali ga karatuna daga baya ma sai na kirkiro sana, ata a kofan gidan mu anan nake suyan warana shima din nan a take na sayar da abina na shigo gida. Hakan kuma sai ya jawo sabon fitina gurin mama again take cewa wai maza nake tarawa a kofan gidan mu ana abinda bai dace ba. Shima baba yai fadan shi har yagaji baida yadda zaiyi ya hanani talla ne da yahana ni yadda ya sha zugi gurin mama din. Ina aji hudu akai min jumping a school din mu don kokarina don munyi debet na sa school din mu tayi nasara na samu wanan daukakan haka. Nan ma mama tace ai inba ina tare da malaiman ba babu yadda za, ai min hakan ni kadai don banfi kowa a school din ba. Nan ma baba ya hau ya zauna akan zance haka ya jawo mama tasawa karatun nawa kahon zuka sai da a ka dakatar dani daga karatun boko na ga baki daya hankalinta ya kwanta. Tsayawa fadin irin bakin cikin da naji alokacin bata bakine gurin fada. A makarantan mu sun samu labarin babana ya fitar dani daga makaranta haka yasa suka tausaya min sukazo har gida suka samay shi kan zancen. Amma yace suyi hakkuri abar zancen da suka matsa mai yace a bari sai yayi shawara tukun. Badakowa zaiyi shawara ba nasan da mamacd idon itace kuma babu yi ke nan na sani. Daya tunkare ta da zancen cewa malam mu ne sukazo akan zancen dakatar dani daga kararu sai cewa mama tayi dama may na fada maka ? Tare take dasu yanzu sunga basu samun ganin ta su kwakwaleta shine suka biyo sawun ta har gida. Nan baba ya kara turjewa bazan koma karatu ba idan mana samu miji aure zai min kowa ya huta. Jifa ga Lawisa ga Rukaiyya da Naja wai amma nice baba ke maganan aure na. Ganin za, a cuta min a gida yasa shugaban makarantar kai karan babana a gidan maigari. Kan zasu cutawa rayuwana kasancewa ta yarinya mai kwazo ga karatu ya kamata ace ko dai secondry din ne na gama ai. Da kyat baba ya yarda koshi sai da maigari yai mai jan ido ya yarda don yasan idan yadawo gida akwai matsala tsakanin shi da mama idan taji zan karasa karatuna a shekaran nan. Haka kuwa akayi don ranan ba karamin tashin hankali akayi ba tsakanin baba da mama. Take cewa ai dama har dashi cikin cin kudin da mazan dake lalata dani suke bani. Idan bashi ba don may zaice sai na karasa karatuna may ye amfanin karatun diya mace na boko da za, a kare shi a gidan miji. Tana kurin tana karatun boko watafi kyau da za, a nace kan sai nayi boko nakai wasu can daban Ni dai tunda naji baba yace na shirya gobe na koma makaranta nake cikin farin ciki da zumudi don ina gani kila ina da rabo ne a duniya. Washe gari tun da safe na bar gidan duk da na saba idan zan tafi sai na sallami kowa na gidan kafin na fita. Yau ma dana shirya munyi sallama da inna na nufi kofan mama tun ban karaso ba tana hangoni take cewa za, a yawon tazubar din ko akuyan daure ta samu saki. Duniya ce dai ayi ta a sannu don maza ba abin goyo bane da sun gama yayin ka su ka hango wata kai kuma ka tashi aiki ke nan. Ni dai ban biye taba nace mama ni na tafi kafin ma naji amsan da zata bani har na fice daga gidan ko. A kofa na hadu da babana da zai shigo gida na dan rabe gefe nai mashi ina kwana yabini da harara yana cewa har zaki tafi ke nan ? Nace eh baba yace Rahama ki kula da rayuwan ki kada ki ja min abin kunya a garin nan. Duk dai har yau babu wanda ya taba kawo min karan ki na assha amma dai kuma maganan maman ku abin dubawa ne. Don diya mace ba, a saka mata ido tayi yadda take so dole sai da tsawatawa akai. Nace nagode baba insha Allahu zan fake na tafi ina tunanen halin baba idan mama bata kusa zakaji ya dan sanyaya ma al, amarin mu . Amma da zaran yaga idon mama damu da makiyan shi duk daya muke gare shi kamar zai yanka mu da ran mu. Bani ba har yan kanne na biyu hakan ya shafa don dai kawai su maza ne basu zama gida su. Ina isa makaran ta ban tsaya ba sai office din malam Mudi don nasan shine kadai zai iya min wanan kokarin. Na samay shi yana shirin fita na duka nagaida shi cikin ladabi nake cewa kuma malam nazo ne nai ma godiya don nasan kaine da wanan kokarin. Yace hakane Rahama don haka kema ki kula da rayuwan ki don ban san dalilin yin hakan ba ga mahaifinki. Ko da yake mun samu labarin cewa takurawan kishiyar mahaifiyan ki ne akan ku ya shafe ki. Ki kula ki mayar da hankalin ki wata rana sai labari idan kin dage Allah zai kawo maki mafita da yardan ubangiji. Nai mashi godiya tare da sallama na koma class sai sheri yan uwana dalibai suke min wai ta fudu ta dawo. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , 4 IDAN KIN BIYA KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA, , , Tafe nake da robar talla na yau doya ce dafafa gishiri sai kuli, kuli da yaji aciki wana nake barbadawa mutum idan ya saya. Daya daga cikin tufafin da Anty ta bani na saka wasu material ne masu walkiya walwal idan kana tafiya da su. Tafe nake nayi irin digirgire din kaya a saman kai din nan hankalina a kwamce nake tafe . Kai kai kai da sauri dayan mutumin da suke zaune a tare ya juya yana kallon gurin da nafarkon mai magana yake kallo, Da sauri suka kawar da kan su daga kallo na don na kusa karasowa inda suke a zaune. Dama yarinyar nan haka take da kyau ashe kamar wata matar gwauna haka da ita ? Wai may ne ne haka salla ni duk ka cika ni da zancen yarinyar nan yace wallahi ranan da kuke zamcen ta bani kusa sai yanzu nai mata kallon tsab ai. Garbati idan kana son abinka kawai ka shige kai tsaye nan ai babban iri ne ga wanda ya samu. Allah na tuba ko kyawawan yaya ake haifa wa mutum a gida ai ya wadatar akan su. Ni fa ko da kukaji nai magana a ranan ba wai har zuci nake zance na ba amma naga kuna gidada abin haka ku ? Garbati kada kaiwa kan ka salalalan tsiya walahi in har kana so kasa kai kawai na fada maka kada ka tsaya garin kallon ruwa wani yai maka tsalle. Kaga dama ina ga ba ai mata wani matsayi ba zuwa yanzu yan uwan tane kawai nake gani suna fitowa hira da dare amma banda ita. Wanda ake wa fadancin ake kuma zuzuta shi a kaina sai yanzu yai magana yace. Kai salla, banki ta naku ba fa akan maganan yarinyar nan sai dai gaskiya a yadda shekaru na yakai yanzu sai nake gani ai na wuce tsayawa koda akan yyayyenta ne da kake magana balle ita. Sannan kaga yarinyar ga ta dai karama ce amma akwaita da kwarji a fuskanta kamar ba karamar yarinya ba. Gashi kuma bata bada fuska kamar sauran mata ko yaushe fuskan ta a daure yake ba fara, a agare ta. Sau tari da yawa nakan so na dan mata magana koda na wasa ne amma da na dumfare ta sai naji gabana yana faduwa tana matukar yi min kwarjini sosai a idona. Salla yace assha Garbati kada ka zama ragon maza mana yanzu kuma manya mata ma mun sha gaban su babu gezau balle wanan yar ficiciyar karamar yarinyar zata kayar maka da gaban ka. Don haka idan har kana ciki ka bari zan maka iso har gida na gabatar dakai tun wani bai riga ka ba. Da zaran nema iso a gidan su insha Allahu komai zaizo daidai koda baka zo tadi ba gurin zance sai kawai ayi yadda za,a a daure aure batare da kowa ya farga ita din taka ce ba. Kai haba salla yaushe rabon da ai irin wanan neman auren yanzu da kai ya waye wa mutane. Sallah yace kai dai in har kana ciki ce min eh kawai kasha mamaki indai har zaka bude bakin aljihun ka komai zai tafi daidai insha Allahu. Har na kawo daidai gurin da suke zaune suna zance na ban ko gaida dasu ba don rabin hiran su ya dan zo a kunne na naji. In ba gulma irin ta mutanen yau ba ina ni ina su Lawisa da koda aka haifesu ba, a auri uwata ba a gidan. Don an kawo sadakin auren su zasu yi aure aiba abin mamaki bane hakan idan anyi la, akari da irin girmuwan da sukai min. Ban saka zancen dattijan banzan nan a raina ba don nasan ba abu bane wanda zai yiyu suke magana don jin dadin fatan bakin su ne kawai sukeyi. Nikan inda naji zance tsofin banzan kamar yadda na sa masu suna a gurin na bar zancen. ****** ********* ****** Sai bayan kamar kwana biyu da zancen ne da dare na dawo daga tallah nayi diban ruwana da wuri na dauko littafaina ina bita don mun kusa zana jerabawan mu na fita tunda na samu an min jummping a school bana zan kare karatun secondary dina. Ina jin lokacin da baba ya shigo gida bai jima da shigowa ba akai mai sallama yafita. Ya dan dauki lokaci a waje kafin ya shigo ina jin mama na mitan wai abincin shi yana sanyi bai shigo yaci ba. Ya dawo cikin gidan yanayin da ya shigo dashi kawai zaka kalla kasan yana cikin damuwa. Sai da ya zauna yagama cin abincin shine sa, an nan ya umurci lawal yaron mama karami ya kira mai Inna. Bata jima ba tafito ta samay su zaune da mama a saman tabar ma guda itama ta samu guri ta zauna don tasan magana ce mai muhinmanci zai yi dasu. Bayan ta zauna ne ya dube su yace ina Asiya tace gani gaban ka ai malam ina sauraren ka. Yace Asiya wani sha, ani ne ya taso gamay da yar ki Rahama. Jin haka da yace yasa Inna ta kara natsuwa tana sauraren shi tunda taji yace yar ta Rahama tasan ba abin alheri bane zai fada mata a lokacin. Don indai lafine a gidan dama bai wuce yaran dakin ta ko yaushe mussan ma ita Rahama din da take kamar ta tsone makowa ido a gidan. Shiru baba yayi na dan lokaci kamar yana shakkun fadin abinda yake son fada masu a lokacin. Sai zuwa can ya dan nisa yace dama wani mutum ne yazo yana son auren ita Rahama din . Nikuma har na bashi saboda naga dacewan hakan don haka na bashi dama akan yazo yaga yarinyar. Inna tace idan da Alheri a ciki Allah ya tabbatar da alherin sa . Baba yaji dadin hadin kan da Inna raba shi ba tare da tsayawa jayayya ba akai ko wani kwankwanto. Tana kokarin mikewa tabar gurin yace idan kin shiga ki turo min ita Rahama din. Inna tace to kawai ta mike tabar gurin ran ta a bace sai dai su basu gane ba. Bata kai ga shigewa ba taji mama na fadin ai ma an mata gata koma waye tunda har yau babu ko karen da ya taba sallama mata gidan nan. Tana shiga daki ta samay ni nabar karatun da nakeyi ina sauraren maganan su. Tana fada min sakon baba na saka hijjab dina nafito gurin da suke zaune tare da mama din. Na durkusa tare da gaida baba ta amsa min a kasalance cikin wani yanayi mara dadi. Sai da ya dan kalle ni Yake cewa Rahama nace uwarki ta kira min ke ne saboda ina son sanar dake Garbati ya gane ki yace yana son ki kuma da aure. Ni kuma naga dacewan hakan na bashi ke ina son ki zama yarinya mai ladabi da biyayya kibi umurni na don dama nice da alhakin zaba maki mijin da ta dace dake. Wani irin mugun faduwan gaba naji tare da wani irin jiri a lokaci daya kila badon ina a tsugunne ba dana fadi a lokacin. A hankali na dago kai nace baba wani garbati ke nan kuma a gatin nan ? Mama ta tare da cewa ungo nan Garbati nawa kika sani a garin nan Garbati dai mana mai arzikin garin nan dai . Kasancewa na ya mai tarbiya ga iyayyena da sanin darajan su tare da sanin hakkin aurena ya rataya a garesu don sune ga kaidan musulunci dama ya dace su zaba min miji aure na fari a rayuwana yasa nai shiru. Amma kuma duk da haka ace kuma Garbati Garbatin da a girmay ya girmay ma baba ba kadan ba. Gaskiya wanan zance na baba da yanayin sa sun bani mamaki matuka ganin cewa duk yan uwana mata zabin kansu ake basu su aura tun farko. Bayan haka aiga Lawisa da Rukkaiyya a gidan duk sun girmay min a shekaru don may su ba za, a basu shi ba sai ni da aka rainawa kurar uwata dani. Ni da ko yaushe nake hango kaina da a mainasara nake ga rayuwana zan tsaya tsayin daka naga nayi karatu mai tsawo a gidan mu, shine zan buge ga auren wani tsoho wanda ma ya girmay ma mahaifina ga shekaru sosai don dai yana da dan abin hannun shine ba, a gane shekarun shi ko may ? Ko kadan bazan iya yiwa babana mussu ba gama yadda naga mama ta gwagwafe ta tsura min ido tana son taji wani rashin mutunci ya fito daga guri na ko inna a lokacin. Na sunnkuyar da kaina a kasa murya a tausashe na ce baba na gode Allah ya tabbatar da abinda yafi zama Alheri . Yace insha Allahu hakan shine alherin ki Rahama tunda kikaga babban mutum haka yazo neman auren ki. Don haka sai ki shirya don zai fara zuwa zance gurin ki duk da yace shi ba irin na yara zaiyi ba zai dai zo koda saudaya ne kuga juna dashi. Ki kwantar da hankali ki kada kika kamar shi ba yaro bane kice zaki ta da hankalin ki akai na tabbatar da zakiji dadi a gidan sa don in kiyi la, akari duk kauyen nan babu maihalinsa ga kuma kula da iyalin sa da yakeyi. Bake ba har mu nan nasan zamu amfana da auren ki dashi insha Allahu. Take naji gabana ya yanke nace a raina watau auren kudi ne baba zai yi dani ke nan ko tunda har ya soma fadar haka. A take naji jikina yai min wani irin sanyi a lokaci daya sai faman sake sake nake a raina wanda daga karshe ma banji abinda yake fadi ba sam. Sai muryan shi naji yana cewa shike nan zaki iya tashi ki wuce Allah yasa mu dace. Da kyat na iya mikewa tsaye sai kace wace kwai ya fashewa a ciki nabar gurin zuwa dakin mu . Nan nake jin muryan mama tana cewa dama may na fada maka tunda makwadaitane daga ita har uwar ai yarda zasuyi. Ina shiga daki inna tace a zaune ta rafka uban tagumi da hannu daya dagani tana cikin tashin hankali ita ma. Zama nayi a kusa da mahaifiyan tawa cikin muryan kuka nace Inna kinji irin abinda yayi da rayuwana ? Inna tace cikin jan dogon ajiyan zuciya, naji yarinya yaya zamuyi tunda shi ya haife ki ? Kuma kin san yadda gidan nan yake da gani ba ra, ayin kasa bane saka shi yin haka akayi don kawai muyi magana ta zama muna abin gori da fade a tsakar gida. Don haka abinda nake so dake shi kada ki sawa kanki damuwa akan zancen nan ko kadan mu bar wa Allah al, amarin shi don yana sane da komai. Na dan dago na kalli Inba nace shi ke nan inna nabarwa Allah din komai kamar yadda kikace. Ina fadin haka na dunkule a saman tabar man da nake kwana zuciya tab da tunane rayuwan da zan fada ciki. A iya sani na dai gidan Garbati babban gida ne don har da sarakan shi zaune a gidan suke. Mutum ne mai mai neman kudi yana noma yana kiwo da kuma hadawa da kasuwanci. Gwargwado akwai kulawa za, ace ga iyalinshi a kauyen mu don baka ganin su a cikin kazanta kamar sauran matan garin. Amma ina yarinyar yar shekara goma sha biyar za, a aura min tsohon mutum kamar Alhaji garbati. Haka na kwana ina mutsutsuri saman tabar mana cikin tunane ga matan shi dukka uku bazasu rasa yara sama da takwas ko tara ba ni Rahama yaya zanyi zama cikin wa yan nan kakanin nawa a matsayin kishiyoyi ? Ashe abinda mu bamu sani ba ta gurin mama suka fara biyowa da zancen itace ma ta hurewa baba kunne akan maganan don yaso yaki maganan. Amma ra kawo mashi kabbali da ba, adi har yaji yagamsu da maganan ta ya yarda akan zai badani ga garbatin. A yadda ya nuna ma baison a dauki lokaci ba ai auren ba don kada a hure min kunne. ****** ********* ****** Washegari dagani har inna ta babu wani mai sukuni a gidan mu sai mamace da yaran ta suke gadan su a tsakar gida. Ina jin Rukaiyya tana wanki tana waka kamar haka yarinya ancuce ki an hada hadaki da tsoho, tsoho wari kakan ki shine kika aure ga hurhura gyamu kamar na kucaki. Inna tace min kada ki kulata Allah yafiso idan da hannun uwar su fa alamarin nan Allah zai saka maki yarinya. Dayake ba makaranra a ranan ban yi sana, a ba don bazan iya tallah ba a halin da nake ciki. Da kyat na iya diban ruwa a randa na tafi na watsowa jikina ko zan danji dama. Na zauna nai kwalliya na tare da saka tufafi a jikina inna tace na fita na gyara mata gurin girkin su kafin ta fito. Mama dake zaune saman tabarma tana sauraren redio kaduna ana zabi kanka na yamma. Ta izo daurin dan kwallinta a gaba kamar wata magajiya da ruwa yakarewa. Ina fitowa tace kayya kyau da kwalliya ya kare kuma a gidin tsoho atafi akarata can a iske su sabuwa muna nan za, a bamu labari mu dai. Wasu hawaye ne naji sun zubo min dana duka na fara shara ashe tagani sai cewa tayi ai idan mutum yace kwadayi ne yakai kashe yanzu kam. An iya shiga lungu da mazan banza sunawa mutum juye ana muna takama wai sa, an talla kega mutum yau ga inda sa, an yakare a gidin tsoho tukuf. Yo Allah na tuba kodai ni din nan tsuhuwa akace za, a hada da garbati ai sai inda karfina yakare to abinka da wanda ya saba da maza ko gezau babu. Daga kofa na dago zan ba wa mama amsa naga inna a tsaye kai da kada min alaman kada na soma na tanka mata. Har muka gama aiki da Inna tana zaune sai maga take sakewa ita da diyan ta a tsakar gida. Bayan sallah na samu guri a dakin mu na shige ban fito ba har lokacin da naji shigowan baba gida. Ya zauna don cin abincin dare Inna na gurin shi don itace da girki. Sai murya wani yaro naji yai sallama ya gaidasu yace wai ana sallama da Rahama . Gabana yai wani irin mugun faduwa daga inda nake zaune a dakin mu naji baba yana cewa waye ? Yaron yace ina ganin kamar Alhaji garbati ne da wani a wajen. Baba yace kace su jira gata nan fitowa daga inda yake zaune, yake cewa ke Rahama kina dai jin ana sallama dake ko ? Na jawo hijjab dina dake gefe na nasaka tare da yan silifas dina da anty ta saya min nafice daga gidan. Suna zaune a gidin iccen durumin dake kofan gidan mu inda wani lokaci samari ne ke zama suna hiran dare idan sun dawo daga gurin neman kudinsu. Su biyu ne bazan iya sheda dayan ba tunda akwai duhu a lokacin sosai. Sai kamshi turare suke irin na yan kauye mai hawa kai ya saka mutum ciwon kai a lokaci daya. Na karso inda suke zaune tare da sallama suka wani amsa min kamar wasu kananan yara dasu. Tare da cewa barka da fitowa hajiya Rahama insha Allahu kila badi dake za, a sauke farali indai kin amince. Dan gajeren murmushi nayi bayan na fahinci mai magana baba sallah ne dan uwan mama. Nace baba ina wunin ku ? Yauwa barka dai Rahama . Kin wuni lafiya dai ko ? Na ansa a fili a gajarce da lafiya kalau. Amma azuciyata cewa nayi ina fa na wuni lafiya bayan bakin cikin da kukajawa rayuwana ? Baba salla ne ya fara magana yace ba sai mungabatar maki da kan mu ba dai tunda naga alaman babaki da Lauratu sun gudanar da komai yadda ya kama ? Na dan kai durkushe a gaban su cikin ladabi nace haka ne kan. Yace yauwa ashe bazamu samu matsala ba ke nan yadda muke tsanmani ? Malama Rahama ga abokina nan kuma amina na yaganki ya yaba da tarbiyan ki shiyasa yaji yana son kasan cewan ki daya daga cikin iyalin shi. Don haka yanzu yakike gani ?. Nace kamar ya fa ? A yadda nai magana tankar ban fahince su ba nayi. Sai shi baba sallah din yace kamar na amincewa da shi amin nawa ga bukatan shi a gare ki ? Nai wani gajeren murmyshi da har ya baiyyana sukajini a fili danayi shi. Nace lah ni na Isa na ketare maganan mahaifina aida ban fito duya ta gari ba mai tarbiya ga iyayyen ta ba ? Nace ai babu komai sai dai Allah ya tabbatar da abinda yafi zama alheri ga rayuwan mu. Sun nuna sunji dadin magana na yadda suke fadin to Alhamdullahi alama ya nuna ke diyace mai tarbiya tun yanzu. Sai lokacin shi garbatin yai magana da cewa na ji dadi kwarai Rahama da kika amince da bukatana haka da sauri don ban taba zaton hakan ba a gare ki. Nace to yaya zanyi tunda umurni ne daga mahaifana ai dole nayi biyayya garesu. Ai ko ban amince don ra, ayina ba dole ne na amice don biyayya ga mahaifa na tunda sune masu iko dani bani ce keda ikon kaina ba. Cikun wani jin dadi garbatin yake cewa. Duk da umurni ne iyayyen ki akaina naji matukar dadi da amincewan ki haka ba tare da wani matsala ba. Insha Allahu kada kiji komai zakiji dadin zama da iyalina don zan kafa masu doka akanki don ke karamace sosai a cikin su. Sukace zasu tafi sai na kara jinsu dama sunzo ne su tabbatar da idon su halin da ake ciki. Kuma Alhamdullahi a yadda suka samu taro a gurina sunji dadi kuma sun gode. Yanzu dai kinga mu ba yara bane don haka bazamu dinga zuwa ko yaushe ba don gujewa idanun jama, a akan mu. Kindai sai komai a kauyen nan yanzu ana ganin mu labari sai yasha banban kuma. Bakar Leda ne baba sallah yake miko min yana cewa fa wanan dan tsaraban rano ne da muka shiga dazun mukazo maki dashi. Na girgiza kaina tare da cewa da kubarshi aiko haka ma nagode kwarai. Haba haba ayi haka kuma diya ta ki karba kawai wanan ai ba komai bane idan mun samu hadin kanki yadda muke so ? Nace kada muyu haka daku baba idan ina karban kayan maza Innata fada take min . Da alama sun gamsu da bayani na yadda naga sunyi sun fahinci dai a karkashin controling din iyayyena nake ba kamar sauran yaran da suka sani ba . Baba sallah ne yace duk da gaka dai diyata ki daure ki karba zan wa mahaufin ki bayani yadda zai gamsu. Kinsan kin karban kayan mosoyi wani alama ne na kiyayya kuma. Haka dai na daure na karba tare da masu godiya na juya nashiga gida raina a bace . ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KI KA BAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA, , , , 5 A haka na juya zuwa cikin gida jiki a sabule min ina dauke da ledan da suka bani a hannu na. Har lokacin Inna suna gurin zaune da babana nazo na wuce su zuwa cikin dakin mu. Tafe nake ina tunane a zuciyata sam bana cikin natsuwa ko kadan a lokacin zuciya bata kwanta ba da wanan hadin da ake son yi min. Sam garbati bai min ba gashi dai dattijo a gurina na ni yar sha biyar tsoho kutuf nake ganin shi, Koma da ace lokacin kuruciyar shi yake nidai bai mun ba don bakine wulluk kakaura dashi sai dai ba can kwarai ba. Ga fuskan shi duk ya bar gemu a ciki baje baje wai shi sunnan kauye babu dai wani abin armashi a cikin sa ko kadan. Sai dai ban da wani zabi ga gakan tunda ba zan iya bijirewa hukuncin mahaifina ba akaina. Duk da har lokacin ba wai ma na fahinci may ye zaman aure ba tunda a gidan mu ba wani zaman auren dadi naga anayi ba ma balle na koya. Nasan irin rayuwan da inna ta tayi na zaman bakin cikin rayuwa ni ma dai din shi zan je naitayi gidan nawa auren ke nan. Ban da wani zabi a hakan don ban isa na bijirewa zabin mahaifina ba haka zan ta kokarin tursawa zuciya na kaunan shi koda kuwa zuciyan nawa na barazanan kamuwa sa ciwo ne. Ganin yanayin da na dawo gidan yasa bayan na dan shiga da yan mintoci Inna ta mike daga inda take zaune ta biyo ni dakin mu. Nan ta samay ni nayi zaune nayi tagumi ga ledan da nashigo dashi na tasa a gabana. Tocilan hannun ta ta haska ledan da shi sabulai ne sai clean manya biyu sai turare fesawa na passition da turmi zani guda biyu sai kudi wai kudin dinki dubu uku. Baki Inna ta ta rike tana cewa kai anya Alhaji garbati bai dauko hanyan riya ba ga alamarin nan kuwa ? Yanzu ace duk yawan iyalinshi zai iya binsu da makamancin kayan nan haka ne ? Gaskiya ni ban son abinda tun ba, aje ko ina ba zai shafa maki bakin jini akai . Duk wani abinda zaiyi a gidan nan tamfar a kunnen iyalin shi ne don dai yaya tana hurda da sabuwa da can baya. Daukan ledan tayi wai zata kai wa babana da mama dake waje da sauri na tura hannu ciki na kwashe kudin don nasan idan ankaisu mamace zata kwashe su da wani dadin bakin ta. Inna dai bata ce min komai ba ta juya ta fice daga dakin ina jin su baba yana cewa kai kaya haka kamar za, a kai lefe ? Mama sai faman binciken ledan take da sauri nasan kudi ne take nema a ciki gashi ta wani tsuke fuskan ta tamau da ganin kayan. Can taja tsuki tare da tura kayan a gaban babana tana fadin kaiyya sai dai tsiyan abin duk wanan gatan tsoho ne. Da yaro ne shine za ai farin ciki da nuna rawan kai amma tsoho ga karamin yaro may za, a gane ciki haka. A, a lauratu inji babana kon san da haka kikace nai maki alfarma na bada ita gare shi tunda da dan uwanki akazo neman ta ? Idan kin san haka ne may yasa kika sakani gaba saida na furta na bada ita yanzu zaki zo min da wanan sabon zance kuma ? A, a ni yanzu may nace kuma ai gaskiya na fada yanzu ba ga abin arziki ya fara sauka maka ba har kuna murna. Cikin mamaki yace murna kuma kamar yaya lauratu akan wanan kayan ne zanyi murna da rayuwan da yata zata shiga ? Nifa don ki na yarda naba Rahama ga wanan mutumin may naci nasa da zanji nauyi shi a baya ? Ashe ke nan ke da wata manufa kika sa na bada Rahama gare shi ke nan ? Manufar may kuma malam banda abin arzikin da na hada ni idan bashi din ba akwai wanda ka taba jin yazo ya sallama akanta ne a gidan nan bayan duk ta gama zubar da mutuncinta ga samarin gari. Daga inda nake ina sauraren su na hade wasu yawun bakinciki a raina tare da hawayen da yazubo min. Koma may zan tarar a gidan gara na tafi na huta da kullin sherin mama da yaranta hakana nida inna ta akaina. Jin hayaniyar tasu zai yi karfi ne yasa na fito waje inda suke don mama ba komai bane hassada ta nuna min karara . Tayi min hakane don ta jefa rayuwana dana mahaifiyata a kunci ne kawai. Basuyi aune ba sai ganina sukayi a waje durkushe a gaban su ina cewa baba don Allah kabar wanan magana haka. Indon nice na yarda da kaddaran da Allah ya kawo min na auren garbati bazan bari kayi kunya ba a kaina insha Allahu. Tausayi na bashi yai shiru tare da yi min wani irin kallo na ban tausayi yagane manufata bazan bari yai magana biyu ba yace eh yadawo yace kuma a, a daga baya. Yace shike nan Rahama Ubangiji ya tsare mun ke a duk halin da zaki riski kan ki a gidan shi nace amin baba na share kwallan da suka zubo min na mike na koma dakin mu. Ina jin mama bayan sun gama hayaniya ta juya dakin ta bata dade ba ta rufo kofan ta hakan ya nuna ranan bazata yarda na kwana a dakin ta ba ke nan. Inajin Innata bata shigo daki ba da taga haka dakin da suke aje shirgin su har bunun dakin ya zabbace ta gefe daya don wahala ta dan gyara min gefe daya tace na kwana a can ko naje gidan mai kuli na kwana. Nace dare yayi Inna bari kawai na koma can na kwanta yanzu mama ta rufe gidan ta nasani. Baba tana ganin haka ya nufi dakin mama ya na bugawa tace daga ciki wai lafiya kake dukan min kofa haka kuma may kuma zan maka ? Yace ki bude Rahama ta shigo ta kwanta tace ai kaba uwar ta daki ka bani don haka ku kwanta tare da ita mana tunda ta zama yar gwal matar Alhaji yanzu. Dole ya juya ya barta zuciyar shi na tir da Allah waddai da halin mace ba haguwa irin ta. Sai ta kaika ta baro kuma ta tsira ma sabon fitina dama wanda ya kaucewa Allah dole ya fuskanci kalubali irin haka a rayuwan shi. Hakana na kwana dakin ga sauro ga beraye suna ta hawa min jikina ba dadi ko kadan dakin don yawan shirgin kayan aikin su dake cikin dakin. Kwana biyun girkin Inna haka tayi shi a cikin kunci a gidan rai a bace mata duk nabi na damu ga bacin ran da mahaifiya ta take ciki ga zancen auren da ake son yi min na dole. Haka nake zaune a takure ga mama ta saka mu gaba da gori ita da diyan ta duk mun kasa sukuni a tare da mu. Na dai yanke shawara zuwa yamma na shiga gurin mama altine ko zan dan sarara a tare da ni. Nan samu mama tana dan aikace aikacen marance na shigo da sallama na na karbi tsintsiyan da take shara a hannun ta na karasa mata sharan. Na dawo gurin da take zaune tana gyara geron da zatayi birbisco dashi na abincin dare na karba ina gyara mata. Kallon yanayi na tayi abinka da babban mace ta fahinci babu dadin rai a tare da ni lokacin. Take cewa lafiya kuwa yar gidan anty na gan ki yau wata iri dake haka ? Maimakon nayi magana sai hawaye ne suka biyo baya tace subbahanallahi may ke faruwa ne Rahama ? Sai da nayi kuka mai isata nake cewa mama baki ji kaddaran daya fada akaina bane halan innata bata samu shigowa ta fada maki komai ba ? Tace Asiya ta kwana biyu bata shigo gidan nan ba gaskiya may ya faru. Ina kuka nw nake labarta mata komai da ya faru a gidan mu akaina cikin kuka tace waye shi wanda aka baki din ne ? Nace Garbati cikin rike kirjin ta tace wani garbatin ba dai Alhaji garbatin dan bida ba dana sani ? Nace a sanyaye shi mama. Tace subbahanallahi yanzu shi mahaifinki da ranshi da lafiyan shi zau dauki ya kamar ki ya mika wanan gidan na sa, an nin kakan nin ki ko may ? Nan ta haufada tana cewa idan Salihu bai yi hankali ba sai Lauratu ta kona shi tun a cikin duniyan nan wallahi ko. Fada sosai mama tayi tare da kara kwantar min da hankali take cewa zan tafi gurin anty ki ance min ita ma bata jin dadi ga abokan zaman ta ba kirki ne dasu ba. Kin san kishin yan birni ba irin namu ne ba na kauye kishi suke suna hadawa da yahudanci aciki. Rayuwan ne na kowa tasa ta fishe shi akeyi wai suna ganin su wayewa ne a gare su. Inbashi ba dan uwan ka baida lafiya ina zaka kawar da kai gareshi haka kana tsabagan gaban ka. Nace mama Anty na bata da lafiya ne ?. Tace ina fa taga lafiya tunda tazo din nan take fada min wai bata da lafiya ajikin ta har zasu tafi kasan waje da maigidan a dubata. Allah yaba anty na lafiya nace tace amin Rahama ita nake gani ta tuna min da mahaifiyar ta don dan uwan ta shi namijine baidamu damu ba kamar yadda ita take kula mu. Na sake cewa mama dama anty tana da abokan zama ne tace tana dasu mana har biyu ma. Ai anyi aurenta ba a kokai shekara ba uwar mijin tasa ya auro yar uwarta shima mahaifin shi wai akwai yar abokin shi da yake son hada shi dashi tun farko shima yasa ya auri yarinyar. Zoki ga irin yadda suka saka min yarinya a gaba da fitina suna ganin itace bare a cikin su sai abinda suka ga dama suke mata a gidan . Allah dai yasa shi mijin yana son abin shi haka yasa basu samu yadda suke so ba akanta. Yanzu ga ciwo yazo ya sakata agaba haka wama yasani ko ije ne aikai mata ya hanata jin dafin rayuwan ta. Nace mama ije kuma may nene ije ? Tace baka ji maganan ba keda zaki shiga kishi cikin tsofon mata Rahama baki san ije ba kuma sai may. Nan tashiga yi min irin kissan ije da dalilin da ke sa aiwa mutum asiri idan anga hankalin miji nagareshi da yaran shi. Nan nai mutuwan zaune nace na shiga uku mama koma don ai min ne yasa mama ta tura baba ya kaini wanan gidan akashe ni kowa ya huta dani kamar yadda take fadi. Har na dawo gida duk yadda mama taso ta fahintar dani hakan bai samu ba daga gare don na kasa fahintar dongon sharfin da take min akan ije wai shirin kishiya . Ko da na dawo gida na samu ranan har baba ya dawo daga kasuwa ko suna zaune da mama yake tambayana daga ina nace na shiga gurin mama altine ne na taya ta aiki . Bai yi magana ba sai bina da yayi da harara har na shige dakin mu ban dade da shiga ba Inna ta kamala abinda takeyi sai ji kawai nayi ta rufo kofan dakin ta garam. Nace ashe yau akwai tsiya a gidan nan ke nan don Inna zata rama abinda akai min ne kwana biyu na barina na kwana dakin shirgi ni kadai sai bera ye. Lawisa ce tashigo gidan daga gurin hira ta fara zuwa dakin mu don ta kwanta taji shi a kargamay. Ina jin ta lokacin data juya zuwa inda iyayyenta suke tana fadin wai Asiya ta rufe kofan ta don haka suke kiran Inna da sunan ta gazatsau ba sayawa. Mama tace kamar yaya ta rufe kofan ta a ina take son ku kwana yau din ? Nace a raina jifa mama da son kai ta manta abinda tai min ni . Ban dai ji baba ya tanka masu ba har lokacin tasowa mama tayi ta shiga dukan kofan mu da karfi amma ko motsi Inna batayi ba ga wani katon dutse da tasa ta kare kofan dashi. Ranan inna tasha zagi gurin mama shima baba yazo ya buga amma taki budewa ban san ya suka karasa ba da yarasu yan so a gidan mudai basu kwana ba a dakin mu. Haka na kwana da wanan damuwan a rana washe gari tun da farar safiya na fito daga dakin da nake mu dana kwana. Ina alwala naji mama na tayar dasu Lawisa wai su fito kada beraye su kashe su a dakin wai sun kwana suna ihun bera. Dariya ya kumay ni daga inda nake nace farau da dadi ramuwa da ciwo ke nan tai min taji dadi yanzu an mata wai taji zafi. Baba da ya dawo daga sallah dakin mu ya fado yanawa Inna fada wai bata kyauta ba da ta rufe dakin ta inda yake shiga ba nan yake fita ba. Har ya gaji ya juya ya fita daga dakin don kan sa ba wanda ya kula shi. Na fito ina shara naga fitowan Inna daga dakin saye cikin zumbudeden hijjab din ta na sallah idanuwan ta yana fitar da hawaye. Kai tsaye na fahinci manufarta da sauri na yada tsintsiyar dake hannuna na nufe ta tare da shan gaban ta na riko mata hijjab din ta. Allah ya taimake ni duk suna daki a lokacin nace inna ina zaki ? Inna ta juyo idon ta yana zubar da hawaye cikin raunaniyar murya take ce min. Yarinya bari na tafi gidan mu na gaji da wanan tauye incin da ake min a gidan nan haka. Take nawa idanuwan suka kawo ruwa a lokaci daya ganin yadda Inna ke zubar da hawaye ga nata idon. Nace Inna may zai sa ki tafi a lokacin da nafi bukatan ki a kusa dani ? Hannun ta na kama sai naga bata mussa min ba na jata muka koma dakin mu ni da ita. Sai bayan mun shiga naji motsi a tsakar gida ashe mama ce tafito don ta hura wutan kunu. Nace haba Inna may zai sa ki bari shedan ya rude ki a daidai lokacin da mukafi bukatan zaman ki a gidan nan a tare da mu. Don Allah inna kiyi hakkuri hakan mama ta dade tana son gani daga gareki. Inna sai kuma da komai ya kusa kai karshe zakice zaki fice kibar mata gida taji dadin gallazawa rayuwan mu yadda take so. Kiyi hakkuri Inna wata rana sai labari insha Allahu. Kallona Inna take yadda karama dani nake jero mata wanan maganan haka. Zama naga tayi bakin gadon ta sai da ta share hawayen dake fuskan ta hakan ya nuna min tayi taushi ga magana na. Tace haba yarinya da za, a daina da zuwa yanzu yaci su daina sai abu yai dan sauki sai kuma abu ya sake dawowa sabo. Ni wallahi nagaji nagaji wallahi duk haihuwan da nayi a gidan nan nayi shi ne bisa rantsatsen rabo kawai amma ba da son raina ba. Nace cikin sanyin murya inna ki dai yi hakkuri ko dan darajan mu don Allah. Cikin fushi tace dani yarinya ina son na kwaci inci mune a gidan nan daga ni har ku an mayar damu kamar wasu bayi can a gidan nan bamu da incin kan mu ko kadan. Nace ki dai dan kara hakkuri inna don Allah komai da sanin ubangji akeyin sa baki san tana din da Allah yai ma hakkurin mu ba. Shiru tayi tana nazari niko ina tsaye na kura mata ido cikin tausayi nasan Inna tana matukar hakkuri agidan mu sosai. Na share hawaye nace inna ki saki ranki kamar komai bai damay ki ba zakiga mama abin ya kuma koma mata ciki. Ai ance mace ko a dakin ta tana yaji ko ? Gashi naga kin fara daukan wa kanki fansa a gare su ai basu taba tsan manin zaki iya masu haka ba da kikeyi yanzu. Nan dai nai ta bata hakkuri har na samu ta sauko naga ta dan sake jikin ta muryan mama ce ke cewa ina mai sharan nan take ne kin bar shara iska zai kwashe. Sai ji nayi Inna na fadi aiki take min a daki a sa wasu su share ba ita kadai bace ai a gidan. Nace a raina taufa ance mai hakkuri dama bai iya fushi ba mama zata kai inna ga bango ke nan. Muna nan zaune wani dabara ya fado min a raina na saurin daukan hijjab dina nace wa Inna ta ina zuwa na fice daga gidan. Kofan gida na koma na tsaya ban dade ba naga baba ya fito gaidashi nayi yana kallona yace Rahama may kike a wanan gurin da sanyin safiyan nan haka ? Nace baba kai nake dako kafito akwai maganan da nake son muyi dakai ne. Kallon mamaki ne yai min nakai durkushe a gaban shi nace don Allah baba alfarma nake nemawa inna ta akan zaman su da mama a gidan nan. Duk zaman da suke na kishi a tsakanin su baba ba wai lalai bane sai ka saka bakin ka a ciki tunda kai ba mazauni gida bane baka san waina da ake toyawa ba a bayan fitan ka. Kallona yake cikin mamaki yace Rahama har ankai lokacin da za ki tari gabana akan maganan uwayen ki. Nai saurin cewa baba ba hakana bane yaune naga inna har ta shirya wai zata bar gidan bata iyawa ta gaji da abinda ake mata shine nace bari nai magana. Yanzun haka wallahi inna batasan zan yi wanan maganan da kai ba ma hakkuri dai nake baka baba ko dan darajan mu a tsakanin ku ka rangwanta ma rayuwan ta hakana. Shiru yayi kamar mai nazarina can yace naji amma ita Asiya ne yau har tai niyar yaji ? Nace kwarai kuwa baba Allah ya gyara ni kadaine a waje na tare ta data fice daga gidan. Yace to jeki naji Allah yai maki albarka idan nadawo zanga ita innar taki zamuyi magana da ita na fahinta nace baba nagode Allah ya kara rufa asiri. Ya wuce na juya na shiga gida zuciyana fes na san ko ba komai killa Allah ya kusa kawo muna saukin al, amarin mu ne a gidan. ****** ********* ****** Tun daga wanan lokacin da mukai magana da babana ta fahinta naga al, amura sunyi wa inna sauki sosai ba inna kawai ba har ma diyan ta da akewa kahonzuka a gidan mun dan samu saida sosai. Ya zuwa yanzu ba karamin alheri Garbati yake kawowa ba gidan mu wani naci wani kuma dangin tufafi ne duk ba, a tabawa sai gurin mama altine ake boyewa. Cikin hakane na roke shi yai hakkuri har na zana jerabawa na na karshe kafin ayi bukina dashi. Da kyat na samu ya amince min wanda zuwa lokacin har labarin zancen aure na dashi yabi gari wanda mama ce da diyan ta suke yada zancen a gari. Don mama har iyalin shi sai da ta fada masu irin alherin da yake kawo muna gidan mu . Wai yanzu duk neman shi a kaina yake karewa komai kawo muna yake dani da uwata idan anga yadda muka koma wasu bulbul damu don mun samu ya rike muna kan maciji muna wasa da bindin shi. Haka yasa matan shi suka tayar da hankalin su su basu yarda ba ya dauko masu yar jikan su a matsayin kishiyar su mafarin nazo ina masu rashin kunya a cikin gida. Yace shi ra, ayin shi ke nan mai zama ta zauna wacce bata iyawa hanya a bude yake mata. GNin da gaske yakeyi yasa suka kama kan su bayan ya saka masu waigi ga zancen da cewa. Kada yaji wani ko wata yaiwa yarinyar nan ko iyayyen ta wani sheri zai dauki mumunan mataki akan ko waye a gidan. Dole suka saka mai ido ba yadda zasuyi namiji idan yaso abu kunya fice mai yake a idon shi. Mama altine ta tafi birni ganin anty da tadawo daga waje ganin likita akan matsalan ciwon ta. Sai washe gari bayan ta huta anty ke tambayan ta wai mama ina Rama na take tana nan tana karatun ko ? Mama tace wani karatu Sa, ade Raman ki kan aure zatayi bada dadewan nan ba. Haba mama wani aure yarinya kamar Rama kuma ? To ai sai kiyi Rahama kan har an kawo sadakin ta itace ma ta hudu a gidan mijin ta. Anty dake kwance tace what ? Mama wai da gake kike ko wasa tace ina wasa dake ne balle na fada maki wasa. Uban ta yaba da ita ga wani tsohon maikudi na garin mu aure yanzu haka karatun data kwallafawa raine ya hana ayi bukin kin san ta samu sa, a don kokarin ta an kaita gaba yanzu bana zata fita daga makarantan ma. Ran anty yai matukar baci dajin wanan labarin da tayi na zancen aure na nan dai mama ta koro mata komai akan zancen. Na bata matukar tausayi tace mama in ba abin kauye ba ko mu da mukai aure da girman mu yaya muka kwashe da kaidin kishiya balle yarinya karama akaita cikin guzamay mata haka ? Mama tace mu a kauye ai hakan ba komai bane gare mu amma duk da haka Rahama tayi kankanta kwarai agidan nan. Da mama zata dawo sakon zannuwan gado da sauran kayan aiki dasu kudi anty ta bayar akawo na shagalin buki na wanda baifi wata biyu ba ayi yanzu. Harda yan din kuna kala biyar da sauran abubuwa duk ta hado min tace aba Inna hakkuri saboda jikin ta bata samun zuwa bukin . Amma idan ta samu lafiya zata zo taga dakina daga baya insha Allahu. Mama tace kice wanan tafiyan na Rahama ne nayi ai taso ta biyoni sosai amma nasan mahaifinta ba zai yarda ba shiyasa na bata hakkuri. Da mama ta dawo daga birni sai washe gari muka shiga taron ta don da dare ta iso garin. Ai nan ta baje muna sakon anty na muna kallo wani abin ma ni ban san yadda za, ai amfani dashi ba agidan. Ban san lokacin da na dunkule na fara kuka ba da kyat mama ta lalashe ni na wanke fuska na. Sai da naje gida nake labartawa Inna ta abinda ya faru ta rike baki cikin mamaki tana cewa kai wanan boyar Allah ni ban san abinda zan saka mata dashi ba a duniyan nan ? Mama ko sai gori take sake muna da habaici wai rana bata karya sai dai uwar diya tai kunya. Daga uwar har uban sai kudi ake ci amma ko roba ba asai wa yarinya ba na aure . Su dai gasu gani wai an bizzine tsohuwa da ranta suga yadda za afita kunya duk tallan da nayi Inna ta kasa saye min wani abin kwarai. Dama tayi haka ne don ta kure inna don tasan ba, a aje min komai na aure ba a yanzu tunda mun sakakance cewa ni boko zanyi ba aure ba yanzu. To yanzu ga aure ya taso suga ta tsiya tasan dai gidan su Inna ba wata tsiya zasu barkata min ba don suma nema sukeyi. Magana duk yabi gari inna bata aje min komai ba ga aure ya taso ba abin kaiwa gidan miji. Lokaci ko kamar jira yake sai kara matsowa yake niko sai karatun jerabawa na dake gabana nakeyi kawai. Ba abinda yai min tsinanen zafi akan maganan mama da diyan ta a gidan mu. Garbati yasa aka gina min daki mai girma da fadi yadda zai isheni aka kewaye shiyan daban cikin na iyalin shi can gefe daya an shafa farar kasa yaji sai kyali yakeyi. Haka ya kara bankantawa iyalin shi rai sosai har suka so tayar da hankalin su. Amma da ya basu dan wani abu suma suyi gyara sai baki ya mutu murus kowa ta shiga sha, anin gaban ta da diyan ta amma kishin yana nan daram a ran su. Duk inda yabi sai ba, a ake mai na ya fado gari ya zarta maza zai bare yarinyar dalleliya a ledan ta sai ya washe baki cikin jin dadi yana dariya. Mama ko sai auki fadawa mutane karya da gaskiya takeyi akan zancen bukin tana zunden inna ta. Inna ta duk tabi ta ramay sai dan wuya daga ita sai uwar dakin ta mama altine suke shirin bukin sai yan uwan su tsiraru da sukaji suka gani. Ko su ba wai sun san shirin da Inna da mama altine sukayi min bane haka ake tafiyan a dunkule. Gaba daya daga inna har baba babu wani mai kwanciyan hankali dama ma inna dake nuna halin ko in kula da bukin. Idan ka cire mama da yaran ta wanda su ko a kwalar rigan su bai shafe su ba. Ta dai zuga shi ya zugu yanzu kuma ta saka mai ido yaji kunya dan kudin sadakina da aka kawo dashi ne yake kokarin sayen komai. Na dan gadon katakon da za, a sai min ma ya gagara daga karshe ganin haka tasa inna dabaran cewa yaba mama altine kudin ta shiga birni ko na hannu ne ta sayo min. Tayi hakane don idan kudin ya shiga hannun su sai su san dabara mama altine ne ce ta koya mata wannan dabaran. Baiki shawaran Inna ba tamika masu dan abinda ya saura takaiwa mama altine ta shirya sai birni da kudin daga karshe anty ce ta cika aka sayi min saitin gado da dan wardrove da katifa har da karin tarkace. Wanan matar ba abinda zamuce mata sai dai Allah ya bata lafiya ya shirya mata zurian ta da albarkan sa kawai. Ganin babu komai a dakin inna ta yasa mama ta samu baba da zancen da yamma bayan ya dawo gida take cewa. Yanzu malam kana ganin haka zaku kai yarinyar na aure babban gida irin haka babu komai da uwarta ta tana da mata na fita kunya kaima sai nake ganin a furin ka hakan ne ? Baba da yanzu ya fahinci mama so take taga wallen shi kuma tasan sirin abin sai ya boye mata ba su mama kudin sadakin da yayi yace anyi auren ne ko kikaga uwarta ta kaita hakana ? Haka yasa taji haushi taja bakin ta ta tsuke ta bar zancen sai ido tana cewa ni dama taimakon ku naso nayi ko mu tafi gida tumba dillaliya adan samu abinda aka tsintar mata gurin ta in yaso bayan bukin abinda aka samu sai abata kudin ta. Baba yace ko tabarma Allah ya hore mata daga gare ni sai na kaita dashi . Yafice abin shi gidan ya barta nan tana mashi dariyar mumuke ta baya tana an daiji kunya wallahi anyi shigewa ai ciki amma ba, a iya fitar da yarinya kunya. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE NA FADA IDAN BAKI BIYA BA KIKA KARANTA MIN NOVEL NA BARKI GA ALLAH. IDAN KIN BIYA KIKA TURA MIN NOVEL WANI GROUP KO KIKA BA WA WANDA BAI BIYA BA KE MA NA BARKI GA ALLAH DON KINCI AMANATA ALLAH ZAI SAKA MIN A KAN INSHA ALLAHU WACE TASAN BAZATA IYA RIKE AMANA BA DON ALLAH TAI MAGANA NA BATA KUDIN TA TAFITA MIN GROUP DON AMANA NAUYI GARE SHI ABINDA KA RAINA SAI YA HANAKA KETARE SIRADI GOBE KIYAMA ALLAH YA BAMU IKON RIKON AMANA A TSAKANIN MU. DON NAGA NOVEL DINA A WANI GROUP KUMA NASAN WACE TA FITAR DON BATAI MAGANA BA NA BARTA GA ALLAH DON ALLAH SHEDA NE GA ALKAWARIN MU DA KU, , 6 Ranan da na zana jerabawan karshe na na secondarya rana ce da ya kamata nai mafarin ciki a raina don kowa ka gani a cikin mu yana cikin farin ciki da jin dadi a ran shi. Sai dai ni a gareni sabanin hakane don ya kasance min kamar rana na bakin ciki a gare ni. Lokaci daya yanayi na ya sauya min naji duniya tai min kunci a raina komai ganin sa nake yai min baki a raina a dalilin tunawan da nayi wanan jin dadin rayuwan ya kusa yanke min. Don wanan auren jarabtan da na tsinci rayuwana dashi na auren tsoho da mahaifina zai min a lokaci daya haka, batare da yai la, akari da irin rayuwan da zanje gidan miji na tarar. Wanda yau baifi saura kwana goma ba naje gidan Alhaji garbati a matsayin matar auren shi nima a gidan. Juyawa nayi zuwa staff room don nai sallama da malam mutumin da yai tsaye a kaina har nakai wanan matsayin na yau a gare ni. Malam yana ganina yace a, a Rahama an kanmala ko ? Maimakon na nuna farin ciki na sai na kai durkushe a gaban shi na fara kuka yace subbahanallahi Rahama lafiya dai ko ? Cikin kuka nafara cewa malam nazo ne nai maku godiya akan tsaya min da kukayi har na kai ga wanan ranan ga karatuna. Sai dai kuma gashi guri na ba zai kai na zama likitan da nake son zama ba na taimakawa yan garin mu kamar yadda nake da gurin haka a rayuwana. Mahaifina ya yanke min wanan gurin nawa ta bayar dani aure ga wanda yaso yau saura kwana goma ayi bikina akaini. Subbahanallahi inji malam yace yaushe haka ya faru kuma Rahama waye kuma miji ? Sai na dan kakaro murmushi a fuskana nakw cewa malam an kwana biyu da hakan ba kuma kowa bane mijin sai Alhaji Garbati dan bida na garin nan. Shi da sauran malamai da suke saurare na cikin tausayi sukace garbati dai garbati wanan tsohon mutumin da muka sani ? Nace shi malam , Malamai suka ce kai amma mahaifin ki ya cuce rayuwan ki Rahama ga wanan tsohonbzai bada ke dan kwadayi ko don may ? A hankali nace nima ban sani ba malam na mike ina masu godiya na ke masu sallama na tafi, Nan na barsu da mamaki kowa na fadin albarkacin bakin shi a kaina na nufi gida. Na shiga gida da sallama na na gaida da su mama da na samu tana raba abinci a tsakar gida. Nan na shige dakin inna na kwabe uniform din jikina fita nayi na debi ruwa don na watsa naji dadi jikina. Mama ta bini da harara wai dan ruwan da zasuyi aiki dashine kuma zan kwashe nai wanka don ni nafi kowa tsabta ko may ? Ina ban daki na fara watsa ruwa ne naji mama tana rafka salati haka yasa nasan ba lafiya ba ke nan. Nai saurin watsa sauran ruwan a jikina na fito da sauri nan na samay su tsaye cirko cirko sai fada mama takeyi ita kadai Inna ta tana tsaye a bakin kofan ta itama fuskan ta a cikin damuwa yake. Na karaso inda take ina fadin Inna lafiya ko may ya faru kuma ? Kafin mama ta bani amsa take cewa dani wai angon ki ne ba lafiya gashi can an kwashe shi zuwa asibitin birni yanzu. Gabana ne naji ya yanke ya fadi min ras ras nace shi Alhaji garbatin ne da kan shi baida lafiya ? Mama tace idan bashi ba da uban ki ko bakiji may nace bane ni. Allah ya sauwa nace na watsa ruwa a kafana dana rage a sauran roban da na fito dashi ban daki da nai wanka. Nashige dakin mu kawai na fara sallah bayan na idar ina jin mama tana karasa aikin ta sai faman mita takeyi akan zancen ita kadai a tsakar gida. Na juya inda inna take zaune cikin damuwa nace inna may ya samay shi ne ? Take cewa dani yanzu nima nake jin zancen a gurin yaya wai ya kwana biyu yana irin wanan ciwon dama. Allah ya sauwaka nace, naci gaba da kwalliya na ba abinda ya damu raina ko kadan. Sai bayan dawowan babane muka samu labari wai ashe ya kwana biyu yana irin wanan lalurar . Fitsari ne ke mai wahalan fita idan zaiyi sai kuma yanzu da suka tafi asibiti ake cewa harda hawan jini yana da shi. Mama sai cewa tayi Allah ya cece mu ga farar kafa mu kan ? Kamar yaya farar kafa kuma baba ya tambaye ta hakanan ? Tace to yau saura sati a saka lalle haka ya kasance dashi ai sai ace yar mu ce zata shiga da farar kafa gidan shi . Ki kadai fadi yanzu inji baba lalurar da kowa yasan ashe yana dashi dama shine zaki fadi haka ? Tace ai idan ni ban fada ba iyalinshi su fada tunda koda yake dashi duniya basu sani ba sai yanzu . Lauratu wai may yasa baki son a zauna lafiya ne ke duk abinda zai kawo fitina a tsakani kin san yadda zaki jawo shi. Idan da yar cikin ki ce za, a kai gidan ai baza, ki fadi haka ba akan ta. Allah ma ya tsare ya ta da wanan rayuwan gaskiya ne baka son a fadi kuma in ni ban fada ba duniya zasu fada ai. Baba yace yanzu na gane may kike nufi akan yarinyar nan mutane suna fada min ban yarda ba amma yau na yarda da hakan. Nan dai suka fara halin nasu na sa in sa a tsakanin su wanda ba mai shiga don ko mutum ya shiga sai yai kunya don ajima kadan zakaga sun shirya ne. Bayan an sallamo Alhaji garbati ne daga asibiti ya turo kiran babana yana son magana dashi. Baba baiyi nauyin kafa ba ya tafi amsa kiran da Alhaji Garbati yake mai a kofan gidan shi inda akai mai shimfida mutane suna zuwa gaida shi da jiki baba ya samay shi. Bayan sun gaisa yai mashi yaya jikin shi da sauran iyalin shi ? Ya bukaci da sauran mutanen dake gurin yana son ganawa da babana akan wani magana sun san alakal dake a tsakanin su don haka suka basu guri. Alhaji garbati ya sake gaida babana yake cewa ya aika a kira shi ne don su yi magana akan zancen auren shi dani. Yace bai san ko don matsalan da ya samay shi za, a iya daga bukin har zuwa lokacin da Allah zai bashi lafiya sai ayi. Baba yace haba Alhaji ai kowa yasan lalurar ciwo inda yin ba zai zama matsala ba sai ayi din a wuce gurin. Alhaji yace amma duk da haka da a shawarci yarinyar da uwarta aji ta bakin su don kada azo ayi daga baya kuma a zo a samu matsala ya biyo baya. Baba yace hakan ma shawara ne zai je yayi shawara da ni da uwata yaji ra, ayin mu ga hakan. Nan dai sukai sallama baba yai mai fatan samun lafiya ya tafi ya barshi a gurin da ya samay shi a zaune. Baba ya dawo ya samay ni da inna ta a daki muna hiran mu cikin jin dadi tai muna sallama ya shigo daga ciki. Nan ya samu guri ya zauna ya na mike zan bar dakin yake cewa dawo ki zauna magana zamuyi daku. Na koma na zauna cikin natsuwa a inda nake yace dama akan zancen auren Rahamane yanzu Alhaju garbati ya kira ni gidan sa mukai magana. Jin abinda ya fadi yasa muka natsu daga ni har inna ta muna sauraren shi muji may zai fada muna. Kaf yadda sukayi da Alhajin ya fada muna tare da tambayan mu may ye ra,ayin mu akai mu ? Inna tace to malam ko dai an daga bukin nan ai ba fasawa za, ayi ba ko ? Don may ba, a ayi a haka ba kowa ya huta da kace nace akai asan ayi an gama ta zaunu a dakin ta. Baba yace ke Rahama may kika ce shiru nayi ni may zance tunda bani ce da ikon kaina ba. Baba ya sake maimaita tambayan shi a gare ni a hankali nace baba abinda Inna ta fada gaskiya ne ayi kowa ya huta kawai. Baba yace to madalla Rahama Allah yai maki albarka yasa haka shine alheri a gare ki. Sai kiyi ta hakkuri da halin rayuwan da zaki tsunci kanki a gidan don kin san manyan mata zaki sama a gidan. Idan kin je masu da taushi yadda na san ki sai kiji dadin zama dasu har iyalin su. Amma idan kince zaki nuna masu halinku na diyan yau sai ki samu matsala dasu har iyalin su. Mama da taji muryan baba a dakin mu ta kasa zaune ra kasa tsaye akan tana son jin may akeyi a dakin wanda ba, a son ta sani. Sai ta hau fadin tsuntsun da yaja ruwa shi ruwa ka doka ai wanda yaci shi ka biya don dai nasan bai wuce ance garbati yace a mayar mai da komai nasa ba ya fasa. Wanan rufa rufan wa za aiwa shi wa zai kwashi mai farar kafa ya jefa a cikin iyalin shi . Baba dai ya fito bai kula ta ya fita da dare ya koma ya fadawa garbati yadda sukayi da iyalin shi. Shiru yayi yana nazari maganan baba na irin halarcin da sukai mai don shi a rayuwan shi yana son kasancewa da wanan yarinyar a rayuwan shi. Don haka ba, a fasa komai na shirin buki ba akaci gaba da gudanar da shirin da za, ayi. Mama a zaton ta an fasa ne ne sai da taga yan uwan Inna suna shige da fice ta fahinci akwai zancen bukin ke nan. Nan kuma hankalinta ya tashi ta sulale har gidan garbati taje a cikin dare ta gana da matan shi take fada masu mugun kalamai na batanci akaina da uwata. ****** ********* ****** Ranan kamu aka saka ni a lalle kamar yadda akewa ko wace budurwa kamu. Duk wanda ya ganni ko inna ta yasan bamu a cikin walwala ana dai sha, ani ne kawai na bukin ba cikin dadin rai ba. Gidan mama altine nake zaune da kawayena don a gidan mu babu fili ga magan ganun mama da basu da dadin ji. Ya kasance washe gari daurin aure nan mama ta dora a tsakar gida ga dakin Inna tab da yan uwan ta sai cewa mama take ita bata gane ba fa. Ace har yanzu ba, a fito da kayan amarya ba aje zuwa jere ko sai mutane sun watse ne za, a tafi jeren kamar marasa gaskiya. Wata daga cikin yan uwan Inna ta fito tana bata amsa da cewa in ma mutane sun watse ai ko wasuwasun mu zamu iya gyara dakin yar mu. Ballanta na rana muke jira yai sanyi mu tafi don bamu fada gidan mutane da rana tsaka ba kamar mun gaji da yar ta mu. Dole mama taja bakin ta tai shiru ta kyale su dai gani ai duk abin da akewa taratara din ake boyo yau rana ce da bata karya sai dai uwar diya tai kunya. Sai zuwa karfe biyar mutane suka fara shiga gidan mama Altine suna kwaso kayan da aka saya min na aure. Wata daga cikin kawayen mama da ta gaiyyata suzo saka ido ta shigo tana cewa mama. Ke laure wai kayan da naga ana fitowa dasu gidan mai kuli na waye ba dai kayan yar taki bace haka? Ni duk garin nan ban taba ganin yarinyar da akaiwa kaya haka ba ? Kinko ga kayan kamar ma na kamfani ne fa don a cikin ledan su ma suke, ga wasu irin manyan zannuwan gado da na fani kamar na makka dasu didin didin dasu. Gaban mama ya fadi tace ke haule wai da gaskiya kike ko ba, a baki ga komai nakai gida ba tace idan karya nake fita ki ganewa idon ki ai. Mama bata saya ba taja wani raggan zani dake shaye a igiya ta nufi kofan gida da saurin ta. Aiko tana lekawa tai tozali da kujerun da ake fitowa dasu tace kan uban nan ni za, aiwa munafunci ke nan. Watau malam yana da kudin yin wanan kayan haka wa yar shi. Shine ya barni da yara a zunbule a daki sun kai sun kawo ga girma kuma ba manema suka rasa ba. Da kyat kawayen ta suka samu ta natsu suka jata zuwa cikin gida dakin ta suna tausan ta akan idan tai haka taba da kan ta. Nan dai aka shiga shirin buki ba wanda ya tsaya kula mama da haukan ta da takeyi ta kasa boye hassadan ta a fili. Bayan sallah jumma, a aka daura aure duk dai ba wani shagali akayi ba tunda ba auren saurayi da budurwa bane, amma an ci ansha an koshi. Da yamma aka dauke ni sai gidan Alhaji garbati gida ne babban gida mai cike da iyali fiye da arbain a gidan. Sai da aka kaini dakina na dan zauna na yan mintina akace na taso akaini dakin uwayen gidan. Dakin uwargidan mama salla aka fara kaini dattijuwa ce sosai don ta manyanta sosai ba sai an fadi ba itace ta wanke shi ya wanke ta. Nan iyayyena suke fada mata cewa ga amanan yarsu nan sun kawo masu da fatan zata rike masu ni amana idan nayi ba daidai ba don Allah ta tsawata man. Tace kada suji komai ai da na kowa ne da fatan nima zan masu biyayya yadda ya dace karami yai wa babba. Suka ce insha Allahu in wanan ne baza, a samu matsalan komai ba a kaina. Nan dai suka mike suka bar dakin ina biye a bayan su sai dakin mai bi mata itama dai acan ba matsala sai cewan da tayi na daiyi hakkuri don su yara ne da su sa, a na dama wa yanda suka girmay ni. Mun bar dakin zuwa dakin wacce nake biwa ita ma din tana zaune da mutane da yaran ta bayan an gaisa aka fada mata zaman lafiya ake nema a gare mu. Sai cewa tayi haba zaman lafiya a tsakanin kishiya da kishiya ai sai dai zama na ki goga in goga tasan gidan da ta shigo ai har ta yar da ra kutso kai don kwadai ita da iyayyen ta. Ai babu wani zaman lafiya illa tazo ga tukunya nan lamba ashirin ta tuka mu tuka da ita don yau an zama daya. Daya daga cikin yan uwan mama tace to shi ke nan Allah ya bata ikin iya tukawa kamar yadda kowa keyi a gidan. Muka bar dakin muna jin ta tana yadda bakaken magana wai haka kawai an koso yarinya karama don jaraba an kawo masu a g raino a gida ace wai an basu amana. Dakina aka mayar dani aka zaunar dani a saman gadona da ya sha gyara nan aka shiga jero min nasiha na zaman lafiya har sai da na rasa na kamawa. Sukai min sallama suka fice gidan suka bar ni ni kadai a daki nai tsuru tsuru dani kamar manya. Ban san lokacin da wani kukan bakin ciki yazo min ba ga daki har daki amma ba ango a gurin ba gidan zaman lafiya a nan. Ina nan zaune a takure ni kadai a dakin naji sallama muryan mama naji uwargidan garbati na amsa mata sallaman ta a sanyaye. Tana dauke da wani zani kamar bargo na rufa da tocila a hannun ta na mike tsaye ina cewa sannu mama. Tace a, a Rahama ke kadai ce a dakin ashe to ga kayan kwanciyar angon ki na kawo maki idan kin kare girkin ki zakikaiwa wace zata karbi girki kayan ita ma a dakin ta. Bayani take min amma gabana sai faduwa yake min a lokacin na rasa fahintar komai da take fada min har ta fita tabar dakin ban fahince ta ba. Na kalli kayan data aje min a bakin gado tare da kura masu ido ina nazarin su. Na koma daga can kuryan dakin na zauna sama kujera tare da kara bin dakin wanda yake mallakina da kallo. Sai faman tunanen irin rayuwan da zanyi a gidan nakeyi ga maganan Sabuwa da ya tsorata ni da tace wai ni kishiya nake a gare ta. Baifi minti sha biyar ba da fitan mama din uwargidan shi sai na ji motsi alaman za, a shigo dakin nawa. Mamace again tare da maigidan nasu tana mashi jagora kallo daya zakai mai kasan baida cikkaken lafiya a tare da shi don yanayin tafiyan shi ma kawai ya nuna hakan. Da sallama ta shigo dakin yana biye a bayan ta ban iya amsa sallaman ba don girman su da nake gani. Tace Rahama ga anginki na kawo maki kin san dai yanayin da yake ciki da fatan zaki lalaba muna shi dai. Murmushi naji yayi ta juya ta fice daga dakin na mike daga inda nake na durkusa kasa nace a cikin sanyin murya ina wuni baba . Murmushi yayi yakai zaune a inda na tashi ya dan kalle ni yace yaya hidimar buki amarya ? Ban iya cewa komai ba sai sada kaina da nayi a kasa kawai babban rigar dake jikin shi naga yana kokarin cirewa tare da aje hular kan shi a gefe daya. Da alaman dama kayan sun ishe shi a jikin shi yake cewa dani sai kuma ga angon naki da matsala amarya. Sai lokacin na dan kalleshi naga duk ya ramay ya fada sosai ga yadda na san shi da farko. Dan tashi mana amarya ki miko min kayan can na saman gado na sauya ko ? Gurin da kayan suke na kalla tare mikewa zuwa daukowa na kawo mai na durkusa tare da bashi kayan. Ganin da nayi yana kokarin sauya kayan ne a gabana yasa nai saurin fita daga kofana na tsaya sai dana tabbatar da ya gama na shiga dakin. Yace yauwa zo ki zauna ko dauko ledan can ki dan samu kici wani abu daga ciki don nasan kina tare da yunwa. Nace a koshe nake baba sai da Inna ta tabani abinci naci kafin na baro gida dazun. Yayi shiru yana kallo na tare da nazarina sai kuma fuskan shi da na dan ga yanayin sa ya sauya a lokaci daya. Yace amma wanan din hakkin ki ne na yau da ya dace na baki ai na kawo maki. Nace a koshe nake shiyasa. Yace to ni miko min na danci kafin na kwanta ko ? Duk a takure nake a lokacin don yanayin yadda ya ke zaune cikin doguwar rigar jallabiya yasa nake kara jin nauyin shi sosai. To zo mana ki zauna nan amarya gaki tsaye kin kasa sukuni ko ? Gabana yai mumunan faduwa nace a raina wanan tsohon may yake nufi nazo na zauna zaman sa, a da sa, a dashi ko may ? Nayi maza na juya can daga gefe nakai zaune a kasa tare da dukar da kaina kasa ina wasa da yan yatsun hannuna cikin dan lankwasa su. Zuba min ido yayi a inda nake a zaune yana kallo na kafin ya bude baki yace Rahama yau gaki Allah ya kawo ki gidana cikin iyali na amatsayinki na mata tata. Yace don haka ina son ki kasance yarinya mai ladabi da biyayya ga wa yanda kika sama a gidan. Idan kinyi min haka kinyiwa kanki da nima adalcin rayuwa. Don bazan taba jin dadi ba a rayuwa idan har wani rashin mutunci ya fito daga gare ki a zaman ki na gidan nan. Idan kinyi haka kin min komai a rayuwana wanda hakan zai sakiji dadin zama dani bama ni kadai ba har ma kowa da zaki sama a gidan. Nace insha Allahu zaka samay ni kamar yadda kake tsanmani a rayuwana yace to Allah yai maki albarka ya tashi kata kata ya mike tare da nufar gadon da yasha shimfida yana cewa ki dai yi hakkuri da yanayi har na dan wani lokaci amarya. Daga haka naji yana bissimillah yabi lafiyayen gadon ya kwanta tare da mimikewa a sama yana sauke ajiyan zuciya. Can yake cewa idan kin gama zaki kwanta sai ki rufo muna kofan dakin daga ciki kinji. Nayi maza nace mashi tau ba, a dauki lokaci ba ina daga inda nake zaune naji ya fara nasari alaman barci ya dauke shi ke nan. A hankali na mike na nufi kofan na rufo kamae yadda ya umurce ni da nayi idan zan kwanta. Na koma kasa na kwanta ban dade ba sai barci dama jikina da gajiyan jigilar dana sha na jama, a atare dani. Bani na falka ba sai asuba ana kiraye kirayen sallah naji motsin shi haka yasa na falka tare da mikewa zaune zubur yace a kasa kika kwanta Amarya ? Ya dauki buta zuwa bandakin da akai min a kusa da dakina basai na shiga na taron gidan ba sai bayan ya fito ne na shiga nai tsarki na dauro alwala na shiga dakin. Bayan nayi sallah ban kwanta ba tunda na saba a gida bana kwanci sai aikin gida idan na tashi na gyara gadon daya kwanta tare da sharo dakin har zuwa kofana inda aka kewaye min shi nagyara ko ina tsab. Na fita zuwa tsakar gidan duk girman shi sai dana share shi kafin gari ya karasa waye, Na hada kayan wanke wanken da na gani birjit ko ina na gidan na fara wankewa . Sai lokacin matan gidan da yaran su ke fitowa daga barci duk wace ta ganni sai ta tsaya tana mamaki hakan . Ina gaishe su daya bayan daya suna shigewa dakunan su da yaran su. Ina gamawa na juya zuwa dakina na debi ruwa na shiga na watsa na saka wani lace mai laushi dashi cikin kayan da anty ta aiko min dashi. Duk da ban san kudin shi ba nasan mai tsadane kwarai ga dinkin yai matukar karban jikina kamar an auna ni kafin a dinka min shi. Can na fara jin hayaniyan matan gidan suna fitowa tsakar gida daya bayan daya haka yasa na gane cewa sun tashi ke nan na yafa gyale a kaina na fito na fara zuwa sashen mama tana kokarin fitowa daga dakin ta tana ganina tai murmushi take cewa a,a amarya baki huta ba gaki da gajiya kika fito kikai wanan aikin haka? Hutun may zatayi bayan dama an saba da komai tun a waje muryan sabuwa ce dake bayan mu hannun ta rike da wani karamin roba kore. Na durkusa na gaida mama da ina kwana mama tace lafiya kalau Rahama yaya dare yaya angon naki ? Sabuwa ta kara cewa dare kan ai kinga inda alaman shi ya nuna ba a wahala ba don ansan komai. Haba sabuwa wai may yake kawo wanan magana hakan ga wanan karamar yarinyar kuma ? Wanan ai ba sa, an yin ki bace may ta sani akan zancen ki dakikeyi yanzu sai muryan maigidan mukaji daga bayan mu lokacin ina durkushe a gaban mama yana cewa. Sabuwa ki kiyaye ni wallahi a gidan nan don zan iya saba maki akan yarinyar nan a gidan nan fiye da tsanmanin ki. Idan ba hauka ba irin naki yanzu wanan yarinyar zaki titsiye a gaban ki kina fada mata wanan magana haka ? Ina yatinyar take tashige daki ta kwana da kai ta fito kemaymay da ita har kake kiranta yarinya. Yarinya kan na bayan uwar ta ai wace bata san shigewa daki da namiji ta kwana ba kuma ta tashi lafiya tarmazazai haka ?. Ganin dayar matar tana cewa kai haba tunda wanan farar safiyan haka za, a tusa muna wani fitina a gida. Na mike daga gurin mama na nufe tare da durkusawa har kasa nace ina kwana mama ? Tace a,a amarya ni ba mamakin bace zaki iya kira na da yaya ko maman Aisha. Nai murmushi na kara gaishe ta ta amsa fuskan ta ba yabo ba fallasa cikin sa dacewa yaya daren Amarya ya angon naki koda yake gashi nagan shi ya samu lafiya ai a gaban mu. Inda sabuwan take na nufa itama na gaida ita a cikin ladabi sai cewa tayi ke tashi da kili bibin ki idan ban kwana ba zaki ganni ne nan ? Yace uhumm kaji ba ke abinda baki taba yiwa yan uwan ki an maki kuma kina jin haushi yanzu . Ni dai ina ganin sun rikice na juya zuwa dakina ban tsaya sauraren su ba. Sai zuwa can naji ya shigo dakin shima dai gaida shi nayi tare da mai yaya jikin yace jiki da sauki sosai. Zuwa can naji anyi sallama ya amsa wata budurwa ce daga cikin diyan shi dauke da kwanon kunu da kosai taje cewa baba ga abin karyawa inji mama akawo maku. Yace kice ana gaida ita da aiki ko inda nake bata kalla ba tafita daga dakin har takai kofa naji ya kirata yace suwaiba kun gaisa ne da sabuwar umman taki ? Tace baba ai ban gan ta bane tabashi amsa murmushi tayi tace ina kwana . Nace mun tashi lafiya yaya gida bata tsaya ba tabar dakin yace taso ki dibi kunun da kosan mai isar ki kisha. Nace sai zuwa anjima bani karyawa da safe haka ai yace to injin ku yan boko ne ?. Da naji alaman suna aiki na fito na samu ashe kowa ce ta fito tana aikin sana, anta da takeyi a gidan . Na kama wa mama dama kokon da takeyi za, a fita mata dashi nan da nan muka gama. Sai mai bi mata dake dafa shinkafa da wake itama na karbi wanke shinkafan na wanke mata tas na zuba tare da gyara wutan da icce ya jaye na hura wutan sai gashi ya kama. Ban koma daki ba sai dana kwashe mata shi a kwano na gyara yadda za, a fice dashi na koma daki na. Na samu maigidan ya shirya zai fita yace ina kika shige ne Amarya nace ina gurin da ake aiki ne. Yace to ni zan fita sai na dawo zan dan leka waje nagani ko akwai abinda zan iya yi a can na neman kudi. Kin san angon naki dan bida ne ba mai zaman gida bane ni. Na durkusa nace Allah yasa a dace Allah yaba da nasara a dawo lafiya baba. Yace kai ni fa wanan baban ba son jin shi nake a bakinki ba da dai za, a canza min suna ko Alhajina akirani dayafi min alheri. Nace to Alhaji Allah yaba da sa, a yasa a fita a nasara yace amin yar amarya ta yaushe rabon da naji anmin fatan alheri haka a rayuna. Nan yasa kai yafice ni gyara dakin na dan zauna sai barci ya kwashe ni afurin mai nauyi ban sani ba. Muryan yan gidan mu ne da suka shigo ganin kwanana ya tayar dani daga barci. Na mike zubur ina masu sannu da zuwa idanuwan su fes a kaina suna kallona ban san may suke son fahinta ba daga gare ni. Na gaidasu daya bayan daya tare da tambayan sauran mutanen gida. Da yake iya yan uwan inna ne sai kadan daga dangin babana sai cewa sukayi kowa lafiya sai maman ku ne dai da ta saka muna hauka wai sai baban ku ya fada mata inda ya samo kudin da yai maki hidima haka na fita kunya. Duk rantsuwan da yai mata ba yarda dashi ba wai idan bashi ya yi ba mijinkine yaba da kudin aka boye mata. Nace cikin murmushi tare da zama kan makarin kujera na kai mama ho yaushe zata bar wanan halin nata ne na hassada da bakin ciki. Ita da tace da tabar za, a kawo ni yanzu da taga sabanin haka shine kuma ta tayar da hankalinta. Rabu da mahaukaci wacce bata son azauna lafiya iji kauna babana ta fadi hakan. To yaya kuka kwashe da matan gidan naku yau da safe da fatan babu wani matsala dai ko daga gurin su. Nai dan murmushi nace babu komai mama batare da na fada masu abinda ya faruba da safe akaina a gidan. Sai dayan mama tawa tace ai ina ganin indan dai ta iya binsu zata samu sauki ga biyun mata wanan dai da take biwa ce matsala nake gani sai yaran su kuma don naga yaran a tsaye suke suma. Nan dai sukaci ga ba da yi min nasihohi na in zauna da zuciya daya dakowa na basu girman su tunda duk sun haifeni baki dayan su. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA KINCI AMANAN ALKAWARI DON ALLAH ZAI TAMBAYE KI HAKKINA NAYI HAKA A KAN KI DON SAI DA NA ROKE KI KADA KI FITAR MIN DA NOVEL DINA DON ONLINE NOVEL NE BA NA SHAGO BANE WANNAN DA FATAN ZAMU JI TSORON GAMUWAR MU DA UBANGIJIN MU ALLAH RANAN GOBE KIYAMA AMANA YAR UWA IDAN BAKI IYA RIKE AMANA KIYI MAGANA NA BAKI KUDIN KI DON BA ZAN YAFEWA HAKAN BA MUJI TSORON ALLAH KADA MU BARI SHEDAN YA RUDI ZUKATAN MU PLEASE, , , , 7 Haka rayuwan zaman sabon gurina ya kasance min agidan mijina kuma babana uwayen gidana da sukai jika dani. Manyan diyan shi maza ko matan su sun kusa haihuwa na don haka mazan nake kiran su da yaya matan su da anty. Haka ya jawo min saukin zama gidan don sun kula ban zo masu da fitsara ba ko kadan. Bani kuma kyashin taya mutum aiki koda na sana, an shi tare dani za, ayi shi har a gama kuma da zuciya daya. Wanan dalilin nee yajawo min sasauci sosai a gaare su gashi zan sha aiki idan an bani naci bana ci don ban saba da irin ciye ciye haka ba barkatai. Wankin kayan Alhaji daya cire kafin ya tashi na kwasa na wanke sai dai ya sake wasu wanka kuma ya zama kullun sabanin da da sau daya ko sau biyu zaiyi wanka a sati. Ga maclean da brushe da yakeyi akai akai yanzu yake wanke baki dashi wanda na kula shi kan shi alhajin zuwa yanzu yana jin dadin sauyin rayuwan da ya samu. Don ko wa yagan shi cikin sati dayan da nayi a gidan yasan ya samu sauyi sosai a rayuwan shi. Don nakan ji matan shi suna mashi ba, a wai auren yarinya yasa shi ya sauya ga abinda basu san shi dashi ba a baya. Sai ya basu amsa da nata sallon ke nan ke ai baki min ba a lokacin ki dana sauya din tun can. Ranan da na cika sati daya ne agidan har lokacin ba wani abinda ya taba shiga tsakani da shi ban maga alaman hakan ba daga gare shi. Ina kasa ya na saman gado kwance da ya kwanta kuma sai barci mai nauyi ya dauke shi sai safe. Amma a gurin mutane suna ganin akwai abinda ke shiga tsakani na dashi a cikin dare don nakan ji sabuwa na cewa dashi ya daiyi a hankali kada ya takura karfin shi kan karaman yarinya yaje yajawa kan shi matsala kuma ? Dariya yakan yi mata yace ai yafi son haka don lokacin ta ne abar ta tayi nata zamanin. Sauran matan ba ruwan su da sha, ani na sai girmamawa amma sabuwa kan kullun sai tayi kokarin sake min magana a tsakar gida wanda zai bata min rai. A banza don wani zancen ma ban san wai dani takeyi ba har ta kare haukan ta. Idan ina zaune wani sain nakan ce ashe haka shine aure ba takura ba matsi ba tsangwama irin na mama a gidan mu ? Gashi duk Alhaji zai shigo sai ya dan sayo min dan abin tabawa watarana ma har kayan shayi da biscuit da su sweet zai bayar akawo min . Haka yasa na sake jikina sosai dasu wani sain har yar hira mukan yi dashi kafin yai barci sai dai hiran tamu nakan ga yana dariya sosai idan ina shirmay na. Ranan ya dawo daga kasuwa ya tara mu a dakin mama Hausi uwar gidan shi kusan nice ta karshen shigowa dakin inda suke zaune. Ina shigowa na samu guri na durkusa tare da gaida su gaba dayan su suka amsa min ina nan dai durkushe sai cewa mama tayi. A, a Amarya samu guri mana ki zauna ai ina ganin magana Alhaji zaiyi da mu. Nace mama har dani ? Tace kai amarya ke ba matar shi bane yanzu har da ke mana. Shi dai murmushi yayi kawai yana sauraren mu can bayan mama Hausi na koma na takure kamar uwata. Can dai yai gyaran murya alaman zai fara magana ke nan a lokacin don haka naga kowan su ta natsu. Yace to Alhamdullahi yau dai amarya ta gama satin ta daya kamar yadda sharia ya tana da. Don haka yau ne zan koma dakin wace keda girki a cikin ku don haka ina rokon alfarma gurin ku. Wanan yarinyar da Allah ya kaddari zaman ta a cikin mu da kuji tsoron Allah ku rike ta amana kamar yar cikin ku. Yar cikin mu kuma Alhaji kishiya ce zan rike kamar yar cikina ta kwana da kai in kwana da kai kuma in rike ta kamar ya ta ? Wanan maganan baiyi ba gaskiya ka dai sake wani maganan inji sabuwa dake magana a hasale a lokacin. Murmushi yayi yace sabuwa ke nan ba laifi yadda kika dauke ta a tafi a haka sai dai saukin abin Allah yasa bake kadai nake aure ba. Kuma bake ce uwar gidan gidan nan ba kinga ashe ba wani matsala ga hakan. Ita Rahama har wani kishi ta sani a yanzu bayan daukan ku uwayen ta da takeyi tana maku bauta may kuma kike so a gare ta. Eh yanzu kan hakane a/a idan ta goge ai babu shegu nan gaba kamar mu, balle yadda naga kana rawan kafa haka a kan ta wai kai ka samu yar jikan ka ka saka a daki kana abinda bai dace ba da ita. Haba sabuwa wai may yasa baki da hakkuri ne ke inji mama Kulu matar shi ta biyu. Yai murmushi tare da cewa ai ba rashin hakkuri bane gani takeyi abinda tazo gidan a lokacin tana maku rashin kunya shine itama yar mutane tazo dashi zatai maku. Sai dai ki sani alama ya nuna tarbiya ba daya ba wallahi don ke ko kwana ba, ayi ba kika fara sakani ga fitina. Amma yanzu ki duba karamar yarinya tasan daraja na tasan naku hakama na iyalina baki daya. Au to kana nufin ta fini ke nan yanzu maji magana ai gara da ka fito fili ka fada min kowa yaji. To bari kaji Alhaji wallahi duk ranan da yarinyar nan tai gigin shiga harka na sai dai uwarta ta haifi wata don ko ban halaka ta ba zaka dawo ka samu ankaita jiya gidan su. Yace ke ko da kin kwana a gadirom rana wallahi da karshen zaman ki gidan nan yazo sabuwa da kinyi nadama mara adadi a rayuwan ki. Yace naga abin naki ba wasa bane yanzu wallahi duk ranan da kikai gigin taba lafiyan yar mutane sai na lahira yafiki jin dadi a garin nan. Lalai ma ba, ayi ba yanzu aka soma ke nan don kayi dandane haukace ka zauce kamar wanda bai taba jin dadin bujen mata ba ko ? Yai murmushi yace kaiyya a fili tare da girgiza kan shi yace ashe kin gane wani bujen yafi wani buje ke nan. Ranta yai matukar baci bata karasa ba taji yace dama abinda yasa na tara ku nan shiine ke hausi ke ce babba ke zan roka alfarma don Allah. Ina son yarinyar nan ku dauke mata nauyin girki a gidan nan don kunga karfin ta bai gama kaiwa ba don Allah a dan sahirta mata wanan aikin har ta dan kara tasawa nan gaba idan Allah ya ce. Cabdijam ba ta iya aiki amma tana iya shigewa da kai daki tai shiru har safe ko ? Kai sabuwa inji mama kulu tace waban bai dace ba gaskiya shi fa ke da gidan shi balle ma wanan yaushe zata iya tuka tuwon gidan nan haka ? Ai dama nasan duk da hadin kan ku don ai min bakin ciki kuka hada baki akawo ta gidan nan idan hakane bazatayi girki ba sai dai nima na dinga yi ni da yarana kawai wallahi. Isan kinyi hakan ma daidai ne inji Alhajin amma ki sani cikin ki tayi don su nan duk suna da sarakai da zasi girka masu ba sai sunyi ba kece mai yara kanana da yawa kuma. Tace koma maye na dai ji muddin wanan yar mussan da ka kwaso baitai girki ba nima bazan yi ba wallahi yace har da shan wallahii tace eh na sha. Mama hausi ta bude baki zatai magana ya dakatar da ita yace Hausatu kada kice komai hakan ma yafi min komai dadi daga yau kowa ta girka nata da diyan ta ita kuma Rahama ta girka wanda zataci can shiyan ta. Dama ba yau ba kike min korafin sai nasa sarakaina suna girkin gidan nan naki biye maki amma yanzu tunda haka kike so hakan yai min dadi wallahi. Sai dai kada ki manta ba leken tallen kowa ba kuma wani zancen na wance yafi nawa na kashe wanan korafin a gidan nan. Yarinyar na kuma ba ruwan ki da ita ko irin habaicin da nake ji kinawa yar mutane kada na kara jin shi a gidan nan. Idan ba haka ba wallahii rai zai baci don haka ke Kulu da hausi ga amanan wanan yarinyar gare ku da diyan ku na danka maku don Allah ku tayani bata tarbiya yadda ya dace. Sukace insha Allahu Alhaji mu yarinyar nan bata tsare muna komai ba wallahi har yaran mu tunda tasan darajan mu. Ko yaran nan suka dawo kasuwa har kofan su takee binsu tai masu sannu da kasuwa yaran su kuma tana haba haba dasu . To yaron da yasan haka may zakace akan shi kuma sai fatan alheri yadda muma muka haifa itama Allah ya bata nata tasaka a cikin mu ba shi ke nan ba. Yace nako gode dama nasan bazaku ki duk wani abinda na koso ba gidan nan indai har alheri ne da jin dadi na don haka Allah yai maku albarka suka ce amin a lokaci daya. Yace ke kuma Rahama tarbiyan nan da iyayyen ki sukai maki ina son kici gaba dashi don shine tubalin zaman ki gidan nan. Can sabuwa tace muma da ba a saka muna ba Allah yai muna shi sannan yaya zancen namu kayan dakin daka saya mata. Cikin mamaki yace kayan daki kuma nine ma na saya mata kayan dakin nata ke nan. Tace idan ba kai ka saya mata ba uban waya basu kudin sayen wanan kayan haka giredi masu kyau ? Yace toni wallahi ko ku yarda ko kada ku yarda ban san komai ba akan wanan zancen. Ita bata da mahaifa ne da zasuyi mata ban san lokacin da nace nikan anty na ta birni ce tai min komai ba wani ba. Yace to kinji tai wani irin murguda baki tace haka dai akace kawai amma wata anty gare ta na birni da zatai mata wanan. Yace to yanzu dai kowa yaji kowa ya tsaya a matsayin shi babba ya rike girman shi karami ma ya rike nashi. Yace ku tashi ku tafi na gama magana na ni ban son wani abu kuma ya biyo baya. Bayan fitan su sai ni ban fice daga dakin ba mama tace Rahama tashi zuwa dakin ki kinji. Nace mama ni anan zan kwana tsoro nake ji ni daya a dakin nan kada sabuwa ta kashe ni. Subbahanallahi inji su suna hada baki ita da mijin ta yace kin gani ko ta riga da ta tsorata a gidan nan da sabuwa. Mama hausi tace kinga tashi na sa zuwaira ta tayaki kwana a dakin naki ba shi ke nan ba. Daga ranan muka fara kwana ni da zuwaira a dakina kafin mu kwanta mukan yi hira na ta karanta muna labarai a littatafai. Idan nace ina da wani matsala kuma nai karya girkin abinda zanci ma sai na so don idan su mama sunyi nasu suna saka min wani lokaci naci wani sain kuma nace na koshi. Gashi ban gajiya gurin kama masu aiyukan su tun suna hanawa har sun gaji sun kyale ni ina yi da zuciya daya don yadda uwa da yar ta suke haka nake dasu su biyun. Idan girki ya zo kaina a dadafe cikin takura nakeyin shi don Alhaji kan min nauyi a dakina har yanzu na kasa sake jikina dashi. Sai ma kwana da zuwaira yafi min ace shine zai kwana a dakin duk da ba komai yake min ba sai lalashi da ban hakkuri wanda ni ban fahinci na maye ba. Nayi kyau dani haskena yafito har dan kiba na kara gani shar fes dani idan kin gan ni. Har kirjina dake a shafe sun fara tasowa yanzu sai dai duk wanan dadin da nake ci hankalina yana gurin Innata ko yaushe don yanzu ban san wake dibar mata ruwa ba wake mata talla wake mata aiki don kanni na duk yan maza ne. Kaunata mace yar karama ce sosai ita aka yaye ba a haifi wani ba bayan ta ko may yasa inna bata kara haihuwa ba oho ? Sallaman wani yaro ne a kofana rike da dakwalen kaji guda biyu a hannun shi sai kayan miya a wani leda mai yawa yace Alhaji ne yace ya kawo min. Na karba yaron zai tafi nake cewa ya tsaya nazo na shiga daki na dauko mai biscuit na bashi har ya fara tafiya yace. Amarya Alhaji ko na tsaya na taya ki gyaran kajin ? Nace to shi ke nan dauki kaje a yanka bari na sa ruwan zafi kafin ka dawo ya juya dasu yafita. Daidai lokacin da sabuwa tafito daga daki yaran ta sun fada mata an kawo kaji a sashe na yanzu sai ko ga yaron tafe dasu za, a yanka. Tabi kajin da kallo har yaron ya fice daga gidan tanisa tace hum, umm ashe akwaita ke nan ? Tare da yaron muka gyara ya kama min nayanka na zauka na shuga jajagen kayan miya kafin wani lokaci har guri ya dauki kamshi. Miya ya kammalu na sauke na dora tuwo duk tare da yaron nan da yace min sunan shi habib ne dan gidan mai faci. Sai yamma Alhaji ya shigo gidan daga shiyana ina zubawa yaron abinci naji muryan sabuwa tana cewa yau wani sabon cin amana ne da muna funci ya taso a gidan nan kuma ?. Kamar yaya kuma ya tambaya tace duk munafuncin da kake a gidan nan nabawa yarinyar nan kayan dadi taci don ta yarda dakai ta kwantar da hankalin ta ka murje ra yadda kake so nagane ka. Mu sai ka tura muna tuwo ita ko daga shinkafa sai taliya kake bata bata taba cin tuwo a gidan nan. Ga kowa yai cirko cirko yana sauraren ta yace cikin daka tsawa ke sabuwa ban son sheri ni kike kira da munafuki yau. In ma har munafunci ne ai ake nakeyi don ke ce munafukan kullun a gidan nan ba mai bani bani sai ke, ke, kenan kullun yin karya da ciwon yara ba ranan da zan fita baki karbi kwabona ba a gidan nan karyan yau daban na gobe daban. Kaji kuma na sayo mata don itace mai girki su nake son ci shiyasa na sayo ke ranan da zan sayo bacewa kikiyi wai nabaki kufin ba ki sayo da kanki dana baki na dawo cewa kikayi n sace kudin ai. Nawa nake ba wanan yarinyar a gidan nan ko bata nayi yadda nake bata sai dai tace na sayo mata duk abin da ya dace idan na fita. Sabuwa nan ta hau borin kunya akan wai Allah dai ya kama ka yau kila ma har gashin dare kake kawo mata kai a dole gaka mijin yarinya ko ? Sabuwa yau dai na gaji da sherin ki a gidan don haka na fada maki akan yarinyar nan zan iya saba maki kifice min daga gida. Ahayye nanaye abin kunya wai aure da mara kwabo yace balle da kwabona ko kin manta kwabon kika gani a baya kika lake min da aike da komai har na yarda kika shigo gidan don haka yau ko wayai maki tsaye a gidan nan wallahi baki kwana min a gida. Maimakon ta ci gaba da gudan da takeyi sai kuma jikin ta yai matukar sanyi sosai don tasan takan mashi fiye da haka amma bai taba yanke irin wanan hukuncin ba a kan ta sai yau kuma akan yar karamar yarinya. Nan dai mama hausi ta saka bakin ta tace asha Alhaji da baka biye mata ba halin sabuwa ne kuma bako a gare ka yau. Yace bari hausatu nagaji da sherin yarinyar nan yau ta kaini kat ne ita bata ji kunyan yaudara na ba sai nine zanji kunyan ta. Ina kazan nan a kowan ku da yai girki sai da na saya mai aka girka min naci amma don wanan yarinyar na da girki na sayo zatai min sheri tace ai ba biyu ka saya muna ba kamar nata. Bai kula ta ba ya shige dakin ta da kan shi ya kwaso kayan shi na kwan ciya ya fito daga dakin nata. Hankali yai matukar tashi sosai a lokaci don nasan halin kauyen mu yazu labari zai sha banban ace daga shiga na na fara watsa matan gidan da na samu. Hakana jiki ba kwari na dinga aiken wanan yaron da Allah ya hadani dashi yau yana kai wa kowa miyan duk sai da na kusa rabe naman don yawan gidan. Mama hausi dake zaune tare da sarakan ta matan diyan ta su uku ta ce kungani ba yanzu ga naman ma karshen ta duk ta rabe shi gare mu. Har ya fita zuwa sallah ya dawo bata bar gidan ba kamar yadda ya bukata haka yasa shi zuwa har kofanta ya daga labulen dakin yace. Sabuwa may kike jira ne a gidan nan wai ai tunda gidan nan bana ubanki bane yau na fada maki wallahi baki kwana min a gida ki tafican gidan ku kikarata can. Idan kuma kin ki fita yanzu na turo masu karfi aja min ke da karfin tsiya har waje. Ganin haka tasan kuma da gaske yake yi yasa ta fara tattara kayan ta tana kuka wai saboda karamar yarinyar da kokwai bai aje da ita zai koreta gidan shi ita dake da yara bakwai a gidan. Haka tafice daga gidan bakin ta bai mutu ba ta nufi gidan su a cikin dare kowana na kallon ta a wullakance. Sai bayan tafiyan tane na fahinci ashe halinta ya ishi kowa agidan sai fadin aibunta kowa keyi. Nan naji abubuwa da dama akan halinta ashe shiyasa take ganin an auro ni zan karbe mata power da take dashi a gidan da gurin mijin su. ****** ********* ****** Washegari tunda safe na shiga gurin mama bayan na gama aikin da nakeyi na kwashi kayan wankin ta sai aune tayi dani ina wanke tufafin ta. Ta saka salati tana cewa haba amarya ai sai kina ace muna bautar dake ko iyayyen ki suka samu labari bazasu ji dadi ba gaskiya. Nace daidai danta babba yana shigowa gidan dauke da dan karamin yaron shi a kafadan shi haba mama don nai maki wanki shine za, ace kina bautar dani kefa uwatace mama ba kishiya ba kamar yadda naji ana fada. Ko a gida nike wankewa su innata har da mama kayan su idan yai dauda don wanan kayan da baida yawa ma. Girgiza kan shi yayi yana cewa a ranshi ikon Allah yanzu baba wanan karamar yarinyar daya kwaso kurciya zalla haka may zai gane a gurin ta ne wai. Nan dai dole uwar ta barni da wankin na wanke su fes na shanya na koma dakina ina jiran su bushe na kwashe mata. Yaron nata mai suna yaya sani ya shigo dakin mahaifiyar tashi ya samu guri ya zauna daga gefen ta yace. Mama dazun sai nake jin ki da amaryan ku a bakin rijiya kuna gaddama kuma akan wanki. Tace bari kaidai ni kurciyar yarinyar na ya fara daure min kai wallahi bata tasan kyashi ba ko hassada a rayuwan ta komai haka zata zage tayi shi tsakani da Allah. Yace haka naji nima sai dai mama gaskiya sai kunyi da gaske gurin rike amana tun da dai ba sanin ciwon kan ta tayi ba yarinyar gashi uwarta tai mata tarbiyan da ya dace duk uwa ta gari taiwa yarta. Tace insha Allahu haka nake kokarin ganin nayi yo har ma may mutum zai cuta a wanan gurin kuma ? Nan dai sukai ta zancen su har suka fado kan maganan sabuwa da irin hallin gallaza masu data dinga yi a zamanin ta a gidan. Mama hausatu tace don yaran ai ayi hakkuri ta dawo dakin ta gashi kuma bazan so ace don wanan yarinyar tabar gidan nan ba. Kada azo a shafa wa yar mutane labbo bata ci ba tasha akama zarginta ga banza kasan haln mutanen yanzu da dauka su dagwarawa kan su maganan da bata shafe su ba. Dan nata yace hakan yana da kyau mama indai wanan mara mutuncin ne aiko ta dawo ba dainawa zatayi ba. Gara dai tadawo dakin ta din zaifi don kaga yanzu idan tafice gidan nan nauyin diyan ta duk akaina zai dawo gasu ba tarbiya ke garesu ba. Yadda mama hausatu tai shawara da danta haka akayi da yamma da Alhaji yadawo gida ta sanya shi a gaba tana bashi baki akan yayi hakkuri ya daure sabuwa ta dawo dakin ta hakana ko don yaranta. Yace wai hausatu ke ce ke auren ta ko ni da zaki isheni naje nayo bikon ta ina indai sabuwa ce koke bata bari a gidan da tsufanki kuwa ? Mama hausatu tace kadai yi hakkuri Alhaji kodan yaran ta ta dawo taci gaba da duba abinta. Yace yara ai bada su tazo ba anan ta samay su kuma a gidan iban su suke ko ? Ya ja tsaki ya dauki buta ya fice daga gidan. Gaba daya yaran Sabuwa sun ishi matan gidan da rashin kunya idan ka cire shi Alhajin da basuyi a gaban shi don tsaye yake akan iyalin shi. Don haka shi zaman su ma babu uwar su a gidan ko a kwallan shi bai taba damuwan shi ba don dan ficewan ta har ya samu natsuwa tare dashi. Satin ta daya shiru babu labarin dawowan ta gidan har wanan lokacin ganin maganan wasa zai zama gaskiya yasa. Mama hausatu samun wani dan uwan Alhaji kuma amin shi akan zancen sabuwa din don yaran sun ishesu ba hutu gareta. Bayan sun gaisa ne tayi mashi bayanin komai akan matsalan da ake ciki tsakanin sabuwa da Alhajin. Malam shehu yace a gaskiya ba yau ba Alhaji hakkuri yake da al, amarin sabuwa ke ma kin sani . Don ko jiya muna tare nan dashi yake min bayanin komai don iyayyen ta da yan uwan ta sun damay ni da zariya agida. Amma tunda kinzo ba komai insha Allahu anjima zan samay shi muyi magana idan ya dawo. Mama tace don Allah malam a taimaka a sa baki ga alamarin a gyara tun bai baci ba kodon yara. Daga haka sukai sallama ta tafi tana godiya don sun saba dashi sosai akan matsalar gidan su. Duk yadda ya raya da Alhaji akan yai hakkuri Sabuwa ta dawo dakin ta yaki yarje mashi. Don haka ya kyale shi malam shehu ya nemi wani amin shi da magariba suka shirya sai gidan wan sabuwa inda take zaune. Lokacin da suka isa gidan sun samu wan nata baya gida dole suka dan jira shi don ba nisa ya tafi ba. Bayan sun gaisa ne suke cewa da shi dama mun biyo bayan sabuwa ne don Allah ayi hakkuri ta koma dakin ta hakana. Don sabani akasamu kuma yanzu kowa ya gane kuresa don ko tsakanin harshe da hakori ana samun sabani balle mutum da mutum don gaskiya iya hakkuri kukan ku kun sani Alhaji garbati yana iya hakkurin shi da sabuwa a gidan shi. Yayan nata yace hakane amma naso ace shi Alhajin ne yazo nan da kan shi don na kara bashi hakkuri saboda nima dan zaman ta cikin iyalina nasan yana hakkuri sosai. Malam shehu ya jinjina kan shi yace hakane amma da zuwan Alhajin da namu duk kusan guda ne don a madadin shi muka zo mu. Koma may nene ai yanzu ta san ta fara kaishi bango don baka kallon babban mutum kamar Alhaji garba tsakiya iyalin shi tace mai munafuki. Yayan nata yace don Allah akara bashi hakkuri kafin nazo har gidan na bashi. Yayan yace kafin ku tafi bari na kirata taji da kan ta don ku kara ja mata kunne mace da girman ta kamar Sabuwa ace wai ta saura yaji don rashin hakkuri irin nata. Bai jima ba suka fito a tare yana gaba tana bayan shi ta samu guri daga gefe ta tsugun na. Yayan nata yace sabuwa ga malam shehu nan sunzo bikon auren ki a madadin maigidan ki. Ta dukar da kai cikin kunya da nauyi zatayi magana malam shehu yace da ita. Haba Sabuwa yanzu lokaci yayi da za, a san girma ya kama a daina wasu halaiya kuma. Don Alhaji ya auro wanan yarinyar bai kamata ace daga gareki ne ba a samu zaman lafiya ba idan kin yi tunanen irin zaman da kukayi ke dashi har takai kina ci masa mutunci a tsakiyan sarakan shi hakana. Don haka idan kin koma dakin ki da fatan komai zai sauya daga gareki yanzu shiga ki dauko kayan ki basai gobe ba mutafi na mayar dake dakin ki. Zatai magana yayan nata dake zaune a gefe yace ya katseta cikin bacin rai da cewa . Kin sani sarai bana son tashin tashin kije ki shiryo ku tafi. Ba don taso ba ta tashi ta shiga ciki can sai gata tafito da lulubinta dauke da dan ledan kayan ta suka kama hanya. Ko da suka iso gidan sun samu Alhaji a kofan gida shi da baba salla zaune suna hira. Yacewa Sabuwa shiga gida ta shige simi simi ciki shi kuma ya tsaya wajen su Alhaji dake kallon shi a cikin mamaki. Nan ya zauna ya dinga bashi baki akan yayi hakkuri ya taushi zuciyar shi akan iyalin shi. Yace babu komai tunda taci albarkacin shi zai kula ya saka ido ga komai a gidan insha Allahu. Muna zaune kofan mama gaba dayan mu gidan ga hasken farin wata ya haske ko ina anyi gungu gungu ana hira. Sai ganin shigowan ta kawai mukayi gidan da kumshin kayan ta babu ko sallama. Kowa ido ya saka mata wasu sun gane cewa itane musanman ma yara ta da suka hau ihu eh mama mama da murnan su. Nan dai duk da batai sallama ba aka shiga gaida ita tana amsawa cikin basarwa ta shiga dakin ta. Ganin akwai duhu a dakin sai gata tafito tana cewa mama yaya ara min fitilar ki na haska naga guri don Allah. Mama tace a dauko mata ta amsa fuuuu ta juya zuwa dakin nata daya daga cikin sarakan mama tace bisimillahi Allah matsala ta dawo ke nan kuma. Kowa nan suke fadin albarkacin bakin su akan dawowan nata kuskus kus daya bayan daya muka watse gurin kowa ya kama gaban shi. Da daddare can sai gashi ya shigo gidan dakina ya nufo don nice da girki a ranan. Ya samu kujeran da yake zama kafin ya kwanta ya zauna na gaida shi da dawowa yace. Amarya kinga wanan fitinanan ta dawo gidan ko ? Nace wa wai maman Suwaiba ? Yace ita , Don haka abinda nake so dake kikama kan ki daga gareta daga ita har yaranta ba tarbiya ne dasu ba. Nace insha Allahu zanyi kamar yadda kace Alhaji bazan shiga tsabagan taba ko na diyan ta a gidan nan. Ashe sabuwa tun shigowan shi gidan tana hankalece wai ita a zaton ta tunda ta dawo ranan a dakin ta zai kwana don haka takeyi wa sauran matan nashi a baya. Tana ganin ya wuce zuwa dakina wani tukukin bakin ciki da kishi ya rufe mata zuciyar ta a lokaci daya. Don haka tafito fuuu zuwa dakin mama hausatu tafada mata daki tana haki tace yaya kinga wanan mutumin baya son a zauna lafiya a gidan nan ko ? Mama tace da akayi may kuma Sabuwa ? Tace amma ai yasan na dawo amma ya iya wucewa ko dakina bai leko ba yana nufin cewa yarinyar nan itace zatai girki ko may ? Ke sabuwa wai yaushe zakiyi hankali ne ke ki san jiya ba fa yau bane ? Idan mu dacan kin samu kina muna yadda ran ki yaso yanzu baki tunanen cewa wata tazo gidan ne. Gara ki rufawa kan ki asiri ki zauna dakin ki ki dubi yaran ki zai fi maki sauki wallahi . Aiko da dakike muna hakan idan kin dawo kema kin san ba hakkin ki bane yin hakan don dai a zauna lafiya muke saka maki ido kawai. Yanzu kuma wata tazo yarinya danya sharaf kice zaki tauye mata nata incin kinga haka zaiyuyu kuwa. Gara ki kama kan ki da mutunci ki a gidan nan tun bakija wa kan ki raini ba ga yar diyar cikin ki da ko uwarta kin girma ga haihuwa. Nan dai taga ba ci idan tace zata ja gashi da kyat ta samu tadawo dakin ta tun ba, a kwana ba kuma ace wani matsala ya taso a gareta haka ? Ta juya cikin kwafa zuwa dakin ta tana faman mita da ace tasan zaman da muke da mijin nata da take ganin na anshe mata data bawa kanta lafiya. Don idan tace taja wani fitina da daren nan wani sabon tonon asirin ta ne zai a bainan jama, a don yanzu maigidan nasu akan yar karamar yarinya baijin ass. Don a dole banda yadda zanyi nake zaune gidan gashi har takai iyanzu na saba da komai ina zamana hankali a kwance tunda ba takura. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NA GANIN KI DON AMANA NE, , , 8 Izuwa yanzu komai na gidan ba matsala saboda kakausar kashedin da manyan diyan Alhaji suka taru a tsakar gida sukayi. Kan abar masu mahaifin su ya samu lafiyan shi don yawan futinan da aje saka shi zai iya jawo mai wani sabon matsala kuma. Sunyi barazanan daukan mataki akan duk wace take kawo masu yawan tashin hankali a gida. Wanan dalilin yasa gidan ya samu kwanciyan hankali na kwana biyu. Gashi dai zan iya cewa Alhaji yana cikin mazan dake kokarin ganin yaba iyalin shi kulawa don bai make aljihun shi ga iyalin shi. Kwanciyan hankalin da na samu ba fitina ba tsangwama yasa na sake murjewa nai kyau nai haske sosai. Nan kan kula da yanayin Alhaji idan yana dakina sai naga ya tsura min ido kawai can naji ya sauke ajiyan zuciya a sanyaye. Ban daukan wanan a komai sai dai naga kamar wani abune ya shige mai a duhu yake saka shi a tunane. Ban sani ba ashe tausayina ne yake ji yana ganin kamar ya shiga hakkina da yawa. Yakawo ni gida ya girke ba biyan bukatan komai a kaina bai san ni haka wani gata ne Allah yai min ba da hakan. Allah bai barin bawan shi mai hakkuri ya tabe banza a duk inda yake watarana sai kaci riban hakkurin ka insha Allahu mudfin kayi shi da zuciya daya. Ranan na tashi da safe na shiga nai wanka bayan na gama yan aiyuka na sai ganin nayi jini yana zubo min a gabana. Tun ina bini bini kewayawa na wanke har tsoro ya fara kamani gashi naki sakin jikina ko cikin gida naki shiga na taya su aikin komai a ranan. Sai bayan sallah azahar da naji kowa ya shige dakin shi na idar da sallah na nufi gurin mama hausatu. Na samu ta idar da sallah tana zaune tana lazumi ita kadai a daki tana ganina tai dan murmushi a fuskan ta tana cewa Amarya . Yanzun fa nake zancen ki a zuciyana yinin yau banga kin fito ba tun safe da muka gaisa nake cewa ko dai lafiya kuwa ? Nakai zaune tare da cewa wallahi mama yau banda lafiya akwai matsala shine nazo na fada maki. Cikin sauri tace subbahanallahi may ya samay ki kuma yar nan ? Shiru nayi ban san may zance da ita ba a lokacin sai dai kaina dana sada a kasa kawai. Tace may yafaru amarya gaya min mana nifa ban dauke ki a kishiya ba matsayi diya ta ta cikina nake daukan ki. Na kara dukar da kaina a kasa nace mama dama sai nai shiru can kuna na dago na kara cewa a sanyaye dama yaune naga jini kawai yana ta zuwa min a karkashina tun safe da na tashi ga marata sai ciwo yake min. Nace barin fada maki ko zanga likitane tun cutar bai min yawa ba ? Tace cikin mamaki ikon Allah Rahama dama baki fadi bane sai yan zu ? Na dago kai da sauri na dan kalle ta tace wanan ne karo na farko da kikaga haka ko may ? Nace mata a sanyaye eh mama. Tace to ki saurare ni kiji da kyau wanan abin da yazo maki zan iya cewa ba cutane ba kuma cuta bane alama ce ta girma yazo maki da hankali da samun natsuwa. Duk ko wace mace da kike gani tana yin wanan abin a rayuwan ta wace bata yi kuma to tana da matsala kuwa babba. Wani irin ajiyan zuciya na sauke taci gaba da fadin kada ki tsorata da hakan nan tafara yi min bayanin yadda zan kama kaina a lokacin da nake cikin wanan laluran na fashin sallah. Kamar yadda uwa zatai wa yarta bayani haka ta zauna tai min bayani sai daga karshe tace da zaran kin gama zakiyi wanka kamar yadda kike yin wankan janaba. Nace wankan janaba mama tace eh idan kin kwana da mijin ki ba kikan yi wankan tsarki ba ? Nace eh kawai ba tare dana fahinci may take nufi ba tace to shima hakan zakiyi sai dai gurin niyya ya banbanta ne wacan janaba zaki ce wanan kuma haila. Nan dai ta kara koyar dani komai nace nagane mama a makarantan boko dana islamiya duk an koya muna shi na kuma rike. Nace mama dama wanan jinin shine jinin hailan da ake nufi tace shine amarya sai jinin haihuwa shima tai min bayani da kwanakin da ake son mace tayi ta fara yin tsarkin shi. Na gamsu sosai da bayanin mama akarshe take ce min sirina ne daga ni sai mijina kawai daya zama dole ya sani ake son ya sani idan ma ina fashin sallah naga kowa ya tafi sallah na shige daki nima kada na zauna a waje kowa ya fahinci ban salla don siri ne babba ga mace. Nai mata godiya tare da mikewa na wuce zuwa dakina na kimtsa jikina kamar yadda tai min bayani nayi. Ina fita na bata tausayi sosai sai dai bata ga laifina ba sai na iyayyena dake da alhakin haka akaina. Gashi yar karama dani a wanan zamanin an min auren cushe ga miji, mijin kuma babban mu kamar alhaji gashi ashe ko hankalina ban gama mallaka ba. Kamar yadda mama ta fadakar dani hakan ne nayi na gyara jikina tsab mai makon na ma dinga shiga mutane sai kawai na dinga nisanta kaina da jama, a baki daya gani one two one ta na kewaya na gyara jikina. Da maigidan ya shigo gida ne mama ke fada mashi cewa ashe amarya sai yanzu ta fadi yau ta samay ni cikin damuwa take fada min don bata san kaiba. Shima yai mamaki kwarai jin sai a lokacin na fadi ashe kuma ban san komai ba akan faduwa hakan na nufin ke nan har yanzu ina a matsayina na cikakkan budurwa as a virgin . Tausayi na ne ya kara kamashi a lokacin ne yai daya sani shiga rayuwa na da yayi da wuri haka nan. Ke nan zancen da kishiyar mahaifiyana ta fada mai nacewa gara ma da yazo nema don ni watsatsace ban da kamun kai na san maza ko zan iya zama dashi ai ban ganin tsufan shi tunda maza nake so a rayuwana. Wanan magana babu inda ya hango kamshin gaskiya a cikin sa don dai halin rayuwa na ya nuna mai ta ko ina ni yarinya ce mai mutunci da kima nasan darajan kaina da iyayyena. Don haka dole ne yai min adalci akan zaman da nake dasu don ya fahinci yarinya ce ni sharaf ban san komai ba na duniya. Wanan dalilin ne yasa ya kara jawo ni jikin shi sai naga yana haba haba dani fiye ma da farko da yake min. Mutanen gidan ganin kwana biyu bana yawan fitowayasa suke shigowa daya bayan daya suna tambayana may ke faruwa dani ne wai ? Sai cewa masu nake banda lafiya ne bana jin dadin jikina na ne shiyasa. Su daukan su na samu cikine, wai, sai naji suna cewa Allah ya ingata ya kawo muna mai albarka. Jin haka yasa Sabuwa ta fara dan sake magana tana fadin an dai ji kunya wallahi . Karshen muna funci ya baiyyana ace muna ba, a da lafiya amma sai ga shi an iya labewa da karamar yarinya har ana dirka mata ciki. Abin kunya girma ya zube kamar wanan yar yarinyar za, a ce wai ta samu ciki da mutum irin Alhaji wanda kewa iyalin shi ikirarin baida lafiya bai iya komai da mace amma ya takure a gidin yarinya karama to ga abin boye ya fito fili ai kowa ya gani yanzu gaskiya ya baiyyana. ****** ********** ****** Tun lokacin da na fara period naga gaba daya na sauya wani girma ya zo min ga kayan dadin da nake samu ina ci iri iri gwagwadon halin yan kauye irin dadin su na kauye. Wani lokaci sai nayi kyauta da wani abin ma na rabawa yaran cikin gida su ci don ban iya ci ni don ban saba da yawan ciye ciye ba a rayuwana. Zaune nake a saman kujeran dakina nayi tagumi da hannuna na hagu na zurfafa ga tunane. Sai ganin shi nayi ya shigo dakin na bishi da idanu kamar shima yadda ya bini da kallo don ganin yanayi na a cikin damuwa. Guri ya samu ya zauna a bakin gado yana kokarin cire babban rigar dake jikin shi. Yace may kuma ya faru na gan ki haka amarya, murmushin kake nayi wanda bai kai ciki ba a fuska na. Yake cewa wai may ke faruwa ne ko anyi wani abin ne kuma bayan fita na ? Nace babu komai tashi yayi daga inda yake ya dawo kusa dani ya zauna saman kujera two seater dani kai a zaune. Yake cewa fada min mana may akayi ne wai naga yanayin ki ya nuna min kina a cikin damuwa. Nace ba komai Alhaji tunane Inna ta kawai nakeyi. Yace wani abu ya samu inna din ne kuma ? Kai na girgiza mai alaman a, a. Murmushi yayi tare da riko min hannuwa na wani irin yar naji har cikin zuciyana tare da jin nauyin shi na ganin ya taba min jikina karo na farko zamana dashi. Ban kai ga karasa mamakina na ba naji ni ya kwantar dani a saman jikin shi yana dan shafana a hankali. A take naji yanayina na neman gagarana zama a gurin da nake zaman tsara dashi. Yace ki kwantar da hankalinki insha Allahu akwai shawaran da nakeyi akan ki idan har nakai karshe wata kila ma zaki koma gurin Inna din da zama na dindindin. Da sauri na dago kai ina duban shi yace ki dai kara hakkuri kinji Rahama dan bani lokaci kadan. Nace ni ban son komawa gidan mu gurin inna ta, zama na nan yafi muna komawa gidan su Inna yanzu hankalin ta a kwance yake don mama bata gani na balle ta tayarwa Inna da hankalinta . Ni nan zan zauna gurin ka kana kula dani fiye da Inna ta da baba na ban cikin matsin mama kuma yanzu. Dukar da kan shi naga yayi a kasa sai naga hawaye suna zubo mai sannu a hankali. Cikin mamaki nai zubur na mike daga inda nake a zaune tare da dawowa gaban shi na tsugun na ina cewa . Don Allah Alhaji idan har na fadi wani abinda ba daidai bane kayi hakkuri kayafe min naji zan koma gidan mu gurin Innata muyi ta hakkuri da rayuwan da zamu tsunta agurin mama. Ji nayi ya tallafo ni daga gurin da nake a tsugune zuwa jikin shi ya rugumay ni yana dan shafa min bayana tare da fadin ya isa haka kiyi shiru babu inda zaki tafi kina nan tare da mu insha Allahu. Wanan ranan ne muka fara kwanciya saman gado daya da Alhaji sai dai yana gefe ina gefe a kwance har gari ya waye . Abinda ban sani ba ranan shi gare shi ko runtsawa bai yi ba sai faman tunanen duniya yakeyi. Ya so it a mayar dani gidan mu gurin iyayyena don yana ganin yana kuntatawa rayuwa na sosai, amma kuma sai gashi ni da bakina nake fadin wanan zaman yafiye min zaman gidan iyayyena dadi. Haka yasa ya fahinci daga ni har innata muna wani rayuwa ne na zaman ukuba a gidan. Dole yabar wanan yarinyar yaga abinda Allah zaiyi akai don Allah kadai yasan dalilin wanan auren don shi baki sa,ata ba ko wace tafini shekaru bai da nufin karawa a rayuwan shi. Sai gashi a lokaci daya Allah ya jarabce shi da kara aurena auren kuma yazo da kaddaran rayuwa gare shi. Yadda na samu kwanciyan hankali na mirje nai kyau dani haka yasa Sabuwa tayar da hankalin ta duk ta fige tayi wani baki da ita. Gashi ta sa a ranta cewa cikine a jikina yasa na koma haka dani lokaci daya. Akwana a tashi hasaran mai rai yau nakai wata takwas da aure har lokacin ban sheda nayi aure ba a rayuwa na. Iyakata naci na sha na kwanta nai kwana idan naso na shiga na taya matan gidan aikin su. Ba mama da mama hauwa ba kawai nake tayawa aiki har sarakan su idan aiki yai yawa nakan kama masu. Ban hakkura da zancen zuwa islamiya ba na kara tunawa Alhaji da kyat na samu ya yarda na tafi sai gashi ya sawo min hijjab har uku maya har kasa da nikaf na rufe fuskana. Ranan da zan fara fita nasha sheri gurin matan gidan wai ni yar izzala ce shiyasa nake da mugun tsabta ashe. Na dai yi murmushi nai masu sai na dawo nafice daga gidan dama Alhaji ya riga yai min register komai a school din. Don haka ban sha wani wahala ba na gane ajina gwajin farko ya fahinci na dan yi nisa aka mayar dani ajin manya. Sosaina dage ga karatu na ba wasako a gida nake banda abinyi sai karatu da yan aiyuka na. ****** ********* ****** A bangare Alhaji ya samu sauki sosai don tsare dokokin da yayi na likita har anfasa zancen yi mashi aikin da akace za, ayi da farko. Hakan da yake ji yasa yake ganin ya samu sauki ya shiga kokarin gwada sa,anshi ya gani . Ranan a cikin barci na dinga jin wani bakon al,amari ya na ziyarta na idan dai ba mafalki nakeyi ba to zan iya cewa kirjina, watau dukiyan fulani na ne kejin ana taba min a lokacin. A hankali na zubura zubur daga mafalki kamar zan fasa ihu sai jin muryan shi nayi yana ce min kamar rada yi shiru amarya nine Alhaji ba kowa bane. Na gyada kaina alaman na gamsu sai naji yana sauke ajiyan zuciya naji yana ci gaba da saukewa a hankali. Bai kuma fasa abinda da hannayen shi keyi a saman kirjina ba har lokacin. Sai faman rintse idanuwa na nakeyi don irin bakon yanayi da nake ji a lokacin. Kama an fisge shi naji ya juya da sauri tare da rike maran shi da hannayen shi yana wani irin nishi kamar kugi a hankali. Shiru nayi ina sauraren yadda yake fitar da sauti daga bakin shi cikin yanayin ban tausayi . Can a kasan makogwaron shi naji yana kiran suna na a hankali da kyat sautin maganan shi ke fitowa a lokacin yana fadin naje na dauko mai ledan maganin shi da ya bari a dakin sabuwa. Ban ki ba haka na daure cikin wanan Uban daren hana na wucw gurin mama hausatu na buga mata kofan dakin ta tare da cewa maganin shi yace na karbo mai a gurin mama Suwaiba. Ita da kanta ta tafi dakin ta buga mata take cewa miko min ledan maganin Alhaji da ya bari a nan ta tambaya da sauri injin dai lafiya yaya ? Lafiya kalau ya manta bai sha bane yace a dauko mashi ya sha ta karbo ta mika min na juya na bar dakin simi simi dani. Nakai mai sai da ya hada ya sha zuwa can ya dan samu relief sai barci mai nauyi ya dauke shi nima na koma na kwanta zuciya na fam da tunanen abinda ya faru yan mintina da suka wuce a tsakanin mu. Wanda har lokacin ina dan jin dan matashin kirjina yana dan min radadi. Washe gari na tashi ina matukar jin nauyin shi da kunya akan abinda yai min a daren jiya gashi alama ya nuna yana dan jin jikin shi . Amma haka ya daure yafita daga gidan zuwa gurin neman kudin shi daya saba yi. Bai jima ba a waje jikin ya tsanan ta mai ya dawo gida ya kwanta min a daki gashi kunya da nauyi nake ji har lokacin ban iya hada ido dashi. Haka yasa shi fahinta halin da nake ciki daga inda yake kwance na shigo dakin ne naji ya kira sunana. Na amsa sai naji yace na gode daren jiya fa ko ba komai na dan more daga ni,iman da Allah yai maki ya fadi hakan cikin dan lumshe idanuwan agi a hankali. Shi kadai yasan irin halin da ya tsinci kan shi a daren jiya sai dai yana gap da biyan bukatan shi a gare ni ne yaji maran shi ya rike mai sosai a lokacin. Hakan ne yasa shi dole neman magani ya hadiye don samun saukin abinda yake ji. Tambayan kan shi yake a zuciyar shi yayin da idanuwan shi suke a rufe yaushe ne zai samu ya more niiman da Allah ya hallata mai ga wanan yarinyar ? Irin yanayin da ya tsinci kan shi da ace shi mai lafiya ne yasan cewa a daren jiya din Allah ne kadai zai kare bai kai ga mayar da ni cikakkan mace ba kamar yadda yake gurin yin haka a gareni a kullun. Ganin da nayi jikin shi ya matsa mai yasa naje na fadawa sauran matan nashi halin da yake ciki. Ba bata lokaci dakin nawa ya shiga ganin yan zuwa yi mashi sannu da jikin shi. Nan sabuwa ke cewa Alhaji kana son matsawa rayuwan ka akan sai kaga ka burge wanan yarinyar a koda yaushe. Idan baka bi sannu ba zaka halaka kanka da kan ka furin budurwan zuciya. Sai ka dinga farwa yar karamar yarinya akoda yaushe yaushi zaka ganewa lafiyan ka tunda kaki na tsuwa da girman ka a koma ana taratara da kai kamar karamin yaro har may kake nema ne gareta wanda baka samu ba a baya. Yana jin ta sai dai halinda yake ciki bai iya bata amsa a lokacin don jin zuciyar shi yake yana mai tafasa . Ga zancen ta na kara kona mashi zuciyar shi akoda yaushe. Shima laifi ne ga maganan sabuwa da take yawan nanata yana yawan kusantar Amaryan shi ne yasa matsalan shi ke yawan tashi koda yaushe. Shi dai a gare shi yadauka kawai wanan wani jerabawa ne daga Allah kawai. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WASU MUN BARKI GA ALLAH YA BI MUNA HAKIN MU A KANKI YAR UWA DA FATAN ZAMU JI TSORON ALLAH MU RIKE AMANA DON AMANA GIRMA GARE SHI. 9 Dawowan Sabuwa gidan yasa yanzu na rage fita gidin darbejiyan da matan gidan suke fita hira ko yaushe. Idan ma na dan fita bani daukan lokaci a gurin don gujewa shiga tarkon ta don ko yaushe ita a cikin fitina take. Gata irin figagan matan nan ne marasa jiki komai nata dan kyamn, ne a fige sai bakin fitina da mita ga yawan haihuwa a yadda naji matan gidan suna fadi wai bata yayewa take samun ciki. Ganin na rage fitowa ne yasa ranan mama hausatu take tambayana dalilin kumshewa na daki yanzu murmushi kawai nai mata batare da na bata amsa ba. Sai cewa tayi Allah ya kyauta halin sabuwa sai ita don mai hali baya barin halinsa komu nan ba barin mu tayi ba ai da girman mu gaban diyan mu da sarakan mu sai taci muna mutunci ba komai bane a gurin ta. Jin da nayi yarona abokin hirana dan makwabbcin mu habib yana da kwazo ga karatu addini gashi karami amma Allah yai mai baiwa gurin garatu. Yasa na ke zama dashi muna karatun mu a shiyana muyi karatu idan mun gama muyi ta shiriritan mu kamar yada kauna muke dashi. Don dan abinda yake samu a gurina gashi na rike shi da zuciya daya shima hakan nake gani a gare shi don bai taba min abu sai ya roke ni . Wasa wasa sai na fahinci ba karamin karuwa nakeyi ba da karatun da nakeyi a gurin habib din. Hakane ya bani daman tunanen na roki Alhaji idan zai yarda na rika zuwa makarantan islamiyan dake kusa da gidan mu. Don akwai daya daga cikin sarakan gidan da kullun ita sai tafita zuwa daukan karatu. Da naiwa Alhaji magana yace haba amarya kofa wata uku baki kai ba da zakice zaki fara fita ? Dole na hakkura naci gaba da karatuna tare da habib din amma abin yana a raina. Dama nayi nisa tun a gida haka yasa na samu saukin karatun a yanzu wani lokaci kuma littafaina na boko na kan dauko nai tabi ina dubawa ni kadai a daki na. Mama Hauwa tana aikin fura sai dai ba kullun takeyi ba daga shiyana nake jin harshen ta tana fada da yarta mai mata talla wai sunyi rana ga aikin kuma yarinyar ta tsaya tana shiririta ga aikin. Na mike tare da shiga daki na sauya zanin jikina na jawo kofan dakin da kuma kofan shiga shiyan nawa don akuyoyin gidan masu bakin barna. Na samu ga gari aje ga aikin gida da yasha mata kai don ita ce da girki ranan. Ina zuwa nai mata sannu na karbi rariyan dake hannun ta na shiga tankade da gyaran garin. Na fahinci su kamar mama lauratu na gidan mu suke don basu damu da koyawa yaro aiki ba a gida. Yar ta Amina tana fitowa ta ganni a zaune ina tankade tace wai har naji dadi amarya dana ganki don yanzu dana fita tunda kin saka hannu ga aikin nan zaki ga na sayar da furar nan a take. Kai ji wani batu daga can kofan mama hausatu Zuwaira tace mama ai ba karya ta fada ba mun gane idan amarya ta taba kayan sana an mu a take muke saidawa idan mun fita. Hannun ta yana da albarka sosai wallahi a kaji min yara da sabon surukulle kuma ? Inji mama hauwa take fadi tana dariya tace muma wallahi zuwaira ta fara lurar damu haka dakuma muka duba muka ga ai hakan gaskiya ne. Nan dai sauran matan gidan aka taru ana wanan zancen ana dariya ni dai akina nake ban yi magana ba. Daga can kofan ta sabuwa ce ke cewa daurewa karya gindi ke nan ita waye da zaku ce haka ko watafi sa, a kuke kara zugata tana ganin ta kai wata aba a cikin mutane ji wani sabon tsurkun da kuma kuka camfa mata don taji dadin iya shege. Ni dai wanan aikin jagwalgwalen badani balle a camfani ni kishiya bata fini ba balle na sa a kaina. Wanan abar ce zaku tsaya kunawa wanan camfin kamar wata babban mace can da ita. Nan daya da kacin sarakan mama ta cafe da cewa ai ba camfi bane dama can a garin nan kowa yasan irin sa, an dake ga Rahama ai gurin talla don komai ta dauka sai kudin shi. Eh hakane dama tunda tana da tsifin dake mata juye subata kudi ta kaiwa uwarta ana cewa sa, a ne yanzu ai gaskiya ya tabbata don mungani koshi Alhajin ba ragowa ne ya kwaso muna ba Allah mudai ya cece mu da daukan ciwon sanyi wallahi. Shiru gurin yayi don jin inda ta biyo da zancen can mama hauwa tace wanan kuma sabon kake ne don ban taba ji bani kan abin garin nan da ba a boye yake ba. Tace kece baki sani ba kuma dole ne sai kin sani ba tunda idon ku ya rufe don kawai ai min sheri a hada min kai a gidan nan aga bayana nida Alhaji ko mutu ka raba. Sai lokacin mama hausatu uwargida tai magana tace kai haba sabuwa in an girma asan an girma mana yanzu wanan yarinyar dako hankalin kanta bata gama mallaka ba zaiyi wanan sheri a matsayin ki na uwa. Ke ma fa gakin nan dasu a gaban ki indai yaran ne ai ba uwar da zata so aiwa yarta sheri haka ? Au to yaya abin yakai can baki zakiyi wa yarana kuma? Ai dama ba yau ba nasan sun kai maku ko ina a gidan nan saboda hassada aiko tashiga bakin ta harshen ta har waje ana jin ta. Daidai lokacin ne mukaji gyaran muryan maigida yana tafe tare da dan shi babba a baya da mai bi mashi. Tun a kofa yake fadin wai yaya ne kuma may kuma ya faru haka da rana tsaka. Ledan dake rike a hannun shi na vaco na je na karbo da sauri yayin da sauran matan ma suka karbi na hannun mazajen su idan ta akan ledan dana karbo take fada. Na nufi dakin mama hausatu da ledan don itace ranan da girki sai yamma zata fita sabuwa ta karba don girkin namu a jere yake muna. Ina nufin shigewa dashi dakin ta yace dawo dashi nan mikawa hausatu a raba abakowa nata ta shiga dashi ya juya yana fadin tambaya nakeyi mai ya faru wai ake wanan fada murya har kofan gida. Shiru kowa yayi babu ma magana a cikin su sai Amina yar shi ce ta shiga koro mai da zancen abinda ya kawo rigiman haka. Ya kalli inda sabuwa take yace kai amma dai sabuwa ke mutumiyar banza ce wallahi. Kina zaton yadda kike watsatsa haka kowa ma yake a rayuwan shi tashinki a garin nan aike ce kika so bata tarbiyan yaran garin nan kaf don ke kka zo da wanan halin ko don su nan basu sani ba har kika samu bakin yiwa wata sheri kuma ? Haba nan ta juye bala,in ta kan shi sai da yai saurin saka mata waigi ta dakata don tasan abin da yake nufi zai iya aikata shi da gasken a kan ta. Malam wanan kuma Yaya za, a yi dashi tana kokarin fitar da gorunan man shanu daga cikin ledan tana jerawa a kasa. Ya dan juyo gare ta yana tsuki abinda ya dakatar da su daga fitinan da suka dauko yi da sabuwa ke nan. Yace ai gora hudu ne ko kibawa kowa nata ke Amarya ya duban gurin da nake ina gyara wutan huran da muka nasa yana zabarbaka daga tukunya. Jeki ki karbi gorunan ki bawa kowa nata kason ta dauka da sauri na nufi gurin mama hauwa din na fara kaiwa mama hausatu ta zaba na mikawa mama hauwa na ta,na dauki daya zuwa gurin yaya sabuwa da nata goran . Tun kafin na karaso na ji tace may kike nufi wai ke yar wayo ko kin zabi mai kauri kn kawo min mai ruwa ko ? Da sauri na juya inda dayan goran yake na dauka na kai mata ta zaba sai da ta karba ta jijiga ta kara juyawa sama da kasa sai ta miko min wanda na aje da farkon na juya don duk a tsorace na ke a gaban ta kada ta make ni. Kaiyya inji mijin su daga gurin da yake zaune saman wani dutse dake tsakar gidan. Yana na kallon yadda muke kwasa da ita kan man shanun da ya sayo muna daga kauyen da suka tafi. Tace ana dai rabon son kai a gidan nan ace da may iyali da mara iyali duk kaso daidai za,ayi shi wai haba wanan ai dul cikin zalumci ne wallahi Allah ko. Zaki soma ko ? Wai ke Sabuwa baki ba kanki lafiya ne ki rufawa kanki asiri ne haka wai ?. Kin manta da yadda aka kwasa a baya ko da kyat fa na samu malam shehu yai bugun gaba yaje ya dawo dake . Au to kina son fada min cewa kece kika tura biko na ko may ? Daga inda yake zaune yace ke dama kina daukan cewa zata canza halinta ne ai mai hali baya barin halin sa. Yace ke hausatu dauko min tsimayn nan nawa na dan sha don banjin alaman dadin jikin nan. Nan dai kowa ya watse ya kama gaban shi muma muka gama hura kusan nice nai aikin huran don na iya dama tun a gida. ****** ********* ****** Kamar yadda mata idan sun taru sai zancen mazan su hakane ke kasancewa yanzu a gurin maza. Taron da akeyi na fadanci a kofan gidan na Alhaji garbati wanan karon ma sun hadu ana fadanci don dan abin da suke samu daga gare shi. Baba salla ne ya fara cewa aikai Alhaji sanyin babana lafiya lau kake ga amarya ga sanyi . Ko ba a fada ma jikin ka ya nuna ka samu lafiya ga hakan nima dai kukewa zanyi naga na samu koda bazawara ce mai dan dama na kawo gida ko zan samu dan gurin hutawa bana. Jin zancen su kawai yake amma zancen yana tsuma shi sosai haka yasa ya yanke cewa zai gwada ya gani dai ko ya samu lafiya shima ya fara murzan amarci da yar amaryan shi. Ranan da akai wanan zancen a dakin sabuwa yake dama ta ishe shi da mitan ita a bukace take fa. Bayan ya shigo gurin ta ya kokarta yaga ya samu gamsuwa amma ya kasa hakan gashi ta isheshi da minta wai ai da amarya ce inda yake kare karfin shi gurin yar karamar yarinya dan yai bajinta ta gani. Shiko ya na samun kanshi daga gareta ya fara wani irin nishi yana jin kamar ranshi zai fice mai a lokacin. Da kyat yaga safiya sabuwa ce ta tayar da mutanen gidan don neman taimako a kan shi. Ba,a bata lokaci ba da safen nan aka nufi asibiti dashi hankali a tashe duk kowa gidan ya koma jigun, jigun abin babban gida take a kashiga tsegumi ga Sabuwa. Wasu suce kila wani mugun abin tai mashi har taso halaka shi, wasu kuma suce dama ba lafiya gare shi ba kila bakar jarabanta da ta sabane ta matsa mashi har ta so halaka shi. Nidai da yake akwai kurciya a tare dani ba fahintar zancen su nakeyi sosai ba amma na shiga halin damuwa don ance sabo turken wawa ne. Dan zama na gidan ko ba komai yana bani kulawa yana tattalina yadda ya dace ayi. Sai zuwa karfe biyu suka dawo tare dashi yaji sauki sosai kamar ba shine aka fita dashi gidan da taratara ba.. Sun tara mu duk kan mu matan shi a dakin mama hausatu sun muna bayani cewa likita yaba da doka kan cewa mahaifin su har yanzu bawai yaji saukin lalurar shi bane don haka akula don Allah kada a dinga matsa mai kancewa lalai sai yayi wani abu da watan mu a bishi a hankali. Ni dai na fahinci suna magana suna yawan kallon inda nake zaune ni da sabuwa ne amma ba wai na gane manufan su bane. Sai da yai mata kwana biyun ta ya dawo dakina kamar kullun idan nice zanyi girki na kammala komai da nakeyi wanda ba sai na fita tsakar gida nayi shi ba. Don ni ai fadan sabuwa zance gaba ya kaini don Allah ya rabani da tuwon taro komai a dan karamin shiya na da aka kebe min nake abina wanda hakan yakaiwa Sabuwa ko ina. Tayi mita akan itama sai ya kebe mata nata shiyan daban kamar yadda ya ke be min nawa ni kadai nake kwamacala na ba wanda ke ganina sai wanda ya shigo inda nake. Girki dai Alhamdullahi don tun a gida nakeyin abina tun mama nacewa wai Innata tana sa ina masu jagwalgwale har ta gaji ta sa ido ranan girkin inna ta idan na dawo tallah da wuri kafin naje diban ruwa zan tsaya na taya ta aikin girki da gyaran gida. Haka yasa yanzu ban sha wani wahala ba a gidan auren nawa da na tsinci kaina a ciki da rana tsaka. Yau da yake ba fita hira yakeyi ba sai gashi ya dawo gurina tunda magariba, anan yai sallolin shi kofan daki inda yasa nai mashi shimfida. Nakawo mai abinci na koma daki na zauna ina ciki naji ya kirani yana cewa fito mana Amarya ki barni kuma ni kadai a waje ina maki gadin kofa. Haka yasa na fito daga ciki na samu gefen tabarman da yake zaune na zauna can dan nisa kadan dashi. Ya soma cin abinci koda na fito yace wai ke waya koya maki girki haka ne yar karama dake amma kin iya girki haka. Nace Lah inna ta ce ai nice ke mata girki idan ina gida, yace kai amma gaskiya ta kyauta min sosai. Yaushe rabon da na dinga cin girki haka acan acan mai dadi a gidan nan ? Cikin shirmay yara nace kai haba Alhaji ga mama hausatu ga mama hauwa ga kuma yar barayan ka duk kace baka cin girki mai dadi ?. Yace ai sunayi amma nakin yafi dadi ne Amarya da ina da lafiya ai wanan girkin da kika iya da na more ma hannun ki . Don ance yadda mace ke aikin ta ko mai nata haka ake samun shi nace to kila magi ne basu sakawa kamar yadda nake sakawa a nawa ? Murmushi kawai naga yayi min yace to ke naga bakici komai ba mana ko har kinci naki ne ? Sai da na dan tabe baki can nake cewa nifa ko a gida tuwo bawai ya damay ni bane nafi son naci shimkafa komai rashin dadin shi ko abu mai dan ruwa. Shiyasa ma mama takan ta fada da inna ta wai itace take koya min rashin cin tuwo gani diyar tallakawa dani sai karya. Nace kuma fa Alhaji babu laifin Inna a ciki nice dai bana so idan an matsa min naci sai na amaye shi kaf. Yace ikon Allah abin naki halita ne ke nan nace haka naji Inna ta tana fadi shiyasa koda zanyi auren nan maganan inna ta ko yaushe shine kada nai sakaci da kunnu don shine abincina. Yace to ashe sai na dinga sawo maki shimkafa kawai kina sarafawa kina ci ko ?. Nace a, a kada ka wahal da kanka ai na saba da hakan don ni abinci bai damay ni ba. Yace ashe shiyasa man shanun da na sayo maku ke naki kamar ba, a amfani dashi tunda baki cin tuwo ? Muna cikin haka dashi sai ga mama tashigo gaidashi tace a, a ango da amarya ake hira ashe Sabuwa na bayan ta tafe. Sai ji mukayi tace ai abinda yakeyi ke nan yana biye mata kullun jiya wa yau abu yaki ci yaki cinyewa an kwaso muna mai farar kafa tana batun mayar damu marayun dole. Haba Sabuwa may yakawo wanan magana haka kuma a gurin nan wanan yar cikin taki ne zaki tsaya yiwa wanan magana haka ? Tace Allah ya raba yata da wanan bakin jaraba na wanan yarinya dubaki gani don tsaban rashin kunya wai zaune take shimfida daya da Alhaji adole ita wai ga mace ? To yin haka laifine kuma mace da mijinta ana raba su zama ga shimfida daya tunda anriga da anzama daya ko ? Dama yaya kune masu daurewa karya gidi ai take gani kamar ta kai mace ? Kai yauko ga wata magana ga sabuwa uku gareki uke ke gareta to mayye banbanci a nan. Ya dakatar da ita da cewa yanzun dai may ya kawo ki nan din don ina fama da kaina ban son fita ? Tace dama zuwa nayi naima yaya jiki sai na samu kana ma a cikin raha ne ashe kai ? Yace eh kin san ina gurin da ake kwantar min da hankali kamar yadda nake bukata ko yaushe. Ai naga alama sai ayi a sannu don kaji dokan likita idan da son samune ma kabar gurin yarinyar nan har ka samu lafiya don nasan kana ganin ta ba kyaleta zakayi hakana ba ? Yace shi likitan ne yaba da dokan na kauracewa iyalina din ? Kada na basu kulawan da ya dace dasu sai na nisance su ko ? Kadai yi a hankali don ko banza ita a ganiyar kurciyar ta take yanzu tunda jarababban yarinya ce ta na iya saka yin abinda bashi ba ? Yace kamar yadda kika sani yin dole shekaran jiya ko kika tashi kashe ni ke nan ? Idan ban kashe ka ba ai wanan mai ido tsakiyar kai zata kashe ka ita. Ta juya ta wuce abinta yace sakariyan banza kawai mara hankali da tunane. Nan mama dake sauraren su tun zuwan su ta nisa tace kai halin sabuwa sai ita kullun ba a girma. Yace ina girma ga sabuwa anan bakin kishin yarinyar da bata ma san tanayi ba yana batun kashe ta don ita kanta kawai ta sani a duniya. Sai lokacin nace mama ina batun zuwa gaida ke da wuni sai gaki kuma kin shigo yanzu tace to na hutar dake ai nazo duba jikin maigidan ne dama. Yace jiki Alhamdullahi da sauki sosai yanzun ma nake batun shan magani na da likita ya ba ni ai. Tace to amma malam a tsaya ga na likita kawai ba a dan gwadawa dana gargajiya agani kuma ko a dace. Yadda aka fita dakai a gidan nan fa shekaran jiya ya tayar wa kowa da hankali sosai. Yace ai ina kan gwadawa ke ma kin sani al,amarin ciwo ne yanzu idan ya kama sai a hankali fitan shi. Ta nisa tare da cewa haka ne kuma Allah dai ya kawo sauki kawai za, a ce . Ta juyo inda nake na dukar da kaina ina wasa da kafana dana ke kadawa a hankali, take cewa to mu kwan lafiya Amarya. Nace mama Allah ya bamu alheri tace amin ta juya tafice tare da rufo min kofan shigowa sashen nawa. Yace bari na koma daga ciki sai ki samu ki shige da kayan nan ciki ko ? Nan ya mike da kyat zuwa cikin daki ni kuma naci gaba da kawar da kayan da yai amfani dasu a gurin. Haka a dadafe yai kwanakin da zaiyi a daki na ya koma gurin sauran matan shi can. Ranan naji shakat a raina don nan yake zaune duk wanda yazo gaishe shi ciki zai shigo su gaisa dashi. Haka yasa na kasa sake jikina a gurin nawa don yawan manyan mutanen kauyen mu da ke shigowa gaida shi. Shi ko na lura yana jin dadin azo a samay shi a gurin nawa da yake acan acan ko yaushe a cikin gyara da kamshi. Don ina manejin dan kayan kamshi da anty ta turo min dashi daga birni saboda mama altine ta kashe lokaci gurin yi min bayani a kan kamshin dakin mace. A ranan da ya koma dakin mama washe gari sai ga Iyyaye na sun samu labarin rashin lafiyan nashi sunzo gaida shi. Ina dakina ban san shigowan su ba ashe har sun dan jima da shigo sai mama Altine ne ne kewa ni banga diyata ba fa ? Lokacin mama ta tura a kirani ana fada min na taso da murna na nazo dakin inda suke da zuwa ina ganin su maimakon nai murna sai kawai na fashe da kuka kawai. A, a ashe da mun san haka zakiyi muna da bamu zo ba sai dai mu tsaya daga kofa mu gaidashi mu koma. Da kyat suka samu nai shiru mama altine tace ashe har yanzun yar tawa bata daina wanan tabaran nata ba ? In banda haukanki ai sai a dauka ko wani mugun hali ake maki gaki kinyi kyaunki bulbul dake daki ya karbe ki. Na kara shigewa jikin mama altine ina cewa wallahi mama nayi fushi ace idan ita Inna ta taki zuwa ta dubani har dake mama bazaki zo ki gan ni ba sai kace nai maku wani laifi ? Yanzun baga mutanen gidan ku masu kirki da karamci suna kula dake ba duk halin da kike ciki fa muna da labari. Mama altine da dayan makwabciyar mune kawai suka bini zuwa dakina ita Inna ta taki zuwa nan ta zauna dakin mama hausatu har su fito daga guri na su tafi. Narasa irin taron da zan masu don murna nace mama ni nama rasa may zan baku wallahi tace, ba mu ruwa ya wadatar damu tunda munsha a dakin yar uwarki amma zamu sha naki. Ruwan randan kasa na da yai matukar sanyi har naso bayan randan ke bayarwa don sanyi. Na debo masu suka kinkima sosai nan muka kara gaisawa dasu suna ta yaba kyaun dakin danayi. Nace mama yaya wajen anty na kuna da labarin ta ko ? Tace Anty ki Alhamdullahi don ta samu lafiya sosai har naji tana cewa tana son zuwa ta duba mu ma nan. Nai murna kwarai dajin wai antyna zata zo garin duba mu mun jima da su mama muna dan hira sukace zasu koma sai ga yarona habibb da leda wai Alhaji yace abawa bakin da sukazo suyi hakkuri. Ban tsaya duba ko may ke cikin ledan ba na mikawa makwabciyar mu ledan sukace ashe mu dawainiya muka kawo maku kuma mu da mukazo duba lafiyan maigidan. Kafin su barni su kara jamin kunne nayi hankali da Sabuwa da diyan ta a gidan don gujewa makircin su. Ban sani ba ashe bayan tafiyan su fitina ya tashi tsakanin Alhaji da Sabuwa wai don may zai ba su mamana leda da abuba ciki ? Wa nafi da zai fifita uwaye na akan su ai itama matan gidan su suna zuwa gaidashi amma bai taba basu komai ba sai ni za , abawa iyayyena. Da kyat aka samu wutan ya mutu bayan kakausan kashedin da yai mata yana hurta sai ya sake ta wanan karon. Jin kalman saki yasa ta ja bakin ta tai shiru tasan tunda ya furta hakan zai aikata ne don bai taba hurta mata kalma na saki ba a duk rikicin da sukeyi tsakanin su. Sai gashi yau akaina yana furta mata cewa ta ishe shi da fitina a gida ai itama wasu ta samu a gidan kuma ba abinda bai mata ba lokacin da take ganiyar amarcinta har zuwa yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA BAWA WACCE BATA BIYA BA ALLAHNA GANIN KI DON AMANA NE A GARE KI YAR UWA, , , 10 Sannu sannu sai gashi lokaci yana ja a wanan lokacin duk wani dan matashin yaro dake gidan idan dare yayi muma shiyana muna karatu, wanda suke jin dadin hakqn anan zamuyi ta shirmay har dare kowaya watse. Bayani nake masu sosai yadda zasu fahinta gakaratun da suke dan tsinta a gurina. Wani lokaci kuma novel zan samu mai dadi da ma,ana da koyar da wani abinda ya shafi fannin rayuwan dan adam. Zan dafa abinci na zuba a babban tire nan zamu taru muna ci muna hira muna dariya abin dai na kurciya zallah kawai. Har zuwa wanan lokacin zama na da maigidan kamar kullun ne ya kan yi iya bakin kokarin shi don yaga yadda zai yi ya dan samu gamsuwa. Sai dai hakan bai yuyu ba a gare shi don da alama matsalar shi tana nan mai bai gushe daga gare shi ba. Don idan yaso ya kai gare ni sai naji yana zufa yana wani irin kugi mai fitar da wani sauti na ban tausayi. Ni kaina nakan matukar jin tausayin shi idan ya shiga wanan halin don haka zai wayi gari ya wuni a wahalce dashi dashi. Na fara fahintar wasu abubuwa duk da dai wayo na baikai na fahinta ba a lokacin amma sai nake fahintar ba gani kadai hakan ke faruwa ba har ga sauran matan shi musanman ma dai sabuwa. Idan ya kwana a dakin ta zanga ya tashi wani lokaci ba dadi har aka fara dan rade radi a gidan abinka da gidan yawa. Ranan mama da kanta take bugun cikina akan zancen take cewa dani wai amarya kuna dai biyewa wa maigidan yaki natsuwa har ta samu lafiya komai ya zama daidai ko ? Nace mama na daina zama ne idan yana daki kike nufi? Ta kama baki tace wane ni da fadar haka amarya rufa min asiri tace ni dama cewa nayi kawai ki dan kaurace mai ga shimfida irin ki dan rika ba da lokaci din nan . Kin san shi namiji kullun a bukace yake da mace ba ruwan su da lafiyan su koda hakan kuwa zai masu illa ne. Nace mama kina dai nufi idan yana daki na fito waje na barshi ya huta ya samu hutu sosai ko. Nan dai ta gane shirmay na bai bari na fahince ta sai ta fito min fili tai min bayanin komai a baiyyane. Cikin canza fuska nake ce mata gaskiya mama ni Alhaji bai taba nuna min wanan abin ba a tsakani na dashi sai mutunci kawai. Kan ta ya daure ba don ta yarda ba don tasan hakan ma ba zai faru ba koda kuwa ace ni ba yarinya bace yaya zan zauna har wanan lokacin. Karshe dai sai cewa tayi dani ki daiyi a hankali kinji kada ki yarda ace an samu wani matsala a kan ki kinji ya ta. Nace to mama nagode Insha Allahu zan kula kamar yadda kikace din. Sai gurin karima sarakuwan tane ranan take kara fayyace min yawan hasashen da ake mun a gidan kan lafiyan Alhaji. Muna hanyan makarata ne take fada min komai tare da jamin kunne akan na kara kulawa sosai. Tun ranan ban yarda ko dan tabanin da yake ya samu relief din da yake yi na daina bari yanzu. Har abin ya fara dan damun shi da yai min magana ban boye mai komai ba na fara kuka ina fada mai abinda akace ina yi mai. Ya gane anja min kunne ne akan haka yasa ya daina kada ya jamin bakin jini ga iyalin shi don su a ganin su nice ban bari ya samu sauki. Ranan dakin mama hauwa yake ciwo ya murtuke shi a cikin dare aka kwasa sai asibiti. Nan suka fara fahintar cewa ciwon ne dai bai bar jikin shi ba ba yadda suke hasashe bane. Koda aka dawo dashi gida wanan karon andai dawo ne amma yana matukar jin jikin shi sosai. Don yakai idan zaiyi fitsari ma kusan zakaji yadda yake faman nishi da kugi kafin fitsari yazo mai. Wasa wasa ciwo sai gaba gaba yake mai ya ramay yai baki sai dan wuya takai ma yanzu bai fita kamar yadda yakeyi a baya. Cikin haka ne ranan aka aiko babana yai faduwan mashi a hanyan shi na dawowa daga kasuwan kauye da yake zuwa. Alhaji ya samu labari don haka yana dakin sabuwa yasa a kirani nazo na dan rusunna daga kofan dakin nata don ban yarda na shiga daga ciki ba don ta cikin dakn zaune a lokacin. Yake cewa dani yanzu nake jin labarin abinda ya faru da mahaifin ki jiya shiyasa na kira ki. Ki shirya sai zuwa ta rakaki ki dubo shi amma kada ku wuce goma ku dawo gida. Nace na gode cikin murana wanan ne karo na biyu bayan aure na da naje gaida mahaifana. Na farko tare dashi muka tafi ban ko kai minti talatin ba baba ya matsa min nafito muka koma gida. Sai wanan daya bani bako mu tafi da zuwaira na dubo jikin mahaifina ko shi nasan don baya jin dadi ne da tare zamu tafi dashi. Tsab na shirya cikin katon hijjab sai nikaf dana dora akai duk d dare ne amma na saka nikaf din na tare fuskana da shi. Har mu uku muka tafi don Aisha ta biyo mu da taga zamu fita tare da zuwaira din. Da sallama muka shiga gidan a tsakar gida muka samay su suna shan iska tare da baba. Nan muka durkusa muka gaida su tare da mai yaya jikin shi da Allah ya sauwaka ya tsare gaba. Sai can yake cewa wai Rahama ke ce ai ban gane kiba ikon Allah ya kuke ya gidan duk kuna lafiya ? Yaya shi maigidan naku da na sa jikin dafatan ya samu sauki ko don ance jikin nasa ba dadi kuma ? Bayan mun gama gaisawa da baba ne da tambayoyin da ya jero min na juya inda mama take tayi tsit tare da kura min ido. Ko may take kallo hakana ban sani ba daga jikina na daiga duk da dare ta kura min idanuwan ta a kaina. Nace mama mun samay ku lafiya yaya gida ashe baba kuma wani kaddarane ya samay shi haka? A cikin basarwa take amsa min gaisuwa na a tsatsaye na gaida Inna ta dake zaune a gefe tana motsa kunu mai zafi data dama ina ga na baba ne. Can na mike na leka dakin mama gurin su Lawisa suma ba wani karban arziki ne na samu a gurin su ba. Na fito na shiga dakin Inna ta na samu kannena zaune suna dan hiran su, suna gani na suka hau murna. Nace dasu ba wani bayan kun yadani ba ku zuwa gurina sai kace ba, a gari daya muke daku ba kamar wacce bata da yan uwa. Nasir yace kiyi hakkuri mama ce ta fadawa baba ranan nan da muka tafi gurin ki shine baba yace kada mu sake zuwa gidan ki. Lokacn Inna ta shigo dakin inda muke ta samay mu muka kara gaisawa da ita cikin mutunci. Nan ta zauna a bakin gadon ta ganin Inna ta shigo dakin yasa su zuwaira da muke tare mikewa suna fadin amarya zamu tsaya kofan gida mu jira ki. Nace haba ku zauna mana suka ce a, a muna dai waje har ki gama mu tafi ai. Bayan fitan su ne Inna ta nisa take cewa yaran suna da da, a da sanin ya kama ta ne. Nace cikin shagwaba Inna nikan dai yanzu ba kya sona nice kawai nake can cikin damuwa daku ? Tace da akai may kuma nace ina ko su Nasir an daina tura min nagan su sai na tara abu don a kawo maku amma babu yaron da zan ba ta kawo nan na ciro wani babban leda daga cikin hijjab dina ina mika mata. Kallon ledan takeyi tare da tambayan wanan may ne kuma a ciki ledan cike yake fam da tarkace iri iri dana tara don na kawo mata. Bayan ta gama dan dudubawa ne race yarinya kardai ince kayan mijinkine kika kwaso muna haka na amfanin ki ? Mijinki fa bai rage ni da komai ba yanzu don inba rashin lafiyan nan da ya kwantar dashi ba kusan duk sati da aiken da yake min daga gurin mamakin mai kuli. Ni ban san irin godiyan da zanwa wanan bawan Allah ba gashi ya rike min ke da mutunci kullun yana yabawa da halin ki na tarbiya a garesu. Ga kuma abin alherin da yake kawo muna don kinga yanzu banda talaucin dangin kayan miya sabulun wanka man shafi da sauran su. Watarana ma har kayan girki kamar shine ya aje mu zai kawo muna da kudi ga hikimar da yayi na bi ta hannun mai kuli ya kai muna ta gurin ta sai dai ta aika nazo ko ta kawo min idan uwar ku tafita daga gidan. Nisawa nayi nace mama shi Alhajin ne ke kawo maku wanan amma ni bai taba fada min komai ba wallahi. Tace shine alherin arziki gashi yanayi ke da yakeyi kanki ma baki sani ba sai yanzu. Nidai ko rike min ke da sukayi da mutunci ya wadatar dani wallahi tun har yau banji wani abin asha ba daga gare ki. Murmushi nayi nace haba Inna baki koya min yin haka ba aikuma bazaki taba jin shi daga gare ni ba ai. Nan dai nace Inna su Lawisa yaya nasu zancen auren ne naji shiru har yanzu ? Tace kin ga yadda baki san komai ba nima haka iyakata dasu ido a gidan nan bana shiga zancen su suma hakan. Sune ma ganina a wadace yake damun su kin san halin uwar taku da hassada da kyashi ai. Yadda taso ta kawar dake a gabana taga na wullakanta sai taga sabanin haka ga taimakon da Allah ya jefo mijin ki a rayuwan mu yake muna. Kedai kikara hakkuri akan wanda kikeyi mai hakkuri baya tabewa ga banza insha Allahu. Nace insha Allahu ina tace idan ma tayi muna hakane da wani manufa to yanzu mu hakan ya zama muna alheri. Don ya koma mata ciki kullun zaka ji ta tana sake magana da habaici a gidan nan. Gashi Allah ba ai mashi wayo ita nata diyan ko tsohon ma Allah bai kawo masu ba sai zaman sa,in sa suke a tsakanin su da ita. Muryan baba ne daga waje yake kiran Inna ta yana fadin ke Asiya bazaki sake yarinyar nan su tafi ba ga dare yanayi ko anan kike son ta kwana. Shine ya katse muna hiran mu da inna na mike ina cewa inna zamu tafi zan shiga gurin mama na gaida ita kafin mu tafi. Tace injin mijin naki yace ki shiga gurin nata don kada ki koyi wanan halin na matan yau da muke daukan hakan ba komai a rayuwan mu hakan ko shine babban koma a gobe kiyama. Sai kiji mace ta fita da sunan zuwa gida daya sai ta biya gida goma ba da bakin mijin ta ba. Nace Inna har na fito fa ya kirani yake cewa na, ratse na gaida mama altine din tace to tashi ku tafi kada dare yai maku. Naba kanne na dari biyar nace su karya dashi da safe suka shiga murna itama inna dubu daya na bata na fita naba babana dubu daya mama dari biyar. Sai sa min albarka baba da Inna sukeyi mama kan tun ce min da tayi an gode bata kara magana ba. Gashi ko ranan da haka zata kwana ba ko sisi a hannun ta don yanzu yaranta sunyi wayo suke rike kudin su a hannun su. Da kyat zata iya karban naira hamsin a gurin su don sai tasha mita kafin su bata wani abu. Mun shiga gurin mama Altine tai murna kwarai da ganin mu tana ta ina aka saka dani. Sai tambayana take yaya muke yaya abokan zaman nawa injin dai ba wani matsala ko ? Tace nayi hakkuri na dage gurin kyautatawa mijina da sauran abokan zamana kamar yadda nakeyi. Tace hakan da kikeyi shine samun kwanciyan hankalin ki a gidan don da kinje masu a tsaye ne ko shi mijin naku bazaki samu kan sa ba ai. Bamu jima ba mukai sallama muka koma gida ina jin zuciya na ba dadin rabuwan da zan sake yi dasu sai kuma wani lokaci mai tsawo kila na sake ganin su. ****** ********* ****** Wanan ganin da mama tai min ya matukar tayar mata da hankali sosai gashi don samun guri wai harda kyauta kudi nai masu har dari biyar. Wa ma yasan abinda nabawa uwata a daki don haka tun da safe tai sammakon barin gidan zuwa gidan aminiyar ta larai bamu da nisa sosai da ita. Tana shiga suka gaisa larai tana ganin ta tasan akwai abinda ya faru don duk tai mata sakko haka agida da akwai matsala ke nan gare ta. Tace may kuma ya faru mutumiyar tace bari kedai larai nai wa kaina abinda ya koma min ciki wallahi. A zato na na hada auren yarinyat nan da garbati don na kawar da ita da uwar ta daga farin cikin da suke ciki . Ashe ban sani ba na dauko wuka ne na dabawa kaina a ciki dana sani daya daga cikin wa yan nan shashashun yaran na cina mashi. Kin koga yadda yarinyar nan Rahama ta koma Larai ? Wai yau har Rahama ce da kanta tabani kyautan dari biyar cas kin gashi gashi nan . Ta baje tayi kyau ta wani murje ta kara haske da ita kamar mai aure a birni yanzu fa uwarta ma bata cikin matsalan komai a gidan nan don sai bushashan ta takeyi. Jin tai shiru larai tace da ita to ai baki san wani abuba ne Lauratu idan da yar taki kika bashi sabanin haka zaki gani fa. Da sauri take kallon Lairai don jin abinda tace tace eh haka nane mana don kinga halin su ba daya ba da ita Rahaman. Yadda nake jin labari fa ita yarinyar ce ta sai wa kanta zaman lafiya da kowa a gidan. Don ko sabuwa dake hauka da farko yanzu ta aje shi gefe don mutuncin yarinyar a kan su ta dauke su tankar iyayyen ta ne bata je masu a tsaye ba. Kin ga kuwa banga dan ki ko daya da zai shiga ya mayar da kanshi kamar bawa ba a gare su don a zauna lafiya. Dama hakane dan hakin da ka raina sai yazo ya tsone ma ido shiya sa tun farko da kika zo min da maganan wanan hafin nace dake kinyi babban kuskure amma alokacin har haushina kikaji don may na fadi haka. Kina ganin ke kin cuta masu ne baki san taimakawa rayuwan su kikayi ba ke . Tace bari larai sabon atamfane ma fa ta daura a jikin ta kuma bana cikin lafen ta ba ne don nasan kayan lefen nata. Gaskiya yaya sallah ya munafunce ni don da yasan akwai ci a wanan auren shine yaki jona daya daga cikin diyan shi. Nan dai sukai ta kulle kullen su har take cewa duk yadda zatayi ta goga min bakin jini a gidan nan sai tayi don bazata bari tana kallo ina cikin daula ba dani da uwa ta. Da tasan hakane da bala mai faci zata hada aurena dashi naje ko abincin ci ya gagare ni. Kamar yadda ta kulla haka ta samu wata aminiyar sabuwa take fada mata wai suna may suka saka min ido ina yadda naga dama a gidan Alhaji gashi sai dinke dinke yake min kullun kuma yanawa uwata aike ba kakautawa. Irin zancen da sabuwa ke so ke nan ranan da sakon ya samay ta nan ta haukacewa mutane a gida da masifa inda take shiga ba nan take fita ba ga miji kwance a daki ba lafiya amma ta tayarwa mutane da hankali. Haka yasa shi daurewa yafito katakata dashi yana cewa ke Sabuwa kin ishe ni da masifa da tashin hankali a gida. Ke lokacin da kika zo gidan nan haka wa yanda kika sama a gidan su kai maki ne shi ? Don haka daga yau na sake jin hayaniyar ki a gidan nan kowa yaya ne nai alkawarin sai kin bargidan ko akan waye haba kin ishe ni Sabuwa kin kai min ko ina. Ba a kan ki aka fara kishiya ba ke ba wasu ne kika zo kika sama a gidan bane wai ko su ba mata bane da basu daga hankalin su ba ga shigowa cikin su. Duk abinda ke fadan wai nayi wa yarinyar nan nayi mata sabuwa sai kizo ki kwata ke ma in na karfi ne ? Ya juya zai koma daki ya yanke jiki ya fadi tun take mata da yaran gida aka saka kururuwa a gidan aka kwasa sai asibitin birni Kwanan shi biyar a ka dawo dashi ba hannu ba kafa tare dashi abu kuma ya koma kasa sabo. Wanan faduwar ya dawo da ciwo sabo gare shi hawan jini yazo ya shiga ciki kuma da sauran ciwar wukan zamani da ba, a rasawa. Aiko yaran gida da matan su suka saka ta a gaba sai tabar gidan nan ko suyi mata dan karen dukan tsiya su kora ta. Ganin zasu iya mata abinda suka furta a kan ta yasa ta sulale ta bar gidan baki alaikum tun basu illanta ta ba. Haka ya sa suka dan sarara mata don ficewan ta gidan ya dan rage masu zafinta da suke ji a lokacin. Kusan kwanan kin da tayi bata gidan duk fama da jikin Alhaji akeyi don jikin yaki mai dadi sosai a lokacin. Haka nan ko yaushe cikin jike jike da dafe dafen magani ake mai wani ai mai tausa wani kuma dafa mai yasha. Muna faman sintiri yi mai sannu a duk dakin da yake haka za, a kwashe shi tara tara zuwa dakin. Ranan sai ga Sabuwa ta dawo wai iyayyenta ne suka zo suka bada hakkuri akai. Washegarin da ta dawo ne ina dakina ina barcin safe misalin karfe sha dayan rana na gama dafawa mama hausatu shimkafa da wanken sana an ta. Shine na dan kwata don na huta a raina can a cikin barci na nake jin ana sallama a daidai kofan dakina. Firgigit na falka ina amsa sallaman tare da fadin shigo daga ciki ina kokarin saukowa a saman gado. Lokacin suka shigo dakin Anty Sa,ade na ce daga birni tayi shigan ta na yan gayu ga kamshi na tashi daga jikin su. Tana tare da wata yar matashiyar budurwa tare da ita sai diyan ta biyu da take tafe dasu. Ban san lokacin da na yanka wani uban ihu ba na makale mata a jikin ta ina cewa wai ni Rahama yau ina zan saka kaina. Sai kuma na fashe da kuka a lokaci daya na durkushe a kasa daidai kafan ta ina rusa kuka gwanin ban tausayi. Naji tace yau ga tsiya taron da zakiyi min kuma ke nan Ramana daga gani na kuma sai ki saka kuka haka ? Tace wa budurwan da suke tare maryam tashi mu tafi wanan bata son zamana a nan. Da sauri cikin kuka nace anty don Allah kiyi hakkuri na daina ina kokarin share hawayen dake fuskana a lokacin. Nashiga daukan yaran ina cewa kai Fatima kece kika girma haka na taba hannun babban dan ta sai ya jaye daga gare ni. Nace baka san ni ba ko kokaga na zama wata bakauya dani ko ina fadi ina dariya tare da kallon fuskan yaron. Nan muka shiga gaisawa dasu cikin murna da jin dadi ina tambayan ta yaushe tazo garin namu ? Tace ikon Allah Ramana ke ce yau haka a dakin auren ki gaskiya naji mamaki da mama ke fada min wai aure zakiyi sai ko gashi na tabbatar da hakan yau da nazo dakin ki na gani. Murmushi nayi tare da fita daga dakin da sauri na fita zuwa bakin randan ruwa na na kasa na debo masu run shi a cikin kofin silver mai marfi. Nakawo masu ba laifin sun karba sun dan kora ruwan suka aje kofin amma yaran su sunki shan ruwan sai turanci suke da uwar su da dayan budurwan da suka shigo da ita gidan. Tambaya na take ina maigidan naki ne mama tace muna yana fama da jiki wai Allah ya sauwaka ya bashi lafiya. Mun dan taba hira dasu wanda akan karatuna ne nake mata ina fada mata cewa nawa karatun ya rushe ke nan tunda zaman gidan nan da nakeyi ba fashi a cikin shi. Tace komai ai na Allah ne baki san ko watarana zai yarda kije gaba ba ai nace cafdi anty bako a gidan nan ba. Tace muje kikaini na gaidashi da sauran abokan zaman naki ko ? Ban bata lokaci ba na mike muka nufi dakin mama hauwa inda yake kwance a ranan. Kwance yake yana ganin mu yake kokarin mikewa zaune sai dai bai iyawa dole ya koma ya kwanta yana masu sannu da zuwa. Kusa dashi naje ina cewa Alhaji anty na ce ta birni da nake baka labari tazo ganin mu yau. Hannu yake daga mata alaman yana masu sannu da zuwa yai matukar bamu tausayi gaba dayan mu a dakin. Gashi dai ya na son yin magana amma babu halin yin haka a gare shi sai in maganan ya zo mai yake samu yayi shi. Muryan anty ce ke fadin an kaishi asibiti kuwa a hakan da yake kwance a daki ? Mama tace an kai shi sai dai ba wani babban likita ne suka samu gani ba suka dawo wai akwai tsada ga ganin likitan. Haba komai tsadan shi ai sai a kashi a ji halin da yake ciki yafi wanan kumshe shin da akayi haka a gida yana wanan wahalan haka. Tace yana da yara manya ne maza suka ce mata eh tace idan suna kusa ina son magana dasu don Allah. Daga haka muka fita na kaisu dakin mama hausatu tabata dubu biyar dakin sabuwa ma haka da mama hauwa. Ai sai aka shiga saka mata albarka kwando kwando a ranan muka koma dakina kafin su yaya Hadi suzo gidan. Tace gaskiya Ramana mijin ki ya bani tausayi mutum yana wahala haka an kunsheshi a gida ba wani maganin kwarai gare shi. Kiyi hakkuri kinji duk wanan jerabawa ne daga Allah kici gaba da biyayyan dakike yi Allah ba zai bari ki tabe ga banza ba a rayuwan ki. Muna cikin maganan ne sai ga yaya Hadi babban dan Alhaji yana sallama daga kofan shiya na. Na fita naga shine nace mai ya iso itama na fada mata zuwan shi nan tafita daga waje gurin shi suka gaisa. Take cewa dama tana so ne idan sun yarda sai akaishi asibitin can birni don zata koma ga jibi kunga sai ku isa ina can amma sai abinda kuka gani ga hakan. Yai godiya yace sun gode zai yi shawara da sauran yan uwan shi takawo dubu hamsin taba shi tace ayi amfani dashi idan zasu zo din. Da zata tafi tabani dubu ashirin wai na dinga amfani dashi tunda mijina da zai bani baida lafiya yanzu. Sau mutanen gidan ta basu dubu goma wai su raba haba sai gida ya kaure da bakin albarka kowa na saka mata albarka agidan suka wuce muna kallon su. Basu ki ba bayan shawaran da sukayi sun yake cewa tunda za, a taimaka masu gara su kaishi su gani kawai zaifi . Haka su ka yanke shawara bayan kwana biyu da tafiyan ta suma suka take mata baya sai garin kano ganin likita. Basu sha wahala ba don ta basu lanban wayan ta idan sunzo su kirata don ta sani. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE. IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA YAR UWA KADA KIBA WA WANDA BAI BIYA BA PLEASE DON AMANA NAUYI GARESA, , 13 Shirin kwanciya sukayi tana saye cikin kayan barcin ta sun matukar karban jikin ta sai hullan da ta saka a kan ta don kariya. Har wanan lokacin mijin ya fahinci tana cikin damu wanda bai wuce nasaba akan yaran ta ne da zaman su ke hannun kishiyan ta. Tsaye yake saitin window dakin yana waya daga inda take kwance tana kallon shi. Tun yana wayan a hankali har yakai ya fara daga muryan shi yana cewa. Wai ke mahaukaciyar ina ce haihun ki nawa a gidana don a sani na ai kina haihuwa har ma yaushe ne kika haihu wai ? Bata ji may ake cewa dashi ba don ba handfree wayan shi yake ba a lokacin ta fahinci indai zaiyi waya bai saka handfree ba da kishiyoyin tane yake waya wani lokacin. Muryan shi taji yana fada a hasale yana fadin wai ke hindatu wata irin mace ce wacce a kullun sai ta fito da sabon sallon tashin hankali a rayuwan ta kada dai a zauna lafiya. To ki sani na fada maki banda kudin zuwa Germany ganin wani likita kan neman ciki duk shekaran yar ki nawa da zaki tayar da hankalin ki kan wai neman ciki yar just three years take nema fa yanzu. To ki sani duk abinda kikaga dama kiyi amma amma ni bada kudina ba cikin wanan shirmay naki. Daga haka ya katse wayan tare da jan tsuki ya nufo gadon don ya kwanta shima. Yana kwantawa yaji muryan salihan matar nashi mai son shi da kaunar shi tsakani da Allah na fadin. Hindatu ce ko ? Yace a hasale itace mana. Anya kishin hundatu ko akwai imani a cikin sa heartbeat ? Yace nima abinda nake tunane ke nan ko dai tana da matsalan kwakwalwane . In ba haka ba yaya da ganin wata da ciki duk tabi hankalin ta ta tayar ga banza ? Ta manta cewa Allah ne ke bayarwa ba mutum ke badawa ba da kan sa. Tace to ai ba fada zakai mata ba tunda abinda take so ne sai ka lalashe ta a wuce gurin. Yace oho na tsaya mata sanya ta ci gaba da min rashin hankali da ta saba ke nan ko ? Tace ba haka bane hankalinta ne ya tashi bata cikin natsuwa ne yakawo hakan . Yace matar da bata damu da damuwan kowa ba kan ta kawai ta sani ita a rayuwan ta. Tace hakkuri dai zakayi ka rarasheta kada ta jefa kan ta cikin wani hali kuma na daban. Yace na fada maki ki bar wanan yarinyar kawai samun daurin gindi tayi a gurin daddy shiya sa take min abinda taga dama. A can kuma gida Nigeria inda Hindatu take zaune gaban mahaifiyan ta tana rusa kuka. Mahaifiyan nata tace na fada maki kibi a hankali kin san halin mijin ku da murdaden hali baida saukin fahinta ko kadan. Maza ki kirashi ki kara bashi hakkuri tun bai ce zai dauki wani mataki ba a kan ki. Uwar tace maza kira min shi nai magana dashi don nasan yanzu yana can hasale duk inda yake. Mama yanzu fa dare ne a can wata kilama sun kwata a lokacin nan ko. Dama dai baki son zaman lafiya aike baki san maza sai da lalashi ba kina ganin komai dole daddy sa ya sa shi dole a kanki. Sai dana fada maki kada ki kirashi yanzu kiyi hakkuri har su dawo don sai ya fahinci kan wanan matar tashi kike wanan haukan haka? Mama ni kunyan kiran sa fa nake ji na fada maki kin kuma ji amsan daya bani har da ce min wai ni mahaukaciya ce. Kira min shi kibani shi nace maki aini dole ya ta tsaya ta saurare ni ko. Dole Hindatu ta kira layin mijin nasu har wayan ta katse ba a dauka ba . Uwar ta rude iya rudewa don tana gudun mahaifin hindatun yaji yai masu tsiya. Sake kira min shi inji uwar cikin kidimaywa taje magana fuskan ta kan yarta. Dole hindatu takara kiran shi yana ji yaki dagawa sai Saade ne ta daga kiran tare da mika mai wayan ya kalla cikin hasala tare da kara mai a kunnen shi. Mama ya dauka Hindatun tace tana mikawa uwar wayan Muryan mahaifiyarta yaji a wayan yasa shi dan gyarawa cikin muryan ladabi yana cewa Yusuf nice a layin, Yace na gane mama kuna lafiya yaya mutanen gida tace duk muna lafiya. Yusuf dama kan zancen da kukayi da yarinyar nan ne nake son maka magana . Yace mama idan wanan zancen ne ni na gama magana na ba hannuna acikin wanan magana. Har yaushe ta haihu da zata dauku tashin hankali tasakawa ranta haka ? Uwar tace na sani Yusuf nasan da haka ai rigimane kawai irin na yarinyar nan don shi ciki ai rabo ne. Don haka kayi hakkuri abar wanan zancen don bana son ko mahaifin ta ya san da wanan zancen haka. Don Allah kayi hakkuri kasan halin kowa da irin nashi tunanen hakan yana damun tane yasa take wanan haukan haka. Inji Saade ke bashi hakkuri bayan sun gama wayan da mahaifiyar hindatu din. Yace ba komai bane ke jawo min haka sai wullakancin da sukaga daddy da hajiya suna min akan su amma yarinya zata gane kuren ta wallahi. ****** ********* ****** Mama ce daki da baba cikin tausan murya take cewa yanzu malam haka zaka bari wanan daman ya wuce mu a gidan nan. Allah ya rufa maka asiri sai masu hannu da shunin gari ke zuwa neman yar nan don sa, an ta. Amma ita da uwarta basu fahinci nasaran haka ba don basu da fahinta akai. Wancan auren da tayi da suka samu dadin su da wasu kaci ko wanna ma idan yai dadi ai sune zasu ci abinsu muna kallo. Dadin baki mai ratsa zuciya mama kewa baba kullun akan maganan tun bai yarda ba har takai ya amince da zancen ta ya shiga zuciyar shi ya zauna daram ya kafe zai ba Jatau ni. Ko ina so ko ban so dole ne na amince da zabin shi tunda shine keda Alhakin zaba min miji ai. Ranan da baba ya koma dakin Inna sai gashi ya fito mata da zancen wai maganan Rahama da Jatau fa yana nan don haka sai ku fara shiri akan aure nan bada dadewa ba za, ayi. Take ran Inna ya baci idanuwan ta sun sauya launi cikin bacin rai take cewa . Malam da ba dakai na haifi yarinyar nan ba sai nace kana hassada da ita ko kiyayya don irin kiyayyan da kake gwadawa yarinya yai matukar yawa a gidan nan. Yanzu kai ko kunya baka ji garin nan aji zaka kara aurar da yarinyar nan ga wani tsoho don kudi don abin hannun su kukewa kwadai. Yanzu Asiya ni kike kallin idona kice saboda kwadan abin hannu nake aurar da yarinyar nan. Inna ta ma rasa may zata ce da shi saboda takaicin daya rufe ta a lokacin. Cikin bacin rai take cewa ai ba karya na fadi ba don duk wanda ma yaji haka yasan abinda kukewa ke nan. Yanzu wancan auren abinda ta samu wa ya amfana dashi ba kai ba ina gidan ne kawai kila zata tsira dashi. Don haka wallahi wanan karon bazan yarda da cin zalun din yarinyar nan da ake muna ba. Har nawa yarinyar nan take da za, a dinga mata haka ina ga yayyin ta nan zube a gida su ko zancen su ba ayi. Yace to tunda kin isa da ita duk matakin da zaki dauka kan wanan zance sai ki dauka mu gani tunda kin isa ke . Wasa wasa magana har takai ga daga murya tsakanin su sai ga mama da ta dade tana sauraren su ta saka baki daga waje tana fadin Malam kada ka biye mata kasan va hankali ke ga Asiya ba don son abinda yarta ke so ya rufe mata ido bata hangen abinda kaje ya dawo. Cikin fushi baba yace mata ki kyale ni da ita Lauratu wallahi Asiya kin yi karya dake da yarki ku mai dani mutumin banza a gari. Duk iskancin da budewan idon ku da kuke ganin kuna dashi yanzu baku kai ni ba don haka ku ci gaba da min rashin da, a ke da yar ki ku gani a gidan nan. Indan kunce haka kuka dauko sai kun kwammace rashin zaman ku gidan nan dani. Kallon shi Inna tayi shekeke tace dashi ai kasan kaine keda rayuwan mu a hannun ka . Indai kan wanan zancen ne sai dai ajimu don nai magana akan hakkin ya ta ai ba haramun bane ko ? Kuke samun riban auren da takeyi shi yasa kuke son kara tursasa mata sai tayi wanan din taje ta ciwo maku kasuwa gidan. Duk masifan baba yana ganin ta haukace mai sai jikin shi yai sanyi yasan duk yadda akayi akwai abinda ta digora dashi take hakan don ba halinta bane haka. Aikin banza inji mama tace may ye bamu sani ba wani dare ne kuma jemage bai gani ba. Auren da sai anyi kifi kowa zakewa da jin dadi shine har za, a tsaya ana muna tijara akan shi. Malam ka kwantar da hankalin ka kana nan zakaga yadda take rawan kafa da jiki ita a dole yarta ta samu gurin zama. Idan ni ban yi rawan kafa ba ai ke sai kiyi tunda ke ma kina da yaya dakin ki sai ki bashi daya daga ciki a wuce gurin. Tana fadin haka ta koma ta kwanta abinta tare da watsawa baba harara tana fadin don an mayar dakai haka bari a turo ka kai min cin mutunci ko. Tun ranan da akai fadan nan ina wuta mama da baba su jefa mu ni da Innata. Duk wani kule kulle da makirci shi mama take kullawa akan zancen sai cin kudin Jatau takeyi tana bushashan ta a cikin gida ita da diyan ta kawai. Duk wani hanya da baba zai fahinta mama ta toshe shi har yakai ta fara dan fita zuwa gurin malaman ta wai a kulle muna baki duk mu ukun sai abinda tace kawai za, ayi. Haka Inna take cikin tashin hankali kan zancen don ta fahinci idan bata yi da gaske ba babu makawa sai anyi wanan auren gamin gan bizan dani da Jatau. Kullun tana hanyan gidan mama Altine kan magana daya duk tafita hayacin ta. Gashi mama taci kudin shi yakai dubu ashirin da biyar tana karba wai tana bani tana kuma kamun kafa da sauran. Bata san cewa komai nashi a lissafe yake mai ba don ba mutun ci ne dashi ba akan dukiyan shi ko kusa bai taka kafan Alhaji Garbati ba gurin tara abin hannun shi ba. Amma mutane don baya ci sai suke gani yafi garbatin ma tara dukiya a garin. Wata rana ina fitowa zan shiga gidan mama sai ganin shi nayi a kofan gidan mu don kusan a nan yake wuni. Yana gani na ya fara washe baki ya na dan soshe soshe kamar mara gaskiya. Ya dan tafo duduke kusa dani yana cewa a, a mutumiyar barka da fitowa ashe yau nazo a sa, a zan gan ki ashe ? Wani kallo nai mai nace yauwa sannu baba . Yayi dariya hakoran shi da wanda babu da rinanun sauran dake cikin bakin shi suka baiyyana a fili. Cikin dariya yake cewa ai ni yanzu ba babane gurin ki zaki dai iya kira na da ango ango mai shirin shan mai ko ? Nace tau ikon Allah baba aure ne zakayi halan ? Kallon mamaki yai min yace kamar yaya kike tambayana haka kamar baki san da zancen ba kuma. Na dan fadada fara, a na nace ban ko sani ba baba a ina kasamu matar ke nan ? Yace ikon Allah gaki tsaye a gabana kike min wanan tambaya kuma ai ni yanzu nan da kika ganni jira kawai nake a shafa a tsakanin mu don har dukiyan aure na biya ko jiya. Nace amma bakasan wace ka biya dukiyan akan ta ba ko don bani bace kake zance akai. Ya sake kallona cikin mamaki yace ai ko ke din ce nan da sati biyu insha Allahu zaki tare a gida . Dadai kin dan tsaya mun fahinci juna naji dan naki tsare tsaren don kin san shi marigayi garbati ya riga ya shagwabaki so sai. Ban tsaya sake sauraren shi ba kada ya kara jefani wani sabon damuwa na shige gida abina na barshi nan yana kwala min kira kamar wani tsohon maye. Na samu inna ta a waje ganin yanayin da na shigo gidan ciki yasa ta barin abinda takeyi tabini daki. Ta samay ni zaune nayi tagumi sai hawaye nake zubarwa a idona babu sautin kuka. Hankali a tashe take tambayana ke kuma da kika fita yanzu cikin dadin rai may ya dawo dake gidan haka ne kuma ? Na dago idanuwa dake zubar da hawaye ina cewa Inna kinji mutanen nan ashe wai har sadakina baba ya karba hannun Jatau. Cikin mamaki Inna tace yaushe akai hakan bamu da labarin komai akai nan dai ina kuka nake fada mata yadda mukayi da Jatau din dana fita. Inna ta zuba min ido cike da tausayina domin tasan irin zafin da nake ji a lokacin take cewa. Yarinya ki kwantar da hankalin ki insha Allahu ba a wanan auren idan kinga anyi shi sai dai bana raye. Bari yanzu naje naga mamakin mai kuli musan abin yi tun kan mu makara akai. Koda hakan na nufin rabuwa na da mahaufin ki ne sai dai mu rabu amma ba mai maki dole akai indai ina raye . Na gaji da wanan mulkin mallakan da ake muna a gidan nan ya Isa hakana wallahi zasu gane basu da wayo wanan zubin. Gidan mama ta fada muka shiga kusan tare a lokaci daya yadda mama ta gan mu tasan ba lafiya ba. Nan Inna ta shiga zaiyano mata duk halin da ake ciki itama dai fada ta shiga yi da tsinuwan mama lauratu tana cewa. Wanan karon saidai abinta ya koma mata amma Allah bai basu ikon yin hakan a kanki. Mafita daya ne idan zaku iya da dare muje gidan maigari mu samay shi mu fada mai abinda ke faruwa don asaka ma abin waigi tun wuri. Inna tace may zai hana ni zuwa indai zaki kaimu mai kuli ai mu mafita muke nema tako wani hanya indai hakan zai samu. Kamar yadda suka shirya dare nayi Inna tace zata shiga gidan su ta gaida wanta da baida lafiya. Lokacin ni dama ban dawo gida ba ina gidan mama Altine don anan zan kwana Akai sa, a baba bai hana ba don dama yana son zasuyi magana da mama kan zancen auren gashi kuma kafa ya samu. Inna na zuwa muka wuce zuwa gidan maigari mun samay shi yana cin abinci muka gaisa dashi da iyalin shi cikin mutum ci. Sai da ya idar muka isa gurin shi nan mama Altine ta koro mai duk halin da ake ciki dani. Ya kurkure baki tare da watsar da ruwan gefen shi yana cewa kai amma malam Audi baiyi ba wallahi. Don ma dai Allah ya hada shi da yar aziki ne ya samu tai mai biyayan akan na farko yanzun kuma shine yake son lakaka mata wani. Kada ku damu dama mun samu wanan dokan daga birni cewa babu auren dole ga yarinya ko yaro yanzu wanda kuma ya karya doka tara mai tsanani a kan shi. Don haka kutafi gida gobe da safe insha Allahu zan nemay shi muyi magana dashi. Mukai sallama dashi muka barshi yana fada yana cewa wasu mutane basu san ciwon kan su ba wallahi ko. Ina jatau ina yarinyar nan ina zai kaita duk yadda zan fahintar da mahaifin ta illan abinda hakan zai haifar zanyi idan ya kiya kuma nai karan shi. Hakan matan shi suka ci gaba da bashi labari akan zaman da Inba take a gidan dafin karfin ta da mama take a gidan tana mata mulki kama karya. Tun da farar Safiya ake kwasa sallama a kofan gidan mu baba ya fita ganin ko waye ? Sai yaron mai unguwa yagani nan yake fada mai ana neman shi a fada hankalin shi yai matukar tashi sosai don idan akwai abinda dan kauye yaki jini shine kiran maigari. Yashigo gida hankali a tashe yana fadin zashi gurin mai gari yanzu yaron mai unguwa yazo yace ana neman shi gidan mai gari shida mai unguwa. Mama hankali tashe take cewa to may kuma ya faru ko anyi wani abin ne kuma. Bai tsaya bata lokaci ba yafita gurin amsa kiran inda mai uguwan mu yai mashi jagora har gidan. Bayan an gaisawa ne maigari ya gabatar mai da zancen karan shi da aka kawo kan yana son yiwa yar shi kuma bazawara auren dole da Jatau. Sai da wani uban zufa ya karyowa baba yana gyara zaman shi cikin kwantar da murya yake cewa. Rankaidade ba haka na bane ba wai auren dole nake son yi mata ba ita da uwarta ne dai basu fahince ni ba. Take dattawan fada suka katse shi da cewa shin yarinya ta yarda ko bata amince ba akan auren. Sai baba ya dukar da kan shi kasa yace a gaskiya ba ra, ayinta bane nawane dana iyayyen ta hakan. Iyayyen ta uwar da ta haife ta ko wa kokai da yan uwan ka ke da wanan danyen hukuncin akan ta haka ? Shiru baba yayi don ba amsa sai lokacin maigari ya karba dacewa ko wancen auren na farko dakai mata mun so mu hukunta ku amma sai muka duba shi garbati mutumin kirki ne zai iya rike maka ita amana. Amma Jatau ko mutumin banza mutumin da bai san darajan kowa ba a garin nan sai kansa. Babu wanan zancen yarinua dai bazawara ce abarta ta yi zabinta da kan ta dan doka yanuna yanzu ko budurwa ce idan bata son aure kada ai mata dole balle bazawara da tasan ciwon kan ta ko. Fada sosai akai wa baba ya baro fada sai dai maigari ya boye mai cewa Inna ne da kan ta ta kawo karan shi yadai ce makwabtane suka zo suka fada mai wanan labarin . Shiko a matsayin shi na maigari yana da ikon karewa yaro da babba hakin su idan za, a cuta masu. Wanki nake yi kafin na shiga gidan mama Altine ina dan rarage kayan daudan mu ni da kanne na da Inna baba yadawo. Kana ganin shi kasan babu lafiya tare dashi lokacin Inna ko har ta shirya tana jiran cin mutuncin da baba zai dawo mata dashi daga gidan mai gari. Yana shigowa mama najin sallaman shi tai but tafito daga daki tana fadin malam lafiya dai ko wanan kira haka tunda sassafe haka ? Yace lokacin da yake zama saman dutsen dake tsakar ana alwala a saman shi bari ke dai Lauratu munafunci baiyi ba wallahi. Wai yanzu aka samu munafuki a cikin uguwan nan yakai karana kan auren yarinyar nan da Jatau gurin maigari. Gaban mama yai mugun faduwa tace kara malam wake da wanan aikin haka yace wayasani yadai ce daga uguwar nan namu ne akai karana gurin shi. Affan malam wa zaiyi karan ta inba ita da uwarta ba kaiwa kake tsamanin zaiyi haka waya damu da damuwan su anan balle ya kula al, amarin su. Umm, umm lauratu daga nan ne dai aka fadawa maigari amma ai mace bata ganin mai gari kai tsaye wane ita nan. Nan suka shiga dura ashar har mama na ikirarin ai ba maigari ne ya haifa mashi ya ba da zai mai iko akan gidan shi. Baba yace Lauratu na rabaki da wanan zancen kada ki dauko min wani sabon rigima kuma don ni yanzu tsoron mutane nake ji su labe ta baya suna sauran ki. Mama tace duk mai fadi yaje ya fadi amma aure ba fashi sai anyi shi tunda bashine ya haifa muna diya ba ba kuma cin shi a gidan mu. Baba ya katse ta da cewa kina da kudin biyan taran da za ai min ke nan ko da kuma dauri kan na shiga hakkin diyata bada son ran ta ba. Cikin mama ya duri ruwa sai da ta kewaya ban daki tafito ta samu baba a gurin yana fada har lokacin. Nidai ina wanki na tare da hamdalla a cikin rai na don maigari da mama Altine sun ceci rayuwana ko ba komai sun kwato ni da shiga bani. Inda nake ina buga zanin da zan shaya mama ta kalla tare da cewa tir dake Rahama kinyi hasara wallahi tunda akan yi yau akai karan mahaifin ki har gurin mai gari sukutum. In yar arziki kike kin haihu cikun malam yau kije kice wa maigari da miyau bakikin ki za ai wanan auren. Ban kula ta ba illa idon da suka sako min daga ita har baba din a lokaci daya. Ganin bazan taka masu ba ne baba yace ai in taki wanan auren nikan ba dai gida na ba wallahi don ba zan zauna da ita ba haka ina ganin bakin ciki a raina. Fat naji muryan Inna a bayan mu tana fadin a hayye nanaye wanan hukuncin yau yafi nono fari a gare mu don na dade ina jiran anan ranan dama. Idan baka zauna da ita ba a gida don tana bazawara ai zaka zauna da gandan gadan din yan mata suna maka manne da dare a bayan katanga da samari. Aure dai ne Allah ya kawo muna saukin shi cikin dadin rai Allah kuma yaiwa wanda yakai kara albarka. Ikon Allah zamani yanzu Asiya bakiji kunyan wanan maganan ba a duniya ana jinki kina guda akan yar farinki don baki da kunya ga idon ki. Kunya kunya fa kace malam ai kunya ya kaura ba yau ba ga idon Asiya don ka sani don baku so haka ba. Gida kuma in kace yarinya bata zama maka gida sai dai dani da ita mubar maka gidan ka a tare don ni ban san zaman da zanyi ba kuma ? Lalai Asiya kin haihu cikin fulani yau kin sheda min kun bar rugga da dadewa tun da idon ki ya kyakyashe haka kan yar farin ki. Mu zuba dake a gidan duk inda zaku tafi ku tafi badai gidan Audi ba wallahi ba mai min gori kan abinda na fi karfi yazo yafi karfina a gida na. Inna tace haka yafi nono fari wallahi yanzu kuwa ba sai anjima ba zamu bar maka gidan ka sai ka zauna da wa yanda kake so kajika kasha. Magana har takai ga makwabta sun shigo gidan namu suna tambayan ba, asi nan baba ya shiga zagin mu dasu yana cewa wai duk munafukaine mu dasu afice a bar mashi gidan shi. Hijjab dina na jawo daya bushe na saka nafice daga gidan inajin mama nace indai baki auren Jatau daga wanan fitan kin fice daga cikin mu ke nan. Nasa kai abina na fice ko waigen ta ban tsaya yi ba sai gidan mama Altine ina shiga take cewa dani Allah mun godema da ya kawo muna saukin al, amarin nan. Ni yanzu damuwa na shine wanan rantsuwan da mahaifanki ke yi sai kinbar maigidan shi ita kuma Inna ki ta rantse kina barin gidan itama ta bari ke nan. Nace mama nima shine ke damuna wallahi don bazan so ace saboda ni Inna ta bar dakin auren ta ba akaina. Zafin raine ke damun su dukan su daga ita har malam Audi din suna cikin bacin rai ne. Muna nan muna magana sai jin hayaniya mukayi ya kaure a kofan gidan mu da sauri mama ta yafa tafita daga gidan. Jatau ne yazo ya zauna yana cin mutunci wai kamar shi za, a tozarta a gari ai karan shi don yace yana son . Indai har ban son shi nafito na bashi kayan shi da naci don shi bai gaji hasara ba akan shi. But nafito daga gidan mama nace dashi dakata malam ga mutane sun taru wasu har a zanan gida matan aure ke lekowa ta kafan zanan gidan su don gulma. Nace tsakani na dakai ko uwa ta ka taba ba mu ko kwandalan ka a hannun mu idan dai ka taba ka fada min yanzu na biya ka abinka. Sai yadan washe baki yace ni da zaki yarda ki amince ai da babu zancen biya a tsakanin mu. Amma ace ba a bani mata kuma a ci min dukiya na ga banza shine ba zan lamunta ba gaskiya. Nace to kayi da wanda kaba kudin ka don ni ban san ka raba bani komai ba, muryan mama Lauratu naji daga ta cikin gida tana cewa tau mara kunya idan ke baki ci ba ai mu iyayyen ki munci don nai amfani dashi gida kowa yaci. Nace kin dai ci ni tundana dawo kin taba girka abincin ki kika bani a gidan nan ko kiba kanne na sai naji tayi shiru nan mutane suka saka salati yan gulma suka hau bakin su. Aka shiga zuga shi na shige cikun gida abina na barshi nan yana haukan shi shida yan kallin shi. Nasa kafa zan karasa ciki naji muryan mahaifina cikin kakausar murya yace dakata nan Rahama badai gidana ba wallahi nai maki itaka da gida na daga yau duk inda zaki kije nayafe ki. Inna dake daki tagama hada kayan ta naga tana fitowa da buhuhuwan data dura kayan ta a ciki. Nan na duka nafara rusa wani sabin kuka zuciyata tana raya min nace kawai na amince da wanan sabon kaddararen auren akaina kada uwa ra ta shiga wani hali saboda ni. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANA NE YIN HAKA, , , 12 Sanye take a cikin kayan sanyi irin na kasan turawa rigan yakai kusan gwiwan ta hakanne ga mijin nata kamar yadda tasaka kayan tare tsananin sanyin da akeyi a garin. Yana rike da ita a kafadan shi suke saukowa daga matakalar benen gidan nasu wayan shi ce dake aljihun shi ta ruri a lokacin yadan tura hannun shi cikin aljihun shi ya ciro ganin wacce ke kiran shi a layin yasa shi daukan wayan nata. Sai da ya sauke wani irin ajiyan zuciya yake cewa yaya akayi ne zulfa ? Jin sunan wacce ya ambata yasata zare jikin ta daga nashi a hankali, tafara tafiya tako biyu zuwa bakin dayan kujeran dake falon. Ta zauna tare da tsura mai ido daga inda take a zaune daga jin yadda yake magana ta tsigan lalashi ta san fitina ne ake da shi ga wayan. Can taga yayi dan murmushi a fuskan yana cewa ke ma ai uwarsu ce zulfa don haka kiyi yadda ya kamata dasu mana. Kofa likita bamu samu gani ba tukun ki ke wanan zance haka idan mun gama ai zamu dawo ne ko. Bataji may tace dashi ba sai dai murmushin da taga yayi a fuskan yake cewa wata rana kema ai zaki bar naki a gurin ta ko ? Don haka ki yi hakkuri kifitar da komai a ranki ina diyana diyan ki ne kema koda ba, a gida kike ba. Can taji yace kwarai da gaske zulfa aiko ita kun san dalilin zuwan namu wannan lokacin ko. Shiru ya dan ratsa falon yana sauraren mai maganan ta waya har ta taji shi yana cewa ok shike nan sai mun yi waya anjima ke nan. Ya kashe wayan tare da dago kai yana kallon inda take zaune, ya dan yi murmushi . Ya zauna gap da ita yana cewa yaya tafi mana ko kin kuma zauna anan ? Ta dago idanuwan ta fuskan shi a cikin damuwa take cewa dashi akan yaran take magana ko ? Bai bata amsa ba don yasan ranta zai kara baci ne ga banza yace tashi mu tafi ko ? Da kyat ta mike tsaye ga dan matashin cikin dake a jikin ta ya turo a cikin rigan dake jikin ta. Rai bace take magana tana fadin kaga abinda nake gudu ke nan tun farko nace ka bari na kai su gurin hibba su zauna har mu dawo amma kace wai a barsu su zauna agida tunda akwai mutane. Ya jawo hannun ta yana fadin ke ma dai kin san bazan lamunci ina da gida da iyalina a ciki kuma na dauki diya na zuwa wani gurin ba. Tace idan baka yarda an kaisu wani wurin ba ai gashi kana shan korafi akai ni dai tsorona kada a cutawa yaran da basuci ba basu sha ba kan zancen mu. Haba Sa,ade Zulfa ce zata cutawa yarana kuma kada ki manta fa a matsayin yar uwa take a gareni fa. Tace a da ke nan yanzu kan ai a matsayin diyan kishiya take daukan diyan ka gare ta. Kofa ya bude masu suka fito daga gidan wani sanyi ne ya daki fuskan ta amma ba yadda ta iya dole haka zasu fita duk da tsananin sanyin da akeyi a garin Don fitan ya zama masu dole sai sunyi shine dole zai sata fita a hakan. Bayan sun gama da asibiti ne suka wuce zuwa wani shago nan ta dan yo sayayan abubuwan da ya dace ta tsinta har da tufafin yaran ta dana yaran abokan zaman nata. Ko da suka dawo gida a gajiye take don bata da kuzarin da zata dinga tafiya haka mai nisa a jikin ta. Zama yayi kasa a daidai kafan ta ya dan fara matsa mata su a hankali tana jin dadi hakan har cikin ranta ta dan fara lumahe idanuwan ta a hankali. Haka yasa ta samu saukin yadda take ji a ran ta a lokacin sai bata samu wani matsala komai ba ga yadda take zato. Washe gari ta riga shi sauko wa kasa don ta karya saboda yace yana son ya dan kara barci. Har sai bayan ta gama ne sai gashi yau sauko kasan a lokacin har yai wanka yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi. Sau daya ta daga kai ta kalleshi taci gaba da duban wayan ta da takeyi tana murmushi a fuskan ta. Da alama hiran da takeyi yana mata dadi a ran ta lokacin ya iso inda take yana cewa madam yaya jikin naki ? Ta dan dago kan ta a hankali ta dube shi tana cewa Alhamdullahi ya kokari bai amsa mata ba sai da yakai zaune yace kokarin yiwa kaine ai nidai gurina naga Alllah ya rabaki da wanan cikin na jikin ki lafiya. Sai lokacin tabar abinda take a wayan ta ta dago kan ta ta dube shi inda ya zauna sai suka hada ido dashi tayi saurin kawar da idon ta cikin nasa . Yace No no no kada ki soma yi min wanan kukan naki dake tayar min da hankalina please ? Yace cikin kamo hannun ta zuwa na shi cikin girgiza mata kai yake fadin ki dinga sakawa zuciyar ki dangana Allah daya baki ciki a cikin wanan halin da kike yasan dalilin yin haka a gare ki. Don haka ki zamo cikin bayi masu rugumar kaddaran ubangijin su ako da yaushe. Wanan tayar da hankalin da kikeyi zai iya kara jefa ki a cikin wani sabon tashin hankali kuma har mu dake tare dake abin ya shafi zukatan mu. Ajiyan zuciya ta sauke tace dole na daga hankalina idan na tuna da lalurar dake tare dani sai ga shi kuma wanan cikin yazo ya shiga again. Murmushi yayi tare da jawo ta ajikin shi yana dan shafa bayan ta yake cewa lafiya lau zaki haihu insha Allah ai ciwo ba mutuwa bane. A hankali tace dashi abin ne ke bani tsoro sosai sai yake hanani sukuni a raina. Ya girgiza mata kai yace ai abin bada ga nan bane heartbeat ke dai Allah ya kawo muna sauki ga al,amarin. Sai da ya tabbatar ta kwantar da hankalin ta ya mike yana cewa zai dan fita amma ba zai dade ba indan ya fita. Nan ya fice ya barta zaune zuciyan ta cike da tunanen yan diyan ta biyu dake gida Nigeria gurin kishiyan ta. Tun ba akai ko ina ba gashi ta fara jin Zulfa din ta bugo waya tana korafi akan rikon yaran nata gashi zasu iya share wata uku basu koma gida ba. Shine dalilin da tun farko taso zuwa da yaran ta ko tabar su gurin yar uwarta amma sai ya nuna mata rashin yardan shi ga hakan . Don shi mutum ne mai matukar son iyalin shi a kusa dashi akoda yaushe haka ne yasa akwai shakuwa sosai tsakanin shi da italin shi don yana fitarwa kowa da hakkin shi yadda ya dace. Wanan zuwan da sukayi dashi ba itace ya dace tabiyo shi ba amma saboda dalilin rashin lafiyan ta yazo da ita din. Wanda kafin su zo saida akakai ruwa rana da sauran kishiyoyin nata akan basu yarda da hakan ba don acewa su yafi nuna kulawan shi akan Sa,ade da yaran ta bisa gasu. Don har kara suka kai shi gurin iyayyen su kan abinda yake shirin yi masu. Ita bata da ko labari sai dai ta fahinci ya dauki zafi da sauran matan nashi a lokacin. Ita da ake abin akan ta sai daga baya ta fahinci rigiman akan tafiyan su ne akeyin sa. Haka ne ya dan haifar mata da rashin natsuwa a tare da ita don haka ta bukaci da ajaye tafiya sai taga likitan ta na nan gida Nigeria. Amma amma mijin tana yaki janye zancen ba irin rokon da bata mashi ba kan ya barta amma sai yaki yarda da bukatan ta. Karshe ma cewa yayi da ita idan ke lafiyan ki bai damay ki ba ni ya damay ni tunda bake ce keda hasara ba ai . Hakkuru ta bashi don yadda taga ya hau tasan itama zata iya samun nata rabon fitina a ciki don haka taja bakin ta ta tsuke tai shiru har lokacin tafiya yayi suka wuce. Don makaran ta ne kawai yasa ta bar yaran ta a hannun kishiyoyin ta ba don taso ba don tana nan ma yaya aka kwashe da su balle bata kusa. Ko ita Zulfa ba don Allah ta rike yaran ba don sai daya zube mata kudi masu yawa ta yarda zata zauna dasu din. ****** ********* ****** Na gama aikin da nake taya mama altine na kwashi kayan na aiki tare da kaisu bakin kwata na wanke komai fes na mayar na kife mama na zaune ta zuba min ido daga inda take zaune ta motsa furan data dama ta sha. Ina yarfar da ruwan dakw hannu na bayan na dauraye kafana take cewa sannu Rahama ai kin huta ke bakajin kiyuyan aiki ko kadan. Da ace uwarki lauratu ta gane haka ta nemi zaman lafiya dake a gidan dan wanan zaman da zakiyi a gida aida ta more maki sosai. Na dago kai da sauri ina kallon mama nace kai mama matar da tun ina yar kankanuwa na fahinci bata kaunana yaya zan zauna da ita ta more min haka. Ni fa yadda mama bata kaunana a sannu nima haka kiyayyan ta ya shiga har kasan raina wallahi. Mutumin da zai iya maka sheri da kazafi aiko kasheka yana iyayi mama. Bata kashe ki sai dai sherin ta ya koma mata baga diyan ta nan ba babu mashinshini a tare da su duk fa cikun mugun halin ta ne amma ita bata ganewa ne kawai. Ki debi abinci kici kada yai sanyi gashi da zafin shi nace ba yanzu ba mama sai anjima kafin na kwanta don tunda na dawo gida idan Innata ce da girki a gidan mama altine nake kwanci na don nasan Mama bazata yarda da na kwana a dakin ta ba yadda muke din nan yanzu kamar annabi da kafiri ni da ita. Muna nan muka ji sallaman dan wurin mama yana cewa Rahama wai kizo inji baba . Nace yau baba lafiya ya dawo gida haka da wuri don nasa sai yamma lis da magariba yake dawowa gida. Ban bata lokaci ba na figi hijjab dina zuwa kiran baban nawa da yake min ko da na shiga yana alwala zaiyi sallah na nufi inda yake zaune saman dutse na gaishe shi da dawowa. Na samu guri daga gefen shi na tsugunna ina fadin baba gani . Yace dan dajan ta min na rarage alwala na mike na koma gefe ina jiran idarwan shi har lokacin daya gama ya mike tsaye. Sai naji yana kiran Lauratu lauratu, lauratu fa da dan karfi ta amsa daga daki da saurin ta tafito tana gyara daurin zanin ta. Tana cewa lafiya dai malam wanan kira haka kamar zaka tsaga min kunne dashi. Yace to ke ce din idan ba haka aka kiraki ba sai ki kyale mutum tsaye wani zubin. Yace ina ita Asiya take inna dake bakin murhu tana kashe wutan da tai girki tace gani. Yace to dama ba wani abu bane yasa nai kiran ku ku duka ukun sai akan Rahama gata nan. Allah ya kawo mata mai nema a cikin sauki ba ko wani bane sai Malam Jatau na hayi dotse abokin maigidan ta marigayi. Shine ya aiki min yau da safen nan akan yana son ta da aure ya hada ta cikin iyalin shi. Don ya yaba da zaman ta gidan aminin nashi da tayi kwadayin hakan yasa yake sha, awan auren ta. Wani irin dariya gami da guda mama ta ranga tare da cewa yarinyar tayi tagomashi ga tsofin gari. Wani irin dam dam naji kirjina yaba da a lokaci guda cikin raina nace wani malam Jatau kuma can ai gara ma Alhaji garbati marigayi din shi a tsaye yake kyam ba irin malam Jatau ba dake tafiya a duke. Gashi da dan banzan kazanta da rowa ko kiyashin gidan shi sun san shi da rowa da mugun halin. Mama sai da ta gaji don kanta san nan ta tsagaita dariyan ta tana cewa injin ka bashi dai. Yace ban amsa mai ba sai naji shawaran ku tukun akan zancen kafin na basu amsa ta. Lalai ma malam yo may zaka tsaya jira da ita Allah ya kawo mata mai so da wuri haka ? Yace ai komai sai a hankali akeyin sa tunda yanzu ita ba budurwa bace kin ga zama dan bata zabi ai ko? Zabin may har nawa Rahama take da za, a tsaya neman wani zabin ta kudine dai akwaishi kaga sai taje taciwo muna nashi kasuwan kuma. Ban san lokacin da bakina ya kufce ba nace ai kina da tan mata zuka zuka har uku a dakin ki kibashi mana. Salati ta saka tare da saka kuka wai naci mutuncin ta a gaban uwaye na ai ba ita bace tasamin farin jinin tsofi balle naci mutuncin ta bakin halina ne dani da uwata ke bibiyan mu. Da kyat baba ya lalashe ta ta koma dakin ta nikuma yai min fadan haka kaca kaca ya fice gidan. Dakin Inna ta muka shiga kowan mu bakin ciki yana cin sa a rai da wanan sabon fitinan dake neman bullo muna kuma. Nace wa Inna ta ni wallahi wanan karon ko kashe ni baba zaiyi ba zan yi auren nan ba ai bani kadai ce diya ba a gidan da zaita badani ga tsufin gari haka. Inba tace kidai bi sannu ke ma kin san idan uwarku ta kafe sai ya bayar dake ko bakya so hakan. Daga daki muna jin mama da yaran ta suna bidirin su cikin jin dadi har da shewan su. Don su burin su dama shine suga bakin cikin mu nida uwata a gidan ga kuma wani dama ya sake samuwa gare su again. Washegari koda na je gidan mama na kasa fada mata komai sai dai ta fahinci ina cikin yar damuwa a lokacin. Ta tambaye ni nai mata yake kawai da cewa ba komai mama don ba ko wani sirin gidan mune zan dinga fada mata ba din yanzu girma yazo min na san wasu abu ba kowane zaka fadawa ba. A kai sallama a kofan gidan mu lokacin baba ya fice zuwa kasuwa ba yara gida mama ta yafa ta fita. Malam Jatau ne a cikin wani tsohon babban rigan shi daya takure don tsufa ga dauda taf ga kayan sai tsohon hular dake kan shi don tsufa har zaren hullan ya fara zarewa daga jikin shi sai shafin dauda daya kwanta akai. Suka gaisa tana washe baki take cewa , a, a Alhaji Jatau ne sannu da zuwa . Ai kuwa ba kunya mama take cewa har an fara zuwa zance ne gashi maigidan ya fita amma ba matsala bari a kira ma yarinyar ai tunda ina nan. Ya washe bakin da duk goro ya bata shi yake cewa ikon Allah ashe kun san da zancen ke nan wallahi yabawa da halaiyar yarinyar don marigayi yana yaba hankalin ta. Hakan yasa nai kwadayin saka ta a cikin nawa iyalin ko banza na taimakawa shi marigayin ga nauyin da ya bari ai. Mama take cewa gaskiya ka kyauta muna sosai ga wanan jahadin don kaga dama yanzu auren ta sai mai dan hannu da shuni tunda ta saba da daula a can. Ya kara washe bakin shi yana dariya tare da fadin kada aji komai zan rike ta amana yadda shima ya rike ta a gidan shi. Mama ta wuce shi zuwa gidan mama Altine inda nake ina dakin mama na dan kwanta don ranan bamu aikin komai. Sai muryan mama Lauratu muke ji yana tashi tun kafin ta kawo kwanan shigowa cikin gidan. Rahama Rahama wai ina mara kunyar yarinyar nan ta shiga ne haka ana kira kamar bata ji. Daga inda nake kwance ina jinta sai mama Altine ce kecewa injin dai lafiya wanan kiran irin haka ? Cikin takaici take cewa ina wanan yarinyar take ne wai ana kira tana kyale mutane to ki fito ga bazawarin ki yazo gurin ki. Bazawari kuma mama Altine ta tambaya cikin mamaki tana kallon mama lauratun dake wani haki. Tace basu fada maki zancen malam Jatau na hayin dutse dake son auren ta bane ko may ? Takara cewa ai kinga matsalan su basu bar kowa ba a gurin kilibibi har dake uwar dakin nasu sai sun gwadawa halin su. Daidai lokacin na fito daga dakin mama ina mata kallon takaici nace. Mama ina tun ranan na fada maki ra, ayina akai ke ma may yan mata uku a daki da basu taba aure ba ai su gwada sa, an su sugani gareshi ko don naga sunfi dacewa dashi bani Rahama ba. Daga haka na shige daki abina na kwanta na barta nan waje tana sallami da zagina sai inda ta tsaya ta fita tana cewa Jatau din kyale jairan yarinyan nan sai an fito mata tabayan gida. Koshi Alhaji marigayin ai ba kasafai ya samay ta hakana ba sai da muka hada kai dashi komai yazo daidai gareshi. Kokai sai mun kai ga hakan in har kana son ta da gaskiya dole sai kayi wani abu don na shiga na fita a samo maka kan ta. Ya gyara tsugun ni shi yace to wo hakane abin yake to yanzu kina ganin kamar nawa zamu kashe ke nan.? Mama ta samu yadda take so takara dan matsowa kusa dashi ta kashe murya tana dan kuskus tare da shi cikin rada. Badon abinda yake muradin samu bane da babu yadda mama zata iya cin naira guda nashi daga aljihun shi komai dabaran shi kuwa. Nan dai sukai sallama da ita tai mashi alkawarin zata san yadda ta shiga tafita aka samu kaina a cikin sauki. Bayan fitan ta gidan mama Altine ne ta saka ni gaba da tambaya ina kuka ina sharan hawayen bakin ciki da takaicin dake cina ne ina fada mata kan maganan. Tace amma ko halin malam baiyi ba wallahi don dai wanan karon in har da adalci bai kamata yai maki haka ba. Abune dai na sunw iyayyen ki ban da iko akan ki da sun ga tsiya wanan karon. Kuma ai ba karya kika fada ma tana da yara dakin ta in har yarinya yake son aure ta bashi daya. Mama ko tana shiga gida sai zagin Jatau takeyi tana cewa kaga matsiyaci ko kudin share kasa wanan yana isa ne balle na wani aiki can a haka dai komai rowan ka sai naci abin ka ta wannan fannin. Baba na dawo wa gida ina jinta tana mayar mai da yadda mukayi da Jatau da ita. Daga can naji yana kirana babu tsoro ko kadan a raina na fito amsa mai kiran. Nan ya hauni da fada inda yake shiga banan yake shiga ba yana fadin ba zai lamunci ina wa mama rashin mutunci ba a gidan shi in har nace ban auren Jatau to nafito da wanda nake so yai min aure don shi ba ai mai dogon zawarci a gidan shi. Inna tana daki tana jin duk yadda muke kwasa da babana a tsakar gida na shigo daki ina kuka ina cewa ban san abinda naiwa baba da mata suka tsaneni ba haka ? Inna tace bake suka tsana ba yarinya nice suka tsana a gidan nan har ya shafe ki an riga an dasa mashi kiyayyan mu a ran shi tuntuni. Nace Inna irin wanan abinda baba yake min wani lokaci har tunane nakan yi nace anya kuwa shine mahaifina kuwa ? Tayi shiru ranta a bace yana mata suya da takaici cikin bacin rai tace dani idan bashi bane uban ki waye yarinya ? Tsaban rashin tsoron Allah da makoma ne dai ke damun su daga shi har ita din. Karasa wacce zaka dinga kuntatawa sai yar cikin ka ko yaushe ita yaya nata haukan kishine ya rufe mata ido take haka akan mu. Don kullun burinta shine taga bacin raina a gidan nan idan taga haka shine farin cikin ta a gidan nan. Ki dai yi hakkuri ko yaya yake mahaifin ki ne daga su har mu bamu isa muja da ikon Allah ba idan kuma Allah ya kaddara shima wanan din mijin ki ne babu tsimi babu dabara sai kin aure shi. Yanzu abinda nake so dake shine ki daina wanan rashin kunyan da kika dauko mata kici da yi mata biyayya a matsayin ta na uwa a gare ki don matar uban ki ce kullun ina fada maki haka. Ina zaune ina jin duk nasihan da Inna ta take min naso na daure amma kuma kukan da nake dan newa ya tsanan ta min zuciyana ya kasa daurewa ita kanta Inna ganin yadda nake kuka gwanin ban tausayi bata san sanda kukan ya kwabce mata ba. Can dau inna ta daure take ce min yarinya yanzu ba kuka ne abin yi ba gare mu dole ne musan mafita ga wanan zancen naki. Muryan baba ne mukaji yana cewa duk abinda zakuyi sai dai kuyi dana ai nasan kece mai daure mata gindi tanayiwa mutane iya shige a gidan nan. Inna tana jin haka tamike tafito daga dakin tana cewa ai dama nasan duk maganan yarinya idan ya taso akaina yake karewa a gidan nan don rashin adalcin da ba ai muna. Idan bani da ita ba wa ake wa wanan ikon haka a gidan nan ya kyale sai dai mu da aka raina muna kuran mu kawai. Baba ya dinga kallon Inna da mamaki yasan duk lokacin da ta va da ansa ga zance a gidan to abin yakai karo ke nan ba dadi. Ido kawai ya tsura mata ya kasa tabuka komai a kan ta sai muryan mama ne daga bayan su take cewa ai har da daurin gindin ka da suke samu suke ganin kamar wuyan su ya isa yaka yanzu a gidan In bashi har yau Rahama take da zatace wai ga zabinta bayan wanda kai mata don ta samu dauri daga uwarta ko ? ****** ********* ****** Da sassafe sai ga Larai kawar mama ta shigo gidan wurin mama lokacin Inna tana dama muna koko da zamu karya dashi don ina daki dun kule har lokacin bana jin dadin jikina. Da dariyan ta suka gaisa da mama take cewa a, a lauratu kice min kuma yar ki ta kara maku babban kamu ne agidan kuma ? Lalai kun iya jefa fatsa a ruwa ko yaushe sai manyan kifin garin kuke kamawa, yarinya ta zama ma uwarta jari a gari don ko shi wanan din kada ku bari ya sullube maku. Don nasan yo Allah na tuba ai kaman wancan din za, ayi tunda shima sai a hankali kinga kun kara samun wani gadon kuma ku haye ai. Da farko Inna taso tai banza da su da suka taba ita da mama sai kuma taga indan tai shiru ta kyale su sun sha da ita. Don ko gobe dawowa zatayi ta kara gasa mata wani don taci riban na farko din da tazo tayi. Inna ta dago kai inda suke ta dube su tana murmushi ace hakane fa kedai Larai. Kuma kin sab jahili shike gagawan yanke hukunci amma shi mai ilimi kullun yana kyautata zaton sa gurin ubangijin sa ne domin shine mai azurta bawan sa a duk lokacin da yaso hakan. Tunda fatsar mu ya iya kama babban kifi ko yaushe idan kamu banza ne wasu sukama koda karami ne mugani . Don ita killa wanan karon kifin da zata kama ba irinsa a wanan ruwan sai na gaba zata kamo. San nan ku sani shi sheri kare ne don mai shi yake bi hassada ga mai robo ko yaushe ai taki ne da ace ko wancan din ansan haka zai zama muna alheri da wasu sun kai nasu sunci. Amma daya abin rabone daga Allah sai sheri ya juye muna alheri a rayuwan mu. Sai gashi a filin Allah an dawo ana hassada akan mu kinga ko ai bamu ga kaico ga kamun manyan kifi don isa ne wani ko uwar ruwa yajefa fatsan shi ko kwai bazai kamo ba. Take suka hasala matuka gaba dayan su don sun fahinci inda maganan Inna ya dosa gare su don kowa na da manyan yan mata a dakin shi. Don idan baki yasan abin fadi baisan ansan da zai samo ba sai suke ji kamar Inna ta watsa masu ruwan zafi ne da safen nan. Nan suka kama masifa da kumfan baki gareta sai ashar da mugun kalamai suke watsowa ita dai inna ta shige daki abinta tana dariya. Bata san baba na gida ba sai muryan shi taji yana cewa haba haba Laira wanan ba girman ku bane kizo har gidan mutane kina masu shagube. Idan ma an kaiki gurin maigari baki da gaskiya anan din babu ruwanki cikin zancen kishin su. Nan suka juya kan baba da fadan suna fadin dama ai baka taba ganin laifin su kamar Asiya ce har zatai muna gori wai namu diyan ko samarin kirki basu dashi. Dama ai nasan duk munafunci ne kokai baka kaunan wanan zancen akan ta sai in yai dadi ne kake fin kowa cinyewa. Idan ma asirin su ne da suka iya yaka ma ka sai dai ya tsaya a kan ka don ni bazasu iya komai dani ba. Yace maza Larai ta fice mai a gidan shi tunda ba alheri ne ke kawo ta ba gidan sai hadin hasumi a tsakanin iyalin shi. Simi simi larai ta juya tabar gidan tana fadan karya inda tasan yana gidan lokacin da batai gigin shigowa ba lokacin. Tana fita ne baba ya juya gurin mama yana cewa ke kuma in kina kama girman ki ki kama don wanan ba halin arziki bane gareki. Mama dai sai faman haushi takeyi wai tana fada an mata gori ita da diyan ta a gidan. Indai don auren tsofin da nakeyi ne inna take ganin kamar wani fin diyan ta nayi su zuba haka zan kare rayuwana a wahalce gidan Jatau. Don duk yadda zatayi shige da fice sai tayi ko bama so sai na tafi gidan nan nai masu bauta su ma kamar yadda na saba yi a gidan garbati bakin ciki shi ya dade bai kashe Inna ba dani. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA DON NAUYI GARESHI YAR UWA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA DON GIRMAN ALLAH, , , , , , 15 Da taimako na muka kanmala aikin girkin rana da muka samu anty ta dora don muna cikin hira na mike don jin kaurin abinci danaji. Kofan danaga ta nufa dazun dauko muna abun sha na nufa sai dai ina shiga kaina ya daure yadda naga kayan girkin zamani ya cika kitchen din ta ko ina. Na rasa yaya zan duba abincin da naji yana nuna alaman ya dahu a lokacin. Gurin gas din na nufa da tsoron tabawa fal a zuciya na don ban taba amfani dashi ba sai dai cikin karfin hali na bude tukunyan dake saman wuta. Na samu abincin har ya tsotse na sauke sai dai ban iya kashewa ba ganin kayan miyan da tai blandinga cikin blander na juya na dora a wutan sai kamshi ne ya ziyarci hancin su a falo lokacin kuma suka fahinci bani falon tun dazun da sauri anty ta mike zuwa kitchen din ta samay ni a tsaye. Cikin mamaki take cewa dani Rama dama kin iya girki da gas ne ? Kaina girgiza mata tare dacewa yau ma na fara ganin shu ai, tace min kiyi a hankali nan take min bayani kan komai na kitchen din muna aiki a tare da ita har muka karasa tana gwada min komai sannu a hankali har na fara fahinta har muka gama aikin na zubo ma mama dani , mukaci mukasha muka koshi. Suna hira da mama nake fahintar akwai matsala a gidan nasu yadda naji tanawa mama bayanin komai dake faruwa. Na bu gidan da mamaki gashi da girma da kyau babu ne kawai babu a gidan amma wai zasu bar gidan bada dadewa ba. Ganin ina zaune a takure na kasa sake jikina yasa ta kallon inda nake tausayi nake bata matuka idan ta kalle ni yadda rayuwa yazo min ina yar karama da ni. Anty ke cewa na taso ta gwada min dakin da zamu zauna a part din ta nan na kwashi kayan mu na kai dakin sai da na tsaya na gyara shi tas na shiga nai wanka tare da yin sallah. Don a kauye na tashi amma ina da matukar tsabta sosai naki jinin ganin daki a ya mutse ko kadan. Kafin wani lokaci nai ma gidan kwal don dama gyara yake so bai samu ba ita gashi tayi tafiya sauran matan gidan kuma ba zama sukeyi ba a gida koma sun zauna basu iya gyara ko kadan don son jiki. Tun wanan ranan da na zo anty tasan ta rage matsala ta wanan fannin sai misalin biyar saura yaran gidan suka dawo daga makaranta su hudu na gani uku mata daya namiji. Na sheda yaran anty daga cikin su, don na sansu kwanaki da taje dasu ina gidan garbati. Biyun yan matan ne ban san su ba sai ranan na fara ganin su don haka nake kyautata zaton diyan maigidan ta ne su din, don akwai dan kama na jini tsakanin su da diyan anty din. Nan suka kewaye ta suna mata hiran makaranta sai can anty tace bakuga Grandma tazo ba da Anty Rahama. Gaba dayan su yaran suka juyo inda muke muna masu kallon sha,awa da namijin ne ya juya yana kokarin cire school bag din shi dake goye a bayan shi cikin rashin damuwa da abinda uwar tace mai. Duk da yara ne an koya masu gaisuwa sai yaran da ba nata bane suke muna wani irin kallon mamaki. Nasir baka gaida Anty Rama ba fa ya dan juye fuska a daure yace ina wuni ? Muka amsa mai a tare da mama lokaci daya sai dayan yarinyar ta dan kwanta gefen hannun kujerar da anty ke sama tace mummy are they going to stay with us ? Gaba daya yaran suka juyo suna son jin amsan da uwar tasu zata bayar a kaina maman tace dasu i think so, cikin jin dadi suka saka ihu lokaci daya suka samu waje suka zauna suna surutu. Kamar yadda nake wa kannena a gida idan sun dawo school zan sa su tube uniform din jikin su na kwasa na wanke na basu abinci kafin su wuce islamiya. Tsab na mike daga inda nake na ce da Amira oya Amira zo na cire maku uniform kuci abinci. Duk sukayo kaina suna rige rigen zuwa gare ni cikin jin dadi a tsakanin su, anty tai murmushi daga inda suke zaune da mama suna kallon mu tace dani ku shiga daga ciki dayan dakin kayan su yanan an kowa ta nuna maki nata aini kin ceceni yau wallahi. Komai na gama masu har abinci a sama sukace zasuci don haka can na hau dashi sukaci muka gyara gurin kamar basu bata ba. Cikin kwana biyun da nayi a gidan na dan fahinci abubuwan rayuwa na gidan yadda take gudanar dashi a tsarin ta. Kaman tashi da wuri da safe a girka abincin yan makaranta ai masu wanka a shirya su a hada masu abincin zuwa makaranta sai rakiya har bakin motan da zai kai su school. Haka yasa ta samu sauki sosai a dan zuwan da mukayi da nayi motsi kadan zata fara cewa wai Rama na nagode nagode kinji idan naji ta fadi hakan. Sai dai nayi murmushi nace kai haba anty wanan har wani aiki ne mai yawa ? Nikan a guri na ai wanan ba wani aiki bane don banga abin wahala ba a cikin sa amma ita sai take ganin babu taimakon da yakai wannan tunda gashi tana samun hutu da yin barci da safe wadattace yadda ake bukata a gareta. A kwana biyun da mukayi kawai shakuwa ne sosai ya shiga tsakanin yaran matan gidan dani sai Nasir ne har yanzu bai sake jikin shi dani. Sosai nake mayar da hankali ga taimakon rayuwan anty a gidan ko ina na gidan sai walkiya yakeyi don yana samun gyara. Idan yara sun tafi zan gyara falo har kitchen na dora abincin rana sai na koma part din anty na hada mata ruwan wanka na dan zauna da ita muna hira har ta mike ta shiga tai wanka sai nai saurin gyara mata dakin kafinta fito daga wanka na koma kitchen gurin girkin rana, kafin wani lokaci na gabatar masu da abincin rana ko. Kafin mu cika sati daya komai na kan gidan nasan yadda akeyin shi zan kuma yi mata shi tsab haka yasa suke samun hutu daga anty har mama sun dan canza a wanan lokacin. Duk wani abinda nasan bata so ko zai bata mata rai da yaran ta basu so, zan gujewa wanan abin . Na zomo mai kafa kafa a kan komai na gidan bana shiga shirgin dabai shafeni ba don ko yaushe ina busy ne. Ganin yadda yanayi na yake bana jin kiwar ko kyashin aiki komai idan ina yi, yawan shi bai damuna don ni a gare ni yar kauye tashin kauye har ina aikin yake anan bisa ga namu na kauye mai wahala sosai. Sai dai ita anty ko yaushe cikin yi min fada take wai na dinga hutawa sai dai nayi murmushi kawai idan ta fadi hakan mama kan ce ai gareta wanan ba aiki bane. Tana matukar bani kulawa ta bangaren ta sosai don tana nuna min kamar cikin mu daya da ita idan tana nuna min so. Yau ma zaune take falo ta mike kafa saman dan stol din katakon dake gefen kujera wanda ta jawo zuwa gaban ta, dauke da waya take hannun ta tanayi tsawon minti goma da fara wayan ta kamar ba kudi ake akashewa ba. Sai tv ke ta aiki shi kadai a falon don mama da suke zaune tare gyangyadi take yi lokacin a zaune ba kallo ba, ai dole mama tayi gyangyadi, taji sanyin AC na ratsa mata jini yanayi ya sauya sai barci duk inda ta zauna. Ferfeson kodan kaza zalla tace nai masu yaji kayan yaji don hadin kauye nai masu take kamshi ya gauraye ko ina na gidan . Na zuba mata shi mai yawa tare da dorawa ga ture da goran ruwa sai dai ba mai sanyi ba nazo gaban ta inda take waya na aje mata kayan abincin naji tunda safe tana cewa tana son cin bread da shi ferfesuf irin dai kwazaban mace mai ciki abinda, bai yuyuwa tace shi take so. Sai ganin na hado mata shi komai kamar yadda take muradin son cin shi kusan kwana biyu ke nan da take marmarincin hakan. Ta manta waya takeyi sai cewa tayi kai masha Allah Ramana Allah yai maki albarka duniya da lahira ya kare ki daga sherin masheran ta. Yanzu abinda nafi kusan wata ina son nayi na zauna naci kamar may shine daga kinji na fada kika hada min yadda nake so. Murmushi nayi ina gyara aje mata kayan abincin da kyau take cewa anya Ramana idan mutanen gidan nan suka dawo zasu gane ni kuwa wanan irin kulawa dana samu a yan kwanakin nan haka. Sai da taji dan murya cikin waya yasa ta tuna waya take tun farko abincin dana shigo mata dashi ya katse ta. Daga cikin waya ake tambayan ta wacece take zukawa albarka haka ne wai ? Tace bari kai dai heartbeat sister na da suka zo da mama ne ta hada komai na gidan nan ta hutar dani daga barci sai ci sai wanka sai ko kallo. Yace good da kyau amma ko na gode mata wallahi tayi min maganin ki tace wallahi kamar ka sani, kafin duk na gama barci na, zan samu komai is ready yarinya karama bata jin nauyin jikin ta ko kadan. Yace kai amma wanan yarinyar ta kyauta min wallahi ki min godiya gurin ta tunda ta kula min da bugun zuciya na. Dago kai tayi inda nake duke ina zuba mata ruwan miyan a plate tace Ramana kinji ana maki godiyan kula dani ko ? Murmushi kawai nai mata na fara kokarin zubawa mama nata na mika mata, lokacin kamshi ya tayar da mama dake zaune tana gyangyadi a saman kushin. Yaran da yake weekend ne na sauko dasu cikin hikima nazuba masu suka zauna ci don abinci bai damuwan su sai dai kayan kwadai kawai shine abincin su. Ganin Nasir yaki saukowa yasa na diban mai nashi zanje nakai mai murya anty ne dake shan ruwan miya da cibi take tambayana da cewa wanan na waye ? Cak na ja guri daya na tsaya tare da juyowa gare ta da hannuna dake dauke da kayan plate dana shirya. Nace anty na Nasir ne yana kwance bai taso ba shine zan kai mai nasa a dakin su. Tace cikin tabe baki Allah yasa ya karba waban yaron halinsa sai shi wallahi ya faye yawan bakin rai zakace bani na haife shi ba. Ni dai juyawa kawai nayi zuwa dakin koda na shiga dakin yana kwance rub da ciki da littafi a gaban shi yana rubutu a ciki. Abincin na aje na dawo gefen shi ta gaban shi na zauna na dan shafo kan shi nace Nasir tashi kaci abinci kaji rana yayi. Ban ci yace batare da ya dago kai ba nace haba Nasir ka tashi ko kadan ne kaci kaji kada mummy tai muna dariya dama tace min bazaka ci ba nace idan na baka zaka ci don ni abokiyar ka ne. Dago kai yayi ya kalleni sai ya duka yaci gaba da abinda yake a littafin, nace ni kasan duk cikin ku nafison ka don halinka na da kyau nasir baruwan ka da rigima. Kaga ko dole na soka na kuma damu dakai gaka yaro mai kirki da kai ko anty ma ta fada min kana da kirki sosai shiyasa take son ka ita da daddy. Sai ya sake dago kai ya kalle ni nace cikin daga kai hakane yace ba ai kazanta ba ga abincin ? Banyi magana ba sai bude mai plate din nayi kaman mai tunane sai naga ya mike zaune tare da jawo plate din a gaban shi ya dan diba kadan yakai a bakin shi sai ya fara danci a hankali amma hankalin shi na wurin littafin shi. Ruwan da nazo dashi na tsiyaya mai na mika mai ya karba ya dan yasha. Ina zaune tare dashi ban daga ba har sai da ya turo min plate din a gabana a raina nace kai lalai maganan Anty ne wanan yaron akwai miskilanci gare shi. Na mike tare da kwashe kayan nace dashi na gode Nasir ya bini da kallo har na fice. Ina fitowa da kayan zan kai kitchen ta bini da kallon tace ai na fada maki ba zaici ba daga inda nake tsaye nake cewa da ita yaci. Na shige da kayan sai dana wanke su komai da aka bata ina yi ina tuna kalamin Nasir watau kazan ta na cikin abinda bai so ke nan yaro dan kimanin shekara shidda wai yasan kazan ta haka. Sai da na gyara komai na fito daga kitchen din na nufi daki direct gurin kayan Nasir na nufa na gyara mai komai nashi tsab yanayi yana kallo na. Na fahinci rashin hayaniya hhalin yaron ne haka hallita ne mai haka Allah yayi shi amma ko ma maye a sannu zan gane komai nasa. Abincin dare na girka nagama da wuri na sa a kula ganin yaran na waje suna lesson yasa nace da Anty nima ina son zuwa na saurara. Anty tace kaman kin shiga raina dama ina son magana da lesson teacher din akan ki don nasan karatun kauye ba wani waya ta dauka kafin na fita tai mashi bayani a kaina. Cikin sati daya na fara fahinta da yake na dan san wasu abubuwa dama don haka ban sha wani wuya ba gurin fahintan karatun. Gashi dan zamana dasu na fahinci halin ko wani yaro ina kuma jan su a jiki sun sake dani sosai. Wanda hakan na fahinci yana matukar yiwa anty dadi a ranta niko a guri na naga ba komai ba ne hakan don tafi haka a gurina ni. Banda abin su na masu hali ni banga wani aiki da take yawan cewa yai min yawa ba amma gashi ita ko wani lokaci sai gode min takeyi. Sosai yaran suke sake jiki dani gashi har Nasir na dan fahinci halayen shi haka yasa yauma tun dawowan su na fahinci yaron bai jin dadin jikin shi amma ya kasa fadawa kowa sai kwanci yake yana mika. Mun dawo lesson nake cewa dashi Nasir bari na hada ma ruwa mai zafi ka gasa jikin ka dashi bai ce dani uffan ba har na hada ni da kaina nai mashi wanka na gasa shi da ruwa mai zafi na shirya shi har da robb na shafa mai na rufe shi da bargo. Na fahinci yaji dadin yadda nai mashi don naji ya sauke ajiyan zuciya dakin anty na nufa don karbo mai magani. Na tura kofan na shigo da sallama tana zaune saman gadon ta ta baje kanta babu dan kwali akai. Tana gani na take cewa dani cikin murmushi maman yara kin samu kanki ko kin gama komai. Nace eh anty yanzu ma nazo ne in da magani ki bani naba Nasir. May ya samay shi kuma nace ina ganin zazzabine ke dan satan shi amma ba wai ya fada min bane nan dai nai mata bayanin komai. Tace wanan yaron sai kinyi hakkuri halinsa sai shi wallahi don ni halinsa na rasa ina ya samo shi. Ta nuna min inda magani yake na miko mata tace Allah yasa yasha don miskili ne wallahi. Murmushi nayi nace haba anty ba kudai fahince shi bane amma yana da saukin kai ai idan abin shi a sannu. Tace ai yanzu kunfi kusa dashi Allah yasa dai ya sha maganin don bai son magani sam. Nashiga dakin na samu yana kwance yadda na barshi da farko na dafa goshin shi jikin ya dan yi sanyi a lokacin ya bude idanuwan shi yana kallona. Nace Nasir dina tashi ga magani ka sha kada jikin ya matsa ma sai naga ya ya mutsa fuskan shi nace ko na jika mane ? Sai ya gyada min kai alaman eh yana son haka na dawo da cup da ruwa a hannuna a gaban shi na jika na nasa spoon na juya na bashi sai ya karba yasha yana ya mutse fuskan shi na bashi ruwa yasha. Ina gyara mai kwanciya sai ga uwar tasu ta shigo dakin tana tambayan yasha ko akai shi asibiti yaga likita nace ya sha anty. Matsowa tayi ta zauna a bakin gadon da yake kwance sai take bin dakin da kallo komai na dakin tsab dashi. Tun dai gurin kayan Nasir komai a natse yake tace dani kai ashe ba karamin aiki kisha ba dakin nan ne haka Rama ? Nace kin san zama da kazanta ba kyau anty gashi yara ne sai anyi hakkuru ana gyara masu dakin nasu. Kakarin amai yaron keyi yasa hankalin mu ya koma gare shi kama shi nayi amma kafin na dago shi har ya bata min jiki da aman . Nan uwar ta haushi da fada tana cewa haba Nasir wanan sakaci ne ai zaka batawa Anty jiki da amai kuma ni ba batun kaina nake ba sai kokarin kamashi muka shiga bandaki yai amai sosai a ciki na gyara shi muka fito har lokacin tana zaune inda muka bar ta. Nace bari na canza mai zanin gado tace haba goge gurin kawai ya kwanta mana. Nace bari dai na canza mai tunda wanan din ya baci yaron cikin san murya da nuna fushi a fuskan shi yace kai mummy please go now. Tace cikin dariya dama abinda yake so ke nan shegen tsabta gare shi kaman ba karamin yaro ba. Sauran yaran ne suka shigo dakin suna cewa anty is time for prayer mun zo muyi sallah ne tare da ke nace tau ayi alwala. Tace masha Allahu ashe har jam,in sallah ake a dakin lalai an samu ci gaba. Suka ce anty ta fada muna cewa idan bamu sallah za, a kona mu ne wai da wuta. Tace gaskiya ta fada maku oya aje zuwa alwala kafin anty tazo nan suka shige bandaki kafin su fito na fitar masu da hijjab din su. Anty ke cewa idan mun koma wancan gidan zakuji dadin shi don yafi wanan girma sai dai aikin zai karune don haka nace a samo min wata yar dattijuwa mai dan dama don akwai dakuna da yawa sosai a kowani part gidan babbane kwarai. Nace cikin mamaki anty yakuma fi wanan girma da kuk ciki tace babban gidane sosai Rama sai in kin gani zaki sheda . Ba karamin kudi ya kashe ba gurin gina gidan don har ginan yaso ya taba mai aikin shi da kasuwan cin shi don mutane nata magana akai. Nace ashe harda babban gari akwai tsegumi kamar mu kauye tace inane babu gulma yanzu haka duniya ya koma fa. Ranan itama a dakin mu tai sallah tana kallo yadda muke sallah da yaran sai sun kalla sun ga abinda nayi zasu kwaikwaya suma suyi hakan. Muna gamawa taji mun fara karatu duk sun haye min jiki na amma haka muke karatun tai mamaki jin har mun kai kulhuwallahu da yaran don tare muke hadda dasu da baki. Abin yai matukar bata sha, a take cewa lalai munyi kure dole a samo malamin mai koyar da addini koda da dare ne sai yazo a dan taba. ****** ********* ****** Fitina yakai fita don Jatau ya saka mama da baba a gaba daya samu labarin bani garin. Haka magana har takai gidan maigari dole sai da aka kira mama taje da kanta. Nan dai ya koro bayani mama tai tsuru tsuru sai kamay kamay takeyi tarasa na cewa gashi babu kudi don har kudin sadakin ta kashe wai tayi sayayya dasu na aure. An basu sati biyu kacal su kawo mai kudin shi ko su dauki hukunci kan ta nan suka bar gurin kan wanan magana. Suna dawowa gida ta saka baba a gaba kan sai dai ya tafi birni yazo dani a daura aure akai ma jatau don bata san inda zata samo mai kudin shi ba cikin sati biyu. Yana gama sauraren ta yace amma kina da wani magana ni ina zanje cikin kano na dauko Rahama ? Altine ce tasan inda ta kaita kuma suna can tare ban san wanda zan tambaya inda suke ba yanzu don ba wanda yasan gidan yan uwan nata. Hankalin mama ya kara tashi sosai har gurin Inna ta taje cikin kwantar da murya take cewa a tsaya a fahinci juna kada abin yakai ga bacin rai. Inna tace rai shi ya dade baici ba ita ko kano bata taba zuwa ba balle ta ce tasan inda muke. Su dai da suka ci kudin shi sai su tafi can su karata dashi ita babu ruwan ta cikin wanan magana kuma daga yau su fitar da rai ga tinanen zasu hada ni aure da wani jatau a yanzu. Mama ta bar gidan cikin bacin rai take cewa yadda ba, a so sai ankai ga yin hakan Inna tace to bissimillah kuma tai mata kashedi akan zuwa gurin ta don babu hadin kifi da kaska yanzu. Haka ta dawo gids cikin tashin hankali ga kwanaki sai matsowa sukeyi tace idan baba ba zai je nemo mu ba ita zata shirya taje kano da kanta ai mai tambaya baya bata sai ta gano inda muke a kano ta dawo dani an mata aure. Yace bissimillah gaki ga hanya nidai banci komai na Jatau ba balle ya damay ni. Haka tashirya ita da Larai kawar ta suka tafi kano tun shigan su garin hankalin su ya fara tashi duk wanda suka gani a bakin tasha sai su tsayar dashi suce don Allah ko yasan wata Rahama tare da Altine mai kulli kulli. Wasu suyi masu daukan mahaukata wasu kuma su tsaya masu tambayan a wani unguwa sukace daku suke ? Basu sani ba sai a barsu a tafi sun koma kamar mahaukata suka dawo gida cikin dare hankali a tashe. Ko sannu baba bai mata ba shiya tayar mata da hankali ke nan ta haufada tana cewa munafuki dama ashe tare dashi aka hada baki don aga bayan ta ai tasan zaman ta dashi. Hankalinsu har baba ba, a kwance yake ba gashi gidan ya fara yi wa baba tsamin har ya fara kewan Innata a lokacin sai dai yana gundu yanuna yaji masifan mama. Har bakon da mama Altine ta aje gidan ta da iyalinshi sai da mama ta tayar mai da hankali tace yasan inda mama Altine take inba haka ba may zai sa ta aje shi gida bata sanshi ba. Nan sukayi tas da mutumin ya nuna mata yafita kwaya dole ta fita batun shi ta kyale shi don yace idan ta sake shigowa ta tayar mai da iyalin shi hankali kan abinda bai shafe shi ba sai yai mata tsinanen dukan da sai an kaita asibiti ta kwanta. Gidan Lairai taje neman shawara nan dai suka kasa kai mafita ga maganan sai larai ne ke cewa nifa ina ganin mafita daya ne a gareki yanzu shine ki daure ki bashi daya daga cikin yaran nan a zauna lafiya. Cikin mamaki mama tace wa kawar nata Larai yaushe kika fara hassada na a garin nan ban sani ba Jatau ne zan dauki yar cikina naba aure ko may ? Larai tace to may ye a hakan ba mafita muke nema ba ko kina da jakka dari da tamanin da zaki ba jatau ne kudin shi. Nu naga haka shine mafita kawai cikin wanan magana ki samu a zauna lafiya don kin san dai Jatau bai daukan kaddara shi. Aiko mama tai cikin Larai da masifa suka dinga tonon asiri a tsakanin su kaca kaca sukayi tabar gidan Larai a hasale kowa ya kama gaban shi daga ranan. Duk wanda yaga mama a lokacin yasan tana cikin tashin hankali sosai don ko ba, a fada ba duk ta ramay ta fita hayacin ta fa fitinan yaran ta da yai mata yawa. Don babu ragowa ko kadan tsakanin ta dasu sai cin mutunci kamar ba uwarsu ba. Ana cikin haka akace an kama Rukkaiya da mai nama a shagon shi suna lalata wanda dama ba ranan ne farkon yin haka ba a gare su. Nan wani sabon magana ya bi gari kwaaa ga kauye da iya daukan magana ko karami ne balle irin wanan. Da labari yaje wa Inna tace ita kan dai ta godewa Allah da yaraba ta salin alin da wanan fitinanen gida a wanan lokacin. Ranan komawan su gurin maigari yazo dole ba don taso ba ta hada dubu goma da kyat koshi sai da ta sayar da yan kaddarorin ta ta samay su. Bayan ta gabatar da kudin da tazo dasu ne aiko Jatau ya buga kasa yace bai san da haka ba shi kudi shi minamina yake so don ba zai dauki hasara ba baiga mata baiga kudin shi. An kai ruwa rana so sai a gurin dole aka bata zabi idan babu kudi a turasu kotun birni ko kuma ta samu mafita ta bashi kudin shi. Maiunguwa ne ya kebe da ita gefe ya bata shawara ta bashi yarta daya a wuce gurin don idan ta bari aka tafi kotu daure ta za, ayi can babu kuma may sanin inda aka kaita. Kuka ta saka ma maiunguwa tana cewa ya cece ta yai mata rai ita bazata iya ba Jatau yar ciki ta ba yadda yake din nan gashi kazami fa tsufa ga rowa da cin mutunci. Maiunguwa yace ni wanan shawaran shine nake gani kawai mafita a gurinki a wuce gurin don gujewa shigan ki gidan yari. Bata da zabi dole da wanan shawaran suka koma tabarman mai gari nan mai uguwa ya gabatar da shawaran da sukayi da ita. Baba dake zaune yace idan haka zai kashe maganan shima ya aminta da hakan . Aka tambayi Jatau idan ya yarda da hakan yace sai dai yayi maneji don dai shi ba cikin su yaso ba. Mama naji ta dago kai ta kalli Jatau mutum haka a kazance har yake kiran wai maneji zaiyi da yarta. Muryan mai gari taji yana tambayan su daga cikin diyan wacece zata bayar. Nan wani sabon tashin hankali yazo mata to ita wa zata bashi don duk yaran nata ba mutunci ne dasu ba ai. Babu wace zata fahince ta ta fitar da ita wanan kangin da take ciki cikin ruwan sanyi. Sai bude baki tayi tace kai kai Rahama Allah ya isa tsakani dake da uwar ki da kika jefa ni wanan halin haka. Maigari ya matsa mata tace a bashi Rukaiyya nan jatau yace wa shi Allah ya sauwaka mai yarinyar da ta zama ba gari dadi zai aura yagane may gurin ta. Ran mama ya kara baci tai cikin shi da masifa karshe dai da aka kai ruwa akai rana yace sai dai Lawisa dan dama dama zai laba da ita hakana. Haka a kawatse kan za a daura aure nan da sati daya ta tare dakin ta mama ta dawo gida cikin bacin rai ta isa gida har da suma sai da tayi hankalinta ya tashi baci ba sha ta shiga wani hali na tashin hankali. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA KI TUNA DA AMANA NE HAKAN A TSAKANIN MU , , , , 14 Ina duke a gurin naji an dafa ni mama altine ce a bayana take fadin taso daina kuka haka zo mu shiga gida wanan tonon asirin haka da may yai kamane wai ? Ban kiba namike na bita sai ga yara na shigo da kayan inna ta gidan buhu har uku duk na komatsen ta ta hada ciki. Ba a jima ba tashigo gidan ran ta abace sai dai kana ganin idon ta kasan ranan ba sauki sai na Allah. Nan mama ta shiga bata hakkuri akan ta zauna amma tace indai ba zai barni gidan shi itama may zata zauna yi a gidan. Dama don ni da kanne take zama badon wani abuba don haka bazata koma ba sai idan nima ya mayar dani gidan. Nan dai abu ya yamutse daddatawan unguwa duk sun taru suna ba baba na baki amma ya kyakyshe kasa yace bai san zancen ba tunda mama da tai jagoran ci muke son tozartawa. Magana zabban kunya yadda baba ke magana kai daji kasan an fi katfin shi. Shi dai jatau anbashi hakkuri akan cewa ya bari a sulhunta maganan nan da sati daya za, a nemay shi insha Allahu. Sai dare Inna ta nufi gidan su can taiwa mutanen gidan su bayani suka ce ta zauna suma halin gidan ya ishe su haka na. Magana har gurin maigari ya koma kan fitinan gidan mu aka kira babana aka bikon Innata amma yace shi ba zai tafi ba kuma zancen Rahama ya yafe ta cikin zurian shi. Ba, a watse gurin ba sai ga Jatau yazo kan zancen kudin shi yace yai lissafi har sadakin shi dubu sittin yaba mama din. Akace wa babana to kai kaji abinda ya fadi sai da baba ya share zufan dake karyo mashi yake cewa baida wanan labarin . Amma abari yaje gida ya tambayi mai dakin shi yadda akayi haka don shi dai bai san komai ba akai. Sadaki kawai ta nuna mai kuma suna hannun ta tace zataiwa yarinya sayaya da su ne ya bar mata a gurin ta . Nan yabar fada maimakon suji haushin shi sai tausaya mashi sukayi don sun san baida tacewa a gidan shi don mama tafi karfin shi. In bashi sadaki da maza ke karba ina mace ina karba sadaki hannun mijin yarta. Washe gari da aka sake tuntuban shi kan zancen Inna sai cewa yayi suje ya sauwaka mata . Wanan labarin yai matukar tayar muna da hankali sosai dayazo muna kowa na ma baba kaico da rabuwa da Inna dayi. Don yayi hasaran macen rufin asirin shi a duniya gashi tana haifa mai diya kyawawa masu tarbiya yace ta tafi da kanne na maza biyu duk ya yafe mata don mama tace bata rika su. Sabon tashin hankali na shirya ni da mama sai gidan su Inna ta a yadda nai tsanmanin na samay ta cikin damuwa sai naga sabanin haka don dan kwana biyun da tayi har ta dan murmure sosai abinta. Nan hankalina ya dan kwanta muka ba juna magana take ce min indai naga zaman bai min gurin mama na dawo nan na zauna tare da ita a gidan su. Nace inna banda matsala gurin mama ko kadan tabkar a furin ki nake zaune a gidan ta don haka zan zauna gurin ta kusa da babana watakila idan yana gani na ya sauko ga fushin shi a samu ku shirya dashi. Tace Allah sarki yarinya idan har kina hasashen komawa na wanan gidan to kina kaunan mutuwa na ke nan. May zai mayar dani gidan Audi kuma indai ba wani ikon Allah ba kuma ai na bar gidan shi har abada insha Allahu. Banji dadin hukuncin Inna ba nashiga damuwa take cewa dani na kwantar da hankalina gurin mama in Allah yakawo min manemin da hankalina ya kwanta dashi a daura min aure na nima na huta. Cabdijam ni zawarci uwata zawarci dawani ido mutanen gari zasu kalle ni dashi ace auren uwata ya mutu akaina ko may. Cikin tashin hankalin da na wuni ke nan a gidan su innata ina lalashinta ko zata sauko in baba ya huce ya aiko bikon ta ta koma dakin ta amma fir inna tace badai ita ba kan. Haka na dawo gida da dare gidan mama ban gane komai ba a gurin Inna sai hakkuri da kwantar min da hankali da tayi. Ina shigowa gida na samu mama tana waya ga alwal mai wayan sadawa tsaye kofan gida uana jiran tagama abashi kudin shi ya tafi. Ko ban tambaya ba nasan da yarta take waya a lokacin don yadda naji suna magana na fahinci hakan. Don naji tana cewa yanzu haka ma rikicin auren ta ake a gari don uban ta ya kara jajibo mata wani tsohon wai ta aura har kai tashin hankalin daya sauwaka wa uwarta tabar gidan nasu. Banji may tace ba sai cewa tayi abani waya naji mama tana ce min karbi wayan anty ki ce daga birni ke magana dake. Nakarba muka gaisa da inta take ce min ashe abinda ya faru ke nan Ramana ? Sai na sa kuka take cewa nayi shiru na saurareta zata dawo wani sati in Allah ya yarda da tadawo zata turo a dauki mama sai mu taho tare da mama na huta da kauyen nan idan ba a ganni ba aibabu mai saka ido a kaina kuma. Nan dai tai ta bani magana har na gamsu da maganan ta mukai sallama muka awal wayan shi da kudin shi yatafi yana godiya. Mama tace min kin dawo a lalace na amsa mata tare da neman guri na zauna ina cewa ehmama. Tace ga abincin ki can dauko kici nace da ita mama na koshi kunu kawai nake son na dan sha na kwanta. Ina cire kayan jikina ne naji mama nace kinji abinda yar uwar ki ta fada ko akan ki. Nace naji mama amma ai al, amarin babane da wuya don nasan mama bazata bari ba idan taji tace nima hasashen da na keyi ke nan Allah dai ya haushe mu kan ta. Mun bar zancen don ko inna ta ban fadawa maganan ba kada hankalin ta ya tashi sai in abin ya tabbata zataji. ****** ********* ****** Bai fadawa kowa dawowan su kasar ba bayan sun gama ganin likita haka ita ma yace bai son ta bugawa kowa waya zasu dawo. Taja bakin ta tai shiru bata fada ga ranan da zasu dawo ba gidan har suka shigo b Nageria ba wanda yasan da zuwan su. Karfe goma sha biyun rana suka sauka gida kano ya daukan masu shatan taxi din airport sai gida. Alama ya nuna matan gidan basu gida a lokacin duk da weekend ne ranan hutu don motocin su baya gida. A can kan hawa step din gidan ne ya hango Nasir a zaune yayi tagumi sai Amira dake tsaye bayan dan uwan nata tana wasa tsaletsalle akan steps. Tun hango yaran ya sauke ajiyan zuciya yaran basu damu da tsayawan mota ba a haraban gidan nasu sai harkan gaban su sukeyi kawai. Muryan mahaifiyar su ne sukaji tace Sweethearts da sauri yaran suka yo kan su cikin murna da jin dadi nan ta durkusa tare da rungumay su zuwa jikin ta sai kuma ta sake kuka. Ya gama sallaman mai taxes yazo inda suke shima suka rungumay shi cikin murna yake tambayan su ina anty ta tafi yaran sukace tun safe bata tare da mu sunfita da yasmin a mota. Ciki suka shige da kayan su wanka ta fara yiwa yaran tare da canza masu kayan jikin su tabasu abinci sukaci don sunce yunwa suke ji a lokacin. Har tagama abinda takeyi bata ga shigowan shi ba gurin su haka yasa ta tsamani ko ya kwanta ne a lokacin don ya huta. Dakin shi ta nufa don taga halin da yake ciki zaune ta samay shi a saman kujera yayi tagumi da hannayen shi biyu ta hayan rike haban shi dasu. Sallaman ta yasa shi dago kai yana kallon ta yake cewa har kinyi wanka kin dai ci abinci ko ? Tace munci nida yara kaine dai naga baka zo kaci ba shine na biyo ka nagani ko ka kwanta ne ? Yace No banci ba kuma banjin ci din . Haba dai saboda my kuma heartbeat kai dake da gajiya tare da kai ka tashi kai wanka kaci wani abin ko ? Yace zan dai yi wankan amma bazan iya cin komai ba gaskiya yanzu sai zuwa anjima . Wankan yayi duk tana zaune tana jiran shi har yafito ya shirya suna dan hira jefi jefi sai dai bai sako mata zancen matan gidan ba itama batai mashi ba tafice daga dakin nashi ta koma gurin yaran ta. Har goma da rabi na dare sai lokacin ne Zulfa ta dawo gidan da yarta daka gansu kasan a gajiye suke tafe lokacin. Wutan falon dake a kashe take kokarin kunnawa a lokacin don akwai dan duhu gurin haske wutan waje ne ke shigowa kawai. Tana kunna wuta sai ganinin shi tayi zaune a falon ya harde kafafuwan shi yana kallon ta yace kashe min wuta ki wuce ciki bayan ya gama kallon wayan hannun shi don diba time. Simi simi ta shige part din ta hankalin ta a tashe don tasan bata kyauta ba bata rike mai amanan da ya barmata ba na yaran shi. Bayan yai bugun gaban ita yar uwar shice tajini yabar mata yaran shi amana suka tafi ganin likita da matan shi a Uk. Shadaya da dan kai sai ga hindu ta parker itama alokacin kamar yadda zulfa tayi hakane tana fada tana cewa don iskanci sai abi wutan ma akashe don sallon mutum ya fadi yaji ciwo ke nan. Gashi a zaune fuska a daure yasa ta cewa dear saukan yaushe babu ko waya a shirya ma dawowan ka. Ido kawai ya tsura mata tare da kallon agogon bangon dake manne a falon . Itama agigon ta kalla cikin firgici yace miko min baby nan ki koma inda kika fito. Tace kamar yaya nakoma inda nafito kuma gida fa na fito yace will you do as i said ? Babu sauki a fuskan shi ta bude baki zata ce dear kayi hakk, , , , ya dakatar da ita cikin daga hannu yace please tun raina bai baci ba nai maki abinda baki zata ba ki aje min ya ta kibar gidan ? Ganin ba wasa yasa tai mai yadda yace yarinyar dake barci a kafadan shi ta aje mai a saman kujera ta dan juta sai kuma taja ta tsaya ya nuna mata hanya da hannu dole tasa kai tafice gidan. Gidan su ta nufa shi kuma yasa maigadin shi ya rufe mai get kada ya fara ya budewa koma waye yazo da daren nan. Yace angama ranka ya dade kamar yadda kace haka za, ayi ban bude gidan nan sai gobe da safe. Yana shiga dakin Hindatu ya nufa ya samu tana tsaye tagama saka rigan barcin ta a jiki tana shirin kwantawa. Daga kofa ya tsaya tana ganin shi ta mayar da hankalinta gare shi yake cewa da ita abinda yasa ke bazance kibar gidan nan yanzu ba kamar yadda naiwa Hindu shine koda kin bar nan nasan gidan Daddy zaki nufa da nan da gidan daddy duk daya ne a gare ki don haka gobe karfe takwas na safe ki tabbatar da kin bar gidan nan baki alaikum. Hankalin ta ya tashi tana shirin mashi magana ya fice dakin nata ran shi a bace ya koma part din shi ya kwanta. Haka suka kwana rayukan su a bace ranan kowa da abinda yake ji a ranshi sai Sa, ade ne tai barci a tsakayin yaran ta hankali kwance cikin jin dadi. Kafin ya kwanta sai da ya shigo dakin nasu ya samu sunyi barci ga wuta a kunne basu kashe ba ya kashe masu yafice daga dakin . Washe gari haka ta tashi ta gyara yaran tare da abin karyan wasu duk lokacin bata san matan gidan basu gidan ba ma ita. A zaton ta ko wace na dakin ta kwance ne don halin su ne hakan ta koma ta kwanta don agajiye take. Hayaniyan da take ji yai yawa a falo yasa ta fitowa dakin ta sai gani sarakan ta tayi a zaune suna magana sai dai babu maigidan cikin su ga Hindu a gefe zaune cikin damuwa. Hajiya ce ta kalle ta a lala ce tace a, a matar iko matar mulki matar so anga daman fitowa ke nan. Hajiya ban ji shigowan ku bane gidan ina barci yanzu naji magana nafito nagani. Bashi na tambaye ki ba ai duk abinda kukayi don kanku ke dashi in cin amana abin yine sai ku matsa kuyi tayi ni dai na fada maki in ma wani abin kukai mashi don ku rabani dashi Allah yafi ku ke da iyayyen ki. Murmushi tayi tare da fadin ayi hakkuri hajiya kamar kullun maganan ta ke nan tsakanin ta da uwar mijin nata. Shi mijin naki ance ya bar garin ko da yake yasan abinda ya shuka na rashin gaskiya. Tace ya tafi nw ko ? Hajiya tace rufe min baki mara gaskiya kawai ai bakin ku daya dashi. Bayan kun tafi shakatawan ku kun bar yarinya da dawainiyar yara kuma zaku dawo ku saka mata da sheri. Ai duk inda yaje zai dawo ne ya samay ni gidan ba inda zai gudu min ko ? Ke kuma koma ki zauna dakinki har ya dawo muji hujjan shi na maki wanan danyen hukuncin haka. Don yana dan wullakanci yabi wayoyin shi ya kashe don kada a samay shi balle ai mashi magana ko ? Hindatu tace yanzu maigadi da zamu shigo ya bani wanan takardan inji shi yace abani. Hajiya da yar uwanta gurin hada baki suke cewa takardan may ? Tace a, a cewa yayi kada na fara na zauna mai a gida har sai ya dawo in ba haka ba a bakin aure na. Salati suka saka hajiya tace lalai yaron nan ya kai dan rainin wayo na gaske yar uwarta tace yaya tunda ya furta haka kada ta zauna tazo mu koma tun abu bai lalace ba. Hajiya tace babu inda zata zama zatayi inda ya dawo in ya isa ya sake ta mu gani. Hajiya ai wanan maganan dayayi a matsayin sakin yake in har ta zauna maigida aure ya kare a tsakanin su ke nan. Inda Sa, ade take ta kalla tana cewa tsohuwar banza kawai kin samu yara kina masu wayo yadda kike so. Shiyasa tun farko ban so wanan bakin auren naku ba don ke sam ba sa, an auren shi bane. Fin karfi na kawai akayi amma wanan da nake gani da wuya in bata girmi dogon sarki ba Hajiya mu tafi tunda baya gari har ya dawo sai asan abinyi don yanzu bata lokacin muke a hanka don ba komai zamu gane gurin wanan ba in ma mun tsaya. Haka suka fita suka bar gidan suna sababi inda suke shiga ba nan suke fita ba akan zagin Saade. Suna fita takai zaune tare da dafe cikin ta da taji yana mata motsi take cewa haba heartbeat yaya zakai min haka ashe yasan abinda ya shuka ke nan yace na shirya yaran su tafi makaranta idan sun dawo kuma anan zasu zauna tare dani. kanta girgiza kanta cikin takaici may yasa ko yaushe yake abinda zai ja min zagi ga mahaifiyan shi ne bayan yasan irin zaman da nake gidan da hajiya. Maigadi ne ya shigo ya katse mata tunanen ta lamban waya ya bata yace inji maigidan wai yabata idan ta tashi barci. Gurin maigadi take ji wai iyayyen hindatu ma sunzo neman shi ya bata takardan da yace a bata kamar yadda yaba Zulfa na ta. Layin shi ta kira ya dauka ba bata lokaci zai fara magana ta tare shi tana cewa heartbeat may yasa ko yaushe kake jawo min abin zagi ga yan uwanka da iyayyen matan ka ne ? Yace ke ki saurare ni kada ki fara kiba kowa nomban wayan nan idan bani nace ba tace kai kana ina ne yanzu ? Yace yanzu na sauka Abuja zan wuce office ke nan ki kula da shan maganin ki a kai kafin na dawo don da na dawo zamu tare sabon gidan mu da yardan Allah. Allah ya kai mu tace yace kada ki manta da zancen zuwan mama na kauye da kikace zata zo ta zauna dake sai ki tura Hamza driver idan yakai yara gobe yaje yazo da ita. Sukai sallama ya barta da mamaki don yaki bari ko suyi wani magana sa ya shafi zancen matan shi da ya tura gidajen su. Suna gama wayan ta kira Awal mai waya ya sada ta da mama din lokacin ina zaune na saka lalle a kafana naji sallaman shi kofan mu. Ya kawo wa mama waya sukai magana kan gobe driver zaizo ya dauke su don haka su shirya da wuri kafin yazo. Mama tace tun ranan da mukai magana dake mu a shirye muke take cewa kiba mahaifin Rahama dubu ashirin hakama mahaifiyar ta dubu ashiri hamza driver zaizo dasu insha Allahu. Suna gama wayan awal ya karbi kudin shi ya tafi mama ke cewa dani kumshinki yazo a sa, a gobe ne tafiyan mu in Allah ya yarda. Zanje na samu mahaifinki muyu magana dashi inji ta bakin shi akan tafiyan ki in ya yarda sai mu tafi idan kuma yaki yarda sai ki koma can wajen Innan ki har lokacin da na dawo. Tunda ta kafe bazata dawo gidan ku ba har abada tabar gidan ke nan , Allah dai yai mata sauyi da mafi alherin sa. A sanyaye na amsa da amin badon naso don dai kawai addua ce ta alheri tai mata. Da yamma da baba ya dawo kafin ya shiga gida cikin hikima mama Altine ta samay shi a waje da zancen don zancen bai yuyuwa a cikin gida don mama lauratu. Bayan sun gaisa sama sama dashi don haushi mama yake ji da ta barni gidan ta duk da gidan dan uwan shi ne amma yana jin takaicin haka don yaso tabarni na bi uwata can mukarata gidan su. Mama acikin hikima takw mai magana tace to Audi dama zancen wanan yar ne Rahama dake gurina. Don gobe zan tafi birni ganin diyata kuma zan kwana biyu shine nake son zuwa da ita don kaga babu kowa a gida idan ka yarda da hakan. Yace Altine na fada maki ba yau ba ki rabani da zancen yarinyar nan a rayuwana na riga na gama magana akan Rahama. Ba kano ba duk inda zata ita dade bata tafi ba babu ruwana a cikin harkan ta na fada maki ko. To shike nan tunda haka kace mu Allah ya bamu ikon rike maka ita amana kamar yadda ka bar muna ita din. Yace indai wanan irin tsiyane ai kice nace maki watarana akan ta mama tace ba amin ba tunda mun gama maganan ta ko dakai. Ta banye kudi a haban zanin ta tana mika mai kallon kudin yake a cikin mamaki yake cewa na maye wanan din tace dama yar tawa ce tace a baka kayi hakkuri dashi ba yawa. Sai da ya dan juya yana kallon kofan shiga gidan shi baiga kowa ba yai sauri ya karba yana fadin an gode ya shige gida har yai dan nisa mama ta juya zata shiga gida taji yace ki dai ja mata kunne ta kula da rayuwan ta a can Allah ya tsare tace amin nagode da karamancin da kai min. Da tashigo ne take fada min yadda sukayi da baba nake cewa Allah sarki baba abin nashi akwai daure kai a ciki wallahi yana son iyalin shi amma tace ta raba shi dasu da karfi da yaji. Mama tace ba abinda ya bani dariya sai waigen da yakeyi kada angan shi yana karban kudi yasan idan ta gani yau basu kwana aljihun shi. Da dare muka tafi sallaman inna ta nan mama tai mata bayanin komai mama tace wa inna ta ina rokon ki Asiya ki bari yadda mahaifinta ya bari ta tafi ke ma kibarta Allah kuma yasa hakan shine Alheri ga rayuwan ta. Don ni zaman ta gurin Saade zaifiye min zamata a kauyen nan ko bazan ta kara sanin duniya. Inna tace ni na isa in hanaki yadda kike so da yarinya tsakanin mu dake sai fatan alheri da neman gamawa da duniya lafiya. Allah yasa yarinyar nan gurin ta na karatun da take son yi ya cika ta wanan hanya. Mama tace zata barni mu dan gana na kwana a gurin ta don sai zuwa gobe da rana zamu tafi in Allah ya yarda taima mama godiya takawo sakin Inna rabata tana godiya. Bayan tafiyan mama inna sai faman nasiha take min na kama kaina na zama ya ta gari abin alfahari ga kowa nan gaba don wata rana sai labari. Naji matukar dadin nasihan Innata ga albarkan da take ta saka min yafi a kirga Kwana nayi ina tunanen yaya rayuwana zai kasance a gurin anty Saade ko baba zai yarda ya barni nakai ga samun cikan burina a rayuwa. Da safe na shirya zan tafi gida gurin mama inna takawo adduoi tabani tace na fake na kula da yin su ko yaushe don suna da falala da faida nai godiya naiwa kakannina sallama nafice gidan tare da jaddawa Innata zancen karatun kanne na kada a bari ya dakata masu. Shiko baba sai da zai bar gida ne washe gari yake fadawa mama cewa kinji wai Altine zata birni da yarinyar nan. Wani uban ashar ta lailayo ta watsa ma mama Altine tana cewa munafuka makira dama ta fahinci duk itace mai hura muna kunne akan halin da muka tsira yanzu ni da uwata . Da sauri tace kai may kace mata kan magan tafiyan da ita ? Yace may zance da ita banda Allah yakai lafiya idan na barta nan din wani abu zatai min ban da karin bakin cikin da zata jefani ciki kawai. Jin haka tace malam kakoyi tunane kafin ka bada bakin tafiya da ita birni tana nan ma bamu inmata ba balle rashiga birni idon ta ya bude ai watarana ma sai tace bakaine ubanta ba don raini. Don haka wanan magana ajeye shi babu zancen tafiya gare ta ba inda zata tafi tana nan cikin mu dadi da wuya haka zata zauna garin nan. Yace yanzu kan sai anjima in na dawo nai mata bayani don na makara kada mota ya wuce ni na rasa. Abinda ita dashi basu sani ba yaune tafiyan mu zuwa burni sai dai baba ya dawo ya samu labarin tafiyan mu kawai gurin jama, an unguwa. Komai na amfani mama ta dauka takai makwabtan ta boyo kayana dake gidan ta tasa an kwashe ankaiwa inna ta gurin su. Haka yasa na fahinci tafiyan namu mai dadewa ne don ban taba ganin haka ba wani bako ta dauko da matarshi da suke yawon neman gida tace ya zauna a dayan dakin dake gidan da iyalin shi. Sha biyu da rabi na Rana hamza driver na kofan gidan mama ba bata lokaci muka kama hanya. Da zamu shiga mota yara sun fadawa mama lauratu sunga motan birni kofan gidan mama Altine sai gata tafito daidai mun fito zamu shiga mota. Nan ta buga kasa tana fafin ba inda mama zata dani don ubana ya hana tafiya dani mama tace da ita kin makara don ni ubanta ya riga ya sallama min ita kamar yadda kika bukaci yai masu ita da uwarta to tun jiya mun gama magana dashi ko. Nan taje har da tare gaban mota ta baje hannayen ta wai sai taga yadda za, a tafi dani birni. Tana jin hamza driver yasa giyan mota tsoro ya kamata ta ruga da gudu gefe tana Allah ya isa tsakanina dake mai kuli kuli. ****** ********* ****** Mota na tashi nabi kauyen mu da kallo hawaye na zubo min a idona una tuna rabuwana da mahaifiyata da yan uwan haihuwana. Biyu da rabi shaf muna cikin garin Kano ta Dabo jalla babban hausa yaro koda may kazo anfi ka . Sai bin garin nake da kallon mamakin ikon Allah gine gine kamar ba mutane ne sukayi shi ba da hannuwan su. Abin hawa tun ina girgawa har bakina da zuciyana suka daina aiki sai binsu da kallo kawai nakeyi. Mutacan mu wuce nan driver na ta aikin tukin shi sai ga mu wani katon unguwa mai gine ginen zamani kala kala. Muryan mama ce ke cewa dani ikon Allah Rahama yau gaki birni a kanon dabo tunbin giwa yaro ko da may kazo anfika. Nace mama harda maita da sata sunfi kowa tace yarinyar sawasa kin ganki mayan ka. Nace aiko har na koma gida bazan taba fitowa waje ba balle a sace ni tace ce Allah kin tuba fita kan ai sai randa babu rai kuma. Wani irin katon gida ne naga driver ya karya kwana ya shiga damu yai horn maigadi ya wagale kofan muka shige. Daidai lokacin ne na sauke wani irin ajiyan zuciya mai karfi mama tace barka da arziki yar nan Allah ya rabaki da rigiman uwarki lauratu da masifan jatau kin huta. Mun fito da yan kayan mu dake cikin ghana most go don sai dana cika jakata da tufafina masu kyau tsufin nabarwa Inna ta su a gida. Anty tana zaune a mamakeken falon su kafata harde a cikin daya ga remote din tv rike a hannun ta tana jin sallama mu ta mayar da hankalinta gare mu. Tana fadin lale marhabin da Ramana yau gani ga Ramana a gidana Allah nagode maka daka nuna min wanan ranan gare ni. Da gudu na naje na rugumay ta naji tace waisshi Allah yi a hankali anty taki rubabace na dago kai nace wayo sannu anty ta dafa min kai tana cewa Sannu Ramana sannun ku da zuwa. Dukawa nayi da kaina sai hawaye shar tace da sauri subbahanallahi ko baki son zuwa ne aka rabo ki da gida ? Sai lokacin ne ta dago kai tana cewa sannu mama mama take cewa ai dole na tsaya har ku gama shirmayn ku ko. Wani bata son zuwa shirmay ta daine wai taji dadin ganin ki ke nan take wanan kukan haka. Nan muka zauna a falo tare da ita tace bari ta dauko muna abinsha kafin abinci ya sauka. Mama tace ina yan aikin naki kuma keda baki jin dadi tace cikin murmushi wai mama yaushe rabo ai duk an watsa su saboda fitinan matan gidan nan. Gulma yai yawa ga fitina yaki ci yaki karewa dole aka sallami kowa daga mu sai halin mu yanzu a gidan. Mama tace naji gidan shiru ina sauran yan uwan zaman ki da maigidan kuma murmushi tayi ta mike da kyat zuwa kitchen sai gata da kayan sanyi da sauri na mike naje na karbo mata kayan na kawo gaban mama na dire su. Sanyi lemon ya hanani sha Anty ta kalle ni tace kisha mana Rama nace sanyi anty sai ya huce zan sha suka sa min dariya ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KI RIKE AMANA DON AMANA NAUYI GARE SHI YAR UWA DON ALLAH MU KULA PLEASE, , , 17 Zan iya cewa tun dawowan matan gidan har zuwa yau kwana biyu ke nan da cewa sun dawo gidan amma banji duriyan su ba har wanan lokacin Ni dai a bangaren mu zan iya yiwa anty na aikin komai da duk wani abinda yaka mata na kula dashi. Sauran matan gidan sai mamaki sukeyi yadda suka samu yaran su ga kuma gidan a gyare tsab kamar yadda da farkon shigowan su gida . Kafin zaman gidan nasu ya canza kala, don ko wace daga cikin su tana ji da kanta bata iya gyara gida in general sai dai ta gyara daidai part din ta kawai ba ruwan su da sauran part din gidan haka zai dauki lokaci a cikin datti. A da suna da mai aiki har mutum biyu da tsohuwa da yar matashiyar budurwa sai ya kasance gulma yai yawa kowan su na kokarin jaye mai aiki ta koma katkashin shi haka ya kawo fitina mai karfi har ya kai maigidan ya sallami duk yan aikin ya ce. Yau da safe anty ne ta shigo dakin mu ina zaune ina gyara kayan yara ina ganin ta na gyara zamana da kyau tare da gaishe ta don nasan ba kasafai take shigowa dakin ba, dakin da muke ni da yaran nata. Bayan na gama gayar da ita ne ta samu guri a bakin gadon Nasir ta zauna tana cewa na fa gane kunfi dasawa da Nasir gidan nan Rama. Murmushi nayi mata kawai nace anty ai shi na daban ne a gurina yana bukatan a ja shi a jiki sosai. Baki ta tabe tana cewa wanan ai halinsa sai shi don baida yadda sam wallahi ina mamaki ma yadda ya amince dake haka da sauri. Tace cikin dan sake, tsaki tare da cewa dama nazo ne naga idan baki aiki ki shirya ki rakani wani gurin don fitan ma dole ne zanyi shi, su Amira ya damay ni na je ni tun jiya yake damuna na akan maganan. Ban bata lokaci ba gurin shiryawa don anty dama da shirinta tazo dakin namu don mu tafi a lokacin. Mun nufo kofan fita daga gidan na hango wata mace shigowa daga ciki kai tsaye yadda nagan ta tafe yasa na fahinci watace daga gidan don yadda take tafe a gadarance. A karo na farko da na fara saka daya daga cikin matan gidan a idona ke nan tun bayan dawowan su gidan daga yajin da suka sha. Wace nagani doguwa ce yar fara ba can ba tana shigowa gidan sabale da gyalen ta a kafadan ta tana kada yan makullaiyan motar ta a hannnun ta. Waya take a cikin sakin fuska amma tana hango mu take annurin fuskan ta ya gushe mata ta hade rai a lokaci guda. Tana ganin mu ta wani bata fuska tare da kawar da kai gefe daya ta nufo mu gadan gadan babu alaman kauce muna gare ta. Hakan yasa naga anty ta dan kauce gefe daya gudun kada su hade su buge junan su. Kai tsaye kamar ban ma san da ita a tafe ba saida kafada na da nata ya gogi juna ko gezau ban yi ba itace ma naga ta dan yi kamar zata tangada don buguwan da junan da mukayi. Kam kaza tace tare da juyawa tana fadin, ke wata irin bagidajiyar ina ne wai kina tafe kamar dabba dake baki iya kaucewa mutane ? Kamar ba dani take magana ba don ban juya inda take tsaye ba a lokacin. Don idan na tsaya zan gwada mata ni yar tallah ce a kauye a baya don bani shayin uban kowa inda ta ganni. Kada na tsaya bata amsa na batawa anty farin cikin ta yasa na dake na wuce ban bata amsa ba don da taji amsa daga bakina sosai. Motan anty muka shiga batare da tace dani komai ba din ban ma yi zaton taga abinda ya faru a tsakani na da hindatu kishiyar ta din ba a lokacin. Tafiya mu kadan yi mai dan nisa kadan daga uguwar su sai gamu a wani irin katon gida mai wani irin wawakeken get mai girma. Horn tayi har sau biyu sai ga wani mutum daga ciki ya bude kofan ta danna kan motar muka shiga daga ciki. Abinda idona ya gane min ban san lokacin dana sauke ajiyan zuciya ba har sai da anty ta dan juyo inda nake tana murmushi Wani guri na hango an tara motoci har kusan hudu sai sheki suke suna walkiya kamar an tara dawakai kosassu a gurin. Ta juyo inda nake tace dani bisimillah ko Ramana fito mu shiga daga ciki mu duba ban tsaya ba kamar yadda ta fita nima haka na fita daga motan. Ko kasan gidan ma abin kallo ne a lokacin don ko ina yaji grass carpet a gurin kore shar da shi gwanin ban sha,awa. Direct wani kofa muka nufa sai gamu a wani katon fili da ya raba sassan gidan kashi biyu ga wani katon part a tsakiya dake nuni hawan bene ne gurin. A hankali muke tafe muka fara shiga side din dake left hand din gidan part biyu ne manya kowani dauke da bed room uku uku a cikin shi mayan an saka gadaje da kujeru baban daban sai muka fito zuwa sashen dayan sai naga ai kamar kayan shi yafi haduwa har dakunan gurin kamar sun dan fi girma sosai part din gaskiya ya hadu. Muka dawo wani katon falo da yasha gyara sosai a gidan da gani shine main falo na gidan na kowa da kowa banda wanda ke cikin ko wani part. Anan muka zauna don ta huta saboda ta gaji sosai a lokacin sai da ta dan huta take cewa dani Ramana yanzu zabi ya saura akan mu cikin gidajen nan biyu da muka shiga wani kike gani zamu zaba a matsayin namu a ciki. Cikin mamaki nake cewa Anty wanab ne sabon gidan naku da zaku tare a cikin sa ?. Cikin sakin fuska take cewa dani shine Rama baban su Amira ne ya matsa min sai nazo na zaba kuma kin san may? Wai fa yau din nan yake so mu tare a gidan nan don haka wani kike gani zamu dauka a matsayin namu shiyan ni daku da yara. Don yace su biyu a dayan part din zasu zauna kowace dana ta ai kin ga ba mai ganin wani a tsakani yanzu kowa yaci gashin kan shi kawai ne. Ta kara tambayana na rasa ma wani zan zaba daga cikine wai farat nake cewa da ita ni sai nake ganin kamar wanan na ka shen da muka shiga yafi haduwa ai anty don haka shine zamu zaba. Tace ashe tunanen mu yazo daya dake Rama don nima ya burgeni gaskiya sosai gashi da girma ga shi komai nashi purple ne da milk colour . Bamu jima ba take cewa mu koma mu fara shiri don haka muka juya zuwa gida . Kamar yadda mijin ya umurce ta tayi hakan tayi don bamu kwashi wasu kaya ba masu yawa muka koma gidan ranan laraba da dare don girman gidan duk a daki daya muka kwana gaba dayan mun cikin shiyan da ta zaba a matsayin nata a gidan. ****** ************ ****** Sai washe gari sauran mutanen gidan suka tare don ina ganin basu san da zuwan mu ba a daren jiya sai washe gari ne suka ga ana kwasan kayan anty ga wa yanda taba ma kyau cikin yan uwanta marasa karfi. Suke tambayan mijin yake cewa dasu ai ya fada masu cewa kowa ya koma can tun two days ago. Suna zuwa suka saka balai wai basu yarda da part din da anty ta zaba ba wai sun zabe shi a matsayin nasu tun farko da suka gane shi. Mijin nasu ya nuna masu basu isa ba don basu zasu fara zaben guri ba sai anty dake matsayin babba a gare su a gidan. Hakan bai masu ba sai da zulfa ta daga waya takira hajiyan shi tana kuka take sheda mata wai ana yawan take masu gakkin su a gidan nan don ko yanzu da suka dawo sabon gidan su gurin da ta zaba da farko nan Saade ta shige da yaranta. Ran hajiya mama mahaifiyar maigidan nasu yai matukar baci ta shiga fada tana neman layin dan nata don taji ba, a sin maganan daga bakin shi. Can ta lalabo lamban shi da kyat don balain da take kan yi yana dauka yaji ta haushi da masifa tana fadin wai mai sunan Alhaji may kake son mayar da kankane wai. Mace daya figaga da ita ta hanaka samun sukuni da iyalen ka ta hana ka shakat don son kai irin nata. Yanzu har wanan gidan ma da kuka koma sai da tai maka iko irin nata data saba don ita bakin hali irin nasa na gado da suka saba. Yadda take takaman ita matarka ce haka su ma suke a matsayin matan ka ba wai finsu tayi ba Shi bai kashe wayan ba shi kuma bai bata amsaba don ya san koma ya mata bayani ba sauraren shi zata yi ba. Suka kashe wayan ya ci gaba da harkokin shi don a lokacin baya gida yana gidan gonan shi. Washe gari muna part din mu duk muna falon anty din bamu faye zama a dayan part din da tace shine zamu zauna ni dayaran ba amma kayan mu yana ciki sai dai mu dan shiga mu fito mun fi zama a gurin ta. Babu sallama sai ganin an fado muna kawai mukayi a shiya anty da ke kwance ga cikin ta da yai girma ya tana shirin shiga watan ta na haihuwa tai zubur ta mike tana yan kamay kamay tare da fadin hajiya sannu da zuwa. Dakata ke ta bata amsa ba gaisuwan ki nazo nema ba zuwa nayi don inji dalilin ki na saurin daukan wanan part dina matsayin naki? Shiko ke kina ganin cewa su sauran ba mata bane sai ke kadai ce macen auren a gidan nan don kina takama kinfi har mijin naku shekaru zaki iya mai wayo yadda kika saba. Anty dai tana duke yayin da mama Altine dake ballan goro ta dakata tana sauraren hajiyan. Idan ba kaddara ba ke har yaushe Alhaji karami zai auro sa, auroki a matsayin matar shi ya aje a gida haka tsofai tsofai da ke. Baba inda yaran nan zasu tafi suna gidan nan daram kamar yadda baki so shigowan su gidan ba sai ki ta zama ke kadai a dole kin samu gida kin mike kafa daga ke sai diyan ki a gida. Ni dai ban san yaya akayi ba ko maganan matar ne yai min yawa a zuciya ta yadda take faman aibanta min Anty na. Sai ji sukayi nace kai amma dai wasu girma kawai sukafi mutum ba wayo ba. Duk babban da bai gyara tsakanin maurata ba baikamata kuma ya bata ba har mutum ya zauna ya na aibanta macen aure wai dama yin haka shine wayewa ? Ni na dauka ai duk abinda dan ka ya dauko yazama naka tundai ga uwaye mata . Abin danka naka ne ba bambanci tsakanin matan shi sai dai kai babba ka hada hankalin iyalin danka ka nuna ma babba matsayin shi haka shima karami yasan matsayin shi shine girma. A ko wani gida wanda aka san tarbiya da mutunci ansan uwargida itace kan gida dole itace mai fara zaban abu kafin na baya su zaba. Kamata yayi uwa ta godewa Allah idan ya bata dan da yasan shimfida adalci a tsakanin iyalin shi bai kauce wa addini. Amma wanan magana ba girman ki bane da darahan ki ba hajiya ace kina zuwa gurin matan dan ki kina raba daya biyu a tsakanin su don suna karkashin ki kawai kema fa uwa ce hajiya tunda nasan kina da diys don haka, , Tau ke kuma fa karamar mara kunya daga ina haka ke kuma wacece a gidan nan da dan tsugunin ki zaki tsaya ki dubi fuska na kina fada min magana ba kunya ba tsoron Allah. Nace hajiya ba haka bane ni naga ke uwace a gurin mu ba girman ki bane da mutuncin ki yadda kike hajiya ace aji wanan irin kalamin na aibanta matar dan ki daga bakin ki. Mutuncinki da kimarki yafi karfin aji haka a gare ki koda ace tsohuwar ce yake aure ai bai dace ba ke aji daga bakin ki kina aibanta abinda yake mallakan danki ne kuma abinda yake so. Cabdi Sa,ade a ina kiia debo wanan fitsararar yarinyar haka mara mutunci mara kunya da ita ? Wai ma waya baki ikon aje ta a cikin gidan nan ne har take ganin ta samu guri da kamar wanan yar zata kalli tsaban idona tana fada min maganan da wani mahuluki bai taba tsayawa a gabana ya fadi ba. Anty saade na fadin hajiya yi hakkuri yarinyar ce shiyasa , Hajiya sannu da zuwa mukaji ance daga bayan mu ashe maigidan ne tunda nake magana da hajiya yana tsaye a kofan daki. Ya karaso yana fadin hajiya kaunan Saade ne tazo kuma kinga abinda nakewa gudu ke nan a koda yaushe idan kina fadin magana na aibanta Sa,ade kada ya fada a kunnen yan uwan ta. Gashi kuma yau karamar yarinya tana mayar maki da martanin maganan ki na kullun akan saaden. Ke nan ran ka bai baci ba ga abinda tai min ba ke nan a gaban ka yace hajiya ai wanan maganan ku ne na mata ni bai shafe ni ba. Yanzu ma nazo fitane naga motan ki a waje shine yasa nasan kina gidan na biyo ki nan don nasan kina nanan din. Tace eh ina nan din don nazo ne kan zancen shiyan da ta mamaye na yan uwan ta. Mu hadu a falo a hajiya nan akwai mutane a gurin sai muyi magana a tsanake. Ba taki ba suka kwasa zuwa falo gaba dayan su har anty sa,ade din tabi bayan su don jin may za, a fada a falon. Zaune suke kallo daya zakai masu ka fahinci kowan su a falon a cike yake a lokacin. Cikin fushi hajiyan ta ke magana tana cewa ka taramu ka barmu a zaune ko kuma wani sabon wulkancin ne yin hakan. A fusace ya ke don daya dago fuskan shi gaba dayan su sai da hankalin su ya tashi don ganin yanayinsa. Sai da yakai kamar minti uku kamar yana nazarin wani abu can yace ina son na fara da tambaya anan ? Don Allah ko a cikin ku gurin nan akwai wanda yasan yadda na samu aiki har na kai ga tara abinda ke gare ni a yanzu har nai wanan ginan da muka shigo. Shiru sukayi gaba dayan su ba wanda yai magana sai hajiya ce can tai karfin halin cewa . Don bamu san yadda ka samu ba shine zai hana mu yin magana idan kayi rashin adalci ko may ? Yace hajiya may ye rashin adalci anan don na bawa uwargidana zabi akan girman da Allah ya bata a gidana. Nakuma bata zabi amatsayin ta wacce ta taimaka ma rayuwana tun ban san ko mai ba na hanyan neman kudi har yakai ta fara lurar dani yadda zan zamo mai dogaro da kaina har zuwa wanan lokacin. A fusace hajiyan shi, take cewa kace ma da kudin ta ka zama haka a yau. A gadarance yace kusan hakane gaskiya don kudin ta da nawa ne muka hada nasai form na sai sauran abubuwan da ya sace nayi kafin na samu na kai ga appointment dina. A lokacin hajiya ke kin sani Abba bai yarda da zancen aikin da nake nema ba yafi da son na kama kasuwanci kawai. Ashe don haka hajiya yau komay nai ma sa,adatu kaman ma ban mata komai bane daga cikin gudun mawan da tai min a rayuwana. Don haka yau hajiya a gaban ki ina son kowacen su ta sani cewa Sa, ade da suke gani ba abin da zanyi wasa ko sakaci da ita bane arayuwa na. Don haka wace zata iya zama dani da mata ta zauna don a tare kuka gan mu da ita auren mu va zai sa na watsar da mata na mai tausayina mai sona da kauna na wace ta san zafina da tausayawa rayuwana. Hajiya ta cabe da cewa ai ka karasa kace wace ta haife ka ta san zafin cikin ka da goyon ka. Aa hajiya bata kai can ba amma dai ina son su fahinci darajan ta a guri na yafi karfin yadda suke tsanmani a yanzu don naga suna son su wuce limite din su agidan nan. Duk wace bata iya zama a gurin da na ajeta hanya a bude yake gareta zata iya komawa inda tafito don babu dole a gareta. Matata dai ce ba zan taba wullakanta taba akan ko wacen su insha Allahu. Kuma ina son ku sani hajiya da kuke kai karana kona matana a gare ta ga hajiya ga ku duk wace ta kara kai karan dayan mu gurin hajiya a gidan nan kan al,amarin da ya shafe ni ko Sa,ade. Mace ta sani kuma ta rike a kanta zan bata mamaki kwarai ga irin matakin da zan dauka akan ko wacece a gidan. Haka ya isa please ban san may kuke so dani ba kowacen ku nan tasan zamana da matana tun farko haka kuma kuka amince da zaku iya zama damu a hakan da muke ban auro ku don na wulakanta matana ba don ina son abina kowan ku kuma ta sab da hakan ta amice don haka yanzu kune kma kuke son bi ta hanyan mahaifiyana don ku cuta mata kuma cutawa mahaifiya don Alhakin yarinyar mutane ya haukan magaifiyana. Saboda may zakuyi muna wana mugun sakkaiyan hakan kuna amfani da mahaifa na don ganin an cutatawa yar mutane saboda hakkurin ta. Kada kuyi tsanmani ban san abubuwan dake gudana a gidan nan ba na bar kowa tana abinda ta ga dama a gidana. Akwai watarana yaba tafe ranan da zan dauki mataki daidai da laifin kowan ku amma dai ina mai kara ja maku kune ga abu biyu zuwa uku. Na farko shine mai son zaman lafiya ya bar hadani da matata da iyayye na fada. Sai kuma ina gargadin ku da ku daina shiga harkan Sa,ade ku barta taji da lalurar da Allah ya jarrabe ta da shi. Don haka zance shiya da kuke cewa ta zaba ta bar maku wanda bakwa so zaku iya komawa can dakunan ku da kuka fito don yau idan Sa, ade tace min bata bukatan zama da kowacen ku a cikin gidan nan ya ya tabbata hakan a gare ni. Aiko na hajiyan shi ta amshe da cewa tau issahe akan wanan figagan matar naka mutu kwakwai rai kwakwai kake wanan magana. May yarinyar nan tai maka hakane har idon ka da zuciyar ka ya rufe yau a gabana kake wanan magana. Lalai Sa,adatu kin gwada min ki kai kin kai matakin daba naki ba a gidan nan tunda har yau Alhaji karami ya rufe idon shi a gabana yake wanan magana haka. Hajiya ya kamata ki sani yau idan haka ya kasance a gidajen auren yan uwan mu mata ba zaki ji dadi haka ba, muma ba zamuji dadi ba don may hajiya ba zaki daina wanan halin ba ko don kwanciyan hankalin diyan ki mata dake gidan mazajen su suna aure. Au to lalai abin har yakai zakaiwa yan uwanka mata baki akan matar son ka duk ka haukace min yau don na taba ko. Ai kafin kayi naka, naga wata fitsararar yarinyar da matar ka ta dauko ta aje a gidan don isa da mallaka ra fara nuna min fitsara don samun wuri. Ta juya gurin antyna tana cewa ban son ganin wanan yarinyar a gidan nan ta gagawan barin gidan nan tun ban dauki mataki ba a kan ta ? Hajiya wanan yarinyar yar uwar Saade ce nina bada bakin ta dauko ta nan don ta samu mai taimaka mata ga halin da take ciki tana bukatan taimako ? Kafin suci gaba da magana sai ga maigidan ta ya kirata yana tambayan ta tana inane wai.? Ta kasa bashi amsa don tasan ya hanata zuwa gidan dan nata saboda wanan halin da take zuwa tayi. Kwata kwata bata kaunan zaman Sa,ade da danta don acewan ta kullun wai ta girmay wa mijin nata shi yasa take masu wayo. Ta manta cewa itama tana da diya mata dake aure a wanu gidan har su uku bata tunanen cewa abinda take wa yar mutane zai iya faruwa akan diyan ta. Mata bamu tunanen cewa mu uwaye ne masu diya duk abinda ka shuka shine kake girma a rayuwan ka. Muryan mijin nata ne ke fada mata cewa tazo gida ga Aisha, yar su ta dawo gida da matsala. Wanan maganan da taji ne yasa ta dafe kirjin ta tana cewa zata tafi amma zata dawo don bata karasa maganan da ya kawo ta ba. ****** ********* ****** ****** Tun da farar safiya muryan Jatau ne ya tayar da mutanen gidan da balain da yazo masu. Yake cewa mama tafito bazai yarda ba tasan yarta honko ne ta dauka takai mashi gidan shi don an raina shi. Shi za, aiwa wullakanci ko may da za, a dauko honkon akawo maigida don an mai dashi tsoho. Gaban mama ne yai mugun faduwa haka ta daure tafito zani na faduwa mata gashi har mutane sun fara taruwa don gulma. Tace a ranta bari ta rufe ido tai mai na mahaukaci kawai a wuce gurin gaba daya. Ta na lekowa take cewa kai Jatau kada ka dauka ko tsoron ka ake ji duk haukan da kakeyi kyaleka na keyi. Mata kace kana so mata kuma na baka banga dalilin da zaka taso tsofai tsofai dakai ba kazo muna kana wanan magana abin kunya. Tace ankai maka honko din sai ka turo min yata yau din nan na fasa auren bazata zauna ba a gidan ka. Da Jatau yaga mama ta fishi iskanci da hauka dole ya kwantar da nashi haukan yace baki da hurimin daukan min mata, don mata zamana take yanzu. Matar ka da kace honko ce ai daga yau ta gama zama dakai a gidan ka don dama kudin bazawara ka biya bana budurwa ba. Yace a shekeke yo ina budurwan take anan kin kai min hinkon diyar ki aiko sai ga su Rukaiyya sun fito daga cikin gida. Mama ta juya garesu tana cewa maza kuje kuzo min da Lawisa gidan nan yanzun nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANI NA BARKI DA NAUYIN AMANA A KAN KI YAR UWA 18 Anty na barin falon ta dawo part din ta samay mu zaune inda ta bar mu ganin yanayin mu kawai zai sa kagane rayukan mu a bace yake dagani har mama Altine a lokacin. A kasa nake zaune kusa da dima diman kujerun dake a falon ta samu kujeran dake daf dani ta zauna . Sai bayan ta zaunane ta dafa ni a hankali tare da ambatan sunana ta riko min hannuwa na ta hade da nata guri daya. Jin ta ambaci sunana da irin rikon da taimin yasa na mayar da hankalina gare ta tare da kura mata ido ina sauraren ta. Rama ina son ki kwantar da hankalinki ki dinga nazarin kowa na gidan da idon basira. Kamar yadda kiia san duk wani gida mai iyali akwai irin kalubalin da gidan ke fuskan ta hakane ma ko a wanan gidan namu. Don gaba daya matan gidan da iyayyen gidan kalubalin su akaina yake wanda ba komai ne yakawo haka ba sai ganin Allah ya dorani kan mijina da kuma su baki daya a gidan. Wanda ba komai ya kawo min shi ba sai hakkurina da kuma halaiyana na gari yasa na cin ma wanan falalan haka. Rama ina so daga yau ki kasance mai hakkuri ga al, amarin gidan nan don zaki ji ko kiga abubuwa da dama na cin fuska a gamay dani amma dole sai kin daure ki kawar da kan ki ga hakan. Babu inda zaki muna nan tare da ke har lokacin da Allah zai nufa ki kara yin wani aure idan Allah ya yarda. Don haka kada ki jefa kanki cikin fitina da rigigimun gidan nan a kaina. Nasan dazu ranki ya baci yadda hajiya bata ji nauyi idon ku ba a matsayin ku na yan uwana tana tozarta ni a gaban ku yadda taso ta saba da yi min hakan ne tun farkon aurena da danta. Amma duk wanan ni bai taba damuna don dai nasan Allah kadai yakai ya rabani da heart beat ba wai wani mahaluki ba. Nan dai taita min nasiha mai tsuma zuciya akan rayuwa har naji gaba daya ma zaman duniya ba dadi a cikin sa. Washe gari kafin wani lokaci na gama gyaran ko ina inda ya dace a gyara sai na dora girki guri ya kaure da kamshi. Ina gamawa na shiga nai wanka na saka daya daga cikin dogayen rigunan da aka sayo min na gyara na fito tsab dani. Na dade a gaban mirro ina kallon yadda halintan jikina ya nuna min sura na a wanan lokacin. Gaba daya dan lokaci guda na sauya nayi matukar kyawo na zama wata young fresh dani . Dakin Anty na nufa don na tambaye ta ko zata ci abinci dana gama dafawa a lokacin. Zaune na samay ta a saman sallaya da alama ta idar da sallah ne a lokacin . Jin shigowana da yasa ta dan mayar da hankalinta ga kofan ido ta tsura min har na karaso inda take zaune durkusawa nayi daidai inda take zaune ina gaida da ita. A daidai lokacin da ta shafa ta dago kai tana min murmushi take cewa dani dama yanzu nake son kiranki don zamu dan fita zuwa unguwa sai dai ba mai nisa bane . Na sharada zamu tafi gidan sister din maigidan ta haihu yau kwana hudu ke nan. Sai da na tabbatar da ta gama magana nake cewa Allah ya raya tare da cewa dama nazo na fada maki na gama abinci ko zakici yanzu ? Tace da hakan nayi zaifi min don ina dan jin yunwa dama kin ga sai na fita da nauyi. Dama fitan nawa kamar fitan dole zanyi shi kin san alamarin dangin miji yadda yake rashin zuwa zai iya jawo min matsala. Kallon ta nayi ta bani tausayi ga cikin ta ya girma kwarai a lokacin gashi tana matukar karfin hali sosai a lokacin. Abincin na kawo mata ta zauna nan inda take zaune a kasa taci sai dai ba sosai ba don yanayin ta ba dadi gare ta. Na tace mu fasa fita sai zuwa gobe idan ta dan kara jin sauki amma sai gashi ina idar da Sallah ta shigo inda muke tana ce min na zo mu tafi mu samu mu dawo in time. Da sauri na mike tare da dan gyara fuskana na saka hijjab a jikina sai naga anty taja ta tsaya tana kallona wani irin. Nima dai din kallonn ta nake don ban san wanan kallon da take min ba sai na ga tayi murmushi ta nufo ni tare da daukan gyalen rigan dake jikina tana mika min take cewa haba ko dai ni macen aure ai kinga shigan dake jikina ko. Dole ba don naso ba na cire hijjab din na yafa gyalen kayan a kaina na fito kamar wata yar birni dani don ni kaina nasan na canza sosai. Tana gaba ina biye da ita a bayan ta rike da hand bag din ta muna fitowa haraban gidan ne mukai kicibis da maigidan wanda da alama dawowan shi ke nan daga wani guri a lokacin. Yana ganin ta ya dan ja ya yatsaya tare da jingina jikin shi a jikin motar daya fito daga ciki. Jikin shi na saye da wani yadin maza mai laushe da daukan ido fari kal zaka iya gano yar farar singlet din ke ta cikin jikin shi Da sauri na basu guri zuwa gurin motan da nake tunane itace motar ta da muka taba fita da ita. Volvo ce yafito daga ciki ban san yaya akayi ina can tsaye dan nesa kadan dasu na kurawa kasa ido ina faman tunanen yadda in mota tashigo kauyen mu zamu dinga binta har zuwa kofan gidan da mai shi zai tsaya. Sai muryan tane ya katse na dago da sauri ina kallon inda suke tsaye gaba dayan su shi da ita sun tsura min ido inda nake tsaye ina tunane. Tace zo a wanan zamu tafi , zaifi muna saukin tafiya ai da sauri na dago na nufo inda suke tsaye yana kokarin jayewa ya bata guri ta shiga motan ne nake cewa cikin yar murya ina wuni. Kamar baijini ba don bai amsa min ba sai kokari yake yaga matar shi ta zauna da kyau a cikin motan yana fadin don Alkah ki ja sannu ban son gudu ko sauri tace ina naga lafiyan gudu yanzu heart beat. Tace zagayo ki zauna mu tafi da sauri na kara na shiga motan da ta bude min dayan gefen na shiga. Ina jin tana mashi horn a inda yake tsaye hannayen shi harde cikin dan uwa yana kallon yadda take jan motan. Daga inda nake na dan saci kallon su naga yadda suke nunawa juna tsatsan kauna zalla tsakanin su. Wani kamshi da sayin ne suka ziyarci hanci na da jikina a lokaci guda wanda ban san lokacin da na sake sanyayan ajiyan zuciya ba don yanayin da naji. Tace yaya dai Rama na naga tun dazu sai faman tunane kike yi may ke faruwa ne wai ? Idanuwa na lunshe tare da sake dan murmushi nake cewa anty sauyin rayuwa ne kawai nake tunane da ina kauye yaushe zan taba wanan sabon rayuwan da nake ciki. Murmushi tayi tare dayiwa wata mota da naji tai mata horn ita ta mayar masu da horm din tana cewa ya dauka ko maigidan ne da kan sa a ciki . Yanzu ke har kin ganki a wani rayuwa ke nan Rama naji ta tambaye ni ta sake wancan maganan da take na motar da ta wuce gaban mu. Nace anty idan da nayi auren gidan Jatau ai da ko jaki sai nayi shekara ban gani don ba fita ake a gidan shi ba. Dariya anty tasa tace kai ai da jin sunan shi kasan mutanen dauri ne ba na yanzu ba wai Jatau. Wani gida ta tsaya tana horn aka bude mata gidan ta danna kan motar ta zuwa cikin gidan. Kishiryata zulfa ce tsaye da wata suka kuro muna idon su har muka kawo inda suke basu daina kallin mu ba suna son ganin ko maigidan ne a motar. Can ta fito daga ciki sai naga sun kawar da kan su ga kallon su basu dade ba naga Zulfa ta juya tana kokarin shiga motar ta. Muna kawowa wace suke tare tsaye bata da niyya muna magana naji Anty na cewa Samira yaya yau ? A, a uwargida yau kece da kanki a motar oga wani kaya sai amali ke nan ? Murmushi anty tayi mata muka sa kai zuwa cikin gidan gidan ya kaure da hayani zaka fahinci akwai mutane a gidan. Wani daki muka nufa inda nake zaton nan ne dakin matar gidan da muka zo gayarwa din. Da sallama muka sa kai a dakin yayin da matan dake dakin suka kuro muna ido su. Matar suna da matukar kama da mijin anty sosai dagani basai anfada ma ba don jini yana aiki sosai. Tun ba su gaisa ba take cewa a, a matar mulki an samu fitowa ke nan dai ai na dauka mulkin ba zai barki zuwa ganin baby ba ai. Tace ai kin san ko don nazo naga dana zan zo ai na duba ku ko ? Tace nasani ai ba don ni kika zo gidan nan ba don yaushe rabon da kizo gidan nan Sa, ade ? Zama anty tayi daga gefen gadon da kyat ta zauna tare da maida numfashin ta. Nan ta fara gaisawa da matan dake dakin ina tsaye daga gefe kofan ina kare ma matan birni kallo. Can ta hangoni tsaye take cewa Rama zo nan mana ki zauna sai lokacin na karasa kusa da ita maijegon ke cewa zo nan ki zauna ga guri kinji donnke kawai zan tara. Anty tace ai duk daya idan kin tari kaunana akai dariya suna kokarin mika mata baby dake nade a cikin showel fari tas dashi. Bata jima rike dashi ba ta miko min shi gani da son yara nan na karbe shi na rugumay ina karewa taron kallo cikin sha,awa. Sai fira suke kwasa tsakanin su inajin suna mata ba,a wai ashe ta tsofe ne haka ? Maijegon nace masu ai kunsan ta da wayo taki bari kannen ta su samu sai ita ce mai daukewa. Anty tace wanan kuma a tambaye ku don kune masu sawa ai bani ba inma rowa ne kukai masu rowa abin. Aka kwashe da dariya maijegon ke cewa yanzu ko kishiyar ki ta bar nan har da gulman ki mukayi ai. Anty tai dariya tace shine aikin ku ai dangin miji yanzu nazo shine nima zakuyi nata dani ko ? Kai ai Zulfa yar uwa tace tace ni kuma yar uwar mijin ki ba kinga ma falo zan koma nasamu Nura muyi zumuncin mu. Sai lokacin na fahinci mijin mai haihuwan dan uwan anty ne ke nan ita kuma matar yar uwan mijin ta. Maijegon take cewa ai dama kuna zumuncin ne sai na damu dake dashi duk abu daya ne ba zumuncin. Waya fada maki lokacin da muke zumutan mu a waya fada maki zaiyi ne ? Saade baki da dama fa yanzu sabon gidan da kowa ke murnan shiga shine kika karbe masu part din da yafi kyau. Kai ni saade na shiga uku wata sabuwa kuma ke nan yanzu wai mayye banbancin wanan part din da nasu Aisha ? Su shi suke so ai, anty tace nikuma shi mijina ya zaba min na zauna ciki sai yaya kw nan. Sai lokacin wata daga cikin mata ukun da muka samu tai magana tace kaji gaskiya haka nake son namijin da yasan kan shi a samu tare a mutu tare. Anty tace kin san su matan yanzu su samay ka da mijinka suce sun fika iyawa ne in bashi ba gidan dai ai duk gidan ne ko ? Maijegon tace barsu kawai indai bros ne karamin aikin shine ya mayar dasu tsihon gidan idan sun matsa ai na fada masu gaskiya, don kowan su sai cika take tana batsewa . Ji min fa don Allah ijin matar dake zaune tace wai da may suke nufi don kina ta ffarko su amare sai ya fifita su ke nan ko? Aini yaya yai min daidai wallahi don bai daukan raini ga kan shi da matar shi ba don haka na da wa yan nan da kike gani ko mu yan uwan shi sai munyi da gaske mu shiga gidan shi. Yanzu dai kuka fada ai da bakin ku inji anty saade tana dariya Maijego tace ni hajiya na rasa may yasa take son saka kanta cikin irin wanan magana ranan naje gida baba ya kirata ina jin suna case din dashi akan maganan. Anty ce ta kawar da zancen dacewa yauwa fatima dama ina son ganin ki wallahi don wanan kaunan tawa nake son tayi joining din school din ku. Matar da ta kira da fatima tai saurin kallona tace har ta gama secondry ne wanan din ? Tagama almost two years ke nan yanzu masha Allahu inji matar tace karama da ita haka ? Tace yanzu zan mata kokari tasamu matric ta jona sai tayi jam idan lokaci yayi mugani. Nan dai sukai ta magana yadda za, ayi kan karatuna ina sauraren su duk dadi ya kamani cikin raina tace wa matar zata turo da komai nawa a kawo mata insha Allahu. Bamu jima ba mukai masu sallama anty ta ciro kudi mai yawa ta dora saman gefen showel din da baby ke ciki tace asaya mai pant dashi. Muna tafe ba wanda yai magana sai zuwa can take cewa zan tura ki da hamza gobe ai browsing din takardan ki mu gani sai ai amfani dashi. Wani shago ta tsayar da mota muka shiga abubuwan amfanin mu da babu a gida ta saya masu yawa ina kallon yadda ake komai har biya muka dawo gida . A falo muka zube mun samu yara sun dawo daga schools lokacin nan muka shiririce dasu don sunyo kaina muna hira na cire masu uniform din su na saka masu kayan gida na basu abincin su . Shi Nasir nasan halin shi don haka na koma kusa dashi ina da yake na zauna yana ci muna dan hira har na samu ya dan ci abincin nasa. Duk abinda mukeyi anty tana kallon mu a fakaice tana yabawa da irin hikimar da nake wa yaran wanda ko ita uwar su bata da lokacin masu hakan da nake masu. Suna gamawa muka fara shirmayn karatun mu ina biye masu kafin lesson teacher din yazo. Sai ga hanifa yar gurin Zulfa ta shigo inda muke ko uniform ba a cire mata ba lokacin ta zauna tare da mu ana ta wasa da karatu a lokaci daya. Bata fi minti ko goma da shigowa ba sai ga wata mata badai tsohuwa bace can ta shigo da sallama tana ganin mu hankalin ta yana kan hanifa dake wasa da Amira take cewa hajiya barka da hutawa . Anty ta karba mata tace hanifa wai kizo inji maman ki sai yarinyar tace bazata je ba nan matar ta shiga lalashin yarinyar amma fir taki bin matar. Nace ki tafi ki barta mana tunda tace bata zuwa matar ta marairaice tace idan na tafi bada ita ba fada hajiya zatayi min . Da kyat na lalashi yarinyar nace yanzu zamu hadu a gurin lesson da ita ta tafi kawai amma yarinyar taki binta. Matar ta juya ta fita sai lokacin anty dake kishingide tana kallon mu tai magana tace ai yanzu dawowa zatayi don bazasu barta nan ba. Suna ganin idan sun barta cuta mata za, ayi ne don haka ki lalashe ta ta tafi don Allah Rama rarashe ta tafi please. Kafin anty takai aya ga maganan ta sai ga matan da dawo falon fuskan ta ba dadin gani da gani an mata fada ne sosai tana zuwa ta sukkuci yarinyar a kafadan ta tana ihu tana kuka ta fita da ita daga falon namu. Anty tace may na fada maki ai basu bari yarinyar ta zauna a nan zuwan ki ne ma har take shigowa inda muke dan zaman da kukayi da ita ta dan saba da nan din. Baifi minti uku ba Nasir na saman kaina wai yana min fakin ina zaune na ishishire kafana zaune saman ties . Maigidan ne ya shigo rike da hannun yarinyar dake kuka suna shigowa ta sake hannun ta da rikon uban tayo kaina tana dariya da cewa itama zatai min kitso ne. Anty na ganin su take cewa kadawo da ita ne kuma yace a hannun wanan bakuwar matar na ganta tana kuka wai ance ta dauko ta da karfi ta maida ita part din su. Nikan ina ganin ya shigo ina kokatin tashi nabar falon kamar hadin baki yaran duk suka haye min jiki wai kitso zasuyi min dukkan su sai kokuwa suke kowa nason ya rike min kai na. Kallon mu iyayyen keyi anty tace kaga shirmay da take so don Rama na biye masu suna yadda suke so da ita. Yace ai yaro haka yake so dama shi ko yaushe yana inda yake ganin fuska ne shi amma su basu ganewa don kishin tsiya. Muryan Zulfane a falon a fusace take cewa oya Hanifa come to mummy what are you doing here. Yarinyar ta bata rai tare makewa a jiki na tana cewa mummy ki barni gurin anty please. Zulfa get out kafin raina ya baci idan ba haka ba yanzu ranki zai baci ga hukuncin da zan yake a kan ki. Wani kallo tai mashi sai dai yadda taga fuskan shi yasa takasa fadin abinda take da niyar fadi a lokacin. Ta juya har takai kofa take cewa wanan ai rashin adalci ne yaya za aiwa mutum dole kan dan shi kowa ai yana da nasa yarinke abinsa mana. Idan kai an mai dakai mijin tace ai ba zaka mayar damu muma sai yadda akayi damu ba da diyan mu a gidan kafin ta ci gaba da magana. Ya kara fadi a hasale ba ita da akaiwa ba har mu dake falon sai da muka kadu idon shi ya kade yai ja yace get out i said Da sauri tabar part din ranta a bace shima yabi bayan ta ba tare da yai magana ba. Gaba dayan mu hankalin mu ya koma kansu kaina na sadda a kasa don sun bani tsoro gaba dayan su. Mama tace ikon Allah zamanin nan ina zaki damu ne wai haka ni na taba ganin irin haka gida daya ace yaro ba zaiyi yadda yake so ba. Anty tai murmushi tace gani suke yadda zukatan su yake akaina hakan ne nima zan aikatawa nasu diyan . Niko yaro koba dan mijina bane ina son shi balle dan da mijina ya haifa yan uwan haihuwa diyana. Allah dai ya kara haushe ki kan su kawai za, ace don sunyi nisa sai addua ai kishi ba hauka bane. Murmushi anty tayi ta mayar da hankalin ta inda muke zaune muna sha, anin mu hankalin a kwance ba abinda ya damay mu. Shaawan mu ne yakamata yadda taga na kwantar da hankalina kamar ba abinda ya taba faruwa dani a baya. Gashi yanzu na kwantar da hankalina a gurin ta na gyagije kamar ba wani damuwa a tare dani. Lesson teacher ne yazo muka fita zuwa lesson gaba dayan mu, nan muka hade da yar gurin hindatu itama a kusa dani tazo ta zauna tana ta zuba min surutu. Uban daga inda yake mu bamu ganin shi yana kallon yadda yaran ke ta shige min a jikina. Mamaki yakeyi yadda yaran sukai saurin sabawa dani haka sosai har Nasir da ke da tsauri a cikin su amma yana yarda dani haka. Yana matukar tausayawa anty saade amma yanzu ya fahinci amun wanan yarinyar a kusa da ita ya sa ta dan samu sakewa sosai. Don ko yawan tashi da jikin ta keyi yanzu ta daina yin haka sosai gashi mahaifiyar shi ta matsa kan sai yasa saade ta sallami wanan yarinyar don yaki yarda da hankan ne yasa sauran matan nashi dauko wasu suma su zauna dasu abinda bayaso a gidan shi amma babu yadda ya iya don samun lafiyan matar tashi ya yarde da hakan badon yaso ba. Yanzu gashi a dalilin haka yaran shi na zama guri daya suyi wasan su da dariya wanda hakan zai kawo masu shakuwa a tsakanin su. ****** ********* ****** Zaune take a dan dakin da aka gyara mata dakin tsoho ne baida fadi sosai rufin shi duk ya tsofe sosai . Tana gefe daya a takure cikin damuwa abinda tsohon nan yai mata a daren jiya tana ganin shi kamar baida karfi amma yafita karfi sosai yadda ya makureta ya nuna mata karfin maza duk ihu da shure shuren da takeyi sai da ya kai gareta. Ga gari ya waye sai wani dan guntu kunu mai sanyj aka kawo mata duk kasari a cikin sa babu ko dadin ganin shi. Ga yunwa yanzu yana damun ta ga wanan abin da take tunane da ya tsaya mata a rai idanuwan ta na kallon kofan dakin. A inda take a zaune taga an bankado kofan dakin da karfi wata dattijuwa tagani a tsaye a kanta tana mata kallon banza tace da ita. Ke may kike nufi da bazaki fito ki yi ko shara ba ko kin samu wurin mike kafa ne sai dare yayi ki cika mutane da ihu irin najiya kamar kanki aka fara aure. Ban masan ihun dakikeyiwa mutane ba kamar sabon abu a gareki bayan kin gama ba yan kwararo kanki a garka. An dai ji kunya wallahi wai budurwa a haka nakashe babu abin kai gida anan duk bakin tallan da ku kai wa uwar ku ta kasa sai maki ko yar katifan kada kizo dashi. Ta karewa dakin kallo tana cewa ni ban maga wani abin kishi ba anan don dake da yar sadaka mai gindin banza duk daya kuke a gidan nan. Kai koma sadaka aka bashi ke ai yafi nan kishi da wanan abin kunyan haka. Indai da kwadai da wullakanci maza ki fito ga sharan gida nan idan kin gama ki wanke kwanukan da aka bata jiya. Daga inda lawisa take zaune ta watso mata kallo tace ni ba zama nazo yi da tsohon mijin ku ba balle ki ce kin samu yar aiki don haka ki nemi mai maki wanan aiki. Har ta kai kofa ta dawo baya tace towoo mara kunya dama nasan da halinki ba yau ba to ki sani kin samu tsohuwar zamani don zamuyu daidai dake ne a gidan nan. Lawisa tace ai bana tsoron muyi daidai din ko kashe ni zakuyi keda mijin naku sai dai ku kashe ni amma bazan taba ko kara ba a gidan nan . Muzuba dake ai jiki magayi wallahi ni dake a gidan nan kafin su ci gaba sukaji muryan su Rukaiyya ga maigidan a bayan su tafe cikin hasala shima. Tana ganin yan uwan ta ta mike tsaye Rukaiyya tace maza tazo su tafi gida yau wanan bakin auren ya mutu ke nan. Kofan Jatau ya tsaya yace sai yaga inda zasu fita da ita a gidan shi don babu shegen da zai fitar mai da matar shi. Kudin shi yasa ya auro ta don haka basu isa su fitar da ita gidan nan ba nan suka shiga zagi suzaga ya zaga. Rukaiya na ganin zai bata masu lokaci ta bangaje shi suka kwasa a guje yan gidan suka biyo su suna atare atare suka samu suka fice daga gidan. Da kyat Jatau ya mike sai sannu yara da mata ke mashi don har ya gurje a gwiwan hannun shi. Gidan maigari ya nufa a hasale yana zuwa ya labarta masu abinda ke faruwa a gidan shi. Nan aka saka salati maigari ya tura aje azo da baba da mama lokacin yaran na mayar mata da yadda sukayi da Jatau a gidan sa da mutanen gidan. Sukaji sallaman yaron maigari Rukaiyya ce ta fita don ganin mai sallama Lawisa sai kuka take wiwi tana Allah ya isa ga iyayyen ta da suka cuce ta suka kaita gidan wanan bakin tsohon kazami. Rukaiyya ta dawo take fada masu ai yaron maigari ne yazo gidan yake neman mahaifin su. Mama tace yafita ya tafi kasuwan kauye akace ance azo da mama nan mama tace babu inda zata sai mijin ta ya dawo. Dole yaron maigari ya koma ya fadi sakon ta akace tana da gaskiya Jatau yayi hakkuri har lokacin da baba ya dawo sai a zauna. Nan suka wuni mama da yaranta suna kulla abinda zasu yi idan sun je gurin maigari don sun san baba ba zai dauki wani matakin da ya dace ba ita ko ta sha alwashin sai ta debi wani abu gun Jatau da zata gyara dakin diyan ta dashi ta fitar da ita kunyan daki. Sai yamma lis baba ya dawo gidan kamar kullun bai ko kai zama cin abinci ba yaron maigari ya sallama mashi yafita gurin shi. Can ya dawo yana kwadawa mama kira tun a kofan gida tasan da maganan tafito cikin shirin ta tana cewa lafiya yake mata wanan kiran haka ? Yace may Lawisa ta dawo yi gidan nan bayan an kaita gidan mijin ta don yanzu yaron maigari yazo yana sanar dashi halin da ake ciki. Mama tace eh tana gida ita ta tura a dauko mata yar ta tunda yazo wa mutane da rashin mutunci har gida saboda yaji dafin ta bashi yarta ai dama kudin bazawara ya bayar bana auren budurwa ba. Yanzu ko bata mayar mai da yarta sai ya zube mata kudin auren budurwa zata bari lawisa ta koma gidan nan nan. Baba yace wai lauratu may kike so ne a duniyan nan wanan abin fa duk kece kika jawo shi ba wani ba don da baki karbi kudin shi ba ba zai saka mu a gaba ba hakan nan. Wanan ma ai rufin asirin ki ne da yar ki don in bashi din ba da ya aure ta ya rufa mata asiri wayazo ya taya ta a gidan da sunan aure. Tace dama ai bazaka ga laifin yarka da ta tsale ke ra gudu zuwa birni ba ita da aka biya kudin kan ta. Don Rahama da uwarta sunfi karfin ka shine zaka ce dani haka ita Rahaman har wani farin jini ne da ita da tsufi ke zuwa neman ta gidan nan da zakaiwa diya na gorin aure. Ko dai tsufi ne ke zuwa ta daifi wa yanda ke zaune gida suna aikata abinda bai dace ba aiko. Don may bazai yi magana ba yaga abinda bai yi mai dede ba a rayuwan shi tace ai yanzu sai kaje kabashi wanda yai mai daidai amma babu inda Lawisa zata sai ya zube mata kudin auren budurwa. Washe gari tun da safe suka amsa kiran maigari da yai masu sun samu har Jatau ya hallara a kofan gidan maigari. Suna zuwa aka fara magana kansu maigari yana tambayan baasin da yasa mama ta tura a dauko mata yarta daga gidan mijin ta bayan an gama magana. Mama ta kwashe cin mutuncin da Jatau yazo har gida yai masu tun dasafe tace wanan dalilin yasa ta rike yarta sama ai kudin bazawara ya biya bana budurwa ba. Maigari yace malam Jatau may yasa ka aikata hakan ya gyara zaman shi yace wa maigari an samu kuskure a nan amma ayi hakkuri don shi gaskiya yana son matar shi don haka adaiyi hakkuri. Nan mama ta kafe kan yarta bazara koma ba sai ya zube kudin da ake zubewa budurwa da kayan aure ko ya sakar mata yarta. Jatau dai ya fahinci idan yai wasa wanan matar tafishi balai zai tashi a tutar babu. Nan dai ya shiga kamay kamay yana bada hakkuri akan a dai yi hakkuri a bashi matar shi. Amma mana ta kafe kan sai ya biya su kudin auren budurwa har aka watse a gurin ba akai ga matsayan zancen ba. Sula dawo gida kowa na cicika gashi shi Jatau yaji dadin dan kwanan da yai da Lawisa duk da yadda yake ikirarin ya samay ta din amma son ta ya shiga ran shi lokaci daya. Haka ya koma kamar karamin mahaukaci ranan har takai iyalin shi sun fahinci ya fada tarkon karamar yarinya da ya jajibo masu a gida lokacin. Nan suka fara sake mai habaici irin na tsufin mata da suka san kan mata shiko bai bi ta kan su ba don ba batun su yake yi ba yana batun yarinyar dan ya sharaf. Da yamma ya shirya yazo gurin mama don su sulhuta dashi amma babu magana mai dadi mama tana a kan bakan ta na sai ya biya sauran kudin auren budurwa zata yarda yarta ta koma gidan shi. Tabarshi nan tsugunne takaicin ta duk ya rufeta badon yana son yarta ba don ya samu gurin sauke manyan ta shi da ba abin da zai hana yai mata rashin mutum ci amma babu yadda ya iya dole yabi ta yadda take so ya samu matar shi ta koma dakin ta. Ita ko mama tana ganin ya fara saukowa ta sa a ranta sai tai mai mugun yaga sun kwashi rabon su sai ta lalashi lawisa ta koma don ko banza hakan yafi mata zama gida ai. Da dabara mama ta fara koyawa Lawisa irin hikimar ta na kwatan abu a gurin miji da sauran dabaran zaman da zatayi a gidan Jatau ta zauna lafiya. Mutanen gari sun saka mama a gaba da tsegumi amma ita ko a jikin ta hakan bai taba damun ta ba kanta kawai ta sani. Har yaran nata suka fara fahintar halin uwarsu don sun fahinci kudine kawai a gaban ta lokacin ba damuwan su ba nan suka fara mata tijara ta kasa gane masu baki dayan su don sun hada kansu gareta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YA NA KANKI YAR UWA, , 21 Sai misalin karfe biyu na rana anty ta falka daga nauyayen barcin da take yi lokacin. A hankali ta bude idanuwanta da sukai mata nauyi muryanta a kasalance ta motsa bakinta da kyat tana fadin tare da bin mu ida muke zaune jugun jungun dakin ni da ma. Rama sannun ku ko jikin har yakai an kwantar dani ko wallahi bana jin dadin jikin nawa kwata kwata. Da sauri na mike daga inda nake zaune na kura mata ido ban ko kwakwaran motsi a lokacin. Nake cewa sannu anty yaya jikin naki mama ma ta mike da sauri ta karaso inda muke tana mata sannu da jiki. A hankali ta daga idonta ta kalli ledan drip din da ake kara mata tace har ruwa aka saka min ashe. Nace yaya jikin karo na biyu ta daure ta kakaro murmushi wanda ya zama mata dabia hakan. Tace Alhamdullahi Rama sannu da kokari kinji tajuya gurin mama tace mama sannu na hanaki hutawa ko ? Mama tace Allah dai ya baki lafiya kin ji nace mama bari na kira likitan yace idan ta tashi a kira shi na mike ina kai kofan dakin aka turo kofan. Mijin tane yashigo dakin da wasu leda a hannun shi na magani da fruits na karbi ledan mama tana mashi sannu da zuwa yake cewa ashe ta falka. Heart beat yaya jikin naki tai mashi murmushi tace Alhamdullahi dear ashe kana kusa bakin gadon ya karasa ya zauna. Tare da dan tausa muryan shi gareta suna magana yanayin shi a cikin damuwa yake sosai a lokacin na juya da sauri nafice zuwa fadawa likita ta tashi. Bai tsaya likitan tare muka shigo dashi dakin nan ya samu suna magana yakarasa kusa da ita yana tambayan ta yadda take ji yanzu. Bayan an rubutun da yayi na dan lokaci ya mikawa mijin nata takardan yace aje a sayo wanan magani a gwada mata a gani. Likita yace za, a cire drip sai a bata abinci ta ci kafin a kawo wanan maganin da ya rubuta mata. Tare suka fita sai ga wata nurse ta shigo dakin ta gaida mu nan ta fara cire mata ruwan dake jikinta tabar canular a hannunta tana mata sannu. Ruwa na bata ta wanke baki tare da dan gyara zama nake tambayan ta azuba abinci ko na hada mata shayi ta sha ne ? Tace tea zata sha kadan ko hanjinta zai dan warware mata don bata jin dadin komai a lokacin yadda tace haka ne mata tea mai zafi da kauri na hada mata. Sai gashi ta dan fara zufa tace na bare mata lemo tasha sosai ta zauna tasha lemon da nake barewa ina bata sanka sanka tana sha a hankali. Ranan dai haka muka wuni faman laluran asibiti don tace akai yaran daga school gidan sister din ta, sai a lokacin nake tunane ashe anty nada yan uwa a garin. Ni dan zamana da ita ban ji tana magana akan yan uwanta ba ko da na rana daya ne amma sai gashi naji tana cewa akai mata yaran ta can gurin yar uwarta. Haka dai na bar wanan mamaren a cikin zuciyana ni kadai naci gaba da abinda ke gabana lokacin. Haka mukai ta fama da ita don taji jiki sosai abin tausayawa idan mutum ya ga halinda take ciki a lokacin. Kwanan ta uku aka bamu sallama muka dawo gida don yanzu ba fever ba kuma dizzynes a tare da ita. A hankali take lalaba rayuwanta inda duk wani motsin da zatayi idanuwan mu yana a kan alamarinta don likita yace tana bukatan hutu da kulawa sosai. Wanan dalilin yasa muka mayar da hankalin mu akan komai da zatayi in ba wanka da kewaya ba babu abinda muke bari tayi a rayuwan ta. Sai gashi cikin yan kwanaki ta gyagije sosai baka cewa itace tai ciwo haka a yan kwanakin da ya shige. Har ta kwata asibiti ta dawo gida ni dai banga daya daga cikin abokan zaman ta ta leko taba da sunan sannu. Abin ya bani mamaki matuka don ashe kishi harda ciwo anayi akai ashe kishi yana birni kauye hauka suke yi da sunan kishi. Ranan da dare ta kirani take sheda min gobe monday zan fara fita zuwa training din data fada min. Nace anty baza, a bari idan kin kara jin sauki ba sai na fara tace a, a haba aiko yanzu Alhamdullahi ai na samu lafiya sosai ni ko wanan adduan da kullun kike min ne waya sani. Don ko da yaushe itace may cewa dani Rama ai min adduan nan mana na sha da sauri zan mike naje na samo ruwa nai mata tasha tana lumshe idanuwanta. ****** ********* ****** Tun da safe na shirya don tare da yara da zasu makaranta zamu tafi saida nayi duk wani aikin daya dace ace nayi a part din kafin na fita na shigo dakin anty cikin shirina . Ta bani wani takarda da zan kai furin mukai sallama dasu na fita gabana sai faduwa yake don ban san may zan je na sama ba a gurin. Makarantar yaran muka fara sauke su sai ya wuce dani zuwa inda zamu tafi mun dan taba tafiya mai dan nisa bayan mun sauke su sai gamu a wani bakin get an rubuta NANA TRAINING CENTER da manyan haruffa. Nan ya saukeni tare da yin min sallama sai shidda zai dawo na yamma ya dauke ni kamar yadda anty ta umurce shi. A hankali nake tafe sai mata nake gani manya da yara nau,i nau,i, kowa tana harkan gaban ta a gurin. Wata yarinya nagani tafe da saurinta har ta dan wuce ni nai mata sallama nace don Allah office din shuga nake nema. Da hannu ta nuna min ta wuce da saurin ta gurin na nufa amma office din a rufe yake lokacin. Nakoma gefe na rakube a guri daya ina aukin raraba idanuwana gurin kallon masu shige da fice a gurin kowa sai harkan gaban ta takeyi. Can naga wata mota tashigo har kofan office din da nake tsaye sai ga wata yar matashiyar mata tafito daga cikin motar rike da handbag din ta tana kokarin gyara gyalen ta. Sai da tazo gap dani zata shige nai mata ina kwana ta juyo tana kallon na tare da amsa min har ta juya zata shige sai kuma ta waigo ta dan tsaya tace amma ke newa ce a gurin nan ko nace mata eh. Dan kallona tayi sama da kasa tace ok ra sa kai tashige office din kai tsaye. Sai bayan yan mintina wata ta leko tace ance ki shigo ina shiga ba laifi don gurin ya hadu sosai tace kece daga gurin anty Sa, ade ko ? Nace nice hajiya take cewa yanzu ta bugo min waya amma na dauka ai ko wata babbace ke ashe karama ce. Idan son samune da zaki iya sai mu jefa ki guri biyu kiyi training din mugani ko ? Nace zan iya insha Allahu wanan matar dake tsaye ta kalla bayan ta gama dan rubutu a wani file tare da kallon takardun dana mika mata dana shigo. Tace ki bita zatai maki bayanin komai idan kun fita nace nagode tace ba matsala muka fice muka barta aciki tana rubuce rubucen ta. Matar da aka hada mu bayan mun fita tace kingane may ye sunan ki nace Rahama Aliyu tace zan fara kaiki ajin koyon zaman gida da sauran aiyuka idan mun gama sai mu koma fannin kwalliya da ado ko yaya kika gani ? Nace nagode anty tare muka shiga na samu mata a zaune wasu harda cikin su wasu kuma dai gasunan. Ta nuna min guri na zauna tai indroducing dina ga sauran mata ba bata lokaci aka fara normal activities din da suke yi gurin. Sannu a hankali na fara fahintar abinda ake nuna muna na na kuma fahinci anty ta kawo ni ne don na fahinci duniya sosai kafin na shigeta. Zama da iyali ne akai darasi a ranan kowa taba da hankali tana sauraren bayanin da akeyi a gurin. Ana gamawa wasu suka fice wasu kuma suka tsaya aka fara darasin ado da kwalliya na jiki dana gida. Haka muka wuni ana fahintar damu abubuwan karuwan duniya a gurin dan har tafiya da nau,in magana sai da na fahinta akwai sallon yin shi. Sai biyar saura aka fito nan naga wasu masu training na shigowa matar tace na shiga tunda ba, azo daukana ba. Fanin girke girke ne nan kuma aka shiga sabin darasi har shugaban gurin tana shigowa yin bayani abin gwanin ban sha,awa dashi. Fitowan mu yayi daidai da zuwa Hamza driver na shige muka nufi gida da murna na. Irin sallaman da aka koya muna yau da shi na shigo gidan cikin tausa murya harda dan tafiyan da aka nuna muna ya dace mace ta dinga yi. Suna ganin haka suka saka min dariya anty dake zaune a kasa tace da kyau kaunata aiki ya fara ke nan. Nai dariya na gaidasu da tambayan lafiyan jikin ta ban zauna ba na shiga na kwabe na dora muna girkin dare. Sai bayan magariba nagama nashiga nai wanka tare da dauro alwala nai sallah. Tun wanan ranan sai ya kasance banda lokaci kai ko kadan don busy nake koda yaushe haka ya rage min duk wani sauran kunci da tunanen gida dake cikin raina. Sosai na mayar da hankalina ga training din dake bamu sai gashi tun ba aje ko ina ba na fahin rayuwa zan iya yin komai in a gentle maner. Hakan yasa anty taji matukar dadi a ranta ko yaushe tana min kallon sha, awa sosai don jina take kamar blood sister din ta har cikin ranta. Banda matsalan komai tare dani don komai nake so yanzu zata saya min shi ba bata lokaci haka yasa ma ko ina son abu ban nunawa a gabanta. Ko abin yan mata tagani yanzu zatace wanan abin ya dace da Rama na bari na saya mata shi. Mama Altine kance Rahama zaki ko iya shan ruwan garin mu idan munje. Nace kai haba mama a ina natashi da bazan sha ruwan kauyen mu ba ni wacece mama? Kwana biyu bana ganin mijin su kila don bani zama ne yasa bamu haduwa ban sani ba. Na koma wata saliha dani don ko matan gidan na iya shegen su bana kula tsabgan ko kadan sai na mayar dasu wasu binan can. An yi bukin yaye mu na course din wats biyu danayi a Nana traning center anty bata samu zuwa ba sai mama da yara ta tura sukazo min. Alhamdullahi abinda akaje nema an samu don na sake gaba daya na koma Rahama ta ta birni komai nawa ya sake gashi makerin kyawona ya gama kera min hallitana na cika na zama budurwa a lokaci daya ko don sauyin abincin dana samu ne yanzu ba irin wanda muke ci a kauye ba nai saurin wanan girman haka ? Sati daya da gama training dina addimition dina ya fito na jorna da BUK nan na fara zuwa makaranta ban samu wani wahala ba don yanzu kan mage ya ya waye sosai. Ranan na dawo da yamna lis a gajiye nake banga anty a falon ta ba yadda na saba samun ta tana dan zama ana hira. Sai da na shiga gurin mu na aje kayana nafito zuwa dakin ta a kwance na samay ta nace anty lafiya dai ko ? Tace da sauki yau ina dan jin jikin ne Rama amma ba wai wani can ba da yamman nan ne ai na, dan ji ba daidai ba. Na dan tsaya tsaye ina nazarinta a gurin sai dai ban fahinci komai ba na juya na fita zuwa kitchen. Abinci na hada muna don baci akeyi ba sai nayi dan kadan nagama na shige dakina wanka nayi na fito zuwa gurin anty na samu ta tashi tayi sallah tana zaune a gurin ta ishishire kafata tana ganin na shigo ta mayar da hankalinta gare ni tana fadin har kin kammala ne Rama ? Eh anty na bata amsa ina nufin gadon dakin dake yamutse a lokacin na fara gyarawa tace ai dama kin barshi har da safe ki gyara nace bari dai a gyara kiji dadin kwanci ai. Fira muke ina dan kawar da kayan da nagani barbaje a dakin take cewa dani ya kamata fa idan kunyi hutu ki dan leko gida hakana. Kada muyu rashin hankali yau fa kin kai wata biyar a garin nan babu wani labarin gida kada ace ko an sace ki ne ai. Dariya nayi nace haba dai ina zasu zaci haka tunda sun san da mama muke nan din ai bazata bar dukiyanta can ba ta gudu. Innan ki nake tunane wallahi nakan so a dan aika mata da dan wani abu sai dai gurin nakune da wuyan zuwa wallahi sai in mutum zan tayar yatafi can din. Anty ai zan tafi da zaran anyi hutu na dubo su nima hankalina yana gurin inna wallahi ga rayuwa yanzu kowa kan shi ya sani. Amira ce ta shigo dakin tana kwala min kira wai nazo ga Nasir zai bata min waya na ya dauka yana game dashi. Amira bari ya gama sai na baki ke ma kiyi game din dashi a, a Rama jeki karbi wayan ki bana so ana ba yaro waya ni. Ba wasa a fuskanta don haka na bar abinda nakeyi naje gurin yaran a cikin hikima na karbi waya na zauna muna game din dasu har zuwa dare sukayi barci. Bayan na gyara wa kowan su kwanciya ne na rufo kofan dakin zuwa dakin anty ta canza yanayin zaman ta yanzu zuwa jingina jikin ta da bakin gadon ta. Anty baki kwanta ba ashe tace har na kwanta naji kwanciyan ba dadi ido na tsura mata ina nazarin yanayinta na dan lokaci. Tace nasan yaran ne suka tsayar dake a daki ko nace cikin murmushi sunyi barci ai yanzu. Ko zakisha ruwan zafi ne a hada maki naga baki ci abinci ba yau tace a kasalance hada min nagani ko zan iya sha. Najuya zuwa hada mata tea din mama na falo zaune tana kallo don akwaita da son kallon wasan hausa. Duk wanan yanayin da Anty ke ciki bata san da shi ba har na hado nakai mata shayin ta. Tasha sosai ina zaune da wayana ina karatu a ciki daga gefen ta tace na bata ruwa mai dan sanyi kadan na mike zuwa kitchen na dauko ruwan. Sai bayan na koma na zauna nake kallon agogon wayana dare ya soma yi lokacin dan goma da rabi ya kusa. A gefen gado ta dan sada kanta kamar mai barci sai naci gaba da karatuna don ina zaton ta samu barci ne a lokacin. Can take cewa dani Rama dan kamani na kewaya gaba na ne ya fadi don ban son jin kalma kamani daga bakinta don tuna ranan da tai wanan ciwon ba dadi. Na kamata zuwa bandakin nafito har na zauna naji ta kwalla min kira da karfi da sauri na karaso har cikin ban dakin da take. Gurfane take a kasan ban dakin nata sai dai duk yanayinta ya sauya idanuwan ta sun firfito waje kaman ba ita bace muke zaune da ita lafiya yanzu ba. Tace yi sauri kizo ki kamani don Allah da sauri na kara ida take duke, a kasa cikin ban dakin nata duk da baida wani datti don kullun ina wanke shi kusan sau biyu ko uku idan ina gida. Irin rikon da tai min sai da kasusuwan jikina suka amsa a lokaci daya naji tana wani irin nishi mai karfi. Duk tsoro da fargaba ya kamani a lokaci daya kara karfin rikon da taimin tayi tai wani irin nisawa da karfi sai ga yaro ya fado kasa yana ta cilla ihu irin na jarirai. Jikina ya dauki rawa sosai yaron da uwar tafiya kusan a tare suka fito lokaci guda sai jikinta yasake rikon da tai min ta sassauta tana fadin Allah nagode ma Allah nagode ma. Jikina sai rawa yakeyi wa zan kama ne uwar ko yar zan kama ban bi ta kan yaron dake ta ihu ba akasa ita na rike da kyau na jinginata da abin wanka, tare da gyara mata zama. Sannan na koma daki da sauri na jawo zanin data cire na dora yaron sama ina faman yi mata sannu sannu anty. Nace bari na kira mama falo kai ta gyada min inajin wayan ta dake saman gado yana ta faman ringing a lokacin ban bi ta kanshi ba na fice daga dakin. Mama dake zaune ita kadai tana magana da tv nace a razane mama kizo anty ta haihu . Wani kallo ne ta watso min tace ke kan akwaiki da shirmay wallahi wazaki ruda ana zaune kalau . Nace wallahi mama ba wasa nakeyi ba na juya da sauri na koma dakin inda take har lokacin tana zaune yadda na barta bata motsa ba ta kurawa yaron dake ta kuka ido. Mama tunda ta sayo kai a dakin kukan yaron ya tare ta tace ikon Allah ashe yar nan da gaske kikeyi Allah mungode ma. Cikin kidima nace mama a kama yaron sai ni na gyara anty ta fito ko duk mama ta rude tana cewa ni mai ma nasan zanyi. Na tuna da Inna ta ta haihu reza akace na aheka na sayo shagon uguwar mu take nace mama akawo reza ne tace yauwa keda wallahi duk ma na rude wallahi. Inda take aje reza na dauko sabon reza na kawo mata da sauri tai yadda akeyi ta yanke cibin yaron. Tayo waje dashi sai lokacin na dabaran kama anty na sake ruwan zafi da dama already akwai shi a tank da taimakona ta gyara jikinta nakamata zuwa cikin daki. Nakoma na tsabtace ba dakin da kyau tare da zuba kayan kamshi ko ina sannan na fita da sauri na dauko wani katon roba a store din mu na wanke na dawo dashi dakin. Nace wa mama ta shiga bari na dauko masu abin zama ta zauna akai komai sai dana tanadar mata shi a gurin. Nace mama na tuna ranan na sayo bakin sabulu da majigi da sauri na dauko inda na aje don wanan ranan. Saboda a training center an fada muna anfi son da an haifi yaro ai mai wanka da bakin sabulu da majigi shiyasa da naga mai sayarwa na sayo mata shi gashi ko yayi rana yau. Na koma furin anty na bata kaya ta saka takoma saman gadon da na gyara da yamma ta kwanta a hankali. Gurin mama na koma ina kallon yadda take wanke yaron ina zuba mata ruwa tana darza mai sabulun sallo da majigi a jikin shi tana wanke mai daudan ciki dayazo dashi har tagama na koma da sauri inda anty ta aje kayan baby na dauko showel a cikin su. Wayan anty dake ta ringing yasa na bar mama ta karasa abinda takeyi wa yaron a lokacin . Daddy ne ke ta kiranta ashe har four miscalled yai mata ba, a daga ba jin an daga wayan yafara cewa heart beat ina kika shiga waya nata kuka haka baki daga ba ? Nace a sanyaye Daddy ba anty bace ga anty nan ta haihu ne a razane naji yace da karfi what ? Ta haihufa ki kace ? Nace eh daddy ta haihu. Kuna asibiti ke nan yanzu ? A, a daddy muna gida a gida ne ta haihu ai. Innalillahi naji ya ambata da karfi, yace tana ina yanzu bata wayan naji nace rana kwance tukun bazata iya waya ba tace. Yace subbahanallahi kina jina ina mama nace gata nan tana wa baby wanka ne amma tagama zata fito. Yace ok yanzu nasan an rufe gida kada ki kwanta bari na buga waya yanzu za, azo a duba su don haka kije ki bude gida kafin maishi yazo. Nace to daddy yasake cewa lafiya da ita antyn naki take dai ko ? Nace to daddy lafiya ke nan amma dazun dai kafinta haihu bata jin dadi yace bari na turo yanzu a dubata dai ya kashe wayan na jira mama tazo na bata kayan shafan yaro da sauran abubuwa na fita daga dakin zuwa bude gidan. Na dan jima a gurin kafin mutumin da daddy yace zaizo din yazo tare muka shiga naga yar aikin Zulfa a tsaye tana kallon mu har muka shige ciki. Nai mai iso har dakin ya shigo inda take likitane ya gaida mama dake zaune ishishire a kasa tana shafawa yaron man Alaiyadi da hulba a jikin shi yana kuka. Yace tare da kallon inda anty take kwance yace madam yaya akayi haka kuma mu dake expecting din kizo asibiti kika haihu a gida kuma ? Murmushi tayi mashi yai mata yan tambayoyi tare da duba idonta har harshenta saida yace ta bude baki ya gani. Ta bude ya duba yana cewa ok da sauki sosai sai dai yanzu bari ai maki allurai mu gani zuwa safe idan Allah ya kaimu. Nan dai yai mata allurai tare da bata yan maganunuwa na sha yai muna sai da safe nabi bayan shi na rufe part din mu. Na dawo nabata maganin da aka bata tasha takoma ta kwanta na gyara rufa mata jikin ta da kyau. Nan mama ta bani yaron ta koma bandaki don ta gyara uwar tafiyan dake cikin wani leda aje. Yaron na kurawa ido duk da jariri ne amma uban shi ne sak wallahi yai matukar kama dashi sosai. Can gefen uwan na shimfide shi a hankali na koma na dan kara gyara kayan da ke baje da akai amfani dasu. Sai lokacin na tuna dasu Amira na fita zuwa na leka su a dakin mu inda muke kwana tare dasu. Suna kwance suna barcin su hankali kwance sai suka bani tausayi ga uwar su a cikin wani hali amma kurciya bai sa su sani ba su. Da ace wani abu ya samayta ne yanzu bazasu sani ba suna barcin su hankalinsu a kwance abinsu. Na rufo kofan na dawo dakin anty na samu ta samu barci sosai na kura mata ido tare da hamdala ga ubangiji. Juyawa nayi zan fita mama tace dani amma anan zaki kwanta ko Rahama ? Nace wani abin ne kuma mama tace cikin damuwa a fuskan ta tau wai dare ko ni yanzu ma ai kin fini karfin hali wallahi. Nai dariya nace kai wallahi mama tace ai gaskiya ne keda har karban haihuwa kin iya haka ai kin fi gaban mamaki. Nace mama daurowa ne fa amma ni ina na taba karban haihuwa a rayuwana. Tace zaman ki gidan garbati ai yasaka maki halin manya kin koyo zama cikin manyan mata. Ranan nan na kwana a dakin tare dasu mama na barcinta sai nice ke fama da yaron da yaki barci yana kuka da tandan baki. ********* ********* ********* Babu ko sallama suka ganta ta fado masu gida duk ta jemay tayi baki kamar ba Lawisa ba uwar tsiwa da miskilanci. Daga mama har su Rukaiyya sai tabayanta sukeyi ko lafiya amma ta kasa basu amsa. Gurin da mama ke aje abinci ta nufa tafara bude kwanukan abinci nan taga wani busasshen tuwo da miyan dayai sanyi na kuka ta hauci kamar mayunwaci. Rukaiyya na ganin haka ta dauko mata sauran kunun da suka rage ta surka mata da ruwa taba tasha sai da tai kat da ita. Sai bayan tagama ne take labarta masu abinda yafaru da ita a gidan da kishiyar ta. Aiko mama ta hau fada da zage zage tana fadin babu inda zata koma akashe mata ya da yunwa da duka haka. Da wani ake son mutum yaji ga yunwa ga duka kuma kamar nakai masu jaka a gida don kishin tsiya har dadin may sukaji ne wai. Budan bakin Lawisa da asiri ke aikin a kanta sai cewa tayi a, a mama tunda na samu abinda naci bari kawai na koma ai zamuyi daidai dasu. Ko yanzu don naga zan kwana da yunwane yasa na zo nan don na samu abinda naci kawai. Salati suka saka mama baki bude take cewa Lawisa kima da hankali kuwa ai maki wanan tsinanen duka haka kice kuma zaki koma gidan tun baizo ba anji ba, asi ai mashi kaahedi akai. Ta sake cewa a, a mama bari dai na koma dakina taimako guda zakiyi min shi a dan dinga kai min dan abinda zanci kawai. Rukaiyya tace Lawisa yaushe kika koma hakane kardai kice min son Jatau kikeyi wai ? Tace kada naso shi ba mijina bane nidai ku bari na koma dakina kawai tunda na koshi. Suna kallo ta mike tsaye tana gyara wuyan hijjabinta tare da kokarin ficewa daga dakin tana masu saida safe. Kallon mamaki tabarsu suna mata tafice da sauri daga gidan tabarsu man a cikin mamakin ta. Mama anya kan Lawisa daya kuwa uwar tace nima dai shinagani wallahi yarinyar takoma kamar wata zautatta da ita haka. Akwai dai inji mama don Jatau mugun mutum ne tsafi da sheri ba wanda bai iyaba indai jatau ne a garin nan. Inko har wani abin ne yai mata zamu hade dashi wallahi don ba yarda zanyi ba gaskiya a illanta mi ua ina gani haka. Tafiya take da sauri takoma dakinta donji take dan zaman da tayi a gida kamar ana tsakaranta tabar gidan ne. Tana zuwa ta samu Jatau a tsakar gida yana ma matan shi tujara kan an wullakanta mai abincin da yai wahalan kawowa. Sai ga lawisa tashigo ko sallama babu hanne tabita da kallon mamaki tana cewa au mara mutunci dawowa gidan kikayi har muna murnan bako ya tafi ashe bakona kofan gida. Lawisa tace ban tafi ba yar bakin ciki nadawo babu inda zani kuma sai dai ki mutu zamana da Jatau a gidan nan daram wallahi. Murmushin mugunta yayi yasan aikin daya shukane ke aiki a kanta inba haka ba yasan mama ba zata kyaleta ba ta dawo gidan haka kai tsaye sai anyi fitina. Ta shige dakinta yabi ta daidai tana cire hijjabin dake a kanta yace yanzu yarinyar abincin da nakawo ne kukai wa wullakanci haka ? Tacs o kai abinci ne gaban ka ba dukan da aka taru uwa da diyan ta. Yace aike kika ja may yakaiki zubar mata da girkin ta da tayi don baki da mutunci na sani. Lawisa tace ko gobe sukace baza, zasu banj abinci naci na koshi ba haka zan masu wallahi. Nan dai yai ta masifan shi bata kula shiba sai shirin kwanciyan ta takeyi ita. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA AMANA AKANKI YAR UWA DON KIN CI AMANAN NA, , , , 20 Mu kan bayan fitan shi muka barbaje kayan bukin mu nan muka shiga ci bayan na cire wa Anty da mama nasu. Zaune muke a tangamaymay falon anty muma kallo tunda ranan ba karatun addini sai ga hindatu buguja buguja tana zuwa tai tsaye kerere a kofan falon tana cewa Sa,ade man yana kiranki a falo, daga haka tajuya ta wuce . Anty dake zaune a kasa tana kallo tai tsaki tare da cewa Allah yasa dai lafiya wanan kira da dare haka. Da kyat ta mike zuwa falo inda suke a zaune su biyun har sun hallara a falon kowan su na zaune tana jin iko da mulki tare da ita fuskan ko wace na fuskan wani gurin sai dan jijiga kafan da sukeyi. Da sallama a bakinta ta shigo falon tana saye cikin katon hijjab da ya rufe mata jikinra lif har kasa. Babu wanda ya amsa mata sallaman nata sai shi maigidan da ya dan dago kai ga abinda yakeyi ya amsa mata. Sai ta samu guri saman daya daga cikin kujerun ta zauna a kai tana sauraren shi. Bayan kamar minti uku da shigowan ta gurin na tsit babu wanda yai magana a cikin su sai zuwa can ya dan dago kai tare da barin abinda yake yi yana cewa uhumm kun shigo ko ? Yace bissimillah Zulfau ina son ki fada min abinda kika kirani ga waya dazun kina fada min cikin hasala don ban fahince ki ba a lokacin . Wani dan harare harare take yi tana kada kafa cikin hasala yace sai kin fadi abinda kikace dazun a cikin waya . Shiru tayi bata da niyan yin magana ya sake harzuka yana cewa a hasale, sai kin fada min abinda wani ya tsare maki a gidan nan ko abinda kike ganin nai wa wani banyi maki ba ke ? Tace ni ba ai min komai ba kawai dai yadda kai min cin fuska dan ka dauko yar aikin Saade a gaban motar ka ka share ni cikin mutane haka kamar wata mara daraja dani. Ke may yasa da kika ganni baki taso ba zuwa inda nake koni kike son cikin mutane na nuna masu kin fi karfi na a gida. To tunda naga bakya son zancen a yanzu na yi shiru zan bar shi idan halinki ne zaki koma ai. Wanan yarinya ai samun gurin ta yayi yawa a gidan nan don tana takama a gurin matar gida take zaune muko su agola ne oho. Muryan shi ne cikin mamaki yake cewa don Allah akwai wata daga cikin ku da zata fada min laifin da yarinyar nan tai maku a gidan nan ? Sannan zancen sister din Saade da kowan ku ke kira da yar aiki ina son daga yau a kashe wanan sunan a gidan nan . Don ba yar aiki bace kainata ce ta dauko don ta dinga taimaka mata saboda yanayin jikin ta. Shiru sukayi ganin Zulfa ta noke kan fitinan data jawo sai ya danne nashi fushin ya kyale ta yana fadin ai gaba da yawa. Nan ya ba kowace kudin da yasaba basu a duk lokacin da ya bushi iska don gujewa shiga wani halin rayuwa a kansu. Anty na dawowa part dinta bata tsaya inda muke ba a falonta muna kallon wani shiri da akeyi a tv din dakinta ta koma don ta kwanta. Nice na mike da sauri nabita dakin ko akwai abinda zan iya taimaka mata dashi na samay ta tsaye tana saka rigan barci a jikin ta. Ganin na shigo dakin yasa ta sakin dan murmushin karfin hali tana cewa har kun gama kallon ne? Nace ina karasowa gareta na dauka zakiyi wankane kafin ki kwanta fuskanta tadan yamutsa tare da girgiza kanta alaman a, a , Takai zaune bakin gado da kyat ina mata sannu daga inda nake tace dani yau jikin yaki min dadi Rama. Nace anty ko zaki kara shan maganin ki kafin ki kwanta yanzu fuskan ta ba dadi take cewa Rama maganin ne har ya fita raina wallahi nace sannu anty ki dai daure ki sha magani. Nafita na dauko goran ruwa nadawo dashi nasan inda ledan maganin yake na dauko na kawo mata tasha ina tsaye na kawar da kayan. Falo na koma nasamu yaran sunyi barci na kwashe su zuwa cikin dakin kwanan mu sai mama dake zaune daga gefe daya tana tasbihi. Dakin anty na koma yadda na samay ta ta bani tausayi a hankali na zauna tare da dan fara tausa mata kafa a hankali sai naji ta sauke ajiyan zuciya tana cewa wai nagode Ramana Allah yai maki albarka kinji. Dama baban su Amira nake samu yadan yi min hakan yanzu ko bani kadai bace, baida lokacin min hakan sai gashi Allah ya kawo min ke a rayuwana. Nace Allah dai ya baki lafiya Anty ki koma kamar kowa tace ai matsalan cikin nan dake jikina ne yanzu shine damuwa na . Insha Allahu lafiya zaki haife shi babu matsalan komai, tace to Allah yasa Ramana nace Amin. Ina nan gurin ban dade da fara mata hakan ba naji barci ya dauke ta ban daina abinda nake mata ba duk da na soma jin barcin nima. Naji anturo kofan dakin dake a saye na juya don a zatona ko mama Altine ce ta shigo dakin sai naga maigidan nata ne ya shigo dakin . Saye yake cikin farar jallabiya ta maza mai dan gajeren hannu iya damtsen hannuwan mutum. Ina ganin shi nai saurin kokarin mikewa nabar dakin yace min a hankali ki zauna abinki tayi barci ne ? Eh tasamu barci yanzu ya dan kai hannun shi saman wuyanta a hankali sai ta bude idanuwan ta. Dan murmushi ta sauke tana cewa bakai barci ba ashe yace yanzu na gama kallon ball shine nazo na dubaki. Gashi kuma na tayar dake daga barcinki, tace ai yanzu ne ma barcin ya dan dauke ni dan nasamu Rama na dan tausa min kafana. Sune ke damuwa na da mugun tauna wallahi yace da safe in Allah ya kaimu lafiya dole mu je asibiti a duba lafiyan ki ai. Ba tace komai ba sai lumshe idanuwan ta da tayi yana tsaye ya kura mata ido na dan lokaci yake cewa ita dawa ke kwana a dakin nan. A hankali nace dashi da mama suke kwana yace ki kwana da su yau don naga alaman tana jin jikin bata dai son fadi ne kawai. No taje gun yaran ai ba damuwa nasha magani da zan kwanta Rama tabani nasha ba wani matsala. Yace shike nan sai da safe Allah ya sauwaka ya juya yafita daga dakin ina zaune gar lokacin ina dan mata tausa a kafan. Naji ta koma barcin ta na mike na koma daki nai shirin kwanciya sai dai hankalina bai kwanta ba na koma dakin nata. Har lokacin tana barci ne mama ma ta shigo dakin na fita na rufe part din namu tare da kashe duk wani kayan wuta dake aiki a falon. Nai ma mama sai da safe na koma na kwanta sai barci na dan samu barci sosai sai zuwa biyu na dare na falka. Mikewa nayi na kewaya ban dakin bayan nafito ne nace bari na leka dakin nata nagani. Ina shiga dakin mamane nagani zaune bakin gado kusa da kan anty da sauri na karasa gurin su. Jin motsina yasa mama juyowa gareni tace kin falka ne Rahama nace eh mama jikin ne kuma, tace ai tun dazu bamuyi barci ba wallahi. Kai kai kai take fadi da sauri na karasa ina fadin sannu anty ta daga min kai a hankali alaman amsawa take min. Da sauri na fita na dauko cup a kitchen din mu tare da goran ruwa na dawo dakin zama nayi a kasa na zuba ruwan a cup din sai na dago shi daidai saitin bakina. Na fara da bissimillahi bissimillahi, bissimillahi, lahaula walla kuwati, inni billahi aliyyal azzeem kafa bakwai, sai li, ilafi qurrashen kafa uku na karanta falaki da nas uku uku na karanto suratul ikilas kafa uku na tofa a ruwan. Na mike zuwa inda take nake cewa anty mike kisha ko kadan ne mama take cewa may ye kuma wanan Rahama nace addu,ane na tofa mata a ruwan tasha. Dariya mama ta dan yi tace kai wanan yarinyar da bakin rigima kike wallahi kece zaki tofa addua asha. Hannu anty ta miko min tace wassh mama bari na sha don Allah ta dan mike zaune na bata da hannu na tasha nace ki dan raga kadan a shafa maki a jikin ki. Ta rage tare da komawa ta kwanta na shafa mata sauran ajikin ta har zuwa cikin ta na shafe ta dashi inajin abin cikin cikin yana motsawa. Da ita da cikin suka ban tausayi sai naji tayi ajiyan zuciya mai dan karfi nace da ita sannu anty a tausa kafan ne tace baki gaji ba da kije ki kwanta kawai kinji nagode ma da wanan din. Na dai fara tausa mata kafan nara har zuwa guiwan ta tace na ja mata hannayen ta ma. Ina ja ina tofa mata Ya fattahu, Ya salam, Ya Arrahaman, sai naji tana dan numfashi daidai alaman ta samu barci ke nan a lokacin. Mama har ta samu ta dan kishingide a gefe barci ya dauke ta a lokacin ina nan zaune ban daina mata adduan da nakeyi ba . Har karfe hudu da rabi sai barci ya dan dauke ni nima a furin na kifa kaina kusa da kafan ta ina zaune. Biyar da yan mintina ta falka taganni a hakan yadda nake kwance tausayina ne ya kamata a gurin. A hankali take kiran sunana na falka zubur ina cewa anty kin tashi nw tace eh ina son in dan kewaya ne bandaki ga lokacin sallah ma yayi. Na gyara inda zata mike ta yunkura da kyat ta tashi zaune harta dan sako kafanta zata mike sai kuma naga ta koma ta zauna can ta mike da kyat ina tsaye ina kallon ta da kyat take cira kafa tana tafiya zuwa ban dakin. Naji tace Rama zo ki kamani jiri nake ji sosai na zo da sauri na kamata zuwa bandakin sai da naga ta zauna saman toilet na fito daga waje sai da taga ta doro alwala sai tace nazo na kamata. Har lokacin da alama tana jin jirin nakaita bakin gado ta dan zauna na shimfida na shimfida mata salaya ta zauna a zaune tai sallah ranan duk kokarin da take dashi gurin yin sallah a tsaye ga halin da take ciki. Nima alwala nayo nan na zo nai sallah ina addua naji tace Rama don Allah ki rufe ni sanyi nake ji jiikin ta rawa sosai a lokacin. Da sauri na dauko bargo na rufeta dashi sai sharking jikinta ke faman yi duk na rude na rasa abinyi a lokacin. Can dabara ya fado min a raina da sauri na nufi inda wayan ta yake na fara duba lamban mijin ta. Naga ta rubuta mai Heart Beat na danna kira duk da babban waya ne gareta amma na gane yadda zan kira dashi. Kira daya na biyu naji an daga wayan da sauri yake cewa heart beat yaya dai sai dana daure nake cewa daddy nine anty ce jikin ba dadi bata samu barci ba tun dare. Yace subbahanallahi Rahama shine baku kirani ba muje asibiti nace harta dan samu sauki ne da farko shiyasa ban kira ba. Naji ya kashe wayan nashi nakoma inda take kwance a kasa saman salaya tana rawan sanyi cikin bargo. Baifi minti shidda ba ya fado dakin a rikice dashi idanuwan shi a kansa yana kallonta da saurin shi ya karasa gurin da take ya dan yaye bargon a hankali. Idon ta yana rufe ya kai hannayen shi yana dan taba jikin ta naga ya mike zubur da sauri yacewa shiryata mu tafi asibiti yanzu da ita. Na mike jikina min rawa na sauri dauko wata doguwar riga na samu ta mike da kyat tasaka na kamata zuwa hanyan waje duk nauyin ta a kaina yake sai gashi da saurin shi ya kama min ita muka fice daga gidan ban ko tsaya kallon inda mama tashiga ba ashe tana bandaki. Nan dai muka kama hanya sai asibiti take aka karbe ta sai dakin likita aka shiga dubanta an fada muna cewa, tana fama da rashin lafiyan masu ciki yashigo mata kuma. Gado aka bata za, a kara mata ruwa da allurori idan ma har da bukata harda niji zaa saka mata likita ya fadi. Hankalin mijinta yai matukar tashi yake cewa ai mata duk wani abinda ya dace a taimaka mata dashi don Allah. Dakin da za, a kwantar da ita aka kaimu nan dai aka fara mata duk abinda ya dace muna waje zaune cikin damuwa dagani har mijin nata kowa hankalin shi a tashe yake lokacin. Ba adauki lokaci ba barci mai karfi ya dauke ta sai lokacin aka bari muka shiga gurinta tana barci sai dai kana gani kasan tana cikin wahala sosai. Lokacin ne yaran suka fado min a raina na sauke ajiyan zuciya nake cewa ina son nakoma na shirya yara a gida saina sanar da mama halin da ake ciki. Nan ya dan dago kanshi daga inda yake zaune yana dan buga kafanshi a cikin damuwa yace zaki gane gidane idan kin fita nace insha Allahu zan gane. Bussimillah yace dani tare da mayar da hankalinshi gareta na fice daga dakin na nufi hanyan fita daga asibitin. Tafiya nakeyi a cikin damuwa yanayina yake ina tafe babu abin hawa a lokacin sosai duk wanda nagani a cike yake da mutane can naji anata faman horn a bayana ban juyaba don ban zaci da ni akewa horm sai da naji horn din ya matsa ne na dan daga kaina mijin anty ne na gani yana min horn din yace shigo na saukeki nima zan shirya ne. A tare muka dawo gidan muna tafe ina kallon hanyan don in gane kada na bata idan zan dawo asibitin, ina shiga gida na samu mama a cikin damuwa tana ganina take cewa ina kuka shiga nafito ban samay ku ba nace cikin wani yanayi mama asibiti aka kai anty an bata gado tana can kwance nake mata bayanin komai. Na nufi gurin yaran da sauri na samu sun falka sai dai suna kwance da sauri na shirya su nai masu indomie kawai ranan sun dan makara zuwa makaranta. Na shiryawa Anty breakfast koda ta tashi tana son cin abinci abinci mai sauki na hada mata jeloup da vegetables sai anta da nai amfani dashi a cikin wani littafi na karanta yadda ake hada shi don mara lafiya na zuba ruwa a flask da sauran abubuwan bukata da za, a nema acan. Nafito na hadu da zulfa tana shigowa main falon na gidan nai mata ina kwana ta amsa a dakile ta wucce abinta. Allah ya taimake ni don droup na dauka sai asibitin mijin na waje yana magana a waya ya hangoni tafe da kaya. Waya yake amma yadan kalloni na wuce shi tare da dan dukawa nagaidashi na shige ciki. Har lokacin tana barci mai nauyi ga drip din da aka samata da allurai acikin sa ya canza launin ruwan. Mama na zaune saman kujera na shiga da sallama tadago tana cewa kin dawo Rahama na amsa da ehmama ina aje kayan a gefe tana ganin nazo da carpet da filo don zama tace Allah dai yai maki albarka Rahama don zama saman kujeran ba dadi. Na karasa bakin gadon ina cewa har yanzu bata falkaba ne ? Bata falkaba likitan yacs abarta ta samu barci don shima cikin lafiyan ne haka, wanan yar dai Allah ya tausaya mata yabata lafiya amna tana wahala wallahi. ****** ********* ****** Zuwan Jatau gidan mu gurin biko yafi a kirga wanan lokacin ganin mama ba zata sauki ba yanemi sulhu gareta. Kudin data yanka mai dole ya fitar yaba da shine suka dan hada ma Lawisa kayan aiki da dan gado madaidaici da sauran abubuwa. Sai dai Lawisa takafe bazata koma ba gidan nan dai sani Allah sani Annabi aka samu suka shawo kanta aka mayar da ita gidan da kuka dakomai bafon ransu yaso hakan ba har mama din. Zuwa wanan lokacin hankalin baba ya dan dawo gareshi don ya fahinci rashina da mahaifiyana a gidan ba karamin kuskure yayi ba. Don gidan gaba daya ya sauya ba dadi gare shi ga cin mutunci ga mama kaman an kara mata hakan ne bata tunanen mutuwa ko kadan a rayuwan ta. Haka yasa ya nemi aminin shi suje ai mai bikon Inna ko zata dawo dakinta. Amma inna tace har abada tagama zama a gidan shi don ita yanzu hankalinta a kwance yake mata. Duk yadda yaso Inna taki daawowa gidan hankalinshi yai matukar tashi ga gida ba dadi ko ga diyanshi agaban shi yaro sai yai abin fitsara ba su dauke shi komaiba garesu. Lawisa na komawa matan gidan suka hade mata kai kan sai an raba girki ta fara tace ita baza tayi ba tace da Jatau ai Rahama da tai aure a gidan garbati marigayi bata girki da matan shi don su suna da iyali sai itace za, ace ta shiga cikin manyan mata tai girki. Jatau dai ya fahinci tana da kaifi irin na uwarta na ya fara shiga da fice yana neman magani ya kafeta a gidan. Yai nasara cikin kwana biyu aiki ya haukanta sai gata tafara yin komai na gidan tukunyane babba duk ranan girkin mace ita zata tukeshi da tuwo. Ba wani cima na kwarai a gidan dare da rana tuwone miyan kadi dasafe ma sai mutum ya danyi dabara neman na karyawa don dimamay akeci sai rana za, a girka abinci kowa yaci. Wani lokaci ma idan yan tsiyan nashi na akai sai dare za, a girka abinda za, aci a gidan irin dai mugun rayuwan mutanen kauye. Cikin dan kankanin lokaci tafara fita hayacinta ta ramay tayi baki sosai da ita ga matan gidan da ita babu dadin zama ko kadan. Komai sai su ware ta ai mata wullakanci ba matan ba ba yaran su ba gashi ita ba sana, a sai zaman baza ga Jatau bai kwantuwa ko kadan amma akwai shi da auki kwana da mace kamar ba tsoho ba. Har gudun ranan girkinta yazo rakeyi don bakin kwazaba irin nashi bai da sauki gurin yin harka da mace gashi gidan shi mata basu fita kasafai sai tsawon wani lokaci. Abindai babu dadi gashi sam yanzu bata son abinda zai fitar da ita gidan duk da bakin wahalan da take sha aikin gida kamar zai kasheta. Sai Rukaiyyane kan da tafi gurinta wani lokaci ta dan taimaka mata da abinda ke hannun ta don ta samu na tabawa don mijin baya kwantuwa. Idan ta koshi sosai sai ranan girkinta amma idan kishiyoyinta suka tuka dan kadan ake zuba mata a kwano ace abincine bai kaiba kowa haka yasamu. Ranan da abin ya isheta ta dauki abincin ta nufi gurin wace ta raba ta gwanmace ko kashe ta zasuyi yau sai tai magana kan hakan. Tana zuwa tace maman Abu wanan abincin da aka zuba min aiko loma uku bazai kai ba dubifa yawan shi ki gani. Matar ta dago kai ra kalleta sama da kasa tace tunda uwarki ta tuka min ba sai kisa na cika maki kwano ba tunda kinfi kowa agidan ne. Wani irin takaici ne ya kama lawisa jin harda zagin uwarta daga magana kan abinci iya hakkuri dai tayi shi a gidan nan duk irin cin fuskan da ake mata tana daurewa don magani na aiki a kanta lokacin. Cikin zafin zuciya tace wallahi ba dai uwata ba sai dai na wanda ya zaga cikin mamaki matar ra wawuro ido waje tana kallon Lawisa da mamaki. Tace lalai ma yarinya baki san wuta ba sai kin taka kina nufin uwata ke nan komay ? Tace ni dai wanda ya zageni dashi nake ai tana yowa kan Lawisa ita kuma tasa kafa tai shuri da abincin da miyan da matar ta cika kwanon ta dashi nata dana diyan ta abincin ya zube a kasa . Haushi yakama matar cikin wata bakar zuciya jikake kiff takaiwa lawisa duka da karfi Allah. Tabita ta hada ta tukwanen dake gurin da kyat Lawisa ta iya mikewa matar ta kara kai mata duka cikin zafin rai da hasala jin zafin da lawisa tayi yasa itama tai kokarin ramawa ai nan dambe ya kaure masu. Abinka da sabon jini lawisa tafi hanne karfi sai ga hanne a kasa tabita ta taushe ta akasa . Kafin mutanen gidan su fito duk sun sha wiyan junan su a gurin yaran Hanne na ganin haka sukayo kan Lawisa suka taya uwar su fada. Sun dake ta sosai sai da suka barta kwance a kasa suna fadin shegiya gobe ki kara cewa zakiyi fada da uwar mu ki gani. Da kyat lawisa ta daga daga kwace cikin karfin hali rake cewa wallahi ko gobe aka zuba min abinci kamar nazo bara bazan kyale ba. To mu zuba dake mugani mara mutunci kawai in ma ba abin baba ba wazai kwashe ki haka ragowan kwararo dake kawai tace oho nadai ji haka ubanku ke zaune dani kuna jin haushi na. Dariya da shewa suka saka mata suna fadin andaiji kunya wallahi an kare da auren tsoho. Haka taja kafata zuwa daki ga yunwa na damunta babu abinda zataci a dakin gashi gurin rashin hakkurinta ta zubar da dan abincin da aka bata. Tana kwance ta rasa dubara ga bakin ciki da yunwa na addaban ta a lokaci daya mikewa tayi ta suri hijjabinta ta saka sai gidan su. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI ALLAH YA GANKI, , , 22 Tun da safe mukaji ana dukan kofan shigowa part din mu ina kitchen ina hada abincin yan makaranta wanda kullun da nauin abincin da nake girka masu. Da sauri na fito zuwa kofan ina budewa naga wata mata tana da matukar kama da hajiyan mijin su anty. Nai ma matar ina kwana ta amsa tana kokarin wucewa ciki tana fadin lafiya kuka kwana ko ? Na bata amsa da lafiya kalau mama sannu da zuwa ta wuce tana fadin ina dakin Saaden yake na nuna mata dakin na koma kicin abina naci gaba da aikina. Daidai na kanmmala ne kuma stil naji ana sallama muryan namiji ne da sauri na fito ina karba sallaman na shi yana tsaye daga kofan mu na gaidashi yace ina maihaihuwan take nace tana ciki yace fada mata ga Bashir yazo. Najuya na shiga dakin suna zaune har wanan bakuwar tana dauke da yaro na sanar da ita zuwan bashir din tace nace ya shigo daga ciki. Na juya na fada mai na koma kitchen don na kawo mata abin karyawan ta. Ina shiga naji mutumin na fadin tun dare ya damay ni da kira sai nazo naga halin da kike ciki ko za, a tafi asibiti ne ashe ke Allah ya kawo maki saukin haihuwa haka ? Matar da ta fara shigowa tace ni ai wallahi Alhaji karami ya tayar min da hankali da kyat naga gari ya waye min wallahi. Tace mata gidan sun san da haihuwan kuwa don ban ji duriyan su ba ko da na shigo sai shi namijin yace anya Yusuf bai fada masu ba. Matar tace bari ai yanzu na shiga na fada masu naji idan basu ji bane amma ai haihuwa da ciwo ya kau da komai da suke ji a ransu cin tuwon kishiya ranko. Mama Altine dake zaune gefe ne take cewa banda yaran nan sun dauki kishi da zafi wallahi ace ko gaisuwa na musulunci babu shi a tsakanin ka da dan uwa balle in yana cikin wani hali ka sani. Ko kwana ki data kwanta asibiti bance matan sunyiwa yarinyar nan sannu ba har ta dawo gidan nan ban gan su ba gaskiya. Matar tace daurin gidin hakan suka samu daga yaya amma ta yaya zan bar gidan dana yana ci da wuta har na mara ma abin naya don son kai. Yanzu cikin su ukun nan waye bare a cikin su tunda duk abu guda suke ma zama sai a zauna a sulhunta komai kowa ya tsaya maysayin shi amma ba ayin hakan. Yanzu ba don Allah ya kawo wa yarinyar nan dabara dauko yan uwanta kusa da ita ba yaya ke nan ga yadda haihuwan yazo mata haka a gida. Bashir yace ai ina ga abinda ke tayarwa Yusuf da hankali ke nan don ma yana jajirce ma akidar tasu ai da abin yafi nan. Mata sam basu da tausayi akan kishi wallahi in bashi ba may ye a cikin hakane wai kazo ka samu mutum da mijin shi suna zaman lafiya da rufawa juna asiri kace ina suka fito kai dole sai naka akidar zaka kawo a cikin gida. Bayan sun san auren su dashi auren kaddarane haka Allah ya nufa dashi don yana mai bin umurnin iyayye akayi shi ai da basu isa ba wallahi. Muryana ne nake cewa anty ki tashi kici abincin kada yai sanyi. Ta dan dago daga inda take tana fadin Ramana abinci kikai min tunda safe haka ? Matar tace to ai shine kyau shine jegin asali kaci a binci sai jikin ka yai kyau da sauri ba wanan shaye shayen zamanin da mata keyi ba. Tashi ki karya kin san jikin ki ko banza ba lafiya ne da shi ba ki daure kina ci koba dadi yafi jikinnki yai kyau sosai. Sallama su anty Aisha ne kannen maigidan su biyu suka shigo suma dau nasan daddy ne ya rudasu suzo suga matar nashi take dakin ya cika da jama, a. Ina ganin haka na sa a raina yau ba fita school gareni ke nan don ga baki a shiyan mu tab. Matar data shigo da farko naji sun kira da mama laraba ashe kina nan tace ba dole ba dana ya hanani barcin dare sai nazo na duba mai matarshi naga halin da take ciki. Su anty Aisha sukace tun da asuba ya bugo muna waya wai tunda na karata nurse nazo na duba jikin ta na gani. Mama laraba tace ai Alhamdullahi yadda yake zaton abin ba hakana bane da sauki gaskiya bari naje gurin wa yan can marasa hankalin naji may ya hana su shigowa har yanzu su duba yar uwar su da tai gwajin arziki . Kai mama ai da kin kyale su inji anty hadiye da suka shigo tace ni banga abin damuwa da lamarin su ba wallahi tunda Allah ya sauke ta lafiya ita da baby a kyalesu kawai shi yafi. Bari tace inji Aisha basu da kirki wallahi kwanaki sai da nai ma hindatu tas akan Saade ta dauki bakin ciki da hassada ta dora kan wanan cikin a ranta. Wai kullun tace bata da lafiya amma ta iya shigewa daki tai ciki da namiji su masu lafiyan ma an ki basu cikin ji min maganan hauka anan . Wallahi ban san lokacin da idona ya rufe ba nai mata tas a gurin sai da ta raina kanta. Take cewa wai ai dama saade duk ta asirce mu hajiya ce kawai tafi karfin ta cikin mu. Nace ni na san batai muna komai ba halinta dai a gare mu ne ya asirce mu ba asiri ba. Basu da hankali kin san halin yaran yanzu ne su shigo gida su samay ka da matar ka suce sai sun rabaka da ita ko ta halin kaka don bakin kishin tsiya da hauka ai kishiya abokiyar zamane. Hadiye tace inda sun zauna lafiya da anty saade ai ba karamin karuwa zasuyi ba da ita mutumin da bai dauki duniya da girma ba ai dadin zamane dashi. Mama laraba ta fice daga dakin tana jaddadawa anty ta ci abinci sosai ta bar tsakura Anty ta ce ni dai wallahi Rama yau kin ja min cin abincin safe haka yarinya da shegen akidan tsofaffi haka ina ni ina cin abinci mai nauyi haka da safe ? Aisha tace ai wanan sister din naki wallahi tayi ranan ta tafi tabar ni da sha, awan ta sai data gyara min gida na tsab ta dawo gidan nan. Duk taron matan nan an rasa wace zata daga tsintsiya ta gyara guri haka muke zaune cikin kazanta sai zuwan ta wallahi ta taimaka min ba karamin dadi naji ba. Jifa part dinki kamar ba a haihuba kimai neat dashi gwanin ban sha,awa wallahi. Antyna tace Rama akwai tsabta ai bata son kazanta ga ta da sanin ya kamata kinganta nan tun zuwan ta wallahi ban taba nuna mata yi min kaza ba itace tasan ya kamata bakiji na daina zancen neman mai aiki ba yanzu. Sai dai yanzu data fara karatu dole na samu mai aiki amma ban son yar birni kauye nake son a samo min yar ma daidaiciya yadda zan iya controling din ta. Aike dai anty da yar birnin da yar kauyen sai dace yanzu duk abin daya ne ai inji anty hadiye. Nan dai sukai ta hiran su a tsakanin su suna raha Bashir yace shi zai koma don zai tafi aiki ne yai masu sallama ya fita tare da cewa matan shi zata zo in an jima. Mama Laraba a dakin Zulfa ta fara shiga tana zaune da kayan barci a jikin ta shiyan nata sai wani tsami yakeyi wanda ma bataji ko rabin shi ba a dakin mai haihuwa daya dace ace can akaji wanan abin. Tana ganin mama tace mama kece da safen nan injin dai lafiya nagan ki gidan yau kuma da safe haka ? Au bani da ikon zuwa ke nan gidan lokacin da naga dama sai anzaba min ke nan ko ? Shiru tayi tasan maganan da taiwa maman yaci mata rai ke nan tabata amsa da hakan don Zulfa bata son taga suna shigowa gidan ko yaushe shiyasa ma da suka fahinci gidan yanzu ba kamar da can da anty take ita kadai bane da suke zuwa gurin maigidan ko ita sukawo koken su garesu kuma ya taimaka masu koma bai nan anty zata iya taimakawa da dan abinda ke gareta. Amma zuwan yaran nan biyu gidan yasa kowa ya jaye daga shiga gidan tun zuwa da wata daga cikin yan uwa tayi Zulfa tace ana yawan damun su da zuwa kullun sai wani yazo kuma rokone su ba, a bari yai masu hidima yadda ya dace sai dangi. Take labatin ya bazu ga dangi kowa ya kama kan shi yanzu basu zuwa suma basu zuwa inda suke zumunci na batun lalacewa. Nan dai take cewa to ni ba wani abu nazo yi ba baki da labarin yar uwar ku ta sauka ne tunda dare halan ? Sai da ta ya mutse fuska take cewa ya bugo min amma ai naga gida daya muke ita bata fada muna ta haihu ba sai shi dake wata kasan zai bugo muna waya. Mama Laraba tace lalai Zulfa kinyi nisa shi mijin naku bai isa ba ke nan ya fada maku kubi sai naki ra, ayin ko anya zulfa kin wa kanki shimfidan arziki kuwa ? Kada ki manta yadda kukai tabin mu keda uwar ki akan akama kafa ai auren nan a tsakanin ku yanzu kina ganin kin samu shiga shine kike fito da kalar ki kina hura hanci ko? To kiyiwa kanki kiyamallaini tun yaron nan baidawo ba naki ya samay ki gidan nan wai ke baki tunanen mutuwa ne arayuwan ki komay ? Ran Zulfa ya baci don mama laraba na yar mahaifiyarta ne data fada mata magana sai dai duk da haka tace mama ai ko ba, a kama kafa ya aure ni ba Allah yayi aure a tsakani da shi dama yaya za, ayi tunda Allah yayi shiga kima daram ba fita. Zulfa ni kike fadawa haka to ki sani ni ko uwarki bata kallon idona ta fada min magana haka kai tsaye don akwai mutum biyu a tsakani na da ita. Ki sani ni tallaka ne cikin dakin mu amma ban dogara da abin wani ba nawa nake mikewa na bida don haka babu mai kallon idona ya fada min maganan akan abin shi. Nasiha ne nai maki ba lalai bane sai kin dauka indan zaki gyara ki gyara Alhaji karami ne kin san halin shi tun baki shigo ba. Idan zaki sauke girman kai ki rufawa kanki asiri kije ki gaida yar uwar ki ki mata barka da arziki daya fi maki. Zulfa tace mama laraba da kece kika haifeni nake cikin wanan daulan bazaki ce najeyiwa matar da bata kaunan farin cikina barka ba. Amma yanzu nagane zumuncin baki wasu keyi wa yan uwan su ba har zuciba saade dai kishiya tace matar mijina Yusuf sai naga daman zuwa gaida ita. Muushi mama tayi don yasan halin rashin kunya irin na yayan yar uwata halima don haka tace ba laifi dunuya ce girma gareta ai . Mama ai tunda naga don saade ta haihu kika yo sakkon zuwa da farar safiyan nan da wani manufa kika shigo. Ba laifi ni na tafi dama nace bari nazo naji dalilin rashin shigan ki gurin tane kuma naji nagode. Ni fa mama kada ki kuma kulla min wani sbon sherin ina zama lafiya a dakina zaki zo ki samay ni da sabon fitana in dake kika haife ni bazakiyi min haka ba ai. Mama laraba da takai kofa ta juyo ta kalli Zulfa cikin takaici tace lalai kan ban haifeki ba zulfa kuma bama zan taba haihuwan irinki jaira ba a zuriata. Tasa kai tafice zuciyar ta cike da kunan mugun halin diyar yar uwar nata dama tasan wanan auren ba wani abin arzikin da za, a kulla a cikin sa. Bata daddara ba Part din hindatu ta nufa ta samu yar aikinta na kwashe kaya don itama gurin kamar ba sabon guri ba babu gyara yadda ya dace. Yar aikin tace tana ciki bata tashi ba tace ta diba mata ita can tafito tace wai tana tafe taci gaba da abinda takeyi. Sai tsawon wani dan lokaci har mama na batun barin gurin sai gata tafito tana cewa a,a mama kece tafe ? Suka gaisa take cewa da ita dama na shigo nace baki samu labarin haihuwan yar uwar zaman ku bane tun daren jiya. Ta bata rai tace bata fada min tahaifu ba mama sai shine ke bugo min waya idan na gama zan shiga na lekata ai. Koba komai mama ta dan jin sanyi gun hindatu tunda itama da ake kira da fitsarara yau dai batai mata fitsaran ba. Kamar yar yar uwan haihuan ta data nuna ta isa a kanta amma ta rufe ido ta yaba mata magana masu zafi haka. Tace hindatu ku dinga ba kan ku shawaran arziki kin ji zaman duniyan nan na dan lokaci ne ba mai daurewa bane kada zafin kishi ya rude ku. Na kuma gode da mutun tani da kikayi yanzu don baki tsaya ja dani ba yadda na zata shi gyara kayan ka baya zama barna ni zan koma nabar ku lafiya. Tace nagode mama zan shiga idan nayi wanka yanzu sai anjima tai sallama ta fito. Nan ta dawo ta samu su Aisha tana fada masu abinda ya faru tsakanin ta da su . Ran Aisha ya baci tace ita Zulfa har ta isa ta fada maki magana mama watau harta manta da lokacin da ta tare a gurin ki don taga an yarda anyi auren su da yaya don tasan cewa yana ganin mutuncin ki da kiman ki cikin uwayen mu ai barta wallahi sai tagane tayi maki rashin mutunci. Shiyasa tun farko ban so ace kin je ba mama don yanzu jinkan su suke wani abu basu ganin kowa da mutunci a idon su. Nan dai nake jin wasu bayanai a cikin hiran su akan family su inda na fahinci yan uwan mahaifiyan mijin anty suna da dan yawa a dakin su. Amma shi maigidan anty yafi shakuwa da mama laraba a cikin su don kamar ita ta haife shi yake jinta. Ashe shine dalilin da yasa ma tazo yanzu din don ita yake ji a matsayin uwa a gare shi ita hadiye yar tace ashe amma a gurin mahaifiyar su Aisha ta tashi. Yinin ranan haka yan barka ke shigowa gaida anty dayi mata barka da arziki. Niko ranan aiki kaman zai kashe ni amma banji komai a raina ba don ma ban dauke shi komai bani a gurina. Sosai na mayar da hankali na ga anty na gurin kula da lafiyan ta wani lokaci har da na dan jaririn ya duk da mama na iya kokarinta akai amma jiki yayi nauyi yamzu mama sai a hankali take. Ba komai zata iya aiwatarwa a kan lokaci ba haka yasa nakoma busy sai dare nake samun hutawa yadda ya dace. Naga mata masu shige da fice nasan yan uwan anty da ban sani ba akan wanan haihuwan duk wacce tazo taga yadda muke da anty sai ta tambayeta a ina ta samau ni sai tace dasu sister din ta ce ni kawai. Sai suce wai amma dai akwai mace a gurin nan yarinya kamar ita ta zauna ta tsara kan ta hakomai nata acan acan dashi. Anty kance to kwalelen ku ban ba kowa kaunata sai nazaba mata wanda ya dace zai kula min da abata ayi wasa da dariya su wuce. Sai bayan kwana biyu da haihuwa ranan sai ga hindatu ta shigo part din mu yin barka sai faman yatsune yatsune takeyi a lalace tai barka ana mika mata baby tace abarshi ai ta gan shi. Tai sallama ta tafi mama tace ikon Allah ana dai kishi a nan harda jajiri da baiko san duniya ba ake kishi kuma ? Zulfa bata shigo ba a cewan ta ai anty ba tura da kanta a fada mata haihuwan ba sai dai a cikin ranta kishi takeyi wai don samun guri anty ta kara haiho namiji tafi hindatu zafin kishi sai dai takan yi kokarin dannewa don hindatu masuyi yanzu ne ya kare yanzu datayi ya wuce ke nan bata da riko kamar zulfa. Shigowan safe daddy yayi garin lokacin ina kitchen ina aiki sai ihun yara naji suna taron shi da dawowa. Haka yasa nasan dawowan shi ina kitchen ina ci gaba da aikina na tuna ruwan flask din anty ya kare da sauri na nufi dakin don in dauko ban tsanmani yana cikin dakin ba a lokacin sai dana shiga na ganshi zaune saman gado kusa da ita sai mama da kasa Anty Aisha da yazo tana saman kujera. Gaishe da dawowa nayi shima yai min sannu da fama da kokari nai dan murmushi na wuce zan dauki flask din. Naji yace wai wama ya karbi haihuwan nata ne haka a gida ? Anty Aisha tace mama mana tunda itace a kusa daga inda mama take zaune tace rufa min asiri wata mama can ? Ungwazo ma dai ta karba Rahama da sauri suka hada baki cikin mamaki sun wata Rahama kuma wannan dai Rahaman . Ita fa iji mama tace sai da suka gama abinsu tazo ta kirani itace kuma ta gyara yar uwar ta aini wanan yarinyar sallon ta yafi karfina tun ranan. Daddy yace kai amma ko kunyi ganganci wallahi yarinyar da bata san kan haihuwa ba zata karbi haihuwa kuma ga mutum mara lafiya kamar ke ? Mama tace ai Rahama itace likitan gida na saade kagan ta nan ko lokacin shan magani yayi zata bar abinda takeyi tazo ta tasa ta gaba sai ta sha shi tafice. Mamaki wai ni Rahama suke tayi ace na karbi haihuwan babban mace kamar anty sukeyi. Anty tace kungan ta nan daidai lokacin da ina shigowa dauke da ruwan flask a hannu na, tace wallahi ban ma taba haihuwan da naji dadi irin shi ba don yadda tai min naji dadi sosai wallahi. Dariya suka saka mata daddy yace kun dai yi risky din life din ki wallahi Allah dai ya gyara kawai amma ku daina wanan gagancin haihuwa ba abin wasa bane ai. Dawowan daddy aiki ya karu min don komai shigowa dashi akeyi gidan duk da dama akwai kayan abinci amma bai hana a kawo muna wani ba. Yau ma kan saniya aka kawo mina wai na kauri shi zamu gyara na samu yar gurin mama laraba da ke gidan ko yaushe yazu tazo tare muke aikin da ita. Aiki sosai mukayi mun wanke kazan tan kan mu jefa spoons a cikin dahuwan don yai sauri nuna kamar yadda aka koya muna kayan kamshi na gargajiya ne na cika sosai a ciki take kamshi ya bure ko ina na gidan. Bayan mun gama na sauke naje na fadawa anty nama ya nuna yaya za, ayi mama Laraba tace bari ta taso tazo tagani wasu kuloli anty ta aika aka sayo tin kan mu gama dahuwan a ciki muka dinga zubawa tana fadin wanan na gidan wance wanan na wani sai da muka zuba a kula goma sha biyar sai kuma ta dauko sweets ta shiga kasawa muna rubutawa don bata. An fitar dana matan gidan dana maigidan su tace naje na kaiwa kowa nata na maigidan abawa mai girki ranan. Part din zulfa na fara shiga bata nan nabarwa yar aikin ta ta bata idan ta dawo na wuce nakaiwa hindatu nata dana maigidan nata. Ta karba a wullakance tana wani basarwa wai wanan may ye hakane dama ai an barshi kawai abawa jama, a nidai na fito na barta dashi. Tare da Farida diyar mama Laraba muka tafi kaiwa nan naga gidanjen yan uwan su dana anty. Gidan su anty babban gidane ginan zamani mai kyau sai dai babu mahaifiyarta a gidan kuma ita kadai ce aka haifa a gidan mamanta ta rasu tun tana karama ne haka ta taso hannun kishiyoyin maman ta da dadi ba dadi cikin su gashi mahaifinta na mutuwan son ta sosai a cikin diyan shi. Wanan dalilin yasa ba wani shakuwa tsakanin ta da yan uwan ta sosai har wanan lokacin don ta kasance ita kadai a cikin su dan dama wata Ramatu daga cikin yan uwan ta suna dasawa da ita sosai gidan tane ma ake kai su Amira da anty bata da lafiya. Saukin ta daya yanzu samun wadatan da mijin ta yayi shine suke dan binta ko shi na munafunci ne bada zuciya daya suke son ta ba. Mun dawo muka tarar da balai a gidan wai Zulfa ta dawo da kayan kairin da aka kai mata tace bazata karba ba don ita ba mayunwaciya bace. Shi ya batawa mama Laraba rai tafito tai matta kwal ita kuma ta kira uwarta ta fada mata shine uwar tazo nan ta samu mama Laraba da masifa abindai baiyi dadi ba ko kadan wallahi don sunyi tonon asiri sosai a tsakanin su a gidan. Har uwar na ikirarin cewa ai ba,a dole kishine tsakanin su da anty kowa tasa ta fishe shi kawai don may mama laraba zata zo ta tare ta saka mata diya gaba da tsangwama. Da kyat aka samu suka bar zancen wanda sai da takai ita hajiyan su daddy ta bugo masu waya ta samu suka daina masifan. Shine da muka dawo mun samu mama Laraba tana kuka tana fadin zata tafi gida daga raban kuma bazata sake zuwa gidan daddy ba tunda yan uwa na ganin kwadayine ke kawota ba zumunci ba. Anty da mama sai faman bata hakkuri sukeyi anty na fadin don Allah mama kiyi hakkuri wanan abin duk bakinciki ne na kin tsaya bisa gaskiya don nasu son suga kowa cikin ku ya rabe ni nida diya na sai ita zulfa din kawai. Har takai nazo har gaban ta na tsunguna ina cewa mama don Allah kiyi hakkuri idan kin tafi ai gurin su ya cika ke nan dama haka suke son gani gare ki su raba ki da danki. Kallon na tayi kamar tana nazarin magana na can sai take cewa hakane kuma yar nan don na fahinci zulai bata son ganin kowa tare da Alhaji karami sai ita da yarta ko uwar da ta haife shima bata gane nufin su bane a kan ta har yanzu. Mama Altine tace ai gane irin haka da sauri wuya gare shi Allah dai ya gyara kawai. Bayan dawowan daddy ne hindatu ce ta labarta mai yau anyi fada da mama Laraba da mama zulai a gidan. Ranshi ya baci ya harzuka tare da mikewa tsaye yana tambayan may ya kawo hakan a gidan shi tace bata sani ba ta daiji fadan su ne tafita ganin may ke faru. Wayan shi ce tai kara anty Aisha ce takira shi nan ta shiga labarta mai abinda ya faru tun ranan haihuwa da kuma na yau da akayi take fadin ya kamata ya dauki mataki don mama Zulai bata bari a zauna lafiya a gidan. Ko a tsakanin iyayyen mu haka take fama saka fitina a ysakanin su ko yaushe abinda kowa yaiwa gudun auren yarta ke nan gare ka tun farko. Ina zaune naga shigowan shi part dina yanayin shi kawai zaka kalla kasan cikin bacin rai yake a lokacin. Sun fito da mama zuwa falo ina ganin su na mike na shige cikin daki na basu guri nan mama Laraba ta labarta mai duk abinda ya kawo fitanan a tsakanin su da mama zulai da yarta kamar yadda anty Aisha ta fada mai. A hasale ya fita bai tsaya ba sai gidan mahaifan shi ya samu mahaifin shi ya dawo gida lokacin dama ya bugawa anty Aisha waya su hadu gida da ita yanzu. Bayan sun gama magana hajiya tace to ai gaskiya ta fadi ita Laraba may zai sa tabar yar uwar ta takama bare ai kamar tana bayan saade ne. Kamar yau saade ta fara haihuwa a duniya kabi ka tayarwa mutane da hankali kan haihuwan tsohuwa haka. Haba mama ki daina aiban ta mashi mata may saade tai maki ne wai haka danki fa take aure mama. Hajiya ta bude baki zatai magana baba ya tare da da fadin ai gaskiya yar ki ta fada maki bani son saka bakina ga al, amarinku ne, Amma yanzu maganan ta shafi dana dole nayi magana kada ki manta da irin halarcin da Laraba tai wa yaron nan yana karami. Yanzu ne da Allah ya kai shi haka kike son nuwa yar uwar ki bata isa ba da danki ko may ? Yanzun ne kike son nuwa dunya kece uwar shi ba yar uwarki ba sai wanan da suke kokarin halaka maki rayuwa sune yan uwanki na kwarai. To ba zan dauki wanan ba nayi hakkuri na kawo ido na sa maku amma naga abin naku babu sanin ya kamata. Daga yau ina son ki cire bakin ki ga duk wani alamarin dake gudana a gidan yaron nan da iyalinshi Laraba dai itace yake shawaran gidan shi da ita don da ita ya bude ido tun farko. Zulai har yaushe ta dauki yaron nan a matsayin da a gare ta ina sai da taga Allah yai mai rufin asiri ta san dake da dan a duniya . Wani irin rashin mutunci ne bataiwa mutane ba lokacin da mijin ta keda wadata ku baku dashi. Yau duk kin manta da komai daya faru a baya idon ki ya rufe ke gaki uwar mai akwai har zakiwa yar uwar ki rashin mutunci a kan gaskiya. Laraba tafiki sanin gaskiya daya kamata ita wanan yar da kike matukar kyamata bata da iyayyene halan. Kin fi kowa sanin gidan su a garin nan da farko ai kinfi kowa sanin wacce ya ke son aure amma baki ce tsohuwa bace sai yanzu da suka hayayyafa zaki tsiro da kiyayyan yarinya ki sa a ranki may wanan yarinyar ta kashe maki a duniyan nan? May ye abinda uban yarinyar nan baiwa danki ba kafin Allah ya kawo shi hakan ina ubanta ne silar zaman shi haka yau din nan. To ban son rashin gaskiya a rayuwa daga yau ki barsu suyi matsalar gidan su kiji dana gidan ki idan zaki gane abinda zulai da yarta keyi a gidan ba daidai bane ki gane ki tsawata masu a matsayin ki na babba a cikin su. Don haka ka tashi kaje ka aiwatar da hukuncin gidan ka gwargodon yadda sharia ya tsara ayi na kashe wanan maganan ba ruwan ki daga yau cikin har kan gidan yaron nan idan kuma bakiji ba daga ke har zulai zakusha mamakina wallahi. Ina kuma son kiwa zulai kashedin zuwa gidan yaran nan tana aikata abin kunya sabo da son kai irin nata. Sai lokacin ne dady yai magana yake cewa abinda nake son fadi ke nan daga yau mama ta fitar da bakinta ga matsalan gidana ni mama Laraba na sani ita kuma nasa. Hajiya ba daman magana an riga an mata shamaki akan maganan dole taja bakin ta tai shiru tana mai karajin tsanar anty a ranta sosai a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA A KANKI DON ALLAH NA GANIN KI YAR UWA, , , , , 23 Ba fada ba hayaniya amma ya cin ma Zulfa a part din ta yace ta tashi taje gidan su. Da mamaki take kallon shi taso tai mai fitsara don tasan dalilin turata gida saboda hayaniyan iyayyen su ne amma a yadda taga fuskan shi ba saukin yin haka yasa bata iya tankawa ba sai dai tayi zaune ne kawai ba alaman tashi a gareta. Yarinyar dake barci a gefen ta ya sa hannun shi ya dauka tsab ya fara tafiya. Sai lokacin tai karfin halin yin magana tace ina zakaje min da yarinya ta, wallahi ban yarda da wanan hukuncin naka ko yaushe na fahinci sai kai ta kokarin nisan tani da ya ta kan dan karamin magana. Bai kula mai take fadi ba ya fice da yarinyar daga dakin ta mikewa tayi tabi bayan shi ta fara masifa akan ya bata yar ta. Cak ya ja ya tsaya tare da juyowa inda take idanuwan shi sun kada sunyi jawur a lokaci daya da kyat ya iya bude bakin shi yace cikin wani kakausar murya. Idan kika kuskura kika biyo ni baya bakin auren ki ke nan a gidan nan mara mutunci kawai. Daga haka yasa kai ya fice daga part din ran shi a bace da yarinyan dake saballe a kafadan shi yarinyar ta bude ido ta ganshi tace daddy ta gyara kwanciya a saman kafadan shi kawai tana mai ci gaba da barcin ta a hakan. Zaune muke a uwar dakin anty muna hira don duk baki sun watse Farida ce kawai ta rage cikin baki don mama Laraba yini kawai take damu da dare driver ke kaita gida sai kuma da safe ta dawo again a nan zata wuni sai dare. Muna ganin ya shigo da yarinya a kafadan shi naji anty tace subbahanallahi daga tsakiyan daki ya tsaya yace Rahama karbi yarinyar nan ki mata makwanci inda su Amira suke please. Da sauri na mike na je na karbi yarinyar ban fita da ita ba don su Amiran a lokacin dul muna dakin anty dasu sunyi barci a nan. Na shimfideta a saman gado gefe daya inda suke kafin mu koma can dakin dasu. Dear yaya akayi haka kuma ina uwar ta take bai tsaya ba sai jutawa da yayi yana fadin nothing kawai a fili. Ya bat dakin yana fita anty tace babu lafiya ke nan tunda kika ga haka don dear bai yarda ai fita mai da yaron shi gidan nan bai hada diyan shi da komai a duniyan nan koke uwar yaro sai yai kokarin saba maki a kan yaran ki in bakiyi wasa ba. Daga inda mama take zaune tana gyara jaririn daya bata permpers din jikin shi take cewa ya wuce kan zancen dazu ne suke rikici akai. Haba suma dai basu son a zauna lafiya wallahi ace ko yaushe babu burbushin zaman lafiya a gida ai haka bai yi ba don dai ma yana da kashin arzikine ai da yanzu ya tabe ko sun tsiyata shi don irin haka komawa baya yake kawowa maigida. Anty tace su ina ruwan su da wanan kan su kawai suka sani shine halinsu da suke ganin wayewa ne amma in bashi yaya zaki zage yar mahaifiyar ki daga fadan gaskiya. Yanzu gashi tajawa kan ta fita ana zaune kalau ta hana kanta farin ciki ta hana wani kinga ba don Allah ya rabani da fitina ba da har dani ta saka aciki ai dazu don mama na nan ne zancen ya juye a kanta da guna zasu sauke haushin su. Yana fita ya koma ya samay ta tana waya daga kofa ya tsaya yake cewa may kike jira baki fita kin bar mingidana ba har yanzu? Kallon wullakanci ta jefo mashi yace idan kin ki fita a arziki yanzu zan baki shedan fita da tsiya idan haka kike bukata din. Idan akwai abinda ta tsana shine yace zai sallamay ta a gidan ta san kuma zai iya abinda ya furta tunda ko banza bawai ta damay shi bane a gidan. Mikewa tayi ta shiga uwar dakin ta ta dan jima sai gata tafito da handbag a hannunta tana gyara hijjab din jikin ta. Ta gaban shi tazo zata shige yace dakata wanan matar da zaki bar min a gida may zata zauna yi min gidana ? Mamaki yake bata don kalamin shi ba sauki gareta dole ta kira yar aikin tace tazo su tafi suna fita shi da kan shi ya rufe part din ya sauke ajiyan zuciya. Ya rasa may zai mata ya huce haushin abin da sukai wa mama laraba ita da uwarta akan su. Mukan har muka shiga kwana bamu sake jin motsin suba a gidan na kwana da yaran na bar farida da mama suka kwana da anty. Washegari mun tashi da aikin shagalin bukin suna wanda muka fara tun safe babu kama hannun yaro. Duk da akasarin aikin abinda za, a ci ai kai wa masu yin na kudi ne don samun sauki amma duk da hakan bamu huta ba don nice ake tambaya komai na aikin da za, a karba din. Ganin mutane a part din mu yasa ban da shakat a gurin yaran anty don duk kan su uku suna lake dani suna zabga shagwaban su ina kuma biye masu a hakan don ni ina da son yara. Tare da sune muka shiga daki gurin anty tana zaune da kawayen ta da yan uwanta na samay na make murya ina cewa muna son muyi party nidasu Amira. Kai amma Rama bakya girma ne ke party may kuma zakiyi babba da ke nace zamu dai yi ne anty tace yanzu may kuke so abaku ne ? Na lissafa mata tace naje duk wanda ake dashi a gida na diba muna wanda babu sai mu saya mu kara ciki. Da murna muka bar dakin nida yaran wanda tai matukar jin dadin hakan a ranta sosai don tana son taga yaranta a cikin farin ciki ko yaushe. Gashi ina biye masu yadda suke so ai masu hakanake tafiyar dasu anty tasha auna son gaskiya nake wa yaran ko har cikin raina da zuciya daya nake da ita da yaran ta. Babu inda na taba samun matsala ga irin gwajin da takan min wanda ni ban san ina yin hakan ba ma don zallar kurciyan dake tare dani. Ban san an muna dinkunan fita suna ba sai daren sunan bayan an dan watse ne ta kirani tana mika min manyan ledoji tace na je dashi namu ne na fitan suna ta miko wani daya karami tace nabawa Farida da muke tare yanzu. Kayan da na gani a ciki sai da na daskare zaune don mamaki les ne dan uban su an min dinkin yan birni mai kama jiki sai shadda zani da riga na yan senegal, atamfa guda biyu dogon riga da kuma zani da riga sai dongon riga abaya yaji duwatsu stone har kasa duk jikin shi mai baga bagan hannnaye da shi. Kala biyar ke nan yadda nawa yake haka na su Amira kala biyar da Nasir sai wanda tace kayan kantine na yara har da yar gurin zulfa dake tare da mu yanzu. Mamakin wanan hidiman hakaka ya kamani sosai bayan na gama gani na koma ni kadai tana zaune na durkusa tare da dafa gadon da take sama zaune akai na dukar da kaina ina cewa antyna nagode kwarai Allah ya saka da alheri Allah ya baki lafiya ya raya maki yaran ki. Ta dafa min baya tana cewa da akai may kuma Ramana da wanan irin godiyan haka ba iya ka ? Ke fa tawa ce wanan ai ba komai bane koda kuwa ace ma biyanki wahalan da kike min nake yin ban maki komai ba ai. Samun yarinyar arziki irin ki yanzu mai zuciya daya haka ai sai an tona bani ba har wa yanda nake tare dasu sun sancewa na samu saukin alamarina zama dake Rama kowa sai dadi yake ji min wallahi. Nai murmushin jin dadi har cikin raina naji dadin yabon da tai mim sosai na dade zaune tare da ita muna hiran yadda abubuwa ke tafiya yadda take son ayi shi. Washe gari suna na gyara ko ina yadda ya dace ga masu runfuna sun zo sun fara kafawa a haraban gidan. Kafin wani lokaci gida ya soma cika da yan uwa da abokan arziki masu zuwa taya murna haihuwan new baby Yusuf yaron da yaci sunan mahaifin shi kuma sunan kakan mahaifin shi ta wurin uban shi. Nan mata suka fara rade, radi wasu najin dadin hakan wasu kuma na gulman hakan wai son da ya kewa uwar yaton ne ya shafi yaron har yaci wanan sunan nashi. Taron mata ba, a rabasu da gulma irin haka irin wanan maganan ne har ya tunzura sauran matan gidan suka kasa boye bacin ran su akan hakan. Har Zulfa dake gidan mahaifanta har lokacin sunan don maigidan bai kara waiwayan ta tunda ya tasa keyan ta zuwa gida. Duk da mama Laraba tayi magana akai yace da ita ba yanzu ba tunda bata farin ciki da karuwan da ya samu mau zai sa adawo da ita gidan kafin suna. Asalima bazai dawo da ita ba sai mama zulai da yarta sunzo sun ba mama laraba hakkuri akan kuskuren da su ka tafka na ci mata mutunci kan gaskiyan ta. Gidan da akwai kishi daga daya zuwa hudu akwai fitana kala kala kullun da wanda za, a bullo dashi ko wani rana da nashi sabon samfarin fitina a gida mata ke nan uwayen kishi da abin mu muke zuwa duniya. Ko karamar yarinyar mace idan suna wasa bakin jin sunce ga kishiyata sai dai ace ga mijina. Hindatu mai farin ciki miji ya zama nata ita kadai yanzu daya ta haihu daya kuma ta samu matsala da maigida. Sai gashi bakin cikin saka sunan yaro kawai ya kauda farin cikin a lokaci guda shedan ya rude ta tafara mugun hali tun mutane basu watse ba. Mijin su jarumin mazane bai yarda mace ta kawo mashi raini don baida wasa da sakaci gurin mace yasan halin matan shi shiyasa yake tsaurara masu sosai bai da fuskan yin raini gare shi. Kowan su fargaban shi take suna taka tsatsan da ala, amarin su don irin hukuncin da yake daukan masu da sunyi mashi abin rainin hankali yanzu ne zai hukunta mace. Gasu su duka ukun kowace na matukar mutuwan son shi a ranta don dai ga ilimi ga kyau ga arziki Allah ya hada ya bashi gaba daya. Sai dai akwai shi da saurin fushi baida sanyi ga duk wanda ya taka shi koda a cikin yan uwa ne. Haka yasa ya zama wani jarumin jarumai ga matan shi da yan uwan shi kowa na kafa kafa da alamarin shi. Muna can muna shagalin buki a part din mu part din Zulfa kuma suna zuba tsiya ne da maigidan. Hala yasa taja kofan part din ta rufe abinta duk wace ta, zo zatashiga zata samu gurin a rufe taki sakewa kowa fuska aga sanyan ta. Shi kan shi maigidan aiken shi ya kai uku amma taki kula shi sai ja aji takeyi wanda shi a lokacin bai ma fahinci may takewa fushi ba hakana. Ya taso yazo da kan shi bai samu fuskan arzki ba haka yasa ya fita batunta ya juya zuwa part din anty. Nan ya tsaya tsakiyan part din yana neman mama Laraba tafito yake fada mata abinci yake son a hada mai akai mashi can tsohon gidan shi don akwai mutanen shi da suka zo mai murna irin su Bashir. Mama tace wanan aikin sai Rahama ita ce tasan kan komai nasu a gidan yana tsaye yasa a kirani nazo na durkusa a gaban shi, yake cewa don Allah ki hada muna abinci kamar na mutum gobe Hamza zai zo ya dauka. Dakin anty na nufa na sheda mata sakon maigidan nasu ta umurce ni da naje na shirys na tabbatar da na hada komai yadda ya dace a hada din. Store na shiga na fito da sabbin kula wanda ta tanada don mijin ta na hada masu abinci irin yadda akai training din mu a training school danayi na two month. Ba a jima ba sai ga hamza driver gida yazo dauka na dinga fitar mai dashi yana jida zuwa cikin mota har nagama komai ya wuce naci gaba da sha, ani na. Yana can yana Allah Allah a fitar dashi a kunya yadda abincin ya samay su yaji matukar dadin hakan don an fitar dashi kunyan abokan shi sosai. Yar aikin hindatu ce taga lokacin da nake mikawa hamza driver abincin maigida taje ta fadawa uwar dakin ta abinda ta gani. Take kuma ran Hindatu ya baci taga ai anci amanan ta don may Saade zata maigida abinci bayan ba ruwan ta da miji yanzu kuma tunda ta haihu ne ? Wani sabon fitina ya sake kulluwa a gidan kuma taiwa maigidan dogon text a waya na tuhumar ya ci amanan ta ya shiga hakkin ta har take cewa tagane kan shi na rawa akan yar aikin saade don yaga kyakyawan yarinyar kada yai tsanmanin ba ta fahinta bane da hakan. Wanan text din yai matukar tayar wa mijin su da hankali idan akwai abinda yaki jini a duniya shine zargi a kan shi yau ga matar shi na aure na mai mumunan zargi a kan shi bayan ta san shi tasan halin shi tasan kuma ko shi waye . Anty ta samu abin arziki sosai ga wanan haihuwan da tayi yan uwa sunzo kuma sun kawo alherin si a gareta wanda ba komai ya jawo mata hakan ba sai halinta na alheri ga mutane shine yau take girban abinta. Yara su sakani a gaba dole na fara masu tanadin party su daga abin snacks da na sha da wanda za aci ai rawa mun gyara gurin tsaban nan yara suka taru Farida tana muna MC ni ina kula da fannin abinci. Can ana ta rawa da ihu har wasu manya sun zo inda muke suna kallon mu, farida ta bada gurin wai mu fito zamuyi rawa ni da Nasir da Hanifa . Muka fito kamar yadda ta bukata aka saka muna kida nan muka fara rawa mu ukun a ka dauki tafe a gurin ganin yadda muke rawa dukkan mu ukn a tsakiyan fili gashi an zagaye muna ana kallon mu. Daidai lokacin ne daddy ya shigo gidan zai shiga gurin anty ganin mutane sun rage yawa sosai shine ya samu muna tsakiyan fili muna ta casan rawa hankalin mu a kwancen. Mamaki ne ya kama shi na ganin harda Nasir yau a tsakiyan fili yana rawa shima tare da mu. Yagirgiza kan shi ya sa kai ya wuce ciki nan yake tambayan anty yadda take son ai mata da naman da aka dawo dashi gurin gadawa a lokacin. Tace bari na turo Rama tazo ta fitar muna ita da mama Laraba ko ? Yace wanan kaunar taki sai ki tafi tsakiyan filin rawan can ki fiddo ta harda Nasir yau a gurin rawan. Dariya tayi tana cewa ikin Allah ashe har an fara party ban sani ba bari nazo na naga may suke yanzu zan turo ta ita da su mama sai ta kama masu . Rawa muke tika sosai a tsakar fili anty tazo ta watsa muna sweets da su biscuits yaran dake gurin suka shiga kwasa ana ihu a karshe tabimu da kudi naira dari biyar biyar dukan yaran dake gurin nawa dana Farida ne taba mu dubu da dari biyar watau guda uku uku. Nan muka shiga sowa kamar wasu kananan yara damu a gurin ta rada min a kunne nazo naje su mama na jira na a waje. Da sauri na fito nabi su mama ban san ina suka nufa ba sai da naga sun nufi part din da duk zamana a gidan ban taba shigan shi ba, koma zuwa kusa da wurin ma ban tabayi ba. Cak naja baya na tsaya sai da mama Altine tajuyo tana cewa dani nazo muje mana nace da dai ku shiga ku fito mama zan jira ku anan. Ke kada ki bata muna lokaci don jiran mu akeyi da sauri na biyo su muka shiga falon yan a zaune shi da bashir da wani mutum da ban san shi ba, nama ne an gada raguna har uku banda na shanun da akai cikin gida masu aiki nata faman aikin tun safe shine kuma tasa muka kwalla da cincin anabawa mutane yan buki. Tsayawa fadin tsaruwan wanan falon bata bakine hura suke suna kallo a tv ana wasan ball sai naji sunyi shiru nan suka shiga gaisawa da su mama can na make bayan mama ina gaidasu suka amsa min a lokaci daya. Anyi kasafi yadda za,a raba nama na kira farida a gaban su mama muka yanka aka shiga aikawa kowa da nasa naman wanda suke nan basu tafi gida ba a lokacin. Nan aka ban na kason Anty muka kama zuwa kitchen din ta nida Farida muka shiga gyarawa. Yaran da na bari gurin party suka kwasa suka biyo ni nan kuma muka kafa wani sabon wasa a kofan har dare muna tare da yaran . Da kowa zai tafi na bashi take awaye da kayan suna suka koma gidajensu don anzo daukan su. Washe gari ban tashi da wuri ba saboda a gajiye nake sosai don haka na dan makara da safe sai dai ina zuwa dakin anty tace na bar yara har monday su shiga school tun da friday ne short day ne dama. Haka yasa na dan kara samun saukin aiki na gama abin karyawa da gyaran part din mu dake bukatan gyara sai goma na gama nai wanka na koma na kwanta don duk nagaji a lokacin sosai. Koda sauran yara suka tashi suna tambayana Anty tace dasu ina nan akwai inda na samu na kwanta kila. Niko na shige dayan part din na Anty da babu kowa a cikin shi na samu guri na kwanta daya daga cikin dakunan part din sai barci. Ban fito ba sai daya saura ko shi yunwa ne ya tayar dani a lokacin na falka ba don barci ya ishe ni ba dai. Ina shigowa kowa na falo a zaune duk suka bi ni da kallo tare da tambayan ina na boye ne ga mama har hankalinta ya daga. Na kalli mama Altine naga duk tana cikin damuwa nace ina wancan shiyan da ba kowa na kwanta na huta. Anty dake ba yaron ta nono tace maza samu abinda kikaci nasan baki karya ba maimakon na je samun abinda nace sai na koma na zauna kusa da ita ina wasa da yaron da ke shan nono ajikin ta. Tace ga yaranki nan tun safe suke ta damun mutane da tambayan kina ina ne na kalli na Nasir dake zaune a takure nace my boy zo gani na dawo kaci abinci kuwa ? May zaici kin san halin shi ai da miskilanci tea yadan sha kadan yana hadiyan bakin rai daya saba nace kai Nasir bana hanaka fushi ba ko , . Zo muje mu karya naja hannun shi muka fice daga shiyan dani dashi sai ga su Amira da hanifa sun biyo mu a baya tare muka zauna muka ci indomie a kitchen din muna hira dasu. Da sauri na tuna jumma, a ne na shirya su suka bi daddy zuwa sallah koda suka dawo nima ina sallah alokacin nan suka samay ni dakin mu suna min hira wai dadyy ya basu kudi sun ba da sadaka a masallaci. Duk abinda suka gani saida suka labarta min shi a gurin ina jin su yanayina dai tun safe dana tashi banjin dadin shi ko kadan a lokacin haka kawai nake jin raina a bace. Sulalewa nayi zuwa gurin anty dake tsaye a kuryan dakinta tana kallon kayan bukin da ta samu jin nashigo take cewa dani yauwa zoki ta fitar min da kayan nan mu gani Rama. Na fara fitar da kayan ne a kasalance cikin yar murya nake cewa anty ko kina da nomban lawal mai waya na garin mu har yanzu ki bani. Da mamaki take cewa yau kuma gida ya biyo maki a rai ke nan ko ? Nace nayi mafalkine da kanina yau shine nake son jin labarin gida naji ko lafiya suke tace gama sai na baki ki kira su. Dama nima ina son nai maki magana idan kunyi hutu sai ki shirya kije ki je ki gane su ko ? Naji dadi don dama ina kewan yan uwana da iyayyena tunda ban taba tafiya haka na barsu ba tsawon lokaci sai auren da nayi ne ya dan rabani dasu na dan lokaci. Turamay kusan guda sabain ta samu duk kuma masu kyau ne sai kayan baby masu yawa sai lokacin ne take gwada min wasu set din akwatina wai daddy ne ya saka masu shi bayan kudin da yabata tai sayayya a kasan waje da suka tafi take cewa Rama ni may zanyi da kaya haka ne wai. Ki duba ki dauki duk a abinda yai maki daga ciki ki bayar a dinke maki su kece yanzu ke da bukatan dinki don ke bazawara ce bace kai anty bazawara kuma ? Nifa nakan manta ma da wai nayi wani aure can inba dai na tuna da marigayi ba gurin addua don kullun nai sallah sai nayi mashi addua sosai. Tace aiko kin kyauta wallahi dama shine tsakanin mu da mamaci ai wanda ke raye a duniya yaiwa mamaci addua a kullun don kyautata naka karshen kaima. ****** ************ ****** Liman ne zaune tare da maigari su biyu suke tataunawa inda maigari ke bashi shawaran cewa yana son ya samu wata gwauruwa ya maye gurbin uwar gidan shi da ta rasu su zama uku gare shi kuma . Liman yacd hakan yana da kyau don sunna ne mai karfi yin hakan sai dai a duba ta gari a gani waccd ya dace don matan yanzu ba kowace mutum zai kwaso ya jefa cikin zurian shi ba ta bata mai zama da iyalin shi. Maigari yace nima Liman tunanen da nakeyi ke nan yasa nabaka wanan shawaran ko za, a tayani dubawa don Allah. Shiru liman yayi sai zuwa can yacd may zai hana mu fada neman wanan yarinyar da ta rabu da Audi mugani ko za, a dace don yarinyar nada mutunci nake gani. Wata ke nan liman yace Asiya mana yar gidan Ali fillo da suka rabu da Audi kwana kin baya tunda taki koma mashi ina ganin zata fi dacewa dakai insha Allahu. Maigari yace kai amma Liman naji dadin wanan shawaran naka din tun tana budurwa naso na nemay ta sai kuma akace ubanta yaba Audi ita shiyasa na bat zancen a raina. Kila rabonkane yasa taki komawa gidan mijin nata don haka sai ka shirya muje mu samu mahaifinta da zancen. Basu yi nauyin kafa ba bayan kwana biyu liman yaje ya samu mahaifin Inna da zancen yaji dadin hakan amma sai yace wa liman zai yi shawara da yar tashi don yanzu ita ba yarinya bace da za, ai mata dole da wanan shawara liman ya koma wa maigari kan za ai shawara da Inna ta bayan kwana biyu zai koma yaji yadda sukayi a can. Da mahaifin inna ya samu inna da maganan sai cewa tayi duk abinda mahaifinta ya gani ita bata da zabi yanzu. Yace shikan idan ta son kan shi ta yarda da auren maigari sabo da yana da mutunci kuma ai bai fi mijinki da kuka rabu ba shekaru nake gani. Haka aka bar zancen kan Inna zata auri mai garin mu ke nan don kowace mace ma zata so ta auri shi idan ta samu. Koda liman yazo jin shawaran da Inna ta yanke mahaifin Inna bai boye mashi komai ba yadda suka yi da yar shi ba aja lokaci ba Liman yace ranan Jumma, a za, a daura aure da yarddan Allah idan ma zata bari sai daga baya tarewa ba matsala. Mahaifin ina ya koma mata da bayanin yadda sukayi da Liman a waje nan inna ta dan shiga damuwa gashi batai wani dogon shiri daya dace tayi ba don bata sa rai zatai aure ba a yanzu. Shiyasa bata shirya ma aure ba yanzu komai bata aje ba da zatai aure ba da shi. Tana cikin wanan tunane ne sai ga Lawal mai waya ya sallama gidan su yace waya ne daga birni akace a kawo wa inna waya za ai magana da ita. Tana jin haka tafito waje da sauri ta saba hijjab din ta zuwa waje don amsa kiran don tasa daga wajen mu ne kiran . Tana dauka taji muryana ina cewa inna ta, kuna lafiya tai murmushi ta kawar da kunya tana cewa kwana biyu ina kuka shige ne ke da maman ki? Nan muka shiga gaisawa tana tambayana labari inda nake nan na shiga labarta mata irin kulawan da anty ke bani da kuma makarantan da ta sakani yanzu ina zuwa. Tace yarinya babu zancen aure gare ki ke nan ko may babakin ba zai yi fada akan hakan ba kike gani ko may ? Nace Inna kwantar da hankalim ki zan shigo zan mai bayani yadda zai fahince ni insha Allahu. Sai naji tace yaushe ne zaki zo garin ne ? Nace sai munyi hutu Inna nan da wata daya da kwanaki insha Allahu anty tace zamu shigo. Sai naji tayi shiru nake cewa inna ko akwai wani abin ne dama ? Tace tau dama dai naso in fada maki ne cewa zan yi aure jibi insha Allahu ranan jumma, an nan mai zuwa. Aure inna gidan baba zaki koma ko ? Tace a, a wani dai zan aura yarinya ai na fada maki bazan taba komawa wanan gidan ba har abada zaman da akayi ya isa tunda shi baida tacewa a cikin iyalin shi sai abinda mace ta sashi yi yake yi. Inna ta wa zaki aura yanzu na tambaya cikin kaguwa da son jin sabon mijin da zata aura din indai ba kuma wani wahalan zata kara fadawa ciki ba again. Tace ba wani bane yarinya sai maigari da ya aiko Liman cewa yana so na da aure ni kuma naga banda zabi a kan hakan sai dai na yarda kawai. Shiru nayi ina sauraren ta har tagama bayanin ta tare da tambaya na ko may na gani a takaice na bata amsa da cewa Allah yasa haka shine alheri cikin rashin dadin rai gare ni. Tace idan hakan bai maki ba ai sai a fasa ko nace haba inna ni na isa na hanaki ra, ayin ki kawai dai ni tausayin babana ne kawai nake ji. Hmm inna tace tace kawai dai na fahince ki yarinya kina kishin mahaifinki ne dana rabu dashi ko ? Na basar da maganan ta nace sai ki kwashi kayan na da suke aje ke nan idan da gyara sai a gyara maki kiyi amfani dasu gaba daya. Tace idan na kwasa kika tashi aure ke kuma fa yaya za, ayi nace Allah ya zai rufa asiri inna kedai yanzu fara amfani da wanan tunda nasan baki shiyawa aure ba a yanzu zuwa yayi maki a bazata kawai. Tace to na gode Allah ya rufa asiri duniya da lahira don Allah yarinya ki kula da rayuwan ki a can kada kiyi watsi da tarbiyan ki da kike dashi a nan duk inda kike ki kama mutuncin kan ki . Nace da ita insha Allahu inna zanyi kamar yadda kike so inna take cewa dani in gayar mata da mama da anty nayi mata kuma godiya akan na nace zasuki Inna Allah ya bada zaman lafiya. Mukai sallama ta mayar da wayan gurin maishi nikuma na shiga wani yanayin tunane nake tuna wani irin zama inna zatayi kuma a gidan maigari idan ta shiga don gidan shima yana da dan jama, a sosai a ciki. Nan dai anty ta fahinci tunda nai wayan nan banda sukuni a tare dani tun lokacin. Batai min magana ba sai da dare take tambayana may ke faruwa taga tunda yamma jikina yai sanyi danai waya ko ance ne na dawo gida ? Nai murmushi nace ba haka na bane anty wai inna ce zatai aure jibi nan take fada min tace ikon Allah Rama inna zatai aure kuma ? Nace fuska a cushe wai haka tace dani da muke wayan, to ke shi kikewa fushi haka Rama ko may , ? Nace anty ni naso ace Inna ta koma gidsn mune wallahi da ta koma tayi hakkuri tunda ta saba da halinsu. Amma inda zata ai bata san halinsu ba can gasu da yara su ma a gidan kuma manya dasu. Wa zata aura ne yanzu nace wsi maigari zata aura tace duk da ban taba jin wani abin asha ba a kan shi tun tasowa na. To aike rama wannan abin alheri ne zata auri maigari dungurun gun kai haba anty don yana mai gari halin shi dana iyalin shi fa a cikin gida. Muryan mamane ke cewa wazai auri maigari kuma Rahama nace wai Inna ta ne zata auri maigarin mu jibin nan mama. Kaikai aiko wanan abin yayi dadi wallahi wani hani ga bawa akace baiwa yanzu Asiya maigari zata aura kaji hukunci Allah kuma ko daga shi har iyalin shi nasan insha Allahu zaman su zaiyi dadi ba irin wancan zaman wahalan da tayi ba a gidan ku na zama karkashin kishiya ko yaushe ba miji ba. Nan dai take kawo halin iyalin maigari wanda jin hakan ya dan sa hankalina ya dan kwanta sosai ga yadda na shiga damuwa da farko. Ranan Jumma,a sai ji kawai mutane sukayi a massalaci ana sanarwa a dakata za, a daura wa maigari aure yanzu. Kowa yai mamaki don basu da labarin maigari na neman aure a garin sai da aka fara gabatarwa ne mutane suka fahinci da Inna ne aka daura mashi aure kaji auren manya ba sai ansan da nema ba sai dai aji daurin aure kawai. Take labari ya karade gari mama na gyaran dawan da zatai madu abincin dare sai ga larai kawar ta tazo da labarin . Nan suka shiga gulma akai suna fafin dama kwadai yasa ta watsar da auren ta don taje hangen nisa gashi ta fada gidan mai gari ai taje su kulu matan maigari sunan nan ta samay su. Lairai tace amma dai kin san taci aba dai ko a hankan gidan maigari fa akwai hutu lauranta kuma akwai ci da sha ba kamar ku nan ba. Sheri kuma zakiyi min inji mama tace ai ba sheri bane sai gaskiya ina zaki taba hada auren maigari dana gidan ku laurantu kuma ko acan fa amarya take. Gashi duk matan shi sun girmay mata ga shekaru kinga ko yanzu amarya take shatafa kuma ta bar maki sudaden mijin ki ki jika kisha ke kadai yadda kike so. Larai nagane dai magana kika zo sola min ba wai gulma ya kawo ki ba tace ai babu soka magana anan sai gaskiya ke dama maigarin kika cuna ma Lawisa ai da yafi mata auren wanan tsohon da takeyi sai aukin susuka kawai kamar bajimi. Ran mama duk a hasale yake dama basu haduwa gulman su basuyi fada ba tsakanin su haka dai suka rabu baram baram. Da dare da baba ya dawo mama ta tare shi da zancen auren inna da maigari. Ran baba yai matukar baci da jin wanan labarin yace amma ko maigari bai kyauta min ba yanzu haka zai min na saki matana ina kokarin mayar da ita sai ya aure ta. Nan dai mama taita zuga shi wai sai ya kwace diyan shi kada ya yarda aje agola dasu gidan wani yace ai haka za, ayi bazan yarda aje min da yarana yawon agolan gidan masu gari ba. Mama tace ita dai Rahama ka barta can gurin yawon duniya ke nan kuma ko ? Kamar yaya yawon duniya kuma shi akace maki tanayi a can inda take yanzu ne ? Idan ba yawon duniya taje yi ba gidan yan uwanka take ko na uwar ta da zata je ta share guri ta zauna can ba labarin komai tare dasu. Shiru baba yayi yashiga nazarin maganganun da mama ke zuga shi akai bai sake tanka mata ba don ran shi yai kololuwan baci sosai a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KAN KI YAR UWA DON AMANA NE ALLAH NA GANIN KI YAR UWA, , , 24 Monday mun koma makaranta bayan an gama shagalin buki na watsar da zancen auren Inna da na saka a raina har yaso ya damay ni sosai. Banda kawa ko daya ni kadai ce ke al, amari na don babu wacce na sani a school din balle na je na daukowa kaina wahala. Idan ban class ina massalaci naje yin sallah sai kuma idan anzo daukana da yamma zan koma gida. Da zaran na dawo banda wani time sai zancen aikin gida girki da gyaran shiyan mu. Sai ma wani lokaci kowa yayi barci an barni ina aiki ni kadai don gudun kada na makara washefgari ke sa sai na rarage aiyukana nake kwantawa. Gashi yanzu na san gari wani lokaci ni anty take aike gurin yan uwanta ko abokan ta ban ta samun matsala da kowa nata ba sai mutun daya daga cikin sisters din ta da tace dani don Allah idan mijinta yana gida anty ta daina aiko ni. A gabana ta fadawa anty hakan sai naji anty tayi dariya tace ina da gaskiya na sister in bake ba wa zai aje wanan zukekiyar budurwa haka a gidan shi mijin shi na gani kullun ya kyaleta. Don dai daddy su Amira ba irin mijina bane aida yanzu ya fara kai mata hari bada sanin ki ba na dauka zanga canji kan wanan maganan da sister tayi a kaina amma sai naga anty ko a jikin ta ita. Haka yasa naiwa kaina kiyamallaini idan daddy yana gari bana yarda mu hadu dashi ta ko ina ina part din mu kumshe sai ko idan nafito zuwa school anty bata taba hankalta da hakan da nakeyi ba don ita zuciyar ta fes yake akaina. Wasa, wasa sai da Zulfa ta kwashe wata daya agidan su mama Zulai ta ga abin bana wasa bane ta nemi sulhu da kanta don da farko takafe sai daddy yaje biko da kan shi ta fada mai son ranta Zulfa zata dawo dakin ta. Sai taga sam diyar ta bata gaban shi idan sun tambaya sai dai taji ai yazo ya tafi ko ace ai baya ma kasan sam ga baki daya. Wanan karon ma basu kasan shida Hindatu sun tafi kasashen turawa don sun kai sati da tafiya gaba daya yaran suna gurin mu a gida. Hindatu bataso barin yarta hannun anty ba amma daddy ya kafe ga haka shine ra, ayin shi sai dai idan zata fasa tafiyan ne ga baki daya dole ba yadda zatayi ta bar yarinyar a hannun anty. Mama zulai ta je gidan hajiyan su daddy inda hajiyan ta kira yan uwasu kaf suka hadu a gidan ta sannan aka aika kiran mama Laraba. Tana zuwa ta fahinci zance ne akan yaransu zasu aiwatar a lokacin, da farko mama zulai ta soma yabawa mama Laraba magana masu zafi sai da hajiyan ta tsawata mata. Take cewa idan har sulhu kikazo nema ki bari ai magana na fahinta a tsakanin ku don wanan abin da kuka dauko hanya ne na koyawa yaran mu wani mugun akida a tsakanin su. Aure dai ne Allah ya hada a tsakanin yaran mu sai hakkuri da junan mu yanzu kada ku bari shedan ya rude ku mu bata zumuncin mu. Gaskiya wanan karon hajiya ta turza don bata tsamaci jin haka ba daga hajiya din. Dole ta sasauta kalamin ta ga yar uwarta nan mama Laraba take cewa Zulai ni banda abincewa don ko a haka alhamdullahi don zumunci yai min rana banda da namiji babba kuma banda arziki amma dan yar uwana ya gwada min ni wata abuce mai daraja a cikin ku. Ban sa Alhaji karami ya kori yarki a gidan auren ta ba asalima ni baiji wanan magana daga bakina ba don dashi da Hindatu duk diya nane. Yadda zan dauki Alhajin haka zan dauki hindatu a matsayi ya a gare ni idan naga tayi abinda ba daidai ba na fada mata ta gyara don goben ta. Cin mutuncin da kukai min keda yar ki daga gyara kayan ka bai taba damuna ba a raina don ni na tsaya a matsayin da Allah ya tsayar dani a cikin na bandashi. Kuma na dade ina bin shi Alhaji karami yayi hakkuri ya dawo da matar shi dakin shi a wuce gurin wanan dalilin yasa yanzu ma ya daina zuwa gurina ya kuma ko daina kirana ga waya yadda yake min kullun. Don haka idan har kuna zargina akan wanan zancen kun dai dauki Alhakina ne kawai shi Alhaji karami baya manta mafari ne shiya sa yai min wanan gatan da kuke gani kamar asiri ne mashi na jaye shi dafa alaka da kowance daga cikin ku don har wasun ku na cewa na asirce ce shi harda ita yaya ina kokarin rabawa da dan ta. Wanda abin ko kusa ba hakana bane shakuwan dake tsakani na dashine tun yana dan karamin shi yakai mu ga haka yanzu ada ai bai wanka ya bushe yana gurina kuma kowan ku ta sani anan. Sai yanzu ne da ya zama wani abu kuma zan mai asiri na jaye shi daga mahaifan shi komay ? Muryan mijin hajuya ne baban daddy ya leko falin yana cewa yin haka ma babban kuskure ne gare ku gaba dayan ku nan wa ya gwada wa Alhaji shi dan shi a baya kamar yadda laraba ta gwada mai. Laraba zata iyayiwa Alhaji laru da kudin ta ba tare da mu nan mun sani ba sai daga baya mu samu labarin hakan a furin shi ko a wani wajen sai yanzu da Allah ya maidashi mutum ne kuke son ku nuna mata bata isa ba da danta. Kinyi kuskure Zulai gurin nuna son kanki dakikayi wa yar uwarki idan dashi ba jarumin maza bane yai maki haka kina ganin diyan ki kaf akwai wanda zai kara kallon daya daga cikin ku nan da daraja a idon shi. Sai sauran uwayen dake zaune suka ce hakane fa Alhaji gaskiya anyi babban kuskure sai dai Allah ya kyauta kawai za, a ce a gyara gaba. Alhaji yace uhum haka nake sin ji don fa abinda kukayi ba abin alheri ba ne don takai har yarki ta fara kyamatar shigan ku gidan dan ku duk kun san da hahakan. Nan sauran suka shiga fadin albarkacin bakin su akan haka mama zulai ta kwatakes ba bakin magana don babu gaskiya. Karshe dai Alhajin su dady ne ya shirya tsakanin tare da kara fahintar dasu karfin zumunci da kuma sakaci da zumunci sukai godiya aka fahinci juna yasa akakira Zulfa dake dakin hajiya tana sauraren su tun farko ta roki iyayyen nata gafara kamar yadda mijin ta yake bukata haka akayi ta tsugunba tsakiyan su tace tasan tayi kuskure don Allah a yafe mata sukai mata dan nasiha tai godiya tamike tabarsu a gurin. Sai lokacin Alhaji yace tau yanzu laraba aiki ya rage naki don kin san halin dakin da tauri tsiya sai kikirashi don yaji da kunnuwan shi gaku a hade an sulhunta asamu yarinyan nan ta koma dakin ta hakana. Shiya kira daddy da wayan shi ya na ganin kiran Alhajin ya dauka lokacin suna tare da hindatu kwance saman gado tana dan shafan shi a hankali kiran yashigo mai. Da sauri ya daga yana mai gaida mahaifin nashi cikin ladabi nan yake ce mai bani ke magana da kai ba uwar ka ce Laraba da yan uwan ta gasu ya mikawa mama laraba wayan takarba da sallama. Saida ta tambaye shi uaya suke can yace Alhamdullahi tace ya gaida hindatu din nan take cewa Alhaji karami zancen matarka zulfame gamu nan gaba dayan mu mun hadu a gidan yaya kan maganan don Allah muna mai baka hakkuri komai ya wuce tsakani ka maida matar ka dakin ta hakana don Allah. Yace mama idan fa zulfa da mama basu baki hakkuri ba kan cin zarafin da sukai maki wallahi bazan hakkura ba. Tace haba dana komai ya wuce nace ma gamuna gaba dayan mu yaya da Alhaji sun sulhunta komai a tsakanin mu ai. Yace to shike nan ta karbi makullin ta a hannun Saade zan fada mata inda na aje mata su ta koma kafin na dawo. Mama Zulai bataso ace diyar ta takoma ba haka zikau sai yazo yaje inda suke amma jin amsan shi yasa tasan ba inda zai tafi ya gama maganan shi ke nan . Mama tai mashi godiya tare da mai nasiha ya tai hakkuri da iyalin shi don mata sai hakkuri komai girman su sukai sallama ya kashe wayan kowa najin yadda sukayi ko banza mama lataba ta kara wankuwa a zukatan masu zargin ta a cikin su. Nan Alhajin su daddy yace gobe yake so mama zulai ta mayar da zulfa dakinta don yau yamma yayi shiyasa ba zau ce ta koma yau din ba gidan ta. Akai sallama bayan yai wa kowan su alheri suka watse kowa ta kama gaban ta cikin jin dadin samun sulhu a tsakanin su yanzu. Hindatu dake kwance a gefen mijinta tana jin komai ranta ya baci don dai ita bataso dawowan Zulfa ba don zaman kishi ke nan bataki ace anbarta daga ita sai shi ba agidan duk sauran su watse ba. Balle wanan yanayin jin dadin da suke ciki a tafiyan da sukayi ji take dama a kullun su kasance a haka tsakanin su dayafi mata komai dadi a rayuwan ta. Ya fahinci bataji dadi ba don yadda ta sauya a lokaci daya ga yadda suke dafarko dashi. Yace kai mata mata wai duk haka suke da bakin kishine gaba dayan su ko may babu wacce ke son ta bude ido taga wata a tare dashi dan dama Saade ce bata faye wanan halin ba sosai a kan su itama tana dan taba nata idan abin ya mota mata ai? Mu dai washe gari sai ga yar aikin Zulfa tashigo tana cewa mama Amira ance na karbo keys a hannun ki already anty ta kwaso keys din yana hannun ta ta ce min na dauko saman drower din ta na bata na dauko na mika mata tafice daga part din. Nace wa anty sun dawo ke nan anty tace ai kin ga shahidi tunda sun karbi key nasan sunyi yadda yake bukata ne shiya sa ya sauko yanzu. Basu da tunane ne abinda yai mama laraba shiyasu don abu daya suke a gare shi amma sai take ganin ita uwar yanzu tafi mama laraba power a gare shi dole ta haukan ta ta taka yadda take so. Ba afi minti goma ba sai ga yar aikin ta dawo tace ance tazo ta dauki hanifa anty tace dani kwaso masu kayan su ki basu ki kira mata yar tazo. Na kwaso na kira hanifa tazo ana kiran ta tana fitowa taga yar aikin part din su sai ta saka rikici tana fadin ita bata zuwa katshe ma ta ruga da gudu ta boye wani gurin na daban. Anty tace a barta idan tai barci za, a kawo matar tafita can sai ga zulfan da kanta tashigo ba laifi tayi sallama nan suka gaisa da anty tana wani cicika tana basarwa ita kadai tace ina Hanifan take ne ? Ai da ki barta idan tayi barci sai Rama ta kawo maki ita zaifi don yanzu idon ta biyu rikici kawai zatayi maki. Tayi mana wayo gareta balle ai da batace zata zauna nan ba na dawo dama rashi na a gidane ai ya kawo tana inbanda nakasa may take anan din haka ? Nakasa kuma anty ta tambaya cikin mamaki tasake cewa Hanifa din ce ke nakashe anan kowa? Ni dai tazo muje ban son dogon zance daga dawowa na yanzu don Allah kuma ace ga abinda mutum yayi again. Anty tace kina so kan Zulfa inda a nakshe take ai da yanzu da kiia dawo batace zata zauna nan ba taki binki wai may yasa ku baku son a zauna lafiya ne wai. Lafiya lafiya dawa dake aike ma kin san ba zaman lafiya tsakani na dake Saade nida kika aure ma mijin da zan aura tun muna yara saboda son kai irin naki kika raba ni dashi da karfi da yaji har kina ganin akwai wani zaman lafiya tsakanina dake yanzu. Tau ai sai kice mijin naki ya sake ni tunda nakine ban sani ba na shiga rayuwan ki dashi kinga sai kisa ya sallamay na bar maki mijin ki. Ban san yaya akayi ba daga inda nake tsaye nace anty babu inda zaki din an samay ki da mijin ki ne wallahi wanan ai rashin mutunci ne duk wahalan da akai maki da ta kuma kizo kina kokarin zagin ta haka ? Ke kefa baki da kunya waya saka bakin ki a cikin zancen mu ni ba saar yin ki bace yarinya don da yarki nakeyi itace saana na. Rama yi shiru kyale ta neman nayi takeyi kije kiji da abinda ke tare dake ni banda likacin haukan ki yanzu. Aiko ranta yai matukar baci da kalman haukan da anty tace da ita tafara balai wai sai anfito mata da yarta kowa ma ya rike nashi ai kowa na dashi. Tafara shiga dakuna neman Hanifa anty ta mike tsaye tace wanan kuma shine bazan lamunta ba kada ki kara shiga min daki ko daya anan . Tace idan na shiga fa may zakiyi tace wallahi wallahi zan maki abinda baki taba zaton ina iya maki ba yanzun nan kuwa. Ke bafa ku kadai ne kuka iya hauka ba kowa ma ya iya cin mutunci Zulfa ina raga makine don zumuncin dake tsakanin ki da mijina kawai. Mijinki gyara dai malama kice mijin mu yanzu kuma ai an wuce wanan tun 1900 sai dai kice mijin mu kawai. Yarinya daine ko to bazan bayar ba tunda bake kiban ita ba ki bari wanda ya kawo ta yazo ya dauke ta da hannun shi idan kuma kin isa bisimilah ki shiga min daki ki gani wallahi ke har tijara kika iya ko hauka haka. Sunyi cin mutunci sosai da gori sai da anty ta daga waya ta kira mijin nasu niko ina tsaye gefe jira nake kawai ta taba anty ta sha kokuwan yan kauye dama na dade ban yi ba tun da na bar zuwa diban ruwan da mama ke turani na barkokuwa a can bakin rijiya. Ganin sun fara magana anty tana cewa heart beat kaiwa matarka magana ta fita min a part kafin nai mata cin mutuncin dayafi wanda tazo min dashi. Yace a hasale Zulfa kuma again wai may zulfa take daukan kanta ne wai nan dau anty ke fada mai yadda sukayi ni dai ban san lokacin da ta sulale ba tabar part din da anty zata barni da naja yar ta nakai mata abinta don ba wani tsiya take muna ba ban da ahagwaba ga fitsarin kwance sai na saka mata permpers da girman ta. Wayan mahaifiyarta ya kira a hasale tana dagawa yake cewa mama kijawa yar ki kunne wallahi nagaji da fitinan da take saka zuciya na koda yaushe a gidana da matana wallahi zan iya datse iyagiyar auren ta akaina bada bata lokaci ba don ta kaini makura wallahi. Hankalin mama zulai yatashi tana bashi hakkuri bai tsaya sauraren ta ba ya kashe wayan ya kira mama laraba da hajiyan shi cikin hasala ya fada masu zai saki zulfa yau din nan. Gaba dayan su su uku sai gasu a gidan nan aka tarasu falon anty ana tambayan baasi anty ta koro magana ta fada masu. Hajiya tace Zulfa banda abinki ai da yarinyar bata jin dadi da batace bata komawa gurin ki ba yadda kikayi baki kyauta ba gaskiya ina laifin wanda ya rike ma da. Sai kawai ta sa kuka tana cewa ita komai tayi sai ace batai daidai ba kowa ta fahinci yanzu an tsane ta bamu tsane kiba baki fadan kan gaskiya ne zulfa. Maihaifiyarta tai mata tas tace kuma tabar yar in mijin su ya dawo shida ya kawo ta ai dole ya dauke ta ya mayar mata da abinta can. Suka ba anty hakkuri don a zauna lafiya suka tagi kowa na fadin albarkacin bakinshi uwar taja mata kunne ra fada mata yace zai sake ta ayau din nan. Tace saki fa mama tace wallahi haka yace min jin kalman saki yasa ta shiga hankalinta da dare sai gata wai tazo ba anty hakkuri anty tace ai ya wuce ko a faki gaba dai don yaro na kowa ne ai. ****** ********* ****** Rashin dawowan dady ne ya hana tafiyana gida gashi munyi hutu kamar yadda anty tace zan tafi gida idan mun samu hutu lokacin har anty tayi arbain ko da haihuwa amma daddy bai dawo ba suna can da hindatu kasan turawa. Ni dai ban san may kuma zan tsaya jiran Daddy yi ba ni da zani gida gurin iyayyena a lokacin. Basu dawo ba sai ana saura sati daya mu koma school suka dawo da safe suka sauka garin. Gida ya kaure da murna don duk yara suna gidan a lokacin ana hutu ko ina makarantuni gaba daya. Nidai ban saka su a ido ba ina ciki ina aiyukan na lokacin Farida ta shigo gurin mu tai muna kwana biyu a bakinta nake jin wai hindatu ta hadu tai wani irin kyau da ita har daddy din shima yai kiba ya kara haske sosai. A raina nace ai dole ya katare ya bar min anty na nan da wahalan yaran da ba a ko gode mata ba dole suyi kiban su ba suna can hankalin su a kwance abinsu. Ta damay ni da zancen su wanda ita bata san ina taya antyna kishin hakan bane a cikin rai da ta isheni da zancen na ce haba Farida labarin ya isa haka mana yanzu bagata ta dawo cikin yan uwa anjima kadan kina iya jin muryan ta inda sune masu fitinan tsiyan nan ni fa basu burgeni don rashin mutuncin su. Dariya tai min tana cewa ke ko ba ai maki abin arziki idan baki so ba fa Rahama ? Na dauki kayan wankin yara dana kwasa na shige dasu dakin mu na barta nan zaune a falo tana kallo. Yaran duk basa nan suna gun daddy da ya dawo haka yasa nai aikina a tsanake har tsawon dan lokaci na koma falo na kwashi na anty na nufi dakin ta dashi. Ban san yana cikin dakin ba a lokacin don da ban shiga ba ina shiga ban jira amsa sallama taba na fada dakin ina cewa anty wai ko kin san yau saura sati da yan kwanaki mu koma schoo, , , Maganan ta makale min ganin daddy danayi zaune tare da matan shi a saman gado tana kwance ya zauna ya raba hannayen shi a tsakiyan ta yadda take a kwance din yai mata runfa suna magana. Da sauri na juya zan koma inda na fito muryan anty ne kece ina kuma zaki rama kun gaisa da daddy ne da ya dawo. Cikin jin kunya ga kaya a hannuna haka na tsuguna ina cewa sannu da dawowa daddy andawo lafiya yaya hanya ? A hankali batare da ya gyara zama a yadda na samay su ba ya amsa min gaisuwa na. Na aje kayan da sauri na juya zan fita daga dakin muryan anty ne ke cewa Ramana don Allah duba can ki dauko coffee ki hada mashi mai zafi kwarai. Nace tau anty na matsu na bar dakin don a takure nake nako kasa daga idona na kara kallon yanayin da suke ciki a lokacin. Nace akwai ma ruwan zafin dana jona yanzu zan hada abu dashi tace ta juyo min sai ki hada mai please . Na koma kitchen da sauri na juye ruwan da har ya tausa ko a cikin dan karamin flaska din da take mai amfani dashi na hada cup na kawo masu shi. Yanzu na samu sun gyara zaman su tana zaune da kyau tana bawa dan ta nono shi kuma yana wasa da kafan yaron saida na tsaya daga kofa aka bani izinin shigowa dakin na shiga. Tace dani yauwa sannu Rama da kokari don Allah hada mashi coffee wai dashi zai tafi can gurin shi. Na hada kamar yadda ta umurce ni nace da ita an hada wanan karon shine yai godiya yace nagode Rahama ya mike tare da mika hannu na miko mai. Har yakai kofa take cewa dashi dama Rama ta matsu kadawo tana son shiga garin su ta dubo gida nice na hanata kada su tafi su barni ni kadai don nasan mama ma kafar Rama kafarta. Tsayawa yayi tare da juyo yana kallon inda nake tsaye yace ince dai lafiya zata tafi ko ? Ni da anty muna hada baki gurin cewa lafiya anty tace kasan tunda suka zo bataje gida ba shine na kwadaita mata idan anyi hutu sai ta tafi sai kuma hutun ya kama baka gari a lokacin gashi har suncinye hutun nasu ma a gida. Yace ok a bari na dan huta zuwa jibi muga abinda za ayi ga tafiyan nasu tace Allah ya kai mu lafiya. Ta juya inda nake tana cewa yanzu sai kwadan ki ya fada Rama nasan dama shi kike son tuna min dazun da kika shigo ko ? Nai murmushin jin dadi nace anty kin san Inna tayi aure shine na matsu naje naga wani irin zama sukeyi a gidan ta da mutanen gidan. Tace gulma dai ina ruwanki tunda kikaji shiru aikomai daidai ke nan a can kada fa kije ki tayar mata da hankali Rama ? Nace wace ni ni dai ina son zuwa ne nagan su kawai wallahi tace to sai ki fara shiri daga yau ke nan ko ? Tunda ma Farida tana nan ai bazan ji kadaici ba zan rike ta har lokacin da kika dawo don yanzu jikina ya saba da hutu kin lalatani zuwan ki. Kuma fa kinga danake samun hutun har nafi lafiya ga baya da ko yaushe ina cikin ciwo ne ba lokaci. Nikan zumudi ina fita na fara shirin kayan tafiya na duk kayan da nazo dasu dama na ajewa Inna su tunda na daina amfani dasu nakuma kara mata cikin wanda na daina sawa tunda ko yaushe cikin dinki nake a gidan anty. Acewan ta fita da mutunci shine hasken mace a lokacin nan don in baka shiga ko mata yan uwanka sai suyi gulman ka. Farida ce ta shigo ta samay ni daki ina ta saka kaya a katon ghana most go tace dani kai Rahama bakin ki bai da kyau wallahi. Ga fada can ya kaure a tsakanin matan gidan dama kin fadi ai anty Zulfa da hindatu ke fada wai bata gama girki ba zulfa ta shige mata gurin mijin ta. Nace jikuma wani fitina don Allah may ye na fada cikin haka ita da taje kusan wata biyu fa suke nema tare da miji shine na dan yau kawai har take fitina akai. Koda yake ma itama zulfan taku maganin ta ke nan don ba mutunci ne da ita ba ai. Fitina sosai sukeyi har takai kowa ya fito yana sauraren su sai kysan fadan yai nisa na fita gurin. Gori da zari sukewa junan su kowa na kiran dan uwa da munafuki a tsakanin su abindai ba dadin saurare wallahi. Shigowan maigidan ke nan a hasale ashe ma baya gida a lokacin yana waje da bashir dayazo gurin shi bai shigo ba. Tun daga nesa yake fadin wai yaya haka may kuma ke faruwa ne wai haka , ? Nan sukai shiru kowa na mazurai sai zulface tai karfin halin cewa jimun wanan banza zuwa tayi ta samay ni wai akan may zan shiga gurin ka bayan nasan ba nice da kai ba sai da yamma. Yace stupid, idiot , akan wanan dan maganan zaku tayar min da hankaln gida haka baku ko jin kunyan ku murya na ne ya ratsa gurin nace oya Amira hanifa Nasir kuzo mu shige ciki may kukeyi anan maza kuzo mu shiga daga ciki. Gaba daya suka juyo suna kallona ina tattara yaran murmushi yadan yi dul yadda yake a hasale yace U C kungani kuna fitina kan abin kuya yaran ku na sauraren ku for god sake wani irin tarbiya kuke gwadawa yaran nan ne haka please. Mukan mun shige mun barsu nan ashe bayan shigewan mu yake cewa babu wace zatai girki yau Saade ce zata karbi girki tunda tayi arbain ina shike nan zance ya kare ko ? Farida ne ta dawo take fada muna hukuncin da ya yanke a kan fitinan wanda hakan baima anty dadi ba don sai naji ta hau fada tana cewa wani irin ni zan karbi girki kuma ni har yaushe na gama covery din ansan wani girki can ni ban son fitina wallahi. Muryan shi ne ya ratsa falon yace hukuncin danaga daman yankewa ke nan a gida na sai kuma may ? Shiru tayi tana kallon shi ta bude baki tana cewa amma dai kasan gaskiya ba a kyau, , , Hy madam na gama magana na ni is left to you now idan ma bazakiyi ba matsalan ki wanan ya juya ya fice rai a bace. Mama dake zaune tace may ma zai hana ki yi sa, a tunda kinyi arbain may kuma yarage yanzu ina ba kece zakiyi wani aiki ba can yaran ki ne gasu nan masu yi may zai kawo maki fitina kuma da mijin ki yanzu. Amma mama bisabillahi har yauahe nai arbain din da zai jawo min wani aiki can kuma yaja min fitina a kaina. Mama tace ke saade na rabaki wallahi da virman ki zaki tsaya a gaban yara kina mussu da mijin ki a kan gaskiyan shi kuma? Shiru tayi tana sauraren mama zuwa can ta mike a hasale ta shiga dakin ta dauke da danta dake barci a hannun ta. Tunda ta shige daki ta rufo bata fito ba ina ganin karfe biyu yayi ina idar da sallah na dora girkin abincin dare . Tuwo nai masu na farar shinkafa da miyar agushi nai amfani da manja akwai naman shanu dashi nai masu amfani sai ganyen dana saka kadan a ciki na egu nai miyan dashi. Sai na hadda mai ferfesun kayan cikin rago ma hada hafin gargajiya nayi na zuba a kulolin daddy na hada fruits salad na aje ban zuba madara ba sai za, a fita dashi. Sai bayan karfe biyar ta fito falon lokacin ina daki na fito wanka tace Amira ta kirani. Hijjab dina kawai na saka na nufeta ina cewa gani anty cikin cicika take cewa may za, a girka mai ne naci da daren nan ? Nace ni da tuwo nayi na farar shimkafa da miyar agusi sai ferfesun kayan ciki da fruit's salada dana hada ko baiyi ba. Sai lokacin naga murmushi a fuskan ta tace kai Rama baki da dama wallahi kamar kin shiga raina kinga nufina don ni ban koyi tunane hada mai salad din da yake son sha da dare ba ai sannu da kokari nagode kinji Ramana. Kai haba anty sai kace wani abu har da gode min tace ai ba don ki ba ni wallahi na ma haune sosai nace kiyi hakkuri anty may ke cikin girki kuma ? Tace hmm Rama ke baki ganewa ne wallahi amma fita ke ga daddyn nan naku wallahi. Bayan na shirya nazo na karbi dan ta da muke kira da jinior na goya shi ina cewa magariba yayi anty kawo shi in saka shi a baya. Har akai sallah yaron na gurina can sai gata ta caba kwalliyan ta ta shigo dakin mu ina tsaye ina jijiga yaron daya dan motsa Farida na saman gado kwance muna hira. Tace Rama zo muje kitchen ki fitar min da abincin nasa mugani tare muka fita da ita zuwa kitchen din ta samu komai na hada yadda take bukatan a hada mata shi tace sannu da kokari yar albarka ranan da kika barni kan ai zan sha fama wallahi. Nace cikin turo baki ni ina zan tafi in barki haka anty muna nan wallahi dake tace bazakiyi aure bane haka zakiyi ta zama a gida ke nace auren may kuma ni da zan zama likita inyi ta aikina ina maku allura. Dariya tayi tace yar sheri akaina ke nan likitancin zai fara nace to anty gani gida wani likita kuma za, a kara kira maki idan na gwanan ce. Baki da dama wallahi tana tsaye tana kallo na na hada fruits salad din na zuba a cikin wani bowl din ta mai fadi dama don salad akayi shi kawai. Nan dai na ta fara fita da kayan nabi bayan ta da saura muka kai part din shi a babban falon shi na gidan muka jera a kan dining table. Zan fito tace na tsaya mu dan kara gyara part din tare muka gyara komai na fito na barta a cikin part din nakama gabana nikan. Har dare yaron na abayana babu duriyan ta a furin mu mama tace dakariya tana so tana kai kasuwa Allah ya rufa maki asiri kin hadu da mai kaunan ki tsakani da Allah. Can gurin daddy kuma yana cin girki yana yaba dadin shi tave wallahi bani nayi ba aikin Ramane Nan take fada mai tashi tayi ta samu kawai na gama hadawa indon itane ma aida har lokacin ba, a gama ba, Yai murmushi yace nadai gane yarinyar nan ta bata ki yanzu da son jiki idan ta tafi ban san yaya zakiyi ba ai. Take fada mai yadda mukayi da ita shima dariya yayi yace a kanki ke nan za, a fara gwada aikin nata tace kyale dakariyar yarinya kawai. Yace amma ni ina mamaki wai kamar wanan yarinyar ace ta taba aure haka mutane basu da tausayi wallahi. Tace aida kaga wanda ta aura din ne ma wallahi yafa fi Alhajinka tsufa Allah ki. Yace kuma ta zauna dashi tace yaya zatayi kasan halin kauye da yaran kauye gurin biyayya. Yace an dai hadu da mai tarbiya aiki kauyen yanzu sun waye sun rage wanan abin don ilimi yakai ko ina babu maiganin ta yace wai tayi wani aure can a baya. Tace a dakin tama fa ta fadi yace kai tace wallahi ai in tana ma mutum hira sai ka sha dariya har yanzu fa Rama bata san kan aure ba barta dai rashin kunyan su na yan kauye yanzu kuma na samu duk ta barshi dan training din data samu yace aikin kyauta mata wallahi. Shi ya bijiro mata da maganan tafiya na tace ya kamata ne a dan yi min sayayya da zan tafi dashi. Yace zai duba gobe ya gani naga ta matsu da zancen ai jibi sai hamza ya kaita ko tai mashi godiya suna ci gaba da hiran su. Zulfa ce ta shigo ta samay su wai zancen yar ta yace wai Zulfa may ke damuwan kine haka please? Anty tace No wallahi tayi kokari bari naje idan batai barci ba na kawo maki ita yanzu ba shike nan ba. Yace No ki barta har gobe idan Allah ya kai mi yanzu sunyi barci ko tace shike nan Zulfa tafice fuuu da ita daga falon tana kunkumi a bakin ta. Ko da ta dawo ta samu na sauke jinior ina cire mai permpers zan saka mai wani take cewa ya tashi ko nace eh ya falka amma na bashi ruwa yasha ya koma barci Tace ko na bar maki shi ku kwana nan ke nan tare nace Anty rufa min asiri kin san halin jinior idan yaso nono ya bare bakin nan baijin lalashi yanzu ma saan shi naci bai min kukan ba ai. Sai da ta hada komai da zata bukata a can na yaro danata a cikin wata yar jakka tai min sallama ta tafi na rufe part din namu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KADA KI TURAWA WANDA BAI BIYA BA PLEASE IDAN KIN YI HAKKA KIN CI AMANAN ALKAWARI YAR UWA ALLAH NA GANIN KI, , , , 25 Da safe bata fito ba sai wajajen karfe goma saura ta sauko daga dakin shi mukan har mun karya muna kallo a lokacin. Sai dai abincin su yana shirye na hada komai daya dace ai masu tayi wankan ta tun a can ta shirya yaronta tana shigowa ta miko min shi ta shige dakinta ta saka tufafi a jikin ta. Bayan tafito ne take tambayana abin karyawan sun na fada mata abinda nai masu na karyawa tace har da pepper chicking kikai muna nace Allah yasa dai yai dadi anty zaku iyacin jagwalgwale na ma kuwa ga yacan dai na shirya. Ta kwasa ra nufi gurin shi da kayan abinci taba shiryawa ya fito a cikin shirin shi dama yana sauri ne . Bashir na jiran shi zasu fita zuwa wani state daga bayan ta yake cewa har ina batun fita nasan bazan samu karyawa ba don yanzu kika fita. Tace ka manta da Ramana tana gidan yace yanzu dai na tuna ya dan dafa mata baya ya ja kujera ya zauna tana fara budewa kamshi ya daki hancin su baki daya kwai yaji albasa a cikin sa sai bread da nai torseting nashi yaji hadi ga ruwan tea a flaska da wanan kazan dana gyara masu. Nan suka zauna ci sai ga bashir ya shigo falon tare dashi suka zauna ya fara ci shima yana zuba santi yana cewa wai ko Saade akwai macen da ta kaiki iya girki jiya na tafi ina sanyun tuwon ki har amina na min sheri yau kuma ga wanan haka . Tace aikin kaunata ce yace wanan yarinyar dake gurin ki kike nufi ko may yanzu itace keda wanan hadin haka ? Don Allah saade ki ban ita mana na aura dama ina son karin mata kinga abin yazo min da sauki ke nan a gida nai gamo. Don wallahi ko banza dai yarinyar dama ra hadu sosai tun randa na fara ganin ta nasan za, a rina anan. Don Allah bashir ka rufa min asiri kada kasa Amina ta fara min kallon up side down muna zaune kalau. Kaji matsalan ku mata wallahi da ankawo zance kuce ga kabali ku bata maganan. Daddy ya dauki ruwan shayi yana kurba a hankali kamshin kayan yaji ya daki hancin shi bashir yace saka min baki mana mutumina. Yace kun fi kusa ba ruwana wallahi matarka ta koreni idan naje yace kaima ka mara mata baya ke nan ko ? Nan dai sukai ta hiran su daddy yana jin su bai tankasu sai da yaga bashir na kokarin su makara yake cewa don Allah idan ka gama shirmay ka kazo mu tafi don Allah. Nan bashir ya mike har yakai kofa ya dan dakata ya juyo tare da durkusawa a kasa yana cewa tau anty mun gode sai mun dawo ke nan ko ? Tace ban son sheri ko da gaske na girmay ku din ne da ake fadi na girmay maku na aure ku ina maku wayo. Ya mike tare da daga kafadan shi yana cewa badani ba cikin wanan zancen ni gwaunatina na fara kafawa don neman kamun kafa. Tace ba gurina ba ni dai tafi lokacin daddy ya karaso inda yake yana cewa don Allah muje da shirmay ku ? Yace kai shirmay fa kace malam ina zancen shirmay ana maganan aure anan nagafa kuna son hade min kai kai da besty ka Yusuf ? Nan suka fice suka barta tana hada kayan abincin takirani ga waya mukazo muka kwashe zu part din ta. Lokacin ne take fada min gobe ne in Allah ya kaimu tafiya na ai mama naji tace gyara zancen ki don nima na tashi ke nan. Dariya muka sa mata anty tace dama na sani mama tashin Rama tashin ki ita da zata tafi ta dawo kwana biyu fa zatayi kawai. Nai saurin juyowa na kalli anty jin tace kwana biyu kawai zanyi tace to da kwana nawa zakiyi kuda kuka koma school. Mama kan harta mike ta shiga shiri ba kakautawa ita a dole gida zata take cewa indai ba so ake sai yaro ya girma ba su kore ni da kafan shi. Duk laladhin da anty zataiwa mama amma mama taki yarda dole itama aka fara shirin nata tafiyan. Kayan da anty ta zube muna wai tsaraba abin ba a cewa komai don ni dai an wa inna sayayya masu yawa da kanne na samu sun samu harda baba bandir din shadda guda biyu ga kudin dinki. Mama Laure ma turamay wax guda biyu su sabulu dasu omo da man shafa an saya mata su har kakanina da maigari da matan shi sun samu tsaraba gurin anty don mijin ta yaba da kudin enouhgh akai muna tsaraba dasu. Ga buhuhunan shinkafa na baba na da maigari da jarkan mai guda biyu da sauran abubuwa abin ba, a cewa komai wallahi. Sutura kan da su kula har da kayan mata anty ta hadawa inna ta su wai duk nata ne ita kadai bayan buhun kayan sawana dana tara masu a lokacin. Tunda yaran sukaji zan tafi suka saka kuka suma dasu za, a tafi har yar gurin su hindatu da zulfa wai sai sun tafi. Ita dai anty ta cewa na shirya yaran ta na tafi dasu kawai taiwa daddy bayanin yaran sun nace zasu bini bai so naje dasu ba amma sai anty take cewa tariga ta yarda naje dasu bata san yadda zata ce kuma kada naje dasu ba. Dole ya hakkura amma yasa akai sai abinda zasuci idan mun tafi can kauye sai da aka shage but din bakin Jeep din Daddy da kaya muka kama hanya su hanifa nata faman birgima wai sai sun bimu. Amma iyayyen su sun rike su ba inda zasu kauye a halaka masu diyan su cewan zulfa yar ta tillo daya akai mata kauye a sirce mata ita nan ma yaya aka kaya da ita tana kin ta balle taje can gindin maganin ai sai tace bata san ta ba ma nan gaba. Daddy ya ce will you stop dat rubish zulfa waike baki da hankali ne ko may su yaran da za, a dasu sunfi hanifan ne ko may ? Tace oho dai koma may ye ba a zuwa min da yarinyar a halakata a banza ya tsawata mata taja yarta suka shige part din ta tana faman turje turje a kasa sai tabi mu. Mun kama hanya sosai Nasir tana lafe a jikina a gaban mota sai daji da yan kauyu ka muke wuce wa. Karfe sha biyu mun isa kauyen mu ina kallon mutane suna al, amarin su irin na kauyuka kamar yadda aka saba a baya da muke can. A hankali na sauke ajiyan zuciya daga inda nake zaune tare da lumshe idanuwa na yau gani a cikin mahaifana zan ga tan uwana da mahaifana da abokan arziki duk da ba abokai ke gareni ba ni. Kofan gidan mama Altine motan mu yaja ya tsaya jiyiiin take hankalin mutane ya dawo kan mu ana son ganin ko su waye a cikin wanan irin dan kareriyar mota haka. Muna na fitowa su Rukaiyya dake tsaye kofan gida da saurin ya illo suka sako muna idanuwa. Ina fitowa gurin ta na nufa da dariya ina cewa Anty Rukaiya ta bude baki tana cewa lah Rahama kece kizama wata yar birni haka kamar baturiya dake ? Tana dafani tana bi da kallona har bayana zuwa takalman dake kafana sai tace eyye Rahama ke kan ai kinji dadin ki wallahi sai faman tabani takeyi. Nan aka turu ana kallon mu cikin sha, awa ga su Amira duk sun make muna ajikina kamar za, a kama su a lokacin. Murtqn mama Altine ne ke fadin ke Rahama zo ki nuna mai kayan da zai sauke muna anan. Da sauri nabar mutane nayo gurin ta sai cewa suke auyyo har da tafiyan ta ya sake wallahi Rahama ke kan kin ji dadin ki wallahi. Na nuna ma hamza kayan mama ya sauke mata na nuna mai wanda za, a shiga dashi gidan mu nan su Rukaiya akabi buhun shimkafa suna ihu da murna an samu na sulalawa. Dama tun can anty ta fadawa mama mu sauka gurin Inna na mu debe mata kewan rashin mu kwana biyu da tayi. Muka shiga mota ina daga masu hannu nace zanje na dawo anjima muka wuce nan muka barsu a tsaye sun bimu da kallon mamaki. Ana shiga da kayan cikin gidan mu mama Laure tana tsaye tana shurin fitowa don taji ana ihun ga Rahama ga Rahama tafito tana ashar tana fadin ina yar jakar uban shegiya ta dawo yawon ta zubar din ta ta debo cuta zata lakaka mun, , , Sai tai shiru ganin yara na mulmulo buhun shinkafan gwaunati a cikin gida ga jarkan mai da doya tagani. Rukaiyya da murnan ta take larabarta mata yadda na koma tace ke rufe min baki wace bata san ciwon kan ta ba . Gashi yanzu taje birni ta bude ido tafiku ke nan fa ake nufi yanzu fa ? Rukaiyya tace don ma baki ganta bane mama ina zaki hada mu da Rahama yar birni da ita ko tafiyan tafa na yan gayu ne yanzu tana gwada wai yadda nake tafiya a gaban mama din. Haushi ya kumay mama takai mata rankwashi a kai tace ja can ki bani guri mara tunane kawai. Kamin mu boye kayan nan daga ciki tun su Larai yan gulma basu shigo sa ido ba yanzu ki gan ta gidan nan tashigo. Suna gamawa kuwa sai ga Laira na sallama tace may na fada maku lairai na fadin ance yan birni sunzo harda abin arziki tana raraban ido bataga komai ba. Tace ance har da abin arziki mana tazo maku ina yake mu rage kyayan idon mu kada a bamu labari. Mama tace sai uban ta ya dawo idan yace a fitar zan fitar kowa ya gani tace ai kin fi danan Lauraru yanzu da ci yazo nine abin gudun ki kuma ko ? Ina nan muka hau mota har birni dake dakyat muka sha gurin neman ta a can yanzu tazo da abin arziki zaki boye min ? Mama tai mindinkis taki nuna mata komai har tagaji ta fice a gidan tana cewa aikoma maye muji ai idan yai wari. Mama tace sai ku jira har tai warin kuji ba dai yanzu ba kan ban son sa ido da gulma wallahi. ****** ********* ****** Kofan gidan maigari nake mashi kwatance har ya kaimu suna zaune ana fadan ci fada tacika da manyan gari sukaga mota ya tsaya kofan shi. Yan fada suna fadin ku gyara ga baki nan daga birni anyi aka shiga kakabe tabarmi don naki su zauna akai. Sai ganin sukayi na bude mota na fito babu wanda ya shedani daga cikin su har na fitar da yaran daga mota dagani har hamza muka nufi inda suke zaune sun kura muna ido kawai. Tun daga dan nisa kadan na cire takalman kafana haka yasa su Amira ma cewa zasu tsaya su cire nasu najasu nace suzo mu karasa hakanan amma sukaki don Anty tace duk abinda sukaga nayiwa babba suma suyi hakan. Mun karasa na dan tsaya daga nesa ina gaidasu suka karba da maraba yarinya sannu ku dai da zuwa suna gaida mu da hanya. Wani daga cikin su yake cewa yarinya daga ina haka bamu sheda ki ba fa ? Nace baba Rahama ce yar gurin Audi mai awaki salati suka saka a lokaci daya suna Allahu akabar an koyi haka wallahi yarinya kece kika koma wata jamian birni bamu gane ki ba ? Mai gari da kan shi ya daga saman kujeran shi yana mika hannu Nasir yazo gurin shi. Tun nan na fara fahintar akwai zaman lafiya a tsakanin shi da mahaifiyata yadda muka samu taron arziki a gurin shi haka. Na mike na nufi cikin gida tsufi suka bini da idon gulma suna ikon Allah birni take da Altine mai kuli kuli gurin yan uwanta tunda uban ya koresu a gidan shi. Liman ne ya dakatar da zancen da aka dauko namu yake cewa haka ba kyau yan uwa ku daina don Allah. An bude bayan buth aka fara fitar da kayan mu daga ciki ai take gulman fada ya koma kan kayan da muka zo dashi. Liman yace masha Allahu alherin Allah ya sauka a gidan maigari ke nan abinda ake wa gudun zuciya ke nan yau gashi yar da ya saki uwar ta akanta ta zama alheri a gari. Nan dai yaran maigari suka biyo bayan mu da kaya daga kofan zaure na biyu na tsaya ina sallama. Wata mata nagani baka doguwa da ita ta amsa min sallama na sai ga inna ta fito daga dakin ta dauke da wani roba a hannun ta. Tana ganin mu tace yaya bakin ki ne daga birni fa matar tace bakina amarya ban ko sheda su ba wallahi. Inna cikin kawaici tace yar gurin ki ce diyar Audi dake birni da mai kuli kuli, matar cikin fara, a tace ikon Allah Rahama kune tafe sannun ku da zuwa ta shiga washe baki kamar ta taba sani na a baya. Nan ta kwadawa wata kira Rahamu fito munyi bakuwa fa ga yar mu tazo yau sai ga mai suna Rahamu tafito daga dakin ta tace to daga ina yaya tace yar gurin Amarya ne mana dake birni tazo. Suka shiga murna da ganin mu Inna ko ta basar kamar bata gan mu ba lokacin. Dakin Inna suka kai mu nan kuma ake shiga muna da kayan mu cikin dakin nata na sheda dakin tane ganin kayan dakina na da aciki basuyu komai ba har wanan lokacin sabbi dasu kamar sabo. Matar ta biyu ne takawo muna ruwa a kwanon sha mu sha sai ni kadai nasha yaraan sunki sha nasan akwai daga ke nan dasu. Kayan mu kaf an shigo dasu gidan sai ga maigari ya shigo yana cewa asama ma bakon nan da yakawo yaran nan dan abin tabawa akace sai dai a sayo mai hura ai mai damu. Hakan akayi harda mu mun sha huran don yaji kindarmo sosai a cikin shi sai gashi ya dawo yana cewa bakon yace zai tafi ke nan na fita nai mashi godiya yake fada min maigari ya bashi zabbi da kaji kyauta nace madallah an ko gode ya gaida su Anty ya kama hanya tafi abinshi na koma cikin gida abina. Na samu yaran sun buge ga huran da suka sha har sun soma barci a inda suke zaune a takure na cire masu takalman su na gyara masu kwanciyar su. Na fita zuwa sallah don lokaci yayi suna cewa wai ba, a kira sallah ba nace lokaci yayi ai nai alwala nai sallah nima na kwanta a gurin sai barci sai da aka kira sallah laasar na falka koshi don sabone dayin sallah a cikin lokacin ta sai kaji da zaran lokacin yayi kamar an tashe ka haka sallah yake ga wanda ya saba yinta akan lokacin ta. Bayan na idar ne na fito zuwa gaida mutanen gidan daya bayan daya nake shiga dakunan su na gaidasu a cikin mutunci na dawo na samu yaran sun falka na kaisu sukai fitsari na rage masu kayan jikin su don su sha iska. Lokacin inna tazo dakin muka gaisa da ita take tambaya na yaya wajen su hajiya Saaden suna lafiya dai ko nace lafiya kalau Inna. Sai dan shiru nace Inna da alama dai zaman gidan nan kamar ba matsala nake gani ko ? Tai murmushi tace gashi kin bada amsa da kanki bamu matsalan komai yarinyar yanzu ne ma zan iya ce maki nasan nayi aure ina da incin kaina babu zaman takura ko kadan. Na dan hade rai jin tace nan yafi gidan mu ta lura dani tace ai gara na fadi gaskiya yarinya kina da wayon ki san zaman da nayi a gidan mahaifinki na takura a baya. To nan din babu shi gaskiya kin ga idan nace maki akwai shi na dauki alhakin mutanen gidan nan. Nace hakane kuma nan nake tambayan ta kanne na tace mahaufinki ya aiko da zan tare an dauke su amma dai sunan su tafi anjima kadan zaki gansu sunzo don anan suke cin abinci dare da rana. Tunda can ba wani kula suke samu ba gurin uwar taku sai wahalan banza shiyasa ma shi malam yace su dinga zuwa nan ko yaushe suna karban abinci yanzu haka da kwanon su dare da rana a gidan kinga ko ina laifin hakan don ko hakan da aikai min ai ya wadatar ko ? Nace hakane gaskiya Inna suka ban tausayi sosai nace suna karatu ko tace sunayi kin dai san yadda kararun kauye yake ne ai sai a hankali in ba irin ku da suka dage gayi ba din. Nan dai muke ta hira jefi jefi ina mata hiran gidan su anty tace wai mata na birni ashe kullun cikin fitina haka ? Ai namiji idan ba jarumi bane sai ya zabge ko yama tsiyace fitana fa ga kishiyoyi baida kyau ga addini halaka maigida yake yi irin hakan . Na fara fitar da tsaraban da muka zo dashi tun Inna tana godiya har yakai tayi shiru ta kura min ido ina mata bayanin komai dala dala. Na nuna mata buhun kayan danazo dasu nace ta tsinta wanda take so sauran sai nakaiwa su Rukaiyya. Nan ne nake cewa niko sai banga Lawisa ba a gida da muka sauka naga kowa acikin su. Inna tace baki da labari Lawisa tayi aure ne a dan yanayin mamaki nace Lawisa tayi aure Inna ? Tace tayi aure a madadin ki gidan jatau kan mudin shi da maman mu ku taci shine hukuma ta tilsta mata bada yarta daya gareshi. Na tausayawa Lawisa kwarai dajin wanan labarin abinka da dan uwa sai naji ba dadi daidai lokacin da inna take ta faman daga kaya tana cire wanda take so a gefe daya take cewa kina tausaya mata ai ke suka so gani cikin wanan yanayin. Nace hakane kuma Allah aiba azzalumin kowa bane ya sama yana kallon halin kowa daya halitta ai. Nan dai muka sha hira take cewa akwai yan mata a gidan suma ta zaba masu kala uku daga ciki nace ba matsala inna. Tafita bawa kowa tsaraban shi take naji gidan ya kaure da murna suna zuba godiya nan suke shigowa daya bayan daya yi min godiya. Maigari da matan sgi al, ajabi da farin ciki ya hana su ma magana sai godiya suke min kanne na sunzo nagane su mun dade muna hira dasu har dare suna furin mu ranan a nan suka kwana tare damu. Maigari yasa aka yanka muna kaji akai miyan kuka aka burge shi cikin kukan mu kaci sosai don yayi mugun dadi. Washegari kuma duk da Inna tai muna breakfast da indomei da mukazo dashi sai da mai gari yasa aka kawo muna kosai da masa da miya mukaci sosai naji dadi da yaran basu da kyakyamin abinci duk abinda naci suma sunacin shi. Na shirya muka kwashi tsaraban mutanen gidan mu dana yan unguwar mu sai gidan mu. Nan muka fara shiga na samu mama yadda na barta daurin zanin nan a gaba yai kazan kazan dashi na samu baba zai fita dama ni ya tsaya jira sai gani. Bayan mun gaisa dashi ne yake tambaya lafiyan wacce nake furin ta nace duk suna lafiya gama yaran ta nan nazo dasu. Yace yaya zancen aure kuma nai shiru can dai nace baba gaskiya aure ba yanzu ba don karatu nakeyi a can yanzu haka ma . Yace ai yaga alama tun daga yanayin shigana ya fahinci hakan ya dan yi min nasiha mama sai kai da komo takeyi nakawo tsaraban su na bashi ya shiga saka muna albarka Mama sai tsuki take tana zuba bakar magana cikin kashe murya yace fita batunta kada ki kulata halinta na nan bata sake komai ba dakika sani. Shiyasa ma daga baya banga laifin uwarki ba dataki dawo min don halin laure sai ita Taso ta daurre fuskan ta amma tunda taga tsaraban ta nan ta shiga washe baki tana cewa ikon Allah wai motsi yafi labewa ke nan harda mu tsaraba haka mai yawa. Rukaiya da Suwaiba har sun shige cikin kayan su dana zo masu dashi ko nace zan shiga naga mama sai muzo muje mu gidan Lawisa. Ina shega mama tace yar halas yanzu fa nake fada dake a zuciya na ina cewa kin samu uwar ki har kin share ni. Nace wace ni nina isa mama na share ki na dai samu inna ne naji dadi jiya naso mu dawo nan ai mukwana sai hira ya kwashe mu har dare yai muna acan. Na bata labarin zaman Inna a gidan maigari yadda take zaune lafiya agidan ga hadin kai da mutunta juna a tsakanin su. Tace bana fada maki ba dama kinbi duk kin tayar da hankalinki ke ga mai uwa a gari. Nan na mike na fara gyara mata gurin don duk gurun nata yai kura sosai a lokacin ba laifi don mutumin da ta sa a gidan yana da kula shi da matan shi da yaran su biyu. Zuwan su Rukaiyya saubiyu sun samu ina aiki sai dana gama na shirya muka tafi gidan tare dasu. Mama bata so ba amma babu yadda zatayi tunda yaran basu jin maganan ta na debi tsaraban da zan kai mata. Muna shiga na hango ta da daure gaban zani kamar na uwarta tana girki a cikin rana. Wani iri naji a raina ina cewa da nice a cikin wanan yanayin a cikin raina tana ganin mu tazo da murna ta tare mu. Ina shiga dakin ta sai da gabana ya fadi don babu komai a dakin kamar ba dakin budurwa ba. Nan dai muka zauna ana hira sai faman kamay kamay takeyi nabata tsaraban ta tana ta godiya take cewa dama ta tara wanki bata da kudin sabulu yanzu ta samu tayi wankin ta hankali kwance idan ta samu mai diban mata ruwa. Mun jima a gidan ta har yamma muna gurin ta sannan mukai mata sallama muka juyo zuwa gida tana ta min godiya kamar na kawo mata wani abu basu gajiya dajin labarin birni a bakina nima ban gajiya da basu labarin abubuwan birni dana gani a can. Mun dawo nan gidan su na zauna zauna mukai ta hira dasu basu nuna min komai ba a yadda na zaci ganin canjin fuska a garesu. Mama dai ne na ciki na ciki dani sai bayan sallah magariba nai masu sallama muka koma gidan mama Altine ranan a gidan ta muka kwana. Can gidan maigari sai tabaya yakeyi cikin damuwa ko anyi muna wani abune muka koma gidan mu kuma inna tace babu komai dama nace zanje can kada babana yace ban kula shi ba. Da safe na tashi nai muna abin karyawa mukaci muka koshi sai ga sakon maigari har gidan mama wai a kawo muna abin karyawa. Mukai godiya naba dan sakon tukwaici yatafi yana jin dadin hakan nace yace inna ta bashi kwalin sabulu da omo yakawo min nan zan bawa makwata bai jima ba ya dawo duk makwabtan mu su da na aika masu dashi sai zuwa rana na koma gidan Inna ta. Mun samu an aje muna abincin rana shinkafa da wake da mai dayaji akai muna, da rana munci shi sosai har yaran sai da nai mamakin su da sukaci shi haka da yawa. Gaskiya ban samu maysaka ba garesu suna da dadin zuwa guri Nasir ne ma mai leke min ko ina muna tare dashi. Naje gaida su mama hauwa gidan Garbati sunyi murnan ganina sosai nakai masu nasu tsaraban suna ta faman godiya, ban dade ba nai masu sallama na bar gidan na dan zagaya gurin dangin baba da na Inna ta nagaida su. Munyi kwanakin da zamuyi cikin jin dadi ana gobe zamu koma ake ta faman hada muna tsaraba irin kayan kauye. An soya muna gyada suya ruwa da mai bawa yaji gadan mai yawa yaji kayan kamshi da maggi, aya da gyada mai sugar, kayan miya na kauye naui naui ga galon din man shanu yasoyu sai kamshi yakeyi. Nono da fura da gunban kunu dakan hannnu kishiyan Inna tai muna haka dai muka hada kayan tsaraban kauye mai yawa. Ga kaji maigari yasa a soya muna yace akaiwa mijin anty ai mashi kuma godiya na ji matukar dadin hakan da akai min don wani tsaraban ma anan na barwa Inna shi. Mama ta somowa anty mai aiki gajiye sunan ta, mijin ta yarasu bata taba haihuwa ba ana mata tayi tace zata tafi ta gwada. Karfe sha biyun rana driver ya iso daukan mu na karaba da kaya daga cikin wanda nazo dashi na amfanina da kudi dubu biyar akaiwa lawisa naba kanina nace kada ma ya biya gurin mama dashi don nasan rashin imanin ta tana ina boye kudin ta hana mata su. Muka kama hanya sai garin kano a na daga muna hannu raina duk ba dadin rabuwa da yan uwa babu yadda zanyi muka wuce suna kallona. ****** ********* ****** Mun sauka lafiya biyu ya dan gwauta muna gida aka shiga muna da kayan mu gida anty sai murna dawowan mu takeyi. Tace kunje kauye kunciyewa inna kayan dadi ko nace mun dai cinyewa mijin ta dai don shine mai masaukin baki ai. Wanka naiwa yaran nima nayi muka canza kayan jikin mu nakai gajiye dakin da zata zauna ba daki daya zamu zauna da ita ba. Sai bayan mun hutane na fitar da tsaraban da mukazo dashi anty tace amma dai kun sasu sun kashe kudi gaskiya nace anty aikuma kun kashe naku akan su. Tai godiya take cewa bari mu gwada ba wa yancan tsaraban ko zasu karba oho in ma basu karba mun dai basu ai komai ta diba taba farida takai masu part din su . Babu wacce ta dawo dashi yadda muka zata hinduce ma tace ace idan akwai gyada a karo mata ta dade bataci gyada da sugar ba da soyayya. Anty ta kara akai mata tai godiya tace sai sun shigo gaida yan tafiya kauye . Sannu a hankali nafara koyawa gajiye yadda abubuwa suke yadda ake kuma amfani da komai don tare mukeyi da ita. Sai bayan mun dawo da kwana hudu ne daddy yazo daga Abuja sun dai gaisa da yaran shi a waya tun cikin waya anty take fada mashi irin tsara ban da muka dawo dashi yace shima ta aje mai gyada yason ci da ayya. Ranan da ya dawo yana manne da yaran shi suna bashi labarin kauye Nasir yana ta bashi labarin dokin da yagani gidan maigari harda yadda doki ke cin abinci sai da yaba uban labari kaf. Monday muka shiga school don ranan muka koma samun Gajiye sai abubuwa suka dan yi min sauki don gaskiya tana da kokrin aiki. Yo aiki ga mutumin kauye ai sai yaso jikin shi za, a ga kasawan shi gata tsabta kodon bata haihuwa ne oho. Na dawo daga school ranan a gajeye hamza driver ya sauke ni ina fitowa ban san da mutane a haraban gidan ba gashi gyale na sa ba hijjab ba kafa na sai hardewa yake wani cikin wani. Tunda na karyo kwana suka tsuro min ido banda daddy da hankalin shi ke ga wayan shi lokacin ina ganin magana sukayi a kaina sai lokacin naga yadan dago kai ya kalli inda nake tafe. Nazo gap dasu zan shige na dan rusunna na gaidasu suka amsa min a cikin sakin fuska na shige abina. Ina shiga Amirace ta fara ganina ta taso tana rugumay ni tana min oyoyo tare muka shige daki dasu bamu fito ba sai bayan sallah ishai don yanzu na dan samu sauki zuwan gajiye gidan. Ko zanyi abu anty kance na huta kawai tunda ga gajiye a gidan ai kuma tana aikin ta baka ganin part din mu da datti duk da munfi sauran yan sauran part din yawa a gidan. A daki na samu anty ta idar da sallah tana zaune ga jinior saman gado yana watsalniya da kafa shi gurin shi naje na daga shi sama ina mashi wasa duk da bai fara dariya ba a lokacin. Anty tace dani wai Rama kin san may nace a, a anty juya gareta ina sauraren ta tace bashir ne fa ya matsa min a kanki. Nace waye bashir kuma anty ? Tace Bashir dai da kika sani ma na abokin daddy ku. Haba kai don Allah don Allah Anty kibar zancen nan mana nifa ma zan bar gaida shi an fada mai ni yar iskace halan da zai wani ce yana so na can. Mamaki kalamina ya bata yadda nai magana yarinta zalla a cikin sa kuma akan serious nake magana na. Tace a, a basai kin ki gaida shi ba zan dai bashi hakkuri yafita batun ki kawai bashi ke nan ba nai fushi karshe ma na dauki yaron muka fice daga dakin ban dawo ba sai da zamu shiga kwana na dawo mata da yaron. Ashe bayan fita na daddy ya shigo gurin ta don haka yake yi duk dare sai ya zagaya wurin wacce basu da girki yai masu sai da safe yakuma duba lafiyan su hakama da rana yake masu indai har yana gari. Yake tambayan jinior take cewa uwar shi ta kwashe shi sun fita daga nai mata magana akan bashir shine ta dauki zafi dani ta fice. Nan ya hauta da fada yace akan may zaki biye mai ki mata magana karatu zatayi ko aure kubarta tayi abinda ke gaban ta mana ai zaifi. Shima Bashir dai hauka yake yi idan matan shi taji nufin ki zata yarda ya aureta ne. Har ya kai kofa ya juyo yana ce itama ki mata magana idan ta saka matsatsun kaya ta dinga saka hijjab don Allah a jikin ta banji dadin ganin shigan da tayi ba ya gashi dan karamin gyale tayafa a jikin ta. Duk anty tai mamaki maganan shi idan anyi la, akari da yadda matashin ke fita dan gyale a kafada har itama anty wani lokaci ai tana saka gyalen idan zata fita. Amma shine kuma zaice wai taiwa yarinya karama dake free bata da hakkin kowa a kan ta magana. Wani irin shiga kuma yake son nayi a matsayina na bazawa ne ko budurwa za ace gani nan dai bata ma san yadda zata fassarani ba dai. Shine bayan na shigo dakin mayar da yaron tace dani hmmm har kin gama fushin ke nan ai nazaci har yaron ma a gurin ki zai kwana ai yau Nace wallahi anty raina ne ya baci ina ganin shi da mutunci saboda daddy shine zai min wanan magana ba dadin ji ni ko zanyi aure ma zanyi dashi bayan kuna mutunci da matar shi sallon yaja maki wani sabon fitina kuma ke nan. Tace to daddy ku ma yai min fada ai don may nai maki magana sannan kuma wai yau wani irin shiga ne kikayi wai Rama ? Don daddy yayi fada yace na fada maki idan kinyi wanan shigan ki rika saka hijjab wai. Nace ba wasu kaya bane wanan ne fada kika dinka min da sunan jinior na saka da gyalen su. Tace kai besty dai da wani magana ma yake may kayan nan sukayi da zace haka naga dai matan shi ba irin shigan da basuyi gidan nan suna fita dashi ai. Ni dai na wuce ina tunanen killa ganin da sukai min ne dazun da yamma da zan shigo bai mai dadi ba yasa yai magana kawai. Haka rayuwa taci gaba da min tafiya a gidan anty saade tun raban da daddy yace tai min fada ban yarda mun kara haduwa da shi ba har tsawon wani lokaci sai dai naji yazo haka kuma naji ya koma. Na mayar da hankali na akan karatuna sosai ban yarda nayi wasa har kuma lokacin banda wasu kawaye sai wata mutum daya ita din kuma ma matar aure ce ganin kamun kaina yasa ta dan shige min ajiki tun ina dan ja baya hardai na yarda da ita tare muke koda yaushe da ita a schoool din . ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI ALLAH NAGANIN KI YAR UWA, , , 26 Yau ba school weekend ne lokacin kuma na shiga level one idanuwa na sun kara budewa ga yanayin zaman duniya. Idan ka gannin na koma wata silent ba hayaniya koda ina guri a zaune da wuya kaji murya na da wani fitan ma sai sa,a nake fitowa koda kuwa a falon mu ne. Har in mutum zaijini to da yaran anty da shakuwa mai karfi ya shiga tsakanin mu zakajini sai ko a school idan tare da Zarah nake zaka danga dariya na don akwaita da barkwanci. Duk abinda tagani sai tai mashi suna kuma ta gimtse fuska kamar ba itace take magana ba sai dai kai na kusa da ita tabarka kana dariya abinda ta fada kawai. Yar karamar riga ce baka mai matsatsen hannu a jikina sai hulla mai dogon igiya a bayan shi ya sauko kamar gashi ke rito bayan mutum zani ne a jikin nawa na daura shi wani iri. Ina kwance Nasir ya zo yake cewa dani wai ba zai sha tea ba da safe indomie zaici. Nasan idan ban fito ba gajiye bazata hada mai ba don tana da matsala gurin taushi da yara sukan yawan kwasa da anty kan rashin tausasawa yara da batayi. Ganin haka gashi garin mu daya yasa nakan mata magana amma bata dainawa sai nake ganin kodon bata taba haihuwa bane yasa bata san lalashin yaro ba oho. Idan nace hakan anty kan ce dani ke da kike kula su kin taba haihuwa ne halinta da ra, ayintane kawai a hakan. Sai dai kuma bayan wanan matsalan Gajiye bata da matsalan komai wallahi tana da dadin zama gurin yara ne kawai take da zafi. Sanin halinta danayi nasan kuma iyanzu ta riga da ta hada abin karyawa zai iya jawo matsala idan ance taiwa Nasir wani abin. Idan kuma anty taji zata iya daukan mataki akan ta don idan tayiwa yaran ba daidai ba ran anty kan baci tace wallahi sai dai ta sallamay ta don ba zata zauna ba mutum yana gasa mata yaran ta shiyasa nakan tare fitina nayi masu abinda suke so da kaina. Don akasatin lokacin da yaran suke gida nima ina gida a lokacin sai aka samu saukin hakan ga kowan su. Nafito na samu Gajiye na gaida ita nace don Allah ko kin gama da gas zan dan yi abune a gurin take cewa tana son ta dora wutan miyan rana ne nace danyi hakkuri na dafawa Nasir idonmie yanzu zan baki guri. Ta bata rai wai zamu bata mata lokacinta rana yayi bata karasa da wuri ba. Duk da raina yabaci ban yi magana ba na hada komai da ake bukata sai na kunna gas din komawa nayi daga bakin kitchen din nai tsaye ina jiran ya dahu na juye yaron na daki a bakin gadona yana game da waya na. Idanuwa suna Lumshe na hada hannaye a chest dina nabi bango kamar mai tunane har suka karaso inda nake ban sani ba sai jin muryan su ne yasa na sauri bude idona a dan cikin firgici don ban san da su ba a gurin. Ramana lafiya may yafaru kuma kika dawo nan kika tsaya tunanen may kikeyi haka a tsaye hsr baki san inda kike ba anty ce ke magana sai shi dake ta bayan ta yana kallo na. Sau daya na kalli inda yake tsaye na dukar da kai ban sake dago kai na kallesu ba gaba dayan su kara maimaita tambayan da taimin tayi. Rama may ya faru kin dawo bakin kitchen kin tsaya nace ba komai anty dama ina jiran indomie ya dahu ne na juyewa Nasir na tsaya a nan. Daddy ina kwana nace cikin dan rusunnawa kadan ashe kina gidan nan Rahama ? Ya tambaya anty kuma cewa tayi yanzu don indomie din Nasir kika dawo nan kika tsaya ke kadai kai Rahama kina dai shagwaba yaran nan wallahi anya kuwa ashe sai kuma tai shiru. Sun wuce store din kayan abincin mu suka nufa a tare suna dubawa daga can ta kwala min kira na shigo take cewa dani kin gane ne kayan nan don Allah duk a kwashe su Rama daddy zai kawo muna wasu kin san azumi ya gabato wanan din a fitar su waje sai mu kyautar dasu za, a zuba muna kayan azumi ne. Nace to Anty bari na gama da Nasir nazo na gyara gurin da kaina yanzu kai wake Nasir dai Nasir dai yanzu ne ma masu kawo kayan zasu shigo muna dasu nace ba matsala ai ya dahu yau my boy yace baya shan tea kin san shi hukuma ne sai lalashi ko indomie din da kyat na samu zai ci wai shi masa yake son cin. Ai fa nikan maigari ya dauko min fitina wallahi da yaron nan bai san masa ba amma tun zuwan kauye ya dawo min da zancen masa da kosai a bakin shi. Heart beat ni zan tafi indan sunzo sai ki fito ayi yadda ya dace kowa akai mata nata part din ta na basu lanban ki zasu kiraki idan sun iso. Rama wai ko kin gaida daddy da dawowa nai saurin daga kai na dan saci kallon shi ya wani daure fuska dama haka yake indai ba yana tare da yaran shi bane baka taba ganin annurin fuskan shi. Cikin daurewa yake cewa ni ban ma san rabona da ganin kaunan taki ba yanzu kin san yar University ce ba a ganin ta kai tsaye yadan yi min barkwanci don wani lokaci yakan min wasan kaunan mata idan yaso. Nai murshi kawai nace anty ni ban ma san daddy ya dawo ba wallahi sai yanzu dana gan shi . Amma baki da kirki daddy yau kwanan ahi biyar fa da dawowa kasan nan mutum ya share kusan wata uku bai kasan. Daga inda nake labe a bayan ta nace sannu daddy da dawowa sai abin yabata dariya tace ina ruwan mai dole. Yace nina fita ba tare da ya amsa min ba tace ai kinga shima yayi fushi tunda yaga sai da na roka kika tare shi . Nasir ne yafito daga daki yana kwala min kira Anty Anty nace daga bayan ta my boy bari na kawo ma. Gurin daddy shi da yagani ya nufa rike da waya na a hannun shi yana cewa daddy kaga irin game din da nake so ka saya min anty tace idan naci na daya kona biyu a class din mu zata saya min shi. Rike shi da yaron yayi adole sai yaga game din yasa shi karban wayan a hannun yaron. Komay yagani sai naga ya juyo yana kallon inda muke tsaye da anty daga can yake cewa Sa, ade amma kinji kunya yanzu wayan yar university ke nan waya duk ta kode haka ? Tun da nazo gidan ban taba jin ya kira anty da sunan ta ba sai yau kuma akan waya na yakirata da hakan. Tace kasan halin mutumiyar wayan ma ai kusan na Nasir ne ita ba abokai ne da ita ba ko sauri sai aukin yin game ko yaushe. Dan dube dube yake a wayan wanda muke zato games din wayan yake kallo Nasir nata zuba mai surutu ya dan rage tsawon shi daidai yaron suna magana. Mutuminnda yace yana sauri zai fitane ya buge kuma ga hira da yaro kai daddy akwai son yaran shi wallahi. Na shiga kitchen na juye mashi indomie din suna gurin har anty sai dariya suke gwanin sha, awa naba yaron indomie karshe dai ni ban san inda suka nufa ba ashe suna falo tare sukaci indomie din da yaron. Sai gaf da zan gama gyara store din ne yaron yazo inda nake yake cewa anty da daddy mukaci fa yacinye min abincina yace wai anty ta iya dafa nudulles sosoi. Ina aiki ina mamakin yadda daddy yaci wanan jagwalgwalen har yanawa yaro santi. Nagama har nai wanka na saka dogon riga baka da gyalen shi na daure kaina yaran ma nayi masu wanka muka dawo falo muna kallon program din yara a tv. Nace Amira dauko min jinior taje sai anty ta koro ta wai bata iya daukan shi anty ta biyo bayan ta tana cewa haka kawai zaki turo min wanan mai rawan kan tsiya daukan min yaro nace haba Anty tun yaushe su Amira ke daukan shi tun fa yana jariri. Bako a gaban idanuna ba don bazan yarda ba yaron nagani na ya shiga washe min naki yana miko hannu na dauke shi wai. Nace zauna can tunda an hana ma anty na daukan ka nima yau ba zan dauke ba zauna gurin mummy. Rama don Allah ki karbe shi kada ya balla ni ina fadin naki ina mai wasa shi duk ya tattaro karfin shi gare ni ya matsu na dauke shi din. Wayan ta dake hannunta ya kara ta miko min yaron na katbe shi muna wasa naji tana fadin gani nan zuwa tafice daga falon. Shiru shiru bata dawo ba har kusan minti talatin can naji hayaniya ya kaure a waje da sauri gajiye ta shigo falon tana cewa dani Rahama fada fa ake kuma da yar uwarki ake fadan nace subbahanallahi . Da sauri muka fita gaba dayan mu daga falon zuwa waje matan gidan da yan aikin su duk suna gurin a tsaye ga kayan abincin su shimkafa taliya tomatoes maggi mai taliya indomie an kasa kashi ukku sai dai kashi daya yafi sauran yawa sosai. Ashe akan shine ake fadan sunce don may kadon anty zaifi yawa watafi da za, a bata kaso mai yawa haka ? Ina jin ba,asin maganan nasu kawai na mikawa Amira jinior nacewa Gajiye duka mu kwashe kayan kawai. Sai gani sukayi na fara daukan kayan aiko sai ga Zulfa tayo cikina tana kokarin bangaje ni da zafin nama na juyo saiko ta kwada min mari kayauuuu. Zafin marin danaji nikuma na kwashe mata kafa sai gata a kuca tafadi aiko tana tasowa ta shakeni nace maman hanifa sake ni taki sai bugu take kai min bugu daya nai mata Allah yaban saan fuskan ta tasaka wani irin ihu mai karfi. Hindatu ta daga waya tana kiran maigidan yazo ga fitinan da ya haddasa a gidan shi takai har na doki Zulfa . Tare suke da Bashir a lokacin yace duka fa tace kazo kaga shahidi mana danbe sosai mukayi da ita na nuna mata karfin yan kauye sai da taji jiki duk ta yakushe min jiki da cizo niko na dake sosai Allah ya ban saan ta ranan. Gaban masu kawo abincin mukayi shi da ita zagi da gori na sha shi a wurin su kuma na kwashi kayan na shige dasu part din mu. Anty hankalinta yai mugun tashi sosai a lokacin amma ai ita suka so dukan da farko don ashe dama sun kitsa su bata tsinanen kashi ayi abin da za ai masu. Sai gashi hindatu ta jaye ta barta ina kakwasan na karshe hindatu ta rike min riga saida ya yage aiko itama na wanke ta da mari kayauu har sau biyu take idon ta yai mugun ja a gurin. A bakin mazan da suka kawo abinci yaji ba,asin maganan ya samay su a kofa ran su a bace. Ya shigo gidan kamar namijin zagi gaba daya yan gidan ya hada mu har yan aiki dakowa yai muna mugun zagi sosai. Zagin matan shi yafi yawa yace dubi abinda yarinya karama tai maku dube ku don Allah hindatu tace dashi ai ba sai ka zage mu ba Man don ba yau ba na fahinci kana son yarinya nan tunda duk cikin yan aikin mu babu wanda kake kyautatawa kamar kwana ki har motar shigan ka ka bayar aka kaita har kauyen su dashi. A hasale ya juyo gareta yace hindatu sherin naki har yakai yau ki kalli idona kice ina son kaunar Saadatu a gidan nan. Ni ke son Rahama Saade ni zakiyiwa wanan kazafin haka don ki bata min suna ki hada ni fada da matana da mutane ? Daga inda anty take zaune tace wallahi Besty in ma kace kana son auren Ramana na ne ni bani bata rai nafi kowa farin ciki dajin haka a rayuwana. Kan shi ya dafe take idanuwan shi suka kada sukai ja yai shiru falon ma kowa shiru yayi a cikin sa. Can ya dago rinanun idanuwan shi yace hindatu ba a taba min kazafin daya kona min rai ba irin wanan. Amma ki sani ni yusuf Rano ba mazinaci bane ban mata taba tunanen yin shi ba a rayuwana don ni ba dan akuya bane. Idan a gidan ku ake haka to ni ba ai min wanan tarbiyan ba a gidan mu zaki gane kin min kazafi mai zafi haka ku tashi ku bani guri. Aka watse falon kowa ran shi a bace sai faman kuka nakeyi don wanan mugun kazafin da akai min damay yai kama haka ? ****** ********* ****** Kuka nakeyi sosai a dakin mu take wata zuciya tazo min mikewa nayi na fara hada kayana dake cikin mamakeken wradrove din dakin ina kuka wiwi. Amira ce ta sheka kiran maman su Nasir kuma yana kwance saman gado ya kifa cikin shi tare da kura min idanuwan shi. Sai ga Anty ta shigo dakin tun daga kofa take fadin may ye kuma haka Rama kin tayarwa yara da hankali Amira ce fa ta samay ni da kukan ta wai ga can kina kuka kina hada kayan ki. Ban daina abinda nakeyi ba har sai data karaso inda nake ta dafani cikin hasalan da ban taba ganin ta ciki ba tai min magana. Wai badake nake bane may kikeyi haka kina nufin sin samu galaba akan mu ke nan dama zaman ki gidan nan ya kai masu ko ina sun yi gulma sunyi tsegumi sai wanan kazafin ne zai bata maki rai Rama. Sai lokacin na juyo idanuna danaci kuka sunyi ja sun kade nake cewa anty saboda Allah wanan wani irin rayuwa ne ni maman husna zatace wai daddy na so na ? Daddy yayi may dani don kazafi kawai suna son na bar masu gidan su shine zasu yi min wanan kazafin haka su hadani fada dake ? Dawa zasu hadaki fada Rama ni Allah dai ya sauwa wallahi akan may zan dauki zafi dake ni ko ba su suka fadi haka ba ai bani fushi balle su suka fadi . May ye kishiya bata iya fadi a kan ka don ta bata maka rai kan shi ni wallahi in ma sunyi ne don naji haushi ni kan dadi ma naji da besty zai taimake ni ya aure ki ai nafi kowa farin cikin hakan. Wani kallon mamaki nayi mata kamar zanyi magana sai na juya naci gaba da kwasan kaya na kawai. Take cewa wai ba zaki ji abinda nake fada maki bane Rama ki daina wanan kwasan kayan da kike yi babu fa inda zaki. Zanyi magana sai ga gajiye ta shigo dakin tana cewa hajiya kiji wa yan nan matan da basu da tsoron Allah. Yanzu naje kai wanki naji suna fadin wai dama ke suka so duka amma Rahama ta kwabsa masu shiya su kuma sukai mata wanan kazafin dan kiji haushi ki koreta su samu su gasa ki yadda suke so. Anty tace to ke kinji ni dama ai nasan sherin su ne hakana barsu nan inda kika gan su an sherin mutana ne. Tace ai naji wallahi suna can har yan aikin su suna dariya wai ai dole yanzu Rahama ta bar gidan don koke ko mai gidan dole ku koreta. Allah yafisu yafi sherin su babu inda zata sai ma suji haushi wallahi don yanzu ma zan sa aima Rama abinda basu taba zato ba a gidan nan tunda haka suke so. Gata nan mara wayo wai ita barin gidan zatayi tunda sunce maigida na son ta ko yace yana son ki ba mace kike ba halan kuma sun san kifi su da komai wallahi. Sai kibar gidan suji dadi su zuba ruwa a kasa su sha niko ki barni da bakin ciki ba shi ke nan ba tana fadin haka ta juya ta fita daga dakin ta barni nan tsaye na rasa abinda zanyi a lokacin. Sai Gajiye tace Rahama kiyi hakkuri idan kin tafi ai dadi zasuji ki mayar da kanyanki ki maida komai ba komai sai bakin ciki ya kashe su kin dai ji abinda hajiya tace ai. Indan kinyi haka baki kyauta mata ba kije ki samay ta ki bata hakkuri a wuce gurin don Allah nan na durkusa ina kuka wiwiwi raina kamar zai fita. Nasir ne ya taso daga inda yake ya rugumay ni yana fadin anty yi shiru kinji kyale maman Husna sai na halbe ta da bindagana. Najawo yaron a jiki Amira ma tazo tasa hannayen ta tana share min hawaye tana fadin nai shiru sai taba hanifa da husna kashi tunda maman su sun sani kuka. Kuka nake sosai sai ga anty ta dawo dakin takawo min jinior daya damay ta da fitina tasan gurina yake son zuwa lokacin yadda yake mata. Yadda ta gan mu sai muka bata tausayi yaron ta miko min tafice itama kukan takeyi a lokacin. Haka na wuni cikin bacin rai yaran ko suna manne a jikina duk inda nake suna saman jikina. Muna falo zaune nake saman one seater amma haka suma suka manne min ga jinior saman jikina mu hudu mun makure a guri daya anty na dakin ta cikin bacin rai. Daddy ne ya shigo part din wanan katon ya sauya kayan jikin shi zuwa kananan kaya wando baki da yar rigar tieshirt ja an rubuta mai THE KING da ruwan zaiba a gaban rigan. Idanuwan shi a kan mu ina saye cikin digon riga light blue mai dogon hannu sai hulla da na dora a saman kaina. Yaran na ganin shi suka mike zuwa gare shi suna daddy Nasir ya rike shi yace daddy please dont live anty to go. Ya shafa kan yaron yace to go where ? Yaron yace she said she is living us soon. Inda nake ya kalla yace kada ki ruda yaran ki Rahama inkin yi haka baki kyauta masu ba kin ga sun shiga damuwa sun ganki a cikin damuwa. Daddy wai zaka auri anty inji mummy husna harda mummy mu inji Amira take tambayan uban nata. Shafa kan ta yayi yace mummy husna bata da hankali karya takeyi jinior ke mika hannu uban ya dauke shi wai. Ya karaso inda muke ya dauki yaron yana cewa big boy may ke damun ka haka kake wanan raman ina mummy tana ciki ko ya juya da yaron zuwa cikin daki inda anty take ya samay ta. Ta na kwance ta dunkule a guri daya jin shigowan shi dakin yasata dago kan ta idanuwan ta da taci kuka ya rine yayi ja dashi. Yace kema kukan kike yi kamar yaran ko may kina son jawa kanki matsala kuma ko bayan kin san ba lafiya ya ishi jikin ki ba. Yanzu abinda Matanka sukai wa yarinyar nan don su fashe haushinna akan ta sun kyauta ke nan besty ? Yace ai ba ita sukai wa kazafi ba ni sukai wa sheri ni maigidan da sukaiwa zatlrgin sheri amma zasu gane kuren su ai sun san halina. Shiru sukayi sai can anty tace Besty may zai hana ka auri Rahama ne shi kadai zakayi min ka fashe min haushina idan sunyi ne don naji haushi sai ya koma masu . Babu daya daga cikin su da zata taba zaton jaka zai iya faruwa tunda sunyi ne don sheri dama. Kina da hankali kuwa Saade nine zakice na auri Rahama may zanyi da wata mace kuma kosu ba dai da rabon aure bane a tsakanina dasu da kuma takuran magabata. Mata uku ma yaya na iya daku balle na kara dauko wa kaina magana shin kin ko san naiyin maganan da kikayi yanzu kuwa besty da wani ido kike son yarinyar na ta kalleni da kuma duniya. Tace an so what ba aure bane kuma Allah ya halasta maku auren mata har hudu a rayuwan ku, kana kuma da karfin yin hakan ta ko ina idan ka so yin hakan. Ban son jin wanan maganan please gashi har yara sun san abinda ake fadi yanzun nan su Amira suka tare ni da zancen a falo ina dadin haka please. Ai sai ki kori yarinyar a gurin ki bayan kin san irin taimakon da take maki a rayuwan ki a gidan nan. Tace ai don tai makon da take min ni da yaran nake son taci gaba da zama damu a cikin gidan nan ko ba komai ko bani nasan zata rike min diya na yadda ya dace ai. Dan Allah ki rabani da wanan tunanen yaran naki ko kema kin haukace ne irin na sauran ban sani ba ban son na kara jin wanan magana daga bakin ki kuma please. Yaron ya aje mata ya fita daga dakin a hasale komai jin shi yaka yai mai baki kunci ya mamaye mai zuciyar shi yana tunanen may zai yi ya bata wasu hindatu rai akan haka. Hajiyan shi ke neman shi can ya nufa amsa kiran mahaifiyar tashi tafe yake a motan shi yanayi yana shafa sajen fuskan shi a hankali. Tunanen maganan da sukayi da Anty yakeyi ran shi na kara mai kuna a lokacin harya kawo gidan mahaifan nashi. A falo ya samu mahaifan nashi su duk suna tare sai Aisha da ya samu tazo gidan a lokacin ganin su nan suka gaisa ya samu guri ya zauna. Ya fuskanci mahaufiyar tashi yana cewa hajiya gani kince kina nema dazun da rana bani gari yanzu na dawo shine na shirya nazo. Hajiya batason magana a gaban mijinta ba amma kuma babu yadda zatayi dole tai maganan a ga ban su hakana. Alhaji yaya akayi haka kuma yar aiki ta daki matan ka kuma baka dauki mataki ba a gidan wanan ai raini ne da wullakanci kajawa matan ka hakan ? Yace yar aiki hajiya ? Ba yar aiki take ba may take a gidan ina matarka ce ta dauko ta kalar dangi ta zauna da ita samun wuri kuma yasa har takai hannun ta ta daki matan ka kamar wata yar chaina da ita tai masu kaca kaca da jikin su. Suma ai taron banza ne suka kasa taruwa suyi wa yar banza duka tsiya sai ta kasa motsi a gurin gobe ta kara gigin kai hannun ta duka wani kuma. Hajiya Rahama ba yar aiki bace na fada maki haka ba yau ba kaunar saade ne ta dauko ta taimaka mata. Duka kuma ita Zulfa ita ta fara dukan yarinyar ita kuma ta rama hindatu taji haushi ta yaga mata riga ta mareta itama ta rama hakan. May zance in ba fadan karya zanyi ba tunda daurin hannu ke garesu daga magana sukai wa yar mutane duka don suna takama sun fita. Dariya Aisha dake gefe tasa tace Rahama ta zama shago ke nan duk ta watsa su amna anyi kattan bamza wallahi. Amma dai basu kysuta ba inji Abba dake sauraren su koni ne tunda su suka fara bazan ce komai ba ai. Haba Alhaji ka bari ai mashi magana haka bai dace ba wallahi yaya zata doki matan gida su da gidan mijin su ina ruwan ta da fadan kishin su da zata saka bakin ta ciki. Yace hajiya har ni Hindatu zata kalli idona tace wai ina tare da Rahama ta sani ba yau ba. Ni zatai wa zargin sheri da kazafi irin haka don ta raina ni ko may saboda suna ganin suna iskanci son ran su ina kyalesu idan mace nake so kasa nawa nake zuwa ina ganin mata iri iri ban nema ba sai kaunan saade zan nema kuma. Ni hajiya yaran nan sun kai min ko ina wallahi saboda ku fa nake zaune dasu haka na amma ba wani jin dadin zuciya da nake samu garesu. Kai mata ho idan ma kana son ta aiba abin boyo bane ko tunda Allah bau haramta maka yin hakan ba sai ka auri abinka shike nan. Mahaifin daddy ne ke fada mai hakan yace in har akwai alheri ga auren yarinyar kaje ka aure ta ni nace gobe su kara kazafi da kyau kuma. Haba Alhaji wanan wani irin shawara zaka bashi haka kuma ana neman mafita ga yarinya tazi ta addabi mutane da gidan su. Ko ni nan ta taba min rashin kunya saida na hada ta da yaruwar nata nai masu tas tashiga hankalinta. Don haka bani son zaman yarinyar nan a gidan man kaje ka sallamay ta tabar masu gidan su takoma inda tafito kaji na fada maka. Ni kuma nace babu inda zata kinji hukunci na wai may yasa ku mata baku da hankali ne komai girman ku ai idan ta tafi sai a dauka da gaske ne haka maganan yake son ta yakeyi din. Ba, a aure mukasa su ya aure su baiso hakan ba a lokacin ban son maganan shirmay dama don wanan shiriritan ne kika kira shi yabar abinda ke gaban shi yazo nan. Ni mahaufin ka na baka baki jeka auri yarinyar in har haka shine mafita a gareka suje su mutu yaran banza kawai da basu san arziki ba tashi kafita na sallamay ka. Aiko da ka auri yarinyar nan yayana daka more rayuwan ka tun da matan ka kaf babu mai zatin ta a gidan ka kishin haka ne yasa suke zargin ka kawai. Gata da tsabta ga kirki ga girmama na gaba wallahi yarinyar tayi hundred percent ni dai a gurina matsala dai Saade da zataga an mata cin fuska kawai. Babu cin fuska gareta don itama haka take so a ranta ban dai amince bane kawai. Idan kana so kawai kayi abinka yayana samay ke dallah rufewa mutane baki mara hankali ba za, ayi ba nace nikuma nace yaje yayi idan yana son hakan sai may. Yai masu sallama yabarsu nan suna zabga muhawara akan maganan hajiya duk ranta a bace yake kan maganan mijinta yaki bari taiwa danta fada yadda take so. Yana tafe tuki yake amma yana tuna maganan shi da iyayyen shi yadda ta kaya masu lalai namiji namijine. Yanzu har Abba ya yanke hukunci a kan shi kai tsaye shi bai dauki yin haka ba wani matsala a gurin shi. Batare da laakari da laakarin abinda matsalan zai jawo ba ga iyalin shi da kuma kusancin dake tsakanin saade da yarinyar ba don ya zama matsayin cin amana ga saaden ke nan yayi. Duk da hakan ba komai bane idan yai niyyan yi amma ba zai iyawa Saade haka ba koda yana son yarinyar ne kuwa amma a wajen wasu mazan hakan ba komai bane ai. Amma hakan da kowa ke bani shawara shine zanyi na rama bakin cikin da yaran nan sukai min kai tsaye da zina suke nufin ina neman ta nikuma sai na aurota na jefa cikin su badon saade ba ko da kuwa yar aikine yarinyar amma Saade tai min katanga ga hakan da sun sha mamakina wallahi ko. Haka yake tafe a cikin damuwa yakasa samun natsuwa zuciyar shi zafi take mashi da radadin wanan masifa daya wayi gari dashi yau din. Haka ya nufi gurin bashir da bacin rai yana ganin shi ya fahinci bai cikin dadin rai ga yanayin shi yake cewa may kuma akayi ne wai nagan ka wani iri dakai. Fitowa yayi daga motar batare da ya bashi amsa ba ya jingina bayan shi ga motan tare da harde hanayen shi guri daya. Bashir yace mai mata biyu ance baida natsuwa kaiko mai mata uku yaya dai sunyi halin nasu ke nan ko ? Yace bari kawai bashir suna son su haukatani nida gida sun azamin tention kaina ya dau zafi wallahi sosai. Ka duba fa wai ni Hindatu zatace ina tare da sister din Saade don wullakanci da rainin wayo ? Kai haba garin yaya kuma wanan maganan yazo mata haka ita kuma hindatun ? Yace garin iskanci da rainin wayo mana saboda samun wuri nan yake fada mai yadda abin yafaru da yadda sukayi da saade a kaina. Aikin banza to kai may zaka tsaya jira tunda har Saade da Abba sun baka go ahead kan maganan ba sai ka amfaka ba ka gwada masu ka isa kai keda gidan ka. Yace haba Bashir kada ka zama dan akuya mana yarinya tana kirana daddy kasa daddy sama nace kuma zan aureta ai da na zama dan kuya dai. Nasan dai bakin cikin da zan masu ai nayi niyar canza masu mota dukkan su na fasa ita zan sayawa a satin nan kuma nace a koya mata suje su mutu da bakin ciki bashi ke nan ba. To may kayi idan kai wanan kawai kada ka tsaya kallon ruwa kwado yariga fadawa ruwan idan zaka nuna mazan taka kanuna masu kawai shine mafita. Tsaki yaja ya fada motan shi yana cewa sai kajini ni zan koma gida komai ma bakin shi nake gani wallahi. Ya wuce Bashir na mashi sheri mai mata uku ba abinka sallah kada kaja muna ayan mata. Bai zo gida direct ba sai da ya tsaya shagon sai da waya ya sowo dalleliyar waya mai kyau da tsada ya nufi gida dashi. Muna falo har anty bayan sallah ishai yashigo falon nan yazauna tare da mika mata wayan yace ki bawa yar ki shi sai na kunsa masu bakin cikin da suka jefani. Takarbi wayan tana yaba kyawon shi tace Rama kin fa faso gari gori da sheri yaja maki alheri gashi inji daddy ku yasaya maki. Na dago kai da mamaki ina cewa ni anty tace ke ma dawa baa gaban ki ya bayar ba na karba tare da zuwa inda yake zaune na tsugunna ina cewa daddy nagode Allah ya kara rufa asiri yace amin tare da mikewa tsaye. Sai da ya soma tafiya ya juyo yana cewa ki koya mata mota nan da sati motar ta zai zo sai na dasa masu abinda suka dasa min su ma. Yafice daga dakin dariya anty tayi bayan tabi bayan shi da kallon tausayi tasan yau mutumin nata yadau zafi sosai dama haka yake inda wani yai mai bakin ciki sai ya rama ta ruwan sanyi. Tace Rama aiki kazafi yaja maki alheri insha Allahu akan su zai kare bude wayan mugani kin ji. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI DON ALLAH NAGANIN KI YAR UWA, , , 27 Hamza driver anty tasa yake koya min mota gani da kan dauka kafin wani lokaci har na iya tuki yakan bani na jawo mu dawo wa gida idan mun gama. Wani lokaci kuma yasa na zagaya cikin gari yana gefe yana kallon yadda nake driving din har ya tabbatar da na iya tukin motan a lokacin. Don anty ta tabbatar kayan store din mu da muka kwashe ta bani na kaiwa mama laraba da su yan uguwan su abin azumi naje na dawo tare da Farida data biyo mu tace a gurin mu zatai azumin ta. Ganin naje lafiya na dawo anty taji dadin hakan sosai takira mijin ta ta sheda mashi iya motana yace yayi kyau sai taji shi. Su ko suna zauneba haraban gidan su fitar da fararen kujerun roba wai suna hira sukaga dawo na cikin motar anty. Hindatu tace yaushe wanan somayen ta fita gidan nan ne ? Zulfa tace ban ma lura motarta baya gurin ba sai yanzu ko ina taje yau kullun kule a gida haka kamar kumshin tsohuwa. Idon su a kaina har nafito nida Farida daga cikin motan Farida na zagin su sai abin ya bani dariya. Kam uban nan lalai ma wanan shegiyar yarinyar ta samu guri wallahi yaushe ne ma har ta iya mota a gidan nan ne wai ? Ji shegiya kamar yar tsana sai karfin tsiya yar iska wanan idan ban kawar da ita gidan nan ba sai tafi uwar dakin ta iya sheri wallahi. Zulfa tace bari mu zuba da ita a gidan nan mugani sai nayi maganin ta tabar gidan nan adole ta samu arziki tana ci kamar na uban ta. Shima na zaci zaiyi zuciyar nashi yace tabar maigida ne wallahi amma sai shiru kake ji ba wani motsi bai dauku maganan da zafi ba. Yaya zakice nai dauka da zafi ba da zai tafi ya sallamay ki ne ke ni fa tun rana yaudauki zafi dani sosai wallahi ko kallon gefen da nake bayayi ma. Kinga kuwa ya dau maganan ke nan kin san halin shi ai bai magana sai dai ta kuntatawa mutum kawai. Muna kawowa sai tin da suke muka gaidasu muka shige abin mu ban tsanmani sun karba muna ba ma mu dai mun shige abin mun barsu a gurin suna shewa nasan zagina sukayi. ****** ********* ****** Ranan da aka tashi da azumi weekend ne baka jin motsin komai a gidan uguwan ma da garin tsit yake kowa na gidan shi ana barcin safe. Nima sanin cewa ba school kuma ba wani aiki tashi nayi na hadawa yara break din su nakoma na kwanta abina don nacewa gajuye tunda asuba tayi kwanciyan ta kawai sai rana muyi aikin mu. Can cikun barci nake jin muryan anty tana tayar dani na bude udona tana tsaye akaina ta caba kwalliya wanda nasan sai Daddy yana gari take yawan kwalliya haka nasan kuma baya nan. Na mutsuke idona tare da amsa mata namike tace to tashi kina nan kina ta barci tundazu ga abin arziki ya samay ki. Nace ni anty tace kefa taso muje muga motar ki da daddy ya zo maki da ita tana waje nima yanzu yazo yake fada min haka. Nace anty Daddy ya dawo ne kuma yazo min da mota kikace fa ? Taso don Allah ban son yawa surutu ina azumi na muje mugani kafin wasu su rigamu ganin ta. Gaba daya part din muka nufi gurin murna da sowan mune ya hankaltan da mutane gidan suka fito sai gani sukayi muna kallo mun shiga muna dubawa a hankali . Mamaki suke tsakanin ni da anty motar waye yadda muke dauki sun rasa may motar a cikin mu. Haka yasa sukai shawaran cin ma maigidan suji waya saya wa mota muke murna haka yan part din mu. Suna zaune da Bashir a falin shi suka shigo falon Zulface take cewa munga ana murna ne wa aka sayawa mota gidan nan. Yace wani ya turo ku ku tambayeni hakan ko may hindatu tace muna dai son sani ne tunda muna gidan yace ok motar farkatace da kukace na sayo mata shi. Wanan ma ai rashin adalcine mu matan ka baka saya muna ba muna binka ka canza muna shi zaka sayowa wata banza can da ita. Rahama din ce banza Zulfa ba banza take ba may take din matakarce ita da zaka saya mata abinda mu baka saya muna ba . Ba matana bace amma a yanzu tunda ana zargina ina son ta shiya nake son kawar da zargin ya zama gaskiya koda kudin ku na sai mata mota da abin zai damay ku kuma bayan da bakin ku kun fadi ina son ta ne. Shiru kowan su tayi sai bashir ne kecewa yanzu dai ba wanan ba kubar wanan zancen haka don Allah don gaskiya baku kyauta ba sanin ko waye mijin ku bai kamata wanan zargin da sheri yafito daga bakin ku ba haka. Nan dai Bashir yai masu fada akan basu kyauta sai cewa sukayi daga karshe sunji sunyi kuskure amma zancen mota fa yaya za, ayi. Yace ba zan saya ba don banda niyar haka idan kuma wata takara min zancen mota a gidan nan ranta zai baci sosai a gidan nan. Wanan magana mu muna can muna murna sashen anty su kuma masu gidan na can suna faman fitina a tsakanin su har takai iyayye sun shigo ga maganan. Mama Zulaine ta biya ta kira mama laraba sukazo gidan tare jin da mama larabane yasa shi dawowa gidan daga inda yake. Suna nan zaune har yashigo falon shi suka shiga yace akira mai anty tazo bata bata lokaci ba ta tafi. Nan mama Laraba ke tambayan may ya kawo haka zaka sayawa Rahama motar shiga matan ka baka saya masu ba? Shiru yayi don ran shi a bace yake sosai a lokacin mama laraba ta sake maimaita tambayan ta yace mama kudina ne kuma ra, ayina ne hakan shike nan. Mama Zulai tai farat tace shike nan zance ya zama gaskiya dama yariyar nan zaman cin amana kawai aka kawo ta yi a gidan nan don samun wuri harda samun matan gida da duka. Ke Saade duk kece da wanan makircin kin san komai kan yarinyar nan amma kika dauko ta kika aje ta a gurin ki takoma baya tana ci miki mijin ku ta baya. Haba mama wallahi haka ba halin Rahama bane ni wanan yarinyar banga abindata tsare masu ba a gidan nan haushinta kawai suke ji don zaman ta a guri ai ba Rahama ce kawai a gidan zaune da mu ba. Ni may yasa ban taba damuwa da duk wani dake karkashin su ba sai sune zasu damu da yarinyar mutane . Ai haka ma zakice tunda ta riga ta asirce ku a gidan tana yadda take so yarinya haka fikiu fikiu da ido kamar ita ta tsara kan ta har zaki jawo wa kan ku wahala da ita. Mama wanan maganan da kuke yi fa yana kara tunzura ni ne wallahi mota dai ni naga dama na saya mata ban damu da duk wanin abinda wani mutun zai fada akan haka. Zargin kuma da suke min na barsu da Allah shi zai saka min ni da wanan yarinyar. Salati mama Zulai ta saka tana cewa yanzu akan shedaniyar yarinyar nan kake jawa matan ka Allah ya isa Alhaji ? Yace ai cewa nayi idan sheri sukai min idan kuma ni neman ta nakeyi ai kinga a kaina abin zai dawo min ko ? Haka dai suka zauna basu fahinci komai ba don sun rasa gane kan shi ga baki daya nan zulfa ta shiga surfa min zagi ni da anty tana ja muna bakar Allah ya isa karshe ficewa yayi ranshi na mashi kuna ranan dai haka akai buda baki rai ba dadi a gidan. Yana zaune yayi buda baki a falon shi wanda ba wani abin buda baki aka shirya mai ba saka makon mai girkin na cikin fushi tana son jan ajin ta a matayin ta na mace gareshi. A kasa yake zaune saman kafet din dake tsakiyan falon nashi goran ruwa da fruis din daya sayo a gefen shi. Kan shi ya dafe da hannu daya saboda kan nashi ya dau zafi a lokacin ji yake kawai ya saki matan nashi ya huta da wanan tashin hankalin nasu dayaki ci yaki karewa garesu. Wata zuciya daga ban gare zuciyar shi ke bashi shawara ya sallami Rahama kawai daga gidan ya huta da zargin dake damun matan shi akan ta. Na yau daban nagobe daban duk akan yarinya daya abin ke faru idan kaji fitina akan wani dake gidan. Bayan duk halatcin da yarinyan ke masu agidan akan diyan su zuwanta yasa ta yiwa diyan shi tarbiyan da iyayyen su suka kasa basu a baya sai bakin kishi da suka sa agaban su. Yanzu yaro daya gan shi zai gaidashi suna karatu na addini komai tare da yaran takeyi bata daukan kan ta wai ta girmay wa yaran don kawai ta saka su a hanya madaidaiciya. Yace a hankali shi kadai zaune a mamakeken falon shi Ya Allah ka agajeni kai min mafita akan wanan matsalan a gidana. Idan nace kai tsaye Rahama ta barmin gida ban kyautawa Saade data dauko taba a gidan kuma tana taimaka mata nima nasan da hakan. Matsala dai dayace rikicin su da matana ko yaushe wanda kuma idan an bibiya sune ko yaushe basu da gaskiya akan fitinan. Fitinan da sukeyi ga Sa,ade yanzu ya koma gun yarinya mutane wanda ba komai ke kawo shi ba sai cin fuskan da suke kokarin yiwa wacce ta kawo ta gidan a gaban ta. Wanda koma waye ba zai lamunci hakan ba a gaban shi don ba kowane keda hakkuri irin na ita sa,aden ba yanzu. Kawai barin su zanyi suci haukan su ai dawowa zasuyi a hanya su fahinci gaskiya da kan su. Haka dai ya kare zancen zuci da mika al, amarin shi ga ubangiji tun da shine ya kaddari zaman su haka a gidan. Sallaman Saade da iyalin ta sunzo gaida shi da shan ruwa ya katse mai tunanen shi. Kusan nice tafe a baya dauke da Jinior a hannuna nan muka zube kasan kafet muna mashi barka da shan ruwa daddy. Ya amsa cikin dan sakin fuska yana cewa kun sha ruwa lafiya kowa yace lafiya lau daddy har dasu Amira da basuyi azumin ba cikin mu. Ganin babu komai na shan ruwa a gaban shi yasa anty cewa yau baka samu abin buda baki ba ke nan an dau fushi dakai ? Inajin haka namike inacewa yaran suzo mu tafi sai naji yace miko min jinior nan na dan taba shi na karasa inda yake na mika mai yaron ya karbe shi yana cewa dat is my boy. Na durkusa nace daddy nagode Allah ya kara rufa asiri yace amin sai a dinga tuki a hankali don kin san garin akwai cunkoson motoci da yawa banda tukin ganganci don Allah. Kuma ki mayar da hankalinki ga kararun ki don ki cin ma burin ki na zama likita dakike so ki taimakawa wasu kema nan gaba. Na sake tausa muryana kasa nace nagode daddy yace ba matsala sai ki yi ta hakkuri da kowa agidan don a zauna lafiya insha Allahu nace muka fice daga falin nashi nan muka bar anty tare dashi. Muna fita tace Allah dai ya kawo saukin wanan fitina haka mutane basu son azauna lafiya agida kullun da sabon fitinan da suke fitowa dashi idan gari yawaye. Na kuma fahinci duk sheri da makirci yana gurin Zulfa da tana boye halinta amma zuwan yanzu tafitar a fili da halin ta sai wani hafin kan sheri da sukeyi a tsakanin su don ganin sun cutata min a gidan nan. Yace hadin kan banza tunda ko kan su basu bari ba ina hadin kan yake anan ? Besty nabaka shawara kaki dauka ne suluntion daya ne shine ka auri Rahama shike nan amma kaki nifa ni na san hikimar dake cikin ha, , , Don Allah Saade ki rabani da wanan shirmay naki naji da abindake agabana please ? Kai ke ganin rashin dacewan haka amma ni nasan da zaka zauna kai naziri dakyau ka hango abindana hanga baza ka ki shawara na ba ai. Nan dai ta mike tana mashi sai da safe ta fice daga part din yayin da yabi bayan ta da hararan jin haushin ta a lokacin. Na yakai kan shi saman kujeran da ya jingina bayan shi tare da lumshe idanuwan shi yana tunanen wai ita sa,ade wata irin mace shin a duniya ? ********* ********* ********* Wanan satin haka azumin ya kasance muna agidan farkon shi babu dadin rai ga matan gidan da maigidan duka. Sai ranan da anty ta karbi girki ne yasan ya samu taron watan azumi da biyan bukata don mun hada mai kayan buda baki kala kala an jera mai. Ita kuma tayi kwaliya irin daya kamata na taron maigidan a gurin ta yadda ya kamata haka ya man ta da damuwan shi. Koba komai Saadatun shi, na son farin cikin shi akoda yau she da itace suke da matsala bazata barshi haka kamar mara galihu ba a gidan shi. Tana zaune a gefen shi inda ya zauna daga gefen ta yana saye da jallabiyan maza daya sauya daya shigo gidan daga gurin sallah asham. Ya kalli irin kayan buda bakin da aka girka mashi inganttaciyar cima ne na zamani aka hada mai mai warawarw jinin dan adam don wanan watan mai alfarma. A haka muka shigo gaida shi wanda duk yamma idan yana garin da watan azumi kowani part zasu shigo yi mashi barka da shan ruwa. Namiji ke nan gashi da karamin shekaru amma Allah ya bashi wanan girman haka mata har uku mai a gida kowace tana ji da kanta kuma duk zaman shi sukeyi. Zaune yake kamar kullun idan zai sha ruwa a kasa da alama ya gama buda baki koda muka shigo falon don yana dan kishingide ne yakara bayan shi ga kujera. Ita kuma anty tana zaune daidai saitin kafan shi suna fuskan tar junan su taba kofan shigowa falon baya. Yaran nasu ne agaba sai gajiye da Farida dake bin su kamar kullun nice a baya koda kuwa da anty zamu shigo gurin. Daga can dan nesa kadan nida gajiye da Farida muka tsugunna muna gaida shi ina dauke da jiniyo a hannuna . Idanuwan shi na akan mu lokacin da muka tsugunna muna mashi barka da shan ruwa ya amsa yana kokarin kawar da idanuwan shi garemu. Anty ce ta juyo garemu tana cewa aa shi wanan ai na dauka ko yayi barci ne fa ? Gajiye tace idon shi biyu yanzun dai suka gama kwasa da uwar dakin shi wai sai ta bar sallah ta dauke shi. Miko min shi nan inji anty na nufo ta da yaron ta mika hannu ta dauke shi daga gurina tana fadin kaji ba dan gatan maman shi harta sauya ma kaya kuma kana mata rikici. Gajiye ke fadin hajiya a rage kayan ne a shiga dasu ta juya tana kallon shi ya lumshe ido yana kada kafa dayan daya daga a hankali. Tace dashi a kwashe kayan ne yace tare da bude idanuwan shi No abarshi in an jima zan dan kara ci ne. Sai dai wanan abincin a tafi dashi nagama dashi ke nan yanzu tace wa gajiye a kwashe gajiye ku tafi dashi idan bazakuci ba a mikawa maigadi kada ya lalace a banza. Rama kin ko ci abincin kuwa don ke idan kina ciwo bakya son cin komai, da sauri ya bude idanuwan shi yana kallon mu tare da tambaya may ya samay ta kuma ? Tace dashi kanta ke ciwo tunda rana take kwance kasan ta da karfin hali haka ta tashi tai girkin nan da ciwon kan. Ki dauko mata panadol a daki tasha ko zai bari ya bata amsa tace don Allah dan jirani Rama wanan mai zukan ya kama nono ko. Shi da kan shi ya mike zuwa dakin shi sai gashi da magani a hannun shi ya miko min tace ga ruwa nan kisha don nasan ba sha zakiyi ba idan kin fita. Ko haka kikeson zama likita kina gudun magani sai son yiwa wasu allura kikeyi ke. Na bare maganin a gaban su ina hadewa Zulfa tashigo da yarta wani kallo ta watso min daga inda nake duke ina shan magani Hanifa tayo kaina ta rugumay ni tana cewa anty zan kwana a gurin ki kimin story. Da wani karfi uwar ta jaye hannun yarinyar a gurina tana fadin mara zuciya kawai zonan na rabaki da irin tsiya bakya ji ke. Wai ke zulfa may ye matsalarki ne yarinya baki bari tayi yadda take so ne wai may ye a cikin haka kuma tace ansha ruwa lafiya? Tana rike da hannun yarta gam ajikin ta ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna. A hasale ya karba mata na juya zan fita jinior dake shan nono ya saka kuka anty take cewa dawo dauki abinki kada ya damay ni. Dole na juya na karbe shi muka fita ashe bayan fitana sunyi kaca kaca kan abinda zulfa din tayi a gidan. Take cewa babu ruwan shi abarta da yarta ita ta haifi abinta tasan zafin abinta don haka ya kyaleta lumshe idon shi yayi yana mai jin kunan abinda suke mai a ranshi. Ya kyaleta ne wanan lokacin don idan ya tsanan ta magana za, a ce akan Rahama ne yakawo fadan ga zargin da ke tsakanin shi da yarinyar. Washe gari tun asuba na taya gajiye gyaran part din mu bamu kwanta ba sai da muka gyara komai muka wanke kayan abinci fariida kan bata saba da irin aiki haka ba ta koma ta kwanta kafin ai sallah. Bayan mun yi sallah gari ya dan haska muma muka kwanta don mu rage lokaci muyi barci. Barci sosai nakeyi hankalina a kwance can cikin barci nake jin ihu na tashin hankali a gidan da kyat na bude idanuwana dake da nauyin barci ihun a cikin gidan akeyin shi kuma ba mutun daya ba kamar ma harda namiji nake jin ihun. Cikin matsanacin tsoro da firguci namike zaune farida ma dake gefe na tamike ai muka kwasa mukayi waje da gudun mu cikin firgici. Nan mukaci karo da anty da tafito daga dakin ta sabale da danta suma barcin sukeyi a lokacin sukaji ihun suka fito. Da gudu muka kwasa muka fita inda ake ihun mutanen gidan kaf suna waje gurin katon rizabuwan ruwan dake a gefen da mai wanki ke wanki da muma mukanyi sauran aiyuka a gurin wani lokaci can ta bayan dakin Hindatu. Mun isa gurin ganin yadda suke ihu muna tambayan ko may ke faruwa sai nuna muna katon rizabuwan ruwan sukeyi suna kiran Hanifa hanifa ta fada cikin tankin ruwa. Innalillahi nace shine kuke tsaye kuna kallon ta hindatu dake kusa da uwarta dake ta ihun neman taimako tace yaya kike son muyi mu yanzu ? Lekawa nayi naga yarinyar tasha ruwa har ta taso sama da sauri na gyara na tsunduma ciki na dago yarinyar tare da dabara na mikota maigadi da shima ihun yakeyi kamar mace yana neman taimako ya cabe ta shida gajiye hakana fito a galabaice don na dade rabona da ruwa haka. Babu alaman motsi ko kadan ga yarinyar nan uwar ta sai faman yanka kuwa tana fadin ta mutu tamutu ko na shiga uku na lalace shike nan hanifa shike nan na rasa yar guda daya da Allah yabani na shiga uku ku taimaka min kudawo min da farinciki na don Allah. Sun kewaye ta sai faman kuka sukeyi ina fitowa nace don Allah ku daina kuka nan, ba kyau aiwa wanda ya fada ruwa saurin kuka haka please. Gurin na nufa da sauri na duka na fara jaye mata ruwan ta hancin ta da ta bakin ta ina zubarwa ba motsi ko kadan gareta, sai cewa hindatu keyi aikubar wahala ta mutu kawai wanan bazata tashi ba ai. Nan Zulfa ta zube kasa somama a kasa don kalamin hindatu ya kara firgita ta su kayi kan ta da ihu suna kiran sunan ta da karfi tare da firgici suke girgizata da karfi. Dukawa nayi dakyau na kuma naja ruwan hancin da karfi tai wani irin tarawa ta bude ido sai kuma ta rufe nace Farida dauko min key din motana da sauri please bata dauki lokaci ba sai gata dashi muka kwasa ni da Farida da mai aikin uwarta dake rugumay da ita sai gajiye sai asibiti. A guje muka shiga asibitin muna zuwa aka karbi yarinyar suka wuce da ita emargyncy da sauri. Babu mai waya a cikin mu balle a kira mu sai da Zulfa ta farfado ne maigadi ke fada masu aina wuce da yarinyar asibiti. Nan anty takira uba su lokacin yana gonan shi yana kallon dawa kan shi a can yaga kiran ta nan take fada mai yadawo gida ba lafiya fa take tai mai bayanin abinda ke faruwa agidan nasa. Cikin razana yake tambayan yarinyar ta mutu ko, take Rahama ta wuce da it's asibiti dai, wani asibiti suka kai yarinyar tace mun dai fice da ita a hannu. Mun kai awa daya da rabi sai gasu daddy da anty dasu mama laraba sun samay mu. A gigice yake tambayan mu ta mutu ko na girgiza kai a hankali nace bata mutu ba suna ciki da ita dai tun dazun. A lokacin likitan ya bude kofa yafito nan ya shiga mai bayani bayani sun gaisa da daddy yake tambayan shi yace ai an auna arziki an rage mata ruwan tun gida shine saukin ta gaskiya an ceci rayuwan ta da kafin Azo nan ruwan zai iya Mata I,lla ya kasheta, amma yanzu da sauki sosai gaskiya sai dai za, a bata gado don ta jirgita da yawa mu gani har wani lokaci. Bayan an bada gado muka zauna a tare da ita dagani sai rigar barci dake a jikina lokacin nake zaune saboda yadda muka fito gidan a firgice damu. Daddy ya shigo dakin da ledan magani a hannun shi kallo daya yaima inda nake zaune ya kawar da kan shi gefe yake tambayan tana numfashi kuwa ? Tanayi daddy naba shi amsa a takaice batare da na dago kana ba hannu na yana rike dana yarinyar ina murzawa a hankali, sai ga gayyan mutanen gidan mu, Zulfa na gaba hankali a tashe ina ganin ta na mike a kujeran da nake zaune akai don in bata guri don nasan tana iya cewa may yakawo ni gurin yarta. Mama Laraba dake tsaye gefe tun shigowan su sun tsura muna ido suna kallon abinda nakewa yarinyar tace ina zauna Rahama ake jaruma ce kinyi kokari wallahi koke ya kamata kiga likita yadda ake fadin kin yi din gurin ceto yarinyar. Zulfa ta zauna a bikin gado tana cewa dani sannu Rahama nagode nagode kinji nan kowa ya shiga fadin albarkacin bakin shi akai. Ni dai na mike nafice daga dakin na samu su Farida nake ce wa dasu muje gida na canza kayan jikinan nawa please. A haraban asibitin muka hade da daddy naji kunyan yarda nake a yamutse dagani sai yar rigan barcin dake jikina sai rigan da aka cirewa hanifa ne ma na dora akaina madadin dan kwali ko hulla. Yake cewa cikin son ji yaya akayi kuma Farida ce tai katfin halin bashi amsa tace zamu je gida ne ta cire kayan jikin ta yace yafi. Muka fice daga haraban asibitin mun fara tafiya na sauke ajiyan zuciya a hankali farida tace ke Rahama ashe kin iya ruwa ne haka. Murmushi nai mata nace kin manta ni yar kauye ce Farida sai dai na manta yaushe rabona da ruwa wallahi. Ai kinyi kokari ji yadda anty zulfa ta gigice tana sambatu da mutuwa tayi killa ita ma mutuwan zatayi. Nace bari maganan Farida insha Allahu zata tashi da yardan ubangiji ban son yarinyar nan ta mutu wallahi. Sai da nake wankan ne naga inda naji ciwo a jikina duk firgici bai bari na sani ba sai yanzu da hankalina yadan kwanta. Nafito na shirya cikin wani wando da riga falo na koma na zauna nan yaran suka rufe ni da tambaya dana shiga ruwa yaya nayi tun ina basu amsa inajin kaina yana dan sara min a hankali. Haka yasa na dan kai kwance daga inda nake zaune har barci ya dauke ni a haka ban sani ba sai muryan anty naji tana tambaya ko lafiya na kwanta lokacin la,asar. Firgigit na falka ina salati sai dai jikina ya dauki zafi a lokacin haka na mike naje nai sallah da karfin hali nazo gurin hada abin buda baki ranan adadafe na taimakawa Gajiye muka hada komai nakoma daki na dunkule saman gado sanyi nake ji a lokacin sosai. Nasir ne yaje yake fadawa maman su wai banda lafiya sai gata a rude tana shigowa ta tsugun na gabana tana cewa Rama baki da lafiya inji danki. Nace kaina ke ciwo anty ta dora hannun ta a kaina jikina radau yake a lokacin . A hankali na runtse idona don sanyin hannun ta da naji a jikina huci na fitar daga bakina ina mika ta mike da sauri tana fadin baki da lafiya shine koka kumshe a daki haka. Maza ki tashi muje asibiti cikin karfin hali nake ce mata bari dai nasha magani basai mun tafi asibiti ba anty. Kin faye gardama wallahi sai ta fice daga dakin zuwa wani lokaci sai muryan daddy naji a dakin yana cewa . Ke Rahama mike muje asibiti dama tun dazun nai tunanen a dubaki ke ma tun a asibitin. Karasowa yayi bakin gadon tare da dan kai hannun shi saman wuya na a hankali. Wani irin yanayi naji a lokacin tundags kaina hae yatsan kafana sai da naji yar ajikina gaba daya. Na rutse idanuwa na sai ga hawaye na zubo min a hankali a idanuwa yace ku fito da ita mutafi ina waje ina jiran ku. Da tai makon gajiye na fito dakin jiki sai kaduwa yake kamar ana shocking dina a lokacin. Tare dashi da anty muka tafi asibitin nan muka karbi kati aka shiga dani ganin likita nan ya rubuta min allurai da maganunuwa da zan sha. Bayan an gama muka juyo zuwa gida a hanya daddy ya tsaya wani shago ya sayo muna kayan sanyi da nama gassasa mai zafi sosai na mikawa anty yace kila bazata iya cin abinci ba sai ki bata wanan taci. Tunda muka dawo gida na kwanta ban fito ba koda asuba tea din da gajiye ta hada min ban wani sha sosai ba . Washegari ba laifi na samu zazzabin ya dan sauka min yanzu na dan samu sauki na dawo falo na zauna da sauran mutane. Anty ce tafito daga daki ta samay ni zaune a gurin tace kin falka Rama yaya jikin yanzu daddy yazo ai har sau biyu kina barci ya tafi asibiti don ance jikin hanifa ba dadi tun daren jiya basuyi barci da dadi ba da ita. Farida tace da suwa suka kwana acan anty tace uwar ta da mahaifiyarta sai mama Laraba. Kai shine bata barsu su kwana da yarinyar ba Anty Zulfau bata da kirki wallahi sai lokacin nai magana nace ba rashin kirki bane tana son yarta ne shiyasa. Dubi yadda taci wa Rahama mutunci ranan sai gashi jiya ta taimaki yarta ni wallahi naga karfin halinki Rahama da kika fada cikin ruwan nan haka na ni may zai kaini. Nace nima wallahi ban san lokacin dana fada ba Farida yadda naga yarinyar a ciki kamar matatta hankalina ya daga sosai wallahi. Har da ciwo naji saida nazo wanka nagani ban ma san naji ba wallahi. Anty tace ai shine daddy ku ke magana tun a asibiti yake cewa bai masan irin godiyan da zai maki ba wallahi. Wayan anty ne yai kara ta dauka daddy ne a layi muryan shi bai fita yake cewa da ita yana ganin hanifa ta rasu fa. Da karfi anty tace hanifa ta rasu besty ? Lokaci daya duk muka mike tsaye muna fadin innalillahi wa, inna alaihin raji,u. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE , , , IDAN KON BIYA KIKA TUWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KANKI YAR UWA 28 Hankali a tashe gaba dayan mu muka mike sai muka nufi hanyar waje cikin tashin hankali. Babu kowa a haraban gidan a lokacin sai mai gadi dake kokarin kunna redion shi na hannu. Anty ke cewa maigadi ba a shigo da gawan yarinyar bane gida ko kuwa yace hajiya shin wani gawa badai Allah yaiwa yarinya rasuwa ba. Take cewa yanzu maigida ya bugo waya yake fada min abinda ya faru akan yarinyar. Cikin karfin hali nace anty bari kawai muje asibitin mu samay su a can asibitin gaba daya . Asibitin na kudi ne mai tsari daki ne harda kayan kallo da naura sanyi akwai a dakin mun samay su jugun jugun a tsaye daga kofan dakin hankalin su a tashe a lokacin. Daga inda muke tsaye muna kallon likita na kokarin ceto rayuwan yarinyar a lokacin. Hawaye ne yake sauka a idanuwana a hankali na dafe bakina da hannu kada sautin kuka na ya fito a lokacin. Na dafa kaina a bango yadda nake kuka shi ya kara tayar wa mutanen dake gurin da hankali sai cewa suke haba Rahama ku daina kuka haka mana. Daddy dake fitowa daga dakin tare da likita ya dago kai ya dan kalli gurin da nake manne da bango ina kuka cikin tashin hankali. Tambayan daddy da likita da suka fito daga dakin su mama ke tambaya da cewa ta tafi ko . Daddy ne ya juyo inda suke yake cewa sai hakkuri mama , Allah ya karbi abinshi ko. Nan gaba daya a lokaci guda guri ya rude da ihu shi kanshi daddy gani daya zakai mai ka fahinci karfin hali yakeyi kawai alokacin. Gaba daya muka kwaso muka nufi gida kowa hankalin shi a tashe gidan mahaifan daddy aka wuce da kayan yarinyar a can akai mata sutura aka kaita makwancin ta Allah ya karbi bakunci musulmi Allah ya gafartawa hanifa. Gidan ya koma shiru baka jin motsin komai sai dan hayaniya jefi jefi daga sauran bangaren gida ita ko Zulfa abin yaso ya mayar da ita kamar wata zautata don mutuwan ya bugeta sosai a zuciyar ta . Ba uwarta ba ko mu da muka dan saba da ita rashin ta yai muna zafi balle uwarta mahaifiyar ta ita ke nan mata a duniya ana neman haihuwan ido rufe don sun saka lamarin haihuwa a cikin kishin su. Bamu shiga gurin ta ba sai da dare lokacin mutane sun rage yawa a part din nata ni da gajiye da farida da Amira da Nasir muka shiga part din mata wani tsami ne ya daki hancin mu kace kamar ba dakin yar kwalisa bace irin Zulfa ashe namane ya rube a fridge yake wanan warin haka. Da sallama muka shiga dakin tana zaune da mahaifiyarta da mama laraba a dakin ta ga kaya a saman gadon an tara ko ina kwamatse a part din kamar dakin tsohuwa . Sallama muka fara yi sai muka fara gaida su muna masu yaya hakkuri Allah yasa ta huta. Mama Laraba tace Amira Amira Allah sarki kaunar ki abokiyar wasan ki yau Allah ya karbi abin shi . Shiru mukayi kowa da yadda yake jin zafi a ranshi sai Zulfa ne da tun ahigowan mu ta fara kuka sosai nasan ganin yaran da tayi ne na anty ya tayar mata da mikin rashin diyar ta datayi. Mun dan dauki lokaci zaune a falon munyi shiru nice nafara mikewa tsaye sai sauran suka mike mama ke cewa sannun ku da kokari kunje. Rahma Allah baiyi hanifa rayayya bace dan ba don ke ba ma ai da bata kara kwana ba kila don zuwan ki ne kika shige ciki aka dauko ta . Mama Zulai tace da ace tazo da wuri kila da bata sha ruwa hakana ba sosai. Nace wallahi muma muna cikin barci ne a cikin barci ne muka dinga jin ihu jin mu ke nan muka fito a lokacin ta dade ina gani a ruwan. Sai Zulfa dake kuka take cewa ai na dauka maigadi zai iya fitar da ita don nace a fada maku Hindatu tace wai a, a a bari mai gadi ya gwada a gani ko zai iya fitar da ita lokacin. Nan uwar ta ta hau fada tana cewa da ita ai idan baki daina bin wanan hindatun ba sai ta kaiki ta baro sosai. Farida tace ni haushi ma tabani data kama kirawa yarinya mutuwa tun bata mutu ba nan dai Farida ta basu labarin komai kaf ai kamar an tunzura Zulfa da Uwarta mama Zulai ne a lokacin. Mu dai muka fice muka barsu nan suna ta maida magana kuwa bayan yaki don mai faruwa ya riga da ya faru ko a lokacin. Haka na farko azumin yazo gidan ba dadin rai rasuwan yarinyar ya hana uban komawa Abuja gurin aikin shi a lokaci sai dai yakan je ya dawo amma ba ya irin dade bai gida din nan ba. An sa an kwashe ruwan tank din da Hanifa ta fada ciki an kara mai tsayi sama sosai ko babba sai yayi da gaske zai iya ganin iyakar shi amma akwai kan fanfo daga kasa inda ruwa ke fita. Mutuwar yarinyan yadan rage yawan fitina a gidan don yanzu ba wani hadin kai na gulma da suka saba hadewa ayi don a kullawa anty sheri da mu ma damuke a karkashin ta a gidan. Da alama Zulfa ta ja baya da hindatu sun samu matsala a tsakanin su a gida don yanzu ko azumine basu yawan zama guri daya da junan su kowa harkan gaban ta takeyi a lokacin. Ranan da maigidan ya kirasu kan abin kayan sallah da za, a saya a gidan nan rikci ya kaure a tsakanin su. Ko wacce na fadin irin abinda za, a sayawa yara a lokacin, Zulfa na daga gefe daya tana sauraren su abinda suke fadi. Har aka kawo kan zancen kayan sallah yaran gidan nan Hindatu ta zake itace mai bayanin abinda za, a dinkawa yara na sallah. Idan kaji yadda take bayani kasan da gaiyya take magana adole sune masu yaya a gidan yanzu don haka magana ya zama nasu bada Zulfa ba da bata da ko dunge a gidan. Sai da ta gama bayanin ta kaf Anty Saade da maigidan suna sauraren ta can anty ta nisa tana cewa ni dai hakan bai min ba ni da Yaran zamu shiga boutiqu mu diba abindaya dace har yan matan dake gurina. But sukaga Zulfa ta mike ta fice daga falon inda suke zaune tana sharare hawayen a fuskanta. Tausayin ta ya kama daddy da Anty shine ya mike yabi bayan ta yana bata hakkuri akan tayi tawakkali tabarwa Allah. Anty ma da yamma ta shiga part din na Zulfa ta samay ta a har lokacin a ya mutse ta zauna taci kuka har tagaji. Jin shigowan Anty Saade dakin yasa ta dago kanta daga inda take zaune a kasa duk ta kode da ita take cewa wa, alaikis salam. Ansha ruwa lafiya maman Hanifa sai kawai ta fashe da kuka jin an kirata da maman hanifa don anty ce kawai mai kiranta da wanan sunnan. Don ita Anty duk kan su da sinan diyan su take kiran su dashi sabanin su dake kiranta da sa,ade kai tsaye haka. Guri anty ta samu ta zauna a kusa da ita tashiga bata magana tana bata hakkuri tace da anty nagode maman Nasir. Yaune rana na farko da ta kirata da hakan anty tace ki dinga kai kukan gi Ubangiji don shi daya baki kuma ya karbeta a inda akeson ta yafi sanin hikiman yin haka dayayi. Idan kin dage da addua dakai kukan ki garshi sai ya baki abinda ma baki zata ba daga garshi ki dage da yawaita karanta Innalillahi waina alaihin rajiu, Allahuma ajirni fi masibati wa, akalif, lil hairan min ha, , , Sai kiga Allah yai maki sakayya da mafi alherin sa amma wanan kukan dakike bashi ne mafita ba a gareki don zaki iya jawa kanki wani ciwo kuma again. Bafa ke kadai ba mutuwan yarinyar nan ya shafa ba kowan mu yataba wallahi Rahma sai da na tashi tsaye sosai akanta take cin abu yanzu don ta saka abin a ranta sosai wallahi. Zulfa tai murmushi tace dole ne maman Nasir don ba karamin shakuwa ne a tsakanin su ba ban kara gaskantawa ba saida naga yarinyar nan tai kundunbala kan Hanifa ta fada ruwan nan don ceto ranta amma kuma Allah bai bar muna ita ba wallahi. Har taji sauki cikin dare saiga ciwo yataso kamar conbultion tana fisge fisge shine bai sake taba har ta tafi da shi. Anty ta sauke ajiyan zuciya tace Allah yai mata rahama yasa ta huta tamike tanace kiyi hakkuri ki fitar da damuwa a ranki kibita da addua shine tafi bukata yanzu a garemu. Tana fita Zulfa ta sauke ajiyan zuciya tare da lumshe idanuwan ta a hankali tace rayuwa ke nan koba komai dai yau Saade tai min rana don duk abinda ta fada min yanzu gaskiya ne. Ita Hondatu ma na fahinci kamar dadi abin yai mata babu wani damuwa akan mutuwan yarinyar nan a kanta ji yadda take magana a falo don kawai ni da ban da kowa yanzu a gidan maji haushi. Yanzu ai nasan zamana da ita a gidan nan dama can dai ai ba wai wani son tsakani da Allah muke wa juna mu ba don kawai mu hade kaine muci karfin Saade kwai yanzu ko tunda babu mutunci ta iya min haka ai kowa ya kama kan shi kuma. Tun wanan ranan gaiyyan hadin kai a tsakanin su ya watse ba ruwan wata da wata agidan kowa tashi ta fitar dashi kawai sai zaman ma yafi dadi a haka don an rage yawan tsegumi da gulman anyi an ce. ********* ********* ********* Mun shirya kamar yadda anty ta bukaci na shirya na rakata unguwa ni da Farida sai yaran da muka fita dasu ranan Gajiye kawai muka bari a gida. Wani katon shago takaimu kayane na redmaid na kasan waje nan muka zabawa yaran kaya masu kyau kala biyar biyar sai ni da Farida dake da kala hudu hudu nan itama ta zaba masu kyau da tsada nata takalma handbag da sauran kayayyaki haka muka dawo gida a gajiye . Ban zauna ba tare muka karasa aikin girki da Gajiye sai baya mun idar da sallah mun sha ruwa aka baje kayan da aka sayo muna kallo. Na kwashe na anty na kai mata dakin ta na samayta a kwance tace tagaji bata jin dadi don azumi ma ba kullun takeyi ba don yanayin jikin nata. Nace bayan na gaida ita, ga kayan ki nan na shigo dasu tace Rama don ki fa na sayo su saboda ba zan iya saya maki su ba a gaban Farida . Don bai yuyuwa na saya maku komai iri daya da ita tunda ba wai wani abu take muna ba banda hira da kwanciya. Nace a sanyayye ma gode Anty Allah ya kara rufa asiri tace amin zaki iya ki barsu a nan sai idan ta tafi ki fitar da abinki. Sallah saura kwana biyu mun samu hutu ta kwashe mu zuwa gyaran kai da jiki a saloon din da take zuwa gyara wanda ko ni daya yanzu tana turawa can. Ba karamin gyara akai muna ba mun dawo muka samu an kawo muna dinkunan da ta bayar ai muna nan kan ta fitar da banbanci a fili don nawa sunfi na Farida sosai. Take naga Faridan ta hade rai naji anty na fadin kai tella dai ho dinkin nan kusa wata uku fa a hannun shi sai yanzu ya hado da wanda na bashi na sallah yai maku. Sai dataji haka ta dan sake ranta nace kai dan adam ho gashi ita ba, a more mata sai aukin hira da barci idan kuma za, a sha ruwa itace ta farko gurin fitowa aci abinci bata jin nauyi da kunyan hakan. Ranan Sallah tun safe muke aikin girki a lokacin har Farida tai wanka ta shirya cikin daya daga cikin atamfan da aka dinka muna. Ban samu kaina ba nida GaJiye sai zuwa shadaya saura na rana don anty ce mai girkin sallah din. Wanka mukayi bayan mun kara tsabtace falo da dakunan gidan muna atamfa muka saka dogon riga ne wanda akaiwa dinkin manyan hannuwa mai dagwari biyu daga hip din rigan ya kamani sosai kasn shi ya wani bajewa sosai ina tafiya yana bajewa a kasa. Kicibis mukayi da daddy dake shigowa part din wanda ina ganin dawowan su ke nan a gidan tun fitan su zuwa sallah. Yana saye da manyan kaya a jikin shi farare kal dasu da hullan shi da ya dace da aikin da akaiwa kayan dake jikin shi. Kayan sun matukar karban jikin shi sosai yadine mai matukar tsada sajen fuskanshi ya kwanta qa fuskan shi lun lub ya kara mai kyau da kwarjini sosai. Gefe na dan rakube ina cewa sannu da dawowa daddy barka da sallah ? Yace an sha ruwa lafiya Allah ya maimaita muna nan naji gajiye tana gaida shi kamar yadda na gaida shi. Ya saka hannu a aljihun shi ya ciro bandir din yan dubu daya daya ya kirga ya fara mikawa Gajiye ya tana godiya ya kirgo ya miko min na rusunna nakarba ina godiya. Saiga Farida itama tana gaida shi itama ya bata nata ta karba tana kallon hannuwana. Ya shige dakin anty yajima sai gashi yafito yanayin shi ya sauya ga yadda ya shiga dakin don gajiye na mashi a huta lafiya bai amsa mata ba yafita da zafin rai. Kusan hakan ne ke faruwa dasu yanzu ba kamar yadda suke ba a baya a tsakanin su da zai fito da fara,a. Lokacin ina cirewa nasir fararen kayan dake jikin shi zaici abinci don nayi mai mutumin shi watau masa da miya yaji kayan hadi yayi laudi sosai. Saida yaron ya fara cin abinci ina gyara mai zama naji anty na kwala min kira da sauri na mike zuwa amsa kiran nata. Zaune take ta caba kwaliya nagani na fada takecewa dani don Allah ku fara fita da abinci falon daddy yanzu. Nace gaba daya zamu kai tace kukai duk abinda kuka shirya mai ba tsaya ma munyi magana ba ya fice yana fushi daga maganan gaskiya kawai. Nake cewa anty don Allah kibar batawa daddy rai tunda shima baya son a bata maki tace barni dashi kawai Rama baison maganan gaskiya ne shi. Naiwa jinior daya falka daga barci wasa yana washe baki yana min dariya nace bari na je na dawo na dauke ka kaji. Tace zai je gaida daddy ne shima nace cikin washe baki anty yanzun daddy ya bamu barka da sallah a falo ni dasu Gajiye da Farida. Tace ya riga ni baku ke nan don yanzu nake da niyar ba kowan ku dama nace to anty bari mu dawo sai kibamu naki ke nan. Mun kwashi kayan sai falon maigidan a can muka samu hindatu tare dashi itama ta caba kwalliya ba laifi tayi kyau sosai. Wasu abokan harkan shi ne yan chaina su biyu tare da wasu masu zubin iyamurai suka shigo falon cikin raha da dariya. Anty na bayan mu nan suka fara gaisawa da bakin da alaman ta san su dama ga yadda take gaisawa dasu din cikin sanayya. Mun kara shigowa da wasu kayan abincin a lokacin duk sina zaune har Zulfa ma ta shigo gaida bakin nasu da sukazo masu yawon sallah. Wanda naji sun kira da mr Benjamen daga cikin bakaken fatan ke cewa woow kubani wanan beautiful sister din mana naku hajiya. Sai aka kwashe da dariya ban da su Hindatu a gurin yace I realy mean it gaskiya idan zaku bani ita ina so don na huta da gorin ku hakana naki aure har yanzu. Raina na hade a lokacin don jin haushin kafiri wai ni yake so haka sai anty ce ke cewa ai ba addinin ka daya da ita ba. Kaga babu aure tsakanin ka da ita yace ba matsala ai in har tana sona zan barta tayi addinin ta nima nayi nawa ba shi ke nan ba. Bamu hakan mu ga addinin mu indai kai mace ne ita namiji zaka iya aurenta . Yace kai addinin ku fa akwai hikima a cikin sa sosai watau shi na miji a wani addini baida dama ya auri wata mace na daban daga cikin addinin ku ko ? Anty tace hakane Mr Benjemen yace gaskiya I love the girl wallahi kuyi hakkuri ku bani ita mana please. Daddy ne ya katse su ta hanya cewa su fara cin abincin da aka jera masu ko don su samu su tattauna abinda ya kawo su yi. Nikan zamu fita don mun gama abinda mu keyi mutumin ke cewa damu muzo mu karbi goron sallah mu. Farida ce ta karasa nikan kallon mai kama dana tsana da daddy ya jefoni dashi sau daya yasa duk na rikice a gurin . Nafara hanyan fita naji mutumin nacewa beauty zomana ki karba please kada kiyi min rowan wanan beautyfubeautiful face din naki please. Juyawa kawai nayi na bar falo do ba zan iya jure irin kallon tsanan da ake min ba haka na ga shi ya hade rai kamar bai taba murmushi ba balle dariya a duniya. Farida ce tazi min da kudi masu yawa wai mutumin yace a bani goron sallah na kuma yace wai abashi nomban waya na amma daddy ya koro ta gurin. Anty dake kusa dashi zaune ta shake murya tana cewa dashi yadda shi kadai zai iyajin abinda take fadi. Malam idan kai baka so ka bari masu so su taya mana wanan hade rai na may ye haka kuma ? Wani kallo ya watso mata tare da tsuki yana cewa baki da hankali nake gani yanzu sai nakaiki an auna ki gaskiya. Suko sauran matan sun zaci wani zancen soyayya suke a lokacin take kowan su ta hade ran ta tasha toka fuska ba fara, a zulfa ta fara cewa ita zata tafi ke nan su huta lafiya. Hindatu ma tamike tana masu sallama anty ce tare da mutanen dama ita sukafi sani don shi benjemen abokin karatun su ne tun a makaranta suke tare da daddy din da ita. Bata jima ba tai masu sallama tafito inda sauran suka bata alheri mai yawa wai su raba gaba dayan su har mu. Ta dawo da kudin a hannun ta nan ta zauna falo tana magana taga ban cikin dadin rai take tambayan may kuma ya faru dani haka ne ? Cikin bata rai nake cewa haba anty kafiri zaice yana sona don ya raina min hankali dariya farida ke min tace kinga sai muje church musha rawa ke nan. Maka nakai mata a baya daga inda nake take cewa daga fadin gaskiya yaga abinda keyi mai ne mana ke wani namiji zaiganki haka bai rola maki ba. Muna zaune anty ke cewa dani raba kudin nan daidai har ku da wa yan can akai masu nasu kisaka Gajiye datasha aiki a cikin rabon ita ma . Sai gashi kowa ya tashi da kusan ashirin ashirin su anty da abokan zama ta na cirewa ashirin ashirin sauran har nacire muna na kuma cirewa sauran yan aikin su hindatu dubu biyar biyar a ciki. Nai mata bayanin yadda na kasa tace kin kyauta haka ake so suma ai su lasa ko ? Tace Farida takai masu nasu har yan aikin nasu abasu nasu don ni bata son ta turani gurin su inba dole ba. Farida nakai kudin tamikawa kowa har yan aikin sai Hindatu tace da ita may nene wanan ana nufin iya kudin da suka bamu ke nan ko may wai ? Farida tacd shi nagani nima don a gabana aka raba tace na kawo wa kowa nashi nakine wanan. Tace ke may kika sani koma kinbsani ne aiba zaki fadi ba don kan ku daya kwadai ya rufe maku ido kamar wata tsiya ake kulla maku banda aikin wahala da kuke mata. Fita tayi ta barta tana bakaken magana a falon ta ta dawo ta fadawa anty abinda tace da ita da takai masu. Anty wanan irin abin nake gudu wallahi duk yadda kayi baka fita a gurin su na boye na gane may wai ? Run gumay nake da Nasir da yai barci a jikina idona akan tv dake aiki ana wasan barka da sallah yara nata mika gaisuwan su ga yan uwa da abokan arziki sai ga daddy ya shigo falon nan muka shiga gaidashi yana amsa muna cikin basarwa. Guri ya samu ya zauna a falon tare da cewa shi wanan baya barci sai a saman jikine ? Anty tace haka ta saba masu dashi wallahi ai akwai aki randa Rama ta bar gidan nan ga yaran nan . Yace yanzu wanan ta samay ni wai kudin da su John suka baku ba a raba daidai ba yaya akayine wai ? Salati anty ta saka tacd kai wanan abin wai damay yai kamane tace Allah yasa gasu a zaune kai maganan nan fada mai Rama yadda kika raba kudin. Nafara koro mai yadda nai kasafi tace to kaji don ni ita namikawa nace tafitar da na kowa har masu aikin su sai da Rama ta fitarwa da nasu amma kuma suce wai hakan baiyi ba. Yace nasan ai bazakiyi abinda bai dace ba akai zargine kawai irin nasu takeyi ina laifi anba kowa yasamu. Anty tace ni idan bai mata ba sai na hada da nawa duk ta rike bashi ke nan ba. Yamike yana cewa akan may zaki bata nata wata fi idan bata so ba sai ta dawo maki dashi ba dama ai ba donta aka bayar ba don wa yanda sukai aiki ne suka ba da. Ya fara tafiya yake cewa ke je shimfede yaron nan hakana ya kwanta ku daina bata shi dayawa ace yaro bai barci sai a jiki zaiyi barci kamar wanan. Na daga yaron tare da jan kafana da duk yai sanyi na fice rugumay da yaron a kafada na zuwa dakin mu. Ya juya gurin anty yana cewa kema ki dinga mata fada ta daina shagwabasu haka mana abin yai yawa wallahi. Rama da yaran nan ne sai Allah nagaji na sa mata ido dasu kagan su na yanzu basu iya zama sai a saman jikin ta sun riga ta saba masu da hakan ko . Nima dana shiga shirin kwanciya na fara yi bayan na shimfide yaron sai dai nasan ko na kwanta a lokacin dole na fito don rufe guri saboda anty a gurin maigida zata kwana ranan. Ban jima da kwanciya ba naji muryan anty tana cewa dani har kin kwanta ne haka da wuri Rama ? Ko fadan da daddy ku yayi na yaran kike wa fushi kuma ai gaskiya ya fada girma fa yaran keyi ke ko kina dada shagwabasu haka. Zama tayi a bakin gadon da nake kwance tana fuskantana sai duk nabi na tsargu da kallon da take min a lokacin . Tace yafara takurawa rayuwan ki ko a gidan nan da sauri nace wa anty ina mikewa zaune daga kwancen da nake tace dani daddy ku mana . Kallon mamaki nai mata nai wani tsuru tsuru dani nace a hankali cikin karfin hali anty daddy ne zai matsa min kuma ? Dake dashi anty ai a karkashin ku nake don may bazan gode maku ba balle ni anty wani matsi daddy ke min a gidan nan mutumin da zan share kwanaki ban gani ba idan ba ya shigo nan wani sain na gan shi ba. Ni idan bakuyi min fada anty ai abin bakyau kuma duk yadda kuka zartan dani ai a karkashin ku nake kuma ni wallahi ma banji yai fada ba a kan yaran nan. Tace na dauka shine kika shigewa daki ai kina fushi don maganan da yayi din ? Nai murmushi nace kai anty wai fushi kuma kin san yau tun hudu idon mu biyu nagajine kawai shiyasa na dawo na kwanta ni da mutumina kada ya falka yaji bana kusa dashi. Ta mike tsaye tana fadi ai na sani tace nidai tasi kafin jaririn naki ya falka din Allah ki shirya min yarona mu tafi ki rufe kofa. Tare muka fito daga dakin da ita zuwa dakin ta ina gana sakawa yaron over roll take cewa dani ta fito daga bandaki ke nan. Rama yadda kika saba yi muna wanan dawainiyar kina kula dani da yaran nan da zuciya daya ina gujewa ranan da zakice zaki bar mu wallahi. Shiyasa nake kokarin ganin baki barmu ba har abada mu zauna dake cikin farin ciki da jin dadi amma bazaki gane ba ke yanzu. Shima din da yake ganin yaran kina ahagwaba su ai bai ganewa ne yanzu ne suke samun kulawa irun na uwa daya dace yaro ya samu. Yaushe suka samu kula irin haka a gurina kullun yau ciwo gobe lafiya nake sai in share watan ni ma basu ganni ba suna zaune ana gwada masu ukuba gurin kishiya. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA HAKKIN AMANA YANA KAN KI DON ALLAH NA GANIN KI YAR UWA, , , , , 29 Bukin sallah akeyi don haka gidan bai rabuwa da baki ta ko ina shigowa akeyi wanda kusan yan uwan dangin mai gidan ne ke shigowa yawon barka da sallah gidan. Farida kan washe garin sallah ta hada abin arzikin ta sai ganin ta mukayi tana cewa anty ni zan tafi gida. Anty take cewa yau din nan Farida babu ko magana ta da yi murmushi tana gyara jakar kayan ta dake kafadan tana cewa akwai friends dina da muke yawon sallah tare dasu sune suke ta damuna da kira tun jiya. Daga inda nake zaune ina mata murmushi nace yanzu kina nufin tafiya zakiyi ki barni gashi munce zamu gida Zarah yawon sallah. Tace tafiyan ta kama ne nayi shi ai Idan ta tafi saina rakaki Rahma inji Gajiye nace shike nan kuwa Gajiye mu dawo idan kin zo mu baki labari ai. Namike na rakata har bakin get da kayan ta Hamza driver ne ya tafi da ita gida a lokacin . Na dawo na samu gajiye na magana da anty take cewa tun jiya da dare take fushi ban san may akai mata ba dai. Ranan dai ce min tayi wai ita da take yar uwar maigidan ma ba, a kulata kamar yadda ake kula Rahma a gidan nan. Anty tace kyale mahaukaci kune baku gane may take nufi ba fa ita adole wurin nan daddy ku take so. Lokaci daya mukace ita Faridan ke son daddy anty tayi yaya da daddy idan ma yace yana son ta. Kai amma Farida bata da kunya mutum mai mata haka kamar daddy zatace wai tana kyarkyaran shi a gaban matan shi. Gajiye Tace yau she ma zai so mace haka kamar Farida wanda keda mata irin haka a gida. Anty tace kada kuce haka ita rayuwan duniya haka take dama kuma Allah yafimu sanin abin daya dace a rayuwan mu don haka idan da aure a tsakanin shi da wata a gidan nan cikin ku sai ayi ai. Kallon mamaki naiwa anty wai ita anty wata irin mace ce mai saukin kai ne irin haka ? Hakan fa ranan da Hindatu tai muna kazafi sai budan baki tayi wai zatai farin ciki idan daddy ya aure ni. Ko wace mace na kishin mijin ta karara a fili amma ita anty sam bata nuna kishin mijin ta irin na sauran mata da sukeyi. Gajiye tace haba hajiya ina Farida ina shiga tsakiyan ku kishi yaushe ma Alhaji zai tsaya kallon wata Farida can. Anty tace kai Gajiye akwai ki da wani magana wallahi ai kamar yadda yaro yake dan son jiki zagi ko duka bai sawa yaro natsuwa haka na miji yake shima. Namiji da zaran mace ta iya tattalin shi tasan takon halaiyan shi shike nan idan tana da hakkuri ta gama da namiji yi nayi bari na bari sai kiji zama ya dore ana wance ta asirce mijin ta sai abinda tace da shi. Yanzu ki duba fadan daddy akan Nasir da Amira duk wanda ke gidan nan yaran nan basu saba dashi ba kamar Rama a gidan don may don ita ta zauna da yan uwanta a gida tasan ta ja yaro a jikin tw baki taba jin Rama ta zagi yaro ko tai fada dashi a gidan nan. Sai dai ta nuna masu soyayya da cusa masu tsoron Allah ta hanyan yi masu nasiha idan sunyi abinda ba daidai ba tare da basu labarin da zai tsoratar dasu bazasu sake maimaita abin da sukayi ba. Kin ga ai ta taimaka muna sosai gurin gyara tarbiyan yaran nan da basu samu ba a gare mu a baya da yaushe yaron gidan nan zai tsaya gaida babba can. Ni kinga in ba yanzu dana dan samu lafiya ba gajiye bana zama a kasan nan haka ko yaushe nike nan bin jirgi zuwa ganin likitana a waje. Gajiye tace hajiya wai may ke damun kin ne hakana don Allah ? Murmushi anty tayi yanayin ta ya juye a lokaci daya batare da tai magana ba tace gani nan dai gajiye abin sai Allah kawai yau ace wanan gobe ace wanan ke damuna. Yanzu haka ko azumin da na dan yi ne tun jiya nake jin alaman ciwon nan na son taso min wallahi. Da sauri nace subbahanallahi anty ai gara kije asibiti kagin ya matsa maki don Allah tai murmushi tace Rama ai nasha magani koda safen nan shine na dan ji saukin shi ai. Nayi shiru ina tunanen matsalan anty na mace mai kawaici da karamci irin anty samun ta a wanan zamanin sai an tona . Ku shirya anjima ina son muje gaida Abbana da sallah don yana gida yanzu nasan bai fara fita ba tunda sallah ne. Bana son zuwa gida idan Abba baya gida saboda yadda ake min a gidan shiya kikaga bai faye zuwa ba idan ba wani dalili mai karfi ba zai kaini gidan. Gajiye ce ke cewa matan gidan fa ba suna nan ba tai murmushi tace sunan Gajiye kin san muna cikin lokacin da kowa nasa ya sani yanzu. Ba kowane zai iya kula dan kishiya ba ni ko zama ma basu yi da uwata ba amma sun dauki tsanan duniya sun saka min a rayuwan su. Don hanin da sukayi Abba na tausaya min rashin uwar da na taso ban dashi a gidan har yakai shi kan shi Abban ya fahinci basu kaunana ko kadan a gidan. Zarah ce kawai nake dan hurda da ita cikin yan uwana duk sun hurewa diyan su kunne akaina wallahi. Mikewa nayi zan shige anty ke cewa ina kuma zaki Rama nace naji kin ce zamu gaida daddy shine zan hada mashi cake da wani abin. Tace ikon Allah yaya kika san Abba yana son cake sosai Rama nace ranan naji yana magana an mashi cake ba dadi ai. Nan na shige na fara hada cake din na kuma gasa mai nama na peppeying din shi da kyau na hada fruits salad mai dadi na sa a fridge zuwa azahar har na kammala na shiga wanka ina wanka nake tunanen maganan anty akan Farida. Lalai biri yai kama da mutum don ko motan da daddy ya saya min sai da tai fushi sosai a kan shi tama dauke kafan ta a gidan a lokacin sai daga baya ta dawo kuma. Idan muna zaune da ita takama magana ke nan Rahama mutum ya samu miji irin daddy ai ya more rayuwan shi tun dai idan matan shi sukai mai wani abu. Ta shiga tsaki da korafi ke nan sai nai mata magana nace ina ruwan ki mutum da matan sa ke may ya shafe ki a ciki. Baki ganewa ne Rahma ita anty Zulfau tana ganin kamar tafi kowa cikin dangine da ya aure ta inba aure mukkadari ba ina ita ina shi mace haka kamar uwarta ba kiba ba wani zati da za, a gani ace wai matar shi ce. A lokacin sai nake dauka don tana yar uwarsu ce take jin haushin abin da ake mashi ashe ita abin ba haka yake ba a gurin ta. Nafito na shiga da yaran na kara yi masu wanka bamu fito ba sai dana gyara su tsab muka fito na samu ita anty bata ma shirya ba tana kwance da taimakona ta samu ta shirya ina shirya jinior take cewa daddy yace shi zai kai mu ai. Ban ji dadin haka ba naso mu fita da ita kawai don mu dan yi yawo saboda mu ga gari da bukin sallah da akeyi. Na fito da kayan dana hada tana gani tace ikon Allah Rahama ashe yau zaki saka Abba cikin farin ciki dama yana min korafin nabar kawo mai abinda nake mashi a da can baya. Muna fitowa dauke da basket biyu ni na dauki dayan Gajiye ta dauko dayan yana cikin mota mu yake jira ya bude buth din motan na saka kayan a ciki. Na koma na karbo jinior dake hannun anty suna fitowa kamar kullun motar shi bakajin komai sai sautin tashin kira, a a cikin sa ta tsaya ta rufe kofan shiga part din mu ta miko min keys din na kada a handbag dina. Tana gaba nida gajiye da yaran muna baya nan muka gaida shi ya amsa muna kamar dole. Yaja mota muka fara tafiya suna hira shi da matar shi nima a baya yaran sun matsa min sai da nai magana dasu har nabiye masu muna hira muma da gajiye. Uguwar su anty tsohon gari ne don gidajen dake unguwar zaka fahinci haka dagani suma gidan nasu daga baya akai mai kwaskwarima na zamani . Sai gidan ya haska uguwar sosai dashi da wasu gidaje daga cikin unguwar. Nan dai muka fito muka shiga ciki a falo muka samu Abban yana tare da wasu dattawa a zaune yan uwan shi. Muka zube kasa har daddy muna gaida shi yake cewa Alhaji Yusuf ka dawo ne kuma Allah dai yai maka albarka kin gane shi nan idan har yana garin nan sai yazo ya gaidani wallahi jiya nan yake da yaran nan sun zo gaidani da sallah. Yafi min sauran mazan yan uwan ki sau dubu wallahi shiyasa nake jin shi kamar ni na haifi abina Saade don yanzu ma kusan ya karbe maki nine ai . Tace kai haba Abba akwai wanda ya isa ya karbe min kai kuwa yace to tsaya kiyi wasa nan dai yaja yan jikokin shi yana wasa dasu wasan jika da kaka. Nan yake fada masu cewa kwana biyu ba, a karasa azumi dashi ba ai don jikin nashi ya motsa mai. Anty tace dashi ai Abba nima haka nake tun jiya wallahi tafiyan nan ma dai na karfin hali nayi don nasan yanzu ne ake samun ka a gida. Daddy yace amma Abba da ka daure idan zamu fita atafi dakai kaga likita kaima a can yace kai haba wani likita zan je gani har waje Allah dai ya yayye kawai za, ace yanzu. Rama baki ba Abba tsara ban ki ba mana sai lokacin na dan motsa shima Abban ya kallo inda yaji an ambaci sunana yace au itace yarinyar da kuke rikicin akan ta ke nan ko ? Rikici kuma nace a raina sai kuma nake cewa killa zan cen fitinan su hindatu ne a kaina yakawo ga kunnen Abba din. Abba itace fa kagan ta nan amma shine wai yake daukan magana a shirmay nakeyi yin shi daddy ne yace damu ku dan bamu guri Gajiye mu gana da Abba haka yasa nafi kowa saurin mikewa na bar gurin muka shiga daga ciki don dama nasan gidan muna zuwa da anty wani lokaci. Dakin wacce nake ganin ita ce uwar gida a gidan muka fara shiga muka gaida ita sai dayan dakin don su biyu ne a gidan. Kamar sauran gidaje su ma da alama ba wani zaman hadin kai kamar sauran gidajen da ake tsara akidar kishi a ciki. Muna barin gurin daddy yace ban san abinda ke damun saade ba ta matsa min akan maganan yarinyar nan har tana kokarin ganin mun samu sabani a tsakanin mu. Murmushin manya Abba yayi tare da jawo basket din abincin da mu kazo dashi a gaban shi yana dan budewa. Yace in ban da abinka Alhaji Yusuf yo tunda kaji har mace ta bude baki da kanta tace ka aura mata kishiya ai tana da hujjan yin hakan. Ai sai ka bari mu saurari hujjan ta muji yanzu ko anty ta nisa tace hujja na akan haka daddy ba wani dalili bane sai ganin da nayi rayuwan yarinyar ya cancan ci hakan a gare mu. Kamar yaya Saade inji Abban ya tambaye ta sai hawaye ya fara zubo mata a idon ta a hankali tace dashi. Abba idan kai la, akari da yadda yanayi yake yau ciwo gobe lafiya yarana suna bukatan taimako suna bukatan kasancewa tare da mai son su tsakani da Allah. Shi kan shi ai yana bukatan kwanciyan hankali tare dashi wanda kwata kwata tunda na fara ciwon nan babu shi a tare dashi. Amma idan ya auri Rahama ko bayan bani ina da yakinin yarana dashi suna da mai rike min su a tsakani da Allah kuma ai Abba wanan abin da nake son yayi kamar taimakon kan mu da kan mu ne za, a yi shi. Ni dai take jiyewa nikuma wallahi harga Allah na yafe ma ya auri yarinyar nan ta zauna damu babu komai a raina na burbushin kishin ta a tare dani sai kuka ya kubce mata a take a gurin . A, a a haba Saade may yakawo kuka kuma ana magana na fahinta anan magana zaki tsaya ayi a fahinci juna ko ? Abba ya kasa fahintar manufata akan yin wanan shawaran danayi ni kuma ina jiyewa makomar bayana ne a gidan. Haba Saade ai ciwo bashine mutuwa ba ga yadda wa yancan likitocin naku masu jajjayen kunnuwa sukace a baya wa ya dauka zaki kai wanan lokacin. Bagashi Allah da hikimar shi ba har da rabon haihuwa kin samu a hakan kuma aikwai may yine bayan Allah. Ki kwantar da hankalinki kiyi nazarin abin da kike kokarin shiryawa kada daga baya kuma kizo abin ya damay ki . Aure ne fa shi sha, ani na aure ana son kwanciyan hankali da natsuwa a cikin sa kada kuma ayi garaje abu yazo ya koma maki ciki daga baya. Abba na riga nai nazari sosai akan halaiyar yarinyar babu wani matsalan da za, a samu a ciki da yardan ubangiji. To maji ita yarinyar tasan da wanan magana ne a yanzu haka ga abin da kike shirin yi a kan ta ? Tace cikin girgiza kan ta bata sani ba Abba don ina son ne shi mu daidaita dashi kafin na tun kare ta da zancen tukun. Don insha Allahu Rahma mai kaunata ce bazata ki abin da nake so da ita ba tunda taimako na zatayi ga hakan. Murmushi Abban ya dan karayi yace kai Saade ban taba ganin mace maitaushi kamar ki ba don taushin ki har yafi na mahaifiyar ki baki rageta da komai ba a duniyan nan. Yanzu kai Alhaji Yusuf kaji hujjan ta dabara ta rage naka tun da ita ke bukatan yin hakan gareta. Daddy ya numfasa da karfi yace Abba kaji abinda take fadi wai hujjata ke nan a koda yaushe. Ita burin ta ke nan shiyasa take kokarin hasasa muna rashin zaman lafiya akan wanan magana da ta a ranta don nata manufan kawai. Tace eh shine burina don ni abinda zai fishe mu nan gaba nakewa bawai son zuciya ba. Hakan ne naga yafi dacewa ayi don samun mafita a rayuwan mu shiya kaji na matsa da maganan. Abba yace wanan shine abin da ake fadi idan kana son kama uwa to kaso dan ta da zuciya daya shine nan. Ita wanan yarinyar na lura ta yi amfani da imanin ki ne gurin gwadawa diyan ki son da take masu da zuciya daya amma baki ganin idan ta shiga ta samu nata watarana zata iya watsar da naki yaran ta kama nata. Daddy yace hakane Abba ba wani abu takewa wanan ba nikuma ban dauke shi a hujjju da zata sani abin da ban da niyya ba akan shi. Yanzun dai da ita da kai kuje ku kara sasanta kan ku a kan zancen amma ni Alhaji yusuf ai naga wanan kamar kai aka taimakawa. Don hujjan Saade gaskiya abin dubawa ne kaje kai nazari zanji daga gareka yadda kuka kaya daga baya. Allah ya tabbatar da Alherin sa Allah kuma yau maku albarka yasa wa zuria albarka dayyaba. Suka karba da amin Abba daddy yace amma ni Abba naso ne ai mata magana ta fita wanan zancen don Allah kada mu samu matsala akan shi nan gaba. Abba ya daga mai hannu yace na fahinci manufar hikiman saadatu ga hakan kaje kai nazarin maganan ta da basira ko zaka fahinci manufarta anan. Sukai sallama ta mike tashiga gida gaida gaida mutanen gidan kamar kullun babu wani kyakyawan taro da ta samu garesu sun dai gaisa da ita kadaran kada ham tai masu barka da sallah tare da fatan Allah ya maimaita muna takawo kudi ta basu barka da sallah sukakarba da godiya babu addua a kai mata kin shi sai su don kishi harda matatta. Muna dakin sister din ta murja don school din mu daya da ita muna dan mutnci a school da ita. Haka yas in nazo gidan sai nanemay ta mun gaisa da ita duk saurin damukeyi. Su ma yan uwanta tai masu alheri muka fito bayan daddy ya bugo mata waya yana waje a lokacin. Tun shigowan aanty gurin mu na fahinci tayi kuka sai naji ba dadi a raina don kusan haka take yanzu kawai sI naji ba daddy a raina. Wani irin hattenes din daddy naji ya tsirgu min a zuciya na ban san rikicin da ke hada su da anty ba yanzu yake yawan bata mata rai haka ko wani lokaci. Hakan ya haifar min da kuncin zuciya a lokaci daya wanda ya sa naji sam bani ma kaunan ganin shi a lokacin. Don idan abin sa naki ji ni a yanzu shine a taba anty da yaran take mutum zaiga bacin raina lokaci guda. Tunda muka shiga motan har muka kai gida babu wanda yai magana a cikin mu ana tayawa ni na fara fita ban tsaya jiran kowa ba na wuce ciki fuuu dani ina jin Amira na kirana amm ban tsaya ba na shige dauke da jinior a hannu na. Ina daki naji shigowan su suma na fara kokarin cire kwaliyan dake jikinana sarka da awarwaro hannu na sai dai ban cire tufafin ba . Nan sauran yaran suka samay ni muka baje dasu kilishin da Abba ya bamu ne suke ci don duk mukaje gidan sau ya bamu kumshin kolishi mai yawa mu zo gida dashi. Gajiye ta shigo dakin tana cewa wai may kuma ya samay ki ne Rahama naga tun a gidan su hajiya yanayin ki ya sake lokaci daya. Babu komai gajiye haka kawai najini ahakakilagajiyan aikin danayi ne ya ja min jin hakan. Gajiyan aiki kan nasakihaka akwai dai koma may ye kiyiwa kanki fada ki daina saka damuwa a ranki don Allah, kin yi karama da tunane balle ma ban ga abinda akai maki ba da zaki saka damuwa a ranki. Nace gajiye bana son ganin bacin ran anty na ko kadan wallahi baki lura da yanayin anty na ba da tashigo cikin gidan su kiduba irin yadda matan gidan ma suka karbe ta kamar ba yar gidan ba gajiye ai wanan dole mutum ya kamu da ciwo. Zama tayi kusa da ni tare da kura min ido tace a hankali kamar may rada tace Rahama ki rufawa kan ki asiri kada ki jefa rayuwan ki ga matsalan da bai shafe ki ba don kin ga wanan mtsalace da ta shafi rayuwan auren su da gidan ba abinda ya shafe ki bane. Lalai Rahama ke yarinya ce karama har yanzu baki san mayye duniya ba amma ina ke ina saka damuwan wani a ranki har ya damay ki haka. Yau na tabtar da cewa yadda hajiya take kaunan ki haka ne kema kike kaunan ta da zuciya daya a ran ki. Altine ta fada min dama irin kaunan da kukewa junan ku a baya ban tabatar da hakan ba sai zuwana gidan nan na fahinci cewa abinda ma altine ta fada min a kan ku yafi karfin hakan. Don haka dai don Allah kibi a sannun kada yazo ya zama maki matsala daga baya. Ina sauraren ta har ta kai karshen maganan ta na saukar da ajiyan zuciya a hankali nace nagode Gajiye tace dole ne na fada maki gaskiya don ke tawa ce Rahama. Mikewa nayi zuwa dakin anty na samay ta ta idar da sallah tana zaune ishishire da kafafuwan ta tana dan murzan su a hankali. Ina shiga nake cewa antu kafan ne ke tauna kuma take cewa wallahi yanzu nake son kiran ki dama ki dan shafa min magani ga kafan. Maganin na dauko nafara murza mata kafanta a hankali tana dan lumshe idanuwan ta da alaman tana jin dadin yadda nake mata din. Maigidan ne ya shigo ya samay mu a hakan yake cewa tun bai karaso ba kafan ne kuma ya fara tauna take cewa shine nace Rama ta tausa min tun bai damay ni ba. Kamata dai yayi nai muna bukin wani sati mu fita zuwa ganin likita tun bai matsa maki ba shiyasa ban so kiyi azumin nan ba wallahi ke kina ganin kamar kin samu lafiya ne amma kika dage sai kinyi din. Yai dan tsaki tare da dan dukawa daidai saitin kafan nata shi ma yana cewa gaba daya ne yake tauna ko iya nan ne kawai. Ganin ya tsugun na gaf da mu yasa ni dan mikewa da nufin barin gurin sai yake cewa No zauna abinki zan fitane may kuke so a sayo maku ne zan dan fita . Tace Rama akwai abinda muke bukata ne a nan ko nace sheltox ne kawai nake ganin ya kare muna tace sai may kuma nake cewa inaga madaran daya rage zai kai kwana uku kila. Tace amma ki tuna kada kuma daga baya aza a tuna ya mike yana ce ta barshi dai zan fita kawai na sayo komai. Ya mike tare da fice tace dashi sai kadawo ke nan baza mu rufe part ba sai ka dawo din yace yayi kyai. Yana fita ina abinda nake ban bari ashe ta kura min ido ni ban sani ba sai naji tana cewa dani Rama may kuma daddy yai maki kike sha mai toka ne haka wai ? Gabana ne ya fadi don ban yi zaton zata fahince ni ba zancen Gajiye ne ya fado min a rai da take cewa kada na shiga maganan miji da mata don ban san abinda ya hada su ba ai. Nake cewa anty may kika gani ne halan tace barshi kawai amma naga daddy bai canci hakan ba ne na kara bata raina nace amma anty may kike mai da koyaushe yanzu yake yawan ganin laifinki haka bayan irin kokarin kyautata mashin da kikeyi ko yaushe a gidan nan. Kai Rama dama nasan maganan ke nan don kinga nai kuka dazun komay ? Magana ce kawai mukeyi dashi shine haushi ya kamani har nayi kukan amma ba wani abu bane da kike zargi. Rama wai yaya zakiyi randa akace babu antyn nan taki ne wai a duniyan nan gabana nane naji ya wani mugun faduwa ras ras mai makon nai magana sai kawai hawaye shar yazo min mikewa nayi zuwa dakin mu can na kafa kai ga filo ina ta rusan kuka sai danayi mai isata nan na dunkule har barci ya dauke ni a gurin. Gajiye ne ta rufe part a ranan bayan daddy ya dawo ya kawo muna sayyayan da yayo muna ko wani part ya kai masu nasu kayan bukatan . ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANI HAKKIN AMANA YA NA KAN KI DON ALLAH NA GANIN KI YAR UWA, , , , , , , , , , 30 Wasa wasa jikin Anty yaki dadi kwanakin nan haka yasa na mayar da hankalina gurin jinyan ta a lokacin. Mun godewa Allah bai wani tashi mata sosai irin da yake matukar kaita kwance ba sosai. Haka yasa koda yaushe daddy yana , makale da ita koda yaje abuja ne zai dawo bayan kwana biyu sai shirin fita sukeyi waje. Ranan da yai wani dawo ne yake sheda mata ranan jumma,a zasu wuce don haka ki shirya. Nan aka shiga shirin tafiya wanda akasari nice akewa sayayyan abinda za, a bar muna na amfanin mu a gidan. Komai da zamu bukata ba sai mun takura ba an saya muna a gidan an zube muna shi. Ana gobe zasu tafi ina manne da anty ban son abinda zai daga ni kusa da ita ko kadan. Take cewa taso ta yaye jinior amma daddy yace da saura nace anty aida kin yayye shi kibar min shi zan ji kewan shi sosai idan kun tafi. Take cewa ai da zata barshi ne sai dai ta dauko mama Altine tazo ta zauna damu a gida kada ya bata min tsarin karatuna. Tun da asuba sun shirya tafiya, idon mu biyu har yaran take cewa dani tare da miko min kudi masu yawa karbi wanan ki aje don bukata idan ya taso maku bana nan. Nace da ita anty wani bukata zamuyi da kudi bayan komai kun tanadar muna a gidan akwai shi tace karbi dai ku aje indan an kwana biyu ki dinga kai yaran yawo kuna sayen abinda suke bukata kada ki bari su shige kewan komai nace insha Allahu anty. Muka fito da kayan su waye nan tace damu zata ta sallami sauran mutanen gidan nan ta wuce tare da yaran ta kowani part sai da ta shiga tai masu sallama. Muna tsatsaye a haraban gidan tafito sai naji wasu hawaye sun zo min a lokaci daya naji wani tukukin bakin ciki da tashin hankali ya toshe min zuciyana idona ya rufe anty na fadin to Rama ubangiji Allah ya sada mu da alherin sa don Allah kiyi ta hakkuri da yaran nan na barki maki su amana a hannun ki. Koda ta juyo don mu hada ido sai taga kuka nakeyi nan ta tako ta karaso gare ni ta rungumay ni take itama ta fara kukan a wurin. Kuka mukeyi sosai sai da muka ba duk wanda ke gurin tausayi gajiye itama kukan takeyi tana dan share hawaye da bayan hannun ta. Daddy yana zaune cikin mota ta ya kura muna ido tausayi mu ke bashi, sosai yana mamakin bai taba ganin so da shakuwa irin haka ba a rayuwan wasu kamar namu. Ganin bamu da niyar sake juna ga yara har sun fara kuka yasa yafito daga mota hannun shi na saye a cikin aljihun wandon shi. Yazo inda muke a hankali ya jawo hannun matar shi yana ce is ok please kuyi hakkuri hakana, kamar wacce zata tafi, baza ta dawo ba wanan kukan haka. Ina tsaye muna kallon suka ja mota aka fita dasu daga haraban gidan ranan haka muka wuni suku suku damu. Da kyat na samu yaran suka sake jikin su don ban sha wani wahala ba gurin ganin na samu sun sauko. Da dare ina shirin kwanciya ne wayan anty ya shigo min ina ganin bakon nomba nasan cewa itace na dauka da murnana na yaran suka taru suka rufa min muka shiga gaisawa dasu. Har daddy sai da ya gaisa da yaran yai hira dasu sosai kamar ba kudi ake kashewa ba. Washegarin tafiyan su na shirya yaran don an koma schools dani dasu bamu dauki lokaci ba mukai sallama da Gajiye tare da kara jaddda mata takula ma anty da part din ta duk da na rufe duk inda ya kamata na rufo a part din muka fice zuwa makaran ta. Can muka hade da Zarah take ta min korafi wai anyi sallah amma naki neman ta har aka kare wasan sallah. Hakkuri na bata tare da fada mata cewa cewa anty na bata da lafiya yanzu haka ma an fita da ita zuwa ganin likita waje. Ta tausayawa anty tare da fatan Allah ya bata lafiya takece aiko taga na ramay sosai a lokacin. Murmushi nai mata don bani wani dogon magana da ita wanda ya shafi shirin gidan su anty na. Haka mukaci gaba da gudanar da rayuwan mu dagani sai yaran babu rana daya da Hindatu ko Zulfa suka leko part din da sunan sunzo su duba mu suga wani hali muke ciki nida yaran . Da farko ina shiga na gaidasu da kwana amma da naga bamu gaban su gaba daya sai muka daina ba ruwan su damu muma ba ruwan mu dasu a gidan. Yau ban shiga school ba muna zaune a falo Gajiye ta mike tana cewa zata shiga ta hada miya don tayi abinci tunda rana. Hankalina naga handout dina da nake karan tawa jikina saye da wani bakin, dongon riga ya dan matseni sosai ya fitar min da surar jikina da kyau kaina babu ko dan kwali akai. Naji ana nocking din kofan part din mu kafin na nace yes naji an turo kofan an shigo . Dago kai nayi naga waye mai shigowan a lokacin wani matashi shine ya shigo saurayi ne da ganin shi gashi da matukar kwarji a tare dashi. Abu daya ne ya dan raba su da daddy shine shi gajere ne amma fari ne sol kamar daddy. Kamar su da daddy yayi matukar yawa sosai da gani ba sai an fada ma ba akwai alaka ta jini a tsakanin su. Karasowa yake tsakiyan falon haka yasa namike tsaye daga inda nake zaune tare da mashi sannu da zuwa. Kallon mamaki nake mai a lokacin don yadda ya shigo muna kai tsaye ga shi da ganin sa ka san boko ya huda shi sosai. Fuskan shi a sake yakarasa ya samu kujera ya zauna sai bayan ya zauna yake cewa dani barka dai yan mata nan na shiga gaidashi a cikin mutunci. Bin part din yake da ido zuwa can yake cewa ya naji gidan kamar masu gidan basa nan ? Na bashi amsa da cewa eh basa nan sunyi tafiya sai mu da yara ne kawai a gidan. For how long zasu kai a can na bi bayan kujera ina cewa ina ga zasu dauki lokaci a can don sunje ganin likita ne a can. Matsalan Saade ke nan na gyada kai a hankali tare da fadi a raunane da eyyh. Yace Allah ya bata lafiya ? Nace amin yamike yana cewa ni zan koma dama na sauka garin ne nake cewa bari nazo na gaidasu. Nace to barin kawo ma ruwa ka dan sha ko kada ka tafi baka sha komai ba agidan. Yace na dauka ai rowa zakiyi min don naga kamar kina tsorona baki sanni ba ko ? Nace gaskiya ban san ka ba. Yace nima ban san ki ba ai ke sister din Saade ne ko ? Na ce dashi eh anty nace ita. Yace ni brother din Yusuf ne maigidan nan mamana da dadd din shi thesame mother thesame dadd suke. Nace Allah sarki bari na dauko ma ruwan na wuce zuwa kitchen can na samu gajiye nake fada mata anyi bako ne yanzu. Na dauko goran ruwa da kwalin juice hade da cup a wani dan ture na kawo mai falin. Bayan na aje mai na koma inda nake zaune da farko na zauna a kujera muna fuskantar juna dashi. Yace amma ban san Saade na da sister ba haka da farko ? Nai dan yake ina cewa bazakan sani ba don ba a nan nake zaune da farko. Daga ina kike daga kai nayi ina kallon shi don tambayan yai min tsauri da yawa nagaji ma da hiran don ban saba tsayawa magana da maza ba mai tsayi. Na bashi amsa a takaice tare da daukan takardana ina cewa daga kauye nake. Anya kuwa sam bakiyi kama da yar kauye ba nagani a nan ?. Nace shi dan kauye har wani kama ne dashi dama can ? Yace well koma dai daga ina kike ni dai nidai nasan bada kauye kike ba don banga alama ba anan. Ya na tsiyayya ruwa a cup yake cewa koma may ye dai ni dama nazo ne na duba su don na dade bani kasan nan shekara na bakwai bana nan sai shekaran jiya na dawo shine nace bari nazo na duba su dama. Nace Allah sarki tare da bude takarduna danake karan tawa ya dauki cup din da ruwan yana tsiyayawa a cup din a hankali yakai cup din bakin shi, yafara shan ruwan yana min kallon kurullla na dago kaina don jikina ya bani yana kallona ne dama. Yai saurin kawar da idon shi a gareni yayi murmushi yana cewa kina karatu ke nan naga kin mayar da hankalinki ka alama handout ne kike karan tawa ko ? Cikin basarwa nake cewa dashi eh ina karatu ne anan b u k nake ya mike daga inda yake ya nufo gurin da nake zaune tare da mika hannu alaman na miko mai takardan ya gani. Ya dan duba yana kada kai yace ok da alama dai zamuyi babban likita ke nan a gidan nan nan gaba. Nace eh to kusan haka din ne in Allah yardan muna da hakan, na bashi amsa. Yayi murmushi tare da cewa wonderful . Shekara nawa kenan kike yanzu da farawa nace ? Nace karshen shekara ta biyu nake zan shiga na uku ke nan insha Allahu nan bada jimawa ba. Masha Allahu hakan yana da kyau Allah yasa mu ci amfanin aikin da ake karantawa a family baki daya. Nace amin a sanyayye tare da gyara zama na saboda yadda yazo gap dani ya tsaya a gaba na haka. Nan yake cewa karatu sai an daure balle irin wanan naku mai tsawon shekaru haka don haka sai ki dage ki mayar da hankalinki sosai don amfanin ki nan gaba. Nace insha Allahu zan dage da karatun duk na matsu ya fice sai dai baida alaman fita yadda ya tsare ni da tambayoyi haka. Don ni ban taba tsayawa hira da wani da namiji ba koda kuwa course mates dina nane bana sakin jiki dasu sam. Amma sai gashi yau shi wanan din da ban ko san sunan sa ba ya kafe ni da surutun tsiya a gida. Daga cikin aljihun shi ya ciro kwalin sigari yana kokarin kunnawa a lokacin. Wani kallo da ban san na watsa mashi ba na harara na watso mai a lokaci daya sai naga yai murmushi yana cewa sorry fa na manta ne ku matan hausawa bakwason cigiratte a kusa daku. Nace ba matan hausawa ba kawai ai duk wanda yasan ciwon kan shi da daranjan kan shi bai wanan dabian mara kyau ko a gaban waye. Murmushi mai kama da yake yayi tare da kakaro murmushi a fuskan shi a lokaci guda. Ya kalli a gogon dake daure a hannun shi yace ok beauty ni zan tafi koda baki fada min sunan ki ba amma ni zanci gaba da kiranki da beauty kamar yadda ya dace dake din. Yace zan tafi gida kada hajiyata taga na dade tai min fada ina na tsaya haka ni kuma ban iya fada mata nayi gamone da wata zukekiyar budurwa a gida brother na. Sai lokacin na danyi dariya har fararen hakora na suka baiyana a fili nace fada kuma kamar wani dan karamin yaro can ? Au baki san ana ma babba ma fada bane idan yana fita yawo akai akai ko yayi wani abinda ba daidai ba a rayuwan shi ? Nace Allah sarki hakane fa amma kuma gashi naga ba aima fadan shan taba ba kuma ? Yace cikin murmushi tare da hade yawun bakin shi tare da dan rankwafowa gare ni kamar mai rada yana cewa. Kin san yaro ya iya yiwa manya wayo yanzu kaf gidan mu ba wanda yasan da ina shan cigari yanzun ma daurowa tayi hakan. Nace cikin mayde bakina kadai bari zaifi ma alheri a rayuwan ka don badadewa ba za, a gane hakan tunda kadawo gaban iyayye. Yace hakane fa kin kawo shawara mai kyau kuma anan zan kula da hakan insha Allahu. Har ya juya ya fara tako yake cewa sai dai kuma beauty bata ban wayan taba mu dan dinga gaisawa ko jefi jefi. Nace ban da waya ai don ni karamace anty da daddy suna hanani rike waya a gidan nan. Kallona yayi cikin mamaki kamar zaiyi magana sai kuma ya ci gaba da tafiya har ya kai kofa sai kuma ya tsaya yana saka hannun shi ga aljiihun shi ya ciro waya guda biyu yana cewa dani. Ungo wanan kafin su dawo sai muna gaisawa dake ta nan ko yaya kika gani beauty ? Nayi murmushi nace kabar wayan ka don ni bani ketare maganan magabata na gaskiya. Yace ba kidai son gaisawa danine kawai amma ai bazakice min baki da saurayin dakike gaisawa dashi ba ta waya yadda kike babba yarinya dake haka ? Nace saurayi ni na kada kaina cikin dakewan fuska nace kun kun kun badai Rahama ba kan sai dai idan wata can. Yace nice name kamarki kamar sunan ki suna mai dadi haka ai yanzu ma koba komai kinga aina karu da sanin sunan ki ai. Yatako zuwa inda nake cikin wani murya mai kama da umurni yace karbi wayan nan Rahama please. Kabar wayan ka ni ina da waya sai dai na baka nombata kawai ka saka a naka ka kirani dashi. Ya sauke wani asirttacen ajiyan zuciya yace dama nasan cewa yarinya haka kamarki bazata rasa waya ba ai. Na fara karanto mai yana sakawa a wayan shi yace ya gode sai kin jini ke nan. Ban amsa mai ba yasa kai yafice daga part din na sauke ajiyan zuciya tare da bin shi da kallon takaici. Nai nadama da bashi nomban wayan da nayi ranan don yana fita ya fara kiran layina wai yana sheda min ya isa gida lafiya. Nace a gaida mutanen gida yace zasuji insha Allahu ya gode. ********* ********* ********* Tun muna damuwa da kadaicin dake damun mu a gida har muka sake jikin mu muka koma normal life din mu yaran sun fimu sake jikin su sosai don ba wani damuwan komai a tare dasu tunda suna samun kulawa tankar uwar su na gida. Idan ka gansu neat dasu ba kazanta ba yunwa ba damuwa akan komai koda yaushe suna lake a jikina yadda suke so. Abinda kuma sule so ban kiuyan yi masu shi ko yaushe haka yasa suka kara sake jikin su sosai damu. Ga gajiye tana nata kokarin sosai don ina bata girma yadda ya dace a matsayin ta na wacce ke gaba dani a gidan. Matsala ta daya yanzu shine bakon da yakira kan shi da suna Ibrahim yada yake kokarin kutso kan shi a cikin rayuwana. Don yawan wayan shi na matukar damuna a yanzu zai kirani a yini kusan sau goma albarka. Sai dai ban yarda na sake jikina dashi ba na fahinci yana son kulla alakar soyayya ne dani wanda ban tashi yin soyayya da ko wani da namiji ba alokacin nan da nake tsakiya ga karatuna. Dama ya damay ranan wani yamma ya matsa yana son yazo gida ya ganni nake cewa dashi yanzu ko lokacin kaina banda shi.. Don karatun jerabawan da nakeyi wanda ya matso min a lokacin don haka yayi hakkuri kada yazo. Yake cewa ba matsala Allah ya bada saan jerabawa zai jira har nagama exam sai ya fara zuwa nace dadai yafi kan. Yace amma zaici gaba da kirana muna gaisawa a waya kamar yadda mukeyi. Nace hakan ma gaskiya ba karamin takura bane a gareni gaskiya don hakan yana yawan dauke min hankali ga karatuna. Ikon Allah Rahama yaya kike son nayi to? Nace ban gane yaya nike son kayi ba da da babu ni yaya kakeyi a baya ? Yace hakkuri nace to ko yanzu shi zakayi din idan kaga kana iyawa. Naji yayi murmushi yace amma idan nazo gaida yaran brother dina zakiyi min alfarma ina ganin ki ko bamu gaisa ba ko ? Nagane wani salon wayau yake son yi min kuma anan. Nace ai gidan ku ne nan kana da ikon zuwa duk lokacin da kaga dama amma ba wurin Rahama dai kan don ban da time ni yanzu. Mukai sallama bayan yai min godiya yakashe wayan nima na kashe tare da bin wayan da harara kamar shine a tsaye gabana. Dama muna waya ina jin call na shigo min na duba naga anty ce a layin da sauri nai salati nace kaji sheri ko har anty ta kirani sau biyu wanan dan surutun ya hanani ji. Da sauri na kirata bata daga ba har kiran ya tsunke dama nasan idan ta gani zata kirani again. Sai ko ba akai ko second ba kiranta ya shigo min a wayana da rawan jiki na dauka ina sallama. Muryan ta radau ta karba min sallama na na fara gaida ita bayan mun gaisa ne take cewa dani. Dawa kike waya haka mai tsawo Rama nai maki kira har biyu baki daga waya ba ina jin ana samin line busy. Nace lah Anty ba wani bane fa wani can yake damun rayuwa na kwanan wai shi dan uwan daddy ne yace wai ko sunan shi Ibrahim ? Tace da karfi Ibrahim Ibrahim kamar tana mamaren sunan can tace badai Ibrahim din gwago Safiya ba nace haka yace. Tace yaushe Ibrahim ya dawo kasan kuma har ya gan ki nace ranan ne yazo neman ku shine ya ganni ya tsireni da surutu har ya matsa min sai da ya karbi lanbar wayana. To ki dai yi a hankali don in dai Ibrahim ne nasan yana da matar dake jiran shi tun bayan tafiyan shi acikin family din su. Nace anty ni ina ruwana dashi shine kawai ke haukan shi shi kadai amma ni inani ina tsayawa wani shirmay yanzu. Tace dadai yafi maki alheri wallahi ki natsu ki kama kanki irin su ba abin yarda bane don sun san yadda zasu sace zuciyar mace. Ta tambayi yaran nace da ita gasu nan sunyi barci yau sunce sunyi game ne a school shine suka gaji sukai barci da wuri. Ta tambayi gajiye nace tana kitchen tana wanke wanke tace na gaida ita nace zataji take cewa dama na kira nane naji lafiyan ku don tun safe yau bamu gaisa ba daku. Nace lafiya kalau muke anty yaushe zaku dawo ne anty duk gidan ba dadi wallahi baki. Tace cikin dariya Rama dawowan mu ba yanzu ba gaskiya don akwai maganin da nake sha ga kuma daddy ku akwai ayukan da yakeyi a nan. Mukai sallama tana cewa na shafa mata kan yaran idan sun tashi ince mummy tana gaishesu nace zasuji anty. Daddy dake tsaye fitowan shi ke nan daga wanka ya kashe ta da ido yana cewa dawa kike waya naji kina kiran Ibrahim. Tace Rama ce mana nakirata har sau biyu bata daga kira ba tana waya shine yanzu ta kira nake tambayan ta dawa take waya take ce min wai Ibrahim din gidan gwago safiya ne. Yace da wani irin murya mai kaushi Ibrahim Ibrahim kuma ? Yaushe ya dawo garin har ya gan ta kuma ? Tace wai ya kwana da dawowa bayan tafiyan mu ya dawo garin yazo gida shine ya ganta ya takura mata kuma sai da ta bashi layinta. Tabashi layinta kuma ita Rahama bata da hankaline da zata dauki layinta taba mutum irin ibrahim mayaudari dashi. Wanan dan iskan yaro tayi haukane halan da zata ba Ibrahim layin wayan ta kuma ? Tana jin hakan yadda yake magana a hasale dariya ya kamata take cewa to may ye kuma don taba dan uwan ka layin wayan ta shiba na miji bane ? Yai mata wani irin kallo yace eh lalai kuwa namiji ne kuwa tace to kagani yashigo layin da maza ke nuna bajintan su ne shima ayi dashi. Yace ai sai suyi din amma dai kin san ko waye Ibrahim tun farko da kike wanan magana balle yanzu da yazo turai idon shi ya kara budewa haka . Tace ni yanzu may kake son nace a nan tunda yana son ya gwada saan shi ne a kan ta kuma. Yace baki da hankali Saade har ke da kanki ke wanan magana haka akan yar uwarki kuma kan Ibrahim. Tace Ibrahim fa dan uwanka ne besty yaya kake son na hana shi hurda da yarinyar dake gidan ka ai Rama na da hankali bazata yarda tai wani abinda bai dace ba ai. Yace ok yayi kyau matsalan ki ne ai hakan banawa ba don haka dabara yarage akan ki yanzu ni ba ruwana. Tunda kin san yaron nan uwar shi ta fada muna an mashi mata a dangin su tun bayan tafiyan shi. Tace aiba aure aka daura mashi da waccan dib ba don haka yana da right din canzawa yanzu. Ya shiga sake sutura a jikin shi ba tare da ya kara mata wani magana ba ita ko sai dariyan mumuke take mashi a ran ta. Washe gari da yamma after five sai ga Ibrahim yazo gidan Allah ya taimakeni ina ban daki ina wanke unders di yaran da nawa nan ya samay su a falo suka shi hira da yaran. Gajiye ce tazo ta kyankyasa min zuwan Ibrahim din a lokacin don haka ma sai na turo kofan bayin na rufe kaina aciki ban fito ba. Sai da yagaji da zamane yake tambayan yaran ina anty sukecewa tana ciki tana aiki ne yace suce Uncle Ibrahim yazo yana gaishe ta . Nasir yazo yana kwankwasa ban dakin daga ciki nake tambayan waye yake cewa shine wai uncle yazo yana gaisheki a falo nace je kace ina amsawa ina abune . Nan ya karaci zaman shi da shirmay da yaran da zai tafi ya basu wani farin leda da yazo dashi a hannun shi. Ya tafi baiji dadin rashin fitowan da banyi ya ganni ba a lokacin ina fitowa kiran wayan shi ya shigo min na dauka naji yana sakin ajiyan zuciya yana fadin nagode. Nazo don na ganki amma kika boye kikaki fitowa nagan ki ko zanji sauki a zuciya na. Amma kika ki fitowa nagan ki Rahama why da kike min rowan ganin ki ne hakawai ? Ya kamata ki tausayawa wanan dan bawan Allah naki da ya susuce da son ganin ki kamat zan yi hauka. Dariya ya bani yadda ya ma rairaice murya kamar da gaske bayan nasan da yaudara yazo min already yana da wace zai aura ko a gida cikin dangin shi. Nace gashi ko fuskan nawa koda ka gani a lokaci ba zakaji dadin ganin shi ba don a hautsane yake yanzun haka saboda aiki kan fuskan dan kauye yadda yake ai dai. Yace babu ruwan ki ni dai ai ko yaya yake ni nace naji nagani zan gani a hakan . Nace next time if you are among the lucky one's. Yace insha Allahuma ina ciki don ba a taba Ibrahim raggo ba a duniya ai. Yace ki karbi sako a gurin dana nabashi sako ya baki da fatan zakiyi farin ciki da wanan sakon da zaki gani. Nace na gode koda banga sakon ba nasan sakone daidai da na yan kauye ai . Murmushi yayi yace ina jinn dadin sunan yar kauyen nan da kike kiran kanki dashi don alamane na sauki kai gareki. Nace to nagode da harka fara fahintar halayena don haka ka kula da sauran nan gaba. Yace indan dai har za, a bani dama na fabinta a hankali ai nafi kowa farin ciki nace yayi nagode sai anjima. A daidai wanan lokacin daddy ya shigo tsararen gidan su da suke can zaune shida iyalinshi idan sunje kasan. Ya samu anty a kwance da danta suna barci a hankali ya dauki wayan tare da kwashe lanban wayan da yake ta muradin samu daga gareta kuma girman kai ya hana ya tambayi matar tashi. Bayan ya yi nasaran kwashewa batare da matar shi ta sani ba ya sauke shu, umin murmushi a fili cikin sanda yafice daga dakin. Can ya koma waje kasa ya sauko gurin motar shi tare da samun kan shi da kiran layin wayan. Ina zaune ina sawa Nasir kayan barci muna shirin kwanciya a lokacin naga kira da lambar kasar waje sai dai ba anty bace to waye nace a fili. Na dauki wayan daidai lokacin da yake shirin tsinkewa tare da sallama cikin murya mai taushi. Daga inda yake a tsaye ya runtse idanuwan shi a hankali don jin wanan muryan da yayi. Ya daure ya amsa min da muryan nan nashi mai gadara sai lokacin nagane dawa nake magana. Yace yakuke nan na amsa cikin ladabi da lafiya kalau muke daddy yaya anty da jinior yace gasu suna barci ne. Sai nai shiru ina sauraren shi yace Rahama kina jini ko nace eh daddy. Yace dama akan wanan yaron ne da naji kuna waya dashi watau Ibrahim nake nufi nace eh daddy . Yace to ina son kiyi hankali dashi kada ki yarda ki fada tarkon yaudaran shi ki mayar da hankalinki ga karatun ki shi yafi maki alheri kinji ko ? Na amsa a sanyaye da eh daddy yace nagode Allah yai maki albarka nace amin daddy kukala da kanku don Allah kafin mu dawo nace insha Allahu daddy. Har zai kashe wayan sai naji yace dani anty ki batasan na kiraki ba don haka ba lalai bane tasan da hakan ? Nace insha Allahu daddy nakuma gode nai massalama na kashe wayan ina mai bin wayan da kallon mamaki. Mamaki nakeyi may zai sa daddy yace don yai min fada da kada na bari kuma anty taji hakan. Ban fahinci komai ba a ciki na dai aje wayan tare da karasa yaron da yai barci ko a lokacin. Sai lokacin ne naga ledan da Ibrahim ya bayar a bani na jawo ina budewa naga turare ne na mata masu tsada guds uku sai set din agogon hannun irin na mata shima ma igiyan daurawa a ciki kala kala duk kayan da ka saka akwai kalarshi da zaka iya sawa dashi a ciki. Abinda daddy bai sani ba idon anty biyu koda ya shigo tunane ya hana ta barci ta tashi tana nazari a ranta har yagama abinda yake yafita idon ta biyu tana kallon shi sai dai batan lanban waya dauka ba a wayan ta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYABA HAKKIN AMANA YANA KANKI YAR UWA DON ALLAH NAGANIN KI, , , , 31 Zaune yake a falo hankalinshi na saman system din shi da yake bincike a ciki. Sai jinior dakebarci da ga gefen shi saman dogon kujera hankali kwance yaron daya gama rikici ya samu ya lalashe shi har yai barci a lokacin. Ya mayar da hankalin shi sosai ga abinda yake yi a hankali take sauko zuwa inda yake zaune. Sai da ta karaso gap dashi ne ta yaji motsinta amma hakan baisa shi ya daina abin da yakeyi ba. Yau kwana biyu ke nan da ya dauki wayan ya ya dauki lanban da batasan ko na waye ba don haka take son ta tabbatar da zarginta a kan shi. Sanin halin mijin nata da tayi koda ta tsaya tambayan shi ba wai zai fada mata bane don ko fuskan haka ma bata gani a gurin shi ai. Inda watan shi ke aje saman desk din da system din shi yake takai hannu tana daukan wayan tare da fadin ara min wayan ka na danyi amfani dashi don Allah. Har yace mata uhum yana maici gaba da abinda yakeyi ko may ya tuna sai yakai hannu alaman ta miko mai wayan tare da tambayan ta ina naki ke ? Tace baida issashen kudine a ciki, yace da ita har yaushe na loda maki kudi a waya may kikayi dashi keda ba wani waye kikeyi ba. Tace ara min kawai ido ya tsura mata kamar yana son gano wani abu a gareta babu zargi ko wasa a idon nata yasa ya mika mata wayan ta dauki nata tana kokarin saka layin mahaifinta data fi zargi sai ga sunan mahaifinta ya fito ta kawar tana dan tunane can Rahama ta fado mata a rai ta kai gurin nombba na tana kooarin sakawa sai taga an rubuta . DHT mamakine ya kamata don haka cikin daurewa ta kira layin nawa sai kusan zai katse na daga da sallama batai magana ba don taji may zance , ina dauka nafara gaidashi tare da cewa daddy yaya anty da jinior muna gaida anty da jinior muna matukar kewan anty daddy adawo muna da anty mu please ? Na karawa Amira dake kusa dani wayan ina fadin Amira ga su anty da daddy sun kira mu. Tai murmushi dataji muryan Amira tana cewa hello Daddy tace amira mummy ce yarinyar tai ihu tace mummy please yau zaku dawo gidan ba dadi baku sai dai anty Rama kuma munajin dadin anty Rama tana bamu abin dadi da bakinan mummy tana kaimu yawo park mun je munga lion ni da Nasir da anty da Gajiye. Saida naji yarinyar nakiran mummy yasa na fahinci anty ne a layin to kuma shine batai magana ba tabarni ina zuba hakana may ke faruwa da ita ne wai ko kuma jikin ne ? Na karbe wayan a hannun yarinya na fara zuba mata shagwaba ina cewa haba anty na dauka daddy ne ai a layin don shekaran jiya yakira mu da wanan layin sai kuma nai shiru na tuna da warning dina da daddy yayi ranan. Murmushi tayi tace Rama ke nan waike yaushe ne zaki girma kidaina wanan shagwaban haka ? Jin suna wacce anty takira yasa shi saurin dago kai da sauri yana kallon ta batare da yai magana ba yana kallon fuskan ta sai murmushi takeyi tana sauraren abinda nake fada mata. Niko cewa nake anty shagwaba kan ai sai ranan da kika yaye ni kila zan bari wallahi anty na matsuki dawo kullun saina bude dakin ki na shiga na dinga shakan kamshin ki watarana har kuka nake don missing din ki da mukayi. Dariya na bata tace aiko sai dai kiyi ta shiga daki shakan kamshi na don ba ranan dawowa gare mu sainan da tsawon wani lokaci. Nace cikin kuka shagwaba wayyo antyna don Allah ki dawo kada na mutu jiya fa har zazzabi nayi na rashin ki a gidan nan. Tace ki mutu kuma Rama rufa min asiri please inkin mutu ai na shiga uku. Nace to anty yaushe ne zaku dawo wallahi muna son ganin jinior sosai munyi kewan shi munyi missing din ku anty. Tace ina ganin likitane Rama kuma daddy kin san aikin shi bana hutu bane shima aiki yai mai yawa sosai anan. Nace to anty injin daddy bai saka ki wanan bacin rai din don fa ni ina tsoro kada yai ta maki fada ban kusa balle nayi kuka ? Kai kedai Rama mashirirciya ne wallahi yanzu don daddy na sani bacin rai sai kiyi ta kuka nace eh mana anty ji nake kamar na shake shi anty don wallahi idan yana bata maki rai nakan ji kamar na make shi shima ran shi ya baci. Ban sani ba ashe tunda tace daddy kike jin haushi anty ya wauce wayan a hannun ta yana sauraren abinda nake fadi gamay dashi. Sai ji nayi yace ai sai ki kasheni ki huta ko stupid idiot na kike jin haushi Rama dip na kashe wayan da sauri tare da dafe kaina a fili ina fadin ma shiga uku. Gajiye da take zaune sai kalloni tayi tana fadin may ya faru nace cikin kwalalo idona waje ashe daddy yaji abinda nake fadi shine ya zage ni. Gajiye tace dani ai maganin ki ke nan ba bakiji ba shiga tsakanin miji da mata basai Allah ba. Nan shiga damuwa ranan ina fadin aiko na gata kaina wallahi yanzu ni daddy yaji irin hsushin shi da nakeji tafaru ta kare min nasan zamana a gidan ya kare ke nan. Tun mutumin da nake zaune a gurin shi yaji ban kaunan shi ai shike nan nawa ya samay ni sai komawa kauye ke nan. Nace idan na koma kauye karatuna fa nace na bashi hakkuri ya yafe min to amma kuma ai abinda kunya gaskiya. Can kuma yana kashe wayan anty ta kalleshi tana murmshi take cewa hmm Rama ta ke nan boyar Allah. Wani kallo ya watso mata mai kama da harara yace wanan yarinyar ko zanyi maganin ta wallahi ni take fadan magana haka a kaina. Anty ta murmusa tare da zama dan gefen shi kadan tana cewa akaina Rama na iya komai besty shi yasa nake son ta wallahi. Yace ai ban taba sanin rashin kunyan ta ya kai haka ba sai yau din nan ni zatace wai zata shake ko ta make ni ? Ita har yaushe ta sanki ta san dadinki haka anty tai dariya tana cewa bar min yarinya na please kada ka damay ta. Ya dan dago kai yana hararan ta yace cikin kutawa zata gane bata da wayo wallahi. May zakai mata besty ? Anty ta tambaya cikin son sanin abinda zai aiwatar a kaina yace ina ruwan ki amma ai naga ni ba ruwana da shiga harkan ta balle ta min wanan mumunan shedan haka. Idan baka shiga harkan ta ba ai kashiga na anty ta ko itako nice bata so taga kana batawa din. Bata makin may nayi ni din, tace bukatana a kan ta mana gareka ? Shine ta fahinci kana sani bacin rai a dan lokacin nan wanda da tasan dalili nasan da ta fi fushi dani bisa gareka. Ai idan baki barima sani zatazo tayi tunda harkin jawo karamar yarinya tana fadin bakaken magana na batanci haka akaina. Maynene maganan bataci data fada a nan kuma daga tana fadin ra, ayin ta kawai kuma. Oh wanan ba bakar magana bane a gurin ki ko har kina dariya haka don bake ta bata ba ke nan. Haukan Ramane baka sani ba kuma besty ai Rama tunda ta watse mama lauratu a kaina tun tana yar ficiciyar ta nasan bata wasa bace akaina. Yayi kyau yace tare da mayar da hankalin shi ga abinda yakeyi bai kara magana ba. Ashe ma kana da layinta a wayan ka ban sani ba ai na dauka baka dashi. Kallon ta yayi yace kamar yaya ina da layinta bake kika bani ba a baya. Tace ni kuwa kadai tuna amma bani ba dai kan Rama dake tsoron ka kamar may zanbaka layin ta kuma? Yace a, a bata tsoro na da batace zata makeni ba ai wanda kake tsoro ai baka ko gigin furta kalami mai sauki a kan shi balle wanan. Gaskiya ni dai ban san kana da layin ta ba sai yau din nan danagani a wayan ka yanzu. Cikin basarwa yace to wai samay idan ina da layinta ba, a gida na take zaune ba don na samu layin ta kuma wani matsalane kece dai baki san ina dashi ba dai. Wani kallon zargi tai mashi tare da kawar da kanta tana mamakin shi ita zaiwa muna funci don ya saci wayan Rama a wayan ta ko may ? Bayan gashi Rama ta fada da bakinta da layin ya kirata shekaran jiya kenan lanba ya dauka daya dauki wayan ta ranan. Shine girman kai ba zai iya bari ya tambayeta ba sai ya dauki wayan ta don muna funcin maza ya kwasa. Baibada kafan ta sake mai maganan ba ita ma bata sake bi takan maganan ba ido tasa mai taga gudun shi kawai. Amma abinda mamaki fa ji yadda take binshi akan zancen yarinyar nan yake wani basar yau kuma don yana son nombata shine zai munafunce ta damay yake son taji a rayuwan tane. A yadda ra san shi miskili bata taba zaton zai iya yin haka ba amma sai gashi ita da idon ta ta gan shi kuma ya basar to may yake nufi da hakan ne wai ? Amma kuma ko ma may ye ai ai yarinyar dai ta fada min in ma har wani magana ne yai mata ai da Rama ta fada mata. Kawai don kana son jin lafiyan iyalinka shine kuma sai ka munafunce ni don girman kai irin na besty nasan dai ba wani abu a tsakanin su sai tambayan lafiyan su kawai da zai yi, amma yana jin girman kan fada min hakan. ********* ********* ********* Abu kamar wasa sai gashi irin matsin da Ibrahim ke yawan kirana dashi a waya yasa har na fara dan sake jiki dashi a lokacin. Don zai kira waya yace na bawa kowa su gaisa har gajiye da muke tare sai sunyi waya da ita idan ya kira. Sai dai a waya kawai nake bari yaji ni bana yarda mu hadu a fili dashi don warning din anty da daddy da sukai min a kan shi. Hakan bai damun shi bai kuma hana shi kirana bayan dan wani lokaci shi dai kokari yake ya samu ya kafa gwaunatin shi gareni kawai. A haka har muka sharare kwanaki kwanki ya koma makwanni makwani ya share watan ni muna shakuwa tawaya dashi kawai. Sai faman shiri muke na dawowan mutanen gidan komai mun wanke mun goge munyiwa shiyan kwalla ni da gajiye gwanin ban sha, awa dashi. Dawowan nasu a lokacin ya samu nasaba ne da aiken da Alhajin shi ke mai na aurar da yaran yan uwasu da za, ayi. Ciki harda sisters din Ibrahim su biyu da zaa auran a lokacin dinkin duk event din da za, ayi Ibrahim yai muna shi har Gajiye da anty da bata kasan. Dawowan dare sukayi muna duk da dare ne bai hana mutum ya fahinci sauyin rayuwan da suka samu ba gaba dayan su. Abu ga yanayi ba guda ba da nan sun yi kyau sun koma freshen dasu ga lissafina dai watan su na shidda suke ciki dan dama daddy yazo dubai a lokacin suna can. Muma mun samu labari ne don matan gidan da suka tafi can bamu sani ba saida aka bugo waya ana tambayana ko an bar husna a gurin mu gida kamar yadda daddy ya bukata ayi. Nace husna anty maman ta bata nan ne take cewa ai basa nan yau kwanan su uku da zuwa Dubai don besty ma yana can wani aiki ya kaishi. Nace to gaskiya bata nan amma anty shine daddy bai kawo muna ke ba nan tace Rama kiyi hakkuri lafiya na yafi komai a gareku likita nake gani anan akwai magani da alluran da ake min duk karshen wata ne. Kinga idan nace nadawo na kuma koma akwai wahala haka a gareni nace hakane gaskiya tace to kuyi hakkuri ai na kusa dawowa din. Sai gashi bayan wata biyu din Allah ya dawo muna dasu lafiya muna zaune falon anty kunnuwan mu yana sauraren isowar su mussanman ma danaga an hada hadari basu iso ba sai nai tunanen haka din ne kawai bazasu dawo a ranan ba ashe sun tsaya clearing din kayan su ne a lokacin. Da murna mukayi waje da gudu don jin dirin motar su data tsaya sai dana dan tsaya don naga ta bangaren da zanga farin cikin rayuwana tafito a ciki. Dayan bangaren nagane ta ta bude mota tafito da gudu na kwasa nai gurin ta da murna na na rugumay ta duk wani dadi ya kumay ni sosai a raina. Gaba dayan su sun yi matukar kyau dasu na karbi jinior dake barci muka shige ciki ni ban ko tsaya gaida daddy ba ma. Hakan ya matukar ci mashi rai danayi nan muka baje a falo tare da gabatar mata da abinda muka shirya mata don bamu sa daddy zaici anan ba tun da ga matan shi a gida. Hira ya dauke muna hankali anty bata ko ci abincin ba shigowan daddy part din yasa mu natsuwa a lokacin. Ya sauya kayan jikin shi zuwa doguwar rigar jallabiya mai laushi da santsi daganin shi a galabaice yake a lokacin. Kujeran three seater dake falon ya nufa ya zauna tare da dan kishingidewa yana kallon yaran shi. Sai yanzu dana gan shi abinda ya faru a cikin waya ya dawo min sabo a raina. Muryan anty naji tana cewa dani Rama kin ko gaida daddy da dawo don banji kin gaidashi ba ni ? Sai lokacin ya dago daga ruguman da yaiwa Amira yana fadin ta gaidani ko ta shake ni tunda bata kauna na a duniya. Mikewa nayi tare da tsugunnawa kusa dashi ina gaidashi anty take cewa haba besty aiko Rama mai kaunarka ne jifa yadda muka samay su hankali a kwance ba matsalan komai. Kaina na sadda a kasa nace sannu da zuwa daddy yaya hanya kokarin kauda kan shi yake kamar bai son ganina a lokacin. Balle ni dake ji a lokacin kamar kasa ya bude in shige don kun ya Gaba daya hankalin anty yana akaman ga kunya ya rufeni na rasa abinda zan dafa naji sauki a lokacin. Banda zabi banda na kwashi tsuman kafana na shige daga ciki don takuran da nayi a gurin. Ina kuma zaki baki bani abinci ba Rama naji muryan ta tana fada min hakan. Dole na dawo na shiga jawo kayan abincin a gaban su take cewa zuba ma daddy nasan baici komai ba kila. Sai lokacin na dan kalleshi don inji may zaice akan abincin yayin da anty sai faman kashe mu da idon ta takeyi kawai. Na bude kulolin tare da dan tambayan may zan zuba masu kallon shi tayi tana cewa dear may zakaci ne wai ? Duk abinda aka zuba min zanci yunwa nake ji sosai wallahi ko barci na kasa kwanci nayi don ban samu an hada min komai ba a gidan. Haka ya sauko suka zauna kasa shi da anty ba su ko hau dining ba suka shiga loda abinci a cikin su. Sai da anty ta cika cikin ta take cewa dashi kan shi na duke yana faman kai loman tuwo a bakin shi ina nan ina kwasan kaya zuwa dakin ta dasu. Rama zo mana ki zubawa daddy fruit's ya kara dashi, don nasan yana matukar sha, awan shi sosai a ran shi. Wani irin faduwan gaba naji irin mai shirin tarwatsa zuciyar bawa a lokacin. A sanyaye na karaso gurin da suke tare da durkusawa gaban kayan ba abinda nake tsoro kamar ya tayar da zancen kuma again. Har na bude zan fara zubawa naji yana cewa No tabarshi zan diba kata ta turmujeni dashi kamar yadda tace zatai min ranan. Dukar da kaina nayi kasa kamar nace wayyo ni Allah a lokacin saboda gigicewa namike da sauri simi simi na bar falon na shige dakin ta ban fito ba har sai lokacin da naji ya fice. Anty ta shigo daki ta samay ni ina rikici da jinior wai shi ya manta da mu ko duk wanda ya tabashi sai ya sa kuka wai bai san mu ba. Tace kai jinior kada fa kaiwa Anty Rahma butulci kaine kuma yau kake mata kiuya nace ai barshi in yazo ya sauko nima nace ban san ka ba. Nace akwashe kayan kingamane a falo tace kwashe kedai Rama daddyn ku ya hanaki tsaya ko ? Nace cikin shagwaba ai wallahi anty duk kece kin san yana kusa kika barni ina ta zuba surutu ni yanzu ma wani ido zan kallesshi wallahi duk na shiga rudu. Tace akan may fita batun shi ki basar da zancen kin ji yayi ya gama ya dawo hanya ai baison gaskiyya ne ai shiyasa. In bashiba may ye na tsayawa mutane wani kwanaye kwanaye can kuma kan gaskiya. ********* ********* ********* Tun ranan bani yarda na hadu da da daddy agidan Allah kuma ya taimakeni bamu ma haduwa koda zai shigo nina fita ko kuma ya fita nina shigo gidan. Ga bukinsu ya kusa lokacin da anty ta dawo ta fahinci rawan kan da Ibrahim yakeyi a kaina amma takawo ido ta saka min taga gudun mu dashi tun da ban fada mata komai ba gamay dashi din data dawo. Nadai nuna mata dinkunan dayai muna na event din da zasuyi a gidan su harda nata a cikin tai godiya kawai. Ranan da yazo gaida anty bana gida shine take mai godiya kan dinkin da yai muna yai dariya yana washe bakin jin dadi. Tace amma Ibrahim ban son yar haka dakai fa bayan kasan akwai wacce zaka aura a familu ku shine kuma zaka batawa yar uwata nata lokacin. Ya shafa kai yana murmushi tare da cewa Anty nifa namiji ne ina da right din da zan zabi matar da nake so da kaina ba sai anzaba min ba. Kuma bayan haka kada ki manta da cewa zan iya aje mace hudu a lokaci daya ida naso yin haka so ni banga wani abin damuwa ba anan sai da sai idan baki son bani ita ne kawai don na rasa gane kan yarinyar gaba daya wallahi gashi ina mutuwan son ta. Ban sani ba ko akwai wanda take so ne amma kuma ga dan fahintana kamar bata da kowa a kasa yanzun haka. Anty tace gaskiya Ibrahim don bani kasan ne har haka ya faru daku don bazan ba da goyon bayan hakan ba gaskiya. Cikin mamaki yake kallon anty don jin kalamin ta yake cewa akwai matsala ga hakan ne ko may ? Tace akwai shi don akwai wanda Rama zata aura a gaskiya ina ga sai dai kayi hakkuri please. Nan daddy ya shigo ya samay su don ganin motar Ibrahim da yayi a waje yana ganin shi suka shiga gaisawa dashi. Yake cewa yanzu naga motan ka dana shigo nasan kana nan ke nan yaya wurin su gwago din ina suna lafiya dai ko ? Yace a kasalance lafiya suke daddy yace yaya kuma na gan ka a hakan dakai ? Ya kakaro murmushi a fuskan shi yace nazo gurin antyn nan nawa mugana kuma banji kwari gwiwa ba a gurin ta. Don Allah bros ka saka muna baki ta yarde min na samu hadin kan kaunan ta don naji ta fara min wani kwanaye kwanaye haka. Tsaki daddy yayi yana cewa maganan ku ce wanan amma wai kai ina yarinyar da akace an, ma zabi a gida a baya. Yace yaya shike nan don wanan reason din banda halin na nemi wata da nake so kuma a ra,ayina ko may ? Matsalarka ne wanan ni ba ruwana da wanan shirmay amma kuma ai naga kai har uku ka aje bros kuma kusan lokaci daya ko? Anty har hudu ma zai aje aiba daya kuke dashi Ibrahim don Allah na fada ma gaskiya bana son kaja min matsala dani da yarinyar nan ga Iyayyen ka. Sunyi ta fafatawa da ita karshe dai yamike yai masu sallama don daddy najin su yana ishishire ya dafe goshin shi da hannu daya kamar wanda kan shi ke mai ciwo. Bayan fitan Ibrahim din yake cewa na dawo gurin maganan motar kuce da suka iso don wa yan nan su damay ni da kai kara kan mota ko yaushe cikin korafina suke na sai wa sister din ki mota ban saya masu ba su. Nima ai hakan yafi min kwanciyan hakali tunda ba rasawa kayi ba kan ada abinda zaka saya masu din. Bai tanka mata ba sai gyara kwanciyar da yayi kawai a yadda yake a furin tare da ci gaba da dafe kan shi. Ibrahim yana fita gidan ya kira wayana ina gani naki dauka don ina hanyan dawowa gida a lokacin ganin yai min kira biyu yasa na daga wayan tare da rage saurin da nakeyi ina sauraran shi. Yana cewa kina inane nake cewa school yace yanzu naje gaida anty ki sai dai banji dadin zancen da muka tatauna ba da ita don haka nake so idan kin koma kikira tambayan ki nake sonyi tsakani da Allah kuma nake son ki bani amsa Rahama nace sai na isa din zan kiraka. Tafe nake ina tunanen wani magane wanan yakeson ya tambayeni tsakani da Allah ? Kodai anty ta fada mai cewa na taba aure ne yake son ji daga bakina idan gaskiya ne tunda ba maiganina ya dauka wai na taba aure a rayuwana. Naja tsaki nace a raina wani aure macan yanzu dana fahinci may ye aure nake gani aini renoma aka kaiwa Garbati ni kawai a lokacin. Ban dauka yana part din namu ba shigo da fara, ata a fuska ina cewa anty na nadawo sannu da gida. Ganin mutum kawai nayi kimkam zaune a part din mu kamar yadda yake abaya. Ina wuni daddy nace mai cikin sanyin murya batare da ya dago hannu kawai ya daga min yana cewa lafiya. Nai saurin shigewa ciki ban tsaya ba ban jima da shigowa ya mike tare da fadin ni zan fita ke nan tai mashi a dawo lafiya yafice kawai bau amsa mata ba. Kirana takeyi daga falo inda take nafito da sauri ina gyara hijjab din jikina na samu daddy yafice a lokacin daga part din na zauna muna gausawa take tambayana Zarah nace tanan lafiya sai dai cikin tane ke bata wahala yanzu ba kullun take samun fitowa ba sosai. Wai wanan ciki na zamani ko ga wanda ya saba ai wahalane balle mai sabon shiga haka kamar Zarah din abune na farko a gurin ta. Tace yanzu mutumin ki ya fita daga gidan nan ai nace wake nan anty tace dani Ibrahim mana ban yi magana ba kuma ban nuna mata ai ya kirani ba ma. Mun dai dan yi hiran yara namike ina cewa wai ina Gajiye ta shiga ne take cewa ina jin tana baya tana aiki a can namike nace ina zuwa anty . Kayan jikina na rage na gyara dakin kwanan mu tsab nafito na gyara na anty na koma falo inda take zauna waya na samu takeyi na ci gaba da gyara don yamma yayi sosai a lokacin. Mutanen ki fa za, a fashe masu haushi gobe motar mu zasu shigo gidan nan bayan ta gama waya naji muryan ta. Da sauri na juyo gareta nace kai anty da gaske amma naji dadin hakan wallahi don ko ranan nan bakwanan sai da akai min gorin shi. Anty Zulfa sai da nazo kusa inda take da kawar ta take cewa babu dangin iya babu na baba amma kin san sun iya tsafi ai yan kauye ta asirce mijin da matan gaba daya har wanan motar aida gani kin san ba don Allah aka saya mata shi ba. Anty tai dariya tace kai kishi dangin hauka da kurciya yanzu su gani suke asiri ki kai muna kenan ko ? Nace Allah ai yasan gaskiya ni ban ma san yadda ake zuwa gidan malam ba ko boka wallahi don ba, a taba zuwa dani ba. Muna nan ina aiki muna hira yaran suka shigo gida gap da magariba nan gida ya rude kuma na shige na dauro alwala don duk abinda nake bani jiran sallah ya rigani. Sai bayan na sallamay kamar jira Ibrahim yake ya kirani na katse adduan da nakeyi ina sauraren shi inda yafara da cewa. Rahama don Allah ina son ki fada min gaskiya don na kasa samun natsuwa a tare dani. Nace namay fa yace anty ki ta fada min akwai wanda kikaiwa alkawari don haka nafita batunki. Nace ni gaskiya ban sani ba kila dai itace tai min miji din ko amma kaima ai baka fada min kana da wacce zaka aura ba da farko. Ko ban da miji wanan dalili ba zai bari na yarda dakai ba uncle don komai nason gaskiya ai. Wani shock yaji don baiso nasan da zancen ba a yanzu yace kai may zai sa Saade tai min haka ne wai ? Na fada mata wanan shirmay su hajiyane kawai amma ni mata saina zabawa kaina gaskiya. Muna nan muna ta takaddama dashi har akai kiran sallah muka kashe wayan . Ina idarwa ya sake kirana nace don Allah dai the game is over kowa Allah ya bashi rabon sa dama ni ban sa aka ba ai inajin yana fadin Rahama kada muyi haka dake ki tsaya mu fahinci juna na kashe waya kawai gaba daya. Washegari ba school sai ga motar su ya iso gidan misalin goma na safe ya kira kowan su yazo waje kowace da kalar nata daga ciki akwai ja a kwai baki da issh colour. Key din bakar ya mikawa anty tace tagode yaba Zulfa key din jan ita ma godiya tayi sai Hindatu ta tashi da Assh colour din. Take ta nuna ita bakar take so a gurin yace sai ki dawo min da key dina ki jira bakar tazo maki ko ? Ta gane baka yai mata don haka ta mike a hasale babu godiya tabar falon yaja dogon tsaki yace yayi kyau. Murna muka shiga yi sosai yace idan suna so su bayar da tsufin kyauta ga wanda suke son ba. Haka yan uwa da abokan arziki suka shiga zuwa taya su murna da farin ciki samun karuwa da sukayi. Damun da Ibrahim yake min yasa na kashe wayana gaba daya kada anty fahinci wani abu tai min fada akan shi. Ya koma kamar wanda ya tabu don ya turo maigadi ya fada min gashi a waje yana jirana bayan sallah magariba ban so fita ba sai da naga anty ta tsura min ido yasa na mike tare da zura hijjab dina na fita daga gidan. Yana tsaye jingine da bayan motar shi ya harde hannayensa a kirjinnshi na iso da sallamta a gurin ya motsa kamar zai zo ya rungumay ni sai kuma naga yaja baya kadan. Yana cewa Rahama idon ki ke nan kwatakwata kin hanani zaman lafiya a garin nan kina neman caza min kai haka why why ? Ki natsu ki bani hadin kai mu cin ma manufar mu na rantse maki yarinyar da suke magana akai banine nace ina son ta ba hada ni da ita iyayye sukayi. Natare shi da cewa bin nagaba kuma bin Allah ba don haka biyayya ga iyayye yazama dole. Don Allah uncle ka bari muyi rabuwan lafiya dakai batare da rayuka sun baci ba so kake kajawa antyna wani sabon matsala ga family din ku kuma bayan wanda take ciki a yanzu. Dagakata don Allah ki saurare ni ina son inji daga bakin ki kina sona ko bakya sona ? Shiru nayi tare da dukar da kaina ina wasa da yan yatsun hannu na a hankali. Shiko ya tsura min ido yana sauraren abinda zance mai jin nayi shiru yasa ya maimaita tambayan shi cikin kura min ido. Kafin nai maga hasken motar dake tafe get din gidan ne da aka dallo muna sai da na kare fuskana don yawan hasken daya kashe min ido. Shima sai da ya kare nashu fuskan don hasken yai mai yawa a idon shi. Yace a hasale who is this baste, , , , sai yai shiru inaga yagane motar maigidan ne tafe a lokacin. Yake cewa haba bros wanan ai bai dace ba gaskiya bazaice bai gane mune a tsaye ba ai. Nace amma gidan shi ne tunda bai taba ganin hakaba anan dole ne ya bincika ko su waye a gurin ai. Ya furzo iska a bakin shi tare da dunkule hannun shi yana kaiwa daya naushi yake cewa ke nake saurare fa. Nace wanan duk babu shi don baida amfani jin amsa ta kawai kowa yai biyayya ga magaban ta shi. Yanisa yana cewa naji zan baki lokaci zan dawo naji amsan da kike yake da zuciyar ki nace naji don na kagu na shiga gida a lokacin. Nai mai sallama ya juya ya shiga mota tare da yin horn nikuma na tura get don na shiga ciki. Maigidan na hango can tsaye a bakin motar shi yana waya ya dafa hannun shi daya a saman motar shi yana dan bugawa. Nazo simi simi zan wuce inda yake tsaye naji yace cikin wani murya ke Rahama daga ina kike tafe yanzu a wanan lokacin. Nace cikin dan in, in niya dama dama ba ko ina naje ba nan nafito bakin get kawai, yace ok bakin get din ma by this our shine ba ko ina ba ? Nace ayi hakkuri yau ne kawai nataba fita a wanan lokacin haka kamar zaiyi magana sai kuma yai shiru yacs you can go baki da laifi ai. Na shigo ciki simi simi dani, anty na dakin ta a lokacin can na samay tana na lafe saman gadon ta ganin yanayin da na shigo dashi yasa ta fahinci ina cikin damu ta dago kai tana kallona tace yaya akayi ne Ramana ? Nisawa nayi na fara fada mata komai har yadda mukayi da daddy yanzu da zan shigo ban kai ga karasawa ba sai gashi ya shigo part din. Kwat ne saye a jikin shi ya bal, balle aninin gaban shi sai farar shirt din shi daya baiyyana a fili. Anty kecewa dashi kadawo ya amsa a kushe namike zan fice dakin yace No dawo ai donki na shigo yanzu. Komawa nayi na tsugun na a bakin gado shima zama yayi yace Saade baki wa wanan yarinyar warning bane akan Ibrahim ko may ? Tace kai tsaye bamu kara zancen shi da ita ba gaskiya amma ina son dama muyi magana don ina ga yaune farko zuwan shi gidan nan gurin ta a wanan irin lokacin. Yace ok ni dai ban son haka a gidan nan ki sani duk hiran da za, ayi ayishi da rana amma bani son hiran dare a kofan gida na daga haka ya mike ya fice daga dakin da alaman ranshi a matukar bace yake a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH HAKKIN AMANA NA TARE DA KE YAR UWA. 32 Tun wanan ranan na kara kama kaina ga alamarin Ibrahim gaba daya ya kasa samun na bashi dama ya shiga rayuwana. Wanda yafi dangata hakan ga ganin laifin antyna da kuma ni kaina din duk wanan bai sa anty ta tsira daga sherin yan uwan shi ba. Don cewa suke wai asiri mukai mai muka hana shi, sauraren maganan su akan umurnin da su kai mai ya auri yar uwarshi. Don takai bai jin kunya kowa dama ba kunya ne dashi ba hakan sai ya zamay mai madogora sosai yace shifa kauna saade zai aura. Ranan har takai dai an kira matan yan uwa zuwa gurin karban laifin sister din shi anty ma ta shirya ta tafi cikin dangi. Irin maganan da aka kama sakewa yasa ta fahinci itace akewa habaici hakana amma ta daure bata tanka masu ba har aka watse daga gidan ta dawo gida. Da yamma na dawo daga school ne na shigo naga kayan da aka basu a falo donut da drinks nace a, a ashe kin samu zuwa kenan anty ? Tace humm bari kedai naje na kuma sha gori da zagi wai ina son na raba ibrahim da yan uwan shi na hada shi da ke don naga gurin ci dama na saba kwace maza ai. Nace kai mutane akwai daukan wa rai zunubi wallahi wa ya damu da wani Ibrahim can ma. Sai faman shirin bukin sukeyi wanda nakan ga daddy yazo gurin anty akan maganan. Gaba daya yanzu hankalina ya koma gida duk da ina zuwa a duk karshen shekara na kwana biyu amma yanzu na dade ban tafi ba don tafiyan da anty tayi ne ya hanani zuwa wanan lokacin. Gashi inna ta ta samu ciki kuma nasan a wanan lokacin bata da nisa da haihuwa kamar yadda na samu labari. Nai wa anty magana bayan ta huta take cewa na bari su gama sha, anin buki sai a san shirin da akaiwa tafiya na. Ranan da za ai kamun amare na gidan su gwagon maigidan gashi ina da zuwa school amma anty tace idan na fita na dawo da wuri don mu tafi tare da ita. Gashi yanzu Farida ta dauke kafan ta da gidan mu sai dai dama gajiye tace min idan daddy ya dawo kasan ai zamu gan ta tazo tunda da manufa take zuwa gidan dama. Karfe uku na shigo gida a lokacin na fahinci kowa na gidan yana gida don ganin motocin matan gidan da nayi gaba daya harta maigidan a harabar gidan. Ina shiga falo Farida ce da anty zaune suna hira ina ganin ta na daure fuska ina fadin ai ki koma kawai tunda abin ya zama haka. Tai murmushi tace Rahama ai kin san yanzu karatu ne ke hanani zuwa ko ina ko yanzu ma don ina free ne na samu dan chans haka har nazo. Tare muka shiga daki da ita ina cire kaya a jikina muna kwasan hira da ita take cewa yanzu anty ke fada min wai yau kamun su Maimunatu ashe ? Na tabe baki nace yau ne wallahi gashi anty ta takura min wai sai mun tafi ni kuma ba zuwan ne bana son yi ba basu da kirki ne ya gidan. Farida tace ashe kin san halin su ke ma haka suke suyi ta wani daukan kai kamar diyan wasu can wallahi. Koma may ye ai muje muma mu gani ba sai an bamu labari ba muga irin karyan da zasu hada a gurin. Nace da alama dai dama don kin san za, a kika zo tace hakane nace kai Farida wallahi baki da dama Allah kuda ba a ganin ka a gurin banza haka kika koma dai yanzu. Anty ta aiko gajiye wai mu shirya lokaci ya kusa kada mu makara, haka nan muka fara shirin tafiya kayan kamu da ya saya muna na yan mta na saka a jikina wanda shine yan matan amarya zasu saka a gurin event din. Gaba dayan mu har gajiye muka fito da sabuwar motar anty zamu tafi ni tabawa key wai na jasu mu tafi. Duk saurin da muke ganin munyi ashe mun makara don gurin a cike yake da mata da yara an cika sosai can na samu guri na parker motar muka fito daga motar ina dauke da Jinior sai su Nasir da Amira da suka sakani a tsakiya. Idanuwan mutane kamar yadda mata keyi idan anje gurin buki da sunga wasu su mayar da hankalin su gare su ana gulma hakane muma muna zuwa gurin ido a kan mu caaa. Wata da nake gani yar gidan ne tazo da fara, a tana taron mu take cewa anty uwargida saurantan mata barka da zuwa dake da mutanen ki zo ga wuri acan ku samu ku zauna. Wasu yan mata dake gaba aka tayar aka bamu kujera muka samu guri muka harde muma muka shiga baza ido muna kallon sauran mutanen gurin. Muna nan zaune sai ga daya daga cikin yan matan amare mai kalar kayan dake jikina ta nufo gurin mu tana zuwa take cewa dani. Yaya kika zauna a nan zo mi tafi can mana ga yan uwan mu a gurin ai sun taru zamu fito da amarya yanzu. Na dan yi yake nace No da kibarni kin ga ina zaune tare da anty dina can ba wai wani nasani ba daga cikin ku ai. Tace kada ki damu tana kokarin jawo hannuna da ido anty tai min alama da na mike nabita . Badon naso ba na mike tare da mikawa Gajiye Jinior dake a hannu na na bita muka fice a haraban filin zuwa ciki. Muna shiga take cewa hi girls ga wata babban kamu na cafko muna a waje can ta koma ta zauna cikin taron mutane yanzu na ganta na jawota zuwa nan. Sai faman kallo na sukeyi don basu sanni na sai watace ke cewa yar uwa sai bamu san sunan ki ba kuma. Nace Rahama Aliyu by name scholing in b, u, k, studying doctoring digree three to four hundrent level. Sukace woow masha Allah ashe ke babban yarinya ce a cikin mu karama dake haka karatun naki yai sauri wallah Allah ya kaimu ga danshin ki yar uwa. Guri suka bani na zauna wata ke tambaya na a wani gida nake a gatin nan ne nake cewa gida Yusuf Abdallah Rano. Y, A, Rano fa mijin su Hindatu da zulfa da saade ke nan nace cikin gyada kaina da eh. Kice a gidan manya kike yarinya dole ina ganin ki naga tsarin ki bana yara bane ai dariya ta bani sai da fararen hakora na suka dan baiyyana a fili. Da sauri amaryan ta dago kai tana kallona cikin mamaki take cewa ko ke ce ke gurin anty Saade a gidan. Nace a hankali eh nice ni sister din ta ce ai tace no warder yaya Ibrahim ya kafe a kanki ashe kin kai haka din ne irin ku sai a hankali. Ke wani Ibrahim badai brother dinki ba ko tace shi mana ai ta sani kinga tayi shiru dama ina mamaki inda ta fito da ankon mu don naga ba wai na waye ta bane hakan. Shiya karban mata ita kausar din shi yace na bashi duk wani kayan program din saida ya saya masu su biyu. Kausar din ma bata iso ba har yanzu dayan tace kin san ta da shegen sanyi jiki ai. Magana suke an rasa wanda zai gabatar da program din a cikin su don ance sai anyi dogon sharhi su kuma duk kunyan hakan suke ji. Wanda na san bawai bazasu iya bane kawai dai halin mune na matan hausawa rashin sabo da wanan. Nikan da koda yaushe a cikin resche muke turanci yanzu kamar zubar ruwan sama yake shiga a kaina don dun dole mutum yayi ko baiwa Allah. Nace muga takardan wacce aka matsawa tayi ta miko min tana fafin ko zaki taimaka muna yar uwa kiyi muna please. Nace ba matsala amma sai ki mun bayanin yadda kuke bakatan ai maku ko ? Nan sulai min bayani na dan duba briefly na fanci may suke nufi akan takardan na dan yi masu yadda zan yi suka ce hakan yayi kyau ashe dama abinda ya hanasu fita ke nan ana zaune ana jiran fitowar su da amarya. An sanar ga amarya fitowa da kawayen ta wanda atake har na dan saba a cikin su ina dan fahintar sunayen su da halayen su gaba daya. Muna cikin jerin layi mun saka amarya a tsakiya a saka kida kaina yana a duke don ban saba da hakan ba har muka kai amarya saman mazaunin da aka tanadar mata. MC ya fara gabatar da abinda ya tara mutane tare da fadar za, abawa mai bude taro da addua sai kawai naji sunan anty na wai itace mai bude taron da addua. Nan dai anty ta mike ta shiga shararo addua sai da kowa ya natsu masu karbawa da amin suna karbawa karshe tai fata alheri ga ango da amarya da fatan taro ya watse lafiya. MC ya ce zasu dan saurare bayani akan Amarya daga bakin kawar ta watau Rahama Aliyu. Daga inda nake gabana yaba da dam dam is not easy mutum yai magana in public idan na wai ya saba bane dama. Ni dai ban saba ba karan banine yau nayi zan gwada nagani ko zan iya nan dai na fito aka fara tafawa nai sallama tare da fara kawo bayanai kamar yadda suka tsara na gyara tsab komai ya fito da kyau sai tafi ake man. A take furin ake tambaya wacece wanan yarinyar haka take wanan turancin masu dauka a waya suka shiga dauka har na gama. Anyi rawa da amarya a lokacin na dan jaye baya na nufi gurin anty na amma sai da wata daga cikin kawar amarya tazo ta jani muka shiga hilin muka dan taka rawa dasu ban dade ba na gudu. Nan guri ya rude aka shiga rabon seveniyan buki ni na daukan wa hindatu da zulfa nakai masu har inda suke zaune da kawayen su. Don da basu samu ba mun samu mu harsu Nasir da Amira saida aka basu nasu don an gamu a tare . Karshe dai Anty tace muzo mu shiga cikin gidan mu gaida gwago ban san gwagon ba nabisu muka shiga ciki. Tana zaune a falo da yan uwa da abokan arzikin ta harda hajiyan su daddy a falon muka shigo. Cikin ladabi muka gaida su suka karba muna kadaran kada ham a guri anty tai mata fatan alheri a kan auren. Mun daga zamu tafi take cewa wanan ce yarinyar da Ibrahim ke magana akan ta dama. Kafin anty ta bata amsa naji wata na fadin itace nima yanzu nake ji gurin su fati a waje. Wanan ai dole maza su rude a kanta yarinya kamar ita tai kan ta haka ai ina ganin ta nima sai da nai magana. Gwagon tace a, a ba cikin kayana ba gaskiya bani ba hada zuri,a da wanan irin a jini na gaskiya can gasu gada. Gwagon ta fadi haka kai tsaye dama daganin ta irin matan nan ne masu son izza da mulki a tare dasu. Gwago ai ibrahim zancen shi kawai yakeyi amma baya gaban yar uwata shima ya sani hakan bazai yuyuba ai. Tana fadar haka tace damu mutafin ku Allah yasa taro ya watse lafiya muka fice daga dakin wata daga cikin matar ke fadin haba hajiya safiya hakan ba girman ki bane wallahi. Yaya zakiyi masu haka kiduba fa yaran nan akwai matukar natsuwa a tare dasu kuma aishi aure mukkadari ne. Nan dai kowa ya shiga fadin albarkacin bakin shi har suka watse a gidan . Ran anty yai matukar baciga abinda gwagon mijin ta taimuna daga zuwa abin arziki zata bimu da mugun magana haka. Dan ta ma da baida tarbiya har take kokarin gayawa mutane magana haka akan shi gaskiya ita bazata dauki wanan irin cin fuskan ba nan gaba. ********* ********* ********* Tun wanan lokacin bamu sake halartan wani event ta ba kuma da akeyi ga wayan da yan matan har amaryan ke min akan may yasa na daina zuwa. Sai dai nace dasu kawai ai zanzo insha Allahu ina karatune shiyasa basu ganni ba. Ranan da zasuyi dinner suka matsa da bugo min waya har takai sun biyo ni gida suna son halarta na gurin don dai na da abinda suke so nai masu a gurin. Anty ce ta matsa sai na shirya mu tafi don itama zasu tafi ai gidan gwago ne dai ta dauke kafan ta da zuwa gidan. Kayan anko na yan matan amare nasaka farine kal an mai ado da zare mai sky colour da duwatsu masu kyau a jikin lace din. Duk wanda yaga ashobe sai ya yaba da kyaun shi dinkin bubu ne mukayi dashi na daura zanin shi mai girma na kulle a daidai tsakiyan baya na. Sai ashobe kai wanda launin sky colour ne shi na dauko na kafa a kaina tare da yar pos shima sky colour anty tace mu fita da motar ta nida Gajiye da yaran sai farida da itama shine a jikin ta don ta sayo kusan colour din mun shirya muka sallami anty kafin ta iso gurin. Gurin ya cika makil da dan mutum daga can gefe daya muka samu kujera a wani table muka zauna . Zamu iya hango masu shige da fice daga inda mukw zaune wayana yai kara na dauka na duba. Ibrahim ne ya kirani nai mai sallama yake cewa idan nace dake kinfi ko wace mace dake gurin nan haduwa zaki yarda dani ko ? Nace ba gaskiya bane yace to wasu zasu iya fada maki bayan ni don ni dai na sheda hakan. Mun gama wayan dashi ban san daga ina yake iya hangoni ba a gurin na dai raba idona amma saboda cikan gurin bazan iya hangoshi ba gsskiya. Wayan maryam daya daga kawayen amarya ce ta bugo tana tambayana ko na samu fitowa nace da ita ina cikin holl din yan zu haka ai. Nai mata kwatancen inda muka ba, a jima ba sai gata tazo da murnan ta tajani ban so ba muka nufi inda suke nima naja Farida muka tafi tare dasu. Nan event ya fara gudana ana gabatar da shigowan group group har akazo kan fitowan kawayen amarya wanda muke ciki mun shigo filin da rawa kamar yadda yake gudana. Ba wani rawa nakeyi ba amma wasu na ganin duk cikin sallo ne da yanga nakeyi irin ma yan matan zamani kawai muna tafe muna watsa flowers a ko ina a cikin rawa. IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE.. WACCE TABA WANI KO TA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH KABI MIN HAKKINA AKAN TA YA ALLAH KA SAKA MIN. ANA CEWA BAN JA ALLAH YA ISA BA SHIYASA AKA FITAR WACCE BATA SAN NAUYIN AMANA BA CE TAKE GANIN HAKAN ALLAH KABI MIN HAKKINA CIKIN GAGAWA GA WACE KE FITAR MIN DA NOVEL DINA WAJE, , , 33 Har muka kai inda zamu tsaya gurinda aka tanadar wa yan mata ji nake kamar na nutse a kasa don kunya don ban taba fita fili bainan jama, a ba irin haka nayi rawa ko wani abu makamancin hakan. Sai dalili wanan bukin koshi don a sakani cikin sha, anin ne bana son a fahinci may nake ciki a gurin. Iyayye, yayye, diya, yan uwa da abokan arziki na ango da amaraya sun halarci wanan gurin muna nan tsaye aka fara kiran babban abokin ango ya fito ya bada biograph na ango ga jama, a. Gurin yai tsit ana sauraren shi bayan ya gama ne mai sanarwa ke fadin yanzu za, a saurari na amarya daga bakin kawar amarya Rahama Aliyu. Wani iri naji dum dum gabana faduwa na kalli marya ta gyada min kai tana fadin kece zaki taimaka muna sister please . Da stly ta miko min takardan da zan karan ta na karba kowa ya tsura ido yana son ganin wacece Rahama din. Nafito a hankali nake takawa karan takalmana na bada sauti kwas kwas sai gurin ya hau tafi. Na fara da gaisuwa tare da yiwa mutane barka da zuwa da fatan Allah ya maida kowa gida lafiya. Nafara da dan bayani kan nice zan gabatar da tarihin amarya nan na fara gabatar da takaittacen tarihin Amarya har zuwa haduwan ta da miji ta cikin harshen turanci wanda mutane da dama ke ganin kamar a waje nake karatu ba a kasan nan ba. Ina gamawa gurin ya dauki tafi da fito na sauko saman tsage din da na hau sai hasken waya da ake daukana ke tashi gurin yab mata na koma na tsaya. Muna nan ana ta gudanar da shagalin buki wayana yai tsuwa na dan duba anty ce kece min yayi ina raba ido naga ko zan ganta tace ki duba kujeran dake dama dake na hudu. Gaba dayan su ne a gurin lokacin daddy ya fita kiran Ibrahim ya shigo daidai na kashe wayan. Yake cewa nazo mu gaisa da friends din shi pleplease don Allah kada na bashi kunya. Ban fita da wuri ba sai da na dan ja ajin mu na mata na sulale zuwa waje. Su uku ne da abokan nashi ina zuwa ake tambayan na wai dama wanan zukekiyar ce taka amma gaskiya ka taka babban saa Ibrahim nan muka shiga gaisawa dasu suna dan jana da hira a hankali muna dan dariya. Jikina ya bani ana kallona daga dayan gefen don duk gurin a cike yake da motocin mutane fal. Daddy na hango tsakan kanin wasu motoci yana waya ne amma idon shi yana akan mu gaba daya. Wani faduwan gaba naji don hango tsana karara a kwayan idon shi lokaci guda naji tsayuwan nason ya gagare ni. Allah ya taimake ni maryam ta kirani a wayan ta wai ina nake ana nemana nace gani zuwa. Nai masu sallama nace zan shiga ciki ana son ganina da sauri na juya ibrahim na magana ban tsaya sauraren shi ba na shige. Ina shiga take cewa wai ana nemana wasu ke son nafito nai rawa zasu yi min mannin kudi. Cikin mamaki nace ni ga muryan MC na ta cigiya na a fagen fili maryam taja hannuna muka haura zuwa sama. Wakan gwanja aka saka muna wai rawan shi zamuyi ni ta ina ma zan fara ne wai ? A hankali na fara takawa sai naga wani guy ya fito an taka mai baya da gani boss ne ga wasu. Yan dubu yafara manna min a hankali yana wani sake shu, umin murmushi kaina na dukar a kasa naji Mc na fadin da kyau major mustapha Sabo . Guri ya dauki ihu da tafe a lokaci daya sai ga Ibrahim ya fito yana lika min yan dubu dubu sai shima guy din naga ya murmusa ya fara manna wasu kudi masu kore shar take guri ya rude da sowa da ihu stage din take ya cika da mutane suna min manni yan uwan su na masu manni suma. Ganin abin nasu nason zama rikici daya a bayana daya a gabana a hankali na juya na nufi hanyan sauka basu barni ba ina tafiya zuwa kujeran dana barsu Gajiye da yara suna bina suna min manni har na zauna mutane sai sowa da ihu sukeyi. Mc yana ta kara zuga su a gurin kaina na dukar a kasa duk kunya ya rufe ni a gurin a hankali gajiye ta mike taja hannuna muka kama yaran zuwa wajen holl din aka bini da idanuwa kowa da abinda yake fadi. Gurin motar mu muka nufa nan ina kokarin shiga bayan na bude wanda aka kira da mustapha ya iso gurin da mutanen shi. Daganin shi kaka dan duniya na kwarai sai dai fuskan shi a daure yake tamau. Muryan shi kamar amon sarewa yake cewa hi beauty ba dai mun hanaki zama ba nida abokin hamaiyyan nawa dan naga kamar kishi ya rufe mai ido ko. Ban yi magana ba sai kallon shi da nakeyi na fada mota na zauna ina kokarin sa key ya sa hannu ya karbe key din a hannuna. Yace ina zaki tafi ban san komai ba a kan ki ni dai ba sai na tsaya fadar sunana ba don Mc ya fada kinji haka ma ya fadi naki kowa yaji. Abinda nake son sani yanzu shine a ina kike da zama kuma ki ban phone nomba dinki don naga wasa ya fita ranki ko. Amma naso ki tsaya don ban gama nunawa mutane shedata ba a kan ki kika fito. Ban iya yin magana ba don yadda nake ji zan iya yin duk abin da yazo min cikin dakewa na mika mai hannu ina fadin bani key dina please ? Murmushi yayi yace mai kyau komai naki na da kyau har fushin ki da zaki daure ki bari na dan daukeki photo a hakan dana gode. Wautan key din nayi daga hannun shi sai yai murmushi kawai yace Daniel execute my lady please. Ban tsaya bin ta nasa ba na tayar da mota muka bar gurin sai da na hau titi dakyau na hango bakar motar su suna bina a baya har biyu. Nace na shiga uku da wanan mutumin gajiye biyan mu fa sukeyi a baya a tsorace gajiye tace suna ina ne nace gasu nan a bayan mu tafe dabara nayi na kauce hanya nabi shorcut. Muna hawa titin da zai sadamu da gida sai ganin su nayi sun sha gaban mu ban tsaya ba sai get din gida nai horn maigadi ya bude muka shige da sauri muka fito zuwa ciki. Ina shiga Farida na kirana wai ina inane nake cewa gida tace what shine kika barni a furin maryam nace yi hakkuri please raina ne ya baci wallahi ban gan ki ba na wuce zuwa gida. Ba, a dade ba sai gasu anty sun dawo fuskan ta a daure yake sosai a lokacin. Ganin yanayin ta yasa na sha jinin jikina batai min magana akan komai ba sai shigewa dakin ta tayi. Nima dai dakin mu na shige na fara rage kayan jikina don duk sun isheni a lokacin dau nauyin su nake ji . Har bayan sallah kowan mu na daki yaran suka damay ni na fiti na basu abinci suci shine fitowa na lokacin. Farida ce ta shigo da kaya niki niki duk muka bita da kallo har anty dake fitowa falon a lokacin. Ta zauna tana fadin wash Allah ke kina nan ina can an tsare ni a kan ki ni yau naga fadan maza a kan mace wallahi. Ke kingani kuwa yadda wuri ya yamutse da fita sojoji sun tayar da hankalin guri haka akan ki. Anty dake zama tace ni san haka za, ayi ai tunda naji besty yace mu tashi muje gida tun ba, a tashi ba nasan da magana gurin. Nan farida ta shiga bamu labarin yadda fada ya kaule a tsakanin Ibrahim da soja. Idanuwana na rintse don takaici tace ai da gudu mutane sukai ta fita gurin wai an taba babban soja. Nace ni ina ruwana da zama babban shi daga shi har mustaphan duk basu cikin tsari na gaskiya. Anty dake sauraren labarin Farida tana kuma kokarin canza chenel din tv take cewa amma gaskiya ni ban ga laifin su ba ga mai babban laifi nan Rahama. Da sauri na dago ina kallon ta tace kin san yadda kike da farin jinin ga jama don babu namijin da zai ganki bai kyasa ba may yasa kika fita tsakar fili yin rawa. Banda na cewa don haka shiru nayi don ba sama nace da ita maryam ce tajani ai. Farida ce ta cece ni take cewa aiko Rahama bataso ba wallahi maryam din nan ce ta fita da ita nasan don kada taji kunya yasa ta fita itama. Koma may ye ai dai yanzu kin ja wanan kuma ni shiyasa ma tun farko ban so zuwan ku gurin nan ba wallahi. Nikan shiru nayi na makure a saman kujera cikin damuwa don naga rayuwan anty yai matukar baci a lokacin. Wanan kayan fa naji anty na tambayan Farida din tace bakin ga na manta ba na Rahamane abinda suka rabane a gurin maryam tace a kawo mata wanan kuma naku ne inji maryam din nasan don Rahama ta bayar dasu. Mika mata kayan inji anty ta fadi cikin basarwa nace ni may zanyi dasu kuma anty ? Ba naki bane ki bude mu gani mana ko haka za, a barsu a leda kuma na dago nace bude mata Farida don Allah na koma na kwanta tare da kawar da kaina daga kallon su ma balle nasan may ke cikin ledan. Tana cikin bude kayan ne sai ga daddy ya shigo da jinior a hannun shi nan aka shiga gaida shi na mike zaaune ina gaida shi ya amsa min kasalance. Yaron da ke barci ya samu kujera ya shimfide shi akai yana cewa sarkin kiriniya yayi barci yanzu . Mikewa nayi zan shige yace ku zauna abinku fita zanyi sai wayan shi tai kara ya dauka anan inda yake tsaye bayan sallama yai shiru yana saurare. Can ya kashe yana fadin ganinan zuwa anty ke tambayan shi yadda yanayin shi ya koma yace da ita gwagoce ta bugo min waya yanzui bari naje naji ko lafiya. Nikan yana fita na sulale na shige daki kayana na fara hadawa gaba daya gidan da garin ma sun fita min a raina a lokacin. Tsab na gama hada kayana duk wani abin amfani na saida na dauka, nabar na bari, jira nake safiya yayi kawai na bar garin. Anty ce ta shigo dakin ganin ta dakin wanan lokaci yasa na daga kai ina kallon agogon dakin idon ba idona ke gezau ba sha daya da rabi na dare wanda nasan a irin wanan lokacin ta kwanta ko ? Idon ta a kan jakkan kayan dana dora saman gadona sai kuma ta juya tana kallon yaran dana shimfide a saman gado na rufe su yadda ya kamata ai masu. Murmushi tayi tare da kara karasowa bakin gafon tace cikin nuna kayan da bakin ta wanan fa kayan may ye kuma ? A sanyaye nace nawa ne, May za, ayi dasu kuma shiru nayi tace bakiji bane may zakiyi dasu a nan nace gida zan koma gobe. Gida zaki koma gobe akan may fa zaki gida da umurmin wa maimqkon na bata amsa sai kawai na zauna na dafe kaina da hannu daya. Ba dake nake bane Rama ko baki jini bane wai ? Anty ina son in koma gida ne gurin su Inna kawai, tace da akai maki may anan din da zaki koma can ? Ni ba ai min komai ba zan dai koma ne can ne kawai. Karatun naki fa idan kin koma gida ? Sai nayi shiru, Tace akan baki son maganan gaskiya zaki zabi komawa kauye ki zauna ki watsar da karatun ki ko may ? Shiru nayi mata batare nai magana ba sai kukan dana farayi kawai inaga bata iya jure sauraren kuka nane sai naga ta mike tabar dakin. Shiko daddy da yaje kiran gwagon shi cikin daren nan ya samu ta cika fam tana jiran shi yana shiga ta tare da zance na da Ibrahim inda take shiga banan take fita ba wai dan ta daya ina son in salwanta mata shi. Daddy yace amma a gabana akai mai kashedi akan Rahama ai itama yarinyar da kunne na ji tana fada mashi ya fita harkan ta ai. Don haka gwago ba sai nayiwa Saade ko yar uwar ta magana ba shi dai za, aiwa kashedi akan ta don Rahama ko banza ba saar auren shi bane ita don haka yanemi wata can. Yai mata sallama yafito ya barta da takaicin cewan da yayi nafi karfin auren dan ta idan tana daukan dan ta wata tsiyace dama. Yana tafe a han ran shi bace shi kadai ke fada komay ma za, ayi da danta da har take son ganin laifin Saade ga banza. Bayan tayi sakaci tun farko ta bari ya lalace shi kan shi wanan mahaukacin sojan ba zai yarda yazo mai gida da hauka ba don yaga kalar shi baida mutunci a ido. ********* ********* ********* Asalin mustapha mutanen katsina ne a garin daura zama ya kawo kakan shi kano nan aka haifi iyayyen shi a kano har su din. Su uku kacal iyayyen shi suka haifa shine na farko a gurin su duk kan su maza ne. Sai dai ya taso cikin rashin ji haka yasa mahaifin shi ya kaishi aikin kakin soja ko zai daina halaiyar shi. Rayuwan gidan su mustapha rayuwa ne irin na incin kai kowa abinda yakeso yakeyi a rayuwan shi ba wani kwabo sosai ga iyayyen su. Auren shi uku yana rabuwa da matan batare da wani kwakaran hujja ba don acewan shi bai isa haihuwa ba a yanzu. Da zaran mace ta samu ciki zai dauki tsanar duniya yasa mata bazata kara jin dadin shi ba, sai kuma yayi sanadin da ya zubar da cikin ajikin ta karshe kuma ya sake ta. Kudin kan akwaisu don sun gada ta kaka da iyayye amma babu halin kai gida gareshi. Baidade da rabuwa da matar shi ba ta uku da ya auro a maiduguri shine nan kuma ya kyalla ido yagan ni a gurin buki ya zo bukin ne ta dalilin mahaifin ango don suna business dashi sosai. Tunda ya kyalla ido ya ganni ya haukace a kaina ya hana kowa nashi shakat a gidan su kan lalai sai anzo nema mai aurena don yaga Ibrahim ma da gaske yakeyi akaina. Haka yasa mahaifin shi baiyi sanyi a gwiwa ba da yake dan so ne dan gata da safe sai gasu gida gurin daddy wai sunzo nemawa dan su aure na. Daddy jin maganan yayi a ban barakwai don jiyane ma fa ya hadu dani shine yau da safe haka har mahaifin shi yazo neman aure. Wanan wani irin rayuwa ne haka da gani babbu kai a cikin ala, amarin ko ga mahaifin don daga maganan su ya fahinci suna matukar tunkaho da kudi da mukami ga mutane. Daddy yace da mahaifin nashi shi a sanin shi bai san ina da wani saurayi ba amma zai kirani a gaban su suji ta bakina. Ina dunkule a daki sai shawara nake ni kadai a zuciyana na gudu ko na tsaya don anty ido ta saka min kawai. Daddy ya kirata a waya yake cewa ta turo ni inzo falon shi ina da baki a nan da kan ta ta shiga dakina ina kwance na dunkule a guri daya kamar may jin sanyi. Ta tsaya daidai kofa tana cewa Rama nasan ba barci kike yi ba kije falo yanzu daddy ya bugo waya wai kina da baki a falon shi. Gabana ne ya fadi ras nace baki anty wasu baki gareni da zasu zo gurin daddy kuma tace kitafi koma su waye ai zakiji ko ? Hijjab dina na dauka na sa har kasa na nufi falon da sallama a bakina na shiga falon suna zaune su uku na samu a falon suka amsa min sallama na. Nakoma gefe na tsugunna tare da fara gaida su na dukar da kaina kasa ina sauren may ya kawo su gurina. Daya daga cikin mutanen naji yana fadin tubarakallah masha Allahu lailai wanan katon boy baiyi zaben banza ba ga ladabi ga addini da mutunci karara mun gani ba sai an fada uwa uba ga kyau kuma. Ikon Allah nacee araina waye kuma boye da suke magana akan shi dan shiru ne ya biyo falon na dan lokaci bayan mutumin ya gama maganan shi. Muryan daddy ya katse dan shiru yace Rahama ga iyayyen mustapha nan sunzo nemawa dansu auren ki ne . Shiyasa nace bari a kiraki muji daga bakin ki idan kin amince da maganan su ba matsala sai mu tsayar da magana tun basu tafi ba. Sai lokacin na dago kaina dake a duke nace mustapha ? Daddy ni ban san wani mustapha ba gaskiya ima ganin watakila dai bani bace ake zance akaina don ni ban san shi ba. Wani ajiyan zuciya naji daddy ya sauke yace to a gaskiya inaga ba gidan nan bane don banda labarin hakan a gidan nan. Eh haka din ne dayan mutumin da baiyi magana ba tun shigowana bayan gaisuwan da nai masu. Yace zaki iya fadin hakan don jiya jiyan nan ne ai kuka hadu a gurin dinner da akayi ko shine ya koma muna gida a rude shii yaga matar da yake so a gidan nan. Nace gaskiya bani bace baba sai dai idan watace yagani amma banice ba gaskiya. Hmm ki kwantar da hankalinki yarinya kece kada kiji komai don ba wani matsala ga hakan zaki huta a gurin boy ga abinda yake so zakiji dadin rayuwan ki sosai idan kin amince da bukatan shi. Nace baba don Allah kuyi hakkuri shima abashi hakkuri nagode da kaunan daya nuna min anan ma yadda nake a cikin jin dadin rayuwana nake. Don Allah yayi hakkuri ya samu wata asalima yanzu ni karatu nake yi babu zancen aure nan kusa a gabana. Nai shiru na dukar da kaina daddy yace to Alhaji kaji daga bakin yarinyar ina ga magana ya kare ke nan yanzu don Allah abashi hakkuri ya samu wata don ita wanan din yanzu haka karatu takeyi na likita kaga ke nan babu zancen aure nan kusa a gaban ta mun kuma gode da karamcin da kukai muna . Rahama tashi ki shige abinki mutumin dake da alama shine mahaifin shi yace dani dakata ki karbi wanan duk da ba yawa ban san zamu gannki a yanzu din ba ne. Na dago kai tare da dan sake murmushi a fuskana ina cewa baba na gode baba ka barshi kawai daga haka ban ko kalli kudin ba na fice daga falon abina. Dayan mutumin yace amma idan baku amince ba zan iya cewa kunyi sakaci ga hakan don ba kowane ke samun irin wanan saan ba yai sakaci dashi. Dakata Alhaji ina an kashe wanan magana anan kun dai ji daga bakin yarinya bata ma san da yaron nan ba ko kana gani zamuyi amfani da kudi ko wani abune mu rude ta dashi. Idan da kudi na gaban ta ga bayanin ka kawai ya isa a samu kan ta ta bada goyan baya ga maganan. Sun fahinci ba zasu samu hafin kai gurin daddy ba haka yasa sukai mai sallama suka tafi sunajin kunan rai a zukatan su. Suna gani duk inda suka tafi nema wa dan su aure sukan yi amfani da karfin arzikin su suci galaba dashi. Amma nan gashi babu alaman samun nasara ga hakan sun gwada arzikin sun gwada mulki amma babu alaman nasara akai. Mahaifin nashi yasan idan ya koma gida akwai rigima don yasan halin dan nashi ba yarda zaiyi ba ga hakan . Ina shiga dakin mu na wuce kai tsaye na koma na kwanta ban ko cire hijjab din dake jikina ba haka na dunkule a cikin shi. Bayan tafiyan su daddy ya nufo part din anty a dakin ta ya samay ta zaune tana amfani da wayan ta tana ganin shi tace ina Raman bakin har sun wuce ne ? Yace sun tafi ina wanan yarinyar Rahama take ne kinga abinda take kokarin jawo muna agidan nan ko yanzu fa iyayyen wanan mara hankalin da sukai fada a kan ta jiya gurin buki wai shi soja sune sukazo wai sun zo nemawa dan su auren ta. Da karfi anty tace What iyayyen shi fa kace suna da hankali kuwa har yaushe aka hadu da zasuce sunzo neman aure haka kimkau. Yace koma may ye ai laifinki ne da kike bari tana fita irin wanan gurin da maza masu jin karfin iskanci a jiki ke taruwa. Harda fitowa tsakiyan fili gata uwar turawa wai tana magana harda rawa tsakiyan maza haka for god sake ? Yanzu laina zaka gani idan batafita ba jikata zanyi insha a gida ko haka kake so taita zama tunda kai bakajin shawara. Shawaran may kuma ana maganan gaskiya zaki dauko wani magana can ki saka ciki. Nan dai ya kwashe yadda akayi ya fada mata komai, tai murmushi tace suna ganin zasu iya rudin Rama da kudin su ne ko may ? Yanzu dai ai kafara gani garin kallon kitse dai, , , Tsaki yayi ya mike yana cewa tana ina ne yanzu tace dashi tana daki tun jiya na kasa gane kanta sai fushi takeyi don nai mata fada. Yanzun haka ma ta hada kayan ta tun jiya wai gida zata koma ita bazata zauna nan ba kuma. May akai mata kuma da zata tafi idan ta tafu karatun nata fa kuma tafasa ke nan ko may ? Wa yasanar ma haukan ta kyale ta ai babu inda zata tafi gaskiya batason a fada mata amma ina amfanin rawa a gaban mutane. Koda yake Farida tace wannan kawar tasu mai rawan kaine tajata zuwa gurin rawan nima naga lokacin da ta jawota ai zuwa saman fada dai nai mata don gaba kawai. Mahifin mustapha ya fada masu duk yadda akayi a gidan daddy yana zaune yana sauraren mahaufin nashi ya mike yana fadin waye shi a garin nan da zaice ba zai bani yarsa ba mai ya taka shi din da zai ki bada goyon baya akai. Dakata boy wanan mutumin da kake gani duk abinda muke takama dashi yana dashi koma ince yafi mu wallahi. Mugun yarone don yana boyon kurwan shi ne ba a ganewa kawai amma shima don ne a garin nan ba karami ba. Ai tunda kaga na kyaleshi kaima kasan akwai dalili hakan don bazamu iya nuna mashi kudi ba sai dai mu fito mai ta wani hanya muci galabar shi a hakan . Jin sunan uguwan su mustapha yasa anty ta kira layin wata kawar ta don tayi bincike a kan shi. Bayan sun gaisa ne suka dan taba hira kwana biyu yaushe rabo anty take cewa don Allah dama ina son tambayan ki karima ko kin san wani mustapha sojane dan gida haruna hadeja ? Tace kai wanan yaron mara mutunci kin san ai yaran gidan ba mutunci ne dasu ba ko kadan. Wayan anty yana a hands free kowa dake falon yanaji abin da take fadi tace kin san shine saade? Indai mustaphane dan iska ne auren shi uku yana saki sai kinga irin matan da yake aure amma kwana biyu kiji ance ya rabu dasu ai. Baida kirki yaron banza ne wallahi ni laifin ma masu bashi diyan su nake gani don shi ko ganin shi kayi kasan tantiri ne ai. Tace injin ba wata naki yake so ba dai saade tace a, a diyar wata kawatace wai yake so amma basu bashi ba ai. Tace sun kuru wallahi da nan da wata uku suna ta bazawara kawai don bai shekara da mace shi a gidan shi. Gaba na ya fadi a raina nace anyi kyaun dan maciji ke nan ga mutum.har mutum a fuska amma babu halin ko kadan. Bayan anty ta kashe wayan tace dan iska shine yazo muma ya yaudare mu ko wai harda son su gwada wa mutane gudi da mulki a fili don sun saba harka da makwadaita. Ai shine daddy ku ke cewa kin burgeshi da baki tsaya karban kudin uban shi ba da haka suke yaudaran mutane ai. Nace balle ni wallahi bai mun ba ko banza ko ba, a fada ba ai da ganin shi dan iskane yana magana yana son taba mutum. Gajiye tace Allah dai ya tsare ai maza na cutan mata yanzu akan abin duniya sai asan halin mutum amma saboda kwadai a dauki diya a bashi. Anty tace kin san mutane son abin duniya yai masu yawa yanzu ko an sani sai a take sanin a cutar da yarinya ga banza. May aka gane ga aure wata uku ko hudu a halaka ma yarinya a maidata karamar bazawara an cuce ta an gama. Nidai haushi da takaicin wanan abin bai barima nayi magana ba don haka kawai sunja min barnan suna ina zaman zamana hankali a kwance. Mai gadine yai sallama a kofan anty yana fadin wai ana sallama da Rahama a kofan gida. Anty tace maigadi waye kuma baida lamban tane da zai turoka kana bakin aikin ka ? Yace wani sojane da soji a waje cikin kakin su da motar su na soja sukazo nan kofa yace a sallamo mashi ita. Nace kace ban nan yace sai dai kiyi hakkuri don Allah don na fada mashi kina gida ko. To kace nace bazan fito ba kuma don Allah kada ya kara zuwa gidan nan da sunan gurina yazo . Naga maigadi ya dan kalleni a dan tsorace kamar zaiyi magana sai kuma ya juya yafice da sauri. Bai dade ba sai gashi ya dawo yana fadin wai yace don Allah ki fito akwai abinda zai fada maki yanzu ba dadewa zakiyi ba. Nace bazan fito ba sai farida tai farat tace bari naje na bashi hakkuri ya tafi nace hakkuri may kuma zaki bashi yanzu. Anty tace bari ta tafi kawai tamike ta fice gajiye tace kin san ta da rawan kai indai ba zuwa zatayi ta cusa mai mumunan ra, ayi ba dai. Duk abinda zataje tayi ai taje tayi ni dai bazan fita ko ina ba wallahi . Tajima sai gata tadawo da ledoji manya manya tanacewa kinga da ban fita ba da wanan damar ya wuce mu ai. Ko baki son shi kici banza kawai kinci bulus nace kidai ci keda kika karbo mai kayan shi. Ledan ta shiga budewa tana washe bakin ta kayane irin na mata a ciki turare agogo shadda earing da sarka da sauran tarkace sai dayan ledan kayan kwalama ne kala kala acikin shi. Ta mayar da ledan tana turo min a gabana na mike na shige na barta da kayan a gaban ta. Ashe ta bashi nomban wayana da ta fita ban sani ba bata kuma fadi cewa ai tabashi layina ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE IDAN KIN YI GANGANCIN KARANTAWA NA BARKI GA ALLAH, , , IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MIN HAKKINA A KANKI CIKIN GAGAWA YARWA ALLAH YA SAKA MIN AKAN WACCE TA FITAR MIN DA NOVEL DINA, , , 34 Haukan kiran da Soja ke min yafi karfin na ibrahim da nake ganin ya damay ni a baya da kira hakan yasa ba shiri na kashe wayan nawa gaba daya. Dama waya ba damuna yayi ba don ban faye amfani dashi ba nazo nagane cewa Farida ce tabashi layi na haka yasa mukai fada sosai da ita. Ta kwashi nata ya nata tabar gidan da yamma wai tayi fushi tana gani zan bata hakkuri ne ta tsaya. Batasan yadda nakeji zan iya yin komai a lokacin ba gashi tsoron wanan bakin sojan ya fara kamani don abu yake kamar mara hankali. Don har zuwa yayi ya samu daddy da maganan cewa ko daddy ya yarda ya aura mashi ni da girma da arziki ko kuma yasan hanyan da yabi ya aure ko ta karfin tsiya ne. Daddy yazo ya samu anty da maganan yadda sukayi da Soja mai sona yace yanzu dole ta samu mafita don wanan mutumin mahaukacin gaske ne. Wani mafita kake son na samu mafita guda ne shine ka yarda da bukata ayita ta kare ko ba shike nan ba. Yafita daga dakin cikin fushi ya barta da tunane ita kadai a dakin ta na fito cikin shirina zani makaran ta nazo na sallamay ta dakin ta. Nan na samay hankali a tashe tace anya Rama fitan nan naki kuwa yau zai yuyu . Da sauri na juyu nace anty lafiya dai ko ? Tace ina fa lafiya Rama wanan mahaukacin da ya like maki yazo ya samu daddy ku da hauka yace koda karfin tsiya sai ya aure ki. Duk da naji tsoro a raina amma a fili cewa nayi Allah ya fishi mugu azzalumi kawai. Nace mata sai na dawo tace fitan zakiyi ke nan Rama ? Nace anty saboda shi na zauna gida karatuna ya tsaya kuma ? Tace to Allah ya tsare nace amin anty sai na dawo ke nan tace Allah yasa nafice. Tun barin layin uguwar mu na lura da wata bakar mota dake bina a baya a guje na kwasa Allah dai ya tsare ni na isa school lafiya. Yinin ranan a firgice na wuni har Zarah ta fahinci hakan a gareni take tambayana ko lafiya nake haka yau ? Ban boye mata ba tace badai boy kike nufi ba dan gidan haruna daura nace kamar haka naji sunan shi fa. Tace aiko kin shiga uku wallahi wanan dan iskan mara mutunci may zakiyi dashi ke ? Tace abu daya zan muyi shine idan mun tashi sai ki shiga motana ni na tafi da naki gida na ko yaya kika gani ? Nace hakan yayi ba matsala ai yadsa muka tsara haka mukayi na samu na isa gida lafiya a firgice itakuma ashe sun bita sai da sukaga ta nufi gidan ta har can suke tafito sukaga bani bace sai suka juya. Washe gari tsohuwar motar anty na shiga basu gane ba sai da naje school suka fahinci nice a cikin motar. Aiko suka darkakeni saida na shige wani guri na samu na isa gida lafiya haka yasa na fadawa anty halin da nake ciki. Tace na zauna babu inda zan kara zuwa sai komai ya lafa zan fita nayi hakkuri da karatun kwana biyu. Shiryawa tayi sai gidan mama laraba tasamu babu kowa a gidan suka gaisa da ita take cewa lafiya dai ko Saade. Nan anty take cewa mama magana nazo muyi dake da fatan zaki saurareni ki fahinci abinda nazo maki dashi. Nasan baban su Amira a duniyan nan babu shawaran da zaki bashi bai dauka ba kuma ya zamo mai alheri a karshe. Tace matsala kuka samu ne dashi tace mama ba matsala bane sai dai kuma matsalar ce. Nan dai ta kwashe abinda ke tafe da ita na neman shawara akan auren da take son yakara ya bijera mata. Mama laraba ra dubeta da kyau tace yanzu ke Saade da kanki koke son mijin ki ya karo maki kishiya bayan wa yan nan ma da kike dasu ba wani zaman dadi kukeyi dasu ba. Nikan Saade da zaki bi shawara na da sai nace hakan ma da kuke ya isa don kishiya fa ba dadi gareta ba. Mama nasan da hakan amma ina sin ki fahinci manufata a hakan don samun saukin mu nan gaba dani dashi da yaran baki daya. Mama kinga da yaje gaba a kasa rike mai diyan diyan shi yace zai dauko wata don nasan halin shi akan yaran shi. Gara ya dauko wacce na sani kuma na yarda da ita da ya dauki fitsarariya wace zata zo ta ganawa yara mugun hali. Umm, umm Saade dadai ki kara tunane matan yanzun ko ince mutum yanzu ba dan goyo bane wallahi. Mama garafa da wanan din nasan ta yasan ta musan halinta kin ga yafi komai sauki a gare mu. To ke saade dakike wanan magana Allah fa shi yai ciwo yai magani ai ciwo ba mutuwa bane don sai mai lafiya ma ya tafi yabar maiciwon a duniya. Tace hakanane mama nidai don Allah a duba min bukatana ko za, a dace ga hakan tunda ni yaki jin magana na. Mama tace kin ga idan har wacce kike son ya aura din batai mashu ba ko kuma ita din butulu ce fa kinga kin zalunce shi ta zalunce ki ke kuma. Jikin anty yai sanyi a lokaci guda hankalinta ya dan tashi take kuma wani natsuwa yazo mata tace cikin kuka mama ba wata bace can daban nake son ya aura sai Rahama dake gurina. Kin dai gane ta kinga ko nasan halinta yasan nata ai banyi tsan manin irin hakan ba daga gareta. Salati mama Laraba ta saka tare da tafa hannunuwan ta alaman mamaki ya kashe ta lokaci guda. Tace Rahama dai Rahama dai Sa,ade dana sani ta gurin ki anya kuwa kanki daya Saade da zakice mijin ki ya auri yar uwar ki. Mama Rahama yar uwata ce amma bata jini ba sai girma da arzikin daya hada mu ya koma yan uwan taka a tsakanin mu yanzu. Jikin mama laraba yai sanyi yadda taga anty na zubar da hawaye tasan irin haka ita kadai tasan abinda take ji a zuciyar ta ai banza baikai zomo kasuwa. Idan ya duba ga maganan ta gaskiya ne don dan nata ai yana son kulla amma Allah bai hada shi da matan arziki ba ita waban mai hankali lalura ya hana ta bashi lokacin ta. Mama Laraba ta nisa tace yanzu tunda ke da bakin ki kika bukaci hakan ai Alhamdullahi da shine yazo da maganan kinga sai muce yayi rashin hankali duk da aure ya hallata a tsakanin shi da ita. Don haka ki barni dashi insha Allahu zamu zauna dashi kan maganan kuma da yardan Allah zai fahince ni don ban taba bukatan wani abu dashi ba bai min ba don haka wanan din ma ai bazaki ba idan na fahintar dashi. Anty tace nagode mama da kika fahince ni haka da wuri ba kowane zai gane hakan ba sai ma ai min daukan banda hankali ban san ciwon kaina ba. Ai maganan aure babban magana ne Saade ba ko wace mace zata iya wanan sadaukar da ran da kikayi ba haka shiyasa za, a dauka ko baki da hankaline. Tsananin son mijin ki da yaran ki yasa har kike masu gwadayin fatan alheri a rayuwa nan gaba. Anty tace ni har ga Allah ina ma mijina kwadayin kasancewa da wanan yarinyar koda kuwa ina da raina na ne nidai bukatana naga ya samu kwanciyan hankalin aure kaman ko wani magidan ci a gidan shi. Naji na kuma gane manufan ki don haka banda abinda zance sai nace Allah yai maki albarka a rayuwan ki yasa a gama da duniyan nan lafiya. Tace amin a sanya tasan takawo maganan inda za ai mata maganin shi indai mama ce don Allah ya bata sa, an dan yar uwar ta sosai. Tace yanzu mama ba sai na sake mai magana ba ke nan ko? Ba sai kin shiga ba Saade ki barni dashi kawai zamu zauna da shi insha Allahu. Tai sallama da mama Laraba ta barta tana mamakin ta da tausaya mata don tana gani don kawai rashin lafiyan dake damunta ne ya kawo mata wanan danyen yanke hukuncin da taiwa kan ta. ********* ********* ********* Ance labarin gari a tambayi dan gari ashe komai nawa dadin hira yaja Gajiye har sunyi hiran da Farida. Wanan labarin ne da sunan kauyen mu da sunan iyayyena yadda za, a samay su idan sunje garin mu kaf Farida ta fadawa soja komai. Haka yasa yafita batun daddy a nan birni suka zagaya shi da iyayyen suka tafi har kauyen mu gurin iyayyena. Kan sunzo nemawa dan su aure na Allah ne ya taimaka babana da maigari yakira shi kan zancen basira yazo mai yace. A gaskiya sunan na haifi Rahama ne kawai yanzu amma uwar rikon ta da maigidan ta sunfi ni iko da ita don ko a gurin su take kun ga idan nace nai masu haka ba kyautawa zama tare ba. Basu so jin haka ba sai cewa Alhaji haruna yayi amma kai ka haifi abinka kana da iko da ita har yanzu . Kayi tunane akai ko nawa kada kaji komai zan zube maku shi yanzu anan basai mun tashi ba. Babana yace adaiyi hakkuri don Allah Alhaji a bari zan ga shi marikin nata don idan nai masu haka kamar naci amanan zamane. Don dai a rayuwa banda abinda zancewa wa yan nan mutane sai godiya ga irin alherin da suke min. Basu so haka ba sai da maigari ya basu hakkuri akan su dawo nan da sati mai zuwa suji shawaran da aka yanke akai. Da haka sukai sallama suka kawo alheri mai yawa na ban mamki suka babana da dama duk wani wanda ke fadan maigari a wannan lokacin. Suka tafi sukan mutane sai gani suke ana dace nayi saa da wanan babban kamu da nayi a rayuwana. Kafin wani lokaci bari ya karade garin ko cewa wasu masu kudi sunzo neman aure na daga birni ai. Bayan tafiyan sune maigari yake cewa baba yadda yayi yana da kyau gara da bai biyewa abin duniya sai an tsaya anyi bincike akai. Don irin haka karshe sai anyi abin yazo ya ya koma ciki kuma don duk auren da aka gwada mai dukiya haka baya karko. Don gaskiya kalaman dattijon nan yasa na zargi wani abu a kasa ko. Babana da kanshi ya tafi gurin mama altine da wanan labarin tace ikon Allah amma may zai sa su zagaye ta bayan shi Alhaji yusuf sozo nan bayan a tare suke can a gari guda. Ai idan ma da sanin shi to tare ya kamata suzo nan ko kuma azo tare da wakilin shi nan din. Koma may ye zan kira ita yar uwar nata da take gurinta naji na bakin ta baba yace haka yafi dai. Ya tafi ya barta tana mamare bayan ya dan bata wani abu daga cikin abinda aka bashi yakai saura ya boye bai bari mama lauratu tasan da maganan kudin ba. Don da zaran ta sani sunan su sorry sai taga bayan su kaf hankalinta zai kwanta da su. Inna da ta samu labari take cewa maigidan ta ita gaskiya mutanen sun bata tsoro don hankalinta bai kwanta ba sam da wanan magana maigari yace zai sayo mata kati sai ta kirani taji may ke gudana ne wai nasan da zuwan bakin ko kuwa ? Sakon kiran da mama laraba kewa daddy ya samay shi don da wayan ta tai amfani ta kirashi. Amma sai aka samu akasi baya gari yake cewa mama injin dai lafiya ko tace babu komai sai alheri wani dan magana ne nake son muyi da kai kawai. Yace ta dakance shi zai dawo nan zuwa jibi don yaji may ke gudana a gurin ta sam bai kawo wanan zancen a ran shi ba don daga shi sai Sadatun shi ke wanan rikicin dama a tsakanin su don ko ni da akeyi a kaina banda labarin hakan. Mama Labara taje gun mahaifin daddy ba tare da sanin yar uwarta ba takai mashi shawaran da Saade ta kawo mashi. Dama shi Abba ya dade da bada goyon bayan hakan don haka bata samu wani matsala ba gurin fahinta. Yake cewa tunda har matar shi da kansa ta bude baki ta bukaci hakan to ya kamata aje agana da iyayyena don su san da zancen suma. Da dare daddy ya dawo don haka bai samu zuwa gurin mama ba sai da safe bayan ya karya yatafi ansa kiran uwar goyon shi kaunar mahaifiyar shi. A falon ta suka zauna kamar ta sani Faridan ta ta canza yanzu tace dashi su fita daga waje magana ne wanda daga shi sai ita sai Allah take son suyi shi don kada abin yazo baiyi ba abatawa saadatu sunan ta ga banza. Suna barin gurin ya bude mota motar shi suka shiga don ya fahinci magana ce mai muhinmanci ta siri kuma da alama bata son a ji koma may ye din.. Sunan shi ta kira a hankali take cewa da fatan abinda zan fada maka bazai zazzafa ma zuciya ba zaka tausasa zuciyar ka ka fahince ni da kunnen basira. Yace insha Allahu mama nai maki alkawari koma may ne indai bai sabawa sharia ba zan yi nazari ko na rugumi ko may ye da zuciya daya da hannu bibiyu. Tace masha Allahu nakuma gode Allah yai maka albarka da fatan samunbalheri ga abinda zamu tatauna din yace amin. Tace Yusufa ina son na rokeka da farko da kayi hakkuri kuma ka kara hakkuri da iyalin ka kowa da irin rayuwan da Allah ya kaddaro mai dashi. Yusufa ina son in roke ka ba don nakai ba ko na isa ba sai don hangen alherin da abin zaizo ya haifar daga baya. Kayi hakkuri bukatar da matar ka ke binka dashi na auren yar uwarta ka yarda ka cika mata burin ta a kan hakan. Don ni gaskiya Saadatu duk ta sare min gwiwa na da wanan zancen don haka zancen abune na a tsaya a duba bisa ga hujjojin da takawo din. Kaga Saadatu dai mace baza, ace bata kishin ka bane tanayi kaima ka sani abinda manufan ta ya hango ne sai an daure za a hango shi din. Sannan kuma aure ne take kokarin kullawa aure kuma kowa yasani sunnan ma, aikine sallalahu Alaihim wassalam. Bai kamata ki daukan shawaran ta ba tunda itace da kanta ta bukaci da ai haka din baiwa kaine ka bijiro mata da zancen ba. Balle tace anyi mata butulci ko wani abin cin fuska da zarafi, tazo ta mutu din da take ikirari kazo kana da ka sanin rashin cika mata burin ta tun tana raye. Ka ga idan abin yai dadi ko bayan ta zata sha addua ga wanan hadin da tayi tsakanin ka da yarinyar nan. Idan ma bata mutum ba dai itace ta bukaci yin hakan da kanta da bakin ta ba wai wani ya tilasta mata yin hakan ba ita ta nema da kan ta. Tazo din ta mutu yaranta dakai da take ganin zasu iya fadawa wani hali kazo kana kukan rashin yin haka daga baya. Jikin shi ne yai sanyi don bai taba tsanmanin wanan magana bane mama Laraba ke neman shi ba dayi. Saadatu ta bashi mamaki matuka da ta nace akan wanan magana haka har yakai tun sunayi su biyu a tsakanin su gashi yanzu takawo maganan ga magabatan shi. Yanzu shi yaya zai iyacewa mama hakan bazai yuyu ba bayan kwararan hujjujin da ta kawo mashi yanzu a gaban shi wanda ita da Sa,adatu ke gani hujjane a garesu. Shi fa bai taba jin son Rahama da aure ba a rayuwan shi ba asali ma dai mamakin mazan da ke ta hauka akanta yakeyi don baiga abin burgewa gareta ba gaskiya sai dai idan farar fatan ta tane ke rudin su. Shi bayan Saadatun shi fa baitaba tsayawa kallon wata mace bata bashi sha, awa haka na ba. Ko su wa yan nan dake gidan shi aure daine mukkadari kawai a tsakanin shi da su har yake zaune dasu don biyayya kawai. Amma bawai don yasan wani dadin zama da mace ba may mace zata iya maka wanda zai iya saka natsuwa ko shagalta a kan ta duk shi bai san wanan abin ba. Can dai ya nisa bayan ya fahinci mama tagama fadar abinda zata fada mai shi take saurare yanzu. Yace mama nagode da wanan shawaran naki tunda haka take bukata da kan ta insha Allahu zan yi kokari naga na cika mata gurin ta akan hakan. Sai dai kuma bazan so jin daga baya tadawo tana wani korafi ba da bakin ta akan yin hakan kuma don mama kin san halin mata akan kishi kuma. Ita Saade na rasa may nene ke damun rayuwa ta data yankewa kanta wanan danyen hukuncin haka ba ? Mama tace yanzu ai koma maye dai itace ta bukaci ganin hakan a rayuwan ta ko naka yanzu shine kayi kokari kaga ka kwatanta adalci a tsakanin matayen naka. Don tserewa hushin ubangijin ka a gobe kiyama Allah kuma yai maka albarka ya daukaka zurianka. Yakare muna ku daga sherin makiya da mahassada nagida da na waje sai ka jajirce sosai gurin kwantata adalci akan iyalin ka don nauyi ne mai girma ya kara hawa kan ka yanzu kuma. Na kuma ji dadi kwarai na rokeka alfarma irin haka kuma kai min shi a take babu bata lokaci don haka yanzu abinda nake son ka dashi shine. Kabar wanan zancen a ranka itama Saade sai dai ka shirya yanda neman auren naka zai kasance idan har Allah yayi sai dai aji kawai anyi auren. Don baiyyana shi zai iya kawo muhawara mai karfi har takai karshe azo a samu akasi a hakan. Yace hakane mama insha Allah zan bi al, amarin a tsanake yadda abin zaizo a cikin sauki ba tare da rayuka sun baci ba akai. Tace hakan na da kyau Allah yai maka albarka tagi ka huta abin baka dama aanan shine maganan kawai . Yai mata godiya tare da sallama tana ta saka mai albarka tafita yaja motan shi yana tafe yanajin wani irin abu a zuciyar shi. Shi yanzu ma ta ina zai fara ne wai takan Saade ko ta kan wanan yarinyar da akalaka mai akai ko kuma da maganan jama, a zaiji. Mahaifin shi dana Saade ne suka fado mashi arai dole ta kan su ne zai fara bai tafi gida ba sai da yaje kasuwa ya samu Abba suka gana dashi akan maganan. Abba yai murna kwarai da jin wanan labarin yake cewa yai matukar farin ciki da jin haka aiko ba komai Saadatu tayi jahadi babba anan, don aure ta hada don farin cikin ka. Yasan Alhajin shi na gona a wanan lokacin don haka ya juya akalar motar shi zuwa gida inda ya nufo gidan cike da natsuwa da karin imani a zuciyar shi. Don maganan da mahaifin Saade yai mashi a yanzu ya kara sa jikin shi yin sanyi ga ala, marin kowa na fada mashi cewa aure ne yayi kawai. Yana shigowa gida ya nufi part din shi duk da sanyin Ac daya kunna a falon bai hana shi jin zafi ba a jikin shi. Zama yayi tare da mike kafafuwan shi saman dan table din dake a tsakiyan falon. Ya dafe kan shi da hannun shi daya yana jin kan nashi na matukar sara mashi a lokacin. Shidai Allah ya gani wanan auren yafi ko wani zo mashi da rikici a rayuwan shi yanzu shi dawani ido zai kalli Saade ko dawani ido zai kalli Rahama wai a matsayin matar auren shi da zasu raya sunna a tare zaman aure fa ba zaman wasa bane anya kuwa Saaden shi tayi la, akari da wanan abin kuwa a yadda yasan mata da kishin tsiya. Yanzu dai zaiga Saadatun don yaji ta ina zasu fara bullowa zancen don komai yanzu yana hannun ta ita da ta kawo maganan. Zai danka mata komai ta gudanar yadda take bukata shi nashi idone kawai yaga iya gudun ta. Yana zancen zuci Zulfa ta shigo falon da ganin yanayinta kasan bata da lafiya a lokacin . Jin an shigo falon ne yasa shi bude idanuwan shi dake a lumshe ya sauke a kan ta. Yace da ita lafiya yau kike kuwa ta samu guri ta zauna daga gefen shi tana cewa yau tunda safe a kwance nake na rasa gane kan jikin nan nawa duk kwanakin nan. Yake cewa ki shirya muje asibiti yanzu adan kara dubaki muji may likitan zaice akai. Ta mike da kyat tana fadi bari naje na dan kimtsa kafin ka gama sai na fito. Tana barin gurin yake cewa a ranshi bari ya shiga gun Saade ya ganta tunda hakkanta ya cin ma ruwa ta kai ga yadda take son ganin su. Fitina kawai take son kirkiro mashi yana fama da fitinan wasu takara saka shi ga wani sabo. Yamike zuwa part din na anty muna zaune sai kwasan dariya muke Jinior ne ke bin mu yana cizo wai hakoran shi na kaikayi inji anty. Ganin daddy ya shigo falon muka shiga gaidashi tare da kokarin mikewa mu bar falon don su gana inda nake zaune nake gaida sai baima tsaya falon ba ya nufi bedroom din ta yana fadin ke may ya hanaki zuwa school yau ko ba a karatu ne yau din. Ta bi yan shi tana fadin ina zata fita mahaukacin soja ya saka security's dinshi akan ta ko ina tabi binta sukeyi yi Yace binta kuma garin yaya haka ya faru ban sani ba kuma ke baki sanar dani abinda ake ciki ba tace yanzu haka kai nake jira ka shigo nai maka maganan ai. Don ashe wai har can kauyen su ya tafi gurin iyayyenta ya nuna masu kudi nan dai tana zama take labarta mai abinda ke faruwa take cewa dashi yanzu haka ita duk a rude take ta rasa yaya za, a bullowa zancen don ta fahinci wanan sojan ba karamin tantiri bane gaskiya kamar aure dole ne ga mata a gari ko ina amma ya nace wa mace daya haka ? Yace yanzu ma zancen ta ya kawo ni gurin ki ai bukatan ki ya biya tunda har kina son hadani da mamana fada. Yace daga gurin mama furin Abba na nufa na fada mashi kina akan bukatan ki sai dai ki sani ba korafi ko wani magana akan hakan daga baya. Don bani na bukaci yin hakan ba kece da hujjan ki mara tushe kin samu mama kin mata dadin baki ta hau ta zauna nai magana tace ban yi mata biyayya ba kuma don haka yanzu dabara ya saura gareku. Sai ki san yadda zaki tsara tunda kece kika hada abinki da kan ki ba wani ya hada maki ba. Tace Alhamdullahi Allah nagode ma dajin wanan labarin farin cikin hakika Rahama alheri ce a gare mu besty ba zaka gane manufana ba sai bayan anyi abin idan Allah ya tabbatar insha Allahu. Idan har kana tunanen zan tsaya kishi da Rama a rayuwana kayi kuskure ni don ka nai wanan hadin amma ka kasa fahintana cikin saukin kai. Kaima kasan abinda mata kewa bakin kishi ai abu daya ne ko toni ina iya hadawa danawa da nata duk ta kwashe na bar mata ita kadai in wanan ne? In dai har zakai muna wanan alfarman ni da ita don ni may yarage gare ni banda bautan Allah kuma yanzu. Wani kallo yai mata yace kada ki soma wanan maganan idan ba haka ba wallahi yanzu nace na fasa tace rufa min asiri idan ka kara botse min kuma wa na san zai taro min kai kuma ? Ban ni dai yanzu nasan yadda zan bullowa wannan yar butsar din tawa don nasan akwai rikici babba tsakani na da Rama nan gaba. Baki ya tabe yace wanan matsalar kune ni dama ban dauka aka ba balle ku tsanmani zan saka maku baki ga zancen ku. Tace ai wallahi dole ka saka don kaine ma zakai jagora gurin lalashin abinka don yanzu ta tashi daga Rama ta koma Raman besty kuma. Haushin zancen ta yake ji fita yayi daga dakin ba tare da ya iya bata amsa ba don haushin maganan yakeji. ********* ********* ********* Duk kwanakin nan biyu idan mun zauna da anty bata da wani zance sai muna huduban yadda zama da miji yake da abinda ya dace mace ta dinga yiwa mijin ta. Sai nake ganin don Gajiye mai son yin aure ita da maigadi takeyin maganan don zancen su yayi nisa sosai kowa yasan shi zai auri gajiye yanzu. Don har daddy yasa a gyara masu can baya inda aka gina wa masu aikin gida ba kowa ke zama ciki ba sai shi maigadin da yan komatsen shi keciki dama. Don haka wani lokaci idan anty na magana har naka yiwa Gajiye dariya mu saka mata wakan shakiyan ci nida su Amira taita murmushi tana jin dadi. Don haka nakan zauna nai ta sauraren yadda anty ke faman mata nasiha kan hakkin da ya rataya akan mata dakuma namiji daya rataya akan shi ga matar shi. Nidai har nagaji dajin hudubar anty akan aure da sun fara zan kunna game muyu ta bugawa nida Nasir muna ihun mu ban tsayawa sauraren su . Ranan Jumma,a da safe daddy yashigo muna falo muna karyawa yana saye cikin wani shadda yaci aiki mai ruwan dark blue sai maiko shaddan ke yi. Anty tace dakyau nawa sai goga na Ram, , , sai kuma tai shiru tanacewa Allah ya bada saan tafiya aje lafiya a dawo lafiya mukuma ji alheri. Ya dan dubeta cikin tsiga maikama da harara yake cewa shi zai tafi sai sun dawo kenan, Anty ke cewa tana gaida mutanen gida idan sun tafi. Bayan ya fitan shi na dago kaina inacewa anty ina daddy zai tafi yau haka aha wanan kwalliya irin haka gashi ko kayan sun matukar karban jikin shi sosai wallahi. Tace da gaske Rama kayan sun karbe shi nace aikema anty kin gani bana gkina ta murmushi ba sunyi maki kyau ke nan kema. Gajiye kece hajiya garin su zai tafi ne ko may dariya tayi tace Gajiye shi ai haifafen dan garin nan ne kowa nasa na cikin garin nan gaba daya yan uwan shi ta uwa ta uba. Unguwa dai zai tafi nan ba nisa bane kwarai nake gani zai tafi a tare muke fadin Allah ya tsare hanya tace amin na mike na kwashi kayan zuwa kitchen ina mai jin haushin rashin shiga na school da wanan fitinanen sojan ya haddasa min kwana biyu ga zarah har gida ta biyo ni kan rashin ganina da batayi kwana biyu. Ban fito ba sai da na wanke kayan na tsane su na dawo falon na samu Gajiye na gyara gurin na samu kujera na haye tare da kwantawa na mike flat tare da lumshe idanuwana a hankali ina jin raina ba dadi ko kadan a lokacin. Yar aikin Zulfa ce tashigo tana tambaye gajiye wai tana da goro ta san ma uwar dakin ta gajiye ta ballo goro cikin wani leda tabara tafice daga falon namu. Gajiye ke cewa nikan hajiya kodai da zaki samune ko ya xon kwanan duk sai matar nan ta aiko neman goro gurina. Anty tace hakanake gani gajiye kamar ciki Zulfa ta samu shine take wahal da ita haka wallahi. Daga yadda nake kwance na mike da sauri ina fadin Ciki kega anty Zulfa Allah sarki har nayi mata murna wallahi tun mutuwan hanifa dama bata sake sake jiku ba a gidan nan kamar yadda take a baya. Keko mutuwar da fa akwai zafi Rama balle irin Zulfa data sawa yar ta rai a gidan nan kamar ikon Allah. Murmushi nayi don nasan ko ita anty ba baya ba ai gurin son yara sai dai na wani yafi na wani ne don ita tana kawaici akan yaran ta. Waya anty ta dauka sai naga ta mike tashiga daki tajima a ciki sai tafito jikin ta duk yayi sanyi a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU .IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE IDAN KIN YI GANGANCIN KARANTAWA NA BARKI GA ALLAH, , , IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MIN HAKKINA A KANKI CIKIN GAGAWA YARWA ALLAH YA SAKA MIN AKAN WACCE TA FITAR MIN DA NOVEL DINA, , , 34 Haukan kiran da Soja ke min yafi karfin na ibrahim da nake ganin ya damay ni a baya da kira hakan yasa ba shiri na kashe wayan nawa gaba daya. Dama waya ba damuna yayi ba don ban faye amfani dashi ba nazo nagane cewa Farida ce tabashi layi na haka yasa mukai fada sosai da ita. Ta kwashi nata ya nata tabar gidan da yamma wai tayi fushi tana gani zan bata hakkuri ne ta tsaya. Batasan yadda nakeji zan iya yin komai a lokacin ba gashi tsoron wanan bakin sojan ya fara kamani don abu yake kamar mara hankali. Don har zuwa yayi ya samu daddy da maganan cewa ko daddy ya yarda ya aura mashi ni da girma da arziki ko kuma yasan hanyan da yabi ya aure ko ta karfin tsiya ne. Daddy yazo ya samu anty da maganan yadda sukayi da Soja mai sona yace yanzu dole ta samu mafita don wanan mutumin mahaukacin gaske ne. Wani mafita kake son na samu mafita guda ne shine ka yarda da bukata ayita ta kare ko ba shike nan ba. Yafita daga dakin cikin fushi ya barta da tunane ita kadai a dakin ta na fito cikin shirina zani makaran ta nazo na sallamay ta dakin ta. Nan na samay hankali a tashe tace anya Rama fitan nan naki kuwa yau zai yuyu . Da sauri na juyu nace anty lafiya dai ko ? Tace ina fa lafiya Rama wanan mahaukacin da ya like maki yazo ya samu daddy ku da hauka yace koda karfin tsiya sai ya aure ki. Duk da naji tsoro a raina amma a fili cewa nayi Allah ya fishi mugu azzalumi kawai. Nace mata sai na dawo tace fitan zakiyi ke nan Rama ? Nace anty saboda shi na zauna gida karatuna ya tsaya kuma ? Tace to Allah ya tsare nace amin anty sai na dawo ke nan tace Allah yasa nafice. Tun barin layin uguwar mu na lura da wata bakar mota dake bina a baya a guje na kwasa Allah dai ya tsare ni na isa school lafiya. Yinin ranan a firgice na wuni har Zarah ta fahinci hakan a gareni take tambayana ko lafiya nake haka yau ? Ban boye mata ba tace badai boy kike nufi ba dan gidan haruna daura nace kamar haka naji sunan shi fa. Tace aiko kin shiga uku wallahi wanan dan iskan mara mutunci may zakiyi dashi ke ? Tace abu daya zan muyi shine idan mun tashi sai ki shiga motana ni na tafi da naki gida na ko yaya kika gani ? Nace hakan yayi ba matsala ai yadsa muka tsara haka mukayi na samu na isa gida lafiya a firgice itakuma ashe sun bita sai da sukaga ta nufi gidan ta har can suke tafito sukaga bani bace sai suka juya. Washe gari tsohuwar motar anty na shiga basu gane ba sai da naje school suka fahinci nice a cikin motar. Aiko suka darkakeni saida na shige wani guri na samu na isa gida lafiya haka yasa na fadawa anty halin da nake ciki. Tace na zauna babu inda zan kara zuwa sai komai ya lafa zan fita nayi hakkuri da karatun kwana biyu. Shiryawa tayi sai gidan mama laraba tasamu babu kowa a gidan suka gaisa da ita take cewa lafiya dai ko Saade. Nan anty take cewa mama magana nazo muyi dake da fatan zaki saurareni ki fahinci abinda nazo maki dashi. Nasan baban su Amira a duniyan nan babu shawaran da zaki bashi bai dauka ba kuma ya zamo mai alheri a karshe. Tace matsala kuka samu ne dashi tace mama ba matsala bane sai dai kuma matsalar ce. Nan dai ta kwashe abinda ke tafe da ita na neman shawara akan auren da take son yakara ya bijera mata. Mama laraba ra dubeta da kyau tace yanzu ke Saade da kanki koke son mijin ki ya karo maki kishiya bayan wa yan nan ma da kike dasu ba wani zaman dadi kukeyi dasu ba. Nikan Saade da zaki bi shawara na da sai nace hakan ma da kuke ya isa don kishiya fa ba dadi gareta ba. Mama nasan da hakan amma ina sin ki fahinci manufata a hakan don samun saukin mu nan gaba dani dashi da yaran baki daya. Mama kinga da yaje gaba a kasa rike mai diyan diyan shi yace zai dauko wata don nasan halin shi akan yaran shi. Gara ya dauko wacce na sani kuma na yarda da ita da ya dauki fitsarariya wace zata zo ta ganawa yara mugun hali. Umm, umm Saade dadai ki kara tunane matan yanzun ko ince mutum yanzu ba dan goyo bane wallahi. Mama garafa da wanan din nasan ta yasan ta musan halinta kin ga yafi komai sauki a gare mu. To ke saade dakike wanan magana Allah fa shi yai ciwo yai magani ai ciwo ba mutuwa bane don sai mai lafiya ma ya tafi yabar maiciwon a duniya. Tace hakanane mama nidai don Allah a duba min bukatana ko za, a dace ga hakan tunda ni yaki jin magana na. Mama tace kin ga idan har wacce kike son ya aura din batai mashu ba ko kuma ita din butulu ce fa kinga kin zalunce shi ta zalunce ki ke kuma. Jikin anty yai sanyi a lokaci guda hankalinta ya dan tashi take kuma wani natsuwa yazo mata tace cikin kuka mama ba wata bace can daban nake son ya aura sai Rahama dake gurina. Kin dai gane ta kinga ko nasan halinta yasan nata ai banyi tsan manin irin hakan ba daga gareta. Salati mama Laraba ta saka tare da tafa hannunuwan ta alaman mamaki ya kashe ta lokaci guda. Tace Rahama dai Rahama dai Sa,ade dana sani ta gurin ki anya kuwa kanki daya Saade da zakice mijin ki ya auri yar uwar ki. Mama Rahama yar uwata ce amma bata jini ba sai girma da arzikin daya hada mu ya koma yan uwan taka a tsakanin mu yanzu. Jikin mama laraba yai sanyi yadda taga anty na zubar da hawaye tasan irin haka ita kadai tasan abinda take ji a zuciyar ta ai banza baikai zomo kasuwa. Idan ya duba ga maganan ta gaskiya ne don dan nata ai yana son kulla amma Allah bai hada shi da matan arziki ba ita waban mai hankali lalura ya hana ta bashi lokacin ta. Mama Laraba ta nisa tace yanzu tunda ke da bakin ki kika bukaci hakan ai Alhamdullahi da shine yazo da maganan kinga sai muce yayi rashin hankali duk da aure ya hallata a tsakanin shi da ita. Don haka ki barni dashi insha Allahu zamu zauna dashi kan maganan kuma da yardan Allah zai fahince ni don ban taba bukatan wani abu dashi ba bai min ba don haka wanan din ma ai bazaki ba idan na fahintar dashi. Anty tace nagode mama da kika fahince ni haka da wuri ba kowane zai gane hakan ba sai ma ai min daukan banda hankali ban san ciwon kaina ba. Ai maganan aure babban magana ne Saade ba ko wace mace zata iya wanan sadaukar da ran da kikayi ba haka shiyasa za, a dauka ko baki da hankaline. Tsananin son mijin ki da yaran ki yasa har kike masu gwadayin fatan alheri a rayuwa nan gaba. Anty tace ni har ga Allah ina ma mijina kwadayin kasancewa da wanan yarinyar koda kuwa ina da raina na ne nidai bukatana naga ya samu kwanciyan hankalin aure kaman ko wani magidan ci a gidan shi. Naji na kuma gane manufan ki don haka banda abinda zance sai nace Allah yai maki albarka a rayuwan ki yasa a gama da duniyan nan lafiya. Tace amin a sanya tasan takawo maganan inda za ai mata maganin shi indai mama ce don Allah ya bata sa, an dan yar uwar ta sosai. Tace yanzu mama ba sai na sake mai magana ba ke nan ko? Ba sai kin shiga ba Saade ki barni dashi kawai zamu zauna da shi insha Allahu. Tai sallama da mama Laraba ta barta tana mamakin ta da tausaya mata don tana gani don kawai rashin lafiyan dake damunta ne ya kawo mata wanan danyen yanke hukuncin da taiwa kan ta. ********* ********* ********* Ance labarin gari a tambayi dan gari ashe komai nawa dadin hira yaja Gajiye har sunyi hiran da Farida. Wanan labarin ne da sunan kauyen mu da sunan iyayyena yadda za, a samay su idan sunje garin mu kaf Farida ta fadawa soja komai. Haka yasa yafita batun daddy a nan birni suka zagaya shi da iyayyen suka tafi har kauyen mu gurin iyayyena. Kan sunzo nemawa dan su aure na Allah ne ya taimaka babana da maigari yakira shi kan zancen basira yazo mai yace. A gaskiya sunan na haifi Rahama ne kawai yanzu amma uwar rikon ta da maigidan ta sunfi ni iko da ita don ko a gurin su take kun ga idan nace nai masu haka ba kyautawa zama tare ba. Basu so jin haka ba sai cewa Alhaji haruna yayi amma kai ka haifi abinka kana da iko da ita har yanzu . Kayi tunane akai ko nawa kada kaji komai zan zube maku shi yanzu anan basai mun tashi ba. Babana yace adaiyi hakkuri don Allah Alhaji a bari zan ga shi marikin nata don idan nai masu haka kamar naci amanan zamane. Don dai a rayuwa banda abinda zancewa wa yan nan mutane sai godiya ga irin alherin da suke min. Basu so haka ba sai da maigari ya basu hakkuri akan su dawo nan da sati mai zuwa suji shawaran da aka yanke akai. Da haka sukai sallama suka kawo alheri mai yawa na ban mamki suka babana da dama duk wani wanda ke fadan maigari a wannan lokacin. Suka tafi sukan mutane sai gani suke ana dace nayi saa da wanan babban kamu da nayi a rayuwana. Kafin wani lokaci bari ya karade garin ko cewa wasu masu kudi sunzo neman aure na daga birni ai. Bayan tafiyan sune maigari yake cewa baba yadda yayi yana da kyau gara da bai biyewa abin duniya sai an tsaya anyi bincike akai. Don irin haka karshe sai anyi abin yazo ya ya koma ciki kuma don duk auren da aka gwada mai dukiya haka baya karko. Don gaskiya kalaman dattijon nan yasa na zargi wani abu a kasa ko. Babana da kanshi ya tafi gurin mama altine da wanan labarin tace ikon Allah amma may zai sa su zagaye ta bayan shi Alhaji yusuf sozo nan bayan a tare suke can a gari guda. Ai idan ma da sanin shi to tare ya kamata suzo nan ko kuma azo tare da wakilin shi nan din. Koma may ye zan kira ita yar uwar nata da take gurinta naji na bakin ta baba yace haka yafi dai. Ya tafi ya barta tana mamare bayan ya dan bata wani abu daga cikin abinda aka bashi yakai saura ya boye bai bari mama lauratu tasan da maganan kudin ba. Don da zaran ta sani sunan su sorry sai taga bayan su kaf hankalinta zai kwanta da su. Inna da ta samu labari take cewa maigidan ta ita gaskiya mutanen sun bata tsoro don hankalinta bai kwanta ba sam da wanan magana maigari yace zai sayo mata kati sai ta kirani taji may ke gudana ne wai nasan da zuwan bakin ko kuwa ? Sakon kiran da mama laraba kewa daddy ya samay shi don da wayan ta tai amfani ta kirashi. Amma sai aka samu akasi baya gari yake cewa mama injin dai lafiya ko tace babu komai sai alheri wani dan magana ne nake son muyi da kai kawai. Yace ta dakance shi zai dawo nan zuwa jibi don yaji may ke gudana a gurin ta sam bai kawo wanan zancen a ran shi ba don daga shi sai Sadatun shi ke wanan rikicin dama a tsakanin su don ko ni da akeyi a kaina banda labarin hakan. Mama Labara taje gun mahaifin daddy ba tare da sanin yar uwarta ba takai mashi shawaran da Saade ta kawo mashi. Dama shi Abba ya dade da bada goyon bayan hakan don haka bata samu wani matsala ba gurin fahinta. Yake cewa tunda har matar shi da kansa ta bude baki ta bukaci hakan to ya kamata aje agana da iyayyena don su san da zancen suma. Da dare daddy ya dawo don haka bai samu zuwa gurin mama ba sai da safe bayan ya karya yatafi ansa kiran uwar goyon shi kaunar mahaifiyar shi. A falon ta suka zauna kamar ta sani Faridan ta ta canza yanzu tace dashi su fita daga waje magana ne wanda daga shi sai ita sai Allah take son suyi shi don kada abin yazo baiyi ba abatawa saadatu sunan ta ga banza. Suna barin gurin ya bude mota motar shi suka shiga don ya fahinci magana ce mai muhinmanci ta siri kuma da alama bata son a ji koma may ye din.. Sunan shi ta kira a hankali take cewa da fatan abinda zan fada maka bazai zazzafa ma zuciya ba zaka tausasa zuciyar ka ka fahince ni da kunnen basira. Yace insha Allahu mama nai maki alkawari koma may ne indai bai sabawa sharia ba zan yi nazari ko na rugumi ko may ye da zuciya daya da hannu bibiyu. Tace masha Allahu nakuma gode Allah yai maka albarka da fatan samunbalheri ga abinda zamu tatauna din yace amin. Tace Yusufa ina son na rokeka da farko da kayi hakkuri kuma ka kara hakkuri da iyalin ka kowa da irin rayuwan da Allah ya kaddaro mai dashi. Yusufa ina son in roke ka ba don nakai ba ko na isa ba sai don hangen alherin da abin zaizo ya haifar daga baya. Kayi hakkuri bukatar da matar ka ke binka dashi na auren yar uwarta ka yarda ka cika mata burin ta a kan hakan. Don ni gaskiya Saadatu duk ta sare min gwiwa na da wanan zancen don haka zancen abune na a tsaya a duba bisa ga hujjojin da takawo din. Kaga Saadatu dai mace baza, ace bata kishin ka bane tanayi kaima ka sani abinda manufan ta ya hango ne sai an daure za a hango shi din. Sannan kuma aure ne take kokarin kullawa aure kuma kowa yasani sunnan ma, aikine sallalahu Alaihim wassalam. Bai kamata ki daukan shawaran ta ba tunda itace da kanta ta bukaci da ai haka din baiwa kaine ka bijiro mata da zancen ba. Balle tace anyi mata butulci ko wani abin cin fuska da zarafi, tazo ta mutu din da take ikirari kazo kana da ka sanin rashin cika mata burin ta tun tana raye. Ka ga idan abin yai dadi ko bayan ta zata sha addua ga wanan hadin da tayi tsakanin ka da yarinyar nan. Idan ma bata mutum ba dai itace ta bukaci yin hakan da kanta da bakin ta ba wai wani ya tilasta mata yin hakan ba ita ta nema da kan ta. Tazo din ta mutu yaranta dakai da take ganin zasu iya fadawa wani hali kazo kana kukan rashin yin haka daga baya. Jikin shi ne yai sanyi don bai taba tsanmanin wanan magana bane mama Laraba ke neman shi ba dayi. Saadatu ta bashi mamaki matuka da ta nace akan wanan magana haka har yakai tun sunayi su biyu a tsakanin su gashi yanzu takawo maganan ga magabatan shi. Yanzu shi yaya zai iyacewa mama hakan bazai yuyu ba bayan kwararan hujjujin da ta kawo mashi yanzu a gaban shi wanda ita da Sa,adatu ke gani hujjane a garesu. Shi fa bai taba jin son Rahama da aure ba a rayuwan shi ba asali ma dai mamakin mazan da ke ta hauka akanta yakeyi don baiga abin burgewa gareta ba gaskiya sai dai idan farar fatan ta tane ke rudin su. Shi bayan Saadatun shi fa baitaba tsayawa kallon wata mace bata bashi sha, awa haka na ba. Ko su wa yan nan dake gidan shi aure daine mukkadari kawai a tsakanin shi da su har yake zaune dasu don biyayya kawai. Amma bawai don yasan wani dadin zama da mace ba may mace zata iya maka wanda zai iya saka natsuwa ko shagalta a kan ta duk shi bai san wanan abin ba. Can dai ya nisa bayan ya fahinci mama tagama fadar abinda zata fada mai shi take saurare yanzu. Yace mama nagode da wanan shawaran naki tunda haka take bukata da kan ta insha Allahu zan yi kokari naga na cika mata gurin ta akan hakan. Sai dai kuma bazan so jin daga baya tadawo tana wani korafi ba da bakin ta akan yin hakan kuma don mama kin san halin mata akan kishi kuma. Ita Saade na rasa may nene ke damun rayuwa ta data yankewa kanta wanan danyen hukuncin haka ba ? Mama tace yanzu ai koma maye dai itace ta bukaci ganin hakan a rayuwan ta ko naka yanzu shine kayi kokari kaga ka kwatanta adalci a tsakanin matayen naka. Don tserewa hushin ubangijin ka a gobe kiyama Allah kuma yai maka albarka ya daukaka zurianka. Yakare muna ku daga sherin makiya da mahassada nagida da na waje sai ka jajirce sosai gurin kwantata adalci akan iyalin ka don nauyi ne mai girma ya kara hawa kan ka yanzu kuma. Na kuma ji dadi kwarai na rokeka alfarma irin haka kuma kai min shi a take babu bata lokaci don haka yanzu abinda nake son ka dashi shine. Kabar wanan zancen a ranka itama Saade sai dai ka shirya yanda neman auren naka zai kasance idan har Allah yayi sai dai aji kawai anyi auren. Don baiyyana shi zai iya kawo muhawara mai karfi har takai karshe azo a samu akasi a hakan. Yace hakane mama insha Allah zan bi al, amarin a tsanake yadda abin zaizo a cikin sauki ba tare da rayuka sun baci ba akai. Tace hakan na da kyau Allah yai maka albarka tagi ka huta abin baka dama aanan shine maganan kawai . Yai mata godiya tare da sallama tana ta saka mai albarka tafita yaja motan shi yana tafe yanajin wani irin abu a zuciyar shi. Shi yanzu ma ta ina zai fara ne wai takan Saade ko ta kan wanan yarinyar da akalaka mai akai ko kuma da maganan jama, a zaiji. Mahaifin shi dana Saade ne suka fado mashi arai dole ta kan su ne zai fara bai tafi gida ba sai da yaje kasuwa ya samu Abba suka gana dashi akan maganan. Abba yai murna kwarai da jin wanan labarin yake cewa yai matukar farin ciki da jin haka aiko ba komai Saadatu tayi jahadi babba anan, don aure ta hada don farin cikin ka. Yasan Alhajin shi na gona a wanan lokacin don haka ya juya akalar motar shi zuwa gida inda ya nufo gidan cike da natsuwa da karin imani a zuciyar shi. Don maganan da mahaifin Saade yai mashi a yanzu ya kara sa jikin shi yin sanyi ga ala, marin kowa na fada mashi cewa aure ne yayi kawai. Yana shigowa gida ya nufi part din shi duk da sanyin Ac daya kunna a falon bai hana shi jin zafi ba a jikin shi. Zama yayi tare da mike kafafuwan shi saman dan table din dake a tsakiyan falon. Ya dafe kan shi da hannun shi daya yana jin kan nashi na matukar sara mashi a lokacin. Shidai Allah ya gani wanan auren yafi ko wani zo mashi da rikici a rayuwan shi yanzu shi dawani ido zai kalli Saade ko dawani ido zai kalli Rahama wai a matsayin matar auren shi da zasu raya sunna a tare zaman aure fa ba zaman wasa bane anya kuwa Saaden shi tayi la, akari da wanan abin kuwa a yadda yasan mata da kishin tsiya. Yanzu dai zaiga Saadatun don yaji ta ina zasu fara bullowa zancen don komai yanzu yana hannun ta ita da ta kawo maganan. Zai danka mata komai ta gudanar yadda take bukata shi nashi idone kawai yaga iya gudun ta. Yana zancen zuci Zulfa ta shigo falon da ganin yanayinta kasan bata da lafiya a lokacin . Jin an shigo falon ne yasa shi bude idanuwan shi dake a lumshe ya sauke a kan ta. Yace da ita lafiya yau kike kuwa ta samu guri ta zauna daga gefen shi tana cewa yau tunda safe a kwance nake na rasa gane kan jikin nan nawa duk kwanakin nan. Yake cewa ki shirya muje asibiti yanzu adan kara dubaki muji may likitan zaice akai. Ta mike da kyat tana fadi bari naje na dan kimtsa kafin ka gama sai na fito. Tana barin gurin yake cewa a ranshi bari ya shiga gun Saade ya ganta tunda hakkanta ya cin ma ruwa ta kai ga yadda take son ganin su. Fitina kawai take son kirkiro mashi yana fama da fitinan wasu takara saka shi ga wani sabo. Yamike zuwa part din na anty muna zaune sai kwasan dariya muke Jinior ne ke bin mu yana cizo wai hakoran shi na kaikayi inji anty. Ganin daddy ya shigo falon muka shiga gaidashi tare da kokarin mikewa mu bar falon don su gana inda nake zaune nake gaida sai baima tsaya falon ba ya nufi bedroom din ta yana fadin ke may ya hanaki zuwa school yau ko ba a karatu ne yau din. Ta bi yan shi tana fadin ina zata fita mahaukacin soja ya saka security's dinshi akan ta ko ina tabi binta sukeyi yi Yace binta kuma garin yaya haka ya faru ban sani ba kuma ke baki sanar dani abinda ake ciki ba tace yanzu haka kai nake jira ka shigo nai maka maganan ai. Don ashe wai har can kauyen su ya tafi gurin iyayyenta ya nuna masu kudi nan dai tana zama take labarta mai abinda ke faruwa take cewa dashi yanzu haka ita duk a rude take ta rasa yaya za, a bullowa zancen don ta fahinci wanan sojan ba karamin tantiri bane gaskiya kamar aure dole ne ga mata a gari ko ina amma ya nace wa mace daya haka ? Yace yanzu ma zancen ta ya kawo ni gurin ki ai bukatan ki ya biya tunda har kina son hadani da mamana fada. Yace daga gurin mama furin Abba na nufa na fada mashi kina akan bukatan ki sai dai ki sani ba korafi ko wani magana akan hakan daga baya. Don bani na bukaci yin hakan ba kece da hujjan ki mara tushe kin samu mama kin mata dadin baki ta hau ta zauna nai magana tace ban yi mata biyayya ba kuma don haka yanzu dabara ya saura gareku. Sai ki san yadda zaki tsara tunda kece kika hada abinki da kan ki ba wani ya hada maki ba. Tace Alhamdullahi Allah nagode ma dajin wanan labarin farin cikin hakika Rahama alheri ce a gare mu besty ba zaka gane manufana ba sai bayan anyi abin idan Allah ya tabbatar insha Allahu. Idan har kana tunanen zan tsaya kishi da Rama a rayuwana kayi kuskure ni don ka nai wanan hadin amma ka kasa fahintana cikin saukin kai. Kaima kasan abinda mata kewa bakin kishi ai abu daya ne ko toni ina iya hadawa danawa da nata duk ta kwashe na bar mata ita kadai in wanan ne? In dai har zakai muna wanan alfarman ni da ita don ni may yarage gare ni banda bautan Allah kuma yanzu. Wani kallo yai mata yace kada ki soma wanan maganan idan ba haka ba wallahi yanzu nace na fasa tace rufa min asiri idan ka kara botse min kuma wa na san zai taro min kai kuma ? Ban ni dai yanzu nasan yadda zan bullowa wannan yar butsar din tawa don nasan akwai rikici babba tsakani na da Rama nan gaba. Baki ya tabe yace wanan matsalar kune ni dama ban dauka aka ba balle ku tsanmani zan saka maku baki ga zancen ku. Tace ai wallahi dole ka saka don kaine ma zakai jagora gurin lalashin abinka don yanzu ta tashi daga Rama ta koma Raman besty kuma. Haushin zancen ta yake ji fita yayi daga dakin ba tare da ya iya bata amsa ba don haushin maganan yakeji. ********* ********* ********* Duk kwanakin nan biyu idan mun zauna da anty bata da wani zance sai muna huduban yadda zama da miji yake da abinda ya dace mace ta dinga yiwa mijin ta. Sai nake ganin don Gajiye mai son yin aure ita da maigadi takeyin maganan don zancen su yayi nisa sosai kowa yasan shi zai auri gajiye yanzu. Don har daddy yasa a gyara masu can baya inda aka gina wa masu aikin gida ba kowa ke zama ciki ba sai shi maigadin da yan komatsen shi keciki dama. Don haka wani lokaci idan anty na magana har naka yiwa Gajiye dariya mu saka mata wakan shakiyan ci nida su Amira taita murmushi tana jin dadi. Don haka nakan zauna nai ta sauraren yadda anty ke faman mata nasiha kan hakkin da ya rataya akan mata dakuma namiji daya rataya akan shi ga matar shi. Nidai har nagaji dajin hudubar anty akan aure da sun fara zan kunna game muyu ta bugawa nida Nasir muna ihun mu ban tsayawa sauraren su . Ranan Jumma,a da safe daddy yashigo muna falo muna karyawa yana saye cikin wani shadda yaci aiki mai ruwan dark blue sai maiko shaddan ke yi. Anty tace dakyau nawa sai goga na Ram, , , sai kuma tai shiru tanacewa Allah ya bada saan tafiya aje lafiya a dawo lafiya mukuma ji alheri. Ya dan dubeta cikin tsiga maikama da harara yake cewa shi zai tafi sai sun dawo kenan, Anty ke cewa tana gaida mutanen gida idan sun tafi. Bayan ya fitan shi na dago kaina inacewa anty ina daddy zai tafi yau haka aha wanan kwalliya irin haka gashi ko kayan sun matukar karban jikin shi sosai wallahi. Tace da gaske Rama kayan sun karbe shi nace aikema anty kin gani bana gkina ta murmushi ba sunyi maki kyau ke nan kema. Gajiye kece hajiya garin su zai tafi ne ko may dariya tayi tace Gajiye shi ai haifafen dan garin nan ne kowa nasa na cikin garin nan gaba daya yan uwan shi ta uwa ta uba. Unguwa dai zai tafi nan ba nisa bane kwarai nake gani zai tafi a tare muke fadin Allah ya tsare hanya tace amin na mike na kwashi kayan zuwa kitchen ina mai jin haushin rashin shiga na school da wanan fitinanen sojan ya haddasa min kwana biyu ga zarah har gida ta biyo ni kan rashin ganina da batayi kwana biyu. Ban fito ba sai da na wanke kayan na tsane su na dawo falon na samu Gajiye na gyara gurin na samu kujera na haye tare da kwantawa na mike flat tare da lumshe idanuwana a hankali ina jin raina ba dadi ko kadan a lokacin. Yar aikin Zulfa ce tashigo tana tambaye gajiye wai tana da goro ta san ma uwar dakin ta gajiye ta ballo goro cikin wani leda tabara tafice daga falon namu. Gajiye ke cewa nikan hajiya kodai da zaki samune ko ya xon kwanan duk sai matar nan ta aiko neman goro gurina. Anty tace hakanake gani gajiye kamar ciki Zulfa ta samu shine take wahal da ita haka wallahi. Daga yadda nake kwance na mike da sauri ina fadin Ciki kega anty Zulfa Allah sarki har nayi mata murna wallahi tun mutuwan hanifa dama bata sake sake jiku ba a gidan nan kamar yadda take a baya. Keko mutuwar da fa akwai zafi Rama balle irin Zulfa data sawa yar ta rai a gidan nan kamar ikon Allah. Murmushi nayi don nasan ko ita anty ba baya ba ai gurin son yara sai dai na wani yafi na wani ne don ita tana kawaici akan yaran ta. Waya anty ta dauka sai naga ta mike tashiga daki tajima a ciki sai tafito jikin ta duk yayi sanyi a lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU . IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKIN WASU PLEASE IDAN KIN YI GANGANCI KARANTAWA NA BARKI GA ALLAH. IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MIN HAKKINA AKAN KI DON HAKA CIN AMANA NE KI KULA YAR UWA PLEASE, , , YA ALLAH DUK WACCE KE FITAR MIN DA LITTAFINA HAR TAI MAI NOMBA ALLAH NAKAI KUKA NA GARE KA DAUKAN MIN FANSA ACIKIN GAGAWA AKAN KO WACCE YA NA KAI KUKANA GARE KA DUK MAI KOKARIN YI MIN ZAGON KASA TANA FITAR MIN DA KAYA BA BISA KAIDA BA ALLAH KA DAUKAN MIN FASAN CIN AMANA AKAN TA YA ALLAH, , , 35 Mota biyu sukai amfani dashi zuwa gurin iyayyen na wanda Abban anty Saade ne ke jagoran tafiyan nasu a lokacin. Dama daddy yasan gidan mama Altine don haka basu sha wahala ba gurin meman gidan maigari kamar yadda anty tace su tafi can ai masu iso gidan mu. Batan gaisuwa da su ka da yi na dan lokaci mai gari dake zaune cikin shan jinin jikin shi ganin baki daga birni sun shigo mai lokacin yasa yake ganin kamar wani magana ne ya kawo su kan garin shi. Cikin natsuwa maigari bayan an gaisa yake cewa sai dai bamu shedaku ba gaskiya. Abba yai dan dariya irin ma manya yace hakane amma ba Jibo bane nake gani nan kanin Dauda gayu. Maigari yace kwarai kuwa nine Alhaji amma sai dai ni ban gane ka ba ai amma ina ganin idin kamar wanda na taba sani a baya. Abba ya yai murmushi sai ya tuna mai da kikrarin da suke mai idan yazo hira gurin mahaifiyar anty Saade da tai zama gurin mama Altine itace ta tayar da ita su biyu ne gun iyayyen su haka yasa da mama Altine zatai aure tazo da yar uwar ta inda ta hadu da wani yaron Alhajin birni dake shigowa da tasa da atamfa da tangaran na mata suna yawo kauye kauye Nan yaga maman anty tana budurwa lokacin sai dai ta, taso irin bata faye rigima ba ta faye zama shiru shiru da ita sosai. Abba yace Ali na Aliya ikon, Allah da sauri maigari ya nuna shi da yatsa yace hadin Allah ba hadin bawa ba. Yace Alhaji Aliyu kaine nake gani yau a gabana ko may Allahu Akbar ashe da rabon zamu kara ganin junan mu. Yace garin naku ne bana son zuwan shi saboda zuwan shi na min fami da yawa a zuciya na. Ina tuna marigayiya Aliya Allah ya kai rahamarsa gareta aka karba gurin da amin. Nan dai aka dan dawo da dogon labari gamay da baya ana hira ana dariya. Abba ke fada masu ai suna zuwa kauyen mu sosai suna kawo tallah tasa da kumbu da tangaran sai atamfa da sauran kayan amfanin mata a lokaci. Karramawa sosai maigari yai masu bayan sun natsune yake tambayan ko lafiya suka gan su a garin. Abba yace sai alheri don ko yanzu tarihi ne ke son maimaita kan shi don yaron nan nawa mu kazo nemawa auren yar ku. Nan dai Abba ya kawo maganan daluln zuwa su ya fada sunzo ne nemawa dan aure na a gurin su mai gari yai murya yake sai dai bani keda haihuwan yarinyar nan ba amma bari a kira mahaifinta muji na bakin sa duk da dai duk irin hukuncin dana zarta ya dauku akan ta ke nan. Tsawon dan lokaci kada mahaifina ya iso kana ganin shi kaga tallaka tilis dashi wando daban riga daban yadin roba har ya dan takure daga kasa ga hular kanshi duk zaren shi ya zare baiko daukan sitaci don tsufa. Yana zuwa ya na zuwa ya furfa na yana gaida da duk jama, an daya samu a gurin cikin mutunci da girmamawa. Ya samu guri ya zauna tare da lan kwashe kafafuwan shi cikin ladabi ga maigari da jama,an dake gurin a lokacin. Maigari ne yaiwa baba bayanin abinda ke tafe da bakinsu a kan yar shi sai lokacin ya dago kai yana dan kallon su ba bakin da suka zo wancan satin bane yagani. Yace amma dai ba wanda suka zo bane satin can don gaskiya hankalina bai kwanta da su ba. Abba ne yai magana yace malam ka saurarari bayani na da kyau, asali dai nine mahaifin yarinyar da yar ka gurin ta ma, ana marikiyar yar ka a kano. Wanan da kake gani ya nuna daddy, shine maigidan yar tawa da take aure Alhaji Yusuf Sada Rano. Wanan dattijon kuma shine mahaifin shi sai wa yannan aminan mu ne da sukai muna rakiya zuwa nan nemawa dan mu Yusuf Rano auren yar ka. Gaba daya fadan kan su ya daure da maganan Abba din ya fahinci haka garesu yai dan murmushi yace. Nasan zakuyi mamakin jin hakan da nai maku bayani yanzu to hakan duk mun sani a nan bai sabawa addini ba yin hakan. Munzo nan da kokon baran auren yar ku ne bisa tsarin ita marikiyar nata watau ya ta ma, ana matar ita mai son auren diyar taku yanzu. Bukatane mukazo dashi da kokon baran nema iri daga gurin da fatan zaku fahince mu da kunnen basira ba sai an tsaya wani tone tone ba ga yin hakan. Sai fatan alheri ga yin hakan don ni kaina ga irin mutuncin dake tsakani na da mutanen garin nan da kuma zaman yarinyar a hannun mu acan. Zan iya daura mata aure kan mutunci da zumuntan dake tsakanina daku tun a baya gaba daya a ka dauka da hakana ne gaskiya baba na yace ai ko mijin hajiya Saade na da ikon yiwa Rahama aure Alhaji balle kai da kan ka dake da iko da abinka. Amma idan nai haka hankalin abokan tafiya nawa zaifi kwanciya ne idan munzo nan gaban ku ai komai a tare da ku. Gaskiya ne Alhaji maganan ka dutse zaka iya zartar da komai akan Rahama don tazama yar ka halal malak. Maigari ya gyara yake cewa Alhaji sai dai mu abinda ya daure muna kai shine jin wanan mijin hajiya Saade shine yazo neman auren yarinyar nan Rahama. Abba yace hakane nasan zakuji maganan wani banbarakwai haka to amna tunda kuka ganin ni maihaifin Saade ai ya kamata ku san da sanin ta ake komai kuma bukata yin hakan daga gurin ta ya samo asali. Nan dai Abba ya kara masu bayani yadda zasu fahinta da zancen akansu nan dai aka shiga yin kuskus akan maganan gurin ya rude da nazarin maganan. Karshe Abba da mai gari ne suka yanke shawaran cewa tunda har sunce mutanen can da suka fara zuwa su dawo to kamata yayi koda zasu dawo su samu an aiwatar da kwakwaran hujja da zai sa su jaye. Don haka kai Alhaji Yusuf tunda kazo da magaba tan may zai hana ayita takare yanzu a daura auren anan a take. Da sauri daddy dake zaune cikin su shida bashir tunzuwa ba abinda suka furta a zancen ya dago kai yana kallon maigari. Maigari yaci gaba da fadin yin haka shine zai kawo saukin wani fitina don naga wa yan nan mutane akwai aki ga al, amarin su basu zo da saukin kai ba gaskiya. Nan dai aka tsayar da magana cewa za, a daura aure a take a firin wanda Abba ne ya bada sadaki naira dubu dari cif daga aljihun shi . Atake mai shela ya fita ya sanar akwai daurin aure yanzu a kofan gidan maigari ga wanda Allah yaba ikon zuwa. Kafin wani lokaci gurin ya cika da jama, a dan su sheda don haka al, adan kauye yake dama da kara. An daura auren kamar yadda ake daura ko wani aure yadda shari,an musulunci da al, adan kasan hausa ya tanadi yi din . Bayan daura aure ne labari ya samu Inna da mama Altine dake gidan ta wanda yazo yana fada mata maganan jin zancen tayi kamar tatsuniya a kunnuwan ta. Da sauri ta yafa ta nufi kofan maigari ta samu su Abba sun gama komai suna batun tafiya sai ga mama a hargitse tazo gurin. Nan suka fito suka gaisa da ita Abba ke cewa yanzu muke zancen zuwa mu gaida ke gidan ki kada kiji munzo mun tafi duk da sauri mukeyi. Nan dai suka koma gefe yake labarta mata sunzo an daura auren Yusuf mijin Saade da wanan yarinyar da kika bata sai dai bamu zaci abin zai zo da sauki haka ba har a daura aure atake da zuwan mu. Sai gashi Allah yayi abin ya kawo shi a cikin sauki sa kwanciyan hankali a takaice dai yadan yi mata baya ni batare da ta iya fahintar bayanin da yake mata ba a lokacin. Sun mata sallama suka kamo hanya zuwa gida kano a lokacin ne da Abba ke magana da mama daddy ya kira Anty yake cewa gurin ki yacika yau Saade kin sa an daura auren ko. Tace an daura aure fa kace yace tabbas an daura yanzun haka gamu kan hanyan dawowan mu gida insha Allahu. ********* ********* ********* Ganin irin yanayin da tafito dashi daga daki yasa na fahinci bata cikin natsuwar ta a lokacin. Bata sake jikin ta ba duk kokarin da muke yi naganin ta dan sake jikin ta da abinda ya sata rashin dadin rai. Mikewa tayi zuwa dakin ta, ta barmu a zaune falon muna ta hira da dariya abin mu. Ganin bata fito ba hankalina yana gurin ta duk abinda mukeyi a falon can dai namike na shiga gurin ta inda na samu waya take daga kwamce. Ganin lafiyan ta kalau sai na tuna da kayan da na shigo da shi daren jiya zan saka a wardrove din ta na barsu a gurin. Su na fara jerawa har ra gama wayan ta tare da tsura min ido ina cikin aiki gap da zan gama ne naji ta kira sunana a hankali. Na amsa da naam anty tare juyawa na bada hankalina gareta ina sauraren commad din da zata bani nayi. Fuskan ta babu sukuni a cikin sa take cewa dani zo nan ki samu wuri ki zauna. Ba mussu na zo gefen side drower din ta na zauna tare da sauraren abinda zata ce dani. Ina son ki bani hankalin ki da natsuwan ki magana nake son muyi da ke ta fahinta a yanzu da fatan zaki fahince ni tare da girmama girman magana ta gareki da kunnen basira. Nace anty ina sauraren ki fadi maganan ki koma may ye zan kiyayye insha Allahu. Tace nasan ki na gujewa bacin raina abinda nake so kina son shi abinda bana so bakya son shi har abada. Nace hakane anty tace dakyau don haka kin dai san yadda so da kaina ke tsakani na da maigidana ko ? Nace nasani anty dake da daddy abin koyi ne ga ko wace mai hankali a duniyan nan yadda kuke matukar mutunta junar ku. Tace ina fata abin da kikaga inayi da mijina kema zakiyi abinda yafi wanda mukeyi da mijin ki nace cikin murmushi to anty Allah yasa hakan. Tace idan kuma na rokeki arziki zakiyi min ko akan bukatan na Rama ? Nace anty kema kin sani zan maki koda kuwa abin yafi karfina zan kwatan ta hakan nagani. Tace to idan hakane zaki zauna damu a gidan nam Rama, zama na din din, din har abada a tare damu. Nace ni ai dama anty haka yafi min ina zan tafi na barki a haka anty shiyasa ma nake ganin wanan sojan a matsayin mahaukaci don ni aure baiko cikin agender dina yanzu. Ta girgiza kai tare da cewa bar batun soja ya zama tarihi a gareki Rama sai dai ya nemi wata kuma ke kan kin fi karfin shi ai. Rama don Allah ki yarda da kaddara da duk yazo muna dani dake a gidan nan don bijerawar ki zai zama barazana a gare mu yanzu baki daya. Don dagani har ke zamu iya rasa farin cikin mu da jin dadin rayuwan mu baki daya a gidan nan. A hankali na dago kaina ina kallon ta don jin bayanan ta yasa na kasa fahintar inda maganan ta ya dosa a yanzu kai tsaye. Ganin na shagala da mata wani irin kallon ta ya sata cewa dani nasan kina jin magana na kamar shirmay nake koro maki ayanzu ko? Nace cikin damuwa a fuskana ban dai fahinci maganan kawai bane da kyau anty. Tace cikin murmushin yake to bari na fito fili yadda zaki gane zance na yanzu. A matsayina na marikiyar ki kuma yayan ki yar uwarki kinsan ba zan taba saki abinda zakizo kiyi na,dama ba akan shi. Ni dai sai kallon ta da sauraren ta nakeyi kawai duk jikina yai sanyi a lokaci guda amma ma kasa fahintar ta gaba daya kalamanta sun rudani. Kada kice don ni bazaki iya daukan kaddaran da nufin ubangiji ba akan mu don haka duk abinda kika gani ko ko koka ji ayanzu da sani na da amincewa na ga hakan don haka nake son natsuwa da hakkuri a tare da ke. Kaina ya kara daurewa tunane ya gagareni don ban san wani mumunan kaddara take shirin sheda min ba yanzu. Sai kallon ta nake don magana take min mai kama da nasiha kuma da zuciya daya take maganan nata. Kallon tayi tare da kiran sunana na dago kaina muka hada ido cikin murmushi tace Rama yau an daura maki aure da daddy akan sadaki dubu dari sauran bayani zakiji shi daga baya a gurina. Da kyat na iya bude bakina danaji harshena yai mugun nauyi tare da juyawan da kaina keyi a lokaci guda. Da kyat furucin da ke son fito min a bakina ya fito a lokacin nace nace haba haba anty wanan irin wasan bai dace ba tsakani dake don Allah anty ki daina wanan wasan haka please. Anty wani irin wasa ne haka ke da bakinki zaki bude kimin wanan wasan da da wani yai min shi yau bake ba mairabani dashi wallahi sai Allah. Daddy ubana yayana mai kula da duk wani damuwa na da lalurama kun rike ni tankar yarda kuka haifa da cikin ku har zakiyi min wanan bakin wasan da wani ido zan iya kallon ki a duniya duk da wasa ne irin maki anty. Idanuwan ta suka ciki da kwallah ta matso daga inda take zaune tare da kamo hannuwa na ta hada cikin nata tana cewa dani babu wasa ga magana na Rama. Ni nan da kike gani nina yarda da hakan kuma na shirya komai yadda za ai nasara . Nasan komai mukkaddarine kawai tofa yawuna, nayi kawai a cikin maganan don tani Allah ya nufa zancen zai fito. Don tunda kikafa haka Allah ya nufa tun fil,azal da akwai aure a tsakanin ku kin ga ba wani mahalunkin da ya isa ya hana yuyuwan hakan a tsakanin ku don nufin Allah ba wanda ya isa yace a, a acikin sa. Ni banda abinda zance sai dai na godewa Allah da bai doro min gardama ko hassada akan hakan ba. Don zai yuyu maganan tazo min ta bazata na tayar da hankalina akai na nuna rashin amincewa na rabo da hakki yazo ya kawar dani kamar yadda ake fadin rabo na kashewa kuma yana rayawa don alkawarin Allah baya taba tashi akan abu. Rama kada kiyi zato ko tsanmani bani kishin mijina ne wallahi ina son Yusuf kuma ina kishin shi to amma shi kishi aikin banza ne. In kinga ana kishi na hauka akan abu to babu kwanciyan hankaline da adalci a tsakani . Ni ina son mijina ina kuma son kwanciyan hankalin shi duk wani tuntiya da zanyi akan yusuf idan baida walwala ko kwanciyan hankali a tare dashi aikin banza ne gare ni. Da yaje ya dauko wata can wacce bamu san ta ba bamu san halinda zata zo muna dashi ba ai gara ke dana sani kika san mu zauna tare har mai rabawa ya raba mu. Hawayene fal ya cika min fuskana wanda ko gurjin kuka na kasa fasawa a lokacin don na fahinci iya gaskiyan ta take fada min yanzu. Rugumay ni tayi zuwa jikina ta itama kukan take yi ina cewa why why anty zakuyi min haka? Anty wanan shine son da kike tunkahon kina min ko shine kaunar da kike nuna min ko yaushe akaina. Rama ki daure ki fahince ni ban yi haka da nufin kuntata maki ba ko rashin son ki nayi hakane don jin dadin rayuwan ki danamu baki daya. Kuka nake sosai wanda har ya jawo hankalin Gajiye gare mu lalashin duniyan nan da ban baki anty da gajiye sunyi min na saurare su amma nakasa yin shiru sai . Itama kukan ne ya kubce mata har Gajiye din dake bamu hakkuri duk da bata san may ke faruwa ba a lokacin. Mikewa nayi kafafuwana basu daukana na nufi dakin mu takawa nakeyi amma ba wai ina gane ida nake tafiya bane sosai. Ban karasa kaiwa bakin gado ba idona naji ya rufe a gurin na yanke jiki na fadi somamiya dani ba motsi Allah yasa Gajiye ta biyo bayana tana ganin haka ta yanka ihu da karfi shiyasa anty fitowa dakin ta da gudu. Yadda ta samay ni ya tayar mata da hankali ruwa tasa gajiye ta debo mai sanyi suka zuba min ina bude ido na ganni saman jikin ta na bude baki zanyi magana sai kuma na kara somay wa karo na biyu wanan karon kan na dade ban farfado ba daga suman danayi. Daddy ne ya shigo part din guriin ta ya samau su a cikin tashin hankali haka duk ta rude sai kuka takeyi tana fadin don Allah Rahama ki tashi kada ki mutu ki barni da dawainiya a duniya. Ranshi bace bayan ya dade tsaye akaina ya kallon yadda nake yace da ita dama batasan da zancen ba ke nan komay ? Tace cikin kuka bata sani ba shiya yanzu na fada mata cikin hikima don ta fahince ni ba sai taji ga wani ba. Tsaki yaja tare da juyawa don shima zuwa yanzu yanajin zuciyar shi kamar zai tsage daga jikin shi ya fito da wani zaiji fitan da ta dauko mashi ko halin da yar mutane ke ciki. Nan ya daga waya ya kira likitan shi yazo da gagawa yana da mara lafiya a gidan shi. Sai gurin karfe hudu na samu dan natsuwa likitan yace a barni na samu hutu sosai. Haka yasa anty tasa gajiye ta kamani zuwa dakin ta ta kwantar dani a saman gadon ta. Falon shi ya koma bayan likitan da Bashir sun tafi a gajiye yake don haka ya shiga falon tare da rage nauyin babban rigar dake a jikin shi yana kokatin cirewa Zulfa ta shigo falon a hargitse take lokacin. Kallo daya yai mata ya kawar da kan shi a gare ta don shirye yake ga duk wanda ya tare da magana a lokacin. Tace bayan ta zauna yanzu nake jin wani magana wanda ban ma tsaya karasa sauraren shi ba na nufo nan. Kafin ya bata amsa saiga hindatu itama ta shigo cikin tashin hankali yanayinya kawai zaka kallaka fahince ta da kyau. Kallon ta yayi ya mayar da kan shi ga masangalin kijeran da yake zaune tare da karkada kafan shi a hankali idanuwan shi a lumshe. Baba husna may naji labari a yanzu wai kayi aure naji ko may auren kuma wacece wanan karuwan da ka kwaso muna gidan nan . Wallahi koma wacece tayi ganganci shigowa gidan nan cikin mu don in tana takama ita karuwa ce ta iya kwatan zuciyar mazan mutane takai karshe wallahi don sai zaman gidan nan ya mata zafi wallahi. Magana take cikin zafin rai bata san cewa har ya mike ba sai saukan marin da ya gigita ne taji akan fuskan ta kawai. Dafe gurin tayi tare da mai kallo cikin mamaki nunata yayi da yatsar hannun shi yana cewa fice min daga falo mara hankali kawai. A gabana zaki kira diyar mutane kuma matata da sunan karuwa don bakin kishin ki duk waya kaini ga wanan abin bake ba ina wanan maganan yafito ba a bakin ki ba. Aure nayi ba wai kuka ji ba na yi aure yau din nan kuma ba wata bace na aura sai Rahama dake gidan nan zaune tare da ku ita na aura don ku sani. Lokaci daya suke hada baki gurin fadin Rahama Rahama dai Rahaman Saade kake nufi ko wa ? Yace akwai wata Rahama a gidan nan bayan ita ne da kuka sani a gidan nan zaune tare da mu ? Shewa Zulfa ta sa tare da tafa hannun tace yau gaskiya yayi halinsa zargi ya kare kafito fili ka nunawa duniya zargin da ake maku. Yace cikin bacin rai kinga yau zargi ai ya kare ko tunda ta zama matata kuma amarya na. Lalai Saade takai makira a gidan nan ko da yake ita cikin ta yayi ai idan tana ganin takawo ta cikin mune sai data gama karanta halayen mu kaf sannan ta aura maka ita a matsayin mata kuma kishiyan mu. Look duk wacce ke son kanta da lafiya agidan nan ta rufawa kanta asiri ta fice min daga falo idan ba haka ba rayuka zai baci yanzu wallahi. Fuskan shi babu alaman sauki ko wasa a cikin sa haka yasa kowan su tafice tana yaba magana cikin kishi da bakar tsana zuwa gare mu. Suna fita yabi bayan su da harara tare da jan tsuki ya dafe kan shi dake sara mai a ranshi yace wanan masifa da may yai kama ne wai ? Kafin wani lokaci labarin auren yabi yan uwa da abokan arziki kowa yaji. Gadan su daddy kuwa hajiya kamar zatayi haula don fitina sai Allah ya isa take ja wa Saadatu da mahaifinta. Saida Alhaji yaji abin yai yawa ne ya sa mata waigi ta hayan daka mata tsawa tare da cewa idan ya kajin tai magana akan wanan aure ko ta tayarwa daddy da hankali sai tabar maigidan shi. Alhaji akan auren wanan yarinyar yau har zaka bude baki kace na barma gidan ka ? Yace isan baki bargidan ba ma kikace zaki yiwa Allah isgili kan abinda ya tsara sai rabo ya kashe ki. Jikin ta yai matukar sanyi sosai don dama ta zugu tahau akan lalai sai ta sa dan ta ya datse wanan aure don bata ga amfanin shi ba ita. Gida ya cika da yan uwan Zulfa da hindatu sai shige da fice sukeyi duk da daren yayi a lokacin. Sin zugu iya zuguwa don jaka suka dauki shawaran sai sun kuntata min a cikin gidan nan ta yadda sai na raina kaina nayi dana sanin shiga rayuwan su danayi. Don cewa sukayi wai asirine naiwa daddy na fitar mai da hankalinshi gareshi har ya aure ni. Ni dai ina kwance alluran barcin da likita yai min yasani yin barci mai nauyi har ban inda nake ba a lokacin. Anty na dakin sai faman zuwa take tana dubawa ko ina motsi a lokacin amma ban falka ba har zuwa dare. Sai can cikin dare na falka ina falkawa na mike zaune tare da bin dakin da kallo ta ko ina. A hankali na mike zuwa ban daki sai ga ta tashigo dakin take cewa Rama kin falka ke nan sannu yaya jikin naki ? Dakyat na iya bude bakina da naji yai min nauyi da kuma daci nace Alhamdullahi. Ina zaki nace alwala zan yi anty tace tozaki iya ko na taimaka maki ne ? Nace zan iya a takaice na bata amsa na shige ban dakin can na zauna na darji kuka na nafito na ta da sallah. Na idar kuma na shiga sabon kuka a wurin anty da Gajiye ne a kaina suka shiga bani baki cikin lalashi da nasiha. Nan na dunkule tana cewa na tashi na haugado nace nan ma yayi min ai. Haka muka kwana hankali tashe bazan iya cewa ranan akwai wanda yai barcin dadi ba in ka debe yaran gidan. Washe gari duk da banjin dadi kamar yadda na saba na tashi na hadawa yara abin karyawan su tare da yin duk wani aikin dana saba yi duk safe. Ina gamawa na koma dakin mu na dunkule na shiga rera kukan da ya zama min no control yanzu a idona. Nasir yana falkawa yazo inda nake kwance ya dunkule a bayana gashi wani irin matsanacin zazzabi nake jin yana damuna da ciwon kai mai tsanani ban ko iya kwakwaran motsi don wahala. Da kyat hakana na daure na tashi naiwa yaran wanka na shirya su sai dai ranan ban iya tsayawa na sallamay su ba yadda na saba yi masu kullun. Anty ce ke tambayan gajiye ko ina kwance tace na dai tashi nayi aiki ina can kuma na kwanta . Tace cikin zaro ido yanzu duk yadda Rama ta kwana a wahalce saida kuma tayi aiki da safen nan. Gajiye tace nace ta bari takine hajiya sai da tayi yanzu kuma tana kwance don yau yaran ma sunga daban a gidan ta kasa kaisu bakin mota. Tea ta hada mai kauri ta aje falo can kuryan daki ina dunkule ta samay ni ta tayar dani nazo na karya zan yi magana tace dani ban son musu fa. Nafito na zauna a kasa tare da dunkule kafana guri daya na tsurawa shayin ido kawai tace dauki mana kisha Rama. Na dauka na kurba kada n naji shi kamar ruwan magani yadda bakina yake komai bana son sha a lokacin. Mama Altine ce ta shigo gida da ganin ta zakasan ba cikin hankalinta take ba a lokacin . Mutum zai dauka ko a kano ta kwana don uban samakon da ta bugo nayi mamakin inda ta samu abin hawa haka dasafe ta bugo wanan uban sammakon haka. Sannu da zuwa muke mata fuskanta a daure tamau dashi babu walwala a cikin sa. Inda nake zaune a takure gaban anty ta watsa min harara tsana ne karara a idon ta da take min. Take na soke kaina a kasa sai hawaye shar ya zubo min kaina a duke a kasa na kasa dago ido na kalle ta murya a raunane nace da ita mama sannu da zuwa. Ta amsa min ciki ciki ba yadda muka saba ba da ita da take jina kamar itace ta haife ni a baya. Anty ta shiga taron ta cikin nuna jin dadi da ganin ta tare da tambayan ta mama anan kika kwana ne ko kuwa ? Tace agida na dai na kwana da yake na kwana da shirin tafiyan ne na bugo sammako mashin aka dauko ni dashi har zuwa bakin titi. Sai lokacin nadago kaina na kalle ta nake mamakin jin wai mashin ta hawo zuwa bakin titi daga kauyen mu da wanan safiyan haka. Ina naga sukunin zama wanan wanan mara amanan ta sakani a damuwa yadda naga dare jiya haka naga safiya ban iya runtsawa ba wallahi. Wanan tashin hankalin da may yai kama Saade may kuke shiryawa ne haka ba tunane a cikin sa keda mijin ki da wanan ja,irar yarinyar. Mikewa nayi zuwa dakin tabini da harara tana cewa Albasa baiyi halin ruwa ba wallahi yarinya a sakaki innuwa kice zaki kai mutum rana ke. Haba haba mama damay yarinyar nan zataji bafa laifin Rama bane wanan maganan yadda kikaji maganan haka taji shi wallahi. Asalima ke kin riga ta ma jin maganan don ita sai baya anyi angama nake sanar da ita. Tun jiya a birkice take muna na rasa gane kan ta gaba daya taki kwantar da hankalinta tafahince ni. May zata fahinta bayan tariga ta san tsiyan da ta shugawa mutane ni yanzu da wani ido zan kalli mutane dashi sai ta fashe da wani irin kuka. Mama don Allah ki kwantar da hankali ki, ki fahince ni, may zan fahinta Saade anan mun dauko tsintarciyar mage mun saka ajikin mu. Yau Ramane za, ace wai kishiyar ki a gidan nan komay ban taba tunanen yariyar zatayi muna wanan irin yankan kaunar ba. Irin aibanta ni da mama yau takeyi har tana kokarin hadawa da iyayyena yasa naji duk duniyan baki daya ya kara min kunci a raina. Mama don Allah kibar zagin yarinyar nan ni na bada wanan shawaran saboda ina da hujjan yin hakan danay ga baki dayan mu gidan nan. Salati mama ta saka tace kina da hankali kuwa Saade yanzu har ki kalli idona kice da hannun ki da bakin ki kika saka ai maki kishiya. Wa yan nan ma da kuke tare dasu yaya kuka iya da juna balle ki kara daukowa kanki wani sabon wahala kuma ? Mama Rama insha Allahu alheri ne a gare mu ba yadda kike tunane bane da yardan ubangiji. Mama tace ita kishiyar kikewa wanan shedan haka Saade yaufa duk wani so da kauna dake tsakanin ku ya koma kiyayya ke nan tunda kun zama kishiyoyin junan ku kuma. Saade ni har mamaki kike bani wallahi waiko banza yarinyar nan tabar ki kin fasan mutum yanzu abin tsoro ne. Mama wallahi ba abinda Rama tai min yadda kike tunane nice dai naga dacewan hakan na bada goyon bayan ayi din. Daga daki nace a raina lalai duniya da ban mamaki yake ni wani irin so anty ke min haka har yakai takai ga hadani da mijin ta abin alfaharin rayuwan ta da kaunan ta yadda nasan zaman takewar su a cikin so da kaunan junan su suke ko yaushe. Samun irin mata kamar anty a wanan zamanin mace ma,abociya karamci ga mazan auren su tare da jiye masu jin dadin rayuwan su don bukatan su kawai. Samun irin su anty yanzu gaskiya sai an tona a duniya don babu macen da zata iya sadakar da rayuwan mijin ta akan wata can. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA YAR UWA DON BA, A YAFE MAKI BA, , , IDAN KIN TURAWA WANDA BAIBIYA BA ALLAH YA SAKA MUNA A KANKI YAR UWA, , , 36 Ina daga daki inajin yadda mama ke ci gaba da aibantani ga anty tana fadin dama ta dade tana shakkan faruwan haka a gare mu . Don son da kikewa yarinyar nan yai muni Saade shi so haukane da har zaki yi wanan danyen hukuncin a kanki. Maganan Lauratu ya tabbata ke nan in ma bakine itace tai maki shi don ta furta dama tunda mukazo da ita sai tai muna abinda har mu mutu bazamu mantaba a rayuwan mu to gashi ko tayi yau. Nan dai mama take ta aibantani da iyyena cikin daga murya yadda zan iya ji daga inda nake a dakin mu zaune a takure. Hankalina idan yai dubu ya tashi kuka nake ni daya a daki ina fadin koma may zaki fada yau mama a kaina na cancanci hakan a gareku da duk wani nakuma. Baku duk duniya ma na ci a zageni a zargeni a matsayin rikkakan yar cin amana a gare ku. Shike nan yau so da kaunar da anty ke gwada min ya tashi a tutar babu tunda kaddara aure ya gitta a tsakanin mijin ta dani. Aure aure fa waini da daddy yau wai daddy ne mijin sunna na da nake aure wanda zanyi zaman rayuwa irin wanda ma aurata ke yi a tsakanin su. Wanan bakin auren yau yaraba tsakani na da matar data zamay min matsayin uwa da ubana a duniya tai ma rayuwa na tsaye gurin ganin ya inganta. Yau banda wani martaba ga idon duk wanda yaji wanan kaddaran a kaina babu ma wanda zai dauke shi wai kaddara ne haka. Mikewa nayi na fara hada kayana duk abinda nake bukata sai dai babu abinda na dauka daga cikin abinda anty da mijin ta suka saya min a gidan. Na jawo wani dan karamin jakkar kayana na cusa a ciki na mayar na tura a karkashin gado ina mai ci gaba da sauraren maganan mama a falo da takeyi. Gajiye ta shigo dakin ta samu ina kuka take cewa dani Rahama ashe abinda ya faru ke nan dake, yanzu nake jin haka a gurin mama da tazo ai. Kiyi hakkuri tunda ba yin kanki bane haka Allah ya nufa dake sai dai ita mama ta bani mamaki gaskiya wanan magana da takeyi haka bayan tasan koke wacece ta san kuma abinda zaki iya da wanda baki iyawa. Na share hawaye na a hankali cikin dakushewar murya nake cewa Gajiye bari mama ta fadi don itace silar hadani da Anty a rayuwana. Yau kuma ga irin kaddaran daya gitta tsakanina da anty wai muna a matsayin zaman miji daya da ita. Gajiye tace amma ai duk wanda yaji idan ya saurara yasan baki da laifi a cikin zancen nan Rahama, Haba gajiye wanan magana wani mai hankaline ba zai konawa rai ba duk wanda yaji dole ne ya zarge ni gajiye. Yaya zan zauna da daddy mijin anty a matsayi wai mijin sunna a gare ni sai na sake sake wani kuka mai tsuma zuciyar duk mai sauraren ta. Ni yanzu ai tankar daidai nake da mujiya a cikin alumma don nasan duk inda na shiga Gajiye nunani za, ayi a matsayin yar cin amana. Rahama ki daina wanan maganan haka ki zamo cikin bayi masu rungumar kaddara akan su walau mai kyau ko mara kyau. Nace Gajiye na yadda da kaddaran auren mijin matar data rikeni kamar yar cikin ta riko irin na fisabillahi ba kisa ba munafunci a cikin sa. Yau shine zan zauna wai a matsayin kishiya a gurin ta kema kin san hakan ai ba zai taba yuyu ba gaskiya. Dagani har gajiye kuka muke a dakin can muka jiyo muryan anty tana kiranta a falo da sauri tamike ta fita tabarni tana share hawaye a fuskan ta a hankali. Ganin gajiye na sharan hawaye yasa anty ta fahinci kuka mukeyi a dakin dagani har ita. Tace ba dai kuka, kuka shiga daki kunayi ba gajiye kiramin Rama don Allah so take tajawa kan ta ciwo ko may kuma ? Gajiye ta dawo dakin ta samay ni na daga kai sama ina kallon rufing din dakin take fada min kiran da ake min ta juya tafita daga dakin Mama ko har lokacin bata fasa aibantani ba da iyayye sai bata hakkuri anty keyi a falon Munan kalamai na aibanci da mama Altine ke fadi a kaina yasa na rutse ido daga inda nake kwance a daki cikin dafe bakina kada sautin kukana yafito Bata kuma fasa fadan ba cikin daga harshen ta ta yadda zagin da maganan da takeyi zai iso gare ni. Hankalina idan ya kai dubu ya tashi ban san lokacin da na mike ba cikin sanda na tura kofan dakin yadda bazan iya jin kalaman mama ba a kaina. Komai da ya kasance anty ko mijin ta ne suka saya min shi ban dauka ba na boye kayan ina jiran na samu kafa ne kawai na balle daga gidan. Kuka nake ina tunane akan rayuwana ina fadi a raina shike nan burina ba zai cika ba a rayuna nida karatu kuma sai wani ikon Allah don idan na samu nabar gidan nan har abada bazan sake waigo shi ba. Ban taba tunanen rayuwa na zai kare a haka ba ba tare da gurina akan karatuna ya cika ba. Gajiye ta turo kofan ta kura min ido tace ya kamata kibarwa Allah wanan alamarin haka Rahama, dafa yarda da umurnin hajiya hakan ya faru. Gajiy asanadin mama nasan anty yau gashi an wayi gari na zamo maciyiya amana a gare su bazasu taba yarda cewa bada sani na haka ya faru a gareni ba. Don haka ba mama ba duk wani shakiki na anty yau na zamo mai laifi ne da bakin jini a gurin shi. Gajiye da mutuwa nayi daya fiye min ganin wanan bakin ranan a rayuna ranan da za, ace ni Rahama wai na hada mijin sunna da Anty Anty da take kamar uwa da uba a gurina. Matar da ta rike ni rikeni riko na tsakani da Allah ba kissa ba cutarwa tsakanina da ita amma yau ga shi wai mijinta mijin sunnan tane mijina nima. Tace to daure kije kiji kiran da hajiya take maki yanzu kinji yi hakkuri don Allah kibar kuka. Na mike da kyat tare da gyara hijjabin dake a jikina na nufi falon idanuwa da suka sha kuka sunyi zurun zurun dasu don kukan da nasha. Ina shiga falin daddy na fara tozali dashi ya shigo gaida mama da zuwa magana suke da mama da anty da ganin shi abuga na miji hankalin shi a kwance yake abin shi . Yana saye cikin shadda ghalila mai ruwan danyen kore sai maiko takeyi a jikin shi yana sheki. Sai naga ta kara min kwarjini a idanuwa na yau fiye da yadda na san shi a baya sajen fuskan shi ta kwanta lub lub a fuskan shi zakace baima taba aje mace ba a gidan shi don kurciyar shi daya fito fili. Wani irin shock naji har cikin kaina da sauri na dukar da kaina kasa kamar na bude kasa na shige don kunya. Da kyat na karasa gaban su tare da rusunnawa a gaban anty kamar kullun ina fadi cikin dassashiyar murya gani anty. Tace dani bakiga mijin ki bane banji kin gaida shi ba da kwana mana ko kin gan shine yau da gari ya waye ? Hmm naji mama tace tare da fadin ikon Allah wai in baka mutu ba baka gama ganin ikon Allah ba aduniya. Jin abin da mama tace yasa daddy ya kai hannu a fuskan shi cikin dan furzo da iska daga bakin shi yana shafan sajen fuskan shi a hankali da hannu daya tare da dauke kan shi daga kallon mu. Umurnin anty na bi cikin dassashiyar murya nace a hankali daddy ina kwana. Dan gajeren murmushi yayi tare da mikewa yana fadin shi zai fita yana ganin zai isa a wudil akwai wanda yake son gani a can. Anty tai mashi a dawo lafiya yafice daga falon ba tare da ya tsaya amsa mata ba ita ma. Anty take cewa dani bayan fitan shi Rama kina son kijawa kan ki ciwo ne haka ko kije kiyi wanka ki gyara jikin ki don Allah ki daina wanan kukan haka mana may ye amfanin kuka hakane wai ? Ikon Allah lalai Saade kin dauko wa kanki ruwan dafa kanki da hannun ki yanzu kamar Rahama yarinya son kowa kin wanda ya rasa kike kokarin cuna ta haka ga mijin auren ki. Yarinya ta zauna a cikin tsofin mata tayi kishi dasu ba wani hayani shine wai har kike gwada mata yadda zatayi da mijin auren ki. Haba dai mama mijin ta ne fa itama yanzu yadda nake da iko dashi haka itama take da iko dashi a gidan nan. Yaya zanga abinda zai iya halakata ban lurar da ita ba hanya madaidaiciya. Mama tace eh lalaine kuwa naga alaman hakan lalai kinyi nisa bakuajin kira yanzu kan dole sai na mike nasan abin yi akai. Don Allah mama kada kice zakiyi wani abin kaucewa Allah anan da hankalina wallahi. To inko da hankalinki kina bukatan addua gaskiya don abin naki bana kai sake bane an dai kaiki an baro kawai anga gurin ci. Na hade yawu masu daci ikon Allah yau ni mama Altine ke aibantawa haka har da zargi akaina wai nakai anty gurin boka da malamai na kwace mata mijin ta. Maimakon na shiga wanka na koma bakin gado na zauna sai sake sake nake a cikin raina ina maijin kunan rai a tare dani. Zuwa tsawon wani lokaci na daina jin maganan su a falo haka yasa na fahinci sun shiga daga ciki ko daya ya tashi yabar daya a gurin. Na mike na fito don na gaskanta hakan kamar zan dauki wani abu a gurin babu kowa a falon har gajiye ina gani tana ciki tana aiki a lokacin. A hankali na nufi kofan fita daga part din na bude shi cikin sanda na fice daga part din na nufi hanyan fita get. Gefen filawa nabi ina tsoron kada na hadu da wata daga cikin matan gidan don ina tsoron haduwa dasu yanzu saboda na zama mara gaskiya a cikin su. Ina kaiwa bakin get maigadi na hangoni yafara washe baki yana cewa cikin jin dadi hajiya Rahama ashe wani abin arziki ne ta samay mu haka kuma ? Sai da safen nan ai nake samun labari gurin mutanen gidan nan ban tsaya sauraren karshen maganan shi ba na bude get na fice daga gidan. Nai saa wani mai Napep ya kawo wasu mata uguwar na tsayar dashi na dauki shata sai uguwar su Zarah na nufa. Nayi saa zarah na gida a lokacin bata fitaba tana gani yamutse dani na hargitse takw cewa dani Rahama lafiya kike kuwa kika koma haka lokaci daya ? Ban tsaya bata amsa ba na fada saman fogon kujeran dake falonta na shiga kuka ba kakautawa hankalin Zarah yai matukar tashi sosai tai tambayan duniyan nan a kaina babu amsa gare ni. Sai itama ta shiga kuka don tasan akwai mugun labarin da zan fada mata wanan irin kukan haka danakeyi balafiya ba dai kan. Sai da mukayi mai isar mu takoma tana lalashi na kuma cikin tsigar lalami da ban ki har na dan tsagaita kukan nawa. Nace zarah na shiga uku na lalace a rayuwana na zama babban yar cin amana yau zarah ina zan sa kaina yau zarah na shiga uku zarah. Tace don Allah don kaunarki da Annabi ki fada min may ke faruwa dake wai Rahama don Allah daina kukan nan ki fada min. Na dago jajayen idanuwa na sauke su ga nata nace cikin kuka Zarah aure aka daura min jiya. Tace aure aure Rahama aure dawa kuma shine kike wanan kukan kamar mutuwa wallahi na dauka wani abu ne ya samu antyn ki ko wani naki. Nace zara dole inyi kuka zarah wanda aka daura min aure dashi ne abin kuka da tashin hankali. Wa aka daura maki aure dashi Rahama ta fada cikin son jin mutimin da aka aura min. Na dukar da kaina kasa tare da girgiza kaina cikin takaici na kamo hannun ta na jimke cikin nawa da karfi na sako wasu hawaye daga kwayan idona nace. Zara Daddy Zarah daddy mijin anty na shi aka cuce ni zara aka mayar dani yar cin amana ga idon duniya yau. Salati ta saka tace cikin dafe kirjin ta Rahama wai da gaske kikeyi wanan mijin yar naki kuma kika aura don Allah. Na tabe baki nace wai haka sukace niko ko kashe ni za, ayi sai na kashe wanan bakin auren da akai min . Hannuna takara matsewa cikin nata tare da girgiza kanta a hankali tana fadin Allah kadirin Allamanyashau . Rahama Yisuf Rano ne mijin ki yau kuma Allah abin godiya amma yaya hakan ya kasance ne wai ? Nan dai na koro mata dan abinda na sani tace yanzu ma ashe da yardan anty ki akai wanan hadin shine kike tayar da hankalin ki haka ? Maimakon ki godewa Allah da yabaki miji malakin iri Yusuf Rano da duk wata mace ke mafalkin samun irin shi a duniya . Yau ke Allah ya baki shi a cikin sauki shine bazaki godewa Allah ba akan wanan kyautan da yai maki na bazata. May kike so Rahama illimi addini na boko arziki kyawo da kuma zati duk ubangiji ya hore ma Yusuf shi. Don haka kamata yayi ki godewa Allah akan wanan baiwan da yai maki haka a lokaci daya. Kallon ta nake galala cikin mamaki don lafazin ta jin shi nake kamar tana watsa min ruwa zafine a jikina bazan iya sauraren ta ba don haka namike tare da daukan jakkana tabini da kallo tana fadin ina kuma zaki haka muna magana ? Gyara hijjab dina nayi na goge hawayen dake fito min nace nina tafi Zarah na dauka zaki bani shawaran da zan samu mafita ne a cikin sa ashe ke ba haka zuciyar ki yake ba kina cikin masu biyewa son zuciyar su kan abin duniya. Nan na barta tsaye tana mamakina na fice daga gidan tafiya nake ban san inda nake saka kafana ba da kyat na iya tare mai adaidaita sahu na shiga tasha ya kaini inda zan samu mota. ********* ********* ********* Karfe biyu suna kofan mai gari sun zo suji inda shawara ya tsaya akan dan su don su samu a tsayar da matsaya akan zancen. Don suna son nunawa Yusuf Rano bai isa ta hana su abinda suka gani suna so ba gari. Don ma sunyi bincike a kan shi an fada matsu irin matakin daya kai zuwa yanzu yana cikin jerin matasa uku da ake ji dasu a gari. Don akwai su da taimako al, umman garin da na kasa dasu gasu da kokari gurin taimakawa matasa samun aikin yi agari. Wanan halin ne ya kara ja masu farin jini ga mutanen gari da daukaka duk inda aka ambaci sunan su zakaga ana girmama su sosai. Haka yasa sukai shakkun taka shi yadda suka saba taka duk wani mara karfi daya shiga tsabgan su a gari don ba mutunci ne da su ba. Cikin girmamawa aka karbe su tare da duk yi masu abinda aka saba taron bako dashi. Sai bayan sun natsune maigari ya fara dayi masu sannu da zuwa nan mai magana yace da maigari sunzo ne su ji inda magana ya tsaya don a shirye suke tafe da komai daya dace. Maigari ya dan murmusa yake cewa a gaskiya bayan tafiyan ku an samu akasi ga hakan don yanzu haka maganan nan da mukeyi daku wanan yarinyar ta zama mallakin wani a jiyan nan. Don an daura mata aure ta zama matar wani ko yanzu sai dai muce ayi hakkuri da wanan kaddaran haka Allah ya nufa ba zata zama surukar ku ba sai wasu. Alhaji haruna ya dago kai cikin mamaki yace aure fa kace an daurawa wanan yarinyar kuma ? Eh hakane Alhaji Allah yayi ikon shi jiyan nan iyayyen yaron nan da take can gurin shi a birni sukazo da yake dama da sanaya Allah kuma yayi shine mijin sai aka daura atake dashi. Kana nufin Y Rano ta aura ko may ban fahince ka ba maigari ? Wanan dai yaron marikin ta can a birni shine Allah ya nufa ya zama mijin ta a jiya jiyan nan. Amma maigari bakuyi muna adalci ba wallahi ta yaya zakuyi muna haka a gaskiya bakuyi muna adalci ba anan. Mikewa yayi fuuu ya fita daga zauren ana kiran shi amma bai tsaya ba makarraban shi suka bi bayan shi suma suka fada motar su a fusace suka bar garin. Can kusan hawa titin da za a sauka a fada hanyan kauyen mu da babu kwalta nan na hadu da motocin su har biyu biye da juna nabisu da kallo ina tambayan kaina ko motar su waye haka kuma suka fito kauyen mu. Muka fada hanyar kauyen mu gwaram gwaram mota shake da kaya da dabbobi a cikin sa muka isa garin bayan sallah la, asar ke nan. Daga bayan gari na sauka naja hijjab dina na rufe samar fuska yadda babu wanda zai gane nice a lokacin don yan gulma. Gidan kakan nina na nufa don can yafi min siri sai zuwa dare na karasa duk inda zan nufa walau gidan mu ko gidan Inna ta. Sun tare ni da ba, a sai dai da mamaki fal a fuskan su don basu tsamanin ganina ba cikin wanan lokacin haka jiya jiya fa aka daura min aure. Nasamu suyi gurasa shi na zauna naci sai da na koshi na sha ruwa na mike nai sallolin da ake bina nan na zauna ina ci gaba da zubar da hawaye. Kakata mace ce ta shigo dakin ta samay ni zaune ina hawaye ta samu guri ta zauna tana kallona cikin tausayawa. Tace dani Rahama may yakawo haka ne wai ko bakyason mijin naki ne kike wanan hawayen haka. Kaina na girgiza tare da gyara zamana kafafuwana dake mike na mayar na lan kwashe su tare da dukar da kaina nace. Attu bazaki gane ba ban san may nayi ba ko wani nawa yayi a duniya wanan irin kaddaran ke samuna ? Dafarko auren garbati an min shi nai biyayya akazo kan Jatau da akaso lakaka min Allah ya kareni daga hakan . Yanzu kuma Attu a rasa mijin da za, a aura min sai mijin anty na uwar dakina matar data dauke ni kamar yar data haifa a cikin ta. Attu a wayi gari kuma yau ace wai mijinta aka daura min aure dashi may nayiwa su baba suke min haka a rayuwana? Idan da can an min haka ina karama ni yanzu ai naci a tabayi ra, ayina akan hakan . Murmushi tayi tace yo in banda abinki Rahama har nawa kike in ba lalacewan duniya ba da zakice sai an tambayi ra, ayinki kan zabbin dakike so ga auren ki. Baki na turo ko ina dai ba dadi ke nan bakin su daya ke nan kowa na goyon bayan a binda bai dace ba su a ganin su wai hakan ya dace ke nan a gurin su? Nace amma Attu ana barin hasal kodan kunya kuma ko ? Tace kaiyya shike damuwa al, aumma abinda Allah bai haramta amayar dashi haramu don al, ada kawai amma in bashi ba ai ita boyar Allah nan ko banza ba wani hadin jini a tsakanin ki da ita sai so da kauna da yarda ya hada ku. Dayake ita ta Allah ce tana da zuciya irin na addini ta san ya kamata kuma ta bukata aka aiwatar mata da bukatan ta. Allah kadai yasan dalilin yin haka a gurin shi don don shiyasa boyayyen alamarin da ya boye a hakan da akayi. Ni wanan matar bamu da abince mata a duniya sai mu bita da addua ita da zurian ta na alheri. Yanzun dai ki tashi ga ruwa can mai zafi kiyi wanka ko zaki dan ji dadin jikin ki, kici abincin dare sai ki kwanta. Ban ki ba don ina bukatan wanka dama namike na je na iske har takai min ruwa ban daki na shiga na watsa nafito na debi maclean nai brush ko zanji dadin bakina tare da dauro alwala nazo na jira lokacin sallah. Kafin na gama shiri naji har an fara kiran sallah na tayar da sallah ina gamawa wani sanyi da zazzabi suka rufe ni a lokaci guda nan na dunkule dadafe na iya sallah isha, i na kara dunkulewa a gurin babu natun fita ke nan gare ni. Zazzabi ne mai karfi ya rufe, ni lokaci daya Attu tashigo dakin ta samay ni ina rawan sanyi cikin hijjabina tace lafiya dai Rahama nace da ita Attu zazzabi ne ya kamani. Subbahanallahi yanzu kuma kinzo lafiya ciwo kuma haka a gagauce ya rufe ki cikin rawan murya nace idan kina da bargo ki kara rufa min don Allah Attu ? Inajin mijin ta ya dawo take fada mai nazo amma banda lafiya yashigo yadda ya ganin a rufe yasa shi rudewa yafita ya samo min yan hadiya ban ko tsaya dubawa ba na hadiye don wahalan da nake ji. Hakana kwana dasu ina ta faman yi masu sambatu har garin Allah ya waye suna kaina sai sannu suke min. Washegari tunda safe inajin Attu nace wa mijin ta kodai yarinyar nan tana da aljannu ne a kan ta ba asani ba jifa yadda ta kwana tana sambatu kamar mai shafan jinnu. Yace bari dai nai sakkon samun iyayyen ta na fada masu halinda ake ciki kar muzo mu aje yar mutane a gida haka. ********* ********* ********* Gajiye wai may Rama keyi a daki tun da rana banga fitowan ta ba falon nan Ramako na da hankali ta kama kunshe kanta a daki kamar wata bakuwa can. Cikin mamaki Gajiye tace hajiya ai na dauka tana dakin kine kwance tun dazu don dai bata dakin su. A razane Anty tace ina ta shige kara duba min ita don Allah suka kewaye gidan kaf bani cikin part din anty tace duba min key din dayan part din nan da babu kowa a ciki ko can ta koma ta zauna. Mama dake bantalan goro zataci tace may zaikaita can aiko data isa rasa kunya beran tankwa ke nan don samun guri. Gajiye tafito daga dakin da key a hannunta tana fadin hajin kin ga ga key din nan bata can ke nan don guri a rufe yake yadda yake ko yaushe ai. Nan dai hankalin anty ya tashi ta kira wayana not rechable ake fada mata, ta mike ta fice daga part din zuwa bakin get ta tambayi maigadi ko yaga fitana yace lalai yaga na fita amma baiga dawowa na ba gaskiya. Da sauri ta koma dakin mu ta bude wardrobe din kayana kayana suna ciki a jere yadda suke tabi kan mirro da kallo taga babu brush dina da man shafina a gurin. Daga tsaye takai zaune saman gado tana fadin haba haba Rama may nai maki mara kyau da zakiyi min haka ? Ban dauka alheri zai zama maki fitina ba a rayuwana cancantaki ahaka yasa nai maki wanan alherin na sadaukar da kaunana a gare ki. Gajiye dake tsaye tace hajiya a daibi sannu babu inda zata inda ya wuce gida ai sai a buga aji idan ta na can gida din. Anty tace wanan ai abin kunya ne aji cewa wai gudu tayi don Allah gajiye ina rokon ki kibar wanan magana iya ni dakw ko mama bana son tasan cewa gudu tayi don kalaman mama suna bata min rai wallahi. Yanzu abinda za, ayi shine dauko min wayana falo naji ko tana can gida kinga mun san inda take ai bana son na kira waya a gaban mama ne. Takira layin da muke kiran Inna ta bai shiga ba sai takira lawali mai waya yaje ya tambayo inna ko nazo. Ya tafi gidan maigari wurin inna bayan yai masu bayani Inna tafito da kanta tai magana da anty kamar haka. Hajiya mun wuni lafiya tace Alhamdullahi Inna yaya yaran suna lafiya ko ? Duk lafiya lau muke, Inna ko Rahama ta karaso gurin ku ne don bata nan ? Cikin raza inna tace bata man hajiya ina tashiga kuma don dai wallahi batazo nan ba. Anty tace don Allah a tambaya gidan sauran yan uwa ko tana can don Allah amma Rahama bata kyata min ba data wuto bada sanina ba yanzu ma dai asan inda take shine ai matsalan. Inna tace hajiya sai mukaji labari ba dadin ji amma don Allah hajiya yaya akai haka ? Wallahi wanan abin har ga Allah bai min dadi ba ace yarinyar tarasa mijin da zata aura a rayuwan ta hajiya sai mijinki uban diyan ki ? Kai haba Inna wanan ra, ayina ne hakan wallahi Rahama bata ma san anyi ba sai bayan anyi na fada mata shine nan ta tayar da hankalinta haka . Gaskiya hajiya abin ne babu dadin ji wallahi dole ne ta zargi kan ta ai don tasan bata kyauta ba wallahi. Ni dai don Allah idan har wani abu ke faruwa zamata da ku don Allah ki fada min hajiya kada ki boye min don Allah ? Wallahi inna iyakar gaskiyar ke nan ma fada maki yanzun dai ki bari sai na shigo zakiji komai ai inna ki kwantar da hankalin ki a duba muna ita zan kara bugowa anjima ta wayan ki. Sukai sallama Inna sai faman hakkuri take ba anty ita ko sai fadi take wallahi babu komai da yardan ta akai komai asalima ita Rahama bata san komai ba ga hakan. Bayan wani lokaci takara kira Inna ta kara fada mata ta aika duk inda ake tsanmani zan tafi bana can . Haka yasa hankalin anty ya kara tashi ta tayar da Gajiye da hamza driver suka tafi gida zarah ko ina can. Tace da Gajiye nazo amma ban jima ba na bargidan don ta fada min gaskiya. Hankalin anty ya tashi ta shirya lokacin da tasan mijin ta yana gida ta nufi falon shi. Yana zaune kasa saman kafet da remote a hannun shi yana ganin ta ya bita da kallon tausayi. Ta samu guri ta zauna tare da gaidashi da dawo ya amsa mata a kasalance sai tai shiru ya mayar da fuskan shi ga kallon news din da akeyi a tv. Can tace besty akwai matsala fa a gidan nan ya juyo da sauri yace matsala kuma ;amay ? Tace wallahi tunda rana mun nemi Rama a gida nan mun rasata kuma na buga waya can kauyen su bata can. Yace shine matsala na dauka wani abin ne kuma ya faru baya na har kin tayar min da hankalina haka ? Tace wanan ba matsala band nata da hankali besty yarinyar nan fa a hannun mu take kuma ace ta bata? Yace Rahama yarinya ce da zaace wai ta bace ta san dai inda ta tafi don haka banga abin tayar da hankali ba anan. Kallon mamaki take mai kafin wanin su yayi maga Nasir ne ya shigo falon yana fadin Mummy ina little mum dina ta tafi ban gan taba tunda na dawo school ? Nasir Rama ta tafi unguwa tana nan dawowa wani irin ba dadi yaji don tambayan da yaron yai min. Nasir ta kara cewa mummy bazan ci abinci ba sai anty ta dawo muci tare bari naje nai game har ta dawo ? Kiran yaron yayi yace zo nan muci tare da kai ko baka ci da daddy Nasir ? Yaron yace zaka bani a baki yadda anty ke min daddy ? Kallon matar shi yayi ta kada mai kai alaman bagashi nan ba ka fara gani. Sai ga Amira ta shigo tace mummy ina little mun tazo ta samin kayan barci tai min addua zan kwanta ne barci nake ji. Nan ya jawo yarinyar yake cewa zo nan nai maki addua sai kije ki kwanta kinji uwata. No daddy na anty nake so ita har a kafa take muna addua idan zamu kwanta tace shedan bai zuwa gurin batcin mutum. Ikon Allah yace a fili Saade yaya akayi haka kika bari komai sai yarinyar nan kewa yaran nan idan da wani guri tai auren yaya zakiyi da yaran nan haka. Tace tafini kusanci dadune yanzu shiya kawo haka kadai san matsalata aiko. Don haka hakkuri zakayi gobe mu shirya mubita tun kowa baiji asan abin yi akai. Ya kallo ta wani iri yace wa ni badai ni ba nina aike ta komay kedai da kika ce kinji kin gani dabara ya rage naki yanzu ai. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA, A YAFE MAKI BA DABARA YA SAURA GA MAI TSORON ALLAH ANAN, , , IDAN KIN TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YA SAKA MUNA A KANKI YAR UWA, , , , 37 Kakana Ada ya tafi gidan mu ua samu mahaifina yayi sammakon zuwa kasuwan kauye don neman na kasan haka muka taso muka samu yana wanan aikin wahala don ciyar da iyalin shi. Gidan maigari ya nufa babu kowa a kofan gidan don safiya ne majalisa ba fara ba kowa na gidan sa a lokacin. Yana jin nauyi da kunyan matsayin shi na suriki agan shi kofan gidan da wanan safiyan. Don haka ya juya yakoma gida a hanya ya yanke shawaran kiran mai chemist yazo gida ya dubani yadda ake a kauye. Ya dawo ya samay ni ina kwance a dukunkune yadda ya barni yake sanar da Attu zuwan mai chemist dubani. Wani matashi ne ya shigo daganin shi kamar ba bahaushe bane yare ne shi, ina kallo ya fitar da wasu allurai wai zai min su. Nace cikin karcin hali parluter da paracetamal zai min ya kalleni cikin mamaki kamar zaiyi magana sai kuma yai shiru. Yana min na koma na kwanta inda nake sai barci mai nauyi yai gaba dani ban kara sanin inda nake ba kuma. Ganin barci ya dauke ni Attu ta fice taci gaba da aiyukan ta na gida da ta saba yi kullun. Gidan maigari basu fita da rana sai da dare amma yau wanan matsala yasa inna ta roke shi ya barta ta fita zuwa gidan su . Bai hana ba don yasan tana cikin matsala a lokacin don haka ya barta ta fita da rana haka. Ta sa nikaf takawo katon hijjab zumbulele ta saka ta goya danta ta nufi gidan iyayyen ta dake can yamma da gidan maigari. Attu ce kawai a gida tana ganin yanayin yarda yar ta shigo gidan a hargitse kada kafa take batasan inda take jefawa ba don tashin hankali. Sama sama suka gaisa take cewa mama kinji abin kunyan da yarinyar nan ke son ta jawo muna a gari. Yarinya kamar ta za, ace ta kama hanya taitafiyan ta ba, a san inda ta nufa ba don kawai rashin hankali irin nata. Yanzu ga matar nan tunjiya hankalinta a tashe yake ta bugo waya tsakanin jiya da yau yafi a kirga a garin nan. Duk inda ya dace naje tun jiya na aika amma batazo ba may take son ta jawa mutane , ina zata in ba rashin hankali ba inda yafi mata gida. Koma may nene ai bazatai kokarin watsawa wanan matar kasa a idon duniya ba haka. Tun da Allah kadai yasan manufan ta na yin hakan da tayi akan ta mumun isa mu kawar da kaddaran ubangiji ne ko kuwa da bazata kwantar da hankalinta ba akai ga mafita sai tasa kafa ta tafi. Allah ya gani mama tunda naji wanan auren jiya hankalina yake a tashe wallahi ace yarinyar ta rasa mijin aure sai mijin wanan boyar Allah mai mutunci da karamci haka. Gaskiya su maza haka suke abin su ba shawara in kai magana ace da kai wai ya halasta ne yin hakan da akayi. Amma ina dacewan hakan anan ace yarinya zatai zaman kishi da uwar dakin ta marikiyar ta da tai mata tarbiya ta ingata rayuwan ta haka. Sai da Inna ta kai ayya Attu tace da ita ina kuwa zata in ba gida ba, yarinya na cikin tashin hankali zaki bita da naki irin fitinan kuma da wani kuke son taji yanzu? Tun jiya da yarinyar nan ta iso garin nan, a kwance take ga ciwo ga kukan da take faman yi jiya yadda mukaga rana haka mukaga dare a gidan nan a kan ta. Yanzun haka tunda safe saida babakin ya dauko mai allura akai mata gashi komai bataci ba sai dan gutun gurasan data gitsira taci kadan take kwance tana ciki jikin ba dadi gare ta. Inna najin haka duk da hankalinta ya dan kwanta amma kuma sai ta kasa natsuwa sai tagan ni da idon ta dakin ta fada ina kwance can kuryan dakin Attu na dunkule guri daya gwanin ban tausayi dani. Tana tsaye akaina tausayi ne irin na uwa da danta ya tsirga mata a zuciyar ta take taji tausayina ya kamata a lokaci daya. Jikina ya bani akwai mutum akaina haka yasa na bude nauyayyen idona da yai min nauyi da ciwo na sauke su ga Inna ta. Ina ganin ta na yun kura da kyat na mike zaune ina cewa sannu inna da kyat nake iya magana muryana suk ya dakushe don kuka da cison dana keyi. Idanun inna ya ciciko da hawaye ta samu guri daga gefe na ta zauna tana baiye yaron dake goye a bayan ta. Tana zama na dan dago kai a hankali na dan kalleta tare da bude baki na da yai nauyi da kyar nace da ita. Inna kinji abinda anty taiwa rayuwana kinji kaddaran da ta jefa rayuwana aciki wai mijin ta zata ce na aura inna ? Inna wai anty da bakinta take cewa dani da sanin ta akai min wanan mugun tabaibayin a rayuwana. Inna wanan shine kaunar da Anty ke ikirarin tana yi min abaya shine sakkaiyan da zatai min ta ce na auri mijinta mu zauna zaman kishi da ita muna cudan yan mijin auren ta tare dani. Mutanen da nake gani a matsayin iyayye a gare ni nake alfahari da kasancewa a tare dasu ko yaushe yau Inna ta da wani ido zan iya kallon su dashi. Innata inna zan iya zaman kishi da cikin iyalin daddy wa yan da suka waye udon su yake a bude. Idanun Inna suka ciko da hawaye ta sa gefen hannun ta tana sharewa a hankali tace dani. Yarinya yadda kike ji haka nake ji a raina na san zafin abinda akai maki. Amma kuma maganan dubawa anan shine ita hajiyan bamu san manufanta nayi haka akan ki ba. Babu wata mace da zata ba mijinta bakin karo mata kishiya in bata da dalilin yin hakan a kan ta. Ni sai ma nake tunanen anya ba mijin nata bane ya tursasa mata yin hakan akan ki yai amfani da damatan ta ya cuta maku ke da ita ? Anya yarinya babu wani abinda ya faru tsakanin ki da mijin wanan boyar Allah da har ta yanke wanan shawaran haka akanki. Amma in bashi ba wani hujja gareta haka mai karfi da har zatace mijin ta na aure yai mata kishiya kuma kishiyar yarinyar data rike kamar yar cikin ta. Na dago kaina nace Inna ta ni ni may daddy zaiyi dani bakiga matan shi bane yan birni kuma yan gayu dasu. Shine nake mamaki abinda zai sa anty ta zabi jafa rayuwana cikin wanan rayuwan na gidan su rayuwan da kullun a cike yake da sabon fitina itama yaya ta kare dasu balle ni Rahama a haka dani. Ke ba mutum bace ko ke ba mace bace duk da ban san suba daga cikin su akwai wace tafiki zatin zama mace ne ko kuwa ? Attu ce daga bayan mu ke fadin wanan magana ba wanda yasan shigowan ta dakin daga ni har Innata. Taci gaba da cewa may manya ke fadi idan kazo gari ka samu kowa da bindi a gatin kaima samo kara ka daura bayan ka sai ka saje da kowa a garin. Don haka zaman su yan birni ko wayayyu ba komai bane wanan mace kike kuma Allah ya taimake ki kin zauna dasu kin san halin kowacen su inda take da matsala. Sai kikokari ke kuma ki amfani da naki hikimar gurin ganin kin dinke wanan matsalar a garshi. Maynene kishi ba wani abu bane yau inkiyi ja inyi fari gobe inkin sake nima na sake kala kowa tashi tafishe shi kawai. Amma wanan matar abin dubawa ne don bamu san manufatar da yin hakan da tayi ba na sadaukar da rayuwan ta akan ki haka. Bai kamata ace kin watsawa tayin kasa ba a ido don da manufa ta aikata haka a gare ki kuma dama can da akwai kaddaran aure a tsakanin ki da mijin nata. Kinga Allah ya taimake ta bata jaba inma har shi ya bukaci yin hakan gareta kada rabo ko hakkin auren ku yazo ya kashe ta ga banza. Inna ta ce ai dagani tun fil, azal akwai aure tsakanin ki dashi tunda hakan ya faru da kuma ranta bata mutu ba akayi. Wanan auren sai dai muce dashi kaddarare ne ga uban giji babu aure da za ayi in dai zaiyi tasiri ba, a samu akasi akan saba da wuyane ayi shi salin alin. Keda kada ki yarda wani rayuwa na kishi ko rudin shedan ya jaki kiyiwa wanan matar butulci akan wanan karamcin da tai maki . Don haka ki sawa kanki hakkuri ki daure ki bi mijinki da abokiyar zaman ki a zauna lafiya. Ki zauna da kowa da zuciya daya kiyi masu biyayya yadda ya dace idan kikai haka kin wanye da kowa lafiya duk wanda ya dauko sheri akan ki ya koma a kan shi. Amma idan kina wanan butulcin kin butulcewa Allah kin butulcewa ita hajiyan taki ke nan don bamu san manufanta ba fa yin hakan da tayi. Shi kishi ai aikin banza ne idan babu zuciyar miji akan ka da kwanciyan hankalin shi may mace zatai tuntiya dashi a duniya. Ki maza ki gyara kafin mijin naku ya fahinci baki kaunar shi baki ra, ayin shi ya dauki mataki a kan ki. Don haka maza ki idan kinji karfin jikin ki ki tashi ki watsa ruwa ajikin ki, kikuma samu abinda kika ci ko zaki kara walwalewa yanzu. Ina tace ji yadda kike kokarin mayar da kanki cikin dan lokaci guda dan Allah ? Da kyat na hade yawu abakina da sukai min kauri da daci nace Inna ji nake kamar kasa ya bude na shige don ban iya daga ido na kalli anty wai a matsayin kishiya nake gareta yanzu. Maza tashi ki watsa ruwa a jikin ki ke nan duk maganan da ake fada maki baki san kibar wa Allah al, amarinsa ba ke. Nace cikin sabon kuka mama bakiji zagi da zarin da mama Altine take min bane har ni mama Altine ke kira da tsintaciyar mage a gabana duk da hakkurin da anty ke bata tana fada mata babu sani ga hakan ya faru. Ita mai kulin kulin ta tafi can ne gurin ku nan dai na kwashe komai na fada masu Attu tace assha aikko mai kuli kuli batai halin manya ba wallahi. Aike yanzu kin zama nasu bai kamata ta tayi maki wanan hukuncin ba har take maki kazafi kan zaman ki gidan garbati. Inna tace mutum ke nan ta nuna nata tasani yau babu komai zata dawo taji kunya in har baki da amanan ta ai. Amma ina dadin ka nuna naka kasani kawai inji Attu take fada cikin hasala da bacin rai yadda mama Altine tai min. Wanka nayi suka tasani gaba na dan sha koko da guntun kosai na koma na dunkule a guri daya. Zuciya na fam da tunanen yadda rayuwa na zata kaya agidan anty cikin kishiyoyin ta ga ta bashi ba ma ni yaya zan kalli daddy matsayin mijin aure na da zamu wai raya sunna a tare. Mutumin da nake ma kallon mutunci da kamar mahaifi a gurina bana son naga na bata masu ko kadan shine wai yau ke da igiyar aurena akan shi. ********* ********* ********* Duk yadda anty taso daddy subi bayana yaki amince mata da hakan sai bashir ne takira shiyazo gidan suka shirya da ita zasubi sawuna kauyen mu su gani. Bashir yace ai kinga irin ta sai danace ki bani ita kika hana kika dauka kika ba wanan mijin naki da kukai ma yawa ya kara. Tace oh dai Rama sai Yusuf Rana ba Bashir Rano ba je kaji da yar matar ka gudu tankar da dubu shi yakai gwarzo ne har kaga yana kari akai akai. To aidai yanzu ya rufe sai mugani idan zai kara kuma tace alaman zama gwarzo ke nan ai kagani. Yace kika dai kaishi ke uwar son dadin miji har da son akara maki kishiya kin zabi jin dadin shi kinbar naki ke nan ke gaki, yar dadin miji ko ? Yace please Bashir ku tafi inda zaku kubar ni don Allah yace eyye kinji ko watau ma ya matsu muje mu dauko mashi amaryan shi har koramu ya keyi ma ke nan. Murmushi daddy yayi inda yake zaune tare da lumshe idanuwan shi wanda hakan ya zama mai dabia duk wanda ya san shi ya san shi da wanan dabian lumshe idanuwan shi. Fitan Bashir da Anty yai daidai da zuwan mama Laraba gidan part din anty ta fara zuwa Gajiye da mama ke fada mata anty tafita unguwa wanda su basu san inda ta tafi ba alokacin. Take cewa Gajiye cikin sakin fuska ni ina amaryan dan nawa ne sarakuwar tawa nagan ta ko har ta fara kunyata ce kuma ? Mama Altine ta tabe fuska daga inda take zaune take cewa tana ciki kunkumay tun jiya ai bata fito ba kunya ai marinda ni za, a kawo wa lalata cin amana a filin Allah. A, a ban gane ban fahince ki ba waye yaci amanan wani anan dan nawa ko ita maryan tashi kowa kike nufi ? Yo inba cin amana ba tarasa mijin wacce zata aura sai mijin yarinyar may Saade ta rage ta dashi a duniyan nan da zatai mata haka ? Ai shi namiji ba kunya ne dashi ba ko yarinyar sa, ar yar cikin shine sai ya aure ya hada dakai kinga ina kunya ga maza ? Amma dai ina ganin baki zauna da yar taki ba tai maki bayanin komai yadda maganan yake ba ko ? Hajiya ga abu a fahince zaman may zamuyi ta riga ta aure mata miji ko a fili duniya ta sheda hakan gare ta. Kai amma kina wani magana wallahi shiyasa bincike keda dadi wallahi yar ki ai itace tai wanan shirin don daga shi mijin nata har yarinyar ba mai hannu ga zancen shirin Saade ne wanan. Kuma abinda baki sani ba shine wanan magana da kike yi zai jawa yar ki bakin jini ga sauran abokan zaman kai har ma ga yan uwan shi. Sai suga sai abinda Saade tace dashi yakeyi kinga abinda basu sani ba zasu zo su san shi yanzu. Don haka kada kiga laifin yar mutane laifi na gurin yarki dakukan ta da komai take bin wasu mu har taci saa ya yarje mata kan zancen. Mama ta da mai da muryan ta kasa kasa kamar mai son gulma ko rada tana cewa ke baki tunanen ko zargin su takeyi yasa ta yanke wanan hukuncin a kan su ? Da sauri mama laraba ta dago kai tanawa mama Altine kallon mamaki ga kalamin ta tace wa Alhaji karami ne za, a zarga akan mace macen ma yarinyar dake hannun matar shi ? Kice Allah kin tuba ga wanan magana naki don wanan mumunan zargi ne hakan kike masu ai kuma bai dace ace kina babban kanki aji wanan kalamin daga bakin ki ba ? In baki sani ba ki sani ita yarki akwai matsalan da take hasashe daga gare ta shine take ganin yin haka da yar uwarta shine mafita a gare ta. Don makomar mijin ta da yaran ta a bayan ta duk da dai ai ciwo ba mutuwa bane na fada maki wanan magana ne yazama siri a zuciyar ki ko dan yadda naga rashin sani ya fara saki ga zargin yar mutane haka. Shiru mama Altine tayi tana nazarin maganan mama sai kuma hankalinta ya daga take cewa may ke damun Saaden da har taga wanan shawara ne mafita a gareta ? Koma may ye babban al, amarine dole ne taji komai fila fila daga yarta don tasan abinda ake ciki da ita. Nan mama Laraba ta fice ta barta zuwa sauran sassan gidan ta gaisa dasu tare da dan masu nasiha don ta samu ko wacen su a hargitse a part din ta sun hau sun cika sai batsewa sukeyi. Tafita zuwa gurn dan nata ta samay shi zaune a faln shi shi kadai yana ganin ta ya kakaro murmushi a fuskan shi. Yana cewa mama ashe kina tafe yanzun nake shitin fita ai anyi saa ban fita ba ko. Tace ai yun dazun nazo ina sasshen Saade ne zaune yace ai bata nan ta tafi kauyen su wanan yarinyar wai bata gidan tun jiya da ta samu labari zuwan wanan maman tasu ta kara tayar masu da hankali nake gani ? Aiko zata tayar don yanzun muka gama takai da ita akan zancen ta samu yar mutane tana zagi tana aibantawa . Yace may ye na zagin ta a ciki ga mai laifi nan Saade itada ta kawo wanan matsalar kan hujjan ta na banza mara tushe da asali tasa mutane a tashin hankali. Ni dauka na sun riga da sun shirya magana da ita yarinyar ne ashe ita ko tuntubar tama da zancen batayi ba akai. Nan dai sukai ta tattaunawa tana kara bashi hakkuri tare da kara nusar dashi kan hakkin zama da iyali daga karshe take cewa tazo ne taji yaya ya yanke shawaran inda zan zauna dakuma maganan lefen da za, ayi min. Yace mama sai kin fadi yadda kuka tsara don ni banda ta cewa akan wanan maganan takuce ku mata. Mama tace wanan dayan shiyan dake kusa dana Saade sai a gyara mata shi tunda kaga ba kowa a ciki ta zauna nan ko dama wani gidan ne zaka nema mata daban ? Ya dago kai da sauri yana cewa wa haba mama ta dai zauna nan ida kowa yake ciki itama don kaita wani gida zai kawo min zargi ai ga sauran matan . Yace hakan dai da kikace dama shine shawara na don ba kowa a shiyan zanyiwa masu gyaran guri magana suzo su duba asa mata duk abinda ya dace aciki. Tace da zakaji sai ince gaba dayan su ka canza masu tsarin dakunan don kada su zarge ka akan hakan da za, ayi in yaso ita da take amarya sai a gyara natan yafi kyau zaifi. Yace yadda kika gani mama zanyi magana dasu suzo su duba su ga abinda zasuyi akai. Mama tace shi batun lefe fa yace yana hannun Saade wanan mun riga munyi magana da ita kafin ta tare sai a saya mata komai. Mama ta kara cewa suma wa yan nan zakai masu nasu na fadar kishiya idan kuma kudin suke so su saya sai abadu a hannun su a dai wanye lafiya dakowa yafi. Yace ba matsala mama zan yi magana dasu naji ra, ayin su akan hakan abinda yafi masu sauki. Sun dauki lokaci da ita tana kara bashi magana don ta tausaya ma yadda zan zauna cikin matan shi haka dani. Yace ba matsala mama Insha Allahu zan a kula kada kiji komai zanyi adalci yadda ya dace a tsakanin su tunda duk zamana sukeyi. Bata koma gurin mama Altine yaba da mota aka kaita gida tana cike da mamakin halin na wasu mutane da basu da ganewa. ********* ********* ********* Inna na batun komawa gida har ta mike tana kara jamin kunne sai ga yar gidan maigari tayi sallama Anty na biye a bayan ta suka shigo gidan. Ikon Allah hajiya Saade ashe kina hanya sannun ku da zuwa gabana naji ya wani mugun faduwa jin sunan da Inna takira a lokacin. Inna ke cewa kinga ta ashe tana nan gurin kakan nin ta nufo shiyasa bamu san da zuwan ta ba garin. Wani ajiyan zuciya anty ta sauke a baiyane tana fadin Allah mungode ma yanzu can gida da muka je cewa sukayi ba a gan ta basu san ma tana garin nan ba ke nan. Tace wa zaiyi zaton zata zo nan din yanzu tunda ba wai ta saba zuwa gurin su hakana bane. Attu ta ce da ita ta shiga daga cikin daki nan aka shimfida mata tabarma ta zauna suka ahiga gaisawa dasu. Da kyat na iya tasowa daga inda nake cikin kunya nazo na dan tsugunna a gefen ta ina cewa ina wuni Anty. Wani kallo ta watso min fuskan ta babu sukuni ko kadan a cikin sa, take cewa dani . Rama baki son farin cikina ashe na girgiza mata kai cikin tashin hankali alaman ba hakana bane anty . Nasan don ni kike wanan borin da kikeyi bawai don baki son Yusuf babe babu macen da zata samay shi a matsayin miji tace bata kaunan hakan. To Rama yau dai ayita ta kare ni Saade nice nazabi yin haka gare mu kuma nice na kawo shawaran ayi haka din gare ki. Na dago kai a hankali ina kallon ta cikin mamakin ta da baya kare min ko yaushe naga magana take da zuciya daya dani. Rama na fada maki ina da dalilin yin hakan danayi zan fayece maki gaskiya yanzu idan kinyi niyar taimakona ko bayan raina ne idan kinji zaki iya hakan gare ni. Idanun ta suka ciko da ruwa nima haka nawa ko su Inna da ke tsaye da Attu suna cikin wani yanayi . Rama nayi haka dan yau ko bani a duniyan nasan yarana da mijina suna hannun na gari a duniya. Suna inda babu cutarwa a garesu suna inda za, a rike min su riko na fisabillillahi. Rama na yaba da tarbiyan ki na kuma yaba imanin ki kina zama da mutum da zuciya daya kin san yakamata kin iya zama da kowa da zuciya daya. Wanan halin naki yasa nai nazari akan haka tun bayan kazafin da sherin da Hindatu tai maki ke da maigidan naga ai kamar shawara ne tabani ga hakan . Shiyasa na shiga nafita ga duk wurin wanda nasan maigida zan saurari maganan shi har akaci galaban shi akan hakan. Nasan ke mace Rahama da sannu zaki samu karbu a zuciyar maigidan kada ki dauka a yanzi bawai aure so ne kukayi ba a, a aure ne da ake fatan dorewan shi cikin nasara da kwanciyan hankalin ku nan gaba. Don haka bana son cewan da kike ke yaya zaki hada miji daya dani nasan da haka ai amma na amince da ayi din zaki koya kuma zaki iya zama dashi din. A ban garen yara ko yanzu banda matsala dake don baki gidan jiya da yaran sun baki tausayin dan rasakin da sukayi na kwana daya. Yau din nan da kyat na samu aka shirya su suka tafi school don shi Nasir ya ce bamai mai wanka sai ke da kanki haka abinci ma jiya kin ci sukayi wallahi. Don haka a wanan bangaren yanzu hankalina a kwance yake a hakan don kon riga kin maye gurbina ko anan saura ta fannin maigadan mu yanzu. Wanan sai idan kin kwantar da hankalin ki a sannu zaki fahinci komai akan shi. Daga haka ta koma lalashi na a ban baki kowa a gurin sai data bashi mamaki da tausayi yadda take magana gwanin ban tausayi wai duk akan mijin ta na sunna take wanan maganan haka. Yadda kuka yazo mata takeyi shiya kara karyar min da zuciya na bani ba har inna da Attu dake gurin sai da suka karya da zancen ta. Tausayin anty ya kamani sosai na fada saman jikin ta ina cewa anty zan yi komai a kan ki indai har yin hakan shine zai zama farin cikin rayuwan ki. Rugumay ni tayi cikin kuka take cewa insha Allahu Rahama ba zakiyi nadaman wanan auren ba don Yusuf mijine abin alfari ga ko wace mace data samay shi a duniyan nan. Sai bayan an natsune take cewa da Attu to yaya za, a bani ita ne mukoma ko yaya za, ayi yanzu ? Attu tace a, a hajiya dadai kiyi hakkuri ki barta har ta dan kara samun natsuwa idan kun aje ranan da zata tare kinga sai azo a dauketa akaita dakin ta kin ga haka ma gata ne gare ta don asan tana da asali kodon gori wata rana kin san mu mata ba tabbas ke gare mu ba. Anty tace ba laifi hakan ma yayi ai ba matsala sai dai tarewan nata ba zai dauki wani tsawon lokaci ba a yadda nake so don karatun ta duk abinda za, ayi nan da sati mai zuwa insha Allahu za, ayi shi. Anyi sallama da ita ni dai ban fito ba duk da ina jin muryan bashir ta kyauren su Attu yana min sheri ina daki naki fitowa waje naji tashin motar su suka tafi. Nan suka bar mu inna da Attu na kara bani hakkuri na daure ko don wanan matar na kwantar da hankalina akan ta. Inna ta tafi gida take fadawa maigidan ta ai ina gidan iyayyenta nan ta samay ni shiya ta dade hakana. ********* ********* ********* A gaji ta dawo gida don ta dade batai tafiya haka ba sai bayan tayi sallah magariba ne Gajiye ta kawo mata abinci taci tasha magani. Daga inda take zaune ta daga kai ta kalli yaran ta suka bata tausayi yadda rashi na, na dan lokaci yasa duk suka shiga damuwa haka inga yau ace nabar gidan gaba daya nayi aure a wani gurin yaya zasu kasance masu hakan. Tafito daga wanka ne maigidan ya shigo ya samay ta bai mata sannu da zuwa ba sai take cewa dashi haba besty yaya zanbi ma amarya na dawo kuma babu ko sannu. Yace na aike kine wanan matsalar ki ce don ke kika zabi yin haka nikin tuna min ma dazu mama Laraba tazo gida nan bakya nan. Da sauri ta dago tana cewa dashi Allah sarki mun sha banban ke nan da ita yace hakane. Tazo ne wai akan tarewan wanan yarinyar tana son taji ina za,a ajeta dakuma wai maganan kayan lefe. Nan dai ya fata mata a furguje yadda sukayi da mama Laraba din taji yace part din dake kusa da ita za, a ajeni da sauri tace dashi na dauka ai ko zaka gyara mata wancan gidan da muka fito zaifi ta sake jikin ta ai. Yace ba; da ra, ayin yin haka ga iyalina idan zata zauna nan inda kowa yake ta zauna don ba fin wani tayi ba nakuma yi magana da masu gyaran guri zasu zo su duba part din kowa suyi abinda ya dace suyi. Sai zancen kayan lefen da tayi zan baki kudi ki hado abindaya dace ayi idan basu isa ba sai ki fada min na kara maku. Sam Anty bataso wanan shawaran nashi ba nace wai na zauna a part din dake kusa da nata ba taso ya kaini wani gurin da bata ganin abinda zai gudana a tsakanin mu. Don ita kadai tasan irin taushe zuciyar ta datake yi kan wanan matsalar shine mafita ga rayuwan ta kawai harta amince da yin hakan gare ta. Amma babu yadda ta iya shike da gidan shi yadda ya tsara dole hakan zata daure ayi shi. Sai bayan fitan shine mama tashigo dakin dama magana nacin ta tun fitan mama Laraba gidan ta barta da tunanen matsalan may ke damun anty ne wai harta yanke wanan danyen hukuncin a kan ta haka ? Tace da ita magana nake sin muyi Saade ni uwarki ne baki da wanda zaki iya fadawa damuwanki bayan ni yanzu ina son ki fada min gaskiya wani matsala ne ke damun ki a rayuwa har kika yankewa kanki wanan shawara ki aura wa mijin ki yarinyar da kika tayar kamar diyarki a duniya. Maimakon ta bata amsa sai kawai ta saka mata kuka itama mama kuka takama sukayi mai isar su subiyu a cikin daki babu mai basu hakkuri. Can cikin muryan kuka take cewa mama ina da matsala a rayuwa na wanda ba kowane yasani ba sai mijina da mahaifina. Da sauri mama ta tsagaita da kukan ta tana sauraren yar nata tace mama wanan matsala yasa naga kafin mai rabawa ya rabani da yaran nan nai masu gata na nema masu uwar goyo na gari da ko a bayana zata iya rike min yarana. Nasan halin mahaifin su bazai taba yarda wani nawa ya dauki yaran nan ba ya rike a gurin shi dole dai a gidan nan zasu zauna. Zaman su da wa yan nan matan mama hatsarine babba ina rayema basu sosu ba balle ace yau na fadi na mutu. Ganin dacewan Rama ga wanan matsayin ne yasa na yanke shawaran hada ta aure da shi ko bani raye dai yarana nada wacce zata rike min su tsakani da Allah. Ban san kuma bayana wazai kwaso masu ba yace ta zauna min da yarana ba ban san irin tarbiyan ta ba da zata basu. Shiyasa kikaga na zabin yin haka amatsayin madogara babba a gareni ko a bayana bazasu wullakanta ba. Shin wai may ke damun ki ne haka kike kirawa kanki mutuwa Saade ciwo aiba mutuwa bane ko sai mai lafiya ma ya tafi yabar maiciwo a duniya. Ki fada min may ke damun rayuwan ki Saade ta dago kai ta kalli mama da ta tsura mata ido tana son jin karin bayani dafa gareta. Tace mama in dauke da cutan sickle da farko shi likitoci sukace yake damuna har ya zama min coronic sai daga bayan nan bayan mun koma suke ce min kuma ya koma min Cancer. A razane mama tace bari kira min wanan balain shine fa akace ya kashe uwar ki a baya can. Tace cikin hadiye miyaun bakin ciki mama shine ke damun rayuwana don ma maigidan yana tsaye sosai a kaina ne da kuma ita Rama dana samu ta tsaya min gurin kulawa dani sosai aida ban kaiba killa ma. Kuka mama ta saka wiwi tana salati tana fadin ta shiga uku yanzu Saade kina da wanan matsala kike boye min shi a rayuwan ki kuka suka saka a tare ba maiba wani hakkuri a cikin su. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA A YAFE MAKI BA DABARA YA SAURA GA MAI TSORON HADUWAN SHI DA ALLAH KAN HAKKIN WANI, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH ZAI SAKA MUNA AKANKI DON BAKI DA TSORON HADUWA DA SHI KAN HAKKIN WANI ALLAH NAGANIN KI IN BAMU GANIN KI, , , 39 Jin fitinan nasu yaki karewa sai gaba yakeyi a tsakanin su ga su mama na ta tsawata masu amma basu daina ba. Tsam namike tsaye na gyara lafaya na da kyau tare da dan fara takawa na nufi hanyan fita daga falon daddy da su mama suka bini da ido. Ina kai kofa naji zulfau nacewa anty idan ma kin ba da goyon baya ne ai muna haka to dake za, a fara don kowa ai yana da kishi bamu kadai wanan yakin zai ci ba a gidan nan. Anty tace sai dai kun makara a, i don gashi an fara daku kun kasa hade fushin ku a gaban ta kuna tonawa kanku asirin zuciyar ku. Aure ne dai anyi shi inma mutum yace iya gatse ya iya ya sara agaban yan amin aiku kuka fara furta hakan yan amin kuma suka amsa maku. Kalaman nasu ba dadin fadi amsan da suka bata ina ficewa mama tace kun gani karamar yarinya tafiku hankali da sanin ya kamata gashi ta fice bata iya tsayawa sauraren ku. Ina zuwa na samu yan uwana zaune a falo suna kallon tv suka ban tausayi mutanen mu na kauye akwai son kallo gare su. Nashiga daki nan nasamu Attu da matar maigari uwargidan su inna ta zaune a dakin Nasir da Amira kwance saman gado da alama jirana suke sukai barci. Na gaida su na gyarawa yaran kwanciyan su na zauna gefe daya suke cewa dani ga ferfesu nan da shayi Gajiye takawo kowa kuma yasha cikin su. Attu ke tambayana injin ba matsala dai ko na kwashe abinda ke faruwa na fada masu take cewa ni nasan akwai aiki ai. Matar mai gari Abu tace ba wani matsala ai mama idan ta iya zama dasu sai a zauna lafiya ki fita batun su kada ki biyewa haukan su don dama dole ne sai sunji zafin abin tunda anan kike zaune dasu. Kusa da Nasir na koma na kwanta na kura mai ido kaman shi da daddy sak nake gani yau har kamar ma ya baci. Tsakiyan yaran na kwanta kewan su na kwana biyu yana shigana a hankali. Idanuwana suna a lumshe muryan Anty ne ya ratso kunnuwa na tana fadin a, a ashe akwai aiki kuwa yaran nan yanzu nan suka zo suka kwanta. Mama Abu tace da ita kin san yaro ida yaga fuska can yake tun fitan ku muna nan dasu har barci ya kwashe su gurin shigowan tane ta gyara masu kwanciya ai. Na bude idona tare da dan mikewa kadan nace sannu anty tace sai na juya ban ganki ba falon murmushi nayi na dukar da kaina kasa kawai. Tace basu son a zauna lafiya idan ba anyi fitina ba su basu jin dadin rayuwan su ko yaushe daga magana ta fahinta sai kice zaki ba yarinya kashi shine ai ya hasala ni ai tasan halin Rama sarai. Take tambayan babu wani abinda ake bukata ko mama tace a, a Alhamdullahi hajiya mun gode wallahi. Dukowa tayi inda nake zaune cikin rada tace dani shirya na kai ki gurin angon ki ko ? Da sauri na turo mata baki gaba nace kai haba anty cikin yar shagaba tace dake may kike nufi haka za, a zura maki ido komay ? Yarinya kinzo hannu ke nan ai may za, a fasa sallah ko salati ai kinzo hannu sai ki shirya don daddy ba wasa. Take idanuwa na ya ciko da kwalla tace daga magana sai kuka ashe akwai aiki kuwa Rama. Kwanta gaki ga mutanen ki ai ba yau ba sai baki sun tafi ai mu fara two two days dai ne aka tsayar da magana idan kin gama Amarcin ki yanzu su mama suka yanke hukunci don da wa yancan sunce sai dai ayi one one day yadda muka saba abaya. Jin ta kawai nakeyi harta gama tai muna sallama takai kofa nace anty ta juyo nace maganin kifa ? Tai murmushi tace ai dole insha Rama yau yadda nagaji din nan tun safe ban zauna ba fa sai dai gobe muyi maganan komai idan baki sun tafi. Washegari da safe sai ga anty a dakin ta shigo Gajiye na biye a bayan ta da jakkar bako. Ta samu guri ta zauna ina shafawa Amira mai ajiki nan na shiga gaida ita take cewa da mu. Attu ga maigidan nan zai shigo gaida ku don zaiyi tafiya ne yau tafiya ya kama shi. Nan suka shiga gyarawa can mukaji muryan shi yana gaida mutanen dake falo daga nan anty taimai jagora zuwa daki inda nake tare dasu Attu suka shiga gaisawa dashi yana tsugunne kamar yadda suriki kewa surukan shi girmamawa. Nasir dake tsaye saman gado yace daddy see me here with my mum, she is now back. Mummy tace itama tazama matarka bazata kara barin mu ba again yariko min hannu yana tambayana wai hakane. Kunya duk ya rufe ni a lokacin ya mike yana cewa su gaida gida ya gode ai mashi godiya gurin maigari da babana. Bayan fitan shi ne anty ta dan rakashi can sai gata tadawo dakin take cewa da Attu ga sakon godiya daga gurin maigidan. Tace Gajiye fitar da turamay nan ta miko kudi tana cewa gashi kowa turmi ne da dubu biyar yace kuyi hakkuri dashi ba yawa. Haba nan guri ya rude kowa da irin adduan da yake jerowa akan aure da maigidan nai magana da Gajiye ta dauko min wasu kayana a part din Anty nan na ba su Rukaiyya da Lawisa da suwaiba yan uwana har ma da wasu daga cikin uan rakiyana. Sai nasiha suke min na zaman lafiya anty tashigo take cewa nazo na yafa mayafi nabi bayanta muka dan tsaya daga dogon coridor dake tsakanin part din ta da nawa. Tace dama kujerun nan da aka kwashe daga part dina nake son a kwashe kayan akaiwa inna su can kauye nata sai tabawa wanan abokiyar zaman nata don naga matar na da mutunci sosai. Kasa nakai na tsugunna a gaban ta ina godiya takai haba may ye aciki ai yiwa kaine hakan ni zan iya biyan ku abinda kike min ne don haka sai ki fadawa Attu ta fada mata ta kwashe kayan zuwa jibi za, a shigo mata dasu. Na kara mata godiya ta dafani ta wuce zuwa nata sasshen nabi bayan ta da kallon tausayawa. Ina shiga na samu Attu da mama Abu nake fada mata sakon anty tai murna sosai da farin ciki tana cewa kaji arziki ba muma arziki ya shafe mu. Nan dai ina kallo akazo Gajiye ke fada masu mota yazo nace wa mama Abu da baba bazaiyi fada ba da an barmin Fatima ta dan kwana min biyu nan tare dani. Attu tace abari idan sun koma sai aiwa magari magana wanda yaje kai kaya sai yadawo min da ita idan ya amince da haka sukai min sallama ina kallo yan uwa na suka tafi suka barni gidan da nake wa kallon gidan danger. Suna fita na fara gyaran dakin sai ga su Zaraha da Nafisa sun shigo gidan da kaya niki niki sakon da suka sayo min. Aikin da suka samu inayi ne suka karba da taimakon su na gyara duk inda bakin su ka bata suka saka kayan kamshi a ko ina a part din. Nan suka baje min kayan da suka sayo min balaifi nima kayan su ban sha, awa sosai sai wasu abubuwan da Zarah ta kawo min wai na amfanin mata ne. Karba nayi cikin ya mutse fuskana tare da mata wani irin kallon raini nace wanan fa na may ye shi ? Tace sa mai gida kuwa ke nan kingan shi nan kamar yankan wuka yake wallahi. Don sai kin toshe bakin namiji nima sister din mamana tazo min da shi tsaraba daga bargu. Nace kai zarah ni wani miji can zai min kuwa dan Allah kibar wanan shirmay mutum da mata haka dirka dirka har may zai kalla a nan. Nidai gani ga Allah kawai ban san yaya rayuwana zai kayya ba cikin wanan gidan. Kamar yaya ke ba mace bace Rahama may kika rasa da ake nema a gurin mace wanda baki dashi a jikin ki sai dai idan kin yi rowan haka gare shi. Ni wai may yasa mutane basu da magana ne sai irin wanan zancen shi ke nan da anyi aure, ba wani magana sai maganan cudanya da miji. Tace to may ye auren Rahama may kuma akewa kishin ba wanan ba duk shine dai tsananin kishin ai wanan dan jijiyan guda kawai. Nace Allah dai ya shiry ki Zarah don ban da kunya sai naje yin wani kakale ga daddy na kalleshi da wani ido ke nan ? Tace anya kuwa Rahama wai ni da kikecewa wai kin taba aure kin ko san harka kuwa a rayuwan ki. Mace ko dan fleeling bata da shi akan namiji hakamar wara dakila can dake haka ? Nace don Allah zarah bar zancen nan barsu da mijin su suyi ta kayan abinsu nikan ai a matsayin yar aiki nake gare su. Nace jiya fa hindatu cewa tayi kashi ma zata bani a gidan nan basai taga na shiga harkan mijin ta ba zata kai ga dukana din. Kece ko may shiga harkan shi Rahama don yanzu ke amarya ce shar gaki baki taba haihuwa ba komai naki a tsaye yake kamar baki taba aure ba. Nafisa tace kardai nace jiya jiya har kun fara da matan gidan nan nace sun dai fara, su da basu danayi sai zancen miji ko yaushe. Umm, umm fa kada muzo muna jin ana cewa kunji abinda honey yai mun watarana . Nace waye honey din daddy din kowa don Allah kice Allah kin tuba Zarah don banda kunya zan kira daddy dina da honey komay ? Tace ai zancen daddy ya kare don yanzu sai sabon suna kin taba jin inda daddy ya danne diyar shi a tarihi. Tsuki nayi na mike tare da kwashe kayan naje na boye kada anty ta shigo girshi dakin ta gansu naji kunya. Ina dawowa da magana daya Zarah ta tare ni dashi tace idan zaki kwanta ki tabbatar da kunlun kin yi tsarki da ruwan dumi a tsarkin ki. Ki samu mai masu kanshi ko yaushe kina shafawa a tsakanin cinyoyin ki don kin san guri ne da baya samun iska ko yaushe. Shiko namiji duk sanda bukata ta ya biro mai baida lokacin a garshi sai ya biya yake samun natsuwa tare dashi. Kada ki din tsayawa miji kerere idan yana neman bukata ke koda ma baya neman komai a garki ki kasan ce mai yanga da sallon kina yauki yadda hakalin shi zai daga dake. Gaki da abinda akasarin maza ke so a jikin mace nono kina dan dinga bankaro mai kirjin ki yadda hankalin shi zai dinga dagawa. Don Allah dai Zarah ki bar wanan zance haka please tace naki bari rigunan nan da aka sayo maki ko ba wani abu zaki dauka ba kina dan dukawa cikin stely yadda nonowan ki zasu dinga baiyyana a gare shi. Koda zani kika daura ya kasance boons dinki sun fito da kyau fili gashi dama daddy kine sai ki samu wanan daman kina mai shagwaba irin na da da uwar shi ko yaushe kina manne da jikin shi. Haka zai kara jawo maku shakuwa sosai a tsakanin ku ya kasance yana cin abinci kina zaune kina dan kara mai ruwa ko miya ko gyara mai bakin shi. Zarah please stop that rubish wanan magana naki da may yai kamane wai please ? Tace da gaskiya mana tace idan kuma kunzo kwanciya kiyi kokari hannun ki yadan taba ciyan shi ko tsakiyar bayan shi kin gama gamawa dashi yarinya. Ke classic baby ce don haka ki zamo may son yawan romace da dan magana cikin sexy voice yadda zai rude ya rasa inda zai sa kan shi akan ki. Oh my Allah Zarah ashe haka kike tace har nafi nan yarinya ki dinga tabbatar da kin mai sallaman da zai tafi ko ina ne yana dauke da tunanen ki a ran shi sai yaji ki a kusa dashi ya samu natsuwa a ran shi. Kina dai nufin in yi haka in shaga tsakanin shi harda anty na ke nan ko Zarah ? Tace bance ba ai ita anty ta daban ce amma dai ai a fagen miji ake yanzu kowa tashi tafishe shi kawai . Nace badai ko da anty na ba cikin wanan plan din tace indai har zakiyi din ai sai ki cire ta ciki ko ? Har tsawon wani lokaci sukai min sallama suka tafi na koma ni kadai a shiyan zaman kadaici ya damay ni su Nasir sun tafi makaran ta a lokacin. Na rufo kofa part din na nufi part din anty Gajiye kawai na samu tana aiki take cewa dani ai Anty ta dan kwanta don jikin ta ba dadi karfin hali kawai takeyi. Ban zauna ba na shiga taya ta aiki kamar yadda na saba yi har dakin muni dasu Nasir sai da na gyara komai gurin ya koma neat har falo sai da na gyara shi yadda nake mai. Na koma dakin mu na zauna sai ga gajiye da abinci takawo min daki ban iya ci ba na dan taba kadan na barshi nan. Tafito daga wanka take cewa dani Rahama ba kici abincin ba ta zauna daga gefena tana cewa dani. Haba Rahama may yazo da bai wuce ba wanan abin fa ba laifinki bane wacce kike jiwa ta fada maki da yardan ta akai hakan ai to may zai sa kina sakawa ran ki damuwa haka ? Don Allah ki kwantar da hankalin ki ki rugumi mijin ki da hannu bibiyu kada kizo ki fadawa sabon Allah alhakin mijin ki dana yar uwar ki ya kama ki. Hawaye naji ya zo min tace sake jiki zakiyi yadda take son ganin ki ki zama mai biyayya a mijin ki da abokan zaman ki in har kin cire komai a ranki zakiga abin yazo maki da sauki. Muryan anty ne ke kiran Gajiye a falo alaman ta tashi ke nan daga barci daga inda take muna jin tana cewa Gajiye kin ko kaiwa Rama abinci taci ? Tave hajiya aiga ta nan ma zaune tun dazun take nan ita ma tai gyara gida da kan ta sai dai taki cin abinci wallahi. Ina Raman take ne ta tambaya na amsa da na,am anty nafito ina gyara gyalen kaina da kyau. Tace a, a wai har yanzu kina fama da wanan mayafin haka kamar wata bakuwa dake ? May yasa baki ci abincin ba ne wai ko har anzu baki hakkura da kaddaran ubangiji bane a kan ki ? Idan har kina son mu shirya dake Rama wallahi sai kin saki jikin ki kinyi biyayya ga mijinki da sauran abokan zaman ki. Ni dai indon ni ne na fada maki da sani na da yardana akai komai da kika fani don may wai ba zaki saki ranki ba ki zauna lafiya a dakin ki. Bazaki taba samun kan mijinki ba Rama idan bakin bada hadin kai akan hakan ba rashinyin hakan gareki kuma kamar rainawa da hukuncin Allah akanki da magana . Haka kuma zaki iya jefa kanki ga halaka da fushin ubangiji a kan ki don haka noroke ki Allah Rama ki zauna lafiya da mijin ki kiyi biya. Na dago kai ina mata kallon mamaki ta miko min hannu tana fadin zo nan yar kaunata. Ba mussu na nufota kamar karamar yarinya na zauna gap da ita ta dan rugumoni tana cewa dani haba Rama. Don Allah kiyi hakkuri ki yi biyayya fa mijin ki mijin ki mutum ne mai murdaden hali sai a hankali zaki fahince shi. Yana da yawan bukata wanda nasan sai a sannu zaki saba da hakan gareki. Don Allah Rama ki daure ki fahinci beasty zakiji dadin zama dashi sosai indan kin fahince shi. Rama nasan zaki iya insha Allahu don nasan halinki nasan na besty na don haka idan kin kwantar da hankalinki abin zaizo maki da sauki sauki sosai. Don haka daga yau ina son ki sake jikin ki ki zama kamar kowa a gidan nan don kin dai san halin matan gidan nan, sarai da son raini wayyo, ba zan so ace kin bari sun fara kawo maki raini ba don ba fashi za suyi hakan don ko halin su ne ba son suke a zauna lafiya, ba. Ni dai ina sauraren abinda take fadi ziciyana sai fal, fal nake ji wanan wa,azin da anty ke min anya kuwa zan iya hakan da take so dani. Tace ban san may suka saka maki a cikin kayan lefe ba don bani na sayo masu ba su Aisha ne yaba kudin suka sayo mashi. Don ni lokacin da akai sayayyan mun dan samu matsala dashi kan zancen auren naku. Na dago kaina da sauri ina kallon ta cikin mamakin jin abinda ta fadi wai akan aure na sun samu matsala da mijin ta. Kada ki damu zan maki wanda ya dace idan na samu lokaci zan dan shiga na sayo maki abin daya dace ayi. Idan na danji sauki sai mu zauna mu tsara yadda abubuwa zasu tafi muna anan a cikin part din cikin rufin asirin mu. Nidai ban ansa mata ba haka ta dinga dan jana da hira nasan tanayi ne don na sake jikina kawai. Muna nan zaune saiga yan makaranta sun dawo gava dayan su sukayo kaina da murnan su. Nai masu sannu da zuwa tare da rugumay su a jikina nakaisu dakin tare da cire masu kaya nabasu abinci suna ci muna hira dasu. Time din islamiya nayi na shirya su zuwa Islamiya suna ficewa na kara gyara gidan tsab anty tana fitowa ta ga ina aiki take cewa dani. Rama don Allah kibar aikin nan kibar gajiye ta dinga aikin nan yanzu hakan ba naki bane. Murmushi nayi naci gaba da aikina kawai ban daina ba sai dana gama na koma part dina naiwan ka tare da bin dakin da kallon mamaki duk wanan gurin wai yau mallakina ne. Wanka nayi na shirya cikin daya daga cikin kananan kayan da Nafisa ta sayo min bayan na idar da sallah ne na nufi gurin anty don wayan da Zarah ta bugo min muna da test a school. Zaune take tana waya sai daga baya ne na fahinci da msigidan take wayan amma bata jima ba ta katse wayan. Ta juyo gare ni tana cewa Ramana yaya gajiya da kewan su Attu suna dai gida yanzu kan. Nan na dan duka cikin murmushi nace Anty dama nazo na fada makine muna da test ranan tuesday in Allah ya kaimu shiyasa nake son na dan leka school din. Allah sarki Rama kin san yanzu ikon ki yafita a hannuna hakkin ki na karkashin mijin ki don haka shi zaki kira ki fada mai. Da sauri na dago kai ina kallon ta mai ma, ana wani ? Nace a hankali anty ba zan iya magana da daddy ba gaskiya ina jin nauyi da kunya anty na fafi a shagwabe take cewa dani. Kikirashi ki fada mashi muji abinda zai fadi kin ga idan ya yarda sai ki shirya ki tafi ko. Nace anty bazan iya ba wallahi kuma ni ban ma da nomban daddy a wayana gaskiya. Taimako dayan zan maki zankiraki na baki wayan sai kiyi mashi magana muji. Ta daga wayan ta ta kira shi bayan sun danyu magana take cewa Amaryan ka ce dama ke son magana da kai besty, ban san may yace mata ba naji ta kwashe da wani irin dariya tana miko min waya. Na karbi wayan a sanyaye a hannun ta don ban san may yace wa anty ba take wanan dariyan irin haka. Ina karba a sanyaye nake cewa cikin wani murya daddy ina wuni shiru naji yayi bai amsa min ba. Nakara fafin haka a karo na biyu sai naji yace hmmm, wace irin amarya ne da bata damu da jin lafiyan mijin ta ba. Rama ko baki damu da angon naki bane haka zamuyi dake ko haka kikaga anty ki tana min bata damu da damuwana ba sam. Mamaki da imanine ya kashe ni a lokaci daya wai yau ni daddy ke kokarin yiwa magana irin haka a rayuwana. Kai watau maza dai basu san kunya ba a duniya ke nan ko may yasan kuma anty na gurin amma yake kokarin yi min magana irin haka kamar wanda bai san kunya ba. Jin nayi shiru ne ya kara cewa ko baki jin abinda nake fafi ne wai naji kin yi shiru ba amsa ke nan dai ko ? Sai da na dan daga ido na kalli anty naga bata sauraren mu tana can tana wani tsabgan gaban ta hankalinta bai gurin mu. Nace a hankali dasdy yi hakkuri don Allah, yace bazan yi ba sai naji hujjan ki na yin hakan ? Shiru nayi yace dole ne na hukuntaki da yin hakan da kikayi don ni ba ai min laifi na yafe kai tsaye kin sani. Nace ban sani ba daddy amma don Allah kayi hakkuri yace bazan yi ba na fada makii sai kin biya bashin yin haka idan kuma kin sake sai nai doubling din yin hakan. Yanzu ina jin ki nasan kina da bukata ne kika nemay ni ko ? Nace daddy dama test ne muke dashi ranan tuesday shine nake son shiga school don an dan wuce ni dama. Yace kibari zanyi magana da Saade zakiji may na yanke a kan haka nai mai sai anjima na mika mata wayan na daga nabar dakin don suci gaba da wayan su. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA, A YAFE MAKI HAKAN BA DABARA YA SAURA GA MAI TSORON HADUWAN SHI DA ALLAH KAN HAKKIN WANI, , , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA ROKI ALLAH YA SAKA MUNA AKAN KI DON BAKI DA AMANA DUK MAI FITAR MIN DA NOVEL ALLAH YA DAUKAN MIN FANSA AKANTA, , , 38 Sin dauki lokaci zaune a dakin ba mai iya yiwa wani magana a cikin su don tashin hankalin da suke ciki. Can mama ta nisa take cewa amma may yasa baki fada muna wannan matsalan ba naki tun tuni sai yanzu. Nan dai take cewa zata tafi ta gwada maganin gargajiya ko Allah zai sa a dace kallon ta kawai anty ke yi tana murmushi kawai. Masu gyaran guri suka shigo gidan kan jagorancin Habbib brother din maigidan ta wurin uwayen su . Sanin ko shi waye yasa daya shigo gidan da masu gyara ba wanda yai magana daga cikin matan gidan. Kafin kwana biyu an fitar wa kowa da nata tsofin kayan an saka sabbi angyara komai sai gurin ya koma kamar a lokacin ne suka tare a gidan gashi badama su dan yi korafi akan komai yanzu habbib yaci masu nutunci. Maigidan baya gari yai tafiya koda akai gyaran gidan duk bayanan akai komai sai daya dawo ya samu an gyara ko ina neat har part din shi sai dai ya samu matan gidan suna cikin hasala sun cika fam dasu. Sai bayan sallah ishai ne yake cewa dasu yana da magana kowace ta karasa yanga da jan aji tazo falon amsa kiran maigidan. Gurin da Anty oe zaune ya dan kalla sai yaga yadda ta dan samu zugi gurin mama Altine tasauya mai baki dayanta ya kasa fahintar ta. Yace dama ba wani abu bane yasa na kira ku nan sai akan zancen wanan aure dana kara . Naso ace kafin auren ne labarin yazo maku amma Allah bai nufi hakan na sai gashi anyi shi a bazata muna zuwa nema aka bamu tare da daurawa don darajan iyayyena. An dai matsu da ita dama ana neman kai abaka daga tayi wani kallo yaiwa Hindatu tare da kada kan shi. Sai Zulfa da tace ai zata gane kuren ta zata san tayi gigin shigowa, inda yafi karfi shigan ta. Ya dan yi murshi yace ko ashe anfi karfinta a nan gamu gani ke nan yana magana yana kallon fuskan anty Saade wacce tun safe yau yake ganin sabanin halinta a fuskan ta. Maimakon ita da ta hada ta bashi full confedence kan zancen amma sai tai wani kicin kicin da fuskan ta a lokaci daya. Abinda bai sani ba shine tasha zugi fam gun mama Altine dake ganin kamar tun farko asiri naiwa mijin anty da anty suke matukar sona da kauna na haka. Yace cikin daure fuska ba wai na taraku don son jin ra, ayin ku bane na kiraku ne don naji bukatan kowa kan kayan fadar kishi da zan maku kudin zan baku ko kayan za, a sayo maku. Har suna hada bakin su, su biyu gurin cewa kudin muke so abamu ya ce ke saade may kikace a hakan ta wani tabe fuskan ta tana cewa ni duk yadda akayi duk daya a gareni. Nan ya kirga kudi kowace sai da tai mamakin kudin daya basu a lokacin. Sai bayan komai ya lafa ne ya mike ya samu Saade a dakin ta zaune take saman salayan da ta idar da sallah take zaune sai nadama da dana sani take auki yi a zuciyar ta afili ta yarda cewa bai yuyuwa ace gaba dayan su suna matukar son Rama haka dole akwai kamshin gaskiyan maganan mama a cikin zancen. Tana jin shigowa shi amma bata dago daga yanayin da take zaune ba ta fuskance shi ta a yadda ya samay ta a, zaune a dakin. Tana ganin shi taji wani tsanar shi ya shigeta lokaci daya yau mijinta masoyin ta shine daga tai mai tayi ya zake akan maganan har tana son finta zakewa ma yanzu yadda taga yana rawan kai haka. Baki jin nashigo gunki ne amma ko ki daga kai ki kalle ni dago kai tayi ta dan kalleshi a nakashe wanu haushin shi ne da tsana taji ya ziyarci zuciyar ta. Kai maza baku da tabbas wai yau besty ta ne ke rawan jiki akan Rama yarinyar data tayar tankar diyar da suka haifa. Wanan gaskiyan maganan mama Altine ce tace dama renon kan shi yaiwa Rahama a gidan don bukatan shi shine yai amfani da ita cikin saukin kai yayi mata dubara har ta yarda da zancen auren da kan ta. A hankali ya tako zuwa inda take zaune yace ban fahince kiba don tunda na dawo naga wani canji daga gareku haka. Wani kallo ta watso mai daidai lokacin da take gyara zaman ta da kyau sai ga hawaye shar shar suna biyo fuskan ta tana kokarin tare su. Tsayawa yayi ya kura mata ido cikin mamaki yace Saade kinga abinda nake wa gudu ko ? Tun farko abinda naiwa gudu kenan muna zaman lafiya kin kawo muna sabun fitina da zai tayar muna da hankali. Dama nasan a karshe nice zaki bari a cikin zancen ina zaman zamana kika dauko minbsabun fitina a rayuwana . Kece kika sakani yin auren banda ra, ayin karin mata a rayuwana ammakika sakani gaba da kai karana gurin magabata na har nakai ga amincewa da zancen. Da kikasan bazaki iya hakkurin hakan ba da saiki barwa Allah al, amarin ki yai muna mafita da kan shi. Amma yanzu gashi kin saka ayi abu kin kuma dawo kin tayar da hankalinki kin kasa samun natsuwa muma na tare da ke mun kasa samun namu. Ya juya a fusace zai bar dakin sai ga mama tana shigowa dakin take cewa yaka mana Alhaji may kuma ke faruwa yau ina jin harshen ka har falo. Mama may Saadatu take son mayar danine don taga ina tausaya mata shine take ganin kamar zata iya juyani yadda ran ta ke so, bafa tsoron ki nakeji ba, abubuwa da dama yasa nake matukar tausaya maki ina maki ragowa akan su. Amma akan may kike son mayar dani wani bi can kamar mijin hajiya a gidan nan auren yarinyar nan kece fa kika tasa ni gaba zuwa gun magabata na . Yanzu kuma Allah yayi abin kina kokarin tayar min da hankali so kike na zama mutumin banza ko may nace eh, na dawo kuma nace a, a komay ? Wani kuka ne ya zo mata a lokaci daya tana fadin besty nayi nadama wanan hadin na cuci kaina da kaina besty. Yanzu na fahinci nayi gangancin hada ka da Rama danayi a rayuwa na na fahinci yin hakan babban kuskure ne a rayuwana. Kallon mamaki yake mata cikin rudewa yake cewa yanzu kina nufin dai kin jaye zancen auren ta a ranki sokike na sake ta ko ? Da sauri mama ta cabe zancen tace shine saukin sakin wanan yarinyar don bai yuyuwa ace kamar Rama ta zaman kishi da Saade. Wanan abin bayin kan ku bane kai da ita sihiri ne ke aiki akan ku kawai da zaka daure ka saki wanan yarinyar salin alin tun bata cinwa manufanta ba akan ku da zaifi saukin rufin asiri agare ku. Kunga aniya makomiya ke nan amma ina Rahama ina shiga cikin ku , yar tallakawa lis da ita , ni ban taba yarda ba cewa ba sihiri suke a kan ku ba dama. Wani irin abu yaji ya tokare mai makogwaron shi a lokaci guda ya gama fahintar mama tai amfani da lafazin tsofin mata akan Saade taji galaban ta, har kiyyayya ya tsiguru a zuciyar ta na Rama. Take yaji idon shi ya canza launi yana jin kalamin mama kamar saukan aradu azuciyar shi da mama tasan kalaman sakin da take kira yaiwa Rahama yadda yake jin shi a ransa da bata kara furta ko a ba daga haka. Yaya mama zata sa Saade ta mayar dashi mutumin banza mai magana biyu idan da yar tane ko jikan ta akaiwa haka zata ji dadin yin hakan da akai masu. Lokaci daya anty ta fahinci rayuwa mijin ta yai matukar baci yadda mama ke ra fadin mugun kalami a kaina. Ganin halin da yake ciki yasa ta fara tare mama dake ta faman zuba shar kamar ruwan sama. Tace mama don Allah kibar zancen nan haka bai kamata kina fadin haka ba a gaban kowa. Yace No ki barta ta fadi yanzu na fahinci komai dake gudana kuma na gane amma ki sani ke Saade idan wanan yarinyar bata da amanan ki kukai mata haka don tozarci Allah ba zai kyale ki ba. Kin sani bani da ra, ayin karin aure a rayuwa na amma kika sakani gaba da fitina sai da na amince har Allah ya nufa aikai wanan abin. Don haka ba asiri tai muna ba ko dauri tai muna bazan sake taba har abada gara ma ki kwantar da hankalin kafin yarinyar nan ta fahinci sauyin rayuwa a gare ki ki sha kunya ga hakan don mutuncin ki ne zai zube gareta. Ina ilimin ki da imanin ki yau yashiga da har dan lokaci kadan shedan zaici galaba akan ki haka , ? Kin bani kunya Saade kin kuma bani mamaki yau duk tarin sanin Allah ki harki bari shedan ya rude ki wai ke an maki asiri idan halintane yin haka ke kinfi kowa sanin hakan gareta. Don kece ke zama da ita kin san komai na rayuwan ta ba sai wani ya fada maki. Yadda yake magana yasa gaba daya jikin ta yai sanyi nadama abinda tayi yazo mata a lokaci guda hankalinta duk ya daga . Ita kanta mama kunya da wani irin nauyin shi duk ya rufe ta saboda tasan ya gane itace ta zuga anty take hakan. Yafara tafiya yana cewa yau din ba sai gobe ba zan samu su Abba na kuma basu takardan yarinyar nan basai ta tare min a gida ba. Anty najin haka tamike da sauri ta tari gaban shi tana fadin dakata don Allah besty ka bari muyi magana ta fahinta dakai please? Yace maganan may zanyi dake ke kika hada kin kuma ce a,a yanzu basai kowa ya kama kansa ba yafi sauki. Kwata kwata ni dama wanan maganan baya a raina saboda kece nake komai da kikaga inayi din farin cikin ki yanzu ko ya kare ai. Daga haka ya juya ya fice daga part din ta ranshi a bace zuwa nashi part din hasale yake don gaba daya kan shi ya daure ta ko ina ba dadi gare shi gaba daya matan sun sawa kan su bakin kishin yar karamar yarinya a duniya. Amma kuma da yai nisan tunane sai yaga wannan abin duk jerabawan ubangiji ne hakan. Allah kadai yasan hikima da albarkan dake cikin wannan aure da Allah ya nufe shi dayi batare da ya shiryawa hakan ba a rayuwan shi. Ita Saade ya fahinci inda matsala ke taso akan ta zai yi kokari yaga ya magance wanan matsalan kada ta samu raunin imani a rayuwan ta abinda baida kyau zuwa gurin wanin Allah boka ko malam kan neman yayewan bukatan ta. Don yadda ya fahinta ko wani lokaci mama na iya cin galabanta zuwa ire iren irin guraren nan na shirka. Cikin kwanakin nan duk yadda Anty taso su shirya da shi abin yaci tura saboda ya dau zafi da ita sosai. Ya dauki abin da zafi so sai a ranshi har takai ta fara shiga wani yanayi don gaba daya ya tsamany taga duk wanibal, amarin shi ya juya mata baya yana harka da sauran matan shi da yan uwan shi. Ko zancen kai lefe gidan mu ga bakin mama laraba da Aisha ta samu labari hankakinta ya kara dagawa tasamay shi da zancen a falon shi. Yace cikin murmushi eh dole ne nayi taka tsantsan dake yanzu Saade . Don na fahinci sauyin rayuwa a gareki don ban taba tunanen zaki yi rayuwa irin na masu yarda da shirka ba. Yanzu ke da kanki kin sani ke kika kawo zan cen yarinyar nan amna kika bari shedan da mama suka rude ki kan karya bayan kin san komai kece kika hada abinki. Why zakibi rudin shedan ki hau ki zauna idan har wani yaji maganan nan in har yau Rahama na asiri kema tabbas kinayin asiri don kowa a tare ya san ku ai . Nadama ne yazo wa Saade a lokaci daya tabbas ba karya ya fadi ba duk wanda taji maganan nan dole itama za, a ce tare suke wanan halin dubun su ne yacika ita da Rahama din kaikayi ya koma ga mashekiyar ta. Tace don Allah besty kayi hakkuri wallahi mamace duk ta kaini ga haka kan dalilin ta mara tushe . Ni dole inwa Allah godiya tunda na gane gaskiya kafin Rahama ta tare a gidan nan nazo naji kunya. Yace dole ne na jaye don kada nima ki dulmiyar dani kamar yadda ke kika dulmiye kanki. Idan zaki fadawa mama gaskiya don azauna lafiya ki kuma yi istigifari ga Allah ki roki yarinyar mutane gafara. Kuka sosai Anty keyi tana mai nadama aranta tace nasan Allah naso na besty tun da har bai yarda naci galaban ka ba akan hakan. Ka bijirewa bukata bamu taru mun cutawa yar mutane ba bayan tauye mata rayuwan da nayi na hata zabin kan ta kuma nabi bayan ta da kazafi da sheri. Alhalin nasan haka ba halin wanan yarinyar bane da iyayyen ta don haka yau ba sai gobe ba nima zan zauna da mama idan ta gane wala ba, asa idan batagane ba ni dai babu hannuna ga duk abinda zatayi. Tai mashi godiya ta fita zuwa nata sashen sai dare ta samu zama da mama cikin hikima da kuma kawo mata Allah ta ja hankalin mama. Tace mama kin fini sanin halin yarinyar nan mama akan kishi zamu bari shedan ya yaudare mu mu cuci Rahama duk irin halarcin da yarinyar nan tai muna a rayuwan ta . Mama dai ta fahinci gaskiya anty ke fadi dole taji nadama yazo mata bai kamata ba ta bi son rai ba taiwa yar mutane mugun kazafi haka ba. Rahama mutum ce Saade gaskiya nima yanzu nayi nadaman abinda nai mata dole ne na nemi yafiyan wanan yarinyar. Anty tace mama kina ganin yau in bani a gidan nan zaki shigo gidan nan koda da sunan ganin jikokin ne akarbe ki da mutunci ? Amma idan Rahama na gidan nan tankar nice a gidan zaki zo kiyi yadda kika sabayi duk lokacin da kika ga dama ganin su. Kuka mama ta fashe dashi sosai tana nadaman abinda tai min tace gobe zan koma gida ayi komai dani yadda aka saba ba zan yarda har akawo Rahama ba ina gidan nan dole ne naje ayi komai tare da ni. ********* ********* ********* Attu da nake gurin ta sai fanan shiri takeyi a kaina tana kara nusar dani yadda zama da kishiya yake tare da abinda zan wa miji na jan hankali. Sai faman bani wasu jike jike takeyi tare da yi min wankan lalle akai akai tana kuma yi min hayaki da ban san ko na may ye ba ga ruwan rubutu da take faman kin kima min ina sha dare da rana. Kashin rakumi naji tace a samo mata da kanunfari sai tasa na dinga tsugunawa ina hauakin jikina dashi. Da nayi wanan hayakin za anji gaba daya alaura na ya wani ciko min yana min kamar kaikayi ko susa a lokacin. Dutsen tama naji tace a tsinto mata naga ta jika a kwano duk zata dibi wanan ruwan da ta jika duwatsun tama a cikin shi ta hada da garin shasha tau da manta uwa da bita zaizai da shashatau tanika su guri guda tace na shanye su. Ni kaina duk da ba abinci nake ci sosai ba nasan na samu canji sosai a jikina. Ana gobe za, a fara shagalin buki ne naga tashigo dakin bayan magariba take cewa dani da mayafin ki kizo mu shiga nan gidan makwabtan mu. Ban bata lokaci ba muka shiyar muka fita daga gidan gidan makwabcin su malam Musa muka shiga mun samay shi a zauren gidan shi muka gaidashi cikin mutunci. Yace Attu kun iso tace dashi eh malam ga yarinyar nan nazo ma da ita na gaidashi a cikin mutum ci yace da Attu yaya sunan ta tace Rahama take. Yace suna mai ma,ana ga musulunci kiyi amfani da martaban sunan nan naki a gidan mijin ki kikai mashi Rahaman dake cikin sunan ki a gidan shi. Naga mijin naki mutum ne kamili mai addini a yadda nagan shi ga bincike na sai dai yana da murdade hali tare dashi ba matsala bane hakan idan har ka fahinci halinci halin mutum. Babu wani dadin aure dayafi yi bari na bari kaso abinda taje so fiye dashi yan uwan shi su zamo tankar naki da zuciya daya. Abokan zaman ki kada ki bisu da sheri bar mugu yaita mugunta shi idan baka rama ba kaine a kan sa duk abinda yayi sai ya koma mai. Attu tace amma malam ya dace abata tsari wanda zaibi jikin ta don ni ina tsoron matan birni wallahi ba imani ne dasu ba akan kishiya. Malam yai murmushi yace Attu ai shi wanan matsala bawai matan birni ne kawai ba har na kauyen idan Allah ya hada ka da maiyi hakane ke faruwa. Ita hankalinta ba a kwance ba kaima naka da kake tare da ita ba akwance yake ba. Bawani abu zan ma jikan ki ba sai tsari da zan bata tasha shi yanzu anan Allah ya tsare mu baki daya mu dasu. Ya fara binciken wani abu a cikin kayan shi muna kallo yajawo ruwa cikin wani gora ya karkada ya mikowa Attu yace tabani na sha tamika min take na sha da bissimillah a gurin namiko mata dan roban da nasha yace Allah ya tsare ya kare. Muka ansa da amin yace kiyi biyayya ga magabatan ki sai a zauna lafiya dakowa banga wani matsala mai yawa ba ga al, amarin ki sai yawan tarin alherin hakan idan Allah ya yarda. Can ya dauko wani abu yace dani karbi wanan na sa hannu na karba yace murzashi da hannun ki biyu sai ki shafe fuskan ki da shi har zuwa kirjinki. Nadaga hijjabina nayi yadda yace nayi yace Allah yabada zaman lafiya ya bada zuria masu albarka mukace amin. Har zamu mike yace da Attu idan an kai ta kada ta shiga gidan sai ta karanta fatiha da kulhuwallahu falaki da nas kin gasu nan ba karamin abu bane faidar su yafi jin su da mukeyi amma muna sakaci gurin amfani dasu. Mukai mai sallama na dawo gida gurin dana shafa wanan maganin ga kamshi gashi kuma inajin yana shiga jikina kamar wani abu na min yado a jikina lokacin. Haka dai na daure har yazo na daina jin hakan da nake ji. Nai mamaki ganin zarah tazo tare da wasu yan mata course mate din mu da muke dan shiri dasu nasan aikin anty ne hakan. Taro sosai akai masu da yamma sai ga mama Altine tazo tana ra yan kamay kamay bata daiga canjin fuska ga kowa ba don an tare da mutunci yadda aka saba. Can daki inda muke Zarah ce ke faman bamu dariya wai tana min lacture din yadda zan dinga yi na sace zuciyan miji ga sauran kishiyoyi na. Dariya ma take bani take cewa oh dariya ma kike min wallahi ko kishiya daya zaki sama dole ne fa sai kin zage damtsem ki gurin zama karuwan gida karuwan dakin ki. Don Allah ki daure ki fitae da kunya ga idon ki Rahama ki rage wanan halin rashin magana a gavan mijin ki don zai iya cutar dake yin hakan. Samu kayan da kika san na jan ra, ayime ki dinga saka mai idan kuna ku biyu kai bama ku biyu ba nuna masu fa ke kece kawai a wuce gurin. Nafisa tace aiko akwai wasu kaya english wear da suka fito masu kyau na mata su ya dace ki saya da mun isa sai ki basa na sayo maki su wallahi zaki shana sosai a cikin su ga jikin ki zai dauki kaya wallahi. Ba wani buki bane akayi andai yi walima wanda yan uwana su Rukaiyya sunzo kuma sun nuna su nawa ne a gurin kuma an shirya dasu za, a tafi birni gurin kaini idan za, a tafi kaini din . Babu abin da mama lauratu ta harta amna duk abinda akaci akasha sai da muka aika mata dashi. Ba laifi iyayyena sun min gata duk da maigidan yace kada akawo ni da komai mata ya bukata mata kawai za, a kai mai. Amma sai da maigari yaba da kudi akai dubula nakiya da alkaki da sauran abubuwan da ya dace aiwa amare. Su mama laraba da ya uwata biyu sai Aisha da Fatima da wasu mata uku daga dangin su suka zo tare da kayan lefen su. Nan guri ya cika da yan kallo ina daki na shirya cikin jan lafaya da anty taba Zarah tazo dashi cewan ta wai shi zan saka ajikina. Kalar shi kamar ja ko purple gashi nan dai mai kyau da shi da tai makon Zarah na shirya jikina tsab. Basu dade ba sukace a fito masu da amarya zasu tafi don kada yamma ya soma lokacin sai da akaini gidan mu nai masu sallama babana yai min nasiha sosai ma ratsa jiki tare da samin albarka ga aurena. Muka fito muka nufi gurin maigari shida mutanen shi da matan shi suma saka saka min albarka ina kuka aka kama hanya dani zuwa sabon rayuwa agidan da na tsawon rayuwa a cikin shi. Sai fanan tunane nakeyi yadda zamana zai kasance cikin wa yan nan mutanen masu wuyan fahinta. Kaina naduke muna a motar dani da Attu da mama laraba dake zaune a gaba tare da driver da suka zo dashi. Attu ta duko a hankali take ce min na fara adduan da malam ya fada min a raina hakan na soma jero adduoi a cikin zuciya na harda ma wanda malam baice ba duk na dinga yi a raina. Nai mamakin jin cewa wai mun iso garin nan na ci gaba da jero addua gaba na sai faduwa yake faf faf faf duk na rude na rikice. Muna shiga gidan naji daya daga cikin matan ta rangada guda irin mai sunan ruda kishiya. Aiko haka din ne ban yi tsanmani zanga mutane ba cike a gidan sai dana gama addua na fito ne naga ko ina makil da mutane yan uwa da abokan arzikin su sun zo. A hankali ina rike a hannun Attu da mama Altine muka fara tafiya zuwa cikin gidan. Anty tasha kwalliya sosai tafito tare da mutanen ta sai ji nayi ta rungumay ni cikin murna da jin dadi muka kara har ciki da yake idona yana a rufe na dauka a part din anty muke. Dakatawa mukayi daga kofan anty na fadin adakata tayi addua ta shiga da kafar dama. Nagama ta duko a hankali ta rada min Allah ba da hassan da hussaini Nasir ya samu yan uwa. Kuka na saka a hankali tana rike dani har zuwa uwar dakin da yake mallakina ta zaunar dani a bakin gado na zauna da bisimillah a bakina. Gaba sai faman faduwa yakeyi abinda ban sani ba shine ashe tunda aka gyara part din sai wanan lokacin ta shigo gyaran da akaiwa part din yafi duk sauran part din dake gidan kyau tsab an kashe kudi sosai a gurin. Take taji wani kishin hakan ya tokare ta yaya akayi besty ta farawa da iyawa yai masu haka akaina wanan ai kamar rashin adalci ne take gani. Nan dai aka gabatar da abinci ga baki da sukai min rakiya daga kauyen inda yan uwana ne sai yan uwan mahaifina dana Innata su goma sha biyu akazo dasu. Mamaki suke wai yau ni Rahama dake cikin su Allah ya kawo cikin wanan daulan duniya hakan. Aka tsiyaye aka barni da yan uwana da kawaye na duk da haka fuskana yana rufe ban bude ba har lokacin. Naji an fado min a jikina tare da rugumay ni naji yace little mum kika tafi ki kika barni why ? Nasir ne jin muryan shi yasa na bude fuskana a hankali tare da rugumo shi a jikina. Sai ga Amira da gudunta tafada min ajiki tana murna da farin cikin ganina rake cewa mummy tace bazaki kara wuce wa ki barmu ba wai kema yanzu kin zama matar daddy mu. Murmushi nayi na jawota a jikina ina tambayan su kunci abinci Amira tace dani Nasir baya cin komai sai dai yasha drinks har da dukan shi mummy tayi. Nacewa Nafisa ta debo min abinci na basu mama Altine na gefe tana kallon mu nan nafara ba yaron abinci ya ko soma ci a hankali. Ina cikin bashi anty ta shigo dakin da kawayen ta sunzo su gannin suka samu yaran na a jikina ina basu abinci da hannuna a hankali. Wata kecewa ji yaran nan da akayi dasu suci abinci amma sukaki yanzu gasu suna ci a nan. Suka dan yi min nasiha suka fice daga dakin aka barni dasu Attu da mama suma nasiha dai suke min anan zasu kwana sai washe gari zasu tafi. Bayan na bude idone nabi dakin da kallo sai lokacin na fahinci ba part din anty muke ba ke nan nima an bani nawa part din ke nan a gidan ikon Allah yau ni Rahama keda part a wanan mamakeken gidan na Daddy ke nan. Bayan Sallah magariba sai ga mama Laraba ta shigo take cewa na shirya zamu falon maigidan dukkan mu. Bata dade da fita ba sai ga Anty na tashigo take cewa oyya mike maza ki shirya zamu hadu a part din maigidan za, a muna magana a can. Ita da kanta ta shiryani tsab cikin wani lafaya mai launin purple colour ta dauko turare kala kala duk ta feshe min jikina da. Duk wanda ya ji yasan cewa ni amarya ce ga zanen lallen da akaimin ya kara haskani ga kitso da aka yarba min kanana akaina. Bakishiya ba ko natare da kishiya ta ganni sai taji wani abu ya soke ta a ran ta balle kishiya. Gaba daya matan gidan har maigidan duk suna falon shi a zaune tare da su mama Laraba da yan uwan ta da sukaje dauko ni kauyen mu tare zuwan mu kawai ake jira sai gamu mu mun shigo anty tana rike da hannuna fuskana yana a rufe lif kamshin turarena sai daya razana duk wani wanda ke falin lokaci sa kishiya fargaba ke nan. Anty na kokarin zaunar dani saman kujera amma saina zamo kasa saman kafet na zauna. Kowan su kishi ya turniketa sai kada kafa sukeyi cikin takaici da jin haushi nikan duk nasha jinin jikina a lokacin. Ina jin mama ce ta bude taron da addua tare da soma kiran sunan maigidan sai na Saade zulfa sai hindu a karshe. Tace to yau ga Rahama Allah ya kawo ta cikin ku a irin matsayin da kuke kuma a gidan nan watau na matar gidan itama. Don haka kai Alhaji dakai zan soma don Allah don Allah kayi kokari ka kwatan ta adalci a tsakanin iyalin ka haka shine zai kawo maka kwanciyar hankali ga iyalin ka. Kowan su anan zaman ka yau sukeyi babu banbanci a tsakanin su sai har idan kaine ka soma hakan . Don haka kowa ya tsaya a matsayin shi babba ya rike girman shi karami yarike girman shi na karanta kada wata ta shiga hakkin wata a cikin ku. Idan kunyi hakan gidan ku zai zama abin sha, awa gakowa kuma gurin zuwa ga ya uwa. Amma idan har ba zaman lafiya kamar kullun babu wanda zaku gani yana zuwa gurin ku. Don haka kuda yau tazo ta sama a gidan ina mai kara baku hakkuri da ku kara yin hannkuri ga yadda auren yazo a bazata gareku haka Allah ya kaddara akwai aure a tsakanin su dama haka abin yake ga Allah. Da fatan za, a zauna lafiya cikin kwanciyan hankali batare da wani fitina ba duk amana kuke a gurin shi. Hindatu tace Allah yasa haka mama amma ina da magana sai lokacin daddy dake zaune a falon kamar baya ciki yai magana yake cewa ki bari tagama maganan ta mana may ye na gagawa. Tace ai ba zancen gagawa bane sai gaskiya don wallahi bazan lamunci yarinya taimin rashin kunya ba don tana takaman ita wai matar gida ne don ba kunyane fa Rahama sai in wa yarinya dukan tsiya wallahi. Yace tunda ga yarki an kawo maki ko? Zulfa tace kinji ko mama tun baki tashi ba dama nasan indai yaya ne ba wani adalcin da zai shuka anan tunda tun farko yana son Rahama dama. Sai lokacin anty tai magana tace wanan kuma zargine irin naku amma babu soyayya tsakanin su a baya gaskiya kuma kun sani. Don Allah malama ki rufe muna bakin ki munafuka kawai ai duk bakin ku daya badake aka hada baki akai muna hakan ba hallan don a tozarta mu. May ye na tozarci a cikin kara aure ba, a kara aure ku aka auro ku kuka shigo inji anty kowa dai tashi tafisheshi kawai. Nan fitina ya fara kowa na fadawa dan uwa bakaken magana a tsakanin su. Hawaye ne ke zubomin daga cikin mayagin da nake rufe har kaina tun ina yi a boye har yafito fili na kasa boye kukana a gaban su ba kowa yajamin wanan zargin ba sai anty na. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, DON BA A YAFE MAKI BA , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA DON ALLAH YANA GANIN, , 40 Duk yadda anty tayi dani wai na koma part dina na kwana ki nayi nan muka kwana nida su Nasir a dakin da muka saba kwana don sai da na bari anty ta shige na fito na dawo dakin na kwanta. Sai washegari ta gan ni kwance a dakin ko shi cikin kargin hali ta taso gabanin asuba don ta duba lafiyan yaran ta sai kawai ta samay mu kwace tare da yaran duk sun haye min jiki muna barcin mu hankali a kwance dasu. Muryan ta naji da asuba tana tayar dani dan sallah nai mamaki yadda yau nai barci haka har sai da aka tasheni wai kamar nai wani aiki. Na mike zubur ina salati nace anty mun makara yau ko gashi ban hadawa babeis dina abincin makaranta ba. Tace yanzu Rama saida kika kwanta da yaran nan don Allah ban tsaya saurarenta ba na fada ban daki kada na kara makara da sallah. Nafito na fara gabatar da Nafila nakawo asuba nayi na dan dauki lokaci ina addua na mike na nufi kitchen. Ranan faten doya nai masu yaji kayan lanbu sosai da drinks na zuba masu a gorunan su. Na hadawa kowa basket din shi nai masu wanka na shirya su da sauri har na dauko hijjab zan kai su wurin mota sai nayi wani tunane naja na tsaya a sanyaye nace Gajiye don Allah zoki kai su bakin mota. Sai bayan ta tafi ne na soma gyaran dakin naiwa dakin tsab na koma falo na gyara shi tare da saka kamshi dakin anty na shiga na fara gyara har nayi nisa ga gyara motsina ya tayar da ita. Tace Rama may kuma kikeyi nace anty ina gyaran daki ne tace haba mana Rama kinga haka zai yuyu kuma ace kin saura gyara min daki yanzu. Don Allah daga yau ki bari ki je ki shirya Hamza idan ya dawo kai yara zai saukeki makaranta maigidan yace bai yarda ki fita ke kadai ba don wanan mahaukancin sojan bai fita zancen ba har yanzu. Ni kaina saida tsoro ya kamani don na tuna yadda mutanen shi suka dinga farautana a baya. Karasa aikin nayi na wuce dakina na part din anty nai wanka na saka wasu zannuwa da riga na kawo katon hijjab dina na dora sama ban yi wani kwalliya ba irin yadda na saba yi idan zan fita. Na dauki takarduna na nufi dakin anty nan jinior ya lake min wai zai bini da kyat anty tai mai wayo na samu na fice ina mata sai na dawo. Ina fitowa na samu hamza ya na jira na a waje sai muka hade da hindatu ta fito a cikin shirin ta zata fita daga gidan tana ganina ta bini da harara. Na kawar da kaina kamar ban ganta ba har ta doshi motar ta ko may ya faru kuma naji ta kwalawa Hamza driver kira ya je da saurin shi gareta cikin girmamawa. Tace wai so take ya kaita uguwa yanzu yace cikin dan girmawa hajiya don Allah kiyi hakkuri tun jiya da dare Alhaji ya bugo min waya na kai amarya school. Kam kazan uban nan hamza ni zance ka kaini guri kace wai Alhaji yace ka kai mai wata can wani guri ? Ka ko san abinda kake fada min kuwa da bakin ka zakace min wai zaka kai wanan mara mutuncin wani guri ? May kake nufi ko shi Alhajin may yake nufi ko kana nufin ta kaini matsayi ne a gidan ko ta fini ? Ba hakana bane hajiya Alhaji ne ya bani umurnin yin hakan yanzu zan aje ta na dawo don yanzu ya kirani yana min fada wai ban kaita ba tun dazun kada ta makara. To bazaka kai taba sai na gama lalura na ai ya saya mata mota tun tana kwartuwan shi ko ? Hamza dai ya dukar da kai don maganan ya soma fin karfin shi don shi namiji ne ba ruwan shi da zancen kishin matan gida. Yace hajiya sai dai kiyi hakkuri don bazan iya ketare umurnin Alhaji ba na gyara maki naki. Ya juyo ya barta tsaye ta rusawa kowan mu zagi na fitan arziki ni dai na shiga mota yajani muka fice daga gidan. Muna kaiwa naiwa hamza godiya na fada mai six zai dawo ya daukeni daga school din yaja mota bayan yaga shiga na aji don haka aka umurce shi dama dayi sai yaga na shiga aji ya tafi. Na samu har an shiga aji Allah ya taimakeni ba mai tsanani bane lecturar dana samu ya barni na shiga. Bamu samu kan mu ba sai karfe biyu muka fito don yin break da sallah lokacin ne yan course mate dina suka fara yi min murna wai ashe na yi aure shine ban gaiyace su ba ? Murmushi mai kama da yake ne kawai nai masu muka fita da Zarah zuwa inda muka saba zama muyi breakfast da sallah. Min dauki lokaci muna magana wanda ya shafi karatun mu tana min bayani na kuma fahinta sosai da bauanin da taimin ta miko min nawa handout din da ta saya muna da bana nan. Bayan mun fito daga masallaci muka koma class don mu dan kara taba karatu don kada a barni baya. ********* ********* ********* Hamza na hanya yana sauri kiran maigidan ya riske shi tambayan shi yayi ya sauke ni yace eh yace babu wani matsalan komai ko ? Yace babu shi sir sai dai an samu matsala a gida don mun fito zamu tafi hajiya Hindatu tace sai na fara kaita inda zata na fada mata zan kai amarya school amma ta dinga zagina har tana cewa sai tayi sanadin da na bar gidan nan tunda ta gane ni munafuki ne . Don Allah sir a fada mata kaine ka sani yin hakan ba laifina bane don ina gudun kada ta jamin matsala kuma . Hamza dani da Hindatu wake biyan ka albashi ka dani da ita, bayan kayi abinda ya dace kayi kuma zaka bata zancen. Ina sauraren sherin da zata kullama akan hakan idan ta isa ita uwar sheri ce a gidan. Nan ma a gida bayan mun fita hargowan Hindatu ya jawo hankalin mutanen gida Gajiye ce tafita taji abinda ke faruwa shine tq dawo tana fadawa Anty a falon ta. Anty tace waiko matan nan suna da hankakali kuwa wanan ai sallon neman fitina ne tun ba, aje ko ina ba. Nadawo gida a gajiye ban tsaya ko neman abinci ba na shiga na gaida anty tana min sannu da dawo wa. Na juya zan fita tace dani dazu nake jin yadda kukayi da Hindatu da safe da zaki fita. Nace anty ni dai idan hakan zai zama matsala ne na dinga hawa Napep na tafi ko idan za, a sauke yaran sai na shirya mu fita tare. Tace saboda may ai ba tsoron ta aka ji ba ko wanan kuma dokane da umurni daga maigidan ai don haka ki fita batun ta ki kama harkan gaban ki don ba zaman lafiya suke so ba su idan kin biye masu kullun za, a jiku a gidan nan ne. Tace koma side din ki ki gyara ki dan zauna don ki fara sabawa da hakan don in kina zama nan anan kike son maigidan ya dinga samun ki ? Na turo bakina ina dan buga kafana a kasa nace haba anty wani maigida kuma zai dinga samuna kuma ? Tace ke to may kike nufi dama wallahi ki shirya da ya dawo kasan nan amarci zaki fara cur wallahi. Ke zo nan ma ai na manta wallahi barin kina Dr mai gyaran harka tazo ta gyara mashi ke kikoma dalleliya dake kamar ba, a taba shigsn ki ba. Na dago kai da sauri nace wayyo ni anty don Allah dai ki bari please ni wallahi ba wanda ya taba shiga na Allah ko . Ji wanan ko kina mantawa da Garbatin ki ne wai kina manta kin taba aure ko don kin raina da zama da tsohon ko ? Ban son irin maganan na kwasa da sauri nafice daga dakin key na karba hannun gajiye na bude part din kafin magariba na dan share na goge ana kira na fada bandaki nai wanka nafito na tayar da sallah. Na idar sai gasu Nasir suma wanka nai masu don suji dadin barci saboda ana zafi saboda yanayin dama da ya fara a lokacin. Daya daga cikin kayan da Nafisa ta sayo min na saka ajiki muka fita zuwa part din anty bayan na rufo kofana. Muna shiga muka samu anty tana zaune falo jinior yayo kaina wai na dauke shi daukan shi nayi naje nai mashi wanka. Nashirya su tsab na debo abinci tare dasu muka zauna muka ci abinci a tare da su mukai ta shiriritan mu suna kallon mu ita da gajiye. Kayan dake jikina take kallo ya fitar min da suran jikina tsab wani abu taji a ranta da sauri ta nemi tsarivga Allah kada ya nufeta da kishina haka. Amma dai tasan akwai aki a kanta na dan lokaci tunda har ta fara jin yanayin kishi a kaina haka. Mace ce Rama da duk namijin da ya samay ta zai more don akwai abubuwan more rayuwan namiji a tare da yarinyar nan wanda kaf din su babu mai ko kwatankwacin hakan daga cikin su. Ta sani sarai idan besty ta ya gane hakan a kaina ba ita gaba dayan su sun kade wallahi don wanda ke da kamar wanan yaushe zai nemi wani abu gurin wata mace can kuma yana da wanan garshi. Jinior ke ta kokarin wai sai yaban abinci ga baki ina ki nace anty kiwa danki magana fa zan make shi. Sai naji shiru da sauri na dago kaina naga dai a zahiri mu take kallo sai dai da alama tayi zurifi ga tunane ne . Nace Anty bakiji bane sai naji ta sauke ajiyan zuciya tace may kikace ne ? Nace kinha Jinior da wanan hannun nashi wai sai ya saka min abinci a bakina kuma make shi zanyi. Kallo mai kama dana hararan wasa tai min tace kin taba jin mata ta doki mijin ta bayan yana son kuyi soyayya dashi. Bata kaji dama ai kaine angon kai ya dace kana bata abinci har ta koshi kamar yaji yako yi ksina wai sai ya saka min abaki har kasa muka kai sauran yaran sukayo kaina suka tayashi tura min abincin a baki su anty nata muna dariya. Ina cikin dariya naji tace Rama wanan kayan sun matukar karban jikin ki wallahi wanan ai idan angon ki ya ganki haka baza mu gane kan shi ba kuma. Da sauri cikin kunya na daga yaron a jikina na jawo hijjab dina dake gefe ina sakawa tace yau ga tsiya may zaki wani rufe jiki kuma? Bari kiji haka nake so idan besty na gari ki dinga yi mai kwaliya da kaya matsatsu yana jin dadi sosai a ranshi, mune dai bama yi mashi kwalliya yadda yake son gani. Nace anty aiko kina kwalliya mana tundai idan ma kece da girki tace ni har yaushe nake wani duty abin daga bara sai bana. Da dare ta sakani gaba wai dole a part dina zan kwana har da kuka nayi mata amma tai kemaymay sai da taga na shiga ta saka suka rufo part din su suka barni ni kadai a part din. Haka na kwanta ga tsoro ga kuma tunane barkatai da nake ni daya kamar manya har barci ya dauke ni. Da safe mun tashi da wuri kamar jiya hamza driver ne ya dauke ni zuwa school ban dawo sai yama yau biyar na dawo gidan. Na shiga muna zaune da anty a falo muna hira saiga yar aikin Zulfa da gudun ta ta fado part din hankali a tashe take magana. Wai anty tazo uwar dakin ta zata mutu anty tace dani taso mu tafi da sauri muka bi bayan yar aikin zulfa din. Kwance take shamay shamay kamar bats motsi muka karasa inda take kwancen hindatu na tsaye tana waya hankalin ta a kwance. Ban san lokacin dana duka da sauri ba na tallabo hannun ta ba tare dan saurarawa na dan lokaci ta bude idon ta ta sauke a kaina zatai magana na nuna mata da hannu irin na yara da shiii sai tai shiru. Nace da ita rufe idon ki ki dan shaki numfashi a hankali sai ki sauke har sau uku bataki ba tayi abinda nace da ita. Duk suna tsaye suna kallon mu bayan tayi kamar minti daya sai tai wani irin ajiyan zuciya a hankali. Nace jini yana zuba maki ne a kasan ki ? Ina ruwan ki da wanan tambayan kuma inji Hindatu cikin fushi. Kibari mana tayi aikin ta mugani tunda shi take karantawa ai ban bi ta kanta ba na sake maimaita tambaya gare ta. Tace yau da safe dana tashi na danga sign din jini amma ba sosai ba na sa hannuna ta bayan ta nace dago kadsn mu gani please ? Tana dagawa ashe kwance take cikin jini na juya kan su cikin tashin hankali ina fadin yanzu tana cikin wanan halin ita bata san inda take ba ku kuma dake tare da ita baku taimaka mata ba. To Docter yi muna fada na juya gurin anty nace cikin ne a jikin ta kuma yana barazanan fita ne a ko wani lokaci iyanzu. Gaba daya hankalin su ya tashi a dakin zama nayi da kyau har numfsshin tana shiga nawa ina dan shafa mata daidai kugunta a hankali kamar ina mata massage din shi. Hindatu na fadin a kira likita yazo da sauri can kuma tace bani guri na daga ta mu tafi asibiti kawai. Cikin wani murya nace da ita kada ki soma ki daga ta bata a kwance tukun a wurin. Nace anty ta dago ido ta dan kalleni lokacin ne uwarta da yarta suka shigo dakin a gigice suke suma. Nace daure ki dan kara shakan iska irin na dazun kinji ta sake maimaitawa a hankali yadda nace tayi din. Yanzu haka zamu zauna da ita ana wanan shirmay haka ai mu tafi asibiti kawai antyna tace da Hindatu ai wanan ba shirmay take mata ba. Nace idan mun daga ta a haka jini zai iya balle mata ko wani lokaci don akwai abinda tasha wanda ke barazana a cikin nata. Hankalin su ya kara tashi cikin hikima irin na likotoci na samu stress din ya dan lafa mata a hankali numfashin ta ya dawo daidai nace wanda zaiyi tulin ya ja a hankali haka kuma idan zaku dauketa ne ku daga ta a hankali. Sai dai da zakubi tanawa a bari likitan yazo gida ko luma na rubuta magani a sayo ai mata allura. Sai duk sukace adai kira likitan zaifi sun kira likita yace bai samun zuwa adai kawota asibiti na nuna masu yadda zasu kamata zuwa bakin mota. Mama Zulai tajuyo gareni tace don Allah ki taimaka mu tafi dake ina ga zai fi ai na juya gurin anty tace ga hijjab saka ku tafi Allah ya bata lafiya muma gamu nan tafe yanzu. Filo na aza mata na tare jinin yadda maranta ba zai motsa ba ko kadan muna tafe ina mata sannu anty har muka shiga asibitin yatta ke jan motan. Muna shiga na kamata yadda ya dace bamu sha wuya ba nai masu bayanin komai likita na dubata abinda na fadi shiya fada muna nace dashi ga alluran da za, ai mata zaifi sauki tunda da alaman akwai poissing a jikin ta ai. Sai bina suke da kallo yace yaya akayi har akakai wanan lokacin abin bai fita jikin ta ba na fada mai taimakon da aka bata tun agida. Yace good hakan na da kyau gado aka bata tare da mata allurai ta samu barci kuma Alhamdullahi jinin ya bar zuba. Nace da mutane don Allah ayi hakkuri a dan fita daga waje a barta ta dan samu hutu please. Muna fita naji mama Zulai na fadin may Zulfa tasha cikin jikin ta ke son fita ni dai nace dasu mama zan tafi gida Allah ya bata lafiya. Muka juya nida Anty bamu tsaya ba don asibitin ya fara cika da yan uwanta a lokacin sosai. Muna hanya Anty tace dani Rama kikace abu tasha cikin ke son fita nace gaskiya akwai wani abuda tasha ya kawo hakan gareta. Tace dani amma kuma yadda Zulfa ke son ciki haka har ta tsaya shan abu don cikin ta ya zuba kuma ? Wayan maihudan ne ta shigo mata don haka taci gaba dayi mai bayani a kan komai yace gashi nan dawowa ga gobe idan Allah ya kaimu. Tace Allah ya kawo ka lafiya suka kashe wayan nikan a bangarene gabana naji ya fadi ras ras don ban ki ma ace yai ta zama ba acan har abada a lokacin. Sallah da ban samu yi ba nayi tare da jero shafa,i da wuturi gajiya da kasala ke damuna a lokaci guda na samu guri na dan kwanta ashe anty ta shigo ta samu ina barci taja min kofa ta fice dakin. Washe gari na dan makara da sauri na mike nai sallah na jero adduoi na namike na nufi part din Anty. Na samu Gajiye ta hadawa yan makaranta abinci na taimaka muka shirya su nima nakoma na shirya na nufi gurin anty na sallamay ta. Bayan mun gaisa take cewa dani jiya ai nashiga muyi magana na samu kin yi barci nace nima koda na falka naga biyu na dare kuma an rufe min kofana. Tace ki saba da rufe kofan ki Rama gidan nan sai a hankali wai kin san kuwa tun jiya ina tunane akan matsalan Zulfa. Nifa sai nake zargin da wata a kasa fa Rama don a sanina dai Zulfa bazata sha abinda cikin jikin ta zai fita ba wacce ke nema ido rufe Allah ya bata. Allah ya sauwaka nace ina kokarin wucewa naji tace yau dai kin san maigidan zai dawo ina fatan kin shirya taron shi dai ko ? Nace anty wani taro kuma gaku tace may kike nufi wai bani fa son shirmay wallahi kada ki dade ki dawo da wuri ki shirya mai abinci. Fuskanta babu alaman wasa ga maganan ta tace naso kikara shiryawa kafin ya dawo gashi lokaci ya dan kure muna wallahi. Amma dai duk da haka zan san abinda za, ayi akai nima zanyi wanka na tafi asibiti na dubo su can. Idan zaku dawo sai Hamza ya biyo dake ki duba su a can nace to anty na fice abina ban tsaya ba . Tunanen duniya ranan nayi shi kafin mu shiga school sai dai muna zuwa na manta da komai nashiga harkana kawai. Sai Four na kira Hamza driver yazo ya daukeni muka fara zuwa asibiti duba zulfa . Asibitin makil yake da yan uwan ta da ma wasu dangin mijin su gaba daya idanuwan su caa akaina ni dai na gaidasu na shige gurin ta. Ina shiga cikin dakin ma mutane ne na gaidasu tare da karasawa bakin gafon nace sannu anty yaya jikin naki ? Cikin wani ya mutse fuska tace dani da sauki baki shigo ba tun safe sai yanzu ? Nace yanzun ma daga school nake don naji likita yace kina bukatan hutu yasa banzo ba da safe kada na damay ki. Nace jinin dai ya tsaya ko ya daina zuwa kafin ta bani amsa wata yarta tace aniyar maishi tabishi mukan ai Alhamdullahi tunda cikin bai zube ba ai. Shiru nayi mai maganan taci gaba da sake bakaken magana ina tsaye ina sauraren ta harda cewa haihuwa daine sai anga Zulfa nayi shi gida Yusuf kamar ko wace mace don sai tai dozen da yarda Allah. Nace Allah yasa sukace amin mama zulai data shigo take cewa Rahama kece tafe ai tun safe likita ya tambaye ki yace ba karamin taimakawa kikayi tun a gida da cikin ya zube ai. Nace cikin murmushi mama ai ina dubawa nasan magani ne tasha a lokacin idan munce zamu dagata haka zai ba abin dama samun hanya fita shiyasa na hana a dagota na dan yi mata dubara yadda yadace ai mata. Don na sani badon haka ba gaskiya cikin zai fita kuma ta samu matsala ita ma sai dai abin da mamaki don kwayan da tasha mai karfine sosai adai kiyayye gaba don Allah. Zulfa tace dani Rahama ban sha kwaya ba don likitama haka yace dani nace zaki iya tuna abinda kika sha awa daya daya shude ko kafin lokacin? Sai tai shiru tana tunane nace koma may kika sha shine sanafin faruwan wanan abin haka gare ki nai masu sallama ban kai ga fita ba naji wata na fadin au itace ta taimaka a gidan gako Asiya har rana sake mata magana. Zulfa tace yarinyar ta taimakeni ai mama sosai don badon taba gaskiya ban san inda nake ba a lokacin zuwan tane da tabani taimako har na gabe gun da nake a dakin. Gida na nufa na samu har gajiye ta dora girki ina shiga anty tace Gajiye bar mata tayi tunda ta dawo yanzu. Hijjab kawai na cire na juyawa gurinta nace anty may za, a girka ne ta dago tare da tsura min ido tace yau naji ikon Allah ga Rama . Ke da mijinki zaki tsaya tambayana may zaki girka kuma ai dabara ya saura gare ki yanzu. Rugumay ta nayi cikin shagwaba yadda na saba nace don Allah Anty may za, a girka maku please ? Tace kin dai san anty tin tuwo yake so shi don haka sai kiyi yadda ya dace dashi ko abinda kika san zai burge ku. Ni dai jiki ba kuzari na shiga kitchen din tunda tace anything tuwo don haka nai tuwon semo da miyan yauki sai jan miya danayi masu daban na hada zobo mai kauri na saka a fridge na hada ferfesun kifi danye yaji kayan kamshi kafin magariba na hada komai nace da ita na hada. Zan je nayi sallah don gaba daya yanzu ta hanani zama part din ta kamar kullun, amma hakan bai sa na bari ba din. Wanka nayi na dauko wani riga na saka robane rigan zai iya matse mutum daidai size din jikin ka yana da ado a gaban shi sosai na sa na rufo kofa bayan na gama komai na nufi gurin ta. Abinci na samu tana ci tana ganina tace Rama ashe kin iya keta ni dai baki taba min tuwo hakan nan ba duk zaman ki dani. Fada mata nayi a jiki ina dariya nace kai anty ashe kin gane baiyi dadi ba ke nan bake kikace nayi tuwo ba shine niko nai maku shi haka. Tace wai kina nufin keta kikayi dama ko may to wallahi yayi dadi sosai tambayi gajiye kiji leda nawa nacinye yanzu. Gajiye tace wallahi na biyu ke nan take ci tana zuba santi nima dariya kika samu ina mata nace oya Nasir zo ka zauna aci abinci kada kai barci. Yace little mumm kaina ke ciwo a razane na juya gurin anty nace anbashi magani anty ? Tace wa yasani in ba yanzu da yake fada maki ba ke ne dai zaifadawa dama don shi bai yarda da kowa ba ai. Mikewa nayi na shiga daki na dauko magani sam baison shan magani da kyat na samu yasha magani sai mukaji hadari ya taso alaman akwai hadari ana son yin ruwa. Yaron yana lafe a jikina ina lalashin shi sam bamu ji dirin mota ba balle mu san shigowan daddy gidan. Sai ganin shi kawai mukayi a tsakiyan falo suit ne a jikin shi fari da wandon shi ya saka hannun shi daya ga aljihun wandon shi. Besty ashe ka iso yanzu naji hadari nake tunanen ko kana ina haka by this time ? Yace ana magariba na shigo na tafi asibiti ne dubo maijikin . Nan muka shiga gaidashi da dawowa ga kamshin turaren shi duk ya cika muna hanci gavana sai wani mugun faduwa yakeyi faf, faf,faf. Cin yar siririyar murya nace daddy sannu da dawowa kamar wanda baison amsa gaisuwan ya amsa min tare da dago kai ya dube mu ina zaune rashe rashe a saman kafet Nasir ne kwance saman jikina ya lafe bayan ya sha magani. Kallon Nasir yake don bai tare shi yadda ya saba taron shi ba yace da yaron my friend my kuma ya samay ka kai ? Anty tace cikin tabe baki gashi nan ai ga uwar shi yanzu ne ma da yaga ta shigo yake cewa da ita wai kan shi ke ciwo. Da sauri tun bata karasaba yace subbahanallahi tare da nufo inda muke ya rage tsawon shi dukowan da yayi a gabana gurin yaton yasa faduwan gabana ya kara tsanan ta sosai. A hankali nake kokarin gyara wuyan rigan dake a jikina yadda ya dan fado kirjina kusan a fili yake lokacin. Magana yake wa yaton kasa kasa suke maganan su ya mika mai hannu ya dago shi daga jikina tare suka fice daga part din da yaron. Anty ta juyo inda nake tace dani may ye haka kinyi zaune kuma baki tashi ki bishi ko an fada maki haka akewa miji idan ya dawo. Na turo baki gaba idanuwa na atake suka ciko da kwalla nai shiru ban mike ba. Tace bazaki tashi kije ki taimaka mashi da ruwan wanka bane ko may kin yi zaune ana magana da ke. Maimakon in tashi sai na saka kuka mikewa tayi cikin tsuki ta tashi ta fita daga dakin tabi bayan shi. Tana fita gajiye tace dani haba Rahama kada fa kikai iyakar matar nan kin dai san abinda ya dace kiyi amma tana magana kin wani basar da ita ki tashi ki dauki abinci kikai mashi mana. Allah ya taimakeni har na gama jera abincin suna ciki basu fito ba a lokacin na saurin barin falon sai da suka fito ne suka samu na jera abinci na fice daga falon. Tace yaushe har Rama ta kawo abinci ban ji ta ba nan shi dai ya zauna yaci abincin shi suna hira da ita sai dai kafin ya gama ruwa ne da iska mai karfi ke zubawa ga cidan da akeyi. Ban tsaya part din anty ba na koma daki na rufe sai na samu kaina da bin shawaran Zarah na tsarki da ruwan dumin da tace dani tunda rana nake hakan. Sai dana gyara jikina nabi lafiyayyen gadona na haye na kwanta naji ana dukan kofana gabana ya fadi dam. Na mike na nufi kofan anty ne tsaye tace badai wai rufe kofan kikayi ba kuma Rama ? Zan mata aikina kuka sai ta raba ni ta wuce daga ciki ta barni a tsaye kofan dole na juya nabita ciki. Na samu ta zauna saman kujera ta tsura min ido sai kuma ta juya tana bin ko ina da kallo tace ki shirya zan je nazo maki da angon ki yanzu nasan dai ba zai tsaya a nan ba . Nadai fahinci so kike sai ya sai bakinki kamar na ko wace amarya kila zaki daina ja mashi aji haka. Ki tashi ki samu rigan barci mai kyau ki saka ki gyara jikin ki ko ina da kamshi da dakin gaba daya part din ki saka kamshi ta ko ina. Ganin ban da niyar yin abinda ta umurce ni ta shiga bed room dina ta bude kayan ta ciro wani rigan barci mai shara sharan hannaye rigar kamar raga yake ta dauki room fresh da turare ta feshe dakin ko ina rigan ma sai da ta turare kusan kala biyar a jikin shi naga tabi ko ina da kallo sai ta miko min riga wai na saka ajikina. Kallon rigan nayi na kalleta tace shiga maza ki wanka ki tabbatar kin gyara jikin ki tsab kafin na dawo. Yadda tace haka nayi har ma abinda batace ba sai da na gyara ko ina nawa tsab na koma saman gado na kwanta ina jero addua a bakina. Falon daddy ta koma yana zaune don an dauke wutan gari an tayar da gen din gidan zaune yake tana waya Hindatu daga gefen shi zaune. Tana ganin anty ta shigo ta bata rai don bata kai ga maganan daya kawo ta gare shi ba shima dai fuskan shi a daure yake tamau dashi. Guri ta samu ta zauna a gefe tana jiran shi ya karasa wayan da yakeyi. Hindatu na ganin anty ta zauna ta mike tabar falon don tasan bazata iya fadin abin da ya kawo ta ba anty na zaune don sun fara magana dashi aka kira shi ga waya ya dauka. Yana ganin zatafita ya dakatar da wayan yace ina kuma zaki muna maga ai ki zauna ayi da ita tunda itama maganan ya shafe ta ai. Tace ba sai da ita ba don ban tsanmani ita ya shafe ra ba ni dai daya shafa nazo naji kan maganan. Kallon mamaki anty ke masu tana son jin wani magana ne ake akai haka taji yace da ita ke Saade fada mata wai tabayana tazo tanayi wai yau wake da girki a gidan don kwanakin girkin Rahama ya kare ko da nai tafiya. Anty tace haba Hindatu idan munyi haka ai bamuyi masu adalci ba anan yarinyar nan fa ko sau daya bai shiga dakin ta ba tafiya ya kamshi. Yanzu kuma muce bazamu barshi da amaryan shi ba ai bamu yi masu adalci ba gaskiya. Haka dai kika ce mu wa yai muna adalci kuma tasan yana da mata ai ta nace sai da ta aure shi to tashigo tazo ta dandana abin da take son ji gareshi. Ni ba ruwana da wani rashin adalci can mijina nasani nice ko ke tunda zulfa bata gida zamuyi girki yau. Kafin anty tai magana yace da ita to bazakuyi ba in ke baki san Allah ba nina sani bazaki halakani ba na dauki alhakin yarinyar mutane ba. Tace haka kace yace eh na fadi jeki fadawa wanda zaki fadawa tace ban fadawa kowa amma Allah ya saka min sai tafice daga dakin. Yabi bayanta da fadin noses idiot yarinya kullun ita bata bari a zauna lafiya sai ta samo fitinan da akayi. Ganin ranshi a bace ne anty ta mike tana fadin muje na rakaka dakin matar ka ni ina son in kwanta ne dare yayi ga sanyi an soma kasan ba bashi yake bani ba wanan yanayin. Yace ke kuma kamar yaya ki rakani dakin matana itace da girki din yau ne ? Yace wanan matar hauka take ni you are ok for me anan zaki kwana ba ruwana da wata wai amarya can yarinyar da bata masan gaida mutum ba sai kunyan tsiyane ko girman kai waya sanan mata ? Tace kana dai zance malam don Allah tashi ka tafi dare ya soma kada tai barci kaga yau yanayin akwai sanyi sosai a garin. Ya dage da cewa shifa itace zatai girki ganin baida niyan tashi tai fushi tare da kara mikewa tace idan kaga dama sai ka samay ta kai kadai ni kaga tafiya na barci nake ji. Niko a lokacin ma nayi barci a cikin bargo na don yanayin sanyin garin ga kamshin kasa mai dadi na damana yana tashi ko ina a hancin mutane. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ALLAH NAGANI MAI TSORON ALLAH TA KULLAH DA HAKAN DON ALLAH.. IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH NAGANIN CIN AMANAN DA KIKAYI YAR UWA DON ALLAH MUGUJEWA SABON ALLAH MU KOMAI KANKANTAN SHI, , , 41 Tana fita daga falon yabi bayan ta da kallon tausayi kawai yasan duk abinda takeyi na karfin haline takeyi don idanuwan ta ya nuna hakan a yadda ya riga ya fahince ta sosai. Ya mike ya kashe kayan wutan dake aiki a falin dakin shi ya koma ya kara yin wanka yai shafe jikin shi da turare ko ina ya kulle kofan part din ya nufi part dina. Ya fitowa yaji wani sabon iska ya gauraye garin alaman wani hadari aka kara hadawa kuma again ya lumshe idanuwan shi a hankali yake takowa zuwa part din. Ya tura kofan da farko ya dauka rufe kofan yake saida ta murda ne yaji kofan a bude ya sa kai ya shiga wani kamshi da sanyin Ac ya ziyarce shi a lokaci guda zuwa yayi ya kashe AC da ke aiki a falon. Yabi ko ina da kallo tsab part din yake yace a ranshi wanan yarinyar badai tsabta ba kan Allah yasa ta dore a haka kada tazo ta zama irin su zulfa daga baya da kazanta. Bedroom din ya nufa bayan ya rufe kofan part din ya tura a hankali can ya hangoni saman gado na dunkule a guri daya duk da cikin bargo nake amma yanayin kwanciyana ya nuna ina jin sanyi a lokacin. A hankali ya tako har zuwa bakin gadon barci nake hankalina a kwance ya sa hannu ya yaye bargon dana rufa a jikina a hankali. Rigar da na saka ajikina sunan riga ne don gaba daya part din jikina a baiyyane suke a fili daga cikin rigan . Ga gashin kaina da wankewa nayi na daure a bayana da bakin ribon ya dan zubo a saman fuskana ya rufe min fuskana. A hankali yasa hannun shi yana yaye suman da ya rufo a fuskana yana mamaki ashe haka nake da gashi dama ? A hankali cikin barcina naji kamar mutum na tabani na bude idanuwa na da sukai nauyi don barci naga daddy ne a kaina. Cikin zabura da tsoro karara a fuskana na dago ina fadin daddy ? Ya sa hannun shi abaki kamar maiba yaro umurni da yai shiru yace shiii na shiru amma ban fasa yun kurin tashi zaunen da nake kokarin yi ba. Kafin nakai zaune sai naji ya hadeni da jikin shi a hankali ya manne ni yana sauke wani irin numfashi shi kamar wanda ke hamdallah a ran shi. Banyi wani yunkurin kwatar kaina ba don nasan yau ma kwatana gareshi sai Allah kawai. Mun dan dauki lokaci yana matse dani a jikin shi yana faman sauke ajiyan zuciya a hankali. Naji maganan shi mai kama da rada daidai saitin kunnuwa na yana fadin. Allah na gode ma daka cika min buri na akan wanan baiwan naka, Allah nagode ma da kai min mafita akan bukatana cikin sauki da kwanciyar hankali, Allah na gode ma da ka yi mu maurata a tsakanin mu. A hankali na fara sake mai kuka ina mamakin lafazin da daddy ke fadi haka a kaina yau. Ke nan daddy na nufin dama yana sonane ko may maganan shi haka yake nufi wai ? Jin ina kuka yakara matse ni a jikin shi kamar wani zai kwace mashi nine a lokacin. Naji yace Rahama kuka why kike kuka maimakon ki tayani fadin cikin da Allah ya nuna muna haka a rayuwan mu. Kada kiyi kuka akaina please please kada ki bata min mood dina da bakin ciki bana son nayi tuntube da bakin ciki daga yanzu har wayewan gari akan komai please don Allah ki daina kukan nan idan ba so kike nima nayi kuka ba. Ina jin kalaman shi yasa na dan tsagaita kukana a hankali yace dani good girl ki tashi ki dauro alwala ina jiran ki yanzu. Na mike da kyat ina laluben zani na yace no ki tafi a haka nake son ganin ki Rahama ga hasken fitilar dakin daya kunna duk ya gauraye dakin da haske ko ina. Ina dan tattara rigan na shiga bandakin nai alwala sai na kara dan shafa turaren da malam musa yabani na fito na feshe jikina da wasu masu kamshi duk yana zaune yana kallona a bakin gado. Kunya kamar ya kasheni nakeji shi ya jagorance mu mukai sallah nafila raka, a hudu ya juyo inda nake zaune ta dafa tsakiyan kaina ya shiga jera adduoin neman muna tsari da zaman lafiya da albarkan aure mai dorewa akan mu. Yana gamawa ya daukeni cak sai saman gado ya dire ni idanuwa na suna a rufe sai tsoro da mamakin daddy yau na keyi kawai a raina. Ban ankara ba sai da naji hannuwan shi sun sauka a saman kirji suna wani aiki a hankali da ya sa na tuno da irin abinda marigayi garbati yakan min kafin ciwo yai tsanani a kan shi. A hankali na runtse idanuwana ina jin wani bakon yanayi wanda ban taba jin irin shi ba ko a wancan lokacin yana shigana. Sannu a hankali ya ke aiwatar da sakon shi a kaina sai jin bakin shi nayi kafe a kirjina kaman dan karamin yaro ya samu abincin sa a jikin uwar shi. Wanan yanayin ne yasa na dan fara sakin wani nishi da ban san yana fitowa daga bakina ba a lokacin. Hakan bai mai ba sai saukan hannuwan shi da naji a kasa na ya sa na wani bankaro kirjina a gaba cikin rashin sani wanda shi a gurin shi hakan yai mashi dadi sosai. Ban san lokacin da hannuwana ya sauka a saman tsakinyan kan shi ba na rike da hannuna da karfi ina kiran sunan shi a cikin wani bakon yanayi ina fadi please daddy. A hankali naji ya zamay zuwa kasa na daga haka hankali na yai nisa ban taba zuwa duniyan da na tafi ba a lokacin . Bakajin komai a dakin sai nishi da karan naurorin wutan dake aiki don bada karin sanyi a dakin. Ina kan kamay a jikin shi banyi aune ba sai jin abu mai zafi yana ratsa kasa, na nayi ban san lokacin da na sake wani kara ba da karfi ama ina babu mai ceto don ban ma tsan mani daddy kamar yana jin wanan ihun da rokon shi da na keyi ba a lokacin. Tun ina roko har na daina sai kiran Allah da neman agaji da nakeyi gare shi. Sai da ya gama biyan bukatanshi niko dadin danaji farko ya koma min wahala ban masan inda nake ba don ko motsin kwarai ban iya yi a lokacin. Can naji yace subbahanallahi yana sauke numfashi daga gefe na yace Rahama its means you are still virgin ? Sai lokacin wani kuka mai karfi yazo min na dan kokarta na jawo gefen bargon dake yashe a kasa ina kokarin saya jikina dashi amma na kasa yin hakan. Zaune daddy ya mike duk ya rikice ya rude bathroom ya nufa ya dauki lokaci a ciki ya fito tare da daga ni cak zuwa babdakin ruwa ne masu zafi ya tara a ciki bai tsaya saurarona ba ta tsundumani ciki sai dana yanka wani irin ihu lokaci daya. Bai saurara min ba ya kara danna ni cikin ruwan tare da ware min kafafuwana tun inajin zafin ruwan har nakoma jin dafin shi na fara lumshe idanuwa na. Ban san ya fita ba don idona da suke a rufe sai da naga ya dawo bandakin muryan shi naji yana fadin ki fito hakana don dare yayi sosai ki kwanta. Kunya ya rufeni sosai ban ko san yadda zan fito din ba gashi ya tsare ni da ido yace kifita sai kiyi wankan tsarki kizo ki kwanta daga haka ya juya ya fice ya barni da kyat na iya watsa ruwan nai wanka na tsarkake kaina sai dai kuma ba zani don suna daki na barsu sai na leko in koma don yana tsaye yana sallah yana sujada nafito da sauri na bude wardrobe najawo zanin dake kusa na daura na ciro wani rigan barci na feshe shi da turare na saka ajikina. A hankali nake takawa don duk tako daya har cikin raina nake jin zafi na shiga na alokacin. Can karshen gado na koma na makure kamar maijin tsoro tun ina jin dogon suran da yake jerowa har barci ya daukeni ban sani ba. Can cikin barci naji motsin shi ya hawo gadon ya rugumay ni tsam a jikin shi yana sauke numfashi. Adduan kwanciya naji yana min yana tofawa kamar yadda nakewa su Nadir sai gashi yau ni akewa hakan kuma. Daga haka ban falka ba sai can muryan shi naji yana fadin subbanallahi haka tasani bude idanuwa na sai hasken ranan daya hasko labulen dakin ne ya kashe min ido na. Da sauri naga ya mike tsaye rigan shi ya dauka ya zura ajikin shi tare da saka wandon boxes na maza da suke agefe da sauri ya fara tafiya ya nufi hanya fita part din nawa yana fadin tashi kiyi sallah mun makara wallahi daga haka ya fice daga dakin da sauri. Na yunkura da kyat namike sai dai tashi ya gagareni da kyat na rarafa nakai kaina bandaki na fara wanka ko jikin nawa zai sake na dauro alwala nafito. Na idar da sallah na jingina kaina da gado take wasu hawaye suka gangaro min a hankali abinda ya faru daren jiya ya fara dawo min araina tiryan tiryan. Na jinke idanuwa na ina mainadama nace yauni Rahama na zamo babban yar cin amana yau minjin antyna nane nai wanan taraiya dashi haka daren jiya. Kuka sosai nayi a gurin sannu a hankali nake jin wani matsanacin zazzabi yana shigana a hankali na kai kwance a gurin na dukule da kyar na mike nakoma saman gadon na rufe jikina da bargo. Shiko daddy yana fita Hindatu ce yagani tsaye a kofan shiga Part din shi tana ganin shi tabishi da kallon mamaki har yakaraso ya sa key ya bude ya shiga tana kokarin cinno kai ya maida kofa ya rufe shima wanka yayi yai alwala yai sallah. Ya dade zaune yana adduoin neman Rahama agurin ubangiji da jero sauran bukatocin ga Allah. Yamike zuwa karfe tara ya shirya cikin tufafin shi na alfarma ya nufi hanyan part din anty na. Anty na zaune a dakin ta gaban mirro tana gyaran jikin ta ya shigo dakin bakin mirron ya samu ya dan yi masuguni akai. Ta dan dago kai sau daya ta kalleshi taci gaba da abinda takeyi batare da tai mashi magana ba. Wani irin kwarjini da kyau taga ya kara mata wanda bata taba gani ba gareshi. Sai shafa manta takeyi kaman bata san yana tsaye agun ba shi kuma ya tsaya ya kura mata ido kawai yana kallon yadda kishi ya bsiyana mata karara a fuskanta. Taci gaba da abinda takeyi zuciyar ta sai turirin kishi yakeyi yau besty din tane don ya kwana da Rama har yakai kusan goma na safe bai fito ba saubiyu tana tura Gajiye ta dubo ni amma tace ba, a bude kofan ba har lokacin. Jin alaman ita yake kallo bai kuma mata magana ba yasa ta kokarin mikewa tsaye sai ya tare ta da hannayen shi. Tana dago idanuwan ta ta sauke akan shi hawaye ne tab a idon nata bai iya mata magana ba sai binta da kallon da yati yana kokarin su hada idanuwan su amma taki yarda su hakan da ita. Yace No, No Saade kada muyi haka dake kefa kika sani yin hakan bada son raina ba da kika san baki shirya jure ma hakan ba may yasa kika tursasa kan ki dani akayi ? Tace amma besty don naba go ahead kayi shine har tau kaine dakai rana gun wata mace haka kuma a dakin ta. Ni nace ayi amma bance a zalunci wani ba ai yace da sauri subbahanallahi Saade may nai maki na zalunci anan kuma ? Maimakon ta bashi amsa sai kawai ta saka mai kuka sosai take ya gigice ya rasa inda zai saka kan shi. Yaki jin yaga ana kuka kukan kuma wai shine yai zalunci akace duk da yasan shi baiyi ba tunda akan kaidan haka yake. Yace tunda abin ya zama haka yau din nan zan saki yarinyar nan kowa ma ya huta nagaji ban son sabon fitina a rayuwa na kece dama kika kaini ga hakan ai. Shima yasan yadai fadine kawai a fatan bakin shi amma yau ko duniya suka taru akan shi ai ba zai taba gigin sakin Rahama ba irin baiwa da niimar da Allah ya tarawa wanan yarinyar ace kuma wai ya sake ta ina ko a mafalki balle a fili. Ya juya kamar gaske zai fita tai saurin tare shi tana cewa dashi nifa bawai kishi nake akan Rama ba gani nayi kamar ka dan zake da yawa kada ace nice ke marama baya kanawa wasu hakan. Yace zakewan may zanyi akan wanan karamar yarinyar inba aure mukkadari ba aini kin isheni a rayuwana Saade. Ya juya bayan ya gama magana zai fita tace please besty kada ka fara ka aikatawa Rama haka ko bayan raina please don ba ta da laifi ko kadan ga hakan. Yace amma kin san da haka kike korin kirana dan cin amana nine zanci amanaki ko wanan yarinyar da kika raina da kanki kika bata tarbi da hannun ki. Kin san ko rantsuwa nayi babu yadda za, ayi naci amanan ki kan halarci da kikai muna balle wanan yarinyar dake matukar tsoron ki da jin kunyan ki tai maki rashin mutunci. Rahama bazata taba cin amanan ki ba Saade don haka don samun zaman lafiya a gare mu ki bari na sallamay ta yau kowa ya huta. Har yakai kofa ya juyo yana cewa da ita, idan zaki samu lokaci kije ki duba ta ki gani don ban tunanen ta taba sanin namiji a rayuwan ta. Yana fadin haka ya fice daga part din ran shi a bace har ya kai kofa daidai mahadar da ya raba nawa da na anty yaji kaman ya shiga wuri na ya duba lafiya na amma kuma sai yai gudun zuciyan Anty don yasan zata iya fitowa zuwa gurina anytime. Haka ya daure ya juya yabar gidan zuwa asibiti dubo jikin Zulfa, dake kwance tana bedrest don a samu cikin jikinta ya zauna mata. Yafita da kaman minti biyar ta gama shiri tana jin zuciyar ta na bata shawara kamar kada taje dubani da sauri wani zuciya ya gargade ta da cewa haba Saade idan kinyi haka kinwa yarinyar nan butulci ke fa kika kaita ga hakan. Take tai istigifar ta mike da sauri ta nufi dakin daga falon tsab yake kamar yadda ta barshi a daren jiya kafinta fita. Ta tura kofan dakin ta shiga idonta a saman gadon dake a hargitse da gani ansha harka a saman gadon daren jiya. Take ta runtse idanuwanta ta maida idon ta inda nake kwance na dunkule a cikin bargo ta tako a hankali zuwa inda nake kwance din. Ta dan dade tsaye a kaina can ta mika hannun ta ta yaye bargon a hankali sai na kare dunkulewa don sanyin da naji ya dan bugi jikina don zazzabin dake damuna sosai. A hankali takai hannunta saman wuya na ta taba don jin yanayi na, zafi taji jikin yai min radau ya gashe sosai. Jin an taba min wuya yasa na dan bude idanuwa na da kyat naganta tsaye a kaina dishi dishi nake ganin ta tsaye a kaina. Take gabanta ya fadi ta zauna gaf dani tace Rama baki da lafiya ne kai kawai na iya kada mata alaman eh. May ke damun ki haka ne ? Na bude bakina da kyat da zuman nai mata magana amma sai na kasa sai kukan da yazo min cikin ban tausayi nake kukan. Karasa yaye bargon tayi idonta ya sauka ga abinda ke a zanin gadon take taji gabanta yai wani mugun faduwa tace. Rama yaya akai haka dama ke you are still a virgin ? Rama dama ba abinda ya taba shiga tsakanin ki haka da garbati ne har ya rasu bai taba kusan taki bane ? Hannunta na riko ina girgiza mata kai a cikin kuka na fada jikin ta jikina sai kaduwa yake min. Hankalinta yai matukar tashi sosai tace amma may yasa daddy ya san haka kuma bai biki a sannu ba ya aikata maki haka ? Mikewa tayi ta shiga bathroom ta hada ruwa mai matukar zafi sosai tazo ta kamani da kyat na tashi muka shiga bathroom din da ita. Ranan ba kunya ko kadan na tufe tana ganin irin surar da Allah yai min, ta rintse idanuwan ta tasa sukan ai sun kade ke nan. Ta tausani a ruwan na zabura da sauri tace daure ki zauna please wanan shine mafita a gare ki. Haka na daure na zauna cikin ruwan zafin na shiga ina dan raki tana jin wani kuna a zucuyar ta har cikin ran ta.. Da taimakon ta na fito na har na saka kaya a jikina muka fice daga part din zuwa nata sashen. Tea mai kauri da zafi ta hado min ta kawo min saida ta tabbatar da na sha sosai tace na kwanta kafin a kawo min magani. Nan na kwata saman gadon ta sai barci mai nauyi yai gaba dani duk da na ji dadin jikina sosai dan ruwan zafin da ta gasa ni da shi. Falo ta koma ta zauna a cikin damuwa tana jin ranta gaba daya babu dadi sam tana jin rashin jin dadi aranta sai take gani batayi min adalci ba sam a rayuwana. Ta dauki tsawon lokaci a zaune ita kadai ganin da Gajiye tai mata a cikin damuwa ne yasa ta fito har inda take tana tambayan ta hajiya lafiya dai ko ? Ajiyan zuciya ta sauke tana cewa bari kedai gajiye nayi abinda ya koma min ciki ne wallahi. Gajiye ashe Rama sunan ta taba aure ne amma ba abinda ya taba shiga tsakanin ta da mijin ta duk tsawon dadewan da tayi agidan har kusan shekara biyu da aure amma miji bai taba sanin ta ya mace ba wai. Ikon Allah hajiya yanzu dama Rahama a matsayin budurwa take ashe ? Haba shiyasa sam ita namiji baya gabanta ko kadan hajiya wanan aure yarinyar nan ta sadaukar da rayuwan ta ne saboda ke haka ma iyayyenta don kine suka amin ta da hakan ai . Yanzu babu abinda za, ace sai dai ace Allah ya baku hakkurin zama a tsakanin ku ya kawar da sgedan da shedanu a kan ku. Don sha, ani na kishi sai ankai zuciya nesa kinyi na mijin kokarisosai gurin sadaukar da rayuwan ki akan hakan da kikayi wanda ko a zamanin da can baya ba kowa ne zai iya wanan sadaukar da ran ba balle yanzu da ba tabbas ga dan adam ko kadan sai wanda Allah yaba ikon rikon amana. Yanzu gajiye kije ki hada mata ferfesun mai kyau yaji yaji sosai idan ta tashi sai tasha. Amma ki duba min idan motar maigidan na gida nai mai magana ya samo mata magani tasha. Gajiye tace to hajiya ta juya ta nufi duba maigidan idan yana gida lokacin. Ta dawa tana fafin wai baya nan inji maigadi bsi shigo ba tunda ya fita dazun da safe. Taja tsuki tana mai jin haushi da takaicin daddy a ranta don yau yai matikar bata mata ranta sosai wallahi. Tace kai namiji dai baida kunya wallahi wai besty ta ne ya samu mace haka har yai mata wanan illar haka. Shine wai har yake ikirarin shi zai sallami ysrinyar mutane azauna lafiya, ko a hakan ne zai sallamayta din oho ? Kiran layin shi tayi amma sai aka nuna mata wayan is swichup a lokacin tsaki taja don tasan ba dabiar shi bane kashewa haka na. Dole ta hakkura hakanan ta kyale shi sai dai tana mai jin tsananin zafin shi a ranta har lokacin. Tanayi tana shiga daki tana dan dubani a kai akai sai ta samu barci nake a cikin wahala da ban tausayi. Bayan karfe biyu ne ya shigo gidan sai dai ya tsunci kan shi da kasa zuwa gurin besty din shi yau don yasan tana a cikin fushi dashi. Itama Hindatu ta dau zafi dashi tunda taga ya fito part din amarya a can ya kwana. Bayan ta tabbatar da babu wace ya taba zuwa kwana a wurin ta duk cikin su uku din. Amma sai gashi yau wai shine da kan shi ya buge da zuwa dakin mace kwana har yana makara da tashi barcin safe a dakin. Hakan yasa ta dau zafi da shi ga mamakin shi da ta wuni dashi a ranta na yau ina wanan miskilanci da fadin rai daukan aji na maigidan na su ya shiga. Na miji ka barshi kawai inda ka ganshi don ba dan goyo bane da wanine ya fada mata cewa mijin nasu zai iya aikata hakan bada idon ta ta gani ba sai ta rantse tace sam ba zaiyi hakan ba. Yana shiga falon ya zube a saman dogon kujera dake falon ya maida kanshi bayan kujeran ya dan kara tare da lumshe idanuwan shi a hankali. Babu abinda ke mai yawo a kwakwalwan shi sai abinda ya wakana a tsakanin shi da Rahama don bai taba zato ko tsanmanin abinda ya tarar gareta ba a daren jiyan. Ada idan ance mai, mata wata tafi wata zai ce karya ne sai dai kawai su ban banta a halaiyya amma ba ga irin gara basan da ya halbo ba a daren jiya ga jikin Rahama. Abubuwan da suka wakana har yasa shi sakin magana da baima san yanayi ba a lokacin sai yanzu ne yake tuna abinda yake fadi. Bai san lokacin da ya dan saki murmushi ba da ba kowa ne ke gane yana yi ba sai wanda ya fahince shi kawai. Yana a haka idanuwan shi a lumshe ne Anty saade ta shigo falon nashi jin motsin a shigo ne yasa shi dago kai yana kallon ta. Fuskanta ba yabo ba fallasa a cikin sa kara daure fuskan shi yayi don ta san har lokacin yana a cikin fushi da ita. Tace cikin murya mai rauni ka dawo ashe nakirs wayan ka har sau biyu na samu yana a kashe. Yace eh nina kashe don ban son yawan magana saboda raina a bace yake yau don kin kara bata min rai sosai wallahi. Don may zaki sani nayi abu ki dawo kuma kina kokarin bata min rai bayan kin san a kan ki nai wanan auren bawai ra, ayina bane hakan. Namiji tace a ranta jifa kamar ba shine ya halaka yar mutane ba haka kaca kaca babu ko tausayawa ga yanin da ya samay ta ciki. Amma a fili cewa tayi ni wanan ya wuce a gurina kaima kasan cewa dole na ji kishi tunda nima mutum ce amma ba wai yadda kake nufi ba har ka dauki abin da zafi haka ba. Yace dole ne na dauka don naga kina son raina min wayyo na akan abinda ke da bakinki kika tursasa ni yin shi bawai nai ra, ayin hakan ba a raina. Tace ni ba wanan ba yarinyar nan fa ina ganin sai ka dauko mata likita ya dubata don tana matukar jin jiki sosai wallahi. Ya dan yi kamar ya tsorata sai kuma yai sauri jawo natsuwa ya sa a ran shi cikin daure fuska yace may ke damun ta kuma ? Tace ai kaima kasan Rama she is still a virgin ashe babu abinda ya taba shiga tsakanin ta da tsohon mijin ta har ta rasu. Don tunda akai kaita gidan dama mutumin baida lafiya har Allah yai mai rasuwa tai wanka shine ta dawo gida daga nan bata dade ba ta dawo nan gurin mu da zama. Shine kai kuma babu tausayawa besty kai mata wanan aika aikan haka dagani don ban son Rama da raki haka ba ka bata wuya ne sosai besty ? Maganan ta ya dan sashi yin murmushin da baita shi yi ba a hankali yace hakan kuma nayi laifi ke nan ko ? Tace cikin dan jefa mai harara kayi mana don baka rragawa kaunata ba gaskiya. Yace to kuyi min afuwan please don dama kin san sai hakan ai ya faru komai dadewa a kanta. Yanzu ma idan da wanine ashe haka zaki bi shi har gidan kiyi mashi wanan masifan an taba maki yar uwa ko ? Maganan shi da yace ai mashi afuwan yasa taji dadi a ranta taga ya girmamata yana shakkan ta ta manta da waye namiji ? Nan dai ta kara tuna mai yaje ya duba halin da nake ciki mana, halin su na maza yai mata yace haba ba sai na tafi ba . Bari dai na dauko likita a duba maki ita kawai ansan maganin da za,a sayo mata tasha. Sun dan yi hira akan ciwon Zulfa yace yana son ta dawo gida ne yaji dalilinta na son zubar mai da cikin dake a jikin ta. Anty tace amna ni sai nake ganin yadda Zulfa ke son haihuwa har zata iya tsayawa zubar da cikin dake jikin ta akwai dai sai dai kabi a bin a sannu don a gane gaskiya. Ya fice gidan cikin zuciyar shi fam da tunanen halinda ya jefani ciki yasan harga Allah bai raga min ba ko kadan ga shi ji yake a ran shi kamar ace ko a lokacin ma ya sake kasancewa dani baiki hakan ba shi kan, amma ina ba daman yin hakan kuma gareshi. Yarinya haka sai zuma da tsuma mutum shikan bai ma san irin bakin da zaiyi godiya ga Allah daya azurtashi da wanan baiwar na mace mai ni,ima da gamsarwa irin haka ba. Don jin shi yake kamar a daren jiya ya fara sanin mace a rayuwan shi gaba daya gaskiya ba laifi. Ba zai iya dauko namiji likita ba don kada ya kalle mai matar shi don haduwan jiya kawai yake jin wani irin kishin yarinyar yakeyi yana fisgan shi sosai a ranshi. Dole ne ya sa kawai yanzu zai iya barin tana fita zuwa school amma zai saka dole ta sa manyan hijjab a jikin ta don rufe wanan manyattacen suran nata da zai iya jawo hankalin wasu maza a kan ta. Dole ne wanan mayen sojan ya rude akan ta haka yasan abinda ya gano gareta ashe. Shine Ibrahim don baida hankali zai cuno kan shi gurin daba kayan shi wanan ai sai manya ba yara ba. Shi kadai ke tafe a motar shi yake ta faman tunanen zuci kala kala har yaje gun doctor zainab. Doctor zainab tasan kan ala,amarin mata sosai haka yasa ya yanke shawaran , zuwa gurin ta yai mata dan bayani sama sama. Tare suka zo gidan sai gasu falon anty tare da shi sun gaisa anty ta kai ta dakin inda nake ina jin an yane bargon jikina na tashi a zabure dani. Ganin su nayi su uku a kaina dan mikewa zaune nayi a hankali nake gaida su. Likitan ta fara tambayana ko may nake ji cikun kunua nake dan mata bayani itace ke bina da tambayoyi irin na likitoci. Na kasa fada mata sai anty ne ta danyi mata bayani yadda zata fahinci abinda ke damuna lokacin. Nan dai tace a, a kace min kai, kai laifi mana ka tsaya kana min kwanaye kwanaye magani harda na allurai ta rubuta min ta bashi ya fita sayowa. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE IDAN KIN KARANTA MUN BARKI GA ALLAH DON YANA GANIN KI, , , , IDAN KIN BIYA KIKA SHIGO KINA TURAWA WASU ALLAH ZAI BI MIN HAKKINA AKAN KI YAR UWA DON KINYI HA,INCI ALLAH NA GANIN KI SHI ZAI SAKA MIN, , , 42 Allurai da magani likta ta bani nasha sai jikin ya kara sake min sosai har na dan zauna don naci abinci. Ban iya ci ba na dai sha ferfesun sosai don yai min dadi a bakina yaran da suka dawo suka zauna suka tayani sha suna min hira. Falo muka dawo muka zauna har anty sai dai sam na kasa koda hada ido da anty a ranan gashi sai yawan jana da hira take yi. Amma na kasa sakin jiki da ita sosai kunya da nauyin ta nake ji gashi sai nake ganin tana bina da kallon kamar tausayi ne ko mamaki. Har dare muka idar da sallah da yaran muna zaune a falo ta shigo falon ta zauna take cewa dani ki koma part dinki don tunda safe na sa Gajiye ta gyara maki shi. Nace cikin sanyin murya anty ni da su Nasir zan kwana nan tace dani kina hauka ne halan ? Shi mijin naki idan kin kwana anan dawa kike son ya kwana yau sai fa kin kwana hudu kina girki a gidan nan kafin wata ta karbi girki a gurin ki. Raina na bata tare da dukar da kaina kasa na rasa may ke min dadi a lokacin. Daddy ne ya shigo falon yana saye da farar Jallabiyar maza wanda hakan halin shi ne duk dare zaka ganshi cikin shigar jallabiya ne hakan yana nuna alaman bazai sake fita ba a ranan sai safe kuma. Nan aka shiga gaidashi kaina yana sadde a kasa nace a hankali ina wuni ya amsa da lafiya ya jikin naki ? Taji sauki ai inji anty gata nan muna fadawa wai ita gun su Nasir zata kwana don hauka irin na Rama. Yace idan nan take son kwanciya da su abarta mana ai duk daya ne ko danan da can din . Wallahi ni bazata kwana min a daki ba tunda tana da nata bangaren don may zan badi na shiga hakkin ku na sani na take sanin. Maganan anty yai matukar bani mamaki sosai a raina na mike tsam tare da cire Nasir da yai barci a jikina na kaishi daki na kwantar ban ko yi mata sai da safe ba na fice daga part din nata. Ina shiga na samu an gyara komai neat ba kamar yadda na barshi ba da safe. Ina shiga daki na shiga wanka na gyara jikina don ruwa masu zafi na zuba a jikin nawa don naji dadi kwanciya. Na zauna na shafa mai masu kamshi tare da fesa turare na bude wardrove na dauko wani rigan barci mai laushi dogone har kasa sai dai kamar ba asa komai ba ajiki yake. Na hau gadon na fara jero adduoin kwanciya nagama na shafa tare da jan abin rufa na rufe jikina. Ban dade da kwanciya ba daddy ya shigo dakin inda yake bin ko ina da kallo har ya kawo bakin side drower din gado daidai saitin da kaina yake ya dan zauna akai. Murmushi naji ya dan sake yace nasan idon ki biyu ba barci kikayi ba yanzu ko duk fushin ne don anty ki tace bazaki kwana a gurin ta ba ? Saade tasan gaskiya ne shiyasa tai maki haka don tasan abinda nake bukata a raina. Nasan nayi laifi, saidai, ban taba tsanmanin cewa daraja da kimar ki na diya mace yana tare da ke ba har wanan lokacin. Yanzu ita antyn naki ke cewa dani dolene ta kara min farshin ki akaina don ita kanta batasan haka kike ba har yanzu. Ko batace ba ni kaina na yaci nai wanan kyautar don haka a shirye nake ga ko nawa zata kara min don ba zai min yawa ba sai dai ma kadan da zai min. Babu daraja da kimar da yafi miji ya samu matar shi a cikin darajan ta da Allah ya halicceta dashi . Zaman ki a kauye har zuwa wanan lokacin da kika shiga babban makaranta amma kina rike da darajan ki na ya mace har wanan lokacin. Hakan na nuna cewa idan mace tai saa da takai wanan darajan dakin mijinta haka na nuna cewa akwai ginuwar tubalin rayuwan da zai kai ga shafuwan "ya"yan da zasu haifa gurin su samu rayuwa inganttaciya da yadace da su. Bawai nayi maki hakan bane a cikin sani na Rahama zance dake kamar bakon al, amarin nake don anty kima a haka na samay ta da mutuncin ta sai dai a lokacin ban malaki hakalin da zan san darajan wanan baiwan ba. Kin ga ai banda laifi ga hakan idan kin yi la,akari da irin rayuwan da nake ciki ya kamata ku tausaya min hakana. Mamaki nake a cikin raina yauni Rahama yar tallakawa wace ba yar kowa ba. Mutum kamar daddy ya tsaya yana min wanan magana kamar diyar wani da wata can a gaban shi. Ni yanzu ashe har ina da wani kima a idon wani kamar daddy mai daraja da kima. Jin yana magana ban bashi amsa ba yasa ya dan taka zuwa saman godo wanda ban san lokacin da har yakai bakin gadon ba ya zauna tare da zare rigan dake a jikin shi. A hankali yakai kwance tare da sakalo hanayen shi a jikina dake cikin bargo jin jikina da rigar barci naji shi yana cewa. Rama ina da wani akidan da nake bukata ga matana idan har ina tare da ita a saman gado. Nafi son idan ina tare da matana naji ta babu komai don nafison mu kasance skin to skin dani da matana. Don sam banda sha, awan wanan rigar da kuke sawa wai rigar barci a jikin ku. Sam ban ra, ayin hakan ga matana don haka daga yau sai ki sani don wanan ra, ayina ne na kaina. Ba tare da nai magana ba na dan mike zaune tare da zare rigan dake saye a jikina. Yace good girl ashe namu zaizo daya ke nan tunda kina da biyayyan akan maganan na gaba dake. Na kwanta naji saukan hanayen shi a saman jikina sannu a hankali yake dan shafan jikina. Har naji saukan hanayen shi a saman nonowa na da suke min tsaye kyam a jikina don ni ban yi saurin yin nono ba a rayuwana. Hannunn shi ya tsaya kyam a saman nipples dina wani irin abu naji yarrr ya sauka a duk illahirin jikina. Kokarin daurewa nake ba tare dana nuna jin abinda yake min ba a cikin raina. Yunkurowa naji yayi yakai bakin shi a saman kafafun nononuwan nawa ya na dan , , kadan kadan. Hakan yasa ban san lokacin da hudubar Zarah yazo min ba, jikin na ya hau kyarma na dan bankaro kirjina sama a hankali hakan ne ya bashi daman jin dadin yadda yake so akaina. Shansu yake kamar babu gobe tun ina daurewa har ya kai na kai hannaye na a saman bayan shi tare da tallbo kan shi da dayan hannun nawa. Banda karan naurar sanyin dake aiki a dakin baka jin komai sai nishin mu a lokacin. Gaba dayan mu mun fice ga hayacin mu ba wanda yasan iya duniyar da muka kai a lokacin don abinda muke ji. Da wasa yai wasa sai jin daddy nayi yana kokarin shiga na nan tsoron abinda ya faru jiya ya fado min a raina. Ina rokon shi da daddy please don't do this to me, tankar zuga shi nake har naji ya shige ni ban daina zubar da hawaye ba shima bai daina abinda yakeyi ba gareni. Saida ya gamsu don kan shi ya kyaleni ya koma gefe yana sauke numfashi kamar wanda yai wasan tseren gudu a lokacin. Jin yadda nake kuka yasa ya rugumoni a jikin shi yana dan shafawa a hankali yana fadin stop cryin dear wanan ai is natural. Daga haka don wahala ban san lokacin da barci yai gaba da ni ba jin nayi barci yasa shi zare jikin shi daga nawa ya mike ya shiga bandaki don ya tsarkake jikin shi. Ya fito ya koma saman gadon ya kwanta tare da rugomin zuwa jikin shi na sauke gajiyeyen ajiyan zuciya na gyara kwanciyana. Ya dan murmushi tare da gyara rugimay ni ya tofa min adduan kwanciya ya lumshe idanuwan shi sai barcin gajiya. Cakin dare na dan falka naga yadda muke kwance rugumay da juna ina makale a jikin shi. Na mayar da idona don a gajiye nake gabobin jikina duk sunyi min tsami da ciwo kamar nai wani aikin wahala. Biyu da rabi daidai ya falka ya mike zuwa ban daki ya sake watsa ruwa tare da dauro alwala yazo ya tayar da sallah. Sai wajajen asuba tun ina jin karatun shi a cikin mafalki har yakai na bude idanuwa na yana zaune a likacin yana hailala wanda nake jin abinda yake karantawa Subbahanallahi, walhamdullahi, Allahu akabar, Na gyara kwanciya na da zuman komawa barci sai naji muryan shi yana fadin ki tashi ki samu falan dake ga gabatowan asubahi. Jin abinda yace dani na dan yunkura a hankali na zauna ina jin cinyoyina sun min tsami sosai a lokacin. Haka na daure na mike tafiya da kyat na shiga ban dakin na yi kamar yadda sukai min shi da anty da ruwan zafi. Ba laifi don naji dadin hakan sosai na tsarkake kaina na fito na dauki tufafi daga cikin wardrove dina na saka. Jin kiran sallah na biyu naga ya mike ba tare da yai min magana ba ya fice daga dakin nabishi da kallo daga inda nake zaune. Sai da nai sallah asuba ne na bar gurin na koma na kwanta don ko ina ciwo yake min. ********* ********* ********* Nasir na ya falkar dani daga dadaden barcin da nakeyi yana fadin anty tashi mu koma dakin mu. Tashi muje kiyi min wanka naci abinci ranan ba school haka yasa na mike dole ba don naso ba na ja shi zuwa bandakina nai mashi wanka. Mun fito ina shafa mai mai saiga Gajiye tace , a,a dan gidan anty kai kana nan ashe har inacewa hajiya kana barci baka tashi ba. Mun gaisa da ita take cewa an shirya abincin maigida hajiya tace na kiraki kikai mashi a part din shi. Nace gajiye nice kuma zan kai wa daddy breakfast din kuma yau ? Tace kai Rahama akwaiki da shirmay wallahi hajiya kike son tai maki hakan ai tayi kokari wallahi. Nan dai ta kara min nadiha tare da cewa ki tashi ki shirya ki tafi kada ya gaji da jira yafice baki ksi mai ba. Nace da Nasir yabi Gajiye ta saka mai kaya gani nan zuwa gurin shi na bashi abinci yaci don na fahinci yunwa yake ji. Suna fita nafada nai wanka nafito na shirya cikin atamfan zani da riga na daura dankwali sai ni kaina naga kayan kamar sun kara min kyau ne. Dakin anty na fara shiga na samu tana kwance har lokacin bakin gadon na karasa tare da rusunnawa ina gaida ita. Ta dan dago tana cewa kin tashi Rama kikaiwa besty abinci mana kada ya fita bai karya ba. Nace da naso naba Nasir abinci ne anty don yunwa yake ji yace min shi ya tayar dani ma. Tace don Allah ban son shirmay Rama kije kikaiwa mijin ki abin karyawa kice wani Nasir can kada ya karya mana in sai kin tsaya bashi. Simi simi na bar dakin ina fita falon yaron na zaune yana jirana nace Nasir bari na kaiwa daddy breakfast kaji na dawo na baka sai naga yaron yai fushi. Inda yake zaune na nufa naja hannun shi nace zo mi tafi mu dawo na baka kaji. Na dauki kayan da Gajiye ta hada gabana sai faduwa yake min muka nufi part din nashi nida yaron. Tun a kofa na fahinci bashi kadai bane a falon shi don ina jin muryan mace kamar cikin fada fada ake magana. Daga kofa naja na tsaya ina sallama don a bani izinin shigowa daga ciki inda muryan mai magana da na fahinci Hindu ce ya hana aji sallaman nawa. Kara dan daga murya na nayi inda hakan yasa yaji ya amsa min na shigo dauke da kayan na nufi inda table yake zan aje mai. Yace No kawo min nan saman kafet na zauna naci sai dana aje na durkusa ina cewa dashi ina kwana daddy. Ahayye wai mamaki daddy ko may naji kince wani daddy kuma bayan wanda yake turmuzanki kwana biyu. Wanan ai kalman da kunya aji shi a bakin ki kuma bayan kin debe kwadayin shi a kanki tun yaushe. Daga inda nake durkushe nace da ita anty hindatu ina kwana yaya husna ta kwana ? Ke ban son munafinci da kilibibi ina ruwan ki da yadda muka kwana iskancin ki daga yau ya tsaya ga wa yanda suka dauke ki wata tsiya a gidan nan . Kada ki sake wani kilibibin gaisuwan ki ya zo kaina a gidan nan again kinji na fada maki. Tajuya gun daddy tace akan wanan yar kauyen har kake son ka raina min wayo baban husna har may kagani gun wanan mai kama da jan gwanda. Sai lokacin naji yai magana yace hindatu ki fice min daga nan tun ran ki bai baci ba kishi haukane halan ? Kina haukan ki na kyale ki na fada maki ra, ayina bama ra, ayina ba abinda sunna ya zartan ne akan mu. Abinda dai ra, ayin ka yaso don ba wanda ya hanaka tsayawa lokacin da aka kawo ta ai ka debe kwadan da kake mata. Yace baki da hankali kuma baki san Allah ba waike ba wasu kika sama agidan bane haka sukai maki da kika shigo ? Jin rigiman nasu ba mai karewa bane yasa na mike naja hannun yaron da zuman mu fice mu basu guri. Naji yace ina kuma zaki Rama, tsaya mana ki zuba min naci zaki wuce kuma ? Kadan ke nan ai ga haukan yan kauye idan kace kwashe kwashe ka iya a gidan ka. Wani irin malolon bakin ciki na hade jin abinda tace yasa na koma na zauna tare da fara bude kulolin abincin na dauko plate na fara zubawa kamshi ya bure falon gaba daya. A hnkali nake komai nawa yana zaune ya zuba min ido yama manta da wata hindatu a tsaye a gurin. Yace ga ruwa da abin sha can a fridge ki dauko min na mike zuwa inda fridge din yake na dauko mai. Tabini da ido kishine karara a idon ta taja wani dogon tsaki daidai lokacin da najuyo zuwa inda suke. Tace karyan banza sai dai kama wallahi amma ba dai hali ba kan muje zuwa mu gani in karya na zama gaskiya ? Yace yaushe kuma ya mike ya sauko daga kan kujera ya zauna a kasa tare da lankwashe kafafuwan shi yana cewa Nasir dake zaune yana wasa da remote cikin rashin damuwa da abinda akeyi. Yace my friend zauna mu karya ko ka karya ne don kai dan gidsn anty ne na sani ? Yaron ya sauko ya zauna gap da uban yace dani Amarya amma kin san wanan abincin ba zai isheni ba nida ku don angon naki ci gareshi tundai abin cin amarya irin haka ? Tsuki taja ta mike tafice daga falon tana fadin ai mu zuba a gidan nan wallahi sai yarinya ta raina kan ta tayi data sanin shigan katsalan dan din da tayi muna. Murmushi yayi tare da dagowa ya mayar da fuskan shi gare ni yana fadin bisimillah mana zauna muci ko ? Nace cikin kunya daddy zanci indan nakoma dakina ai . No no no tare nake karyawa da matana ko baki san da haka bane don haka zauna muci ko sai na baki abaki zaki ci. Kunya ya kamani yadda daddy yake abinshi hankali a kwance cikin rashin jin kunyana da nauyi kamar yadda ni nake jin nashi. Zama nayi tare da daukan spoon din ina dan juyawa a hankali cikin plate din abincin sai dai na kasa kawai a bakina don kunya. Debo abincin yayi ya nufi bakina dashi yana cewa ina ganin sai nabaki zaki ci don wanan kunyan naki ba zai bari kici ba nasan kuma bakici din ba . Oya bude baki ki karba maza karbi kici kada ki zauna da yunwa nasani sarai baki cin komai yanzu. Zanci nace cikin jin kunya yace karbi wanan din kici haka na bude bakina yabani na hadiye da kyat kamar an bani magani naji. Da kyat na taune shi sai Nasir shima ya debo ya mika min murmushi ya sani daddy yace. Kinga danki ma yasan bakyaci gashi nan yana baki ai na karba na kara hadewa daga haka kuma na kasa sakin jiki naci. Sun kan sai cin abincin su sukeyi hankalin su a kwance dankali da kwaine bai ma damu da ruwan shayin ba. A haka har suka gama ci ya goge bakin shi yana cewa zan tafi asibiti na duba Zulfa da yamma idan nadawo zamu shiga ki gaidasu hajiya da Alhaji. Don haka ki zauna da shiri bayan karfe hudu idan na dawo na amsa a sanyayye da Allah ya kaimu. Ya mike ya na shirin fita nace Allah ya tsare ya kare Allah yasa a fita a sa, a adawo cikin nasaran rayuwan duniya da lahira. Da alama yaji dadin wanan adduan yace Allahuma amin nagode kwarai da wanan adduan naki mai daraja. Yafice ya barmu na fara kwashe kayan nacewa nasir yazo mu tafi nakai kayan na dawo na kara gyara gurin ranan har cikin bedroom din saida na gyara shi tsab komai nai mai muhalin shi don dakin gaba daya bakacewa akwai matan dake kwana acikin sa ma. Na dawo na samu anty ta fito falo take cewa dani ai na dauka kin kwanta ki huta ne daban jiki ba ? Nace cikin kunya anty naga part din daddy yayi daudane na tsaya na gyara shi. Tace tana gyara zaman ta aiko kin kyauta don idan baki gyara ba ma haka gurin zai tabbata da kazantan shi. Don dai babu mai gyarawa acikin mu nice ma danake da dan lafiya ai nakan dan gyara mai sai ko shi idan yaga abin yai yawa ya gyara da kan shi. Mamaki naji a raina wai har namiji mai mata uku ya tsaya gyaran part din shi da kan shi haka mutum kamar daddy ga komai na rayuwa a dakin amma babu gyara. To su may sukewa kishi haka bayan ko kara basu kawarwa a gidan saidai mace tai wanka ta fita sau goma a yini shine kawai aikin su. Can naji tace Nasir ke fada min wai mama husna tana maki fada kun samayta a falon ke nan ko ? Na gyada mata kai tare da cewa eh anan muka samy ta da muka shiga dazun tace kada ki biyewa haukan su su haka suke kulun cikin jan fita don basu taba zama lafiya ko a tsakanin su haka suke badubar junan su ba shirin karya sukeyi tsakanin su. Ni dai banyi magana ba sai naji tace amma don Allah daga yau ki daina zuwa da yaran nan gurin shi idan zaki tafi don kinga abakin shi nake jin komai fa. Nace cikin murmushi anty abinci yake son na bashi shiyasa muka tafi tare dashi ai. Tace to daga yau dai ki bari yaran yanzu wayon tsiya ne dasu wallahi sun san komai don ba yara bane yadda kike zato. Remoto na dauka ina kunna tv tace dani bazakici komai ba ke nan haka zaki ta zama da yunwa ko ? Ina ma son nai mashi magana akai maki kayan abinci a part din ki don ki dinga dafa abinda ranki ke so idan kin tashi. Don ba zai yuyu ace sai kinzo nan ba ko yaushe cin abinci shi kan shi ai wani lokaci zaiso ace kin mai wani abu idan yana bukata. Nace anty ba sai nazo nan nayi ba ni hakan ma yayi min wallahi tace haka nake so ban son gardama fa. Sallaman su mama Zulaine ya katse mata magana suka shigo nan aka fara gaisawa dasu. Mama zulai ce ke fadin munzo ne muga yar aikin hindatu don Zulfa tace muna ita ta kawo mata zobo don tasan tana so tasha da rana. Kin ga kuma ance kwayar zubar da ciki aka bata tasha don ta rantse muna ita bata sha komai ba daga bangaren ta banda wanan zobon data sha. Ikon Allah inji anty ita hanne din ta kawo mata zobon tasha ke nan ko ? Mama zulai tace ai har ita wanan din ta nunani tace, tace wani abu tasha shi ya jawo mata matsalan kuma haka shima likitan ya fada muna ai. Yanzu muna son jin ta bakin ita hanne din ne kafin mu tabbatar da hakan garesu ko ? Anty tace amma sai nake ganin kamar wanan matsalan ta cikin gida ne don haka abari mana maigidan ya dawo sai a sanar dashi kinga ai shi zai san yadda ya bullowa al, amarin ko ? Hakane amma ai kin san wanan kishiyar taku da shegen wayon tsiya anya zai fahinci gaskiyan maganan kuwa don tun shekaran jiya muka fada mai komai amma banga ya dauki wani mataki ba akai. Zai dauka anty tace don munyi shigen maganan haka dashi ina ganin dai bincike yake a hankali don ya gane gaskiyan maganan. Mama tace to Allah yasa idan har yana bincike ai mu bamu da tacewa kuma sai mu kyakeshi muga gudun shi ko ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU IDAN KUMA KIN KARANTA DAKE DA ALLAH. IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI MUNA HAKKN MU AKAN KI RASHIN KARANTAWA SHINE ALHERI AGAREKI IDAN BAKI BIYA BA DON GUJEWA DAUKAN ALHAKIN WANI A KAN KI, , , 43 Na gama kwanaki na hudu da zan yi wanda daga wanan ranan zuwa turakar maigida ya hau kaina. Anty ce ta karbi girki bayan ni inda duk wani aikin da za, ayi na maigida nice nake aiwatar mata dashi iyakan ta ta shiga dakin da dare. Ni kuma zaun kwana tare da yara a part dina har jinior dashi muke kwana a tare da mu. Idan nayi sallah zan zauna na roki ubangijina Allah nakan fara gode mai da irin rayuwan dana tsinci kaina a cikin dan shi ke da masanayan yin hakan a gurin shi . Sai kuma na roke shi da yai min kariya da tsari akan duk wani abin ki ko shedan da zaitaba lafiyan jikina da rayuwana. Na kan zauna sosai na tsayar da duk wani abinda ke a gabana gurin rokon ubangijina akan wanan rayuwan da na riski kaina a ciki na kasancewa da mijin matar da tafi ko wace mace daraja da kima a gare ni bayan mahaifiya na. Yau gashi na kasance da mijin ta a matsayin nima matar aure a gareshi ya Allah kada ka nufe ni da cin amanan wanan boyar taka daidai da rana daya a rayuwana. Satin Zulfa biyu aka sallamo ta daga asibiti nan ta dawo gida ta karasa jinyan ta tana zama da mama Luba kaunan mahaifiyar su maigidan ke nan. Da kwana biyu ya kira mu gaba dayan mu a falon inda ya zaunar damu ya fara magana kamar haka. Ba komai yasa na kiraku ba sai maganan abinda ya faru a cikin gidan nan kan abinda ya shafi zulfa gata nan. Wanda ba don Allah ya gyara ba da anyi sanadin fitar cikin dake jikin ta yanzu. Kuma wanan abin ya faru ne a cikin gidan nan inda aka bata magani tasha don cikin ya zube ba tare da sanin ta ba. A iya bincken da nayi na gano inda matsalan ya dauko asali shine daga gurin mai aikin hindatu ce hanne. Da sauri hindatu tace hanne fa yace kwarai sai dai nayi iya binciken da zan yi nagane cewa itama a cikin rashi sani ta aiwatar da hakan don ta rantse da abinda zai kashe ta bata san ta hada wanan abin da kayan hada zobon ta ba. Shine dalilin da yasa zan dan ragwanta mata naso na kore ta ma gaba daya a gidan amma ance na kyale ta idan halin ta ne ai zata sake wani karo. Magana yake amma gaba daya falon ba wai mun yarda bane dole dai akwai wani abu a kasa ai sai dai halin maza baka gane gabas din su kawai. Nan hindatu ta haufadan karya wai kazafi akai ma hanne ita dai tasan inda ta sha maganin ta kawai. Suka fara cacan baki a tsakanin su kowa na fadawa dan uwa bakar magana ni dai ina zaune na sada kaina a kasa ina sauraren su kawai. Muryan anty ne ke fadin tashi mu tafi Rama muna da abinyi a part din mu tana gaba ina binta a baya muka barsu nan ba musan yaya suka karasa ba. Sai da daddy ya shigo ne naji anty na mashi magana akan hukuncin da ya yanke yake cewa da ita, Ki sa masu ido nasan abinda nakeyi kuma akwai abinda nake son na gano ayin hakan da nayi. Ni dai kaina a duke yake don sam idan daddy yana tare da anty ina furin balain kunyan shi nake ji. Shima sam baya sake min fuska sai ya nuna tankar bai ma san ina gurin ba lokacin. Har na kanyi mamakin hakan amma daga baya sai naga ai hakan ma yafi sauki da ya sake min fuska kima ya ja muna matsala ai gara hakan kawai yafi sauki. Har girki ya dawo kaina nayi shi a dadafe ba don naso hakan ba don sam ban son zancen girki a raina. Yai tafiya haka yasa na sake jikina naci gaba da harkokina ina zuwa school sai dai cikin katon hijjab da daddy ya sawo min har guda biyar manya har kasa. Na dan mai da jikina ko yaushe ina manne da anty na don babu canjin fuska akaina da tai min. Bayan sati biyu ya dawo kowa na rawan kai suna futina mu dai part din mu ba wanda ya kula da haukan su don ni haushi da mamaki ma suke bani. Akan namiji suke wanan haukan yanzu zaka ji su anjima kuma kaga sun shirya a tsakanin su. Ni dai na fahinci cewa ina da rauni a gurin kasan cewa dana miji don hakan da nake ba wai rashin sabo bane ko wani kawai dai hallitane min hakan. Tun da la, asar anty tace dani naje na gyara part din daddy don nasan nice da girki ranan. Saida gabana ya fadi haka na dauki kayan gyara na shiga part din, yadda naga an hargitsa shi ba kamar yadda na gyara ba ranan da anty zatai girkin ta. Komai a yamutse yake ban dakin ma bai shakuwa don da gani ba a wanke shi ba. Ai gara zulfa ace tana bedrest ne sai dai ai a nan take kwana da mijin ta, amma ita hindatu mai yaci katfin ta da bazata gyara ba. Nan na takarkare na gyara komai na darje makewanyin don nafi jin kyamkyamin shi sosai. Gurin ya koma neat sai kamshi ke tashi yana kyali da dadin shaka komai nayi mai muhalinshi. Ban dade da fita ba ya shigo part din tun a falo ya fara ganin sauyi don ya shaki kamshi maidadi. Ya sauke ajiyan zuciya a fili yana fadin Allah yai wa wanda duk yai aikin nan albarka dama da safe da kyat ya iya yin wanka a bayi don kazantan shi. Duk, lokacin da akace girki ya dawo kaina har kuka sai danayi a daki ni kadai ganin banda niyan zuwa gun daddy da dare anty ta matsa min da na shirya dole na tafi tun takwas na dare ta gargadani zuwa gurin shi. Da kuka na na karasa falon ba laifi nayi kwalliya na cikin material mai ruwan milk da flower ja a jikin shi. Na dora hijjab a sama nai mata sai da safe na wuce zanin da zan kwanta da rigar barcina duk da nasan ba tasiri rigan zaiyi ba acan amma dai na dauka na tafi dashi. Nai sallama yana zaune idon shi akan tv sai wayan da yake yi jin sallama ya sashi ya dan dago kan shi yana kallona har na karaso kusa da inda yake zaune. Durkusawa nayi ina mashi ina wuni daddy hannu ya mika min alaman inzo inda yake. Ban musa ba na nufi inda yake ya kamo hannu na ya zaunar dani gaf dashi hakan naji wani nauyi da kunyan shi ya kamani. Sai da ya gama wayan shi wanda na fahinci wani harka ne na business yake magana akai. Ya sauke ajiyan zuciya tare da fadin amarya duk ni keda wanan kwalliyan haka ? Kaina na dukar kasa don nauyi da kunyan shi da nake ji ya rufe ni amma shi ko a jikin shi hakan. Yace sai dai kinyi mantuwa don wanan hijjab din bai dace ace kinzo min nan dashi ba don baida amfani a falon nan. Jiki a sanyayye na kwabe hijjabin a hankali, naji ya sauke ajiyan zuciya yana fadin may zai sa ki boye min wanan kyakkyawan suran naki Rahama ki daina min rowan jikin ki please. Tashi ki sauko min da abinci na nan don ni nafi son naci a kasa na saba da hakan tun ina karami a gida haka mama laraba ta koya min kin san ni zance rabin rayuwana a gunta nayi shi. Shiyasa kike ganin ina matukar mutunta mama don duk wani tarbiyan rayuwa itace tabani shi gashi kuma ina amfana da abina a yanzu. Na aje abincin tare da zaunawa na fara zuba mai baiyi magana ba haka yasa na dago ina tambayan ko ya isa. Yace duk yadda kika zuba min ai cinyewa zanyi tunda shi kike bukatan naci. Mamaki nake a raina wai ashe daddy haka yake amma idan ka gan shi a waje zaka dauka ko da matan shi bai maganan uffan dasu. Amma ashe ba haka abin yake ba a badini sakewa yake da matan shi sosai fiye da tsanmanin mutum. Ya fara ci inq zaune a gefe ina wasa da yan yatsun hannuwa na naji yace dama ina son magana dake. Haka yasa na dago kaina da sauri na dan kalleshi naga abincin shi yake ci hankalin shi a kwance. Sai da yai kamar loma biyu ne yace dama ina son tambayan ki wani sana,a baba yake yi a kauyen nan ne ? Sai da naji gabana ya fadi to ni may zance ne yanzu sai dai na fadi abinda na sani kawai akai. Nace ni dai na taso naga yana zuwa cin kasuwan kauye ya na samun abinda zai ciyar da iyalin shi kullun. Yace nasan da hakan wani sana, a ne yakeyi taka maimai kike gani yake wanda ke kawo mashi kudi ? Nace yafi sayen dabbobi yana sayarwa sai kuma sanan kayan masarufi suma yana dan tabawa wani lokaci. Yace na dabbobin yafi aminci ai don shi sanan irin kayan abinci hanya ce wani lokaci na halaka ga bawa mutane ne basu ganewa. Sai na tuna da wa, azin wani malami da na saurara a wayan anty kan masu tauye maauni irin azaban da Allah ya tanadarwa yin hakan. Har yagama cin abincin shi bai kara magana ba sai ruwan da ya kara tsiyayyawa ya kora na mike na kwashe kayan na mayar part dina na rufo. Koda na dawo yana kallon national new a wani tasha na zauna nima ina kallon abinda yake kallo ba tare dana fahinci komai ba sai naji na sake hamma. Baiyi minti daya ba naji ya dauki remote ya kashe tv ya nufi gurin Ac din falon ya kashe har wutan dauka na yayi cak a hannaye shi sai cikin master bed room din shi. Yana ajeni ya shiga wanka nima ban kwanta ba na dan mike tsaye na kara gyara shiri na. Na koma na kwanta yafito yana tsaye yana shafa turare nabi fadadar bayan shi da kallo. Har ya gama yazo gareni tankar dai ranan ya fara sani na a ya mace don sai da na raina kaina matuka a gun daddy. Allah Allah nake gari ya waye na bar dakin don bazan iya kare jurewa ba don na kasa sabawa da matsin irin nashi haka. Nake mamaki ko hakan ke sa anty na da duk tai girki sai jikin ta ya dan motsa mata tayi ciwo ne ? Washe gari bai barni na fito ba wajajen tara na safe na samu fitowa daga gurin shi. Haka ya jawo min sabon tsana daga matan shi don har anty sai da naga dan sauyi a fuskan ta dana shiga gaishe ta. Amma bata dade ba ta sake don dana dawo tambayan ko tana da abinda za, a ai mata kafin mu dora girki take ce min cikin wasa. Ke aikin may zaki yi ku zauna ki kula da mijin ki kibar gajiye tai muna aiki kada kuma anjima kice ke bazaki iya ba. Kunya naji na fice daga dakin naje na dama mata kunnun magani na kuma zauna saida na fifita mata shi don yai sanyi taji dadin sha. Tana falo zaune na tunkaro ta da magani tana gani ta bata rai tana fadin Rama yanzu baki manta da dama maganin nan ba so kike muyi fada ko ? Nace ai newa mama alkawari zan dinga dama maki shi duk lokacin dama shi yayi da kyat na samu tasha tana bata rai ina mata sannu har ta shanye na dauki cup din na fita dashi daga falon. Na dawo na samu daddy ya shigo suna zaune tare nai mashi sannu da dawowa. Yace yau ina son shiga da kaunar ki gurin su Alhaji mu gaisa tun kafin nai tafiya naso mu tafi ban samu lokaci ba. Tace hakan na dakyau ai yace daga can har gurin Abba zan shiga da ita su gaisa tace amma ba don zaku biya ta gida ba da sai ince zan je naga Abba nima. Yace may zai hana don zamu bi ta gida ne ba zaki ba ko may tace ba hakana bane kasan yaune zaka fara shiga da Rama gurin su shiyasa bazan biku ba kawai. Inda nake ya juyo ba wani sakin fuska a tare dashi yake ce min ki shirya karfe hudu zamu fita. Daga haka ya fice ina mamakin shi cikin raina kamar bashi bane da safe yai ta jagwalgwalani har tsawon wani lokaci. Sai da ya jima da fita nake cewa da anty may za, awa Abba dashi da Alhaji ? Tace kije kiyi abinda ya dace idan kin gama ai maci ko don nasan baki wasa da alamarin Abba ai Rama nace ba dole ba anty mahaifi ba wasa ba ai. Tai murmushin jin dadi yadda nake mata kara da mahaifin ta na mike na shiga kitchen. Cake kamar kullun na hada masu sai miyan dana shiryawa Hajiyan daddy kafin wani lokaci komai ya dauki kamshi na sa a kula na shirya komai yadda ya dace na kuma gasa kaji nai peppeying din su. Na idar da sallah na shirya cikin wani lace light blue mai kyau da tsada na kawo after dress fari mai duwatsu na aza sama tare da rolling din dakwalin shi a saman kaina. Na juyo zuwa falon anty sai kamshi ke tashi a jikina takalmi masu tsini na saka a kafana. Ban dade da zama ba ya shigo dakin shigan kananan kaya yayi kayan sun matukar karban jikin shi sajen fuskan shi da ke kara mai kyau ya kwata lub lub a fuskana shi, fuskan shi yai matukar kyaun gani. Ya dan duka yana wasa da jinior yana cewa yaron baba ka fa isa shiga school haka na. Anty tace daya huta da gorin Rama kullun zasu fita sai tace dashi No school bye suna mashi sheri. Ya dan dago yana kallon inda nake yana cewa kyaleta kaji mai suna kaima zaka fara fita kamar kowa wanan school din da aka bude sabo zan kai ka. Ban san yaya akayi ba yau nai magana sai cewa nayi daddy amma har dasu Nasir za, a mayar can ko ? Kafin ya bani amsa anty ce tace si dai zauna inda suke don kada akai min dana shi kadai zakice wai wani Nasir can . Nace haba anty Nasir fa soja ne ba wasa gare shi don kar ya shigo da bindiga kiji tsoro wata rana. Sai naga ta canza fuska tace kaiyya Rama da Allah zai gwada min haka danafi kowa farin cikin ganin haka ga rayuwa na sai dai Allah kawai. Cikin bata rai naji yace da ita zaki fara ke nan ko may ya kawo wanan irin maganan ku ba zaki daina ba ko ? Ya juya inda nake a fusace yana cewa dani ke kin shirya mu tafi ne ? A sanyaye nace eh sai dai bazan iya fita na bar anty na cikin wanan yanayin ba gaskiya ya juya ya bar falon da sauri tace kira gajiye ta fita maki da kayan har lokacin magana take cikin sanyin murya. Bayan na kira gajiye maimakon na fita tunda ana jirana a waje sai na dawo na zauna a hannun kujeran da take zaune akai na dan kwanto da kaina ga jikin ta sai naji ta rugumay ni. Cikin hawaye nace anty ban san magana na zai soshi zuciyar ki ba a wanan lokacin da ban yi shi ba wallahi . Itama dai hawayen takeyi tace dani Rama ai fatan alheri kikai mashi nice dai nake ganin da shawan son ganin hakan a gareni amma hakan da wuya gare ni. Anty don Allah dai ki daina fadar hakana ciwo fa ba mutuwa bane yin haka kamar shigewa Allah gabane. Tace babu komai Rama ai na bari ku gaida su hajiya idan kunje ina gaida Abba don Allah kinji. Ina shirin tashi daddy ya dawo falon yana cewa yaya baki fito bane kallon yanayin mu yayi kowa na sharan kwalla a fuskan shi. Ko da muka fito mun samu Hindatu suna shan iska ita da wata kawarta sai hanne mai aikin ta dake dauke da abu zata kawo masu inda suke. Daddy yana gaba ina nin shi a baya sai dai mutum zai dauka ko jerowa mukayi gashi nai matukar kyau damu. Kawar Hindatu ke cewa da ita kai kai kai kardai nace wanan ce armaryan taku hindatu ? Ta tabe bakin ta cikon dan dago kai ta dan kalle mu sai kuma ta kawar da kanta gare mu tace itace fa kinganta nan sai wani rawan kafa yake akan ta. Wanan ai ba bakauya nace ku kuna may kuka bari ya kwaso maku wanan zankadediyar yarinyar haka a gida. Nifa na dauka irin yan kauyen nan ne da naji kina ta wai wata yar kauye gaja da ita ashe yarinya sunan muna kauye ne kaiwa wallahi. Wanan idan har bakiyi da gaske ba wallahi tana kwace maki miji kina ji kina gani ke ni har sai da naji wani abu fa jita fa don Allah ji yadda suka dace dashi. Don Allah kubura ki bar maganan nan don zafi nake ji a raina na tsani naji ana koda yarinyar nan wallahi. Har muka shiga mota maganan mu sukeyi inda daddy ya bude min gefen mai zaman banza na shiga yadawo ya bude gefen shi ya shiga yaja muka fice gidan. Sai da muka dan yi nisa da gida har lokacin rai na a cunkushe yake min sai naga ya ciro handkici a wani guri ya miko min yace ki share fuskan ki don bazan fita dake haka ba azaci ko dole nai maki kibiyoni. Karba nayi na dan goge fuskana ba tare da ya kalloni ba fuskan shi na a titi yace kamata yayi ace kina kara mata kwarin gwiwa ba wai kina biye mata kuna karaya ba haka. Nace daddy ban iya ganin anty tana irin haka na jure ganin ta ban san har yau may ke damun anty ba take irin wanan kalamin haka. Bata da lafiya ne a jikin ta shine take ganin kamar zata iya rasa rayuwan ta ta wanan sanadin ta manta da Allah shine mai kashewa da rayawa a duk lokacin da yaso. Rahama idan zaki taimake ni kan anty ki zan fi kowa farinciki da hakan duk da dama kina yi amma zan so ki kara taimaka min gurin kawar mata da mumunan akidar yarda da tayi da maganan likitoci gurin fadakar da ita cewa shi ciwo Allah na iya kawo saukin shi idan ya tashi yin ikon shi don ba ko wani magana ne likita zai fada ya zama gaskiya ba. Nace insha Allahu daddy zan yi yadda kace dani yace nagode da hakan . Mun isa gidan su mun samu Alhajin shi yana gida a lokacin dama ya kwatanci hakane don mu samay shi a gida. Suna falo zaune da hajiya da Aisha da anty kubura yar wajen mama laraba da sun zo gaida su don atare suka taso kuma ko yanzu komai a tare suke abin su. Anty Aisha ce ta hango mu tafe tun daga nesa, tace ga yaya nan kamar da amaryan shi. Hajiya tace hauka yake da zai kwaso wanan yar matsiyata ya kawo muna gida shi dai da yaga yana iya hada jini da jinin matsaiyata sai yaje yai tayi ai. Ko da ta gama maganan ta a cikin kunnawan mu munji komai don muna tsakiyan falon bamu kai ga zama ba. Alhaji karami ina kuma zaka shigo min gida da wanan yar matsiyatar mai farar kafar tsiya daga shigan ta gida har an fara neman kashe matan gida ana zuba masu guba ga abunci. Cak naja na tsaya guri daya naji kafana bai daguwa daga inda nake tsaye a bayan shi. Duban uwar yayi da mamaki ya kara duban ta yace haba hajiya matata ce fa kikewa wanan kalamin haka ba dadi. Cikin matsanacin bacin rai yake mata magana tace eh nagani matarka ce kuwa yar gidan matsiyanta da aka cinna maka ko ? Ta juyo gare ni tana cewa wai ke shin ko manyace bamu sani ba yarinya haka da bakin nacin tsiya kamar bakar mayya dake kin nace don bakin jaraba sai da kika shigo gidan shi dasunan wai mata gare shi ? Wallahi tir da halin naci irin naku na yan kauye da son kwadayin duniya ke kinga arziki adole kin nace saida kikayi wa uwar dakin ki asirin data amince dake. Itama din ai wata shasha ne da kamar ki shine take son mayar min da da kamarta har kana wani ce min wai matatace fa har ina matar take nan ? Daga baya muka ji ana fadin idan ba matar shi bace farkan shi ce ko ? Kinga kuma idan naci ne ai sai ince ke tabiyo ko don ke ma ai yar tallakawan ne kika aure ni da arzikina ko ? Kai samu wuri ku zauna kabar yar mutane a tsaye haka baku bata gurin zama ba. Nan na zube a kasa saman carpet tare da dukar da kaina ga tsoro da bacin rai sun cika min zuciya na fam. Anty Aisha da kubura suna ce wa dani zo nan ki zauna ga guri mana zaki zauna a kasa. Eh zata zauna a sama mana tunda nida ita duk yan gidan tallakawa ne an fada mata taji yau kuma da vaku sani ba kunji na auri karuna mai kudin duniya. Wanan kuma yanzu ya saura gare ki inji Alhaji dake kokarin dogara sandar hannun shi yana son ya zauna a daya daga cikin kujerun falon. Sai da ya zauna na juya gare shi ina cewa Abba ina wuni ? Yace an wuni lafiya ya ta ince dai duk lafiya kuke gidan yaya sauran abokan zaman naki da yaran ku ? Na amsa kaina a kasa da duk suna lafiya Abba. Yace masha Allahu sai ai ta hakkuri kinji a zauna lafiya da kowa ke karama ce a cikin biyayya ga babba yana da matukar rana Allah yai maku Albarka nace Amin Abba. Na juya gurin hajiya nace Mama ina wuni kaina yana kasa cikin kunya da ladabi. Tace ke ban son makirci irin naku idan zaki kirani da hajiya da kowa ke kirana ki kirani wai harda wani shake murya wai mama ina wuni tana kwaikwayona? Da ban wuni ba zaki ganni a yanzu shiru nayi kaina a kasa na kasa dagawa na kallesu. Wanan dai ba girman ki bane wallahi kin gama da Saade yanzu kuma kin fado ga ita wanan din ? Yo da ita da Saade duk ba barayin na tsunta bane may ya raba danbe da kokuwa ? Daddy kan shi na sade ya dafe goshin shi da hannuwan shi yana sauraren irin cin mutuncin da mahaifiyar shi ke min wanda ya kasa fahintar wanan halin da takewa matan shi haka? Saboda haka yasa hindatu ta daina zuwa gaida su idan yazo gidan da matarshi hajiya tai murmushi sai idan yazo da Zulfa ne zakaga fara,anta. Muryan Alhajin su ne ya katse shi yana cewa dashi sai na samu an kawo min maganin da na da sako na dade ina bada sakon shi ba, a samo min shi. Daddy ta dan sauke ajiyan zuciya yace eh Alhaji sai dana tura can kasan larabawa aka samomin shi don yana da wuyan samu anan dakai da Saade na sa a sawowa ai. Yace Allah yasa mu amfana da shi yace amin Alhaji suka dan taba hira da mahaifin shi can hajiya ta juyo inda yake tana cewa dashi may ake ciki batun kwayan da aka sakawa Zulfa? Yace iya bincike na na kasa gane gaskiyan maganan don matar ta rantse ba itace ta zuba wani abu ga abin shan ba. Yanzu sai akayi yaya yace hajiya laifin da baka kama mutum da hannun shi yana aikatawa ba wuyan sha ani gare shi har ga Allah. Don haka ina nan ina bincike a hankali don ina son in fahinci wani abu a tsanake. Tace wai kai wani irin mutum ne mai bakin sanyin halin tsiya haka a cuce ka kace baka ramawa ita hindatun tsoran ta kakejine dabaza kafito fili kai mata magana ba ? Haka akayi munaji muna gani yarinyar hanifa ta mutu aka cewafata ruwa an rasa yadda tayi tafada ruwan nan sai gawanta. Yace hajiya wanan duk zargine tunda ba wai mun gani bane da idon mu amma ai in halin sune za, a gane gaskiya komai dadewan shi. Baba yace ki barshi yayi yadda yake so ai iyalin shi ne shike zama dadu kuma shi yasan halin su yake zama dasu ai. Nan dai suka kara dan tattaunawa kan maganan baba ne yace ya kamata ya mayar da hankali ga irin rayuwan da akeyi a gidan kada kishi ya koma hauka kuma har ana kadhin kai. Ya amsa da insha Allahu Alhaji inayi sai dai na kara don ba mutunci ne dasu ba su buyun nan. Hajiya tace su biyun kuma suna da mutunci ke nan ko? Yace ba haka nake nufi ba hajita sanin kowa ne irin hakkurin da nake dasu waya sani ko wurin yawon ta ta sha wani abu tunda suna fita sau goma albarka nace zan dauki mataki akan su kince ba haka ba. Alhaji yace ai kinji irin ta ban san may yasa kikewa yaron nan haka ba da iyalin shi kin hanashi yin yadda ya dace da gidan shi. Tace amma ai ban hana shi aure ba ko tun yanayi har yakai ga daukowa mutane mugun iri a gida. Alhajine ta kawar da zancen cikin cewa yaushe ne tafiyan naka ne nan suka buge akan hiran tafiyan sai canya juyo inda nake ina duke kamar mai sauraren wa,azi yace muje ko Rahama don akwai inda zamu tafi. Nace bari na dauko tsaraban su mama a mota yace ok na tashi na fita sai ga ni na dawo da kuloli niki niki har biyu na anjewa baba nashi na cake da nai masu tare da Abba mahaifin anty sai ita kuma hajiya na mika mata kullan dana soya kaji nagyara mata kamar miya nace gashi mama mu zamu tafi. Baba har ya bude nashi koyana fadin a, a, a duk ni keda wanan abin haka yaushe rabo danaga haka gareni. Itako ta karba tana wani tabe baki Aisha ne ta fito ta bude taga abinda ke ciki tace , a, a, a muma bari mu tsaya mu kwashi rabon mu nan. Baba sai albarka yake saka muna da fatan alheri da gamawa da duniya lafiya. Muka fice dan tafiya kadan don unguwa gudane sai gidan mama laraba muka shiga mun samayta a falon ta tana ganin mu taji dadi tana lale marhabi da sarakuwa na yau kune a gidan an tuna damu ke nan. Jin haka yasa Farida dake dakinta lekowa taga ko suwaye tana ganina ta sake labule zata koma ciki. Nace ai idan ni bazaki gaidani ba kya tsaya ku gaisa da dan uwanki ko may yai zafi hakane wai. Ta karasa fitowa tana cewa saidai haka amma bake ba tunda kin munafunce ni muna tare. Zaki fara haukanki da wauta ko itadai Farida ta gaida da daddy ya amsa mata a dake ta shige sai bayan na gaisa da mama ta tambayeni sauran mutanen gidan nace duk lafiya muke. Tashi nayi na shiga gurin Farida na samay ta kwance ta ba da baya na zauna ina dafa ta nace haba mutumiyar maiyai zafi hakane tsakanina dake ? Tace bar ni don Allah ni ai kin bani mamaki wallahi ace muna tare wai zaki auri daddy ban sani ba Rahama ? Nace Allah sarki yadda kika ji zancen wallahi Farida nima haka naji shi ban san komai ba akai har yanzu na kasa fahintar inda zancen ya fito har yau din nan. Tace ina ko zaki sani tunda bukatan ki ya biya dama haka kikeso ai shiyasa kikaki soja dake son ki kamar may. Nan dai mukai ta fafatawa da ita wanda hiran namu duk kusan gatse ne take min kan auren daddy danayi. Can naji mama na kirana nazo mu tafi nai mata sallama nafito taki rakani nan mama ke cewa dani naita hakkuri da kowa kada nasa zancen hajiya a raina nace lah mama ai babu komai hajiya ai uwatace duk abinda zatace dani ya nake gareta. Muka fito muka nufi gidan Abba shima sai albarka yake sa muna daga haka muka juyo zuwa gida. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU ODAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU, IDAN KUMA KIN KARANTA DAKE DA ALLAH YAR UWA DAN NA FADA MAKI, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU A KANKI DON RASHIN TSORON ALLAH YA KAIKI CIN AMANAN ZAMA, , , , , , 44 Mun dayi nisa naji yace dani ba tare da ya juyo inda nake zaune ba cikin damun akan hajiyan shi da al, amarin farida. May ke faruwa tsakanin ki da Farida ne haka naga kamar tana fushi dake ko ? Sai da nai ajiyan zuciya nake cewa dashi nima ban sani tundai da zancen auren nan yazo naga ta dauki zafi haka dani. Yace kyale mahaukaciyar banza bata da hankali nake gani wanan yarinyar Zulfa na gidana take son ita ma wai na aure ta ? Cikin mamaki nake kallon shi yace kwanaki ta turo min da sako mara dadi, nayi bincike na gane ashe itace take hasala wanan mahaukacin sojan dake son ki ashe ? Shiru nayi cike da mamaki wani shago ya tsaya da mota ya shiga shi kadai sai gashi ya kwaso muna kayan snacks da su sweet da sauran abin yara sai drinks masu tsada da ya sawo. Yake cewa tsaraban yaran ki ne don zamu samu sun dawo gidan yanzu nace Allah ya saka da Alherin sa. Daga haka yaci gaba da tukin mota tare da mayar da hankalin shi ga titi sai sautin kira,an ke tashi a motan. Muna gaf da shiga gida ya dan rage sautin kira,an yace cikin wata murya mau kama da na tausyi tare da dan shafo fuskan shi tun daga kai har zuwa haban shi yace. I hope abinda ya faru tsakanin ki da hajiya baki dauke shi da zafi ba a ranki ? Murmushi nayi tare da harde yatsuna cikin yan uwa ina dan wasa dasu na dan kalle shi nace daddy ai hajiya uwace kuma gaskiya ta fada don babu karya ga maganan ta. Ban kai wanan matsayin na Allah dai ne ya nufe ni da hakan a kaina amma nima nasan gaskiya ta fada sai dai maganan zargine kawai matsala. Wallahi tunda na dawo a matsayin mata a gidan ka ban taba taka part din wata mace ba sai na anty sai ko da wanan abin ya samu anty Zulfa anty tace na rakata. Stop thinking that babu sunan ki ko na Saade ga wanan matalan matsalarsu ce can da ta shafe su. Na sauke ajiyan zuciya muna shiga gidan har Zulfa na a haraba zaune saman farar kujera tana shan iska tare da wasu mata biyu. Bin mu da kallon mamaki takeyi bayan motar ta tsaya bai bari mun fita ba ya juya yana dauko kayan dake seat din baya daga nisa inda suke hangen mu sai mutum ya dauka ko nice yake runguma a mota a haka. Zuwa can muka fito ina kokarin karban kayan a hannin shi ne yace no barshi jida hand bag din ki kawai. Ina gaba yana bina baya naji sunyi tsit basu magana da alama mu suka bi da kallon. Ina shiga da sallama yara sukayo kaina da gudu kamar nai tafiya ne mai nisa suna min oyoyo. Na rugumay bayan sun sake ni na je inda anty take zaune na dan rugumay ta tana fadin lun dawo nace da ita eh lokacin daddy da ya tsaya waya ya karaso da ledoji a hanayen shi. Na mike da sauri na karbi ledan anty tana mashi sannu da zuwa tare da tambayan shi yaya su Alhaji da Abba ? Yace suna lafiya bai zauna ba yake cewa zai tafi yai shirin zuwa sallah lokaci ya gabato. Wanan ledan kuma fa na may ye nace nasu Nasir ne tsaraba aka sayo masu. Nasa hannu ga jakkana na fidda kudi nace anty gashi wanan yan dubu Abba ne ya bani sai wanan kuma Alhaji mama laraba taban wanan turaren wutan na fito da kwalban na aje a gaban ta. Tace masha Allahu ai an gode kuwa motsi yafi labewa ke nan na mika mata tace cikin kallona kamar da mamaki may zanyi dasu kuma Rama ? Nace ki karba ki aje a gurin ki mana tace haba dai wai ke ko yaushe yarinya ce ke ko may ? Don Allah ni rabani da abin dariyan ki kin ji na kirga dubu uku naba gajiye sai anty tace abude ledan muga tsaraban ko ? Ina kiciniyar bude ledan naji tace dani kun samu hajiya a gida ko take annurin fuskana ya sauya nace eh a hankali daga haka ban kara magana ba. Haka yasa ta fahinci akwai matsala duk yadda akayi kawai dai ban fadi bane na barshi a raina. Bayan na bude ledan yaran suka kewaye ni suna na basu na shiga dunbuzowa ina mika masu uwar tace Rama duk ina zasu da wanan haka? Nace Anty nasu ne fa su aka siyawa shi abarsu su sha abin su ai nace da gajiye tazo ta diba. Kiran sallah da aka fara shine ya tayar damu gurin mu ka watse zuwa sallah zuwa yanzu na dan fara sabawa da part dina can muka nufa ni da yaran gaba dayan su. ********* ********* ********* Bayan na idar da sallah yaran nata nasu suna kallo suna gardaman su na jingina kaina a bayan kujera kaina ya na sama. Maganganun hajiyan shi ne ke fado min a rai da take cewa wai yar matsiyata mai farir kafa . Ni dai na san gaskiya ne ni diyar tallakawa ne ba diyar kowa ba a duniya don ubana bamai kudi bane ba basarake bane kuma ba wani babban malami ba a kasa. To amma shi farar kafar da tace min na maynene don a sanina anawa macen data shiga gida aka tsiyace ne wanan lakanin na farar kafa. To ni may ya sa zatai min wanan mugun taken haka mai mumunan saurare da ji. Ita kuma farida bilhakki fushi take dani na aure mata daddy bayan ta kwallafa ranta ga auren shi don tun tana karama ake cewa da ita matar yusuf shine ta rike hakan a ranta har ta girma dashi. Bara ga laifin Zulfa ba da tai masu shamaki a tsakanin ta dashi sai laifina ni da banci ba ban sha ba ga zancen ta leke min. Na dan zakuda na gyara kaina da wuya na yai min tsami nace akwai Allah don shi ya riga yai wanan hadin. Kiran sallah akeyi shine yasa na mike na tayar da sallah isha,i tare da jero adduoi na shafa jinior ya tako zuwa inda nake ya haye min jiki yana cewa abinci zai ci wai. Nace to bari nazo muje sai na baka ko amma ku tsaya ai wanka kafin mu fita na kwashe nai masu wanka sai ga gajiye ta shigo take cewa hajiya tace wai kizo kikaiwa Alhaji abinci dare ya soma yi. Nace to gamu nan zuwa yanzu zan shafawa Amira maine tai murmushi ta juya taje tana fadawa anty. Tace yaran nan maimakon su tsaya nan ai masu wanka shine sai sun tafi can sun sata aiki da wani zataji. Gajiye tace hajiya ai Rahama bata gajiya da yaran nan barsu kawai suyi ta sha, anin su tace aina barsu. Mun fito daga part dina na rufo don anty ko yaushe tana nanata min idan zan fito na dinga rufe kofa don a kwai hanya daga nan cikin dogon coridor din part din mu wanda ya bulla waje ta bayan gida inda wurin zai sadaka da hanyan part din su Zulfa sai falon sai part din maigidan dake tsakiya shine ya raba part din su da namu din. A falo suke muna shigowa yaran na dan wasan nin su anty tace to bissimillahi sun dawo ke nan yanzu zasu saka kan mutum ciwo kenan. Na durkusa na gaida ita ta amsa min take cewa kina can kina biyewa wa yan nan har mijin ki ya dawo yai ta jiran abinci. Nace kai anty wai kuma mijina daddy ne mijina mijin ki dai anty tace ji min yarinya ni dai dauki abinci kikai kada yai ta zaman jiran ki. Saye nake cikin wani dogon riga baki anyi hanayen shi da wuyan shi da material blue yaji duwatsu sosai yana walkiya na daura dan kwalin shi a kaina daurin na dan kwali ba rolling ba. Ina zuwa sallama na keyi amma ba, a amsa min ba na sa kai na shiga falon zaune yake shida Zulfa suna fuskantar junan su sai dai suna gani na sukai shiru. Sai da na jera kayan abincin a kasa na juya inda yake zaune nace daddy ina wuni yace Alhamdullahi. Anty ina wuni nai mata ba laifi don ta amsa min a takaice tace amaryan daddy ke nan ? Kai wallahi kuna bani dariya wai daddy shu wannan suna ai sai a canza shi don abin da nauyi wallahi. Daddy yace sai ki canza mata keda ke jin nauyin hakan ni banga abin nauyi ba anan ? Haka kawai ta wani dinga kiranka da daddy kamar wata yar ka can ko karamar yarinya ne ita yarinya na shigewa da kai daki har safe ta wa mutane kilibibin kiran ka da wai daddy ? Yace ku kuma na gane shine zafin ku ko wai Zulfa may yasa baku son a zauna lafiya ? Ke in kina da hankali wanan yarinyar ai ta gama maki komai idan kinyi dubaiyya irin halarcin da tai maki a baya ? To abin zai kuma zama na gori ne yanzu wanan ai halin zama tare ne amma wanan ai ba zai sa na yarda da kishiya ba ko wacce ke tare da kishiyana a da can baya. Allah ya kyauta yace Rahama shiga ki dauko min charger na bedside yana nan makale. Tankar banji abinda suke fafatawa ba da Zulfa a kaina na mike tabini da kallo yadda jikina yake shocking duk takawan da nayi sai mutum ya dauka yanga nakeyi a hakan. Bayan na shige ne taja wani uban tsaki tare da dawo da kanta gareshi tana cewa wai yaushe wanan kucakar yarinyar har ta koma hakane ban sani ba ? Murmushi yayi tare da gyara zaman shi yace kuna dai zubar da mutuncin ku ga wanan yarinyar ranan da zata fara baku amsa zaku raina kan ku don na tabbatar na bakunta take maku kawai idan kunci gaba ba zata juri hakan ba gare ku. Ko yanzu ma idan zata iya ai bissimillah Hindatu ce ta shigo sai maganan nasu ya tsaya anan. Tana ganin Zulfa zaune suna magana ta dauka maganan girma da arzikine sai ta hade ranta tana cewa dashi. Na dauka kai kadai ne dama magana nazo dashi zan tafi na dawo idan ba zan samu lokaci yanzu ba. Zulfa tace kina nufin in tashi zakiyi magana dashi ke nan ko may kike nufi da wanan maganan taki ? Nan kuma suka kaule da fada a tsakanin su shi dai yana zaune yana jin su sai dakilan wayan shi yake yi kawai. Ina fitowa na samay su a hakan suna ta fitina a tsakanin su ganin na fito ina bin su da kallon mamakin abinda ya kawo masu fina yanzu yanzu don ban ma san shigowa Hindatu ba. Na kara inda yake tare da rusunnawa nace daddy gashi ya dago daga abinda yakeyi yace min tnxs. Maimakon na zauna sai na juya zan bar masu falon lokacin ya dago kai yana cewa dani ina kuma zaki ki bani abinci naci na kwanta. Duk sai sukai tsit suka juyo kamar suna min kallon gareni komawa nayi na zauna daidai inda abinci yake na fara bude kulolin abincin . Tuwon Alkama ne da miyan karkashi danye sai bussashen kifi da yaji da kayan yaji. Ok idan kun gama sai ku bani guri zanci abinci yanzu . Haba dai ai magana kowar mu tazo dashi sai dai mu yi mu fita kawai yace ba yau ba don banda time din hakan kuma . Yana fadin haka ya mike ya sauko daga saman kujeran ya zauna akasa kusa da inda nake zaune yana gyara zaman shi tare da jawo roban ruwan wanke hannun dana aje a gaban shi. Basu baya yayi yana fuskan ta na ina gamawa nima zama nayi a kusa dashi tare da gyara zaman gaf dashi muna fuskantar junan mu. Bussimillah yayi ya soma cin abincin shi haka tasa Zulfa fara mikewa ta fice a hasale itama hindatu tabi bayan ta dama ba zaune take ba tana tsaye bayan kujera ta dafa ne don ganin Zulfa da ta sama a falon tare da shi. Abinci yake ci hankalin shi a kwance ya miko min wayan shi yana fadin saka min cajin wayan nan. Karba nayi da hannu biyu na mike zuwa jona cajin ya dan bini da kallon tausayi. Bai san may yasa mata akan kishi basu da tausayi ba yasan ina dakon bacin ran abinda mahaifiyar shi tai min a raina da yamma. Yanzu su kuma a kan hauka sunzo suna kara dada min wani sabon tention don baki kishi mai kama da hauka don ko kan su basu bari ba kuma wai suna kishin wata. Na dawo na zauna a inda na tashi yake cewa dani ba zan so ace wata rana zaki kasance cikin irin wanan rayuwan ba. Rayuwa irin wanan baida amfani da ace kamar yadda suke caza min kai irin haka Saade take da yanzu zaman garin nan ya gagareni. Bana son rayuwa da fitina irin haka amma sai gashi yau Allah ya nufi rayuwa na da irin haka. A da can baya idan naga mata suna caza kan gidajen su haka nakan ga sakacin kamar daga maigidan yake. Ashe abin ba haka yake ba hakkuri ne da kawaici tare da dubaiyya irin na maza ke sa suna sakawa matayen su masu yawan fitina ido haka. Yau sai gashi na wayi gari a cikin irin wannan rayuwan da ban taba tsan mani zan yi hakkuri irin haka ba. Ya jawo roban ruwan wanke hannu ya fara wankewa yana fadin nasan komai daren dadewa idan ba su daina ba hakkurina zai iya koma min ciwon zuciya. Da sauri na dago kai ina kallon shi don jin abinda ya fada yace kina mamakin hakane ko. Haka din ne zakiji yanzu an kwanta da mutum sai dai a wayi gari ace babu shi bakomai bane zuciya ta gaji da magana nauyi yai mai yawa ya buga. Yanzu dai yan kinji abinda hajiya tace a gaban ki duk da tasan irin rayuwan hakkurin da nake da yaran nan a gidan nan amma ita bayan su take goyo ni nata nine mai laifi . A sanyaye nace daddy kayi hakkuri Allah zai kawo ma mafita dayar dan shi insha Allahu. Allah yasa su gane gaskiya su daina a koma daidai a gidan don ni banga abinda akewa wanan fitinan ba haka. Jan jikin shi yayi ya jingina da kujera tare da zaman dirsha a kasa zo nan Rama yace na dago kai na kalleshi. Yadda yace hakan nayi na dan yunkuro zuwa inda yake din yace naji kince baki san may yasa suke haka ba ko ? Ina a durkushe na gyada mashi kai alaman eh yake cewa dani har yanzu Rahama baki fara so na bane a ranki balle ki faran kishin nawa ke ma ? Kunya maganan shi ya bani sai na koma na zauna zama irin na mai shin cin abinci tare da dafe dayan hannuna a kasa daga gefena. Yace tell me har yanzu da alaman ban samu gurbi ko kadan ba daga zuciyar ki wanda ke ma zai sa kiji abinda suke jin din don ance kishi a jinin ku mata take ? Da zan iya fada danace dashi nafi kowa jin zafin kinshin shi a dan zaman kwana kadan da nayi dashi ya lasa min zuman da ban san akwai shi ba aduniya haka ? Amma na daure na cije bani fatan ko rana daya na nuna wanan irin haukan kishin haka. Bazaki bani amsa ba ina tambayan ki shiru nayi sai can nace dashi na hada ma ruwan wanka ko . Yace kin matsu mu kwanta ke nan ko kunya da mamakin yadda in muna tare mu biyu yake sake jiki yana min magana irin haka. Yace dauko min cajin da kika saka tunda baki bari na kalli news sai mu shige ko ? Nace bari dai na kwashe kayan nan na shiga dasu ciki na dawo ban wa yara adduan kwanciya ba kuma ban sallami anty ba. Yace you can go amma kada ki shanyani anan please kan yaran nan naki masu shagwaba. Na danyi murmushi kawai na mike na fara tattara kayan na fice zuwa cikin gida ban dawo ba sai da nakai ga yin wanka na gyara jikina tsab naiwa anty sallama na koma part din shi. Sai dai ina shiga naji muryan shi sama sama kamar yana fada yana cewa ban son rashin hankali may zai kawo ki nan wanan lokacin. Ki fice min daga falo bani son fitina. Dana fita da ita ina ranan girkin tane na fita da ita din ko kece da girki da zaki zo min da maganan banza ai da kika isa sai kije ki tambaye ta may nasayo mata a ledan da kikaga na shiga dashi. Daidai lokacin na shigo falon don a zatona ma da waya yake magana amma sai naga Hindatu a zaune tana cika tana batsewa. Kamshin turarena yasa ta dago kai tana kallon na ban yi magana ba na kama hanyan bedroom kawai na shige na barsu nan. Bai jima ba naga ya shigo dakin wanka ta shiga ya fito ya tsaya ya gyara ko ina najikin shi ya hawo gado ya kwanta. Rugumoni yayi zuwa jikin shi yana sauke numfashi tausayin shi naji ya kamani na lumshe idanuwa na ina tunane. Nasan cewa tunda har ya iya bude baki ya furta min damuwan shi yau abin yakai mai inda yakai don na fahinci hakkuri yakeyi kawai. Barci mu kayi ranan ba wani abinda ya wakana a tsakanin mu sai dai ina rungumay a jikin shi har safe . Da safe zan shiga school don haka ban bata lokaci ba na abinda zanyi a gagauce na shirya nafito cikin shirina na bayan nayi sallama da duk wanda ya dace na sallama na bargidan. Sai daya tashi ya shirya yazo part din anty nan ya dab zauna tare suke hira da ita tace dashi jita sai hajita ta ganka da amaryan ka ko ? Kamar yadda na bata fuska haka ya bata nashi yace da ita eh sai dai ai kin san halin hajiya. Ban taba tsanmanin zata iyawa wanan yarinyar cin fuska haka ba sai gashi tai mata abinda bai dace ba har tana kiranta diyan matsiyata mai farar kafa for god sake. Subbahanallahi Rama ce kuma mai farar ka mai tayi kuma na farar kafa har yaushe ta shigo gidan ma ? Yace halin hajiya ne baki sani ba kuma haushin ki akan ta ya koma tunda tace kece kikai hadin. Amma kuma kaga Rama bata fada min komai ba wallahi. Asalima dana tambaye ta suna lafiya tace lafiya suke suna gaishe mu ai. Yace bazata fada ba aiko can ta bani mamaki don bata nuna komai ba har muka dawo dama nai mata magana sai cewa tayi dani ai hajiya uwace a gareta. Ji yayi anty tace Alhamdullahi Allah mun gode ma ka fara ganin hasashen da nai maka ke nan akan son auren yarinyar nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, IDAN KUMA KIN KARANTA DAKE DA ALLAH, , , , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH SHI ZAI BI MUNA HAKKIN MU A KANKI , , , 45 Ruwan sama aka tashi dashi agarin tun da asuba ake tsula ruwa ba kakautawa. Hakan ne ya jawo rashin yawan firan wasu daga gidajen su har da mutanen gidan mu don ranan ko yara basu samu hanyan fita zuwa school ba don ruwan yai yawa ga sanyi. Sai zuwa goma da rabi na safe aka dan rage yawan ruwan sai dai still ana dan yayafi mai karfi. Na shirya don dole sai na fita zuwa school din part din anty na shiga wacce yanayin yasa ta dunkulewa a cikin abin rufa. Na gaida da ita muka amsa take cewa dani fita zakiyi ne haka cikin ruwan nan Rama , ? Nace anty dole na fita don kin san rashin fitana ba zai hana aiyi muna karatu ba sai dai wanda bai fita ba yai hasara kawai. Nace ba zan dade ba zan dawo ai har nakai kofa tace kada ki fita baki sallami besty ba fa ko kun gaisa ne dashi da safen nan. Naja na tsaya tare da ce mata a, a bamu gaisa ba da shi yau. Jeki ku gaisa dashi, ai yanzu killa yana falo shi ya fito har ga raina ban so haka ba don idan ban da girki bani zuwa part din nashi hakana. Da sallama na shiga falon suna zaune da Hindatu ta wani dan kwanta da gefen jikin ta a saman jikin shi kamar suna wani maganan arziki ne idan ka gansu. Jin sallama na yasa shi dago kai daga bin computer din shi dake a hannun shi da yakeyi. Wani harara Hindatu ta watso min sai da naji yan hajin cikina sun kada min lokaci guda. Cikin dakewa da gyara natsuwa na nake ce wa ina kwana daddy anty ina kwana ? Tace malama lafiya kika shigo mina muna hutawa ko jarabar taki kuma ya kai ki kasa hakkuri kijirashi yazo gareki. Ke kan tir da halin jaraba wallahi irin naki bazan daukar maki wanan rainin ba don ni ba saar ki bace. Allah ya baki hakkuri anty dama nazo gaida daddy ne na sallamay shi zan tafi school ne yanzu. Ke dan Allah rufe wa mutane baki jarababban banza kawai mara tunane. Hindatu zan saba maki yanzu akan wanan haukan naki keda kike shigowa idan tana da girki ashe kin fita jaraba ke nan. Jaraba kuma ai isa ne a gun miji tayi jaraban sai may tunda har kin fahinci jarababba ce ita. Ya juya inda nake yake cewa ina ga ai ba a tsayar da ruwan saman ba har yanzu ki bari na sauke ki. Ka sauke ta ina ranan girkin nawa zakace zaka fita da waban kwailar mai kama da mage. Ke fice ki bani guri ana mazuru ana shaho ace wai ana fita karatu kullun. Maganan yai min zafi don haka na kasa danne zuciya na na juya na dan kalleta nai murmushi nace ai ko gara dani. Don ni har ina da inda na fake ga fita na kowa yasan inda nake zuwa ashe fitan ma da ake fiye da sau goma a wuni mazuru da sha akeyi sai yau na gane hakan. Dama abinda kakeyi shi kake tsamanin kowa ma haka yake ni banda lokacin haukan ki don ban dauke ki cikin masu hankali ba tun farko. Daga haka na juta na fara tako takalmina yana ba da sauti kwas kwas kwas na fice daga falon ko ba komai dai yau na bata amsa ai. Ina jinta tana hargowa wai fada ban tsaya sauraren ta ba nabar falon na mike hanyan fita zuwa inda kowa ke aje motan shi a gidan. Ina kokarin bude mota naji muryan shi a bayana yana cewa ba nace ki bari na sauke ki ba. Tsayawa nayi har ya karso ya jawo motar da zai fita dashi muka shiga tana tsaye daga coridor tana ta zabga masifa wai ita anci mata girkin ta. Tana kallo ya ja mota muka bar gidan muna fita daga haraban gidan mun dan yi nisa naji wani hawayen bakin ciki ya silalo min a fuskana. Jin sheshekar kuka na yasa yadan juyo ya kalleni baiyi magana ba sai mika min hankicin da yayi. Ban karba ba naji yayi murmushi kawai yaci gaba da tukin shi har muka kai school din nai godiya zan fita yace karfe nawa zan dawo daukan ki ? Nace hudu a takaice na fice daga motar banji ya tayar da motar ba ni ma ban juya ba na shige ciki don ruwan da ya dawo da dan karfi. Ranan haka na wuni a cikin bacin rai har four yayi sai hamza driver ne yazo daukana yace maigida ne ya turo shi ya dauke ni. Na dawo na fara shiga gurin anty na gaida ita ban tsaya ba na wuce part dina ina cire kaya gajiye ta shigo take cewa dani ashe kin dawo ? Na dan kakaro murmushi a fuskana nace nadawo na duba kitchen baki ciki. Tace abinci fa bari na kawo maki nan nace a, a dakin barshi idan nai sallah zan fito sai naci. Har ta juya kamar zata fita sai kuma taja ta tsaya tace Rahama kiyi hakkuri akan sherin matan gidan nan dama hakan shine kishi ai. Dazu bayan fitan ki anyi fada sosai kaca kaca da maigidan da hindatu har sai da mahaifanta suka zo gidan nan. Murmushin takaici na kakaro nace da ita na gode kawai a raina kuma nace ashe shiyasa daddy bai zo daukana ba da kan shi ke nan ? Bayan na fito na shiga gurin anty tana zaune falo na gaishe ta na samu kujera na zauna na dan daga kaina sama ina tunane. Muryan gajiye naji tana cewa ga abincin ki Rahama na karba tare saukowa kasa na zauna saman carpet din tsakiyan falon. Cibi biyu naci sai naji abincin ya fita min a rai ina ta dan juya spoon din na kasa cin abincin alaman ina a cikin damuwa. Rama naji muryan anty na kirana tace kada halin matan nan ya tayar maki da hankali a gidan nan haka halinsu yake ko yaushe. Hawaye ne masu zafi suka fara zubo min shar a idanuwana tace nasan zakici gaba da cin karo da abubuwan bacin rai masu zafi ko yaushe a cikin wanan gidan. Amma idan kin fahinci halin kowa zaki iya zama da su da halinsu don su a kullun burin su ne su ga rayuka ya baci kawai. Basu kaunar suga besty yana hurda da wata mace ko da a tsakanin su ne bayan su. Naji abinda ya faru dake da kuka je gaida su hajiya wanda sam banji dadin jin hakan ba. Sai dai na yaba da kaifin hankalin ki yadda kika nuna a gaban ita hajiyan da kuma shi kan shi maigidan. Hakan da kikayi ya nuna cewa nan gaba ma zaki iya hadiyan duk wani fitinan da zai bullo a gidan nan ko a gare mu. Rama sanin kanki ne ban da wani buri a duniya da ya wuce naga yaran nan, sun samu ingantattacen rayuwa da kulawa yadda ya dace wanda Alhamdullahi zan iya cewa mun samu ko yanzu. Don ni dai banda ta inda zan raina maki akan irin kulawan da kike bawa yaran nan wanda tun yanzun ma sun dsuke ki tankar ni a gare su. Aikin dake gaban ki shine na besty wanda ya kamata ki kara kaimai gurin kara fahintar halin da yake ciki a gida da waje wanda yana da matukar bukatar taimako da surport din mace a bangaren shi. Rama zaki iya komai idan har kin saka hakan a ranki nasan cewa a yanzu nice ke maki shamaki akan komai da kikeyi don kina kawaici a kan hakan nasani. Ina mai rokon ki da ki sake jikin ki kada kiyi amfani dani ki cutawa kan ki ki kwato hakkin ki ga kowa dake son nakasa ki a gidan nan acikin hikima da basira basai kinyi fada a fili ba. Akwai hikimomi na mata kala daban daban wanda zaki iya don kinga bazan tsaya akan ko yaushe nace sai na tsaya a bayan ki ina fada kinga sai a dauka nice nake saka ki yin wani abin. Yau ayi va dadi a gidan nan tsakanin besty da hindatu har sai da mahaifan ta suka zo wai akan may zai fita dake bayan ita ce da girki. Don haka ina son ki natsu ki kiyaye duk abinda zai kawo shiga hakkin wani don ki samu bakin magana idan hakan ya taso a kan ki. Sai lokacin na daure nai magana ina cewa anty ban san may na tsarewa wanan matar ba nan dai na fada mata irin abubuwan da take yawan yi min tun shigowa na cikin su. Rama nasan komai bani dai magana ne kawai don naga kina da fahinta irin wanda ake son mace na gari ta dinga yi. Ba ko yaushe zaka tsaya kana maida martani ba akan abinda ake maka sai idan ka tara rana guda ka tsiyaye shi yafi zafi ga kishi. Yadda kika rufe ido kika bata amsa daya dayace da maganar data fada maki magana daya yasa ta haukacewa bayan itace ta fara fada maki shi. Idan ma tayi ne don neman fitina da son musgunawa yanzu tayiwa kanta ai don taja wa kanta saboda ansaka doka a gidan babu mai fita nan da can bada izinin miji ba kuma. Kamar yadda suka saba a baya sai dai mace ta kada kai tafita duk inda taga dama babu mai magana bayan sun saba da hakan . Gashi yanzu an saka dokan tabaci a gidan kinga sun jawa kan su ba wani ba don sune masu fita ba wani ba. Kiyi hakkuri don Allah kinji Rama kada ki sawa kanki damuwa akan komai a gidan nan. Ki sake jikin ki kamar kowa a gidan kiyi yadda ko wace mace keyi a matsayinta na mata a gurin mai gida bawai ina zuga ki bane kiyi rashin mutunci ga mutane a,a ki dai nuna kema fa mace ce shine zai kwato ki ga wa yan nan don ba fasawa zasu yi ba don halinsu ne. Amma idan kin faso kema zaki samu saukin cin fuska irin nasu zasu rage maki shakiyancin su sosai zasu san kin iya kema. Nai ajiyan zuciya don na gamsu da bayanin ta kuma na gane may take nufi da maganan ta. Nan dai naita tunane ina dan juya spoon din dake hannuna a cikin plate din a hankali naji abincin ya fita raina. Hiran mama Altine ta dauko min shi ya dan kawar min da damuwan da nake ciki. Nake fada mata naso Fatima yar wurin maigari ta danzo min zama na kwana biyu sai dai ban fada mata bane kawai. Tace ai hakan yana da kyau Rama don zama da naka akwai dadi sosai wallahi gashi yanzu naga wata yar kunya da shakku ya shiga tsakani na dake sosai. Na dago nace kai anty ni kuma tace ke mana Rama in ba haka may zai sa ki boye min abinda hajiya tai maki da wanda matan gidan nan ke maki yanzu. Nace ba hakana bane anty bana son kina fama da lalurar ki na kuma kara maki wani akai. Nidai da Allah ya nufa da fanin hakan sai naji dashi tace haba Rama, ya kamata fa ki gode min gaki ga daddy ki lafiya lau bako yadda na tsanmanin kiyi ba ? Kunya ya kamani sosai na dukar da kaina a jikina nace hai anty idan kuma banyi bakice ban maki mutunci ba fa ? Tace cikin dariya to aini dai bance komai ba da kina gida kikaga yadda yau dadi ya haukace da fada gidan nan da kin sha mamaki wallahi. Nace anty ba dai a kaina ba kan sai dai in wani abin can dama ya hada su. Wanan matar tashi da yake ji da ita ko fa tana abu a gaban shi daddy baya daukan mataki sai dai yai kamar baiji ba ko bai gani ba. Tace lalai da sauran ki Rama Allah ya taimakeki, baki da rawan kai dakin gane kuren ki ai. Baki san yadda take taka masu burki bane bai dau yiwa wata wani abin ne a gaban wata hakana sai in kuna ku biyu zaki gane kuren ki ai idan kiyi mai ba dadai ba. Shi besty mutum ne mai baudadden ra, ayi abu mai girma bai faye bata mashi rai ba sai dan kalin abu don haka kiyi taka tsantsan da halin shi don watan watarana. Nace ashe haka daddy yake bari na kara shiga karatun na natsu dashi kada na fada watarana. Kagin tai magana kamshin turaren shi ne ya ziyarci hancin mu sai muryan shi da mukaji yana fadin . Besty yau kuma gulmana kike yi da kaunar ki haka da kanki besty kike gulmana ? Tace rufa min asiri don Allah mu ba gulma mukeyi ba hira dai na duniya mukeyi da yar uwata. Yace in baki hankali ba wanan mai kukan banzan yanzu tana jike ki da hawayen ta don bata da aikin yi ita sai saurin hawaye kan dan magana kadan. Tace Rama ai ba dai shagwaba ba anan ita kuka Jinior kuka shiko Nasir din ta zuciya. Nace hai anty har da ke ma gurin min wanan shedan haka ni kan ina nai kukan jinior mai kukan banza yace see you ni wanan kukan ai na kusa maganin shi don ma tsani inga ana kuka hakana. Dan dago kai nayi cikin kallon mai kama da shauki da ban san ma nayi mai ba nace ni dai ansani gaba cikin shagwaba. Muka hada ido dashi yana tsaye ya saka hannayen shi ga aljihun wandon shi, wa yasaki gaba yace min yanamin wani irin kallo da baima san yanayi ba cikin so. Zauna nake dama irin zaman dirsha, na mike kafana ina dan kadawa a hankali banyi magana ba sai yun kurawa nayi zan mike na fice na basu guri. Sai ya dan jawoni na fada jikin shi wani iri mukaji dukkan mu anty da wani abu ya dan tsikari zuciyar ta don tun shigowan shi ta. Da sauri ta kawar da kanta daga ganin rugumar da daddy yai min don ba zata iya jure kallon hakan ba ga idon ta gashi ya rike daidai kirjina ya matse ni a gaban shi yana fadin ina zaki sai kin fada min suwa suka saki a gaba nace ? Cikin tsigar kauna yake rike dani wanda ina ganin ya ma manta da tana gaban shi a lokacin ne. Muryan anty ke fadin nikan bari na baku guri kada idona ya gano min abinda bashi ba a nan. Da sauri ya sake ni ya juya gareta yana fadin kiba mu guri don may ke kuma don na rike kaunar ki a gaban ki ko may ? Tace kai kaji besty kuma da wani fassara dai ni dai bance ba bari na barku kawai nace ma ko ? Hankalin shi na gurin Anty na samu na sulale falon na nufi part dina, da sauri nima banji dadin kamani da yayi ba a gaban ta don ya barni da nauyi da kunya. Sai da ya dan juyo ne yaga har nafice daga falon bai sani ba lokacin . Tace naga kamar ka manta ina gurin ne ai zaka sake layi ba matarka bace ina hanaka rugumar abinka ne ? Murmushi yayi cikin dan jin nauyi da kunyan ta yasan shima ya dan sake layi a hakan da yayi. Yace kuna dai da matsala ku mata wallahi, dan rike tan danayi yanzu kuma har kinji zafin hakan bayan ke kika halasta min ita ga hakan. Maganan dai kake son yai nisa kawai naga alama amma ni na isa na hanaka rugumar Rama ne ? Kan shi ya girgiza kawai ya juya ya fita daga falon nata itama binshi tayi da kallo don tasan ya kamu da tarkon Rama sosai inbashi ba bai taba rike ko hannun wata mace ba a gaban ta haka balle runguma kuma. Yana fita falon ta har zai wuce sai wata zuciya tace ya lekani part dina kafin ya bar gidan. Ina zaune tun shigana part din saman dogon kujera na dan rufe idanuwana ina kallon yanayin fuskan anty na cikin rashin jin dadin abinda daddy yai min a gaban ta. Banji shigowan shi ba sai jin da nayi ya riko kirjina nai saurin bude idanuwana da sauri nagan shi duke a gabana. May yasa kika gudu muna magana kuma shine zaki barmu ki taho nan ki zauna kuma ? Nace daddy agaban anty fa ka rike ni haka kasan ranta ba zaiyi dadi ba ai yadda ka rike ni. Yace and so what ? Harda rikeki kuma ba zanyi ba a gaban wani don ina tsoron a kirani mr lover, lover ko may ? Nace hakan ba dadi ne ai daddy bazata ji dadi ba kaifa mijin ta ne na aure itama kuma matar kace fa ? Yace ba mai hanani yadda nake so a gidana yana magana yana kokarin kara cusa hanayen shi cikin kirjina a lokacin. Saukan hannun shi ya sani lunshe idanuwa na tare da fadin washhh, don Allah daddy ka bari bafa a guna kake ba yau. Yace shine akace don bana gunki kada nayi yadda raina ke so da gidana ko ? Bai daina abinda yakeyi ba sai cigabama da ya kara na lumshe idanuwa na sosai da kyat na bude baki nace dashi please daddy ka bari mana don Allah haka ba kyau fa ? Da kyau ya jawoni ya matse ni gam a jikin shi yace haka ba kyau sai may ke da kyau akace. Rama iam in need of you ina bukatan ki ina son shan wanan abin sosai a jikin ki ina jin dadin hakan kina da matukar dadin al, amari Rama. Ganin yana kokarin kauce hanya yasa na saurin dan dukawa na zille daga jikin shi nai kasa ya dan kalle ni a kasalance yace rowan su zaki yi min nace inda kake ma yau akwai irin shi a can daddy kada kasa muyi sabon Allah please. Ajiyan zucita ya sauke tare da kada kanshi yace banzaci zaki hanani abinda zuciya na ke muradi ba. Saboda ke na kasa tafiya aikina ina jiran dawowan girki na dana na wuce abinda ka fisheni Rama. Nace daddy kaji ranan ai ba yawa yafi mu fada ga sabon Allah haka ba kyau ai kasani. Baiyi magana ba sai gyara kwalar rigan shi yayi yadan kalleni ya juya ya fice daga dakin nawa kawai. Nabishi da kallo ina jin wani abu a raina shin dadin abinda yai min ne ko tausayin halinda yake cikine a lokacin bandai sani ba.. Daga haka na mike na shiga ban daki na dauro alwala har nai sallah ban daga ba ina wurin a zaunr kunya da nauyin yadda zan fuskanci anty nake ji lokacin. Babu yadda zanyi dole na mike ina saye da hijjabi mai hannu a jikina na nufi part din yara na samu sin dawo. Na shiga suna ganina sukayo kaina kallo daya naiwa jinior na fahinci baijin dadi da sauri na karasa gun su na dan riko shi ina tambayan shi may ke damun shi ne ? Sai ga uwar tafito daga daki itama bata kwabe bijjab din jikin ta ba da tai sallah take cewa ni koro shi ina sallah yazo yana damuna. Nace anty jinior fa baida lafiya ne, tace lafiyan shi lau kalau yake fushi yake na koro shi kawai. Najawo yaton zuwa jikina inda nake tsugune nace ga jikin shi da zafi sosai tana kokarin gardama nace maike damun ka jinior yace goshi na ke ciwo nace da ina kuma ? Ya bude baki zai min magana sai amai yazo mai shar ya amaye min duk jikina da amai ban damu ba duk na rude na da sauri itama ta karaso tana cewa ikon Allah. Har ina gardama ashe ko baijin dadin jikin shi ne haka banyi ta kaina ba sai da na tube yaron na goge mai jikin shi nace gajiye don Allah dauko min rigan shi da sauri daki. Ta fice ta dauko rigan na saka mai na kwantar dashi namike na cire hijjab dina daya baci da aman yaron. Dagani sai dan karamin riga daidai cibina sai dogon wandon dake jikina surar jikina ya fito gwanin ban sha,awa dashi. Na dan duka gurin yaron dake kwance ya dunkule a guri daya ina dan tausa mai cikin shi a hankali. Daddy ne kaman an jefoshi falon a lokacin ya shigo yadda ya samay mu mu uku akan yaron ne yake tambaya tun bai karaso ba mai ke faruwa ne kuma. Juta mukayi inda yake tsaye yanan shigan shi ya nuna ya dawo ke nan ba zai fita ba kuma indai kagan shi a cikin jallabiya a jikin shi. Anty ce take cewa baida lafiya ne sai amai yake ta faman kwararawa tun dazun. Ya nufo inda yaron yake ya dan duka gareshi tare da kura mai ido kamar yana nazarin shi. Inda nake ya jiwo yana may ya samay shi yanzu yanzun fa na dauko su daga islamiya lafiyan shi lau. Fever ne ya kama shi ina ganin sanyin da akayine ya dake shi hakanan. Yace sai da nai magana da na ganshi da dan riga karami haka a jikin shi wanan wani haline irin sanyin da akayi yau za, a sawa yaro wanan dan riga haka ? Yanzu gashi anja mai ciwon haka ga banza saboda rashin sanin zafin kai don may baza, a kula da yaro ba irin wanan ? Gajiye dake daga gefe itace ta saka mai kayan a jiki da zai fita tace cikin sanyin murya wallahi shi ya matsa sai su yake so. Yace don ya matsa shine dole sai su za, a saka mai baida wasu masu nauyi ne da za, a biye mai son ran shi haka ? Ranan munga fadan daddy cikin bacin rai yace a shirya shi su kai shi asibiti a gani . Ni dai ina gefe na makure guri daya don ya bani tsoro yadda yake faman fada haka ido rufe kamar yaron ne kawai dan shi kwaya daya a rayuwan shi. Tare da anty suka fita sai bayan fitan su na sauke ajiyan zuciya. Sai wani lokaci suka dawo gidan yaron ma yayi barci yasha allura da magani. Naso na kwana gurin shi amma anty ta hana tace naje na huta ba ga gajiye nan ba gobe akwai makaranta kada na wahala. Washegari tunda safe na shigo duba yaron yana barci har lokacin na dan dade tsaye anty tace kada fa ki makara Rama. Koda naje school sai da na bugo wa anty waya ina tambayan ta ko ya tashi yaci abinci tace gsshima zaune yana shan tea zamu koma dashi asibiti idan baban su ya fito. Haka yasa hankalina ya dan kwanta naci gaba da karatuna don Allah ya gani har cikin raina ina matukar jin yaran anty a raina. Ba dole na so su ba so kuma na tsakani da Allah ni da uwarsu taiwa hanyan alheri a duniya iri iri wani ma ban iya tuna shi. Sai shidda saura na shigo get din gidan na kai motana inda ake aje mota na aje na fito tare da dan tsayawa ina kwaso takardun dana dawo dasu daga school din. Sam ban kula da suna gurin ba sai dariyan su da naji a lokacin yasa na dan dago kaina su biyu ne a tsaye da gani rakiya tayowa kawar ta wacce na sha ganin ta tana zuwa gidan gurin ta sosai. Daga inda nake ina iya jiyo hiran su bawai a, asirce suke magana ba yadda zanji suke maganan. Kai maza ho shi wai farin fatan ne yaha shi a nan ko may wai ? Hindatu tace kin san yan kauye kamar dabbobi suke basu san makwancin da ya dace da su ba ko ina sai su dauka matsayin su yakai su shiga. Wani za ai wa bRkado kila haka taga anayi a gidan ubanta zama da cin amana don rainin wayo ni da girki ki sa min miji gaba ki fice dashi wai ita karamar yar iska. Wallahi jira nake ta kara gigin fita dashi taga yadda zan mata a gidan nan sai ta raina kan ta yar jakar uba kawai. Ni duk iskancin da rawan kan da yake a kanta kar nake kallon su bawai na kyale bane a banza shiri nake kafin na fara aiwatar da nufi na yar abu kazan uba. Zuciya ne yazo min na karasa fitowa daga cikin motan kawar nata tace ashe ba matar so bace tunda ya barta tana shiga wanan motar da ya sha jiki. A zuciye na karasa fitowa na aje takarduna a cikin mota tare da gyara saitin hijjab dina na ce hindu kike ne ko wa ? Idan baki aiwatar da nufinki a kaina ba ashe ba Adamu kwangila ya haife ki ba. Yar kauye nake kuma Allah yai min zaben makwanci daidai dani don ban raina da kyautan Allah ba akaina. Ni kika zaga lalai yau akwai balai gidan nan nace bala,i a kan ki keda kika kirashi mahaukayiciyar banza da wofi ke wakika fi kishi da hauka. Shiru shiru ba tsoro bane wallahi ke kuma tsohuwar kilakiya na fahinci aure ta gagare ki sai yawon bin gidaje kina kashe aure mota kika ce ba, a canza min ba ko may ? Nace na baki sati biyu ki dawo zaki sha mamaki a gidan nan don kin sara a kan gaba ko . Nace dibeku don Allah idan ni farine ya rude shi a kaina ke may ya rudeshi a kanki shafafen baya ko shafafen gaba mace haka kamar an daurawa kara zani dake. In ba halin aure ba ko auren ma na cinne ai ko a kafa daddy ba zai jaki ba nai tsuki na kwashe su na watsar na juya zan shige naji motsinta tanufoni a zuciye . Shiryawa nayi da nufin tana zuwa tasha mamaki yau amma sai naji muryan Anty tana cewa daga nesa ke Rama shigo ciki hakana ya isa. Tace ke kuma ki kama girman ki ga yarinyar nan wanan ai zubar da kaine shifa kishin nan kowa na dashi amma ya danne nasa don a zauna lafiya. Tace ko zaki shigar matane don dama kece kika tura wa mutane alkakai ai anty tace banda lokacin hauka ni yanzu ma kirana akayi nazo. Muna shiga falo gurin jinior dake kwance na nufa ina kokarin dago shi daga kwance ina cewa yaya jikin jinior da sauki dai ko ? Anty tace yaji sauki ai mun koma dashi yau ma an mai allura na fever din. Tace waiko hindatu na da hankali maigadi ne ma fa ya kira gajiye yake fada mata ta fada min babu lafiya a waje na fito. Nan nake fadawa anty yadda abin ya soma tace kyale ta ai baki yasan abin fadi bai san ansan da za, a mayar mai ba. Na jima zaune ina lalashi jinior na mike zuwa part dina don nayi sallah sai da nai wanka na fito hira. Ban dade da zama ba sai ga daddy ya shigo falon fuskan shi babu annuri a cikin sa. Gurin jinior dake zaune ya nufa ya dan yi hira dashi can ya dago kai yace Saade may ya faru tsakanin Hindatu da Rahama a gidan nan har ta zagi ubanta ? Shiru falon yayi ba wanda yai magana yace ba tambaya nakeyi ba kun kyale ni nan ba babu amsa kowa shiru yayi. Yace gaskiya bazan dauki kishin da zagin iyayye ba a gidan nan har yaushe Rahama ta shigo da zata dinga zagin iyayyen na gaba da ita haka cikin rashin sanin darajan su. Tacs dakata besty itama Rama ai matarka ce ita da ta fara zagin iyayyen ta nata sunfi nata daraja ne ko may ? Idan da ta rike girman ta ai da bai kai ga haka ba mata ke nan kullun bata son a zauna lafiya ita ? To itama Rama ta gaji da cin mutuncin da ake mata yau ta tsaya ta rama . Yaya zata zagi iyayyenta don ta rama ace kuma ya zama laifi wanan ai zalunci ne don uba baifi uba ba ai. Idan bata son a zage ta ta daina zagin iyayyen wasu ba kowa ne za, a zaga ya kyale ba haka har da tanayi kawar ta nayi don tana matar so a gidan sai a kyale ta ta taka kowa yadda take so komay ? Yace koma may tai mata bata jira na dawo ta fada min shine zata tsaya harda zagi irin haka bazan dauki wanan shashancin ba gaskiya. Tace aiko da sake wallahi don ko ba zan hanata daukan mataki akan hai,inci ba. Naga alaman da sanin ki ake komai haka don gashi kin nuna min zahiri nagani na kuma gane komai ? Nan suka fara mayar wa juna da magana a tsakanin su a raina nace lalai yau na tabbatar kuwa hindu yar so ne kamar yadda ake fadi a gidan daddy. Nace anty don Allah kiyi hakkuri ba zan so ganin wanan ranan ba a tsakanin ku haka. Don haka anty indai don nice ya kwana gidan sauki dama ban sauke ba balle a tayani azawa gara na bargidan nan ku zauna lafiya yafi tunda don ni ake wanan fitinan haka ? Na dire karshen magana na ina mikewa tare da kama hanyan fita part din raina a bace. Ina fadin ai talaucin da take min gori ko yaushe a kan shi ba fin mu tayi ga Allah ba ya bata. Daga haka na fice na barsu ina fita anty tace nasan za, a rina don mai hakkuri bai iya fada ba. Yanzu kai daga kaji zancen ta shine zaka zo ka hau mutane da masifa in ace kullun abinda ake ana fada maka ne ai ba, a zaman lafiya gidan nan. Tsuki yaja ya fice daga part din ina shiga part dina kuka yazo min yanzu shi ke nan don ya kasance anmin dole sai kuma aita musguna min ban ramawa ko may ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, DON HAKA CIN AMANA NE YAR UWA , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA NA BARKI GA ALLAH YABI MIN HAKKINA AKAN KI NA CIN AMANAN , , 46 Tun wanan ranan na kama kaina ban shiga tsabgan kowa agidan tun safe nake ficewa sai shidda zan dawo gida. Na dan shiga gurin anty na gaida ita daga haka kuma sai gobe ko zaman hira banayi idan tai magana sai nace karatun exam na keyi shiyasa. Ido ra samin wani lokaci gajiye kan shigo mu dan yi hira ta dan min magana mai kama da nasiha ta wuce. Gaiwan da nakeyi wa matan gidan yanzu na daina sai dai su wuce in wuce idan mun hadu su bini da harara. Yaran ne kan shigo duk dare mu dan bata lokaci dasu wataran inda sunyi barci tare zamu kwana dasu. Yau Na dawo da yamma lis duk da agajiye nake kuma yamma yayi sosai ban wuce ba na shiga na gaida anty tace min ya karatu nace Alhamdullahi. Daga haka na wuce ciki nai wanka nafito da alwala na tayar da sallah na dade zaune a gurin bayan na gama adduoina na shiga tunanen duniya. Sallaman anty ne naji ta shigo har bedroom dina ina ganin ta namike zaune ina cewa anty ina wuni. Bata amsa min ba ta samu guri ta zauna tare da kura min ido na tsawon wani lokaci gyara zama na nayi da kyau don nasan tunda naganta magana ne yakawota guna. Tsawon dan lokaci mu haka da ita ccan tace dani Rama haka zamuyi dake yanzu ? Na dago kai a hankali na dan kalleta sai kuma na dukar da kaina a kasa tace ban taba zaton tun yanzu zaki iya watsa min kasa a ido ba haka ? Nace anty ni kuma tace ke mana Rama dan maganan da akayi ya wuce kin rike shi a ranki kina ta fushi da kowa a gidan. Kina ganin matakin da kika dauke shine mafita a gare ki ko may ? Nace anty gara na bar masu mijin su kowa ya huta tunda nice matsalar su agidan. Dana zauna ina jawo maki matsala keda mijin ki akan gaskiyana fa ya rufe ido a gaban mu yai maki rashin mutunci. Bazan tsaya don ina yar kauye diyar tallkawa ba adinga ci min mutunci da mahaifana da basuji basu gani ba. Shine matsalan ki ke aiko in kishiya ne har fiya da haka zakiji a gareta tunda burin kishiya shine kullun taga bacin ran kishiyar ta a fili kinga sunyi nasara akan mu ke nan. Amma kina haka basu ba koshi may gidan dariya zai min yace aigashi abindana shuka tun ba aje ko ina ba ga abinda aka girba akai. Tausayi ta bani tunda ita har yanzu gani take a ranta itace ta sa daddy ya aure ni bawai yana so bane yayi. Namiji fa mai mata fiye da daya dama haka yake idan halinsu ya motsa basu tsaya bincike sai dai su yanke hukuncin da suke gani shine daidai a garesu. Haka halin maza yake kin sani ra, ayin kan su suke bi bawai abinda sharia ya kidanya ba. Nace anty ni kan ba zan tsaya kullun ana zagiki da iyayyena ba kuma ace mutum wai kada ya rana dan ta fada min na fada mata shine kuma zai zama laifi anty ? Ki daina wanan maganan Rama abinda ta fada mashine yai amfani dashi amma nasan ai zaizo ya gane gaskiya wata rana da kan shi. Nace ai ba sai ankai wata rana ba mijin su daine na bar masu abinsu ba shi ke nan ba dama don kine na daure nake wanan rayuwa yanzu ko anty don Allah a hakkura dai hakana. Ke yanzu matakin da ki ka ga yafi maki ke nan Rama watau ban isa ba dake ke nan yadda nake tunane a baya ? Nace anty kin isa ke ma kin sani da ba don ke ba wa ya isa yai min haka a zauna lafiya sanin kankine duk abinda nake akan ki nake yin shi a duniya. Tace to naji na kuma gode don nasan kina min bawai ban sani bane Rama ? Yanzu fada min matakin da kika son a dauka nan gaba nace wani mataki zan dauka anty banda na bar maku mijin ku na koma gaban iyayyena ko kasa suke ci su kwaba su bani yafi min darajan akan wanan irin balain haka. Fitinan safe daban na rana daban kullun cikin tunane da zulmi gari ke wayewa mutum don bai san da wacce za, a tare shi ba duk kuma baka tsira ba kaine mai laifi dai. Tace ashe Rama da sauran ki ina cewa kin kai ashe baki kai ba dama hakan ai shine kishin . Idan zaki jawo mijin ki ku zauna lafiya yafi maki inkuma kince ba zaki tausasa zuciyar ki ba akan kishiya kinaji kina gani ki koma yar kallo da reno a gida. Don hakan da kikeyi ba zai kaki ga komai ba akarshe sai tarin nadama da dana sani nan gaba. Nace idan na zauna ganin kwam ke nan a cikin ku anty exam nake jira na gama next week na kama gaba na don ban zama a na wullakantani har abin kema ya shafe ki. Lalai ma Rama wai kina hauka ne ko may da kike fadin wai ke zaki tafi zaki tafi ina wai ? Har kina ikirarin kin bar muna mijin mu kishiyace zakiyi fushin zuciya kice kin barwa miji Rama aiko in haka zakiyi wataran za, ayi bake wallahi. Nace ni yafi min anty nagaji wallahi bazan iya ba ai tawa mutum cin mutunci har iyayyen shi in kuma kai magana ka rama ace ka taba matan gida a sauke ma balai. Ni dama nasan Allah ne ya jefoni cikin ku ba wai son raina bane don bazan iya wanan bakin fitinan ba haka. Gara na bar gidan kowa ma ya huta in dai don nice ban ko sauke ba balle ince a tayani azawa akai. Wai ko Rama kin ko san aure kuwa auren ma kuma na mai mata da zaka zauna da kishiya ? Nace ai in ban sani ba yanzu na sani tunda zahiri nan na gani akan gaskiya na akaci maki mutunci. Badai ke akaciwa bani akaciwa ko kuma ni din dakike jiwa na sake kece bazaki sake ba ke nan. Ashe hasashen da nake a kan ki na zaki iya ashe abin ba haka yake ba ke nan tun yanzu gashi kina son watsa wa mutane kasa a idanu. Na dauka ko a bayana zaki rike min alkawari ashe ni ke haukana agurinki abin ba haka yake ba. Kina ganin idan kinyi haka kin kyautawa iyayyen ki damu ke nan Rama. Anyi magana kice ke zaki wuce zaki wuce zuwa ina don dan wanan magana kawai. Nace anty da na zauna ana min sheri ace kuma ban magana don ana takama da an fini asali ko wani abu gara na bar gurin tun ana sheda juna da ido biyu. Na dukar da kaina wasu irin hawaye suka fara zubo min a lokaci guda ina fadin ni ban iyawa anty gaskiya mijin su daine yasa suke min haka ko to na bar masu abinsu azauna lafiya. Kuri tai min da ido tana kallon yadda nake kuka cikin tausaya min don tasan cewa itace tasani cikin wanan rayuwan haka da nake ciki. Ga dukkan alamu magana na ya shigeta sosai don tasan nikeda gaskiya ga maganan babu dai yadda zatayi ne kawai akai. Sai dai duk irin yadda nake ji bazata bari na tafi ko ina ba don tasan bacin raine yake damuwa na haka irin namaza da suke kunsawa mace. Don ko ita da farko ta dau abinda zafi amma yadda taga na dauka sai take gani idan batayi saurin kawo iyakar abin ba zai iya jawo matsala fa kowa ma. Naji tace yanzu dai kin nuna min ke nan ni bban isa dake ba Rama kin daina jin maganata ko ? Cikin kuka nadago nace anty ba hakana bane don Allah kiyi hakkuri ki barni na tafi gidan mu ki raba wanan auren da babu komai a cikin shi sai bakin rigima da rashin kwanciyar hankali komai nayi a gidan nan ba fita zanyi ba . Don ni nazo na samy su da mijin su kinga kuwa idan nace na nace sai na zauna nan gaba abinda za, ayi min sai yafi wanan ma . Don Allah anty ki barni in tafi ki huta su huta ba sai ina nan ba za ai fitinan dani. Kiroka min a sallamay ni na bar maku gidan ku ku zauna lafiya dakowa shine mafita. Na karshe maganan ina mai fidda sautin kuka cikin ban tausayi ita dai ido ta kura min kawai tama rasa may zatace dani a lokacin. Idan anki sakin fa ? Muryan daddy ne da bamu san yana tsaye daga kofa ba yake magana tare da karasa shigowa dakin kai tsaye hanayen shi zube cikin aljihun shi. Dagani har ita muka daga kai muna kallon shi don ba wanda ya tsanmanci zuwan shi a wanan lokacin. Nace aiko ba saki zan tafi don shine sauki a gareni dana zauna inda matsayina baikai ba ana zagina da iyayyena idan nai magana ace naiwa matan gida rashin mutunci haka. Ban saba sakin mace ba ni a rayuwana don haka in ma shine gurin ki a ranki kiyi gagawan kawar da wanan shawaran don baki da nasara anan. Laifi kikayi kuma nai magana kewaye da baza, a maki magana ba kan abinda bai dace ba kice ke baza, a gyara maki ba ? Nace ai wanan ba adalci bane daga jin maganan mutum daya sai azo a samu sauran da fada da cin mutunci ni gaskiya wallahi bazan iya ba. Don ana takama anfini anfi iyayyena sai na zauna a na takani yadda akeso har da baren gida kuma ace kada na rama. Wanan yanzu matsalarki ce wanan nidai ba zan yarda ana min rashin tarbiya ba agida na kyale ko ma waye ? Nace ni duk wanda ya sanni bai cewa banda tarbiya a cuce ni kuma nai magana karo na farko ace banda tarbiya ai Allah na gani yasan mai gaskiya. Yace hmmm haka kuke ashe duk mata ke kingani da idon ki ba labari aka baki ba ko yake cewa anty hakan ? Ya juya zai fice daga dakin nace ai ita tasan halina bazatai min hukuncin da bashi ba akaina. Anty tace ana magana kuma ka juya zaka wuce ba akai karshe ba. Yace may kike son nace mata kuma bayan kinji magana tun farko zagine bani so ko ita ai nai mata magann haka. Daga haka ya juya abin shi ya fice anty tace kin gani kinga galin maza ke nan shifa bawai ya rike maganan bane fa yayi a lokacin kuma ya wuce gareshi. Nace ya wuce mana tunda ita an mata yadda take so taji dadi tai dariya tace anya Rama ba kishi kika fara yi ba kuwa ? Nace anty aiko kishi nake ba zan so na jawa wani halaka ba a rayuwa su dai da suke kishina zan bar masu miin su a huta. Don Annabi yace kasowa dan uwan ka abinda kakeso wa kan ka ba zan yarda don ni ki zauna ana bata maki ba haka. Tace to ni dai na baki hakkuri kiwa Allah kibar zancen nan hakana don Allah dai ya wuce hakan ma da kikayi ya isa. Don ko ba komai gobe idan wani abu ya faru a tsaya ayi bincike kafin a farwa mutum daya. Don Allah kiyi hakkuri ki koma normal kamar yadda kik da farkko da kowa kinga ko yaran ki yanzu da sun fara damuwa da rashin ki. Ta mike tace na barki lafiya komai ma ya wuce don Allah ban son a kara tayar da zancen kuma. ********* ********* ********* Ranan da zan karbi girki nayi komai sai dai kafin ya dawo masalaci har na jera komai na dawo dakina na zauna don nasan idan anty ta fahinci wani abu zatai min magana. Ko da daddy ya dawo daga sallah ya samu abincin shi a falo sai dai bani a cikin falon kamar yadda na saba idan nakai na zauna sai yaci na kwashe kayan. Haka ya zauna zuciyar shi a vunkushe ba dadi ko kadan ya dan taba kadan ya bari duk da abincin yayi dadi kuma yasan nina girka shi da kaina. Shiru shiru baiga na shigo ba yanayi yana kallon agogon falon har gooma saura ya mike ranshi a bace zuwa cikin gida. Part din anty ya biya bani ciki sai yara dake kallo ya shiga gurinta yai mata saida safe ya fito. Direct part dina ya nufa kofan yana a rufe ya murda sai yaji shi abude yake ban riga da na rufe ba ko. Ina zaune a kasa nayi rigingine da kaina a saman kujera idon a rufe ina karatun kur,ani da kai ina dan juya kafana daya dake a dage. Yashigo har yai tsaye a kaina ban sani ba sai kamshi shi danaji yasani gane yana dakin. Na dan bude idanuwa na a hakali na gan shi a tsaye akaina na maryan na rufe tare da kai aya na sadakallahul azeem. Yana tsaye dai ya kura min ido baiyi magana ba sai yakai zaune saman kujera. A hankali ya mika hannun shi ya dan rugumoni na jaye jikina sai ya dan sauko ya kama yatsun kafana a hankali yana dan ja cikin tsigar wasa. Ina jin hakan har cikin raina sai na dake kawai ban yarda na sa a raina ba balle abin yai tasiri a jikina. Ganin ban bada wani reaction ba yasa naji yace humm Rahama ashe haka kike da riko ban sani ba. Yana batun rugumoni na ware idanuwa na nace please daddy stop nace daddy ina ganin kimar ka da darajan ka sosai dakai da matar ka shiyasa nake rage wani abu. Ni ba yar kowa bace kuma ba yar birni bace face yar kauye fakiriya kamar ko wace yar tallaka. Yana jin abinda na fadi naga ya mike ya koma saman kujera ya zauna yai shiru can naji yace. Rahamaa zauna da kyau muyi magana dake bani son irin wanan rayuwan da matana sam. Jin abinda ya fadi yasa na dan kara gyara zamana don girmamawa gare shi. Yace nasan kin san dai aure mukayi wanda ake ganin a bisa kaddara mukayi shi ni dake. Amma iyanzu dani dake mun san aure ne na so da kauna mu Allah ya tabbatar muna akan mu. To dan may kike kokarin son tarwatsa muna farin cikin mu a hakan da kikeyi yanzu ? Wanan abin da kikeyi zai sa dani dake dama antyn ki ai muna dariya don idan tayine daniyar fanshe haushi to haushin ta kara akaii. Duk macen da kika gani a gidan nan nasan halin kowa a cikin ku dakuma haka nake zama da kowan ku. Yadda na dauki kowa a gidan nan haka kema na dauke ki don a matsayi daya kuke gare ni. Idan naa kyale ki har kika saba da zagin iyayye irin na Hindatu haka zaki saba dayi kema baki jin nauyi da kunyan yin haka ga kowa. Amma ni magana ta nayi shine akan gaskiya sai dai ku kun kasa fahinta saboda akidar ku na mata. Koda ban gurin kukai fadan nasan wa zai fara zagi a cikin ku amma sai na fifiita ki nai maki fada don ki gyara tunda ita nayi nayi ta daina ta kasa bari ya zama mata hali zagi a bakin ta ba komai bane ita a wurin ta. Nace amma daddy shine zaka hada har da anty kai mata tas matar dake iya kokarin ta akaina akan may zan zauna ana bata mata rai sabodani ko yaushe bayan tana fama da kanta. Yace nafa san abinda nakeyi Rahama ita saade da tasan halina aikin ga bata dauki abinda zafi yadda kika dauka ba ke. Daddy ni banin son har wata rana magana ya kai ga hajiyan ka tazo tai min yadda naga tawa anty kaga kawai ka sauwake min kowa ya huta tun ba, aje ko ina ba. Tun yaushee hajiya taji zancen ai sai dai kada akara kawai amma tun ranan mahaifiyar hindatu tai mata waya. Nace daddy kagani don Allah kayi hakkuri hakana don gudun abinda kaje ya dawo kuma don kaga laifin zai dawo ne ya taru akan anty daga baya. May kike nufi da hakane wai Rama kekina tunanen zan iya rabuwa dake ne ko may a yanzu ni sakin mace baya a cikin tsarina ko yana ciki bake ba kuma. Wai ma may kika dauki aure ne ke kina daukan aure abin wasa nagani ko ? Daga yau ki cire irin wanan zancen na zaki bar gida a ranki don ba a gida na ake wanan maganan ba. Nai haukane da zan samu zukekiyar mace kamar ki na saka akan dan maganan da bai taka kara ya karya ba. Don haka ki cire komai a ranki ki tashi muje ki bani hakkina dake kanki kada ki cuta min da yawa. Kin hana ni ganin fuskan ki kwana biyu kin boye min wanan surar da nake gani naji sanyi a raina yanzu kuma zakice abinda Allah ya halsata min ma zaki min rowan shi to ba zan iya jure wanan ba gaskiya. Don ya fita ya barni sai kawai na saka mai kuka wiwi maimakon ya tashi sai ma daukana yayi cak zuwa cikin bedroom dina Allah ya taimake ni tsab nake don bai kyale ni ba duk da kukan da nake sai da ya samu gamsuwa a gareni. Ranan anan dakina ya kwana sai safe warwas yafito duk matan gidan sun fahinci komai ni abangarena koba komai na gwadawa hindu nima din mace ce kamar kowa duk da ni diyar tallkawane da take gani. Washe gari ban fito da wuri ba kuma ba zuwa school don haka na baje nai hutun gajiya nai ta barci abina sai sha daya na tashi don banda damuwa nasan anty zata bashi abin karyawa idan ya nema. Na tashi nai wanka na shirya na nufi gurin anty mu gaisa yaran na gida su suka fara tarona. Nashiga daki tana zaune tana waya na samu guri a gefe na zauna har tagama wayan ta juyo gareni tana fadin kin tashi Rama ? Nace ina kwana anty tace kin dai huce naga alama yau sai dai ashe haka kike baki ita turewa Rama ? Murmushi nayi na dukar da kaina kasa nace anty ba hakana bane tace to komai mutum zaiyi idan an bashi hakkuri ana son ya sake yabar anin don gaba. Nace nagode anty tace may ye na godiya Rama yanzun dai ki tashi ki batun ba mijin ki abinci na bashi na safe saura ki na rana don bazan daukar maki ba. Na juya ina dariya nace kai anty ki dai cika ladan ki mana tace dayake baki da tausayi ba. Zama nayi falo muka dan yi shirmay mu da yara hiran game ne muka taba karshe nace kowa ya kawo min haddan da akai masu atare dasu muke biyawa. Haka uwar tafito ta samay mu muna karatu tace Rama rana fa yayi kin san yau weekend ne da wuri may gidan zan shigo gida. Nace yanzu zan tashi ta koma tana kallon mu yadda nake ma yaran gyara karatun boko ne bamu samu yi ba nace sai da yamma zamuyi shi. Namike ina fadin oya Amira taso muje kitchen muyi girki shima Nasir ya mike yace little mum nima dani za, a nace mu tafi shima jinior ya biyo mu. Abinci lafiyye na hada kamar ranan za, ai wani bako ne sai biyu muka kammala komai a gurguje naje nai sallah nai wanka na shirya cikin dogon rigar material mai ruwan dark blue da kore. Dinkin shi mai dogon hannu ta hannuwa an mai stly ya baje haka kasan rigar ma free stly akai min. Kamshi kawai ke tashi ban dade da fitowa ba sai ga daddy ya shigo nan aka shiga gaidashi kunya da nauyin shi nake ji na kasa dago ido na kalle shi. Yace akai masu abincin shi saida ya fita da yan mintoci na mike nace oya azo muje mukaiwa daddy anbici yau weekend ne muyi hira da daddy suka mike cikin jin dadi mukarbar anty da Gajiye kawai. Yana zaune da waya magana yake a hasale koda muka shigo ya dago idanuwan shi da suka nuna akwai bacin rai a cikin su ya sauke a kaina. Simi simi na fara aje kayan tare da gyara wurin sai naga duk falin ya hargitse min kwana biyun da nayi. Ban zauna ba na juya na dauko abin gyara na gyara komai tsab na har ya gama waya na dawo gurin su. Hira yake da dariya sosai da shirmay da suke zuba mai kowa na fada mai abinda zaiyi idan ya girma. Da Amira ya fara tace ita idan ta girma police zatayi ta tare hanya da bindiga nace kai Amir police kuma tace eh mum bakiga police din hanyan school ba na tsaya a hanya duk wanda yazo na harbe shi Nasir yace karya kike yi ko mummy nine sojan little mum na harbe kowa har da maman ihisan dake sa little mun kuka. Cikin harshen turamci daddy yace you see what you people are course to my children they start hetting people with dis eges. Sai yace kai Nasir soja ai ba halbi yake yadda yaga dama ba yace daddy ni dai soja zanyi bakaji little mum na kirana da sojan ta ba. Nan ya shiga jero muna haukan wa yanda zai halba in ya zama soja sai dariya uban keyi yana tambayan shi may zai sa ya halbe su ? Yana fada mai laifin da sukai mai yace Amira tace har da gajiye zamu halbe idan bamu tashi barci ba sai taita dukan mu ko in zata muna wankan safe tai ta zagin mu a bathroom. Nasir cikin halin nan na shi yace eh da ita zan harba first ranan kin manta ta doke ni wai na balla buttle din uniform dina. Banji dadi ba yadda suke maganan abinda gajiye ke masu haka shima uban sai naga ya lumshe idon shi. Hindatu ce ta shigo falon ta samay mu cikin raha haka da yaran ta ce ashe ka shigo yace eh, tace tana son zuwa unguwa ne dama. Wai ke hindatu shi fitan nan kullun sai anyi shi ne jiya kin fita fa yau kuma kice fita zakiyi kowa na gida da yaron shi yana weekend. Bin yaran tayi da kallo tace eh ai na gani tunda ga yaran so an tara ma a gaba sai dariyan ka akeji tun a waje suko wa yanda ba, a so su mutu. Ni bance ba in ma sun mutu kwanan su ne ya kare tace ana dai makirci a gidan nan wallahi. Idona na dan rintse kamar na bata amsa sai na daure muryan daddy ne kecewa makircin may kuma akayi ? Tace ai dai akwai Allah don ko wani dama haihuwan shi akayi baga dalilin ware wasu ba anan kana hira dasu. Yace kin bari yar ki tana hurda da yan uwanta ne ko tazo ne aka kore ta nan din tace tazo nan yin may cikin ku ta gane may anzauna ana maka wani kilibibi haka. Yace dakata ya isa haka na idan shi ya kawo ki kaman hanya ki fice min uguwa dai ne ba kuma yau ba ba mai fita gidan nan yau. Eh da yake mune ba amma wa yanda ake so ai su ko yaushe fitan su sukeyi ko ba tambaya. Yace bako a gidan nan ba yanzu duk macen da zata fita dole sai da izinina idan kuma mutum ya isa ya fita ga kofa a bude ai. Ko bani gari kuma mace ta fita bada sanina ba nace ban yafe ba fakat abinda ba, a yafe ba ai yawa garesu gidan nan tunda wasu don milki da isa har dakin su ake binsy akwana can. Yace na kwana ina dakin matana na kwana ba dakin farka ba dai ko gida nane ina da right din da zanyi abinda nake so. Wata fi a gidan ita da kake kokarin fifitata haka yace ya ishe ki haka kifice min da fitinar ki da baki da aiki sai tsegumin tsiya kullum. Tsegumi kan ai kowa nayin shi bani kadai ba in ma kayi ne don ka gyara ma ta rai saboda ita yar gwal ce tayi fushi to ka sani yadda ka kwana da ita dakin ta kowa ma sai ka kwana a dakin shi. Yace to ki jirani nazo kwana dakin naki get out from here mara tunane kawai ke kullun da sabon fitinan da zaki bullowa mutane dashi. Ba sai ka koreni ba ai fita zanyi dama ba zama nazo yi ba ra, ayina ne na fada ta juya tafice tana fada har ta bace yai tsuki ni kuma na sauke ajiyan zuciya inda nake. Amira ne tace kai maman ihisan fada fada da duka ranan ma akan ihisan ta daki jinior wai ya ciji ihsan kuma fa daddy ihsan ce ta shanye mai swwet din da little mum ta ba mu. Amira bana hanaki yawan surutu ba hakana tace tana kama bakin ta na bari little mum. Yace ai ki barta ta fadi anyi ne tunda kikaji sun fada tayi ne don bata da kai, ko kadan. Ina kwashw kayan da sukaci abinci sai ga Zulfa ta shigo tana ya mutsan fuska ta samu guri ta zauna saman kujera. Tace zan tare da bin kowa da kallon sai ta sauke ajiyan zuciya tace dan fita ne nazo fada ma. Yace ba fita yau ko ina yanzu hindatu tazo na fada mata hakan ita don haka ku barni in huta please. Inda yaran suke suna wasannin su takai ido ta bi su da kallo cikin takaici ni dai ina daga bayan kujera na tsaya tare da dafa makarai yan kujeran ta baya daidai saitin daddy din. Batai min magana ba nima ban mata magana ba ta dan yi jim kamar zatai magana sai kuma ta mike ta fice rai bace. Na sauke ajiyan zuciya a hankali na ce a rai na gidan danger ke na wanan gida kowa da tashi kalar fitinan. Mun dade tare da daddy da yaran da alama yaji dadin samun lokacin da ya danyi dasu. Ina ganin uku da rabi nace dasu oya muje mubar daddy zaiyi sallah muma zamuyi sallah. Suka fita da murnan su muka kwashe kaya zuwa cikin part din anty nakai kitchen idan na idar da sallah nazo na wanke su. Bayan na idar da sallah ne na dan zauna da casbi a hannuna ina ja a hankali cikin lumshe idanuwa na daga inda nake zaune. Tunanen rayuwan gidan ne ya tsaya min a rai na sosai nace wanan indan mutum bai yi da gaske ba sai ciwon tunane ma ya kama mutum. Da dare sai ga kiran wayan daddy akan duk muzo mu falon shi yana neman mu. Nice ta kusan karshen shiga don ina bayan anty tana gabana mun samu su saraki matan gida a zaune a kusa dashi. Na kula haka sukeyi idan ya kiramu gaba dayan mu sai suyi saurin fitowa don kawai su zauna a kusa dashi. Ni dai ina zuwa na zauna kasa a gefen kujeran da anty na take zaune a kan shi daidai saitin kafan ta. Yana ta aiki a cikin system din shi bai kula kowa ba a cikin mu har tsawon wani dan lokaci. Sai can ya dan sauke numfashi tare da dago kai yana kokarin rufe laptop din nashi a hankali tare da fadin yaiwa kun zo ko. Ya fara da bissimillah yana cewa dama nace a kira ku ne don ni tafiya ya kamani zuwa Australia. Don haka nake son naji wace keda tafiya a cikin ku dan ina ganin zanyi wata uku ko hudu ban dawo ba. A take gurin yai tsit bakajin motsin komai sai na na,uran da suke aiki a lokacin. Kowa tana sakan zuci sai anty ne tai magana farko tace badani ba cikin wanan tafiyan gaskiya. Nidai ina zaune karatu ma nake a cikin wayana ba sauraren su sosai na keyi ba. Daddy yace nasani amma dole ne abaki hakkin ki akai ai. Sai shiru ya biyo baya can dayaji shirun yai yawa yace ku nake saurare fa. A lokaci daya suka hada baki gurin cewa dani zaka, sai yace to ban fahince ku ba dai ? Wanan tace da ita wanan tace da ita yana jin su ya lumshe idanuwan shi sai da suka ishe shi yace a tsawace stop . Kada kuyi min hauka anan ba shi na kira ku ba don Allah duk baku da tunane da adalcin gava dayan ku dakuke wanan haukan haka ? Inda ku masu adalcine da sanin ya kamata bazakuce naje daku ba sai dai kuce na dauki Rahama mu tafi da ita. Nima ba don uzuri ba babu wani tambaya da zan tsaya yi don nasan ita ya dace naje da ita din yanzu. Hindatu tace tunda tafi mu ko may ko kuma mu bamu da hakkin zuwa ne daba za, a damu ba? Zulfa tace nasan hakane ya kamata amma sai tun farko banji ka fadi hakan ba shiyasa nai shiru. Yace naso zuwa da Rahama sai dai karatun da take yi bai son wasa acikin sa wanan uzirin ne yasa ba batun zuwa wani guri da ita a yanzu. Amma ku sani nan gaba inda halin hakan za, a maimaita tafiyan idan hakan ya taso. Don haka daga cikin ku ina son naji wacce za, a tafi da ita din ? Sai kuma gardama ya kaure masu basu ko tsaya batun jinda sukayi yace nan gaba za, a maimaita tafiyan dani ba. Nice na dago kai ina cewa amma sai naga kamar tafiya da anty Zulfa zaifi don taje ta samu kara ganin likita a can don lalurar ta. Ke muna fuka waya saka bakin ki yar bakin ciki ni zakiwa bakin ciki ko bukulu ? Ta na gargade ki da kiyi gagawan fitar da bakin ki cikin maganan nan don babu sa,ar ki anan kaji min yarinya karama da iskanci. Nace wallahi yarinya na bayar uwarta daga fadin gaskiya sai ki dinga fadar magana wa mutum kamar kin haifi mutum ? Magana ce ta gaskiya ake so shina fada amma idan nayi laifi kiyi hakkuri don Allah ? Kaji kilibabba ki gama nuna min kiyayya yanzu a filin Allah kuma ki dawo kina wani yin hakkuri. Ni dama can nasan babu mai kaunata a cikin ku da kike cewa aje da Zulfa may Zulfa ta fini da za,a da ita ko kuma may zata je ta tsinana mai a can. Muryan shi ce yace Zulfa dama nima tunane akanki yake sai ki shirya mu tafi aje a duba lafiyan ki dana baby a can. Shi ke nan kuna iya tafiya har anty na batun mikewa yace na tuna dakata sai ta koma ta zauna kawai bata dai yi magana ba ita. Yace Rahama shiga ki dauko min briefcase dina a ciki wana ashh colour din, zaki dauki min nace to tare da mikewa zuwa daukowa. Bayan na dauko ne na mika mai cikin girmawa ya bude tare da kirga kudi ya ce zo karbi ki mikawa antyn ki wanan tare da ci gaba da kirga wani. Ina mika mata na samu wuri na zauna ya kirgo ya mikowa Zulfa nata dake kusa da ita sai hindatu. Nice ya kirgo yaba a karshe ina karba hindatu na fadin kamar daidai ka bamu da ita nake gani ? Yace ita wa wai tace wanan yarinyar da bata da kowa a tare da ita muko ga yara ga yan aiki da sauranvsu. Yace eh daidai na baku ma ita ba mamata bace ko may ? Tamike tsaye a fusace tana fadi kai kai ana dai rashin adalci kan agidan nan yanzu wacce bata da kowa za, a bawa komai daidai damu ? Yace ashe da nake baki daidai da sauran abaya hainci nakeyi ke nan tun wanan lokacin ko yanzu ne rashin adalcin ya soma akan ita Rahaman. To shi naga zan bayar kudin ki ko nawa ko wani abin kikafita dashi ke naga baki son azauna lafiya wallahi duk kika kara cewa tak a gurin nan sai ranki ya baci yace ku tashi ku tafi nagama daku ke nan. Gaba daya muka mike zamu bar falon yace ke Rahama zo ki mayar min da wanan jakkar daki. Na juyo na koma na dauka na mayar daki inda na dauko da farko na fito na zo zan wuce yace dani idan kin shiga turo min anty ki. Kwana uku suka shirya suka tafi bayan mun sha nasiha mai kama da gargadi a gare shi kan fitina da kuma fita ba bisa kaida ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE HAKAN BA, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA DON ALLAH ZAI TAMBAYE KI 47 Muna barin wurin daki na nufa na shirya tsab sannan naje naiwa anty saida safe. Na samay ta tana saka kayan barci a jikin ta na shiga da sallama na dakin ta juyo tana fadin baki kwanta ba ashe nace eh nazo yi maki sai da safe ne. Tace dani gashi ko kamar kina sauri da naso muyi magana dake ne, nace cikin mamaki sauri kuma anty ? Na karasa bakin kujeran dakin na zauna tace na sani ko mijin ki na can yana jiran ki ne ? Haba dai anty kuma tace dazun yake ce min na tambaye ki kan gajiye da yaran nan ya dai min magana kamar akwai matsala ko ? Shiru nayi na dan lokaci can dai nace eh to ba matsala dan zan saka ido sosai nima ban so kiji hakan ba gaskiya don ba dadi. Yaran dai ne a cikin hiran suke fadin kamar tana dan masu mugun hali a bayan idon mutane. Nan dai na fada mata abinda suka ce a falon ranta yai mugun baci take cewa akan may zata dinga dukan min diya nimay na ragata dashi a gidan nan ? Idan da kece kike dukan su wallahi Rama raina bazai taba baci ba kona digo don nasan harga Allah da zuciya daya kike dasu ke ban kara tabbatar da hakan ba ma sai yanzu. Dakike yawan kusanta su da mahaifin su har yana jin korafin diyan shi, wanda ni da can baya bayi hakan ba saboda gudun zuciya. Nace Anty don Allah kiyi hakkuri zan saka mata ido akan su sosai dama naso daukan mataki a hakan ba sai kin sani ba kada ranki ya baci haka ? Amma don Allah kiyi hakuri don mutum yau abin tsoro don kinga babu wanda zai taba tsanmanin hakan da take masu ai. Amma kamar jinior zata dinga duka kan snocks da sauran ko wanka tace shine ai nima nagani Rama ? Shekaran ki nawa dasu amma wallahi har yau banga wani abinda ba daidai ba akan yaran nan daga gare ki. Yi hakkuri anty zan mata magana insha Allahu ta yadda ba zata gane su suka fada ba don kada ta canza masu sallo. Tace idan ta gaji ne ta tafi mana nace yi hakkuri anty insha Allahu bazata sake ba da yardan Allah. Tace gaskiya kina da hikima wallahi da baki haka ba saita ta cuta masu ba,a sani nace hakane. Kudin da nashigo dasu a hannu nake mika mata tace na may ye wanan kuma ? Nace kudin da daddy ya bamu ne anty, . Ni may zanyi da su kuma ta fada ? Anty ki aje wurin ki ki muna lalura dashi tunda ta fara fada sai yanzu naga murmushin ta tace cikin murmushi kai Rama akwaiki da shirmay wallahi. Ke matar shi ne ni matar shi ne yabaki yabani shine ni zan aje a guna ? Nace anty ni may kika ragani dashi har may zan saye dasu don Allah anty ki karba ki barsu a gurin ki don Allah dai ? Kallona take cikin mamaki gashi sai hada ta da Allah nakeyi akan ta karba dai. Ta mika hannu ta karba sai ta kirga dibu goma ta miko min tace karbi wanan don shan mai a mota, kada ki zauna ba kudi a hannun ki. Nace akwai dubu biyun da kika bani ai last week suna nan ban kashe ba tace to ki kara da wanan din. Na karba da godiya tace kai Rama ho, sai da safe nace Allah bamu alheri anty. Na wuce ina tunane a raina gaskiya Gajiye bata kyauta ba anty mace ce saliha gashi son diyan ta ya rinjayi zuciyar ta kullun maganan ta shi tausayin su take ji ko Allah zai barta ta rayu da yaran ta. Ina shiga yana tattara kayan shi zai shige dakin shi na karba nashige mai dasu ciki. Ina gyaran su ya shigo dakin bathroom ya fada yai wanka ya fito yai shirin kwanciya. Mun kwanta nake cewa daddy na so fada ma motan nan yanzu tana bani matsala sosai yace yaya baki min magana ba sai yanzu da tafiya yazo min sai dai ki dauki nawa ki amfani dashi mugani kada ki kara shiga mota ba lafiya bana son haka. Yana gyara kwanciya yace ki dauki farar CRV din nan dake aje kiyi amfani dashi. Ga keys din su can cikin drower na fada maki kada ki sake shiga motar nan kuma tunda tana da matsala nace insha Allahu daddy yace sai ki shirya kin san yau na sallama zaki min don zanyi wata hudu ban ji laushin wanan jikin danake bukatan shi ba a tare dani. Murmushi nayi nace ai da wani jikin zaka daddy ba kai kadai ba fa zaka tafiyan. Yace bayan kin min zaben raguwa may zan gane ga tafiyan sai maneji kawai ai. Nace daddy ai gara kaje da ita saboda cikin ta ina ga bai zauna ba a jikin ta har yanzu don kaga ko yaushe jikin ta ba dadi gareta. Yace haka nagani nima shiyasa ai na amince da tafiya da ita in bashi ba may zai kaini daukan mai ciki yawo da ita nagane may banda gaiyan barci. Daga haka ya jawoni zuwa jikin shi ya fara shafana yadda yake so saida ya jagwalgwalani son ranshi ya gaji ya barni hakana. Da safe ma bai barni na na huta ba bayan ya dawo sallah sai da ya kara biyan bukatan shi a kaina ko yaushe ji yake kamar ko yaushe sabuwa, nake gare shi. Sai four na fita girki na na dawo dakina don yinin ranan daddy na gida manne dani bai fita ba. Ina shirin zuwa dakin anty wayana dake gefe ke ruri alamar kira ya shigo min lokacin. Bakon nomba ne na dauka muryan mace naji muka gaisa gashi nasan muryan amma na kasa gane ko wacece. Tace dani Rahama kina waya da Zulfa ne yanzu nasa farida ta turo min nombaki. Nace a raina Farida kan ta zama munafuka idan ana neman nombana itace mai bawa mutane ke nan . Don haka taimin tabawa mahaukacin sojan nan layi na ya dinga damuna lokacin. Yanzu kuma ta dauka taba kishiya na wanda na san da magana haka kawai zata kirani ta waya kai tsaye muna gida daya da ita. Muryan Zulfa ya katse min fadan zucin da na keyi da Farida lokacin. Tace nakiraki ne nai maki magana don Allah kiyi hakkuri abubuwan dake faruwa a tsakanin mu nasan kina kokari dani sosai sai dai kin san ala,mari na kishi. Yanzu mama ne tace na kiraki kan wanan karamcin da kikai min shiyasa na kiraki din. Nace a rai na ji yar rainin wayo watau badon mamanta tace ta kirani ba ita bazata iya kirana ba ke nan. Sai nace ai babu komai duk mai tausayi ai yasan ciwo yasan kuma lalurar mai ciki tace ke kika san haka ita wanan da bata da tausayi ai tana nan tana hauka kan tafiyan wai bata yarda ba. Nace to Allah ya kyauta nagode Allah ya kai ku lafiya ya kuma bada sa,an tafiya tace amin na kashe wayan kafin ma ta kashe ita. Nabi wayan da kallon mamaki akarshe ma cillan da wayan nayi saman kujra na ci gaba da gyaran dakina kawai ina mita a raina. Bayan na gama na rufo na nufi dakin anty don sai dare zan dawo ke nan idan na tafi. Anty na daki ni da gajiye ne a falo nake cewa da ita, yaran nan sun kusa dawowa yanzu. Tace wallahi su dawo su cika mutane da surutu da yimini yimini basu bari mutum ya huta wallahi. Nace haba Gajiye don may muke nan ni dake ba don mu taimaka ma wanan baiwar Allah ba. Don haka yaran ta sune farin cikin mu muma batawa yaran ta kamar bata mata raine gare mu. Matar nan bata rage mu da komai ba a duniya ta dauke mu tankar yan uwanta na jini yadda take kyautata min tun farko yasa bana yarda ko kadan na saba mata. Mussanman ma akan yaranta da take jin su kamar rayuwan ta tun zamana dasu ban taba daga hannu na daki yaron ta ba haka kuma banta yiwa yaron ta koda jan idone a bayan ta. Don nasan idan nayi ji zatayi komai dadewa a wurin su shi yaro na kowa ne ai kahaifeshi baka san iya wanda zai amfana dashi ba a duniya. Wallahi gajiye bani fatan daidai da rana daya ko a gabanta ko bayan ta na kuntatawa dan ta don ita bata kuntata muna ba. Yanzu dubi fa ba dangin iya babu na baba amma ko yaushe zancen auren ki da maigadi take tana tausaya ma zaman ki hakan nan. Yo gajiye may muke dashi mu da zamu saka mata dashi banda muso jinin ta tsakani da Allah. Kai nifa ko ba dan anty ba bani fatan in cutawa dan kowa bayan idon uwar shi a duniyan nan. Balle wanan salihar matar mai mutunci da karamci irin haka mu may zamu iya saka mata dashi a duniyan nan bayan haka ? Tunda na fara magana jikin ta yai mugun sanyi sosai naga nadama karara a udon ta tace dani . Wallahi Rahama kin min maganan da yai min tasiri yau a zuciya na maganan ki dutse bamu ko da abinda zamu saka mata bayan hakan. Nace yaran kan ai yanzu muka fara son su tunda sune farin cikin rayuwan ta ko yaushe. Tace masu iya magana ko sunce idan so na Allah kaso da kaso uwar shi da zuciya daya. Daga haka muka dauko zancen auren ta da take son yi ina kara bata dan shawara daidai iyawa na. Ranan talata su daddy suka bar garin shi da zulfa da dare bsshir ya kaisu airport. Hindatu bata san ina amfani da motar maigidan ba sai ranan na dawo yar aikin ta ce ta ganni kuma nasan itace ta tsegunta mata hakan. Muna zaune falo da dare dariya muke kwasa wai Jinior na gwada muna tafiyan wani makwabcin su. Sai ganin an bankado kofa mukayi tabi mu da kallon daya bayan daya muma ita din muke kallo . Ta juya inda anty take tana cewa Saa kin san lokacin da wanan mai isar yar kauyen ta dauki motar maigidan ta fita dashi ko may ? Mota ? Wace mota ke nan fa nace ai da kiyi dani amma ba da yar uwata ba nida na shiga motar har ya damay ki ? Tace ke har wani matsayi ko mukami ke gareki da zaki dauki mota maishi bai nan ? Nace malama banda lokacin ki amma idan kin damu sai ki kira maishi ki fada mai babu ruwan anty cikin wanan magana. Sati biyu na baki gashi ko cika baiyi ba kinga caji da idon ki idan zaki daina gori da hassadawa mutane ki daina shine saukin ki kawai. O yanzu na gane may kike nufi dayin hakan wallahi wallahi zaki san ba hindu ake tabawa a zauna lafiya ba. Don ni kowa yaci tuwo dani miya yasha sai na mayar dake abin tausayi a gidan nan keda wanda kike kwadayin sai hange da ido. Nace saukin abin dai kuma bakece Allah wanan Allah kadai yakai can ga bawan shi amma bake mutum yar uwata ba. Mu zuba wallahi ni da ke banza yar kauye kawai zan gwada maki na fiki sanin hanya nake sherin na yan kauye ne. Sai kin bar gidan nan da kafan nan naki da kika shigowa mutane yar cin amana kawai. Ke ko kunyan kanki bakya ji kinzo kin asirce mata da mijin ta ki aure mata miji don sheri kullun kina mane da ita da yaran ta kina cusa masu mugun abu suna ci. To ni wallahi nafi karfin ki ke har boka da malam kika sani zaki gane kuren ki wallahi. Anty tace hindatu may ye zafi hakane don mota zaku tsaya kuna wannan tayar da jijiyan wuyan haka har kuna sabon Allah akai. Ai ba mai iya yiwa wani wani abu sai Allah shi ganin bayan mutum ai ba alheri bane. Dallah rufa min baki almunahuhu kawai wa zakiwa wa, azi bayan duk sherin kece mai kullawa kina wani lafewa a daki kullun wai ke baki da lafiya . Haka zaki kare a nakashe cikin daki kina kulla kilibibi a zauna makira bamza kawai. Tai tsuki tare da juyawa da karfi zata bar dakin nace an dai yi hasara anji kuya haka za, a kare ga hassada da kyashi a rai. Anty ai ta godewa Allah don kaffara take don kowa yasan ciwo kaffara ne keko fa sai bakin hasaada da kishin tsiya dake cinki baki iya komai damu wallahi ta Allah ba taki ba. Ta juyo tana fadin haka kikace muzuba mugani shege ka fasa ni daku muna fukai kawai. Gaki munafuka yar hassada da bakin ciki tafi haka zaki kare wazaki zo kina zare wa ido nan kowa kika aje ke ? Tana fita anty tace wai sannu Rama ashe ke ma kin iya wanan irin haukan na su ai zakuyi daidai. Ta zaci iri nane da suka raina su kwaso sharan su su yaba min duk lokacin da suka ga daman hakan. Nace anty ni yanzu nai alkawari bazan kara ragawa wanan mara mutuncin ba wallahi tunda ana bata girma ita bata sani ba. Tace ya isa hakana kyale ta basu da aiki sai gadara da jahilci ai kun hadu yan bana kun saje ke nan. Nace haka wai fa dayar abokiyar sherin nata ranan sai ga waya ta bugo min nan na fadawa anty yadda mukayi da ita. Tace ji rashin wayo harda fadin wai uwar ta ce tace ta bugo maki waya watau ba kashin kanta ra bugo ba saida aka sata ke nan. Nace ita, dai ta sani ni duk bugu daya na dauke su dukkan su ai bazan yarda da shiri da kowa ba na sheri. Anty tace ita Zulfa tana da dan dama sosai bisaga hindatu don ita hindatu gani take duk tafi mu a gidan. Hakama ake fadi yadda ake ganin tana karya da rawan kai yanzu ko taga wata tashigo kin san dole haukan ya karu mata. Nace sai tayi ni banda lokacin ta Allah dai ya baki lafiya anty mutum harda ciwo yake gori ? Anty tace ni ko makiyina bana fatan yai ciwon nan balle wani nawa su da basu san halin da nake ciki ba yazama masu abin gori gare su. Allah dai ya baki lafiya anty ki koma kamar kowa gajiye tace Amin wallahi mutum ya dinga kirari kamar shi ya halicci kan shi don kishi. Muka gaji dayi dole muka kyale ta sai dai maganganun ta sun tsaya min a rai sosai tunda ta fadi nasan zata iya abinda tai niyya akaina din. ********* ********* ********* Munje school bayan mun fito daga lectures ne Zarah ke cewa sai naga yau gaki nan wani iri dake nai ajiyan zuciya nace bari kawai Zarah. Alamarin matan daddy ne abin ba dadi wallahi sai nake fada mata duk yadda al, amarin yake muna. Take cewa dani ke yanzu wani mataki kika daukar ma lafazin ta ke nan ? Nace wani ko mataki zan daukar Zarah idan naga abin go no go na bar masu mijin su ban iyawa wallahi sai dai anty tayi hakkuri dani kawai. Rahama kina hauka ne da zakice wai kibar masu mijin su, tabdi jam ai wallahi basu isa ba sai dai ai ta tafkawa din. In sun sani ai kowa ma ya sani ina dai duniyan ce din kowa tashi ta fishe shi. Na kalleta da mamaki nace saboda may kikace haka zarah ? Tace saboda ko mijin kowa ne ba don su, su kadai aka hallice shi ba ai. Ko bake ba haka zasuyi ga kowa ma don haline zanen dutse zafin kishi da hauka ke cin su ita anty Allah ya bata hakkuri ke nan. Bafa bata son mijin ta bane ta sadaukar maki dashi wallahi tana son abinta kuma duk yadda akayi wani abin nacin ta na kishi akan ki daurewa kawai takeyi bata nunawa a fili. Nace kai haba Zarah ina gaskiya wanan kan ba gsskiya bane. Tace kika dai ce amma wallahi tana kishin ki kice ni zarah bukar na fada maki wanan magana wata rana zaki tuna. Nace ko dai tana kishina tunda bata nuna min ba nima bazan taba nuna mata ba. Yana da kyau hakan amma kiyi raka tsantsan don watan watarana wallahi wurin boye mata wani abinki. Nace naji kawai nifa duk na antyna mai sauki ne zarah bisa ga na wanan matan da ke ikirarin halakani. Tace wanan sai Allah ai kema ba zama zakiyi hakana ba yanzu wa ya saura da wanan in ba don Allah na tare dake ba ai da yanzu sai buzunki kila. Nace ni Zarah yaya zan yi ne dasu ni wallahi dai na shiga uku aure babu kwancitan hankali haka ? Yaya ko zaki in banda kema tashi tsaye zakiyi kamar yadda suke tsaye kyam akan zaman gidan ko yaushe wake kwanci irin ki yanzu. Nace nikan in dai sai naje gurin boka ko malam wallahi sai dai na bar masu gidan su Allah ko. Tace ke don Allah an daina yayin boka da malam wanan ai sai jahilai keyin shi yanzu wanan wa,azin da akewa mata ko yaushe ai ya ishi mutum tsoron Allah. Gyara kanki zakiyi sosai wallahi yadda zaki zarce kowa a shimfida indai shimfida na daidai akomai kanzo da sauki ga mace. In kina gyara wallahi sai ta raina kanta shima bai kara ganin ta da wani kimacan balle makircinta ya hauki garshi. Nace Zarah duk wani abinda zanyi Attu fa tai min shi da zan zo may kuma ta rage yanzu nayi. Tace tunda an fada maki guri daya ake tsayi ga harkan ba zauna nan har su kwace maki miji kina kallo wallahi. Wani abu zatayi bayan wanan duk burgan aikin dai yanzu shine gyara ga mace. Ko ki jayon mijin ki akanki ko kinaji kina gani ki zama yar rakiyan mata duniya don haka ki tashi tsaye kinji na fada maki. Nai dai gyara tare da sauke numfashi nace ni ma duk kaina ya rude na rasa may zanyi yanzu wallahi. Wani abu kuwa zakiyi banda ki tsuma kanki ta hanyar sha da tsuguno, wanka da shafawa da kuma matsawa wanda ya dace ba mai cutarwa ba. Nace zarah duk ni kadai tace dake dawa dake da wanda kuke shan dadin tare kike son yi ko may ? Don Allah dai Zarah daina wanan zancen wasan muyi maganar gaskiya please. Nace ni ki fada min abinda zanyi kin tsaya kina min shakuyanci kuma. Tace ni dai gaskiya mama na ce ta hadani da matar da nake karba a gurin ta idan zaki iya sai mu samu lokaci daga nan mutafi ai maki kafin wanan bakin baturen mijin naki ya dawo mai kaidan tsiya. Na sauke ajiyan zuciya nace sai ki fadi ranan da zamu tafi don na fito da shiri na ko tace ki bari banda gobe sai mu tafi ai ba nisa sosai da nan din. Mun rabu ina ta tunanen zancen zarah da mukayi nace wai yanzu wanan abin ya zama ma mata al,ada ke nan su ma mazan zamanin sai da hakan ? Ita ko Hindatu takira mai gidan ya kai sau barkatai bai daga waya, sai zuwa dare ya dauki wayan ya fara mata masifa yace haba hindatu kin kira dayakin kira biyu ai sai ki gane ina da uzuri ne hakan. Ni ina zangane tunda bana tare dakai ni dama ba wani abu bane illa tambaya nake son yi da sanin ka yarinyar nan Rahama take fita ma da mota ? Yace yanzu saboda wanan kawai kika daga min hankali da kira ina cikin meeting. Ai ba kawai bane sai gaskiya ita waye da zata dauki motar ka tafita dashi don ace mata wa a gari ? Yace mama tana mana tunda motanane ba na wani ba tashiga koda wani magana ne akan haka ? Tace magana kai Allah dawo dakai lafiya don haka ba zai taba yuyuwa ba yace ya riga ya yuyu tunda kinyi magana da dai baki min wanan fitsara ba kin bini da lalama dana fada maki dalilin yin hakan danayi. Amma yanzu ina jiran inga abinda zaki yi din tunda wani ya saya min motar da zai hana ni yin son raina daga haka ya kashe wayan ya shiga mota sai masaukin su. ********* ********* ********* Kamar yadda muka alkawari muna fitowa bamu tsaya shiga pratical ba ranan da motana muka fita don ita bata shigo ba da mota. Wani gida mukaje a uguwar sharifai gidan baida girma sosai mukai sallama muka shiga daga ciki. Matane agidan birjit da masu nikaf da masu gyale da masu hijjabi suma sun zo don gyaran harka kawai kan mazajen su. Muka samu wuri muka zauna watace ke hira mijin ta da kishiryar ta tana fadin wai saida tai shekara bakwai mijin ta ya kaurace mata tunda yai amarya. Amma yanzu gashi tunda ta fara amfani da kayan hajiya mai gyaran harka mijinta sai rawan kafa yake akanta. Jikina yai sanyi nace a raina Allah dai yasa ba shirka a wanan gurin wanan dadin danaji matar nan nayi haka. Mun kusa awa daya muka samu shiga wurin ta wani falo ne babu komai sai tarin kaya nau,i nau,i irin na amfanin mata. Wata farar mace ce mara jiki fara tas da ita tana ganin Zarah tace manyan gari ashe ana ganin ku ke nan ? Zarah kwana biyu suka gaisa nima na gaida matar tace ikon Allah ana kama a duniya wallahi. Wanan yarinyar kamar su daya sak da autar mu komai nasu iri daya wallahi sai mukai dariya tace ikon Allah har dariyan ma naku daya wallahi ko. Zarah tace haka ake kama wani lokaci matar tace dani ke yar nan garince halan ? Nace eh tace niko kinga asalin mu daga damagaram muke aure ya kawo ni sokoto daga can mijina ya dawo nan har Allah yai mashi rasuwa dayake ina waban harkan sai naji dadi ban koma gida ba na zauna nan nida yarana. Allah ya jikan musulmi yai masu rahama tace amin nagode. Zarah tace hajiyan harka wanan kawatace ta kut da kut tare muke karatu da ita sai dai tana da kishiyoyi itace ta hudu a gurin mijin su. To kin san dai komai anan zuwa mukayi don Allah hajiya a haska muna ita don ita haka take zaune cikin su zikau. Tace asha kaunata wake zama yanzu haka kawai ai mazan yanzu baki samun daukaka a gare su sai da wanan harkan. Duk wacce tace zata zauna wallahi ba zugi ba zata koga ba daidai ga maigida. Balle ke dake da kishiyoyi har uku ina zama ya ganki ai ance in kana da kyau kara da wanka. Nan dai ta shiga yi min wa,azi da nasiha kan zama da miji har ma da kishiya kan kada na yarda nai aikin da baidace ba ga rayuwa na. Naji dadin nasihanta don na hango akwai addini sosai tare da ita don sai wanda yasan Allah zai maka wanan nasihan haka. Tace insha Allahu zan taimaka maki da abinda ya dace wanda ba zaki nakasa ba a gurin mijin ki ki daina tsoron cika bakin kishiya tanayi ne kawai don ta razana ki. Tace dani ke, ke bashi ruwa yasha ko shi ke sha da kan shi ma,ana ya dauko nace ni ke dauko mai tace ya kwana gidan sauki ai. Ruwan nan sai ki bude ki juye a cup sai ki karanta bissimillahi kafa dari uku da goma sha uku ciki ki dinga bashi ya sha ko kuma dari bakwai da tamanin da daya kina bashi yana sha har tsawon sau bakwai. Zaki iya kuma tofa Allahu ya wadudu a ruwa kafa arba,in daya har sau uku ki bashi yasha a ruwan da kika tofe din. Zaki samu kwalli wanan fari mai dutse ki nika shi ya zama gari sai ki tofa mai (wara fa, anahu man kanan aliyan ) kafa arbain da daya, dinga shafawa a ido duk lokacin da namijin ki ya kalle ki zai ga kin kara mai kyau da sha,awa gare ki. Zaki samu ruwa na kanzon tuwo sai ki barshi ya kwana a wuri mai kyau amma a fili sai da safe ki dauko shi ki zauna zama irin na bauta ki karanta la,illah ha, illah kafa uku sai li, ilafi quraish kafa uku a cikin sai rabbi ziddini ki fadi sunan mijin ki sau uku ki shanye. Yana kawo daukaka da farin jini a gurin namiji sosai ba kadan ba a gwada yana da alfanu mata. Tace wanan ke nan sai kuma wanda yanzu zan baki na amfanin ki kuma. Kin san kina da kama da kaunata sai naji kawai ina son ki har cikin raina ganin ki nake kamar autar mu wallahi. Ta jawo wani roba tafito da wani sabulu tace kinga wanan sabulun yana da hadi a cikin shi sai ki samu sabulun wankan ki ki hada dashi ki kwaba kina wanka dashi ko yaushe akwai lalle da majigi da habba da hulba duk a cikin hadin sai abin mallaka da akai amfani dashi ciki. Ta kara miko min wani turare mai kamshi tace karbi wanan turaren na motsa sha, awa ne shi kafin ki je gun maigida ki tabbatar kin motsutsuke jikin shi dashi sai ki kawo wanda kike amfani dashi ki dora sama don ya kawar da kamshin wanan din kada a gane mudai mukatan mu ko kadan ne ya shaka kawai. Wanan kuma hayaki ne zaki dinga tsugono an hada shi ne ta igiyar akalar rakumi a cikin sa. Na dago kai na kalle ta tace kaunata ke nan idan ke baki jashi ba kina kallo sai wata ta jaye maki shi ai. Wanan abin ba tsafi a ciki bokan ki ne a dakin ki don sai dashi aure yanzu muddin kina son tsufa a dakin ki to sai kin hada da hakan ko. Kinji ance ki nemi lahiran ki tun aduniya da kuma so da kauna a gurin mijin ki to sune nan babu boka babu malam sai ayoyin da akai fani dasu a gurin hadin. Tabani gumba tsumi da sauran abubuwa har da wanda zanyi kumshi koda a yatsan hannuwa nane . Tace naje na gwada su kawai sai wani lokaci idan mun hadu zata bani wani tare da jadda mi cewa ayau fa mace bata kamaluwa idan babu kwaskwarima gare ta don mazan sai da haka ake zaman lafiya. Keda kada kiyi wanda zaki kaucewa imanin ki ki cutar da miji da kishi amma indon wanda zaki gyara kanki ne malaimai sunce kiyi . A sanye na sauke ajiyan zuciya na dago kai tare da duban ta nace hajiya nawa zan bada ? Tace cikin murmushi gaskiya kinci albarkacin yar uwata don gashi na baki harda abinda ban taba ba Zarah irin su ba. Zarah tace ai mamaki kawai nakeyi wallahi ina jira kigama ne naciki tara. Tace wanan autar muce ai kin san dole kuma na gyara autar mama ko kada kishiya ta koro muna ita. Gaskiya ne hajiya inji Zarah . Na sake cewa na gode hajiya nawa zan bada ? Tace a gaskiya ita zarah ta san kayana takuma san amfanin su da wata ce Allah sai dubu hamsim zuwa sama zaki bada. Amma yanzu kibani yadda zaki iya ai yanzu muka fara dake sai nan gaba zan baki har wanda zakiyi nafila dashi. Nace to haji in na bada ashirin ban so kaina ba da yawa tace babu damuwa kawo goma kawai kaunata ko zan samu ladan zumuci a kan ki don autar mu na baki hakan. Nai mata godiya mukai mata sallah kan duk yadda naji zamu dawo insha Allahu. Bayan mun bar gidan ne muka dawo gidan zarah ita tabani abubuwan hadi wasu ma ta hada min na wuce dasu gida nai mata godiya. Ban shiga dakin anty ba sai da nakai kayan part dina na boye nai wanka sannnan na dawo gaida anty. Tun daren ranan na fara amfani da wasu daga cikin kayan da ta bani don su girdu a jikina kafin mai gidan ya dawo. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YABI HAKKIN HA,INCI GAREKI, , , 48 Sannu a hankali nake aiwatar da komai da hajiya mai gyaran harka ta bani. Sam ban bari kowa a gidan ya fahinci abinda nake yi ba sai na fakaici idon mutane nake yin yadda ta fada min so nake na fahinci gaskiyan al,amarin. Haka yasa na dage gurin gwada amfanin su ko hakan zai yi wani fa,ida. Ita ko Hindatu nacan ba zama ba tsayi ta fada nan ta fada can bata gurin bokaye gurin malamai da masu kayan mata. Burin ta daya shine ta samu kan maigidan ya kasance bai ganin ko wace mace da kima da daraja sai ita. Gashi duk inda ta tafi sunan Rahama ne dai a bakinta ita dai ai mata aikin da zai dakushe haske Rahama ga mijin su a baki daya takoma ita da babu ita agidan duk daya. Kudin ka yasha kashi sosai ita kuma tasha kayan kulli da wanka har da shafawa. Duk ta yo kayan su ira ta tafi hanne yar aikin ta ta tafi mata uwarta taje mata yan uwanta suje mata haka ma aminan ta suje mata duj kan dai abu daya takeyi. Sai da ta tabbatar ta hadu akan komai yadda take bukata ta sawa kanta sauki da hakkuri hakana. Jira kawai take maigida ya dawo ta fara aiwatar da nufinta akan shi kamar yadda nima nake jiran ya dawo na gwada kayan mai kayan harka akan shi. Bani wasa da tashi cikin dare nayi nafila na roki Allah ya kare ni da duk wani sheri da kulli akan duk wacce ta bini da mugun nufi Allah ya mayar mata da aniyan ta akanta. Sai na gamsu da addua na nakan dan koma na kwanta kafin ai sallah asuba na tashi kuma na kara tilawa. A bangaren hindatu nasha binne binne da yayafin rubutu a duk inda zan taka. Allah ya rufa min asiri bana fita daga part dina ko wajen gida sai nayi addua a bakina na neman tsari daga gurin ubangiji na Allah. Na kuma gode don Allah yai min dauki akan hindu da sherin ta don kar nake kallon ta. Inda na san akwai magana kaina cikin dare ina part din anty a zaune hira muke a kan Abban ta muna dariya Gajiye bata riga ta rufe kofan baya ba don tana son fita ta kwaso wasu kaya da ta bari a baya . Haka yaba hanne yar aikin hindatu dama samun shigowa don ta yayafa abinda wani malami ya basu su zuba min a kofa na. Gajiye na fita ta hango kamar innuwar mutum a gurin yana zuba wani abu da karfi tace waye waye a gurin nan ne ? Da sauri Hanne ta juya tabar gurin jikin ta na ciri taa gudu zuwa part din su Gajiye tabi bayan ta amma ta saurin shigewa babu kowa a gurin. Jin ihun ta yasa muka mike muka nufo gurin tace da karfi kada kuzo nan hajiya akwai matsala wallahi. Cak mukaja muka tsaya tace bari ta haska wuta a gani ta kunna wutan ta Hanne ta kashe mai haska dogon coridor din. Wani ruwan rubutu ne ko tsimay oho, da wasu bakaken abu a cikin sa. Gabana ya fadi ras anty tace na shiga uku gajiye waye ya zuba wanan abin anan ta fada muna abinda ya faru. Anty tace yanzu wake da aikin nan haka Allah ya mayar wa mai shi da aniyar shi don Allah yafi shi. Gajiye tace ina zuwa ta wuce zuwa baya sai gata da wani abu a wani tsohon roba ta zuba a gurin. May ye wanan din kike zubawa Gajiye tace hajiya fitsari ne kin san yana kashe dafi da asiri shi. Bayan ta zuba tasa abin shara ta share tafita dashi takawo moper ta goge gurin tsab gabana sai faduwa yake min. Anty tace mu koma daga ciki ranan a dakin anty na kwana duk jikin mu yai sanyi sosai kan wanan abin. Gajiye ke cewa Hanne nake zargi wallahi don babu tantama itace nagani ba wani ba. Yanzu ai zato muke idan baka iya kama barawo ba sai shi ya kama ka. Gajiye tace ranan fa da safe koda na fito naga kofan falon mu kamar an tona muna shi sai aka kawo ruwa aka zuba ko ina mutum bai gane komai. Anty tace shine baki fadi ba Gajiye tace hajiya may fadin zai yi amfani na dai zuba bowli a gurin ma ranan don ban yarda da hakan ba. To Allah ya kyauta mukace amin baki dayan mu haka yasa na kara kula da kaina sosai nasan da akwai sherin da ake kokarin kulla min. Haka yasa na kira inna ta na fada mata halin da nake ciki itama hankalinta ya tashi. Tace zata fadawa maigari halin da ake ciki takuma je ta fadawa Attu ta koma gurin malam Musa ta fada mai. Yake cewa ta fada min na kwantar da hankalina ba dai ina yin adduoin da ya bani ba da zanzo kuma abinda yai min insha Allahu wani asiri bazaiyi tasiri ba akaina Allah zai kare ni insha Allahu. Sai da nai kwana uku ban shiga part dina ba ina tsoro itama anty tsoron hakan take ji. Sai dai takan min sheri muyi ta dariya ga kwana na hudu nagama addua na na fara shiga naji kuma hankalina yai matukar kwantawa sosai. Kwana biyae sai ga Fatima yar gurin maigari an turo ta guri na da abubuwa daga shi maigari din ya turo min. Na dawo school na samay ta tazo da murna na tare ta mun dan zauna part din anty muka kwasa muka koma guri na. Sai da dare muna shirin kwanciya bayan mun rufe part din ne ta fitar da sakon tai min bayanin su dalla dalla. Banyi sanyi a kafa ba na fara amfani dasu kamae yarda yace min duk na tsari ne kayan. Naji dadin zuwa Fatima a gurina muna zama muyi hira bata da son jiki kafin na fito ta gyara min part har na anty takan gyara udan aiki yaiwa gajiye yawa. Anty takan ce wai haka yan garin ku suke ne da saukin kai Rama duk wanda ka gani sai kaga yana da mutunci ji yarinyar nan kamar ba yar kishiyar inna ba komai tsakani da Allah takeyin shi. Nace daga tarbiya ne anty amma ai akwai marasa mutuncin bamu dai hadu dasu bane kawai. ********* ********* ********* Daddy ya bugo waya next week zasu dawo insha Allahu haka ya kawo ba zama kowa na kokatin gurin gyara a lokacin. Duk wani abinda hajiya mai gyaran harka tabani banyi wasa dashi ba na maida hankali a gurin yin sa. Na kwashi yara saura kwana daya ya dawo mukaje gurin gyaran jiki mazan akai masu aski ni da Amira da fatima kuma aka wanke muna kai mukai kitso mai kyau don muna hutu a lokacin. Sai da muka dawo ne anty taga abinda mukayi don tana barci muka fita gidan bata ma sani ba. Ga kayan dana sayo masu na taron daddy taji dadin hakan soai da yama na shigo dakin da tsinken kitso da cumb nace ta zauna na gyara mata kan ta. Don ni bayan kitso an gyara min jiki an min kumshi na sa lallen da mai gyaran harka taban a yatsuna. Nai matukar kyau sosai har yaran ma anty tace dani kai Rama ni ina zan tsaya yin wani kitso kuma nace haba dai Anty don Allah dai ki bari ko shidda na kwashe maki . Bataki ba da fada da komai nai mata kitso mai kyau haka yasa fuskanta ya fito da kyau bakin ta yana sheki sosai. Na zauna kafin magariba na gyara mata yatsun kafan ta da sauran abubuwa tace dani Allah dai yai maki albarka har najini kamar bani ba wallahi ko. Washe gari munyi aiki sosai irin gyaran part din daddy da girki itama hindatu tayi nata gyaran har girki ta shirya mai bayan mu ya bugo waya ai mai tuwo. Da yamma suka iso garin take gida ya rude da jin dadin dawowan su lokacin. Ina part dina da fatima Nasir yazo ya fada min dawowan shi sai da muka dan dauki lokaci na kwashi yaran da muka aha kwalliya mukaje taron shi. Yana zaune a falon shi shida Bashir muka shigo gaba daya kallon shi ya dawo kan mu har sai da bashir din ya juya yaga may yake kallo haka ne. Mun karaso muna mashi sannu da zuwa nakuma gaida bashir din suma yaran haka sun gaida abokin baban nasu. Ina fadin akawo abinci ne sai ga hindatu tashigo dauke da kayan abinci tana ganin mu fara, ar fuskanta ya dauke. Ta samu guri ta aje abincin tana fadin ga abinci kaci kai wanka ko zakaji dadin jikin ka . Ina jin haka na mike ina cewa a huta gajiya daddy zamu mu gaida Anty Zulfa itama. Yace ku kawo min tuwon ko ba ai min bane nace anyi maka daddy yace kawo min tun bashir bai tafi ba muci. Tace wanan fa dana shirya ma ko may kake nufi da akawo ma wani kuma yaya zanyi da wanan din kuma ? Yace ai bance ai min ba wanan ra, ayinkine hakan tuwo nace Saade tai min ai. Yaya za, ayi wanda zaiyi girki daban may kawo tuwo davan kuma ? Yace bisimillahi hindatu zaki fara kuma ko da dawon mutum bai huta ba zaki saka min bacin rai kuma ? Tace may ye na bacin rai a nan tunda nice zan yi girki daka tafi ai dakin Saaden ka kwana ko ? Yace idan hakane kwana nawa nai a gurin ta, ke banson fitina yadda nake so haka za, ayi kinji na fada maki gaskiya. Wallahi wanan bai yuyuwa haka kawai kan wata can in bari ka danns min hakkina yace indai wanan shine danne hakki tona danne din . Hakana tsara kuma hakan zanyi ke duk yadda akayi dake ba, a daidaine wai bafa gurin Rahama nace zan sauka ba balle kice zaki min fitina haka. May ye banbancin Rahama da Saade karshe ma ai munafunci za, ayi ace wai ita Saaden ta yafewa wanan din girkin tunda kun riga da kun shirya. Ke hindatu kin isheni wallahi ban son rashin hankali wallahi ko addini yabani daman zaben inda zan sauka amma nai haka don a zauna lafiya dai. Muna fita part din Zulfa muka nufa nida yaran mun samay ta tare da maman ta da yarta a dakinta sun baza kaya sai yan dararakun su sukeyi. Muka shiga da sallama suka amsa muna sun daure fuskan su a lokaci daya. Muka gaida ita tare da mata sannu da zuwa ta amsa muna bamu tsaya ba muka fice abin mu. Tun bamu karasa fitaba naji yarta na fadin kai Zulfa haka yarinyar nan ta koma ashe ? Tace wallahi nima haka na gani, yar tace jita kamar ma itace tai tafiyan da miji ba ke ba wallahi. Uwar tace Zulfa koma may ye yarinyar nan ki mata uzuri please tana dai dan kokarinta a kanki. Yanzu fa ba wanda yazo gaida ke sai ita da yaran kin ga koma may ye ai dai tayi ko da kuwa na munafuncin kishiyace. Tace gashi itace silar tafiyan ma gaba daya koba komai ki samu abinda kika bata ko ba mai yawa bane inji uwar tace aramawa kura aniyar ta. Yar tace yaran fa tace ai dole ne inba haka ba tsiya zai shuka min ban ba yara shi komai ba kin san shi bai hada komai da yaran shi ba ai. Mun koma gun anty tana kallon mu cikin sha, awa tace har kun dawo ko na zauna ina cewa ai har gurin anty Zulfa muke muka gaida ita. Lalai Rama akwaiki da kalula wallahi ki dai yi a hankali wa yan nan da kike gani basu da tabas wallahi. Nace ni don yaran kawai naje gaida ita don su saba da hakan don shi yaro ba ruwan shi ki san race nagane hakan ? Kin yi hikima Rama na fahinci nufinki don yaro ba, a sashi ga zancen kishi yin hakan haukane da batan kai baka san may rike ma yaron ka ba wata rana in babu mutuwa akwai rabuwa mata mu kula don Allah da wanan kishiya bata iya yiwa dan ka komai sai in Allah ya nufa. Ba,ace ta ka zure ba amma yadda Rahama ta shiga dasu sha tafito shima wani dan hikima na ne na gyaran zaman gida hakan. Tace kin zauna abinci fa nace may girki takai mashi abinci ko anty shiyasa banyi batun kaiwa ba. Tace to wata sabuwa ana dai drama a gidan nan wallahi kafin nai magana sai wayan daddy ya shigo mata yana cewa nace wa Rahama ta kawo min abinci mana naji shiru. Tace dani kinji kuma wai akai may abincin nace dama nasan rigima zasu yi shiyasa muka basu guri ba dadi kullun yara suna ganin irin wanan fitinan haka. Tace tashi muje da abinci muji may ke faruwa namike na dauko basket din da muka shirya kayan na fara fita dasu anty ma tabini da sauran drinks din da na riga na tofe su da ayan Allah ciki muka kai mai. Muna shiga tana fitowa a fusace daga falon dagani anyi ba dadi a falon lokaci tace damu muna fukan banza kawai wallahi sai kun gane kun shiga hurumi a gidan nan. Nikan na jera masu kayan abincin Bashir na ma anty sheri wai uwargida sarautar mata ke saade wai may ye sirin wanan abin ne haka ? Tace Allah ! Ya ce naga gaskiya ai kan Allah ya barki da besty ki daga inda nake duke nace Amin. Ina gamawa na mike na bar falon yabini da kallon sha, awa kai mutumin yaya haka kuma wai inji bashir ? Tace kasan amarya ce fa gata yar shila banga laifin shi ba ai wata nawa rabon shi da ita haka ? Bashir yace ikon Allah waike saade wata irin mace ce baki ko jin darr a ranki kan yarinyar nan haka wai ? Tace na fada ma ai Allah ko baka gane ba har yanzu ne abin daga Allah ne fa. Yanzu dai zuba muna abinci muci na baku guri ni dama an kwadaita min ne na tsaya ci kawai. Yace a, a barta na zuba muna kada tace kuma bayan ta zai karye yanzu lalaba abina nake don nasan halin kayana sarai. Shi ya mike ya bude sai kamshi ya daki hancin su yace no warder ka kore kayan shimkafa da miya don nasan shine dai abincin nasu. Sunci sosai suna hira su uku sai da suka gama ne Bashir yai masu sallama ya tafi anty bata fito ba sai washe gari da safe ni na kwana da yaran a gurina ranan. Washegari ma nina hads breakfast na hada komai nakai masu saida ta karya tafito ta samay mu zaune ina shirya yaran zasu islamiya don ba boko lokacin. Nan muka shiga gaida ita ta amsa muna cikin fara,anta nake cewa da ita yanzu nake son wai da na hada maku fruits salad nakai maku gashi kuma kin fito. Tace kai barshi kawai Rama ki huta kawai sai anjima ni zan ma kwanta ne yanzu bana jin dadi wallahi. Subbahanallahi may kuma anty ko a dauko maganin ki ki fara sha kafin ki kwata ko ? Tace kai Rama mutum na shan magani kulun abu jiya wa yau ni na barwa Allah sani ko ma may nene hakan nagaji wallahi Rama. Mikewa nayi na shiga na hado mata magani tare da ruwa na kawo mata tasha sai dan wani lokaci takoma daki ta kwanta. A raina nace wai kuwa anya ba jifa ne je damun wanan boyar Allah ba haka mace ba dama ta dan sake da mijin ta sai ciwo ya taso mata haka ? Tunda ts shiga har muka gama abincin rana bata fito ba haka na daure nakai mata yana gida tare da yan uwan shi na samay shi a falon tun auren na da daddy sau yau naga Ibrahim. Koda na shiga suna yan dararakun su yana ganina yasha toka na gaidasu na aje abincin ban tsaya ba don ba hijjab ko gyale a jikina a lokacin. Tun shigowana naga kallon da daddy ya watso min nasha jinin jikina har nakai kofa mubarak ke cewa dani ina Saade ta shige ne baiganta ba tunda ya shigo gidan. Nace ayya tana kwance bata jin dadin jikin ta ne shiyasa baka ganta ba ai duk suka ce Allah ya bata lafiya a gayar da ita. Sai bayan la, asar lis daddy ya shigo part din namu inda ya samu dagani sai gajiye da fatima a lokacin mai part din na ciki ta tashi har na shafawa kafanta da tace yai mata nauyi magani. Nafito daga kitchen ina saye da wando tie da purple da dan riga mai karani ya matukar matse min jikina komai na suran jikina a baiyyane yake din kayan sun matukar daukan jikina sosai. Sai nai kicibis dashi ya shigo falon bai damu da wai Gajiye na nan ba ko fatima da yagani bakuwa yai wurina tare da kamoni a jikin shi Allah yasa ta hanya kitchen nake ba kusa dasu ba sai dai ai suna iya hango mu daga inda suke. Ya rungumoni tare da matse ni a jikin shi yana fadin ke baki da hankaline ga maza zaki shigo falo ko dan hijjab baki saka ba dadin su gama kalle min wanan jikin da kike daukan hankalin mutane dashi. Na dago na dan kalle shi cikin dan murmushi nace dashi ni ai ban san suna ciki ba ne kuma na riga da na shiga falon ko. Nidai bana son hakana please nace to ai haka naga kowa na shiga ba rufe jiki yace ai kowa kikace kowa irin nashi suran daban ne, suma ai bada son raina suke wanan dabiar ba. Nace na bari daddy ai min afuwan na yau please yace naki don sai na hukuntaki ga hakan ga wanan mara hankslin a falo ina ganin shi sai da ya kalle ki wallahi. Nace ayi hakkuri yace naji ai ance matar na tuba bata laifi amma ni gaskiya an min gaskiya don haka ki kula . Nagode nace ni dai so nake ya sake ni kada mai dakin ta fito ta samay mu a hakan taji zafi don kishi kishi ne. Shiko yaki sake ni sai kokarin mu hada ido ni dashi yakeyi ina kawar da kaina kar abin yai muna nisa. Na dai samu ya sakeni da kyat ya juya zuwa dakin anty ni kuma na gyara rigana daya squzeeing. Mun kitchen naji gajiya tace Rahama kin dai shigo gidan nan da kafar dama maigidan nan naku banga macen da yake ji da ita ba haka a ran shi. Don bai iya boye son shi gareki a gaban kowa wallahi sai dai sauran suyi hakkuri akan haka don ko ita uwar dakin namu tasan da hakan don ta leko tana ganin ku a haka naga ta koma da sauri ciki. Na juyo gareta da sauri nace gaji don Allah anty ta fito yana rike dani tace tafito amma tana ganin ku ta juya ciki da sauri. Nace subbahanallahi Gajiye shi na kewa gudu wallahi amma shi daddy ko a jikin shi ga hakan. Ni yanzu yaya zan kalli anty don haka cin amana ne kamar nai mata yin hakan data gani. Hakana na daure na ci gaba da aikin dake gabana sai dai zuciya na yana ci gaba da rashin dadi. Daddy yana shiga dakin anty ya samay ta zaune a saman gado ta dukar da kan ta a kasa yace da ita kin tashi ke nan ashe ? Tace na tashi kagama runguman naka ne da kake yi yace ruguma kuma rugumarwa kuma ? Tace wanan ai rashin adalci ne yaya har cikin falona zakazo kana rugumar mace haka a gabana in zakuyi iskancin ku kuyi a bayan idona mana amma ba sai anzo nan ana ci min fuska ba haka ? Yace cikin mamaki iskanci fa kikace Saade matar tawa dana rike ina mata warning ta shigo falo ga maza ba hijjab a jikin ta shine iskanci kuma ? Ni dai ban son hakana gaskiya ayi duk abinda za, ayi a bayan idon na yafi min nace bani so daga yau kaji na fada ma gaskiya. Saade kina ganin ni zanci amanan ki ne ko Rahama zataci amanan ki kike gani idan kin muna wanan zaton wallahi dukkan mu baki muna adalci ba gaskiya. Tace ni dai nace ban so na fada ma yace idan baki son na riketa tana matsayin mata na sai ki raba auren kowa ya huta bashi ke nan ba. Kallon mamaki yake mata sosai bai tsaya karasa maganan shi ba ya juya ya fice daga dakin rai bace. Naga lokacin da ya fito hakan rai a bace ya fice daga part din baiko kalli inda nake ba yafice. Ashe akwaita ke nan to ni may ye kuma laifina ga hakan don ai bani na rike shi ba shiyazo ya rugumay ni kuma na kwace kaina ai daga gareshi. Ban yarda na shiga ba sai dai itama bata fito ba haka na daure na shiga ina fada mata an gaba abinci a dai bo mata ne nan ? Tace fuska a daure barshi idan na tashi ci zan fito naci ai nace to wanka fa ko zaki ji dadin jikin ki ? Rama don Allah dai ki barni please banajin son surutu yadda nake din nan bana jin dadi wallahi ko. Nace Allah ya sauwaka na fice simi simi banji dadin yadda tai min ba amma yaya na iya ni na shigo ai cikin su. Nikan ban koma ba nai zamana da yaran a falo sai da sukai barci naja Fatima muka koma part din mu ko saida safe ban tsaya nayi mata ba don ta san nima ai mutum ce ya kamata tai min uzuri ai tunda bani taga na rike shi ba. Da safe ma dana tashi ban shiga gurin ta ba da wuri sai da rana ya dan yi sosai nashiga naje dakin ta nagaida ita. Ta amsa min kadaram kada ham ban tsaya ba na juya na fita mun dan zauna nai hira da yaran tana jin mu suna ficewa muka bar part din ta din. Tun da tace bata son surutu may zan tsaya yi har laifin nawa yafi wanda take tsanmanin nayi ta kara min wani. Ban fito ba muna ciki ni da Fatima kallo take niko ina resch dina sai dai raina ba dadi har lokacin. Da dare naja Fatima muka nufi part din tana zaune a falon ta muka gaida ita tace Fatima kina gidan ashe ? Tai murmushi tace ina nan hajiya yaya jikin mun baki guri ne kada mu damay ki kina son hutu shiyasa baki gan mu ba. Tace OK, Ta fahinci magana karamar yarinya tai mata tadago kai ta kalleni taga ina magana a hankali da jinior yana kada kai shima yaron alaman amsa min yakeyi. Muna ta hiran mu da yaran ta mayar da hankalinta ga wayan ta muma sha,anin mu muketayi. Sai wani dan lokaci na mike ina masu sai da safe ita dake barin mu yau ni na barta a gurin muka fice ta bimu da kallo. Ranan daddy yaci ya sha daga shirin hindatu da tai mai wanda ta tabbatar da babu sauran wace mace da zai kara kallo a gidan da sunan sha, awa kuma. Don ba karamin kudi, ta kashe ba ita da uwarta kan shirya ta kawai wai don kada wata mace tazo ta zarce ta a gidan. Don su a ganin su babu wata mace a gaban shi data wuyace ta sai gashi nazo ina yadda basu so ko kadan a gidan. Don su inta son ransu ne kowa ma ya fice yabarta daga ita sai shi wanda haka ko wace mace ke gurin gani a gidan mijin ta. Sai dai abin mamaki ga ikon Allah da safe ina barci na don hutun da mukeyi naji ana shafa na a hankali. Da kyat na bude idona don ina ganin kamar mafalki nakeyi sai da abin yai yawa ne na bude idanuwa na. Daddy na ke shafana son ranshi nace daddy please kada mu shiga hakkin wasu please bani ce da girki ba. Yace and so what sai akace kuma kada na taba matana don wata ko ? Nayi kokarin hana shi amma nauyin da yai min a jiki na kasa daga shi sai da naga yana son wuce gona da iri na tattara karfina na ture shi gefe daya. Ya dan kwanta da kafada daya yana mai da numfashi yana cewa why Rahama zaki hanani abinda Allah ya halasta min akan shi. Nace daddy bata wanan tsigar ba na cin amanan zama tare, daddy hakan da kake son yi nima idan an min bana jin dadi. Yana jin haka naji yai tsuki ya mike ya gyara rigan shi ya fice daga dakin ran shi a bace nace a raina yafi min. Barcin da ban koma ba ke nan namike na shiga wanka nafito na gyara jikina a part din anty na samu Fatima don tun shigan shi ta fice sasshen mu. Gajiye tace yau fa hajiya jikin nan sai a hankali don tun safe kwance take bata fito ba ko gado bata sauko ba. Na nufi dakin da sauri nake cewa anty ashe kuma jikin ne yau ba dadi haka da kyat ta bude idon ta tace dani wallahi Rama bana jin dadin jikin nawa gaba daya ya dibge min ne. Nace bari na hado maki tea ki karya ki sha magani ko tace dani banjin cin komai yanzu na dai fice ban bi ta nata ba na hado mata tea mai kauri nakawo mata. Da kyat na kamata tasha tea din na dauko maganin ta na harhada mata tasha ta koma ta kwanta saii naga ta dan fara zufa a hankali. Ina zaune gefe nace anty Daddy ya sani kuwa kina jin jiki haka tace ya shigo da safe dai ina kwance. Har ta danji sauki zuwa yamma kuma sai jikin ya motsa mata haka muka kwasheta zuwa Asibiti nida Gajiye don bai dawo gida ba shi. Mun sai da aka bata gado kusan awa biyu muna kanta ya shigo nan duk ya rude hankalin shi ya tashi sosai. Baidade da zuwa ba wayan shi yai kara ya daga da alama tambayan shi akayi yace eh nadawo nafita gani nan asibiti wurin Saade ba lafiya . Tace to tana jiran shi don dare ya somayi a lokacin yace da ita ban fa son rashin imani kina jirana may zanzo nai maki wanda yafi wanda nakeyi nan yanzu yai tsuki ya kashe wayan. Barci take an samu nunfashin ta ya dawo daidai yakai dare sosai tana barci bata ma san yazo ba har ya tafi. Ranan a gurin anty muka kwana nida Gajiye banyi barci ba ina zaune a kanta cikin damuwa da halin da take ciki. Sai kusan uku na dare ta falka ta sauke idona a kanta tabi dakin da kallo tace Rama kwantar dani sukayi ko ? Nace eh anty sannu yaya jikin tace da sauki Rama sannu da kokari kinji nagode. Nace haba anty bari gode min don Allah, Allah dai ya baki lafiya ki koma cikin yaran ki lafiya tace to Amin Rama. Barci ya kara daaukanta sai da nai sallah na dan runtsa kadan shigowan daddy kuma na falka ban kara kwantawa ba. Ta samu sauki sosai bisa ga yadda aka kaita da daren don tana dan mikewa zuwa bandaki takuma zauna idan ta gaji da kwanciya. Ban je gida ba haka na zauna da ita komai nike mata ina bata kulawan da ya dace sosai. Abinci ma bacin sa nake iya wa ba sai dai na dan taba na barshi ban iya tsayawa naci don damuwan da nake ciki. Babu wacce tazo duba anty har dare mune da ita sai yan uwanta dake shigowa dubata jefi jefi. Sai bayan sallah magariba sai ga daddy ya dawo tare doctor din suka shigo dakin nan ya dan dubata ina yi ina mashi bayanin improvement din da ake samu. Yace wai Alhaji na tambayeka wanan yarinyar ta gidan ka ko dai likitace itama naga tasan komai akan harkan mu haka wancan karon naga tayi. Yace insha Allahu nan da dan lokaci ta zama kamar ka ita ma don shi take karantawa yanzu haka. Yace very intrested amma tana da kokari wallahi don tasan aikin ta sosai wallahi. Ina son naga mace na aikin likita don yana da kyau hakan sai dai matan mu basu son yin haka sosai. Muna da karamcin likitoci mata a arewa amma a kudu suna dasu sosai don sun san amfanin hakan garesu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENnABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , , IDAN KIN BIYA DON ALLAH KADA KI TURAWA WATA DON HAKA CIN AMANAN ZAMA NE DON BA A YAFE BA SABODA ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , , 49 Bayan likita ya fita ne daddy ya dan karasa gurin anty yake cewa da ita yaya take ji yanzu tace da sauki kanta da kafa ne kawai ke mata ciwo. Ya zauna ya jawo ledan lemo yana wade mata a hankali yake mika mata tana sha. Sai da tasha lemon sosai tace ya isheta ya barta hakana andan taba hira ya juyo inda nake yace to ke yaya muje ko ? Nai saurin dago kai ina kallon shi tare da cewa daddy nan fa nake zaune tare da anty. Anty tace Rama tashi kibi mijin ki mana baki da tausayi ne yaushe rabon shi dake da zaki zauna nan . Alhamdullahi ai na samu sauki ga Gajiye tare dani da kuma hafsat wata yar uwarta ce tazo tana zama damu. Ban so ba banda yadda zanyi na mike a hankali don shi har yai masu sai da safe ya fice ko. Nima nai masu sai da safe nafice daga dakin na samay shi a mota yana jirana. Na shiga banyi magana ba har ya tada mota muka kama hanya ba wanda yai magana cikin mu. Ya tsaya hanya yai yan sayayya muka nufi gida muna shiga na wuce part din mu ya ce nazo na dauki leda daya nakai wa yara suci na koma na karba na shige abina. Suna falo suna ganina suka taso suna cewa basu gannin ba tunda safe ina naje nace baku san mummy ba lafiya bane halan. Allah ya bata lafiya suke fadi nace amin namika masu leda kazane da fresh milki nace suci su sha sai a kwanta. Part dina na nufa na gyara jikina yadda ya dace na fito na sa suka kwanta Fatima ta rufe gida na nufi gurin daddy da shirina. Na shiga da sallama na samu shima ya fito wanka yace dani ki rufo kofa ki shigo min da ledan nan yuwa nake ji sosai. Nace baka ci abinci bane daddy yace wa zai bani tunda keda zaki bani bakiyi tunane na ba wakike son ya tuna dani kuma ? Nace daddy ba hakana bane kaga anty tana son kulawa yace ba mutane ne a gurin Rahama nine ban son kulawa ko may ? Nace naga ita bata da lafiya ne ai yace to ni baki kyauta min ba kimazo mu dawo gida kika tsaya min gardama gaban mutane. Nace daddy kayi hakkuri idan ranka ya baci don Allah bawai nayi haka da wani manufa bane. Yace dadina dake saurin ban hakkuri idan kinyi laifi ko mutum nason kamaki da laifi sai ki kashe mai jiki da ban hakkuri. Bani naman nadan ci ko kadan ne na mike na dauko mai ledan na dora saman plate din da na shigo dashi daga falon. Ni da kaina na nake yaga mai yana ci har yaci sosai yasha milki din na fahinci yaji yunwa sosai ashe. Nakawo mai ruwa ya wanke hannuwan shi ya hau gado sai da n zubar da ruwan na kawar da kayan na wanke hannuna na shigo dakin na samu har ya kwanta ko. Nima kwanciya nayi naji ya jawoni jikin shi yana sauke numfashi, a sannu ya fara aika min da sakkonnai wanda ban san lokacin dana fara mayar mai da martanin hakan ba ya jefa mu nida shi cikin wani duniya da ban taba shiga ba koda a mafalki ne. Ranan mun murji junan mu don ya matar dani damuwa akan komai na duniyan nan sai kace a ranan ne muka fara sanin junan mu dashi. Nai mamaki wanan mahaukacin son da daddy ke gwada min kamar da ya dawo bai kwanta da ko wace mace ba a gidan sai ni. Wata hudu da kwanaki ai ba wasa ba ga maurata ba, a tare sai da muka gaji dan kan mu bawai mun gundura da juna ba yakyale ni. Gashi daddy yakai jarumi wurin iya sarrafa mace gashi baida saurin gamsuwa sai yakai ga more bukatan sa akan ka. Ya kuma tabbatar kema din kin gamsu dashi sosai yake sauke gajiyan shi gareki. Dakin yai tsit na dan lokaci guda sabanin kukane ko haniniya irin na ingarman doki da yakeyi saboda irin ni,imar da yake kwasa a wajena ranan. Naji ya furzar da iska tare da mirginowa inda nake nai lankwas a saman gado yadan yi kamar murmushi yace. Rahama ke komai naki na davan ne ko may yasa ko yaushe nake jin ki tankar a ranan na fara sanin ki na kullun sai ya zarta na baya ? Na yarda dacewan da akayi mata suna kuka tara amma kowace da kalar niimar ta a jikin ta wai shin may yasa nake jin ki ko yaushe daban da sauran ne ? Na lumshe idona a raina nace baiwa ne na Allah da kuma gyaran mai gyaran harka wanan karon kam. Ya kara rugumay ni yana sunsunar sumar kaina yana lumshe idon shi a hankali a haka barci ya kwashe mu. Da safe ma bai barni ba saida ya debi rabon shi na samu nafito duba yaran don hankalina yana gurin su. Na samu fatima tai masu abin karyawa na hada a gurguje na daddy da wanda zaa kai asibiti nai wanka na shirya muka tafi dubo anty da jikin ta. Kallo daya zakaiwa daddy kasan yana cikin walwala da kuzari a tare dashi mun shiga tana zaune saman kujera muka gaida ita take tambayana kwanan yaran nace suna lafiya sai anjima zanzo dasu su duba ta. Sai tai murmushi tace kin san fa jinior yana tsoron asibiti tunda akai mai allura bai son sunan asibiti shi. Nace sai mu barshi gida ya zauna gadi mukan zamu zo gaida ke tace dama nasan baku son shi ai. Hafsat tace kuma gashi angonta shine kuma basu shiri Anty tace kyaleta ai nagane takon sayayya take mashi hakan don sunan shi. Ni dai murmushi nayi nace wanan mai wuyan sha,ani wake gane kan shi, ma ga abin karyawa nan ku karya na turawa Gajiye basket din da nazo masu dashi. Ta zauna ta fara hadawa daddy na zaune kusa da anty yana duban wayan shi naji yana magana akan dabbobi ina ga saya zaiyi ko ma yayi din. Don naji yace a shigo mai dasu yau din nan dasu ban dai fahinci komai ba tunda waya yakeyi. Ashe abinda ban sani ba shine ya turawa babana kudi masu yawa wai a sayo masu shanu kuma yace idan ya sawo din ai masu kudin su su biya suna son saka su a gidan gonan su ne ai kiwon su ciki. Ba karamin dagawa baba ya samu ba a wanan harkan sosai don riban ma kawai ya ishe shi dogaro da kan shi. Mun dan dade asibitin mukai masu sallama muka barsu don zanje inyi abinci saboda daddy da yara dake gida. Gajiye tace dani ai Fatima zata iya girka masu mana nace daddy kin san jiya da ban koma nayi ba haka ya kwana da yunwa baici abinci ba. Anty tai murmushi tace ai nasan ba zaici ba dama na matan shi ma yaushe ya tsaya yaci balle na Fatima. Nace anty bai tausayawa yaci yayi dadi fa shi dai yana da wuyan sha, ani ne kawai duk training din ki ne hakan fa anty . Ta zaro ido tace ni Rama sherin da zaki kulla min ke nan kuma kisa matan shi suji suce gaskiya ne dama suna kuka dani ga komai. Muna cikin magana sai gashi ya leko yana fadin malama kin shanyani a mota kin barni fa. Nai masu sallama muka fito tare yana gaba ina binshi baya har muka kai inda ya aje mota muka shiga. Maimakon mu tafi gida sai ya biya dani gidan gonan su mukaga shanayen da aka sayo mai iri ne masu kyau idan sun samu kiwo zasu kara bun kasa ne sosai. Ban ya gama gani muka bargona muna hanya yace dani kin san wanda yasoyo min su Rahama nace a, a . Yace baba na turawa kudi a kauye ta sayo min su na juyo da sauri ina mamaki nace dukka daddy yace dukka mana wasu ma zai karo min su Nasir da jinior zan sayawa da kudin maman su dake gurina. Kallon mamaki nake mai yace kina mamakine nace ai dole daddy yace may ye na mamaki kuma ya samu da kamana yanzu. So nake ya bunkasa ya bar aikin wahalan nan idan ya samu sai irin wanan business din tunda muna saya nan gaba kuma idan mun tara sai a canza wani sana,an. Nace a hankali daddy na gode yace namay fa nace wanan karamcin haka ba kowa ne zai iya shi ba. Yace ni da yaiwa karamci fa ya haifa min zukekiyar mata ina more rayuwana har tana sani kuka ? Nai murmushi ya kamo hannuna yace wallahi Rahama duk wace ke gyara min ke haka da zan santa danaje nai mata godiya. Nace kai daddy wa kuma zata gyarani kaima kasan abin ai natural ne tace na sani amma najiya gaskiya na daban ne don kin so zuzutani wallahi. Yace banki ba kullun ace na samu wanan ni,imar a rayuwana dagani sai ke a rayuwan mu. Na danyi mai har da ido nace daddy kabar wanan mafalkin don Allah kaima kasan hakan bai taba faruwa a kan mu ai. Yace ai hasashe nayi bawai nasan zaiyi ba sai dai kuma kada ki manta da Allah. Nace ni daddy insha Allahu bani daga cikin matayen dakan shigo gida su samu mata da mijin su su wargaza masu farin cikin su. May zai sa nayi fatan haka tunda Allah bai mai dani baya ba a cikin su a gurin ka. Muna shigowa gidan muka hadu da hindatu itama dawowanta ke nan ashe satan hanya tayi ta fita zuwa wani wurin sherin ta. Sai gashi Allah ya kamata maigida ya ganta sai ji nayi yace good yau Allah ya kama min yar iskan nan watau ita bata jin magana ko ? Muna parker itama tafito tun a mota yace dakata koma inda kika fito kada ki sake ki shiga min gida ki koma inda kika fito. Na bude mota nafice na barsu nan suna rikici ban san yaya suka kwashe ba a can na shiga na samu fatima na aiki mukayi tare da ita. Sai la, asar muka kwasa muka nufi asubiti don nayi abinci har na dare saboda sai dare zamu dawo ni nakai su sai dai ba motar hindatu a gidan yasa nasan suna cikin fitina ke nan. Allah ya kyauta nace dasu muka fice abin mu anty na ganin yaran taji dadi suka manne da junan su suna murna da hira tsakanin su. Na sulale na fita Zarah na kira ina fada mata ke zarah wallahi hajiya mai gyaran harka tayi wallahi sai na samu fita zaki rakani in kai mata tukwici. Tai ihu tace abu yayi daidai ke nan mutumiyar nace kedai kika sani tace waya fada maki borno gabas yake yarinya kina zaune dip za, a wuce ki ga mata. Koda na dawo dakin muna hada ido da anty tace ina kika shige nace ina waje ina waya da Zarah ne. Nan muka shiga hira sai da naga yaran hayaniyar su na damun ta na kwashesu mu ka wuce gida don kila a gobe za, a sallamay ta akace. Ashe bayan mu yan uwan hindu sunzo sukai ra cin mutunci a gidan a wurin maigadi nakeji yace don Allah hajiya kada ki kula mata koda sun dawo gareki don sunce zasu dawo su samay ki. Nace ai a shirye nake da zuwan su muka shige Fatima ta rufo kofa tana bani dariya. Can gida da ra koma da kuka ta shiga gidan su tana fadin wai na asirce miji na hanata zaman lafiya dashi a gabana ya koreta gidan. Tace mama ki duba fa duk irin kudin da muka kashe wai amma ace har ya dawo yana rawan kafa a gun wanan yarinyar haka. Shine yan uwanta sukace zasu zo gidan su min dukan tsita suga abinda za, ayi akai. Allah ya taimakeni bani gidan har yaran shine suka koma da cewa zasu dawo. Da maigidan ma ta dawo maigadi ya fada mai komai ranshi yai matukar baci yace ai zai je yaiwa mahaifinta kashedi kan haka. Yana fitowa sallah gidan ya nufa ya shiga har ciki ya samu mahaufanta yai masu magana yace wallahi duk wanda ya taba mai mata sai yasa an daure shi kuma ya saki hindu din. Mahaifinta ya bashi hakkuri yace yaya zancen komawan ta gidan yace ba yanzu ba baba sai tagama yawon ta duk inda take son zuwa sai nabata izzinin dawowa gidan. Tana kallo ya barta gida ya dawo shi kadai nan ta shiga hauka da zagi saida ta gaji. Ya dawo gida yauma irin najiya ne ta kasance tsakanin mu nasha murza saida na yabawa aya zaki ranan . Da safe aka sallamo anty muna shirin zuwa sai gasu sun dawo gida da ita nan muka cika ta muna murnan dawowan ta. Nan dai muka sha hira don taji sauki sosai tabi part din ta da kallo komai tsab kamar tana nan ba wani canji a cikin sa. ********* ********* ********* Ranan monday da safe daddy ya shirya yace zai tafi abuja tunda muna hutu na shirya tare zamu tafi. Ban so ba don ban son barin anty tunda bata gama warkewa ba sosai amma yai min jan ido dole na shirya muka tafi tare dashi. Acan daddy ya gwada min ba wata mace a gaban shi bayan ni don ya gwada min so na sahihi a can bamu komai sai murzan junan mu kawai da mukeyi. Satin mu biyu muka dawo inda na dawo masu da tsaraba mai yawa naba kowa a gidan mun samu hindu ra dawo dan Alhajin shi da kanshi ya dawo da ita gidan . Yaso ya nuna bai yarda da dawowantw ba gidan amma yana jin mahaifin shi ne ya dawo da ita dole yai hakkuri ya kyale ta sai dai ya kudurta a ranshi zai dauki mataki akanta sosai. Tun wannan lokacin takon zaman su ya sauya a baki daya tsakanin shi da ita ta rasa gane kan komai a gidan. Sai ta dauki laifin gaba daya ta dora akaina cewa nine nayi mata asiri takoma haka da mijin ta. Ni dai ban kula a haka mukai rusuming makaranta na koma inda wanan time din pratical yai muna yawa muna zuwa asibiti gurin gwaji ban da time ko kadan ga fitinan daddy daya sani gaba bai iya boye fleeling din shi a gaban kowa. Zulfa ta haihu ta samu yarta mace yaso saka mata sunan mama Laraba watau Fatima, amma tace bata yarda ba har yaso ya kawo masu fitina tsakanin su anty ta raba gardama tace tunda bata so kayi hakkuri kada a saka ta dinga cusgunawa yarinya a banza kaikuma bazakaji dadi ba gaskiya. Dole ya hakkura ya barta tasa sunan da take so din suna Nusaiba yarinyar taci dama dashi tazo duniya ke nan. Kamar kada ta haihu sai ita kuma ta fara bulo da nata tsula tsiyan a cikin gidan don ita macijiyar soshiya ce mai sari kanoke ta iya munafunci sosai. Idan ba mutum yayi da gaske ba bai taba gane sherin ta amma da yake anty ta taba fada min sai nake hankali da ita sosai bana shiga harkan ta duk yadda taso jana ajiki naki yarda da ita sam. Harkan business din cf shi yana ci gaba ga aikin su da yake samun girma ya kkara zama bunkasashe sosai matashi mai tashen naira. Tafiya ya kamashi zuwa waje inda kai tsaye ya nuna cewa dani zai tafi bai tsaya tambayan ra, ayin kowa ba bayan ya taramu yake fadi. Ina jin hukuncin da ya yanke nace daddy da sauri daddy karatuna bazai bari nai tafiya mai nisa haka ba don Allah a taimaka min ajenye wanan tafiyan dani. A hasale yace karatun ki yafi maki tafiya dani ko may Rahama ? Na duk da kaina kasa sai hindatu ce tace ai dama hakane ga rashin adalci ita da kake son zuwa da ita bata damu ba muda ke son zuwa ka hana mu. Tsawa ya daka mata yana cewa ki rufe min bakin ki ke yanzu in kina da hankali ba abin kuya bane a gurina ace ban taba fita da Rahama ko ina ba duk zaman ta gidan nan. Ita kuma da anyi magana sai tace wai ita karatun ta karatu kike ko bauta aure da zaki dinga fakewa ga karatu kina kuntata min. Kowa a gurin ido ya sa mai yadda ya rufe ido yana fada haka akan tafita da mace a gaban kowa ba kunya kuma kowa ya gane manufar shi. Anty da dama ba halinta bane idan an zauna yin magana don kama mutunci sai tace baka riga ka yanke hukunci ba yace hakane tace to ai shike nan ke Rahama sai ki fara shirin tafiya bashi ke nan ba zance ya kare kai kuma kayi hakkuri tayi kuskuren yi maka mussun da tayi. Tana fadin haka ta mike ta bar falon hindatu tai tsuki tace munafunci dai baiyi ba wallahi. Wai mutum ya dinga karya da cutar kan shi wai shi don ace dashi nagari salihi ko may oho ? Zulfa ta mike tana cewa wanan kuma matsalar mutum ni dai nasan idan zuwa na yazo babu mai tauye ni ga zuwa ai ya kwana gidan sauki. Ta mike ta saba yarta a kafada ta bar falin sai nima namike nafice abina na barshi da hindatu tabi bayana da harara. Taja tsuki tace ni banga abinda wanan figagan yarinyar tafi wani dashi ba amma kake wanan rawan kafan akanta. Yace kema ai nayi a kan ki dai ko kuma har yanzun din ma inayi ko akwai abinda nai wa wata a gidan nan ban maki ba ? Tace gashi kuwa kai min akwai ranan da ka taba jajircewa akan sai nabika a bainan jama, a haka yadda kayi yau akaina ? Kyaleta yayi yaci gaba da abinda yakeyi tagaji da zama ta mike tafice falon rai a bace. Sai da dare dana shigo gurin anty na zauna take cewa yanzun nake batun tura Gajiye ta kira min ke sai gaki. Nace na tsaya gyara wardrove dina ne da akai min gogu jiya nake cewa da ita wai anty ni sai naga kayana har guda biyu an yanka min ta kasan zanin sai rigar ta wurin hammata shima an gutsira. Tace yanka fa nace wallahi anty to kada kiyi amfani da su ki bayar dasu a sadaka don ba a san may akayi da shi ba. Shiru mukayi kowa da abinda yake tunane a ranshi kan wanan bakon al, amarin sai can anty tace dani Rama may zai sa mijin ki yace ga abinda yake so ki ki tsaya kina gardama dashi a gaban kowa haka. Nace anty ni ba wai nayi gardama bane kawai naga karatuna zai tsaya ne don yanzu kinga ko yaushe muna zuwa gwaji asibitoci. Wai karatun may Rama kina ganin cewa ko kinyi wannan karatu besty zai barki kiyi aiki ne. Cikin mamaki na dago kai ina kallon ta tace sa,arki daya shine kin fara karatun nan kafin kuyi aure kuma yasan yadda kike son karatun nan shiyasa ya daga maki kafa kawai. Amma idan kina mai wanan gardaman haka kan bukatan shi zaki iya jawowa kanki matsala nan gaba. Nai shiru na dan lokaci can nace anty nagode insha Allahu zan kiyayye hakan na fara shirin tafiya ba wasu kaya na dauka ba sai dogon riga guda biyu. Tashin dare zamu yi don zamu biya saudiya muyi umura yace haka yasa nai shawaran idan naje can sai na saya kawai. Ana jiran afito da kayana sai ga yar jakka na fito dashi duk matan nashi suna tsaye suna ban kwana dashi. Duk suka bini da kallon mamaki na karasa gurin anty duk wanda ya ganni yasan ban son wanan tafiyan a raina na karasa gurin anty . Na rugumay ta sai kuka tadan kashe murya tace dani may ye haka Rama kada kiba mijin ki kunya please. Na daure na share hawayena nake cewa da sauran sai mun dawo a takaice daga haka na shiga mota muka bargidan da yaran suna daga min hannu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA GASKIYA, , , , , IDAN KIN BIYA KIKA TUWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON HAKAN CIN AMANAN ZAMANE, , , , 50 Mun isa Aminu kano international airport kai tsaye muka nufi gurin screening don mun zo a makare. Bamu dade ba aka fara shiga jirgi ina wanan ne karona na farko da zan fara shiga jirgi a rayuwana. Sai da na dan dafe kaina bayan belt din dana daura saboda yadda na ji dagawan mu. Tsawon lokaci muka dauka a zaune tun ina marmari har na fara gajiya da zaman. Da asuba muka isa saudiya inda naga wani yusuf yazo taron mu a jidda nan ya dauke mu zuwa masaukin da aka tana dar muna mu dan huta. Hotel ne tsarare mai hawan bene kusan goma sha tsayawa fadin tsaruwan wurin bata lokaci ne nidai yar kauye sai aukin baza ido nake ina kallon ikon Allah. Na fahinci daddy yana fushi dani ne wanda bai rasa nasaba da kin biyo shi danayi da girma da arziki. Sallah nayi tundaga magariba ishai da asuba ban ko tsaya neman abinda zanci ba don barci da gajiyan dake tare dani. Barci nayi sosai sai sha biyu na falka koshi yunwa ne ya falkar dani lokacin dole na tashi abinci na gani an aje min na fada ban daki na sake wani wanka nafito na zauna naci na koshi sannan namike na kimtsa jikina. Daddy bai dawo ba sai da yamna lis suka shigo shi da abokin shi ina jin bashi kadai bane nai sauri jawo hijjab dina na saka. Nai masu sannu da zuwa tare mikewa na bar falon nan suka zauna tare da baje wasu takardu da ban san ko na may ye ba. Ina ciki kwance sai gashi ya shigo dakin da saurin shi yana cewa na miko mai wani jakkan shi da muka zo dashi shi kuma ya dauki laptop din shi ya fita nabi bayan shi dauke da jakkar. Na tsugunna don girmamawa na aje mai a gaban shi inda yake zaune saman kujera masha Allah yusuf yace cikin hausan su na yan saudiya yake fadin. Wanan dabiar na matan hausawa yasa nakeji nima naje nageria nayo aure a dinga min haka. Murmushi daddy yayi kawai ni dai nabar gurin tun ba, a jamin wani sabon fitina ba kuma ina fama da wani. Sun dauki lokaci a tare sai dare so sai ina shirin kwanciya naji daddy yana kirana a falo. Na mike da sauri na nufi falon suna tsaye tare da mutumin yake cewa Yusuf zai tafi yana son ku yi sallama ne. Yusuf din ya juyo gareni tare da cewa hajjiya Rahama na gode ni zan tafi sai ki kula min da mutumina kin san shi da ka,ida don nasan halin shi sai kinyi hakkuri sosai duk da naga alaman kina da saukin kai sosai. Daddy yai murmushi yace yusuf sheri kuma zakai min kasa ta dinga dauka na mugu kuma yace na san ka ne ai. Kudin su na can ya miko min masu yawa yace amarya kiyi hakkuri da wanan mijin naki bai fada muna da ke zai shigo ba shi yasa ban shiryawa zuwan naki ba. Na karba cikin girmamawa tare da godiya suka fita daga dakin sai baya fitan su na kallin koren kudin dake hannuna masu yawa an rubuta masu Riyal , , , , Na bude bakina don mamakin yawan su duk da ban san adadin yawan su ba a hannuna amma nasan ba karamin kudi bane hakan. Na koma daki tare da dora kudin saman drower na koma na kara mulke jikina yadda ya dace na kwanta. Ban dade da kwantawa ba barci ya dauke ni koda daddy ya dawo ya samu nayi barci ko bai tayar dani ba sai da ya gama abinda yakeyi ne ya zo kwantawa yaga kudin da aka bani, na aje a saman kujera yasan shi nake jira dasu barci ya dauke ni. Bai tayar dani ba don yasan gajiya ne don haka shima dama a gajiye yake ya samu guri ya kwanta. Sai da asuba na falka ranan ko sallah nafila ban samu yi ba na idar ne yana zaune saman sallaya yana karatun kur, ani. Ban zauna ba na koma na kwanta tare da dauko wayana dake kashe tun a jirgi na kunna. Gari na haskawa sosai ya mike ya fada yai wanka ya fito dogon riga kawai ya zura ya hawo gadon shima ya kwanta nasan dan hutu yake so a ran shi. Mikewa nayi daga kwance don har barci ya fara dauka na nace dashi daddy ina kwana ya gajiyan hanya ? Alhamdullahi yace dani a takaice ya gyara kwanciyar shi da kyau tun ina tunane a raina har nima barci ya dauke ni. Ban falka ba sai lokavin sallah azahar nai wanka nayi sallah sai kuma na fito falo ashe yana falon zaune sai aiki yake cikin laptop din shi. Banyi magana ba na wuce wurin fridge din falon wanda sai wanan lokacin na bude shi drinks ne a ciki shake na zaro wani danaga anyi da mangoro. Na samu kujera na zauna ina dan tsotso ina duban takardan da nazo dashi na karatuna kamar nasan da wanan kadaicin na dauko takarduna wanda sune suka cika min jakkata dama. Karatuna nake hankalina kwance inayi ina tsotson drinks dina mai sanyi sosai jikina ya bani kallona yake ban dago ba naci gaba da karatuna sai da na kwatanci lokacin sallah yayi na mike na shiga ciki nai sallah ban fito ba kuma ban nemi abinci ba. Ina gamawa na shafa addua na nafito na dauki takarduna dana bari na koma ciki can na ci gaba da karatuna ina yi ina hutawa sai tunane kawai a raina. Ranan yin zur daddy bai fita ba yana zaune yana ta fama ture ture a laptop din shi bai kula ni ba nima ban kula shi ba. Ina gama magariba na kwanta abina sai barci sai da ya gama ya shigo dakin ya samu nayi barci hankalina a kwance. Ya dan tsaya yana kallona yaga yadda gashin kaina ya barbaje a kaina har ya dan rufo min fuska, ga takarduna danake karatu sun zube a kasa ya karasa bakin gadon ya duka ya kwashe min ya aza saman drower. Yai wanka ya fito sai da ya shirya ya koma gefen gado ya kwanta zuciyar shi fam da tunane yaso ya tayar dani amma sai ya daure ya ja ya rufe jikin shi. Kwanan mu uku a jidda muka kwasa zuwa birnin madina bamu kwana ba saida muka mika gaisuwar mu zuwa ga mafificin halitta tare da sallah a masallaci mafi daraja muka dawo masaukin mu. Shirin kwanciya nake ya shigo dakin ya danyi abubuwan da yake na al, ada ya tako zuwa inda nake kwance zama yayi dap dani yadda jikin shi ke gugan jikina yake cewa Rahama nasan idon ki biyu kina jina ki tashi muyi magana. Don bazan yarda falala da daukakan dake cikin garin da mafi fiyayyen halitta yake kwance ba ya wuce muna cikin wanan halin na rashin fahintar juna ni dake ? Jin abinda yace yasa na bude idona tare da cewa daga kwance fushi daddy ni bani fushi da kai ai. Akan may zanyi fushi da daddy na riban may zanci idan nai fushi dakai a rayuwana daddy kana a matsayin mijina kuma gin shikin rayuwana ? Murmushi naji yayi tare da cewa ban tabbatar da ina da wani kima ba a gunki tun da har kina iya share ni na tsawon lokaci. Rahama kin bani mamaki don da wani yace zaki iya tauye min hakkina ki hanani abinda Allah ya halasta min akanki zanyi mussu ga hakan. Amma sai gashi kin rufe idon ki kin juya min baya ba ruwan ki da damuwa na bayan kin min laifi amma girman kai ya hana ki ki bani hakkuri ga hakan. Nace cikin wani murya daddy nice kuma nai laifi bakai da ka rabani da diya na ba kazo dani nan kasar mutane ka watsar dani, dani da babu duk daya a gare ka. Yai murmushi tare da sa hannayen shi ya juyo ni gare shi yace ke shine naki fushin na rabaki da yaran ki ? Niko ashe sai na fadi na mutu ko ni da aka watsawa kasa a idon kowa na fifita akan kowa amma kika watsa min kasa a ido gaban kowa. Nace to daddy ba gashi nabar komai dake gabana na biyo ka ba kuma duk da haka ban tsira ba a gun ka. Badon san raki kika biyoni ba Rahama ban taba zaton akwai matar da zan wa tayin tafiya wani kasa da ita ba har tai min mussu akan hakan ? Rahama ko don kin ga na mutu ga son kine har kurciya ya rude ki a gaban kishiyoyin ki kikai min haka? Jikina yai sanyi nasan ban kyauta ba to amma ni kuma hujjana shine ban son nayi wasa ne da karatun dana wahala akan shi sai da nazo gap da cin ribar karatun kuma na watsar dasu. Sai dai a fili cewa nayi nayi kuskure daddy a yafe min bazan koma yin hakan ba insha Allahu. Ido ya kura min na dan lokaci can ya nisa yace dani ya wuce sai dai bazan hakkura ba sai an biyani bashin da aka daukar min. Nace bashi kuma daddy yace au baki ci bashina ba ko may kike nufi kina nufin kinci bulus akaina ko may ? Ban aune ba sai jin da nayi ya kwanto min tare da cire min hannaye na dake kare a kirjina daga haka muka fara mantawa da komai a ran mu. Mun dauki tsawon lokaci bamu san inda muke ba sai da muka biya junar mu bashi muka hakkura da junar mu. Wanan ya kawar da hushi da zafin junan mu da muka shigo kasan dashi da asuba ma a masalacin harram mukai sallah a can kuma muka wuni sai dare muka dawo masaukin mu. Yau ma ba abinda ya fasa wurin gwada min kaunarshi a gare ni asuba zamu mike mu nufi gurin sallah a babban massalacin Annabi. Kwanan mu takwasa muna bauran Allah bilhaki sosai muke kai kukan ala, muran mu ga Allah washe gari muka wuce birnin makka can ma ba abinda muka fasa ibada sosai mukayi muyi umurah mun kuma yi dawafi yafi a kirga kwanan mu biyar yakaini nai sayayya sosai. Ya ciro kudi zai biya nace ga kudin da Yusuf ya bani nace dashi yace wanan aike yabawa sai ki san yadda zakiyi dasu. Wani shago mukaje da wata kawar da nayi don masaukin mu daya dasu nan muka dan saba dasu har mijin ta. Na saro kaya masu yawa da kudin sai da nai mamaki wanan kudi wasu irin albarka ne haka dasu. Gida ya turo da kayan inda zasu fada a hannun bashir har lokacin da zamu dawo kasan ya bamu. Daga saudiya muka kwasa zuwa kasan Chaina inda zasu hadu da wasu abikan shi suyi abinda ya fito da mu daga gida watau business. Tun zuwan mu kasar chaina abubuwa sun taru sunyiwa daddy yawa akai ddon ko lokacin kan shi baida balle na wata Rahama can don basu zauna ba sai kokarin shige da fita sukeyi. Wanan daman nai amfani dashi naga wani guri da ake lectures akan likitoci na roke shi da ya bari na dan jona su kafin mu bar kasan bai ki ba don dama zaman da nake na kadaici ya na damun shi sosai. Don bai san aikin zaiyi zafi hakan ba akansu sosai sai da mukaje ne ta fahinci abin ba haka bane. Ranan da na fara zuwa daukan darasin sai da na raina kaina a gurin sosai don sai naga kamar mu ba karatu muke ba acan. Haka na daure na kuke na mayar da hankalina nakuma samu karuwa sosai ga abinda naje nema a gurin. Sai idan na dawo da yamma nakan kira gida mu gaisa dasu anty wani lokaci na samu yaran wani lokaci kuma ace sunyi barci ko sun fita. Daddy wani lokkaci har yakan yi kwana biyu baya tare dani idan sun je wasu garuruwa na kasan dole sai sunyi kwanaki zasu dawo. Na kwantar da hankalina ina samun karuwa a gun karatun da nake zuwa dauka can. ********* ********* ********* Barina garin ya ba matan daddy damar aiwatar da shirin su sosai akaina dukkan su biyun ba wacce ta zauna kowa da irin nata aike da take tura min. Inda Anty kuma rashina kusa da ita yasa tasan muhinmancina a gareta sosai don ba karamin kewa na tayi ba a lokacin. Ga yan rainin wayon matan gidan bata da shakat a kan su sun saka mata yara a gaba da kiyayyan da suke masu. Bata son fitina dole take kyalesu don ruwan ciki irin nata tana ji tana gani yara da gidan uban su amma an hasu shakat a gidan. Wani lokaci sai Gajiye ta rufe iddo tayi magana da kanta akan abinda ake a gidan haka yasa anty ta takura kan ta sai kafa kafa take da yaran ta da ita kanta don yaran sun riga sun saba da irin abubuwan da nake masu yanzu gashi kuma an hanasu sakewa su da gidan uban su. Ranan a gajiye na dawo ban ko hutaba na kira wayan su yadda naji muryan ta sai banji dadi ba take nagane bata cikin daddin rasi. Walau ciwonta ko akwai abindake damun rayuwan ta haka dai muke magana sama sama da ita. Gashi kuma bawai fushi take ba balle nace ko dani take fushin don harda tambayana tayi Rama kina dai maida hankali ga karatunki ko ki samu ki dan diba kafin ku dawo nace da ita eh anty . Tace don Allah ki ta hakkuri da mijin ki maza sai hakkuri balle maa yanzu da kike can ke kadai dole sai kin hada da hakkurin wani abin. Bayan mun gama wayane na zauna ina tunanen may ke damun anty ne wai nidai in ba ciwon tane ya taso ba take boyewa ? Fatima na kira nake tambayan ta tace lafiyan ta kalau kila dai rigimar da akayi akan yara ne nace shine har zai damay ta haka take cewa . Mama ihisan ce ta daki Nasir wai don suyi fada da ihisan a school da suka dawo shine takama yaron ta mamare shi kuma tasa ihisan tai ta dukan shi nan dai ta labarta min irin halin da ake ciki a gidan. Raina ya baci har nai sallah na idar raina bai daina baci ba ina zaune na kunna tv wanda kusan kallon dai kawai nake bani fahintar abinda ake a tv . Har ya shigo banji zuwan shi yazo ta bayana tare da dan rufo min idanuwa a hankali na sauke ajiyan zuciya tare da kamo hannayen nashi ina mashi sannu da dawowa. Nan ya zube saman kujera yana fadin wassh Allah nagaji wallahi mikewa nayi na dauko mai goran ruwa da cup na kawo mashi tare da balle marfin goran na zuba mai namika mashi ya shanye na kara mai wani ya sake shanyewa again. Bayan naje cup din daya sha ruwan , ya mayar da kanshi bayan kujera tare da mike kafafuwan shi na duka a hankali nafara cire mai takalman kafan shi tare da cire mai safan dake saye a kafan nashi Yace Rama idanun shi still a rufe na amsa da na,am daddy, yacce may kike tunane haka har nashigo da sallama bakijini ba ? Kamar nace dashi gida sai dai na dake a fili nace naga yau tun safe daka fita ko waya bamuyi bane dakai. Yace nasan zaki damu da hakan amma ba wanan bane tunanen ki fada min may kike tunane ne wai ? Daddy babu komai na bashi amsa tare da mikewa na kwashe takalman da nufin mayarwa inda yake aje takalman shi a falon. Ban yi aune ba naji ya jawo hannuna na fada a jikin shi ya mayar da hannayen ya rufe dani yai min zobe da hannuwan nashi. Ya kura min ido na dan wani lokaci yace dani Rama ki fada min may ke damun ki nace ? Maimakon nayi magana sai idona ya kawo kwalla kawai gida kike son komawa ?. Kai na girgiza mai ban dai yi magana ba dashi yace kin gaji da nine ko nai saurin dago kai tare da kallon shi na girgiza mai kai kawai. Yace idan ba kin gaji da zama nan dani ba akan may zaki sawa ranki damu ki shirya sai na sakaki jirgi kii koma gida . Don ni ban gama abinda ya kawoni ba nan din, cikin daurewa nace dashi ba hakana bane wallahi wai hindatu ce ta mari Nasir akan ihisan har sai da ya kwanta ciwo. Yace a zafafe what ? Mari fa kika ce Rahama marin karamin yaro may ye mata haka har haka ya faru. Nace cikin kuka wai sunyi fada da Ihisan a mota ta yaga mai note book din shi shine uwar ta mare shi har uku takuma rike shi ihisan din ta rama bugun ta son ranta. Ita uwarshi fa tana may hakan ya faru dabata dauki mataki ba kuma bata fada min ba. Nace daddy may kake tunanen anty zata iya yi akan hakan koda lafiya gareta balle halin da take ciki na rashin lafiya. Nan dai na fada mai komai ranshi yai balain baci sai maimaitawa yake yana fadin mari fa abin da mamaki gaskiya. Amma kyale su dukkan su zan dauki mataki ne a kan su ya daga waya ya kira waya bayan sun gaisa ne yake cewa da anty din yace ta bashi Amira aka mika mata wayan ta karba suka gaisa da uban yace abawa Nasir din. Amira tace daddy Nasir baida lafiya yau two days ke nan sai aka karbe wayan a hannun ta yace da uwar mika mata waya muna magana zaki karbe wayan a hannunta? Yaro baida lafiya baki fada min ba ta na fada min kuma ki karbe wayan gurin ta mika mata muyi magana da ita. Zatai magana yace ba Amira wayan yanaji ana cewa yarinyar kada ki fadi wa daddy abinda ya samay shi. Yarinyar ta karba tace daddy yace Amira na may ya samu Nasir ne baida lafiya tace maman Ihisan ce ta do sai kuma tai shiru. Yace maman ihisan tayi mai may Amira tace daddy baida lafiya ne yace Amira bakya son na sayo maki katon teddy dakikace kina so ne tace ina so daddy. Yace to fada min may taiwa Nasir din tace dukan shi tayi daddy ita da ihisan har bakin shi ya fashe idon shi ya kwantar da jini. Kuma ta shure shi a ciki ya runtse idon shi yana jin zafin maganan a ran shi bai bari anty tai magana ba ya kashe wayan. Yana mamaki ita Saade wai wani irin sanyin raine da ita haka wai da har za ai wanan aika aikan taki fada mai kuma ta hana a fada mai. Daga haka yamike ya shige daki wanka yayi ya canza kayan jikin shi ya fito na gabatar mai da abincin shi. Ci yake kamar bai son ci haka yasa na dan matso kusa dashi na karbi spoon din a hannun shi ina diba a hankali ina bashi har na samu ya danci sosai. Na kwashe kayan zuwa kitchen dasu ya zauna wurin yai shiru naga ya dan shiga damu na dan daure na kawar da nawa damuwar nace dashi. Daddy kada wanan zancen ya damay ka haka duk abinda mutum yayi don kan shi idan ta cuta mashi yau ai gobe bazata cuta mai ba. Shi yaro an haife shi ne ba, asan mai cin amfanin shi ba watarana zata ji kunyan abinda tai mai da yardan Allah. Ya numfasa yace ita ai bata san hakan ba da batayi ba ni bani daukan hindatu cikin masu hankali da amfani da ilimin su shi kishi haukane Rahama ? So take tasa kiyayya a tsakanin yara na komay abinda yai Nasir shi yai ihisan ai nace hakane daddy shi zai sa ka kyale ta idan halinta ne ai zata kara. Ya limshe idanuwan shi tare da mikewa saman kujera na karaso tare da saka kafafuwana na zauna a saman jikin shi yadda kirjina zai iya gogan jikin shi. Ajiyan zuciya ya sauke nacs hakkuri za, ayi don kowa da halin shi ake zama dashi amma bata kyauta ba gaskiya. Kamo hannaye na yayi yana wasa dasu guri daya yace hindatu bata san don iyayye da dubaiyya nake zaune da ita ba har yanzu. Dadin may naji ga auren ta ba kwanciyan hankali a kaina babu ga abokan zama. Babu gwani a gurin hindatu kanta kawai ita tasani sai yarta bata damu da damuwar kowa ba a duniya. Ta manta da yadda aka sakani a gaba kan auren ta na daure nayi shi badon naso ba don ni a lokacin Saade ta isheni rayuwa nake gani. Ban taba tunanen zai zo nan gaba na ci karo da wa yan nan abubuwan ba a raayuwana ya nuna kirjina da hannun shi. Na kara manna maisu nace kafin kai gamo da wa yan nan ai kayi gamo da wasu ya jawoni jikin shi da kyau yace ummumm hakane kuma sai dai su wa yan nan na daban ne ko ? Nan wasan ya canza sallon anan falon muka murji junan mu sai da na matar dashi komai a ranan na samu natsuwa. Hasken safiya ya hake min idona na bude su a hankali na sauke kan daddy daya dunkule a jikina mun rufu acikin fadin zanin rufa duk jikin shi yana a kaina. A hankali na zare jikina daga nashi na fada ban daki nai wanka saida na fito nazo na tayar dashi yai sallah ruwan dake a jikina ne. Yasa shi bude idanuwan shi ya sauke su akaina sai kuma ya dan zabura yace what Rahama makara nayi haka yau ko nafila ban samu ba ? Ya mike da sauri ya fada bathroom sai da ya karya ne ya shirya tsab dashi yace yau ba zan dade ba zan dawo mu shiga gari kiga gari don ki samu bakin bada labarin kasar chaina da kyau. Yadda yace hakan yayi ya dawo muka fita tare zuwa wani unguwa mai nisa can cikin garin gidan wani abokin business din shi muka je. Da alama su a garin ma suke zaune don har iyalinshi na garin sai dai wai mutanen kasar ghana ne su mun dan jima gidan da zamu dawo matar da mijin ta sukai min kyata na bajinta. Ba karamin alheri na samu ba ga abokan arzikin daddy ga abinda akaje nema Allah ya bashi saa sosai an yi signing din contrac din su wanda ba karamin kudi zasu samu ba ga hakan idan sun shigo dashi Africa. Shi da bakin shi naji suna hira da abokin shi suna cewa basu taba saan tafiya ba irin wanan karon don komai yazo masu yadda suke so don basu taba zaton hakan ba garesu. Shirin da naga yanayi yasa nasan mun kusa dawowa gida lokacin don haka nima na dinga sayen abin bukatan da nake so acan komai zan sayo dani da anty nake sayo muna shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANCE BATA BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANAN ZAMA TARE DAKIKAYI, , , , 51 Abubuwan sun daure mai kai tunda yake zuwa tafiya da mace bai taba irin wanan tafiyan ba da wata irin hakan . Zai ci ya sha yadda yake so zai samu kwanciyan hankali yadda ya dace ko ranshi ya baci da ya dawo gida zan san yadda nayi na sashi ya sake. Haka kuma yana mamaki yadda nake sayayyan kaya haka da kudaden da nake samu a gurin abokan shi da kanzo ko mu mutafi inda suke idan zasu tafi su kan min kyauta mai matukar daraja. Ni kuma sai nake dabaran sayen kaya ina jefa a cikin kaayan shi da ake shigo masu dashi a gida Nigeria. Babu wani wanda ke a cikin damuwa daga cikin mu munyi kyau sosai farina ya matukar karuwa don har da dan kiba nayi . Shima mI gidan yayi haske sosai ya kara kiba jikin shi da gashin jikin shi yai mashi lub lub lub dasu gwanin ban sha, awa. Ashe idan yai tafiya da mace ba karamin karuwa suke samu ba ga tafiyan shi yasa suke fadan zuwa tafiya idan ba da su za, ai tafiyan ba, don ba karamin alheri suke samowa ba idan antafi dasu a hakan. Bai kara mamakina ba sai da yabani irin kudin da yake bawa mace in zasu dawo gida nata dana sauran yan uwa tai masu tsaraban irin kayan kasan da suka tafi. Bayan na sayi wa kowa abinda ya dace na kuma yo nawa sayayyan da yaga yawan su sai da yai mamaki sosai don babu macen da yazo da ita take sayayya haka kuma kudin suna samu amma bai sanin inda suke kai kudin su agidan. Ba karamin sayayya nayi ba da kudin daya ban don na saro bedshet na kasan chaina masu kyau pure cotton na saro takalma da bags masu kyau da sauran kayan amfanin mata nima ina son na soma yar sana,a idan na koma gida. Kamar yadda muka bar garin da dare haka ma mukai wa garin saukan asuba da zamu dawo. Hamza da Bashir ne suka dauko mu dare ne kowa na barci da kyat na samu layin gajiye ta fito ta bude min kofan part din mu. Na fito saye cikin dogon riga purple, yaddin rigan mai mugun taushi da santsi, silk ne kayan sun matukar karban jikina sosai. A hankali nake takawa na fito daga motan bashir din ina tare dashi ya riko dayan hannu na ina rataye da handbag dina mai kyau da tsada a kafada na. Kowa yasan da dawowan mu ranan don haka suna jin motsin bude get suka fito don taron maigidan. Idanuwan su kar a kaina babu wacce bata razana ba da gani na gaba daya na canza masu lokaci guda. Na koma gefe daya duk da bai saki hannu na ba a lokacin yana rike da ni still ko wace tazo ta rugumay shi. Balaifi shima yai masu murnan ganin su nan guri yadan rude da surutu duk da dare ne Bashir yai mashi sallama ya juya zuwa gidan shi bayan ya sauke kayan da muka shigo dasu wanda kusan duk nawa ne don shi bai tafiya da kaya haka masu yawa. Yace dasu kowa yaje ya kwanta kafin gari ya karasa wayewa don karfe hudu saura a lokacin yace zamu dan kwanta mu huta don a gajiye muke. Basu so hakan ba sai dai babu yadda zasuyi dole suka fice suka bar mu don yaki sake ni na koma part din mu don ita antyna bata fito ba. Basu bar juna ba sai da sukai gulma na tare hindatu tace Zulfa kinga yadda wanan yar kauyen ta koma kodai ciki ne da ita ? Zulfa tace nima mamakin da nake ke nan gaba daya ta juye wata iri kamar yar wani da wata ? Sukace ba dole ba Allah kadai yasan abinda sukayi haka acan hindatu tace kin san namiji muna fuki ne ai. Bamu tashi ba sai sha dayan rana daddy ya baru na fito part din ko shi sai da naita hada shi da Allah ya bari naje naga anty don yace sai two zan fito wai ina da gajiya kafana duk sunyi wani suntum don zaman jirgi da nasha. Nashigo part din Anty dake zaune sai ganina tayi kamar a mafalki tace wai da gaske dama kun dawo ne Rama na rugumay anty da sai kallona take cikin mamaki don gaba daya na canzawa idon ta baki daya zaka rantse da Allah kace injin aka sakani na koma haka a lokaci guda yadda na goge na waye nayi kyau sosai kamar wata yar gidan wasu masu fada aji. Nace miss you anty na ina cewa ina yaran tace sun tafi school ai tunda safe Gajiye ke fada masu dawowan ku sukai ta ihu suna neman ki. Na zauna ina cewa kin san daddy da son rigima ko yanzu sai da nayi da kyat yabari nazo na ganki tace shi wanan yanzu wake batun shi ai duk ya burge ne gaba daya baijin has. Nai murmushi don na gane nufinta Fatima tazo da murnan ta muka rugumay juna cikin farin ciki. Itama ta yi kyau da ita fes kauyancin ta duk ya goge ta zama wata babba a idona. Na tambaye ta lafiyan jikin ta take cewa dani da sauki nan muka zauna mukai hira sosai da ita tace bari taje dakin maigida su gaisa nima na mike zuwa nawa part din don na huta. Tana shiga falon shi taci karo da kayyan dana muka dawo dasu a falon tabi kayan da kallon mamaki haka don tasan shi ba gwanin tafiya da kaya bane amma yau gashi yazo da kayya haka duniya juyin juyi ke nan. Yana kwance barci yake ya dunkule a guri daya kamar maijin sanyi ta dan dade tsaye a kan shi tana kallon shi ta juya zata bar dakin tunda barci yakeyi. Taji yace Saade karaso mana na gaji da yawa ne wallahi, tai murmushi ta karasa bakin gadon da yake kwance ta samu wuri ta zauna tana fadin an dawo lafiya yace Alhamdullahi. Yace yaya kuke da yaran ya jikin naki ya juyo yana fuskantar ta da kyau tace duk muna lafiya. Tace ban dauka zaka dawo yanzu ba ai ko da kace a satin nan zaku shigo yai murmushi yace ba dole na dawo maki da kauna ba hankalin ta nagareki da yara sai karatun ta da ta bari. Tace Rama ba dai rigima ba kan gashi kuma daga kai har ita tafiyan yai maku kyau sosai wallahi doon kunyi wani fresh da ku kamar ba aiki kaje yi ba ? Yai murmushi yace kuma ga tafiya anyi nasara sosai fiye da tsanmanin mai tsanmani wallahi don bantaba samun nasara ba irin wanan. Masha Allahu abu ko yayi kyau wallahi haka muke son ji ko yaushe Rama tai tafiya a sa,a ke nan yace gaskiya kan don ni abin ya ban mamaki wallahi. Nan dai yai mata bayani kan irin nasaran da ya samu ga tafiyan itama tayi mamaki kwarai kuma tai murna ta mike tana cewa bari ta barshi ya huta kada ta damay shi da yawa. Ta mike take tambayan shi abinci fa yake cewa da ita zai tashi yai wanka sai yaci. Tana fita hindatu ta shigo itama sun gaisa take cewa ta hada mai breakfast fa. Yace saboda may zaki hada min bayan kin san da wacce nai tafiya sai yamma zata fita girki mai dauka ya dauka. Bataso jin haka ba don ta shirya sosai tana son ya soma cin abubuwan da ta aiwatar akan shi lokacin. Tace ai ba don wani abu nayi ba don kawai na taimaka mata ne tunda ta dawo da gajiya ba wani abu zata iya yi ba nagani. Yace No ki barshi ai zasu kawo min daga part din ya mike zai shiga bathroom tabishi da kallon mamaki ina mukaje muka koma hakan harshi ga shi yai wani haske da kiba ya murje yayi kyau ke nan babu abinda yaje yi sai hutawa kawai da wanan shegiyar yarinyar ai zata gane kuren ta yar iska kawai. Idan tayi tayi idan bata yi bata yi ba don in maggi ya hau kan mage sai tarihi bar yar iska zanyi maganin ta sai dai hange ita dashi a gidan nan. Ya fito wanka ya shirya cikin kananan kaya ai matukar kyau dashi ya samu an kawo mai abin karyawa daga wurin anty ya zauna yana ci Zulfa ta shigo dauke da yar ta a kafadan ta. Ya mika hannu ya karbi yarinyar yana cikin mata wasa ta samu guri ta zauna tana tambayan shi yaya hanya yace Alhamdullahi. Shigowan hindatu ne ya katse masu maganan su itakuma zulfa ta daure fuskan ta don bataso hakan ba. Itama wuri ta samu ta zauna tana cewa tafiyan wanan karon harda tsaraba haka muka samu ya dan dago yana kai cibin ferfesu abakin shi saida ya hade yace. Tsaraba kuma yana ina tace gasu ko dauri dauri mun gani aje can yace kayan Rahama ne ni ban ma san may ta sayo ba ciki. Duk wanan kayan na Rahama ne haka lalai ita ina ta samu kudin sayen kaya haka kuma ? Yace sai ki tambaye ta ai tana gidan ya mike dauke da yarinyar yana kokarin bin kofan shiga gurin mu yace da su ina zuwa. Ina zaka da ita kuma miko min ita har ka dawo inji uwar yarinyar tace dashi yace hakan. Yace doka zaki saka min ni da ya ta ko may Zulfa tacee ba doka bane ina dai kafakafa da abina ne ita nake gani naji dadi a raina. Bai bata amsa ba ya fice da yarinyar ran uwar ya baci don ita dai tunda ta haifi yarta bata taba shiga da ita wani part na gidan ba sai yau zai daukan mata yarinya zuwa waani gun kuma ? Wurin anty ya fara shiga tana falon ta zaune tana waya ta kashe wayan tana cewa yau yae rowa ce aka shigo muna da ita nan ? Yace gata nan yau nazo da ita ashe ko rowan ake muna don ko ni yanzu saida akai min korafi ina zan tafi da ita kuma danayo nan ? Tace mayar mata da yar ta don Allah kada kuma ace anzo da ita nai mata wani mugun abu. Humm yace yana tambayan ina yaran basu dawo ba ke nan tace basu dawo ba ai basu san mummy su ta dawo ba ma. Ya zauna sun danyi hira da ita yana wa yarinyar dan wasa duk da ta nuna tagaji tana son uwarta da ta saba da ita. Ya mike yana cewa bari na leka wanan nasan tana can tana barcin gajiya tace Allah ya sa indai Rama ne kila dai wani abin take naji ta shiru. Ya shigo muuna zaune da Fatima kallo take ita niko ina duban waya na nan Fatima ta gaida shi da dawowa ta mike ta fice falon. Nace a, a baby kece kika girma haka namika hannuna sai ko yarinyar tazo guna na karbeta ina mata wasa. Yace taso muje ki bani magani Rahama har yanzu jikina yaki walwale min ya juya na mike nabi bayan shi dauke da yarinyar. Muna shiga falon uwar na ciki zaune ita da hindatu yadda ya barsu tana ganin yar ga hannuna take cewa miko min ita don Allah abinda nake gudu ke nan kabawa wata ya ta wallahi. Ya juyo cikin mamaki yace waye watan Rahama data dauke ta ko may ni dai na mika mata yarta data lafe a jikina tace ni dai nace abani ya ta don haihuwa wuya gare shi. Kowa ma ya haifi nashi ya dauka ban hana ba ni nawa na sani don ni na san wuyan da nasha akan abina. Tana katban yar ta wwuce a hasale tana kallon jikin yarinyar kamar may son ganin wani abu ajikin yar nata. Murmushi nayi ban tsaya ba nashige don na dauko maimaganin inda na aje mashi su na barshi da hindatu falon. Na dauko ruwa a fridge na kawo mai tare da maganin batai min magana ba nima ban mata ba. Ban fita ba don tana ciki na samu dogon kujera na zauna yake cewa kisa a kwashe kayan nan a shiga maki dasu ciki kafin a fara shigowa . Munyi waya da Tahir yace zai sa a turo maki da sauran kayan zuwa gobe humm naji Hindatu tace cikin mamaki. Nace wanan kayan kan ai daukan shi sai su Lawali mai wanki don yafi karfin daukan mace. Mikewa hindatu tayi tana fadin anga banza ba dole ai cin amana a kwaso kaya haka kamar hauka ba. Da kike kwaso naki banza ba wanda ya hanaki ai don haka dole ki bar kowa da nashi. Ke Rahama bana son magana har yaushe kika dawo da zaki tsaya wani fitina haka ku baku raina magana. Hindatu tace idan kin min rashin kunya ni yanzu zaki jini wallahi don ni ban daukan rashin mutunci yarinya. In ba samun guri ba wa yaa taba tafiya dashi ya dawo da kaya haka sai kece kikafi kowa da zaki ce ba za ai maki magana ba ko may ? Wanan kuma ai matsalar kice keda abin ya dama a rai, mace baki da aiki sai hassada da bakin ciki a rayuwan ki da kike naki sha, anin waya saka maki ido balle ke ki saka min ido haka ? Eh lalai ma yarinya wuyan ki yai kauri wallahi samun wuri har yakai ki mayar min da amsa haka ko ? Nace ke uwata ce da bazan fada maki ba ko mai yadda kika kada girman ki a gareni haka nima bazaan ji kunyan fada maki amsa daidai dake ba daga haka ma namike nakai kwance saman kujera da nake zaune akai. Haushi ta kara ji kafana da yai fari sol ya fito daga cikin dogon rigar da na saka ko shi abin haushi ne gareta. Kada fa ku sani magana ko ku fice min yanzu tace yarinya zaki san da wacce kike a gidan nan muje zuwa nida ke ne yar iska kawai. Na dago zan bata amsa ya harare ni na koma na kwanta nai shiru tafice rai a bace da bakin ciki tab a ranta. Rahama idan kina biyewa wanan haukan bazamu shirya dake ba na fada maki halin hindatu ne baki sani ba komay ? Amma daddy kana ji ta take zagina yaya bazan rama ba tunda bata dau girman ta ba ita. Na gane wanan matar baza, a taba zaman lafiya da ita ba wallahi may nai masu may na tare masu da zasu sakani gaba haka ? Su basu tafiya da kaine wake masu haka idan sun dawo ko ni da aka raina za, aiwa haka kawai. Mikewa nayi naji bama zan zauna falon ba yadda, yake son na zauna dashi gurin su lawali na nufa na samu suna wanki nai masu magana sai gasu na shigo nake cewa ga su Lawali zasu shigo su kwashe kayan yace OK kawai. Sun kwasa suka nufi gurin mu dasu nace su shiga dashi inda anty su aje min a nan nan falon ta suka jibge kayan . Ba ta dai yi magana ba tabi kayan da kallo kawai sai da na zauna na fara mata bayani da kuma wa yanda suka bani kyauta a can komai dai nai mata bayannin shi. Sai dai ban fada mata na sayo mata wani abuba na kare da cewa sai su Amira sun dawo mu bude tare da su a gani. Tacd indai an bude ai zamu gani tunda mu ba, a budewa damu dariya nayi nakai kwance don duk gabobina ciwo suke min lokacin. Nan na kwata sai barci barci nayi sosai a gurin anty na zaune tana kallona yadda nake barci a gajiye. Shedan yaso yai galaba a ranta inda yake kiyasta mata cewa ai dole in barci haka tunda banda aiki sai mannewa miji wai kamar Rama tasan yadda zata kwace zuciyan namiji kamar besty. Sai kuma wata zuciya tace kai Saade ba girman ki bane fa hakan asalima kece kika saka ta yin tafiyan nan da tayi. Yarinyar nan bata nuna maki komai ba a rayuwan hada miji da watace ai haka bazaki gane komai ba a kan ta. Amma gashi yanzu ta zauna tagama fada maki komai bata boye maki ba don may zaki yarda daman ki da Allah ya baki a kanta komai fa kece silar shi a kan ta. Tai saurin fadin astangafurullah Allah na rokeka kaba ni ikon cinye jerabawan nan da nake ciki a cikin nasara Allah kada ka nufe ni da bayar da kaina a gun wanan yarinyar. Duk da bata son sanyin AC amma sai ta tashi ta kunna min don na kara watsakewa tana jin tausayin nisan tafiyan da nayi dole ne ta gaji haka ai. Hayaniyar yara da suka dawo ne suka fada min a jiki suna murna suka tayar dani nima rugumay su nayi cikin murna ji nayi kamar nai hawaye. Anty tace ai yanzu gashi kin tashi amma tun dazun nake tayar dake kiyi sallah kikaki yanzu ba gashi sun tayar da ke ba ? Na rasa wanda zan taba a cikin su don daukin ganin su duk suka zauna min a jikina muna ta zuba surutu. Da kyat na mike naje nai sallah suna biye dani ranan kan basuje islamiya ba muna tare sai da mukai sallah la,asar muka fito zuwa part din anty. Nan muka fara bude kayan tsaraban da nayo masu duk wanda na fitar mai da nashi sai yaran su dauki ihun murna duk mun ruda mata shiya da hayani tana zaune cikin jin dadi na ware na kowa naba gajiye takaiwa sauran mutanen gidan nasu. Ita Zulfa ta karbi nata dana yar ta amma hindatu taki karban nata har na yar nata tace ace min ban isa ba kuma ban kai ba, bakuma zan taba kaiwa ba nasani. Ni dai na karba abina nace tayiwa kanta bani ba dama mijin ta yabada a sayo ai bani ba. Anty tace bari nai wa besty magana ai shi yasa ta karba dole ba wani jayayya akai. Nace anty kiyi hakkuri ai shi cin tuwon kishiya ranko neAllah ya bamu rai da lafiya kawai. Dana nunawa anty kayan sayarwa na sai da tai mamakin su run nan ta fara zaba nace anty ki dauka kawai tunda kina son su. Tace barsu kawai, biya zanyi ba aiwa sana,a haka sai mutum ys tabe idan bai ksrban kudin shi. Bamu dauki lokaci ba yamma yayi yara sai murna sukeyi na samun tsaraba haka abinda suka dade suna bukatan su gashi na sawo masu shi basu ko fada min ba. Rayuwa ya ci gaba da gudana a haka da dadi babu dadi a gidan ko yaushe da irin fitinan da zai bullo kai. Gashi tunda suka fahinci banda komai a tare dani sai gori ya fara biyo baya kuma da anzauna zakaji sun fara habaici suna fadin. Mutum sai kace juya a gida sai da aci a juye a maza haihuwa ai ba banza bane dama idan mace ta faye mannewa miji yaushe wani ciki can zai tsaya mata a jiki kullun kai kenan cikin zungura. Wanan gorin da sukw min kan haihuwa har ranan ya dawo kowa na falon don yanzu ya kirkiro a dinga zama a falin na wani dan lokaci bayan la, asar. Ihisan ta shigo tana fadawa uwar wai na ba su Amira sweet na hana mata ihisan ba sweet ba ko company sweet ne sai na saya maki ai tunda na haifeki na san zafin ki. Wanda bai san zafin daukan ciki ba da wahalan yaro shi ke wanan haukan to ni Allah na tuba may zai damay ni in haihuwa banza ne mutum ya haihu mana. Wanan wani irin maganan banza ne haka baki tambayanta dalilin da yasa aka hana mata sai ki shiga sake maganan banza wai ke may yasa baki son raina fitina ne. Ina shi haihuwa Allah ne mai badashi ba mutum ba ke ma ai naga kina son haihuwan kamar kj mutu. Au to gori zakai min don an taba yar gwal din ka da bata laifi a gidan ko may ? Tace ina dai na gwada haihuwan kuma kowa ya gani ansan kuma niba juya bace dai ko ? Nace ko ban haihufa ba hindatu Alhamdullahi don su Nasir sun wadatar da ni don basu rageni da komai ba a gidan nan . Tace aikin banza sannu hankaka maida dan wani naki in kin kai mace sai ki haifi naki a gani ? Zanyi magana yace rufe min baki Rahama kyaleta taitayi don abin ba hankaliba cikin sa. Anty ta mike tace Rama tashi mu tafi ban iya wanan jidalin abu kullun maimakon ya rage amma sai gaba yake yau harda girin haihuwa. Tace ce anyi ko kema zaki saya ne a sayar maki din don ashirye nake da kowan ku an mata gorin haihuwa ta haihu mana in baku son gori. Haihuwa kuma isa ne keda haihuwa Rahama a gidan nan sai gani sai hange sai ko bauta da diyan wata don kin zama hankaka mai da dan wani naki. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON CIN AMANAN ZAMA, , , 52 Raina yai matukar baci da farko amma da na zauna nai nazari sai naga kamar nima zanyi wa Allah butulcine. Na watsar da zancen naci gaba da harkokina na koma ga karatuna mai tarin tsawon shekaru. Wanan hutun da zamuyi ina son zuwa dubo iyayyena kauye don haka na fara shiri na a hankali, sai dai gaskiya na fara hango da akwai matsala sosai yanzu a gidan . Don ga nawa fahintar hindu da maigida sun dinke sosai ba kamar baya da na san su ba. Al,amarin kishi naso sakawa raina damuwa amma sai na roki Allah ya yayye min komai ban sawa kaina damuwa ga hakan ba don ko banza ai a tare na gan su da abin su. Ni in ba shigan tsugula ba may ye nawa na daukan zafi ga haka sai dai kishi kawai to ba, a kishi ni suke kishina. Taimako na ga Allah ina fita karatu sai yamma lis zan dawo gidan ga dan business da nakeyi kuma Allah na rufa min asiri ta hakan. Idan ya bamu na karba idan bai bani ba wala,ba,asan duk daya a gare ni ba dai wani abu nake saya ba ni sai ganin dama kawai don babu ne kawai bamu dashi. Gashi Allah ya taimakeni hajiyan harka tana karban kaya a gurina sosai tana bayarwa ga mata masu zuwa gurin ta sai dai a lalo min kudina cas a bani kawai. Sunyi tafiya da hindatu wanda dawowan mu tafiyan su karo na biyu ke nan da farko sun tafi lagos sukai sati daya acan har da yarta suka tafi. Sai kuma yanzu da suka tafi Abuja satin su biyu suka dawo garin kamar yadda yayi da muka dawo daga chaina hakane suna daki ba wanda ya gansu sai bayan karfe ukun rana suka fito. Ranan weekend ne saturday ba mu shiga school nai barci na na sauke gajiya bayan na tashi ne na shirya na fito zuwa wurin anty. Tana zaune tayi tagumi da hannu daya hannu na rike da kwalin lemu da dan tsunke tsotso don akwai ni da son shan zaki . Ina shiga ta dago kai tana kallona tace dani kin tashi na tambayi Fatima tace barci kike yi dazun . Na zauna ina fuskantar ta nace na tashi anty dama kwanan a gajiye nake saboda kin san asibiti muke yanzu. Na fara tsotson lemuna ta dago ta kalle ni tace Rama ashe besty ya dawo tun daren jiya amma har yanzu bai leko mu ba. Nace to fa ashe ya dawo ne ni ban ma ko sani ba ai sai yanzu tace sun dawo jiya da dare amma wai suna barci akace. Na maida kamana saman kujera tare da dunkulewa guri daya nace ashe sati mai zuwa tafiya na ke nan tunda ya dawo ? Tace zancen tafiyan na nan ne har yanzu ? Anty ai dole inje gida na dade rabona dasu fa tun shigowa sau daya naje shima kinga ban kwana ba muka dawo. Shiyasa nake son da mun dan samu break din nan na samu na tafi nagane su in dan zaga dangi na gaidasu. Har kwana nawa zakiyi haka nace cikin murmushi sati daya ko kwana goma idan an barmu. Wai da wuya gaskiya ke kina ganin besty zai iya barin ki har kiyi kwana goma ko sati da wuya gaskiya. Take annurin fuskana ya canza nace anty idan na zauna may zanyi a nan nikan gaskiya ya bari in tafi in ga gida haka. Nan da kauyen mu ace mutum ya share shekaru haka bai leka ba ai sai suce ina gudun su ne ma hakan. Kwanaki fa da mama tazo sai da tai min fada kece kika kwace ni gareta kuma mama na da gaskiyan ta wallahi. Ita mama Altine ta manta da halin shi ne ko ni da yaya yake bari na na tafi lokacin yanzu ma idan nace zan je na dubo mama cewa yake in sa a dauko ta naganta mana. Nace cabdi ashe ko akwaita ke nan don gaskiya ina son zuwa gida ni kan. Yanzu yadda kan nan nashi ke hayaki baya ganin kowa a gaban shi sai matar so itace bata laifi a gidan nan yanzu. Nace wanan kuma matsalar suce anty don sai wanda ya damu da shirmay su zai kula nifa anty alamarin su baya gabana. Tace naga alama ai Rama don ranan na dauka za, ai fitina da tace bata yarda ku fita tare ba kuma ya zauna hakan. Nace taiwa kanta indon ta Rahamace ko a jikina wallahi, ba sai kasa abu ga rai zai damay ka ba anty. Rama wani abu yana da cin rai ne wallahi, ya sani fa sarai abinda take shukawa amma ji yadda ya koma kamar wani soko dashi wallahi. Na ce anty kada ki sa zancen daddy a ranki ai duk wanda ya zalunci wani dashi da Allah. Gamu yaran ki muna debe maki kewan komai may zai damay ki da alamarin shi anty don Allah kada ki sa damuwan haka a ranki idan ma taga an damu dadi zataji ai. Rama ace nai ciwo baya gari amma ya dawo sai ya share ni haka nace gaskiya ba dadi amma kiyi hakkuri don Allah Allah dai ya baki lafiya kawai. Nace waiko anty kin san kayan nan sun kare har ana neman su bedshet da takalma sunyi kasuwa. Sai da ta nisa ta sauke ajiyan zuciya naji dadi a raina don nasan ta fitar da damuwan ta ke nan. Tace kai Rama kice min mun shigo da kafar dama ashe kwanan zamu fara shiga Dubai debo kaya ? Dariya nayi nace kai ai sai ace dani da jirgin tafiyan duk a matse mu a daina ganin mu dariya ta kwashe dashi nima dariyan nake muna cikin dariya sai ganin shi mukayi kofan falon. Shi bai shigo ba bai kuma juya ba sai bin mu da kallo yakeyi nace La, illah ha, illah muhammadan rasulliha sau uku. Shigowa yayi yabi mu da kallo ita ta fara cewa dashi an dawo lafiya fuska babu walwalla acikin sa ko kadan. Zakace ba itace ke dariya ba haka yanzu dan second daya wuce sannu da zuwa nai mai daga haka naci gaba da tsotson lemuna kawai. Yace amma ai kun san na dawo tun jiya babu wacce ta shiga gaidani cikin ku ko ? Wai Saade may kike nufi ne da kike min abubuwa haka son ran ki kina ganin haka shine mafita a gareki ko may ? Tsam na mike na nufi inda takalmina yake zan saka yace ina zaki a na magana zaki fita ke nan daban ne komay ? Idan kuna ganin banda darajan da zaku je nayi tafiya ku gaidani sai na tako nazo to mace ta rike gaisuwan ta na yafe. Anty tace idan kai muna haka bakai muna adalci ba gaskiya kuna dakin ne zamu fita zuwa gaida kai ko may ? Yace kamar ya ina daki tace tare kake da matar ka fa tun dawowan ku yace shine don tana tare dani baza aje ai min sannu da zuwa ba don an mai dani dan banza ko ? Wanan kuma kai kace hakan babu yadda za, ayi mitum ya shiga maku daki kuna kwance sai dai in kaso ganin laifin mu kawai. Nagane so kike ki koyawa yarinyar nan rashin mutinci ta raina ni don baki je ba itama bazata taje gaida ni ba don sai yadda kikace akan ta. Ina saka takalmina nake cewa ni ciki ciki nikan kada a dorawa wani laifina don ko ita bata ganni ba sai yanzu na fito. Yace a cikin hasala may kike fadi ? Banyi magana ba sai juyawa nayi zan bar masu falon yace idan kika tafi sai ranki yai matukar baci a gidan nan yau. Nace cikin murya may kama da shagwaba ko wauta ni to ina ruwanta da rashin zuwa na balle laifina ya shafeta. Daga haka na juya na bar masu part din yabini da kallon mamaki har na bace daga ganin su. Ina shiga daki na mayar da kofa na rufe ranshi yai matukar baci sosai yake cewa kin dai gani da idanuwan ki ko ? Tace besty kai yanzu tsakani da Allah gaskiya ne ace ka dawo gidan nan tun daren jiya amma ba wanda ya saka ka a ido sai yanzu ? Wanan haka Allah yace ayi dalcin ke nan ko may a hakan da kake muna ? Ciwo fa nayi ka sani amma baka damu da sanin yaya lafiyan jikin nawa ba sai yanzu da yai maka dadi zaka shigo muna kowa ma fa mace ce. Yace ai matsalar ku ke nan mata kishi dana zauna da ita a daki wacece bani zama da ita daki a cikin ku wai ? Tace kake dai zama dasu kada ma ka sakani cikin wanan magana may nake a gareka da zakace wai zaka sakani. Don kin min sheri Saade yanzu bani mamaki zaki iya ma wanda yafi hakan wacce ma kika sa na aura din kin yi bakin ciki a kan ta balle wata. Tace na gode badai auren ta nasa kayi ba zaman banza ba ai abin da sauki tunda ba zaman zina kukeyi da ita ba nagodewa Allah tunda aure na hada. Sai dai ka sani don kana auren mu bashine zai sa ka samun kafan ci muna fuska ba wai kana takama da aure kowan mu a nan zaman ka mukeyi. Saukin abindai ba ke zaki gwada min Allah ba ita kuma da take ganin kamar ta isa har take raina magana na zata gane bata da wayyo a gidan nan. Part dina ya nufo Fatima uwar kallo tana zaune tana kallo bata ko damu da yanayin da na shigo ba sai faman kallon ta takeyi. Shigowan shi yasa ta sa puss a tv ta mike tafice kaina yazo ya tsaya yace Rahama har ke kin isa ina magana ki wuce ki barni a tsaye. Ban dago na kalle shi ba yaci gaba da magana ince kada ki wuce shine zaki shura takalman ki ki wuto ki barni ko ? Na mike nace in ba neman fitina kake yi ba daddy akan may hindu na dakin ka zakace na shiga ai kasan muna gidan zamu kuma zo gaishe ka amma ka rufe kofa da mace har hudun yamma ? Wallahi ni duk da ba diyar kowa bace banga zan iya jure wullakanci ba irin wanan. Nike fadawa magana haka Rahama ashe baki da kunya ban sani ba shiru nayi na koma zan kwata ya finciko da katfin shi har sai da wuya na ya amsa nai dan kara na dafe wurin. Yace bari kiji ni ba namijin da mace zata raina bane ko yaya ko nike da ita, nace balle ma ba wata nake illa Rahama yar gidan Aliyu maska. Kara hankado ni yayi da kyau da hannu daya sai da naji gabobina sun amsa min lokaci daya nasan daddy geant ne kuma ga karfi don akwai shi musess din jiki sosai karfafa ne bana wasa ba. Idon shi ya kura min nima na kura mai ido don zuciya na ya bushe a lokacin, ya yarfar dani saman kushin din yana fadin. Kishin banza kishin wofi sai na balbalaki yanzu na balla banza wallahi in takamar ki rashin kunya ne ? Nace may zanwa kishi in wahal da kaina ga banza abinda ya damu dakai kake damuwa dashi ai ba wanda ya ajaka ya tare gun mace daya ba. Wanda ma suka san zafin ka kasan nasu may aka mai dasu balle ni karan kada miya da ban aje ba ban ba wani ajiya ba a gidan. Ya juyo yana kallona ban daina magana ba nace ni wallahi da zaman zalunci gara ka sallamay ni yafi min sauki. Tas tas ya aza min mari biyu masu lafiya sai da naga wani wuta ya gitta min, na dafe kumci na sai hawaye yaja tsaku yafice yana fadin ashe ke karamar yar iskace ? Nan ya barni zaune dafe da kumatuna ina ambaliyan hawaye masu dumi dake fito min na takaici. Lalai daddy ya mare ni kan gaskiya na amma sai na Rama nima insha Allahu lalai ko wani abu sai aure wallahi ni Rahama yau aka mara kuma kan gaskiya na don fadan karya yakeyi wallahi duk borin kunya ne hakan. Ni ya kamata nai girki ban yi ba ranan shima yasan zamu kwasa bani gaban shi bai kuma damu da hakan ba ma. Har na gama bai sani a ido ba bai nemay ni ba kuma ranan monday da safe ban shiga mota na ba na fita na tare taxis na wuce ban kuma ma fita da wayana ba na kashe. Har rana idan ya fito yana ganin mota na a gida shi yasa yake zaton ina cikin gidan ban fita bane kawai. Sai dai yadda ya sanni da son karatu na yau monday may zai hanani fita ashe ? Washe gari ma hakane bayan la, asar ya shigo wurin anty tana tsaye tana sa kayan data cire a wardrove sai gashi. Yace ita wanan kwana biyu may ke hanata zuwa karatu ne wai ? Da mamaki tace wa wai Rama ta fita mana yace jiya da yau bata fita ba don motar ta yana ajiye yadda yake. Tace Rama kan ta fita bata gidan nan tace bari ma na kirata kaji takira wayan baya shiga tace tun jiya wayan ta baya shiga. Amma da safe ina barci naji kamar muryan ta tana sallama na ai, tace jiya ai tare kake da ita ko ? Bai yi magana ba yasa kai ya fita ranshi bace ya duba part din yana rufe fatima kuma da Gajiye sun fita don bai gansu ba. Babu wanda ya fahinci muna da matsala da daddy a gidan sai hindatu don ita any time suna tare kuma bataga na shigo part din ba har duty na ya kare. Tambayan maigadi yayi ko yaga fita na yace gaskiya bai gani ba gaban shi ne ya fadi don ko anty ba wai tana da tabbas din ko ina nan bane. Sai after six muka dawo gidan Zarah ce ta sauke ni da mota yana tsaye bakin get yana waya ya dafa motar shi. Jin shigowan mu yasa ya juya don ganin ko waye ya shigo gidan a lokacin. Zarah tace taufa ga gogan na ku nan tsaye yana gida ke nan bai fita ba ashe, na ce da ita ta bani takardan da ta amsa ta kwashe abinda na rubuta. Haka ya dan sa bamuyi saurin fitowa ba na bude motar na fito ina mata sai da safe. Tun bata fita ba daga gidan yace dani ke ina kika fito haka waye wanan da ta aje ki kuma ? Ban juyo ba kuma ban yi magana ba yace cikin tsawa my friend will you stop there ina magana don baki da kunya zaki wuce. Na juyo nace idan ma kace na bargidan kada na shiga ba matsala bane gare ni tunda ba nan aka haife ni ba. Shiga zan shigo na samay ki ai part din anty na shiga muka gaisa da ita take tambayana cikin damuwa. Rama ina kika tafi baki je da mota ba nace ina asibiti tun safe anty kin san bamu amfani da waya can. Ga hankalin mijin ki duk ya tashi shine yazo yake fada min ma wai jiya da yau baki fita da mota ba ? Nace anty mota ai ba nawa bane kuma bana ubana bane don may zan kama amfani da kayan gori. Gori kuma Rama wa yai maki gori kuma akan mota ban yi magana ba na juya na fita tabi yanayi na da kallo nan ta fahinci akwai magana. Ina cire safa a kafana ya bankado kofan dakin ya shigo yana huci yace ashe baki da hankali ? Duk motan dake gidan nan baki shiga ba sai motar lift zaki shigo don ki bata min suna ko may ? In ma motar ki bata da lafiya ne baki magana a gyara maki ita sai ki kama shiga motar mutane da izinin wa zaki shiga motar wata ? Nace ai banzo da mota daga gida ubana ba don haka banga abin da zai kai shiga motar makiya na ba ? Wanda basu san darajan dan adam ba balle na aure ko jaki ubana bai dashi a gidan mu balle mota na tsaya matsayin da Allah ya aje ni. Karya kike wallahi karya kike daga baya ke nan may yasa kike shiga da farko kina wasa dani wallahi in kin isa ki kara shiga motar wata ko wani ki gani ? Nace bani ganin komai sai alheri don shi na saba gani dama ni dai bani iyawa wallahi nace banayi ko dole ne wai auren ? Kin makara yarinya don kin shigo inda ba fita ki zauna nan kishi ya kashe ki gabanza. Allah tsare ni da kishin abinda bai damu da damuwar wani ba wallahi. Na juya na mike na shige bathroom dina na barshi nan wanka nayi nai alwala na fito zuwa sallah. Fatima ta dawo daga inda suka tafi kitso da gajiye sai da muka gama komai muka shigo part din anty. Daga dakin ta ta kirani naje tace samu wuri ki zauna na zauna tare da sauraren ta don inji may zatace dani. Rama yaushe kika zama mara kunya ban sani ba ? Ko abinda kikaga anayi ne kike kwaikwayo kin dauka abin alfanu ne yiwa miji rashin kunya haka ? Banji dadin jin wanan halin gareki ba ban kuma san sanda kika fara hakan ba ma ? Idan yana haukan shi ki kyaleshi mana yai tayi shi da kan shi ai zai dawo ya gane gaskiyan abinda yakeyi din. Kuka ne yazo min ban iya magana ba har tayi tagama ban tanka mata na dade a zaune can namike nace da ita nagode na fita. Washegari hamza driver nabi da zai kai yara ya sauke ni nace ya dawo shidda ya dauke ni. Bayan kwana biyu da dare na shigo nace da anty zan je nai maganan tafiyan mu wurin daddy tace Allah yasa a dace na fita. Yana zaune da matan shi na shigo da sallama na duk suka bini da ido gaidashi nayi ya amsa min a dakile faban su. Nace dama magana nazo yi yace maganan baiyi anan ke nan ko Zulfa najin haka dama da alama zaman kawai take a tsakanin su. Mikewa tayi ta dauki yarta tabar falon saura hindatu dake kan kare mai abu a kafan shi. Na ce dama zancen tafiyan mu gidane zan samu break na two weeks shine nake son na tafi. Kamar ba da daddy nake magana ba nai shiru shima shiru yayi yana kallon tv nagaji da zama namike yace naji sai nayi shawara. Ban juyo ba na fice abina ina fita hindatu da gaban ta ya fadi ance abinda kakeyi sai kai tsanmanin shi kowa keyi. Tace may zata je yi gida kuma yanzu yace ba maganan ki bane tace ayi hakkuri amma naga dai kamar ba abinda ya faru ne ai ? Yace sai abu ya faru mutum ke zuwa gida don zata gun iyayyen ta shine wani zance kuma can. Ya nuna mata bai son maganan don ba maganan ta bane wanan dole tai shiru don bai ba da fuskan ba dama shishigin tane yasa kowa ke ganin zaman dadi sukeyi. Duk da dai abu ya hau kan shi amma ba irin yadda muke nufi din nan ba yana dan namijin kokari akan ta wani lokaci. Sam naki sakin jikina da kowa a gidan sai yaran da kan dan jani da hira ko shi ba sosai ba kullun ina daki abina. Ranan da zan karbi girki anty da kan ta ta kara yi min magana dole nai girki nakai mai sai dai ban tsaya ba . Haka yasa yai tsanmanin da dare ma ba zan shigo ba don har goma da rabi muna zaune muna kallo da Fatima wanda ni karatuna nakeyi. Sha daya saura yan min tina na shirya nai mata sai da safe nasan lokacin kila yayi barci ko. Ban ko tsaya wani gyara ba ko dana shiga ya kashe wutan ko ina yashige na rufe kofa na nufi bedroom din shima wutan a kunne yake lokacin. Can na koma bakin gado na makure tare da rufewa da hijjab dina a zatona yayi barci ne lokacin. Ban dade da kwanciya ba naji ya mirgino zuwa inda nake kwance ya fara romacing din na ko gezau banyi ba kamar yana taba dutse yakeyi. Naji yace humm ya fahinci zuciya na ya bushe sosoi a lokacin don duk wani weak poit din da yasa zai sani girgirza yabi ban motsa ba. Yai kidan shi yai rawan shi shi kaidai har yagaji bai min magana ba nima hakan da safe duku duku na bar dakin ko wanka da sallah a dakina nayi na hada break fast nakai mai nabi yara muka bar gidan. Sai yamma lis na dawo na samu gajiye har tagama abinci da nai sallah nakai na jera nafito ban zauna ba. Yau ma haka na daure na tafi kamar jiya ba sauki ko kadan a kaina sai na Allah ya gama abinda zaiyi ya koma inda yake yake cewa yaushe zakuyi hutun? Nace thursday din nan in Allah ya kaimu yace sai ki shirya sunday ku tafi kwana nawa zakiyi a can ? Nace goma ko sati daya yace wai ko kina da hankali Rahama may zakije ki zauna gida kiyi har sati daya, ? Saida na hade bakin ciki nace ganin iyayyena da yan uwana zanje nayi yace to ban yarda ba idan kwana hudu yayi maki sai ki shirya ku tafi din. Banyi magana ba na gyara kwanciya na kawai ina adduan barci da safe na fice abina yana zaune yana lazumi. Yabini da kallo kawai yana mamakin karfin hali haka irin nawa watau mata kowa da inda take da nata matsalan ke nan. Wanan yarinyar karama tasan wai ta dakile namiji ita adole fushi take yi wawuyi kanki kikaiwa nina kwashi rabona ko ai. Da kanki yarinya zaki dawo kamar yadda kika kawo kanki yanzu akai maki susa. Tun ranan na fara shirina sai dana shirya tsab kafin ranan na danyiwa anty bayani sama sama sai dai ba komai ba. Mun yi kitso har kumshi don tafiya kawai jiran gari ya waye mu dauki hanya ga yaran nason bina anty tace sai nice zanwa daddy magana amma na rasa yadda zan mai magana don basuyi hutu ba. Hakana nai masu dabara nace daddy yace idan sunyi hutu zai kawo su mu dawo tare anty ma taban tsaraban da zamukai gida nai mata godiya. Na dawo part dina ina cewa Fatima ta fito da kayan mu falo sai gashi ya shigo yabi jakar da Fatima ta dauko da kallo, fatima kan na ganin shi ta shige ciki. Kudi ya miko min yace ga wanan ina ga zasu isheki ai har ku dawo nace akwai kudi a hannuna zasu isheni bai tsaya bin magana naba ya miko min kudin dari biyu ne zur yan dubu da kuma dari biyar. Yacd nace Hamza ya shiya zaku samay shi a waje zaune yana jiran ku nace na gode a sanyayye. Yace ku gaida mutanen gida kiyi min godiya wurin baba kafin mu hadu dashi. Mun fito muka rufe kofa na nufi wurin anty nai mata sallama don naci arziki ba yaran suna makaranta. Tace kun fito ko nace eh anty to idan kin je ina zaki sauka wurin mama laure ko kuwa nace anty wurin Inna ta dai zan sauka tace anya Rama bazaifi kyau ki sauka gida ba wanan karon ? Nace anty kin san halin mama ba fasawa zatayi ba bari dai muyi nisa da nisa da ita a rabu cikin mutunci yafi tace shine kuma ai. Tare muka fito da anty mun samu har an saka kayan a mota ko yana dan kakabewa ba anty ba koni nai mamaki ganin ACURA din daddy ce zamuyi tafiyan da ita ashe. Mukai sallama da su anty Gajiye ma zata bimu taga gida su dawo da Hamza fatima ita ta shiga gaba ni da gajiye muna baya muka kama hanya. Sha biyu daidai muna kauyen mu inda kowa yaga motar sai bin mu da kallon mamaki ake don ba, a san ko su waye ba cikin wanan tsaleliyar motar haka ? Fadan mai gari yana makil da jama, a dagani wani sharia sukeyi a wurin zuwan mu ya dawo da hankalin su a kan mu. Mun fito aka gane mune ga yara sun kewaye mu sai faman ihu da murnan ga Fatima ga anty sukeyi. Ba karamin kaduwa nayi ba danaga irin tsaraban da daddy ya lodo muna a bayan motan shi don ban san da su ba saida na zo yanzu ake saukewa. Nauyi da kunya ne ya kamani duk rashin mutuncin dana tsula masu gashi kuma ya bini da abin arziki kai gaskiya hindatu shu,umace wallahi don nasan ba banza ta barmu ba haka rashin fahinta na shiga tsakanin mu haka. Don gaba daya gaskiya bakin daddy nake gani ina jin haushin shi haka kawai ba wai marin da yai min ba tun kan haka nake jin wanan yanayin a tare dani. Abinda ban sani ba ashe shine aikin da akai muna ma daba duka ba so akayi gaba daya ma sakina akaso yayi ranan . Sai abin ya tsaya iya mari kawai da nasha Allah baikai abin ga saki ba tsakanin mu don gaba daya lokacin haushina da takaicina yakeji. Marin da yai min ne yadan ji sanyi a zuciyar shi sannu abin ya dan rage mashi yadda yake ji a kaina din. Nima yadda yake ji haka nake ji idan na ganshi wani haushi da takaicin shi nake ji sai naji ma bani son ganin shi sam a raina. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA ALLAH YABI MUNA HAKKIN MU A KANKI DON ONLINE NOVEL NE WANAN, , , , 54 Mun yi saurin barin uguwar nace ma mama Altine zan dawo tana ta zabga min addua muka bar gidan. Har mutane sun fara taruwa a kofan gidan mu amma haka muka wuce bamu tsaya jin takaici ba sai ma Rukaiyya ke fadin mama bata taba fadan gaskiya. Yanzu tasan Lawali baida gaskiya amma ta zage tana biyewa matar nan suke tijara. Yanzu ai ta samu daidai da ita ba kamar yadda ta samu innan ki tana gasa mata kwakwa ba a baya ita wanan sunyi daidai don makirace sosai matar . Murmushi kawai nai mata a raina nace ai sin gamu da sun dace sai suyi tayi yanzu. Gidan Jatau muka nufa daga gidan mu tare da karin tsaraban da nazo masu dashi. Tun a kofan gida muka hadu da shi yana ganin mu ya fara wagale baki ya kara tsufa sosai duk furfura ne ko ina fuskan shi har kan shi. Yana fadin hajiya Rahama ashe an shigo garin namu sannun ku da zuwa nace malam jatau ya gida ya iyali yaune rana na farko da mukai magana ta arziki dashi. Nace na taki sa, a dana samay ka a gida dama akwai maganan da nake son muyi da kai akan anty na ne. Ya kara washe baki yace to to Allah yasa alheri ne nace in sha Allahu alherin ne idan ka yarda. Dama ba wani abu bane so nake a samu dan injimin nika wa anty wanda zata dan rika samun kwabon kashi kaga yanzu ga yara sunyi yawa dole a dan kama ma wani wurin kaima ka huta. Yaji dadin yadda na fada sai washe baki yakeyi yace to hakan na da kyau idan har zata iya ai yar uwar taki ce ba haguwa ko kana son taimaka mata bata iya tattali ba a rayuwan ta. Nace in har ka yarda ba matsala sai a gwada agani ko Allah zai karba muna ta wanan hanyan . Nace babu damuwa za, a gwada a gani idan zai karbu gareta yai min godiya nasa hannu na ciro dubu biyar na bashi nace ga wanan ayi hakkuri dashi hakana. Sai ga Jatau da tsufan shi har yana dan rusunnamin wurin karban kudin yana ta zabga godiya. Dama muna tsaye yaran gidan na leko mu har sun koma sun fadawa iyayyen su ga yar uwar Suwaiba ta birni can ta tsaya da baban mu a waje suna wani magana. Nan dai suka fara sake magana a tsakar gida mu ana gwada muna birni mu da muka ga gwauna. Sai gamu mun shigo da sallaman mu Rukkaiyya ta kwasa zata wuce su babu ko gaisuwa nace haba dai anty na. Direct inda suke zaune na nufa tare da masu sallama suka amsa a gyatsire fuska babu walwala nace mun samay ku lafiya yaya yara ya gida ya kuma bayan rabo suka amsa da lafiya kalau sai dayan ce tace anzo lafiya ya mutanen wurin ku nace Alhamdullahi. Na juya nabi Rukaiyya data fara tafiya don bata daukan wanan a gareta sai ga Suwaiba zanin jikin ta ma dai bai ko kalluwa tayo kan mu da murnan ta. Inajin suna cewa an dai yi hasara wallahi muka rugumay juna da murna ta rasa inda zata sani don dadi. Tace Rahama kece kika koma haka kamar baturiya aiko birnin ma ashe amsa ne don naga wasu yan birni da suka zo kwana ki gidan nan ko mu mun fisu dadin gani. Ashe wai wata yar uwar kishiyarta tazo daga can shine take wanan haibaicin muna shiga dakin ta sai da gabana ya fadi don bazakace mutum mai raine ke kwana ciki ba haka wai kuma harda miji a hakan. Godiya naiwa Allah a raina da ya rabani da wanan rayuwan na mutanen mu mace da kurciyar ta amma don kazanta da talauci takoma kamar tsohuwa. Hakana muka zauna takawo muna ruwa cikin wani kofin silver duk ya dafe don tsufa. Kowa yace bai sha na karba na kafa kai na ji wani mugun karni ya doki hancina haka na daure na hade zuciyana yana tashi. Mun gaisa muka barke da hiran yaushe rabo a tsakanin mu mun dan jima a zaune nace Fatima miko min jakar nan ta miko min. Turmi uku na fitar da kudi dubu uku sai sweet da sabulun wanki da omo nace Fatima mikawa matan can wanan kice su raba . Rahama don may zaki ba su wanan himilin uban kayan haka dako mijin da ta aje su bai iya basu shi. Ai harshi sai da taba yanzu har dubu biyar kamar na taushe shi na kwace naji sai son banza amma shi bai iyayiwa mutane hakan. Nace haba dai Anty wanan fa shine sayen girma da mutnci a gareki ba don wani na ba dashi ba sai don ke din nan. Haka zai sa su gane kin fisu har abada tunda har kina da wanda zai basu abu su karba a bangaren ki. Hakane kuma inji Rukkaiya dake zuga zancen ita dai Suwaiba duk bakin ciki ya kashe ta akan an ba abokan zaman ta alheri. Abinda basu taba yi ba sai gasu tare duk kan su sun zo yin godiya sai faman farin ciki suke suna ta zabga godiya da fatan alheri gareni da maigida. Bayan tafiyan su na fara yiwa Suwaiba da Rukkaiyya bayanin abinda nake so dasu tare da masu fada akan su canza rayuwan su don banji dadin abin da na sama ba a gidan Suwaiba din. Nace gobe gobe ta kwashe kayan ta zan turo a gyara mata dakin ta zanyi magana da mijin ta sai Rukkaiyya tace a dai gyara muna nima dakina ai ko daben kasa babu kin san auren nawa ba shiri akayi mama kuma wai bata son auren. To Rahama nagaji da yawo hakana gashi duk babu sa,a na a gari ita mama kin san hakan ko a jikin ta bata damu ba wallahi. Nace Rukkaiya sai hakkuri da iyayyen mu tun da sun riga sun haife mu tace yanzu ma da zamu fito bakiji abinda take fada min ba wai kada na bada kaina gun Rahama. Yo Allah na tuba yaya zan rabu da yar uwata ko baki haka balle irin taimakon da kike muna ko bakizo ba ko yaushe aiken ki na saman hanya ana kawo muna duk Altine zata dawo. Nace ni dai yanzu abinda nake so daku shi ne ku kama kanku don Allah lokaci yayi da zaku dage wurin mai da kan ku abin kwarai don mahaifin mu yai alfahari da haihuwan mu. Sai naga Suwaiba na kuka tace Rahama laila ke mutum ce dake da mahaifiyar ki duk irin abinda mukai maku a baya baku taba rike mu dashi ba. Haka ma wanda mahaifiyar mu ke maki baku taba kallon mu dashi ba balle ku rike mu da hakan a ranku. Don Allah Rahama ki yafe muna duk abinda mukai maki da wanda kika sani dama wanda baki sani ba. Nace Anty don Allah kibar wanan magana don ni ban taba rike dayan ku da wani abu a raina ba ni dai fatana naga mun rike zumuncin mu da Allah ya kulla a tsakanin mu. Nan dai mukai ta magana nai masu bayani kan gyaran gidan da maigidana yace aiwa baba idan nazo sukai murna sosai suna cewa. Ai wanan abin Rahama ba baba akaiwa ba mu akaiwa don mu zamuyi alfahari da hakan a gari. Ban bar gidan ba sai da na dan masu nasiha na zaman lafiya a fakaice sukai min godiya muka barta. Gidan Rukkaiya muka tafi naga dakin ta tabani matukar tausayi nasan auren take son zama shiyasa harta daure cikin irin wanan rayuwan haka. Bayan na dawo gida na samu mutane da dama sunzo gaida ni, wanka nayi don nagaji sosai bayan maigari ya dawo cikin gida taro ya watse a fadan shi ya zauna dani muna hira. Har cikin raina naji dafin hakan sai nake ji dama ace shine mahaifina, ban boye mashi komai ba na halin rayuwan da muke ciki da kowa a gidan don ina jin shi tankar shi ya haife ni. A rin yadda ya daukeni a matsayin diyarshi tankar wacce ya haifa yace dani na kara kwantar da hankalina su dai basuyi wa mutum sheri amma duk abinda mutum ya debo akan dan su zai koma a kan shi in hairan in sheran. Nai mashi bayani kan gyaran gidan da nake so aiwa mahaifina yayi murna kwarai kamar shi akaiwa alheri haka. Nace ina son asama min wanda zaiyi aikin muyi magana dashi inji yadda aikin zai kaya. Ba bata lokaci ya aika akira mai Ado magini yazo yana neman shi maza maza. Ba, a jima ba muna wurin zaune da shi sai ga Ado maginin yazo yai sallama bayan ya dan fita sun gana ya aiko a kirani nai bayanin yadda nake son ginan ya kasance. Yace nan zuwa safe insha Allahu zaizo min da list din komai aji yadda za, ayi ginan. Sai bayan sallah isha,i ne muka shirya Fatima ta rakani gidan mu don inga mahaifina. Mun shiga gidan da gani ba zaman lafiya ko kadan na wuce gaida mama da kyat ta amsa min gaisuwan da nai mata. Na wuce inda babana yake zaune saman shimfida, muka gaisa dashi yana murna da farin cikin ganina yace ai harda nace idan baki shigo ba da daren nan sai na shiga da safe na ganki can wurin uwar taki. Nace baba ai na fadawa mama amarya cewa zan dawo da dare yaji dadin har cikin ran shi jin nakira matarshi abin son shi da mama. Yace ai na dawo Lanto taks gwada min irin alherin da kika zo kikai masu bayan wanda kika aiko dashi jiya kuma ? Nace ba komai baba ai uwaye na naiwa ba wasu ba, nan na fada mai yadda daddy yace ayi da gidan . Yace anya Rahama bamu takurawa mutumin nan ba da bani bani ga irin taimakon da yai min kuma yanzu a ce yayi haka akan mu. Nace baba ni wallahi ban taba rokon shi akan yai man wani abuba ko wani nawa ganin daman shi ne da ganin dacewan hakan dai yasa yakeyi. Baba shifa daddy haka rayuwan shi yake don akwai shi da tausayin na kasa gareshi sosai. Yace to Allah ya saka mai da alheri abinda yake nema na Alheri Allah ya bashi duniya da lahira mukace amin . Sai ga amaryan baba tafito da abinci daga daki tana fafin har ina batun na aika maki dashi can su Jabir ne basu shigo ba ai. Tuwon masara ne da miyar busassan kubewa sai kamahin kayan yaji yakeyi munaci muna hiran rayuwa da mahaifina yana fada min irin alherin da ya samu ga taimakon da daddy yai mashi. Daga can naji mama na fadin an dai ji kunya wallahi babu kunya a fake ga maula a gurin suruki don kwadayi kawai. Lauratu ki kama min bakin ki in ba haka ba kin san halina yanzu ranki zai baci a gidan nan. Yo bakin ciki kikeyi don Allah ya mayar da yar da bakiso ganin da digon farin ciki ba a rayuwan ta haka ? Kin sana rabu da iyalina masu so na da zuciya daya don mugun halinki don baki da kunya shine yanzu har zaki wagale baki kina fadin magana son ran ki idan fitsari banza ne kaza tayi mugani. Banda marasa tarbiya da rashin mutunci da kika tara min a gida suna jawo min magana da abin kunya a gida dagari may kika tsinana min. Sai naji amarya ta cabe da cewa ai dama duk wanda yace ruwan wani bai tafasa shiko nashi ai ko dumi baiyi haka abin yake. Nace don Allah dai kuyi hakkuri kubar wanan zancen don Allah yanzu girma yazo ya kamata ku daina hakan. Haka dazun kuka tara mutane a kofan gidan nan abin ba dadin gani don Allah don Allah na roke ku ku daina yin haka a rayuwan ku. Daga kofan ta da take zaune tace ke kama kanki ke har yaushe kike da zaki wani tsaya wai kina muna nasiha inda bamu san asalin kolo bane da sai yace muna daga masar yake. Baba yace Rahama kyale wanan mara mutunci don shedan ya auri zuciyar ta ba yau ba na kusa yadda kwallon magwaro na huta da biyan kuda. Baba kayi hakkuri ka daina biyewa irin wanan maganganun na mata don ba girman ku bane hakan. Ke kama min bakin ki ke har yaushe kika gama da naki matsalan don kin iya cin amana daga taimako kuka san asirin da kukaiwa mata kika aure mata mijin ta wallahu tir da halin yan cin amana irin ku a duniya. Shiru nayi sai babane yace kaiyya ace halin mutim jarin sa ke kina ganin abinda kikeyi ko shi kowa keyi ne a duniya wai. Don ba yarki bace ai da yarki ce ko ni mahaifinta baki bari taiwa alheri balle har makwabta su ma su samu. Ganin nayi shiru ne yasa baba ya fahinci raina ya baci don haka shima sai yaja bakin shi yai shiru. Mun dan zauna jugun sai nake cewa baba dare ya soma zamu tafi gida don akwai duhu yau a garin yace hakane Rahama Allah yai maki albarka ya tsare muna ku daga duk wani abin ki a duniya. Nace amin baba mun gode namike mun tsayar da magana dashi da safe za, azo a samay shi ya nuna yadda yake son tsarin. Nai masu saida safe sai ga yaran amarya sun shigo gidan tace yauwa hajiya ga yaran nan kin gasu tace kuyiwa anty ku godiya ko . Nace au sune nan sannu ku ko kuna lafiya na dan shafa kanun su suka rusunna suna gaidani. Uwar tace ai gobe in Allah ya kaimu zasu shigo su gaida ke can gidan. Mukai masu sallama na fito inajin mama na fadin munafuncin banza da wofi kawai mutum bai iya da gidan shi ba yace zaizo gyaran gidan wasu ai duk zaman da mutum keyi a can muna da labarin shi a nan. Ban da boyi boyi may aka gane a can din anzo za, a cimu da burgan aiki wai anga yan kauye ko ? Naje gida ina fadawa innata yadda mukayi tace Allah ya kyauta ai ta riga tai nisa batajin kira tana fadin hakane don ta hanaki aikin ki na alheri ga mutane kin san shu,uma ce ta gaske ai. Washe gari ma bayan mun tashi ina da gurin zuwa wuni gidan kakan nina daga can na biya gidan mama altine don ban sha, awan shiga gidan namu ko kadan. Ado magini yazo muka fito ni da maigari ya fada muna nawa za, a kashe nai mamaki kwarai nace garin dadi na kauye gaskiya komai nasu da albarka yake. By Na shiga na kawo mai kudi yace a ranan zasu fara saka foundation din gina nagani idan yayi kyau. Sun tafi sun samu baba ya shiga dasu ciki don a auna yadda ginan zai kasance sai mama ke cewa ita kada a taba mata dakin ta abarta da abinta hakana. Baba yace baki isa ba tunda ba gidan ki bane kuma bada kudin ki na gina abina ba dashi kika ganni kika shigo yadda nake so haka za, ai min. Sai da takai har baba ya shiga ya linkida mata duka da farar safiya sannan ta natsu. Aiki ya fara gadan gadan tanaji tana gani ga kuma jiki yai mata tsami ga banza. Gidan kakanin na na nufa bayan yaran amarya sunzo mun gaisa suka tafi muka kama hanya. Muna shiga Attu ke cewa dani tayi fushi sai da nagama ganin iyayyena da yan uwana nazo ganin su . Nai dariya nace haba Attu ke fa ta daban ce bari nayi nazo mu sha hira a tsanake daku. Nace ina tsohon mijin ki tace mijin ki yafishi yarinta ne balle ki kira min miji da tsoho. Nan muka zauna aka shiga hiran yaushe rabo a tsakanin mu daga ni sai Atika mukazo don Fatima tana can ta shiga gurin yan uwan mahaifiyar ta. Hira sosai mukayi da Attu take tambayana yaya baiwar Allah nan mai mutunci da karamci yaya jikin nata kuma ? Nan dai na fada mata komai don wanda baici ka boyewa magana ba najikin ka dole ka fada mai wani abin. Tace ki dai daure aita hakkuri ai tayi kokari wallahi ko a zamanin da can baya da wuya a samu macen da zata sadaukar da rayuwanta da komai nata ta zabawa mijin ta macen da zai zauna da ita don samun farin cikin shi tana kallo. Da ace mata zamu kawar da kishi a rayuwan mu muna sadaukar da ran mu ga abinda zai amfane ne mu duniya da lahira da babu sauran macen da zata shiga wuta a lahira. Gsshi kuma mutunci da kimarta zai karu sosai a gurin miji don dole nauyi da kunyanta ya hanashi wani abin koda yayi niyar yin hakan idan ya tuna da kawaicin da akai mashi shima. Nace Attu Allah dai ya gyara amma ai maza yanzu ba sanin hakan sukeyi ba don suma yanzu mazan ne sai a hankali dole sai mace ta kai ranta nisa akan su. Nace waiko Attu mai zogala na nan kuwa tace tana nan wallahi nace bari dai yau na shiga na leko ta. Na hada tsaraba sai gidan makwabciyar Attu duk da suna da dan jayawa kadan tsakanin su da su Attu din. Da sallaman mu tana ganin mu tace ikon Allah wa nake gani haka yau a gidan nan ko dai ido na ke min gizau ne wai. Sai naga kamar Rahaman Attu nake gani a gidan nan nace cikin dariya nice din dai Nana mai zogala tace wallahi kama kawai na kurciyan ki ne nagani nai amfani dashi. Tabarma ta shimfida muna muka zauna nan muka shiga gaisawa tana ta murna da jin dadin ganin mu. Tace yaya kuke na dawo wani lokaci nake tambaya najiki shiru ake cewa wai ai kina birni kin yi aure a can. Tace ke kadai ne ko kina da abokan zama ne nai dariya nace Nana abokan zama har uku nice ta hudu Nana. Tace wai, tau Allah ya kyauta sai a hada aita hakkuri nace in sha Allahu Nana na mika mata ledan da muka shigo dashi ta karba tana cewa zan baki wani shawara. Na gyara ina sauraren ta sai ta dakata ta na bude ledan da na bata take cewa ikon Allah harda tsaraba na samu haka Rahama wanan ya da alheri kike tun kina karamar ki. Taita godiya can ta gyara zama tace kada ki yarda ki sabawa ubangijin ki akan dan wanan rayuwan da bai kai ko cikon cokali ba . Kedai ki saka Allah a gaban komai sai kiga da farko za, a fara gwajin Imanin ki da abubuwa da dama. Sai kin saka imani a ranki sai kiga da sannu ubangiji na walwale maki al,amuranki sannu a hankali. Kin san Assma,ullahil, husna idan da zaki tsaya ki fake a garesu sai kiga da sannu ubangiji na maki falala a rayuwan auren ki. Zaki iya karanta Ya Allahu yahu, 1000 zaki kuma iya nafila raka, a biyu, sai salatin Annabi da hailala saiki karabta Allahu yahu, kafa 66 shima wannan anayin sa don neman bukata a gurin Allah. Ya Azeez minazeen 41 bayan duk sallah farillah na asubahi har tsawon kwana 40 akwai fa,ida sosai a cikin wanan kalman. Idan kuma kina da matsala da mijin ki ko kishiya ta sakaki gaba zaki iya yin wanan zikirin Al Khaaliq kafa 5000 insha Allahu zaki sha mamaki sosai ga matsalarki. Don samun tsari ga duk wani sheri ko kaidin da za, ai maki zaki iya karanta Al Mutakabbir sau goma safe da yamma. Zaki kuma iya karanta subbahanallahi walhamdullahi Allahu Akbar ko yaushe ba adadi don samun farin cikin zama da mijin ki. Naji wani irin dadi sosai ta kuma fara jero min irin hikimomin zama tsakanin kishiyoyi irin dubarun su na baya naji dadi sosai shiga na wurin Nana mai zogala don na karu sosai da ita. Nai mata sallama na dawo gidan Attu ban bar gidan ba sai da yamma yayi na dawo gida a gajiye dan tafiyan da nake a kasa kwana biyu gabobina kamar nai wani aikin wahala dasu. Gashi tun da nazo ban samu kiran maigidan ba shima banji ya kirani ba sai dana idar da sallah ishai ina gurin zaune na jawo wayana sai naga ashe ma a kashe wayan yake ban kuna ba. Na kunna wayan sai naga ina da dan sauran caji aciki maganan da mukayi da Nana mai zagale ya fado min a rai data girman kai da son jan aji ga matan zamani shine ke kawo yawan fitina a tsakanin ma aurata a wanan zamanin. Bayan mace tasan cewa a karkashin iko da mulkin mijin ta take amma sai wayewa da boko yasa mace ganin ai daidai take danamiji bazata iya kwantar da kanta ba ta samu aljannan ta dan boko da take takama ya ratsata ko wayewa. Dil na danna kira a layin daddy kira daya biyu gana uku naji ya daga wayan tare da fadin Assalamu Alaikum. Na karba mai sallaman nashi cikin girmamawa yace yau an ga daman jin motsin mu ke nan ? Nace ba hakana bane ba mu da sevices ne daddy inda nake yace ok su baba maigari suna dashi a gidan su da nake samun shi mu gaisa ke nan. Shiru nayi yace kin dai ga daman kiran layin mu ke nan yanzu kowa na lafiya ko nace lafiya muke daddy. Nace naga sako gun Hamza an gode Allah ya kara arziki yace ai ba sakkon ki bane da fatan anyi yadda nace dai nace a sanyaye anyi daddy kuma sun gode. Sai shiru nace sai anjima yace Allah bamu alheri na kashe wayan sai na kira layin anty tana dauka tace dani. Kai haba haba dai Rama yanzu fissabilillahi kin kyauta ke nan Rama ki kashe waya gani da yara muna son jin lafiyan ki shike nan tunda kika samu gida da yan uwanki kin manta da kowa nan. Nai dariya nace afuwan anty services ne babu shiyasa tace shine ko wurin kira na kudi baki zuwa ki kira kiji lafiyar mu Rama ? Ga yara sun hanani shakat da tambayan yaushe mummy zata dawo sun damu na kiraki suji muryan ki amma ke kin tafi kin share mutane can. Nace ai min afuwan anty abani su mu gaisa tace ai gasu tsaye sun min cirko cirko sunji ina kiran sunan ki a waya. Nan ta basu muka shiga gaisawa Nasir yace na karbo mai ragon shi a wurin maigari ita kuma Amira tace na karbo mata lalle a wurin inna ta da kuli wurin mama Altine. Mun gama wayan na lumshe idanuwa na daga inda nake kwance rigingine sai tunanen su da kewar su yazo min a raina . A gaskiya ban kyauta ba ko ga Anty na da yaran ban masu adalci ba don nasan zasuji kewa na dama. Gaskiya zama da manya ko zitartan su mutum zai dan samu wasu hikima a gun su gashi yanzu dan hikimar da Nana ta bani yai mun amfani yanzu yanzu. Da ace sai na koma ne zan gan su da banji dadi ba sai nauyi da kunya zai biyo min baya. Amma dan kiran da nai dabara yanzu nayi zai dan rage min wani nauyi a kaina ke nan. Bayan na kwanta naji dadi a raina ko ba komai dai nazo gida naga yan uwa da abokan arziki na kuma godewa Allah da baiwar da yai min na zama abin kwatance a idon yan uwa da abokan arziki. Zama mukayi mai ma, ana ni da maigari inda ya bani shawar warin zaman duniya tare da fada min wasu sirikan da ban sani ba a rayuwa naji dadi sosai da wanan taimako. Nan na fara shirin komawa gida cike da farin ciki da jin dadi a rayuwana don wanan tafitan ba karamin dadi da karuwa na samu a cikin sa ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA IDAN KIN KARANTA BAKI BIYA BA, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YA SAKA MUNA AKAN KI DON KIN SAN ONLINE NOVEL NE WANAN, , , 55 Da dare ina zaune tare da maigari a kofar turakan shi bayan ya idar da sallah yaci abinci ke zaune yana ta sakatan hakoran shi yake cewa dani bayan ja zo na zauna. Gobe ne tafiyan ku idan Allah ya kaimu lafiya nasan da safe zamu iya ganin driver din ku yazo daukan kan ku don haka nake son mu kara tataunawa dake. Nace a ladabce da to baba yace shi lamari na duniya yakan zowa bawane ta fanin da bai zata ba a rayuwan shi. Wanda yansan Allah ne ya kawo mai jerabawa hakkika ya godewa Allah da hakan don yana daga cikin imanin bawa yadda da kaddara mai kyau ko mara kyau. Don haka daga yau ina son ki cire wani tunane a ranki nacewa ko zaton wani zai iya maki wani sheri a duniya. Rahama ina son don Allah ko da yaushe ki dinga sawa a ranki cewa kin fa shigo ne kin samu mutumin nan da matan shi a tare. Ma wuyacin abu ne mutum yace ya samu yadda yake so kai tsaye a rayuwan shi sai ua hada da hakkuri tare da addua na neman tsari daga shedan da makiran mutane. Don haka bana son naji kin kasance daga cikin matan da suke da son kansu fiye dana dan iwan su. Ace kece aka sama a gidan a matsayin matan shi shin yaya zakiji a ranki, ? Wani mataki kuma ke zaki iya dauka akan wacce tazo ta samay ki da mijin ki a gidan kuna zaman ku na lafiya. Nissawa nayi tare da sauke ajiyan zuciya nace afili ba dadi baba yace to haka ne suma a yanzu suke ji a kan ki. Ita wanan boyar Allah matar shi abar zanceen ta don sai ince ashe har yanzu akwai sauran salihan mata a duniyan nan basu kare ba. Don ta sadaukar da rayuwan ta saboda farin cikin ku keda mijin ta da "ya"yanta don samun farin cikin ku a duniya. Don haka don Allah Rahama ki sawa zuciyar kii hakkuri akan duk wani abinda kike ganin suna maki na musgunawa wanda a shirye suke sai inda karfin su ya kare a kan ki. Amma idan hakkuri yana gaban al, amuran ki baki biyewa shedan ya rinjayi zuciyar ki ba zakiga abubuwan suna zo maki a cikin sauki yadda ma baki taba zato ba a rayuwan ki. Abinda nake so yanzu yazama dole ki kwanta ki bisu a hankali kiga gudun kowa a kanki. Don yanzu a shirye suke da suga ko ta halin kaka ssun kawar da ke daga shiga rayuwan mijin ku wanda hakan haline naku na mata. Ko wacce bata kaunan taga kishiyarta ta darata dako digon allura ne a gurin mijin ku. Amma sai naga kamar ya ta kin kasa ga irin hakkurin da na sanki dashi kin fara biyewa rudin shedan har kina son yin sakaci da daman da ubangiji yai maki na samun miji mai nagarta da mutuncii abin alfahari ga kko wace mace data ssamay shi a rayuwan ta. Rahama mijin ku ba mutum bane da za ai sakaci da samun irin shi don haka don Allah kiyi haakkuri ki kara akan wanda kike dashi a baya. Don gaskiya Rahama na faahinci kin fada son mijin ki yanzu ga yadda mahaifiyar ki tai min bayanin komai. Amma kuma sai gashi kina son yin sakkaci da daman da Allah yai maki a kan shi ai da kika ga cewa waccan dayar matar nashi kamar ta fara rinjayan ku a tsakanin ku . Ai kamata yayi ki kwantar da hankalin ki har kiga iya gudun su shifa asiri baya taba tasiri iyakar shi kwana arbain ne a duniya. Daga yau ina son ki sa, a ranki cewa babu wani asiri da zai sake tasiri a kanki sai dda amincewan ki don da kin fahinci da akwai matsala to kada ki kara bari har wani ya fahinci hakan yai tasiri a kanki ki yaki zuciyar ki gurin kyautatawa mijin naki a lokacin koda kuwa yana muzanta ki a gaban kowa gada ki damu da hakan don mijin ki ne ba wani ba can ki kaiwa ai kinyi ne don samun lada a gare ki. Karbi wanan ya miko min wani abu a kofin dake gefen shi na karba nayi yadda yace dani din naa shanye na shafa sauran a fuska na. Yace da yardan ubangiji babu abinda zai samu rayuwan ki sai abinda yafito daga Allah dai. Rahama ki godewa Allah don a dan binciken da akai min a kanki kina tare da tsarin ubangiji sun sani su ma babu abinda zasu iya maki yai tasiri don ke hasken mata ne a rayuwa wanda ba ko wace mace ke dace da hakan ba, sai wacce Allah ya halitta da hakan. Allah ya baku zaman lafiya a tsakanin ku ya kawar da ahedan a tare da ku ko yaushe ki ta hakkuri ya ta don Allah don shi hakkuri makami ne ga bawa maiyin shi. Nai mashi godiya namike zuwa dakin inna ta a can ma dai maganar dai duk nasiha ne mai kama da jan kune da daurewa da hakkuri. Na kai kallona ga tarin kayan da aka aje muna na tsaraba wanda duk yan uwa ne da abokan arziki suka kawo muna shi da kuma maigari daya kashe zarahin shi sosai a kaina haka kakannina suma sunyi nasu kokarin sosai a kaina. Da safe mun shirya sai ga Atika ta samay ni da kukanta wai dole da ita zan tafi na rasa yadda zanyi don yarinyar ta bani tausayi sosai dabara nai mata nace ta bari idan zan akawo min kaya sai azo min da ita. Amma ina taki yarda sai kuka take tana turjiya a kasa haka yasa ta ban tausayi nace zan tafi da ita idan ta kwana biyu sai a dawo da ita. Uwar taji dadi sosai itama yarta zata birni ta ga gari tasan bazata dawo haka ba babu karuwa a garesu. Sha biyu da yan mintina Hamza na kofan gidan maigari nan aka fara fitowa da kaayan mu ana jerawa a motan da yazo dashi katon rago maigari ya bayar wai akaiwa abokin shi Nasir. Naji dadi sosai a raina nake cewa baba duk wanan ragon na Nasir ne haka ? Yace to bai samu doki ba ai sai ya samu rago ko nai godiya sosai muna nan bamu kai ga fitowa ba sai ga amaryan babana ta shigo gidan da kaya niki niki wai da ita da baba suka hada min tsaraba. Sosai naji dadin hakan yau ni Rahama ne babana yaiwa wanan gatan haka a duniya aiko na san komai ya canza ke nan a gidan mu. Can muka kebe da ita dakin inna ta taciro wani leda daga jikin ta tace cikin kashe murya hajiya kin min abinda ban taba zaton zan samu ba ga rayuwan aure na a gidan ku. Don haka nima yadda kika soni kuma kika so jini na babuu nuna banbanci a garesu naga ya dace na taimaka maki da dan nawa siriin namu na mata dake taimakon mu zaman aure. Tsakani da Allah na baki kamar yadda bakki dauke ni da zuciya biyu baa haka nima wallahi ban dauke ki da hakan ba wallahi. Don Allah kada ki dauki wanan abinda dana baki a shirmay na bata lokaci sosai wurin hada maki shgi tun shekaran jiya don Allah da kinje na rokeki kiyi amfani dashi. Nai dariya nace mama Amarya kefa uwatace don may zan yi zargin zaki cuta min wallahi ni a uwa na dauke ki harga Allah. Tace nako ji dadin haka wallahi kuma na gode da hakan da kikai min niko insha Allahu sai inda karfina ya kare wurin yi maki duk abinda ya dace uwa taiwa yarta nai mata godiya muka fito. Sai ga jama, an gidan Garbati danaje naiwa abin arziki niki niki sai da nai kuka don murna da tunna baya. Har sabuwa sai da naje na gaida ita a gidan ta don rayuwa ya juya mata baya fitina ya hanata kwantar da hankalin ta tabari tai zumunci da yan uwan yaran ta har yanzu. Yan uwa da abokan arziki suna tsaye muka fito nabi duk wanda yazo muna Allah sauke lafiya da dubu daya Rukaiyya da Suwaiba ne naba dubu biyar biyar su kara don kudi yaa saura a jakkana. Muka kama hanya zuciyana cike da damuwa da rabuwan da zanyi da yan uwa na in kkoma can cikin bare da ba su san darajana ba gashi nan sai haba haba akeyi dani. ********* ********* ********* Karfe uku da yan mintina muka shiga get din gidan mu bakina yana dauke da wallahu galibun alla amrihi, kamar yarda Nana ta koya min. Zulfa muka fara cin karo da ita ga mamakina sai naji tace a, a mutanen kauye ne sannun ku da dawowa ashe kuna hanya ? Nace anty mun samay ku lafiya yaya su baby suke tace Alhamdullahi yaya mutanen gida anbarsu lafiya ko ? Nace duk suna gaida ku nagode ta shige motar ta ina ganin unguwa zata tafi don tayi shiga na alfarma sosai. Sai ga yaran su fito daga part din mu da gudun su suka fada a jikina da murnan su na rugumay su ina jin dadi raina. An fito da ragon da yasha wahala sai Nasir ya nufi gurin nace Nasir ga ragin ka nan inji baba maigari akawo ma. Haba murna tsalle da ihu yaran suka shiga yi gashi kuma suna tsoron ragon nace kaji nakine Amira ke da Jinior inji inna tace akawo maku. Nan na barsu sun kewaye dabbobin suna kallo suna ta magana a kan su don sun zama masu abin kallo saboda sai dai a kawo masu shi a yanke suka saba gani. Ragon ya shiga kuka don ganin shi a bakon wuri sai ga anty tafito da murnan ta da gudu na nufe ta na fada ajikin ta ina jin dadi. Muna cikin murna mukaji muryan hindatu na fada kai waye ya shigo muna da wanan abin gida kuma ? Yaran sukace da ita mummy Ragone fa na Nasir ne tace kai ku rabani dan Allah an kawo wa mutane abin tsafi a gida shine wai wani na Nasir can. Tsafi kuma hindatu Ragon ma kuma ake tsafi dashi don Allah wai may ye haka kuma ba dain ji komai na duniya na asirine ke ? Ba a, yine ko karya na fada ba ayi din ne may ye bamu sani ba sai dai mu kalli mutum wallahi duk abinda mutum yaje ya dauko ya kare a kan shi. Kazalika nace da ita a fili ban yiwa mutum sheri ba idan ya nufe ni dashi ya koma mashi. Hamza ne yace haba Hajiya Rahama keda kika dawo yanzu ina ke ina fada yanzu fa kika dawo daga kwasan albarka ji irin taro da dandazon da akayi maki na gata da zaki wuce aiko shi ya isheki mantawa da komai a duniya. Tau kai kuma fa wai naga fa raini ne ya shiga tsakani na da kai yanzu wallahi in kai tsiya akaina hamza kana batin gidan nan. Yace ai da zaki iya da ban kai hakan ba ko don ba yau ba burin ki ke nan a kaina a gidan nan nan ki ka samay ni sai dai ke ki barni. Tace banga laifin kaba hamza kaje an dura maka agumo kasha ka koshi dole ka zare ai. Hamza bar maganar nan don Allah kuzo mu shiga ciki kun debo gajiya inji anty. Tace a, a Rama ashe harda bakuwa kike tafe sai yanzu na ganta ai nace Atika ba rigima ta saka sosai sai ta biyo ni tazo ta kwana biyu ta koma ne. Ta koma kuma Rama kamar yaya ta koma inace tazo zama damune ta rike hannun yarinyar muka shiga ciki. Fatima ce ta bude part dina suna saka kaya a ciki nikan muna part din Anty ana murnan ganin juna mun samu gajiye ta hada muna abinci mukaci sai na mike zuwa sallah naja yaran muka fice tare. Atika sai raraba ido takeyi tana kallon ikon Allah muna shiga kamshi da sanyi ya tare mu don har Fatima ta gyara ko ina ko a part din tana ban daki tana wankewa lokacin. Na dauki remote na kuna wa yaran kallo na shige dakina nabi dakin da kallo na dan sake murmushi kadan. A gurin anty naji daddy baya gari wai yai tafiya nace shine kuma yasan bayanan yasani barin yan uwana ban gama ganin su ba. Mun huta don muna da gajiyan hanyan mu na project da baida kyau sai kura da ramu a hanyan. Ban fito ba bayan nai sallah sai biyar da wani abu na fito na samu yaran sun fice har Atika sun tafi islamiya daukan karatu. Na dan zauna nan muna hiran gida ni da Fatima sai can nace waiko ni Fatima may ke tsakanin ki da hamza ne ? Tai dariya cikin kunya take cewa dani may kika gani anty nace ban ga komai ba tunda makauniya nake ai ? Mun bar maganan don na fahinci akwai wata a kasa tsakanin su sai fatan alheri ga hakan. Sai da muka idar da sallah muka nufi gurin anty mun jima acan har su Fatima suka fara barci muna ta hiran gida da anty. Ganin suna jin barci na mike mukai mata sai da safe muka wuce part dina tare muka kwana mu uku a dakin da Fatima ke kwana don har lokacin ina kewan gida. Washe gari muka bude tsaraban mu naga irin kokarin da yan uwa da abokan arziki sukai muna. Na bar na bari na kwashi saura muka kaiwa anty tai matukar mamaki kwarai da ganin kokarin da akai min. Tace Rama wanan himilin kaya haka ke may kika kai masu haka nai murmushi kawai ban fada mata komai ba sai cewan da nayi anty gida naje fa kuma suna kewa na . Tace hakane Rama nima da ina da yan uwa masu sona da kaunata da wallahi na dinga zuwa ina son in ga ana zumunci wallahi. Mun dibarwa kowa har yan uwan daddy da iyayyen shi sai da anty ta sa aka hadawa tsaraba. Ta sa Hamza yakaiwa kowa nashi a ranan sun karba kuma da murnan su don da Fatima da yaran suka tafi. Nan gida ma mun aikawa sauran shiya Zulfa ta karbi nata tace ta gode don tun a gaban Fatima ta fara diban ayya tana ci. Hindatu ko tace bada ita ba maza a fita mata da kayan da aka tsafe don sheri za, a kawo mata wani shegen tsaraba can. Murmushi nayi banji zafi ba don nasan za, a rina ai indai itace bata san abin arziki ba dama. Ko da na dawo na ji Alhaji daddy baida lafiya dama ashe kuma jikin na shi ya kiya haka yasa daddy baro abinda ya kai shi ya dawo gida yaga jikin mahaifin na shi. Sai ganin shi mukayi kwatsam ya dawo kamar yadda ya saba yi idan ya dawo ana zuwa gaida shi haka ma tare da anty muka je gaida shi. Yana tsaye yana waya da alama da likita yake wayan a lokacin don yadda yake magana muka fahinci hakan. Ya gama ya juyo gare mu anty ke cewa jikin Alhajin ne kuma ya kiya har yanzu ? Yace wallahi suna son bashi gado amma yakiya ya bari kuma a fita dashi waje shima yaki hakan. Nace a sanyayye sannu da dawowa daddy yace yauwa kun dawo lafiya yaya su baba da sauran mutanen gida ? Nace suna lafiya suna gaida kai daga haka nai shiru suka ci gaba da magana da anty yake cewa mu shirya idan anyi magariba sai aje a dubo shi. Ban san cewa tafiyan gaba dayan mu bane sai da kowan mu ta shirya ne muka fito zuwa gaida Alhaji a zatona dagani sai shi da Anty ne amma muna fito sai gani nayi ana rikici a bakin mota. Zulfa ne da hindatu ke rikici suke gardaman ka zama a gaban mota wai tare da maigidan. Gardama da fada sukeyi sosau a wurin yana fitowa shima ya samay su a hakan. Tsawa ya daka masu yana cewa what all dis noses for wai baku da hankaline may ye haka kuke min hauka zallah ? Don ba mahaufan ku bane baida lafiya shine har kuka samu wurin caza min hankalina kuma ? Ni dai na bude bayan mota na shiga na zauna abina ina sauraren rigimar su na fitina. Yace ke Saade zo ki shiga maza fito daga wurin don Allah yake cewa Hindatu data shige ta zauna ko ? Zulfa tace sai dai haka wallahi amma ba wanda kikafi anan balle kice komai kece gaba gaba ? Tana shiga ta takani sai da na danyi kara takuma juyo tana cewa dani may ye haka kuma zaki cika mu da ihu ke kuma ? Nace malama amma dau kinji kin takani aiko da wanan takalman naki yanzu. Hindatu ban fa son hauka wallahi zan bata maki rai yanzun nan a wurin nan. Suka zauna ya figi mota sai sababi yakeyi ran shi a bace yake fada inda yake shiga ba nan yake fita ba. Mun kai gidan kowa ya fito ta tsaya a baya itama Zulfa ta koma kusa dashi tare da mika mai yarta ya karba. Mutanen gidan na falo hardasu mama laraba da suka shigo gaida shi nan muka shigo duk kallo ya koma a kan mu . Aisha tace yau tafi da gidan ka akai muna rangas wazamu kalla a nan uwar gida ko may bi mata ko yar uku mai gumban uku koko amarya mai batun hankali zamu kalla. Kowa taimai kirarin shi don haka aka washe suna muna sannu da zuwa nan suka samu kujera suka haye. A kasa na zauna naga zaman su haka baiwa hajiya dadi ba don ta tsuke fuskanta ba fara, ar da takeyi da farko na ganin mu. Daya bayan daya muke gaida su inda su ko sukace ina wunin ku cikin jam,i muna tambayan ya maijiki ? Nace Allah yasa ciwo kaffara ns yace amin Rahama ashe kinje gida ne kwanan nan bamu bada tsaraba ba sai gashi an kawo muna mai yawa haka ? Nai murmushi na dukar da kaina yace Alhaji karami baka kyauta min matarka zata ganin gida baka fada muna ba. Dana sani aida nai aike garesu don mutanen na sa mutinci da sanin ya kamata gaskiya. Naji dadi sosai ga yabon da akaiwa iyayyena a gaban kowa ko ba komai an karama min iyayyena kowa naji tunda bani kadai bace a wurin ai. Sai hiran su suke zubawa ina zaune daidai kafan Anty, a takure na kasa sakin jikina dakowa a wurin . Can dai na sa hannu a cikin handbag dina naciro goran zuman da dan wurin garbati ya bani tsaraba da zan dawo har galon daya shine na ciko gora dashi na kawo wa Alhajin daddy kada nazo hannu sake naji kunya don ban san abinda sauran suka dauko mai ba. A hankali na mike daga inda nake zaune na karasa kusa dashi na tsugun na nace Baba ga zuma asha magani dashi. Gaba daya aka mayar da kallo gare ni yace tare da dan yun kurowa kai yar nan ubangiji Allah ya albarkace ki da zuria masu albarka. Nagode nagode kinji Allah ya saka maki da mafificin alheri hajiya tace Allah yasa mai kyaune gashi muna ta yawon neman zuman da baida hadi dama an gode Allah ya rufa asiri. Daga inda daddy yake zaune yace wanan tafiyan na Rahama dai ne ke nan don gashi tasha addua muna zaune. Yanzu ai babu zuma mai kyau sai dai hadi ko inji Zulfa nace wanan mai kyaune baida hadi ko kadan. Da wuya a samu zuma mai kyau sosai yanzu sai sunyi mashi surki nan kuma aka shiga hiran zuma din. Can nace ai zuman dake da kyau ba bace yake ba har ma idan mutum bai yarda da kyaun shi ba zaka iya zuba shi a kasa ka gwada shi. Idan baida kyau kasa zai tsose shi ne a take idan kuma mai kyaune haka zai tsaya a saman kasa baya tsotse shi. Kaji wani hikima kuma na mutane yanzu sai kuma a gane gaskiya a hakan inji daddy nace mu haka mukeyi a wajan mu. Don Allah dear ku tashi mu tafi dare ya soma ana ta faman hira tunda munyi abinda ya kawo mu din inji hindatu data suka tana cika tana batsewa. Yace gaki ga hanya ai idan kin gaji ne don ba mahaifin ki akazo gayarwa ba zaki bude baki ki fadi hakan. Alhaji yace a, a ku tashi ku tafi ai na gode da zuwan ku Alhamdullahi kuma ai na samu lafiya ko . Bai tashi ba duk da mahaifin shi yai mai magana sai zuwa can mama laraba tace Alhaji karami kwashi matan ka kuje gida hakana don dare ya soma yi. Ya amsa da to mama muna nan dai a zaune bai tashi muma ba mai ikon tashi a cikin mu. Sai shadaya da rabi mukai masu sallama muka dawo gida a hanya yace da anty Saade wanan kaunar taki fa kada ta amshe maki fada gurin Alhaji fa ? Tace ai ba matsala komai Rama zatayi ai na alheri ne ga kowa sai wanda bai san da hakan ba gare ta. Neman suna ne don a san da ita take hakan ai abinda mutum yayi badon Allah ba don yabo ai baida, , , Will you keep quiet my friend ke zaman ki ke nan hassada da bakin ciki a rayuwan ki duk abinda wani yayi idan bake bace ba daidai bane ? Dama shi dan bakin ciki ai haka yake kan shi kawai ya sani bai san wani ba inji Zulfa dake da takaicin Hindatu din a ranta. Kai ku bar wanan maganan haka please ba a zaman arziki kullun sai tsiya hakan baida wani amfani wallahi anty ce ke wanan maganan. Har muka shiga gida kowa na kule da dan uwan shi a rai ni dai ana tsayawa na bude gefen da nake na fice na basu guri. Har na fara tafiya naji daddy na fadin Rahama ki hado min tea don shi kawai zan iya sha in kwanta yanzu. Kamar yaya ta hado ma tea kuma kasan dai koda kai tafiya ban fita girkina ba ka tafi. Hindatu ban fa son wanan haukan naki nace ta hado min tae tunda baki da hankali ke baki san Allah ba. Nan fitana ya kaule masu anty tace dani wuce mu shige ki hado mai tea din kada dare yayi fadan su ba mai karewa bane su. Ban bata lokaci ba ina shiga na wurgat da jakata na fada dakin abinda amaryan baba na tabani takuma hada ni da Allah nai amfani dashi na dauko na nufi bathroom na aiwatar kamar yadda tace min nayi. Daga nan na fito na nufi kitchen na fara hada mai tea din daya bukata take naji na fara hadewa jikina yana bani abin akwai shi da ma, ana. Koda nakai mai tea din yana wanka na aje mai na tafi nima na kimtsa jikina na dawo. Kafin na gama komai naji na hade kamar wata chewgun dani ga wani irin desire da nake ji duk kasala ya rufe ni nasan wanda nasha ne ya fara aiki a jikina shima. Yana zaune yana shan tea na shigo dakin yace kin rufe kofan na amsa da eh na samu wuri na zauna. Bai juyo ba bai kuma dago kai ba yace to yaya kuka bar mutanen gidan nace suna lafiya suna gaida ku. Yace shi baba maigari harda dawainiya haka yaiwa Nasir wanan babban rago haka ? Nacd Nasir dama mutumin shi ne bai samu doki ba ya samu rago ai yace hakane wata rana ai zai iya bashi dokin ma inda halin hakan don duk wanda ya baka kadan akwai ranan da zai baka babba ai. Yana gamawa ya hawo gadon yana cewa kin fadawa anty ki zancen ginan da akewa baba ne nace ban fada mata ba tukun. Yace wani amsa kika shirya bata don kin san zataji ko tagani ranan da duk mama Altine tazo garin nan. Shiru nayi don nasan maganan shi gaskiya ne yace sai ki ce da ita kudin kine tun tuni kike tarawa kikai aikin dashi. Nace dashi nagode na lumshe idanuwana don sai godiya nakewa Allah da ban fada mata komai ba tun farko tunda nagane bai son asan shine ya gyara muna ko may yasa oho. Kamar ya karanci zuciyana sai naji yace bana son abinda zai kawo bacin ran wani daga cikin ku ne. Kuma ya kamata a taimaka masu duk da nasan ina da amsa ga kowan su don ba wanda banyiwa shigen hakan ba daga cikin su. Gori da habaici irin naku na mata ne ban so ga alheri idan nayi shiyasa ban son yawan surutu haka. Daga haka ya rungumoni nan wasa ya canza sallon shi ranan daddy ba karamin jirkita ni yayi ba don kamar ya zauce min ya koma a ranan da kyar na samu ya barni na huta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH YAR UWA DON CIN AMANAN ALKAWARI DON KIN SAN ONLINE NOVEL NE, , , , 56 Washegari nafito shar dani cikin dogon rigar material kayan sun matukar karban jikina sosai. Nayi kyau dani kaina na sani don na bata lokaci wurin shiryawa na samu an hada breakfast dan fruit na hada mai da ferfesu. Nakai mai har lokacin daddy yana kwance bai tashi ba na shiga na hada mai riwan wanka a bathroom. Inda yake kwance saman gado yana barci na nufa na zauna a bakin gado nafara ja mashi dan yatsun kafan shi a hankali. Da kyat ya bude idanuwan shi ya sauke su a kaina nace daddy ka tashi kaje ka duba yadda baba ya kwana don naga ko jiya yana dan jin jikin nan nashi. Ya gyara kwanciya gami da mika yace dani da safe haka Rama ? Daddy tara fa ya kusa yanzu ai gara kaje ka duba shi don hakane kawai yanzu tsakanin mu dasu. Murmushi yayi ya jawo ni zuwa jikin shi yace kwalliyan nan naki ya burgine sosai Rama. Nace nagode daddy Rama ban san godiyan da zan maki ba a daren jiya kin mantar dani duk wani tarin matsalolin dake a cikin rayuwana. Kunya naji na noke kaina kasa yace Iam telling you the true kina sani a farinciki ko yaushe wanda ni ban san dalilin shi ba Rama ? Na dan yi kokarin raba jikina da nashi sai naji ya kara matse ni yace da ace zan san wake gyara min babby na haka ko yaushe zan iya yi mata kyauta a rayuwana. Nagane so yake ya gane may ye sirin nawa sai nace cikkin dariya daddy ka godewa Allah don shine yai min hallitta na hawainiya kila mai canza kama ko wani lokaci. Rama ya fadi a kasalance na amsa a hankali yace bana so kina fushi dani kina min rowan farin cikina a kan ki. Baki san irin halin da kika jefa daddy naki ba yan kwanakin da suka shige ko kin saka ziciya a cikin garari a gidan nan ? Bana so kina daukan zafi haka dani bake ba duk wanda ke a karkashi bana son ya bata ran shi a kaina ko kadan. Wanan dalilin yasa nabarki kije gida har tsawon kwana hudu don ki samu ki huce ko zan samu kwanciyan hankali. Bana so ina fadi mutum yana fadi nakan ji zafin hakan a raina sosai gashi harkin hasalani nakai ga taba lafiya jikin ki wanda ko yaushe nakan kalli hannuna dana daga na mare ki da shi a matsayin bai min adalci ba ko kadan. Kara lafewa nayi a jikin shi nace daddy ni yar kace daka raina da hannun ka kuma yanzu ina a matsayin matarka don haka kana da ikon daukan ko wani irin hukunci ai a kaina don ka cancanci yin hakan a gareni. Idan babba bai nuna matsayin shi na babba a na kasa dashi ai ko yauahe karami baya sanin yai laifi don haka nima ina mai baka hakkuri da kayafe min duk abinda nai maka a lokacin. Sai dai ba yina bane don a lokacin wani irin yanayi nake ji a kan ka daddy ina jin zafin ka ina jin takaicin ka fiye da kima raina yana matukar baci sosai koda kuwa sunan ka naji an ambata min. Sai naga ya dago ya kalleni kadan ya mayar da kaina a saman kirjin shi ya sauke ajiyan zuciya bai yi magana ba sai dai ina jin yadda kirjin nashi ke halbawa sosai can naji ya sauke ajiyan zuciya. Yace, Rama akwai matsala a wani wuri don abinda kike ji nima din shi nake ji sosai a raina akan ki sai da nayi kokari na sa ai min rokon Allah don na dan samu sauki don gaskiya koda zamu zauna a hakan ba zan iya rabuwa dake ba a rayuwana. Yace na kuma ji dadin fada min sirin zuciyar ki da kikayi don haka shine zama na tsakani da Allah halinku ne na mata shiyasa ko yaushe bani zama ban saka an min sauka ba akan iyalina dani kaina don neman kariya daga fititinu masu haddasa fita a tsakanin ko da yaushe. Rama ina son ki nima nasani wanda hakan yakai ban iya boye hakan a gaban kowa duk yadda naso na boye irin yadda nake jinki a raina ba zan iya hakan ba a gareni. Don haka ki kara hakkuri akan wanda kike dashi ki zama mai juriya akan komai ki kawar da idanuwan ki akan kowa a gidan nan. Nidai ke zama daku nakuma san halin kowace daga cikin ku ance kowa da halin shi ake zama dashi ai. Kin min abin da yasa raina jin dadi a daren jiya kin gwadawa duk wanda ke guri ke yarinya ce mai tarbiya da sanin yakamata. Ba komai ba sai daraja min iyayyena da kikayi a gaban kowa wanda nasan ko a bayan mu zasuyi magana a kan hakan da kikayi nakin zama aaaman kujera suna sama su ma. Don haka shine girmama iyayye da daraja su wanda matan yanzu basu san barin haka a gare su wani sakaci bane maigirma sun dauki yin hakan garesu a matsayin wayewa ne. Kin ba Alhaji zuma wanda har yasa ba Alhajin ba har hajiya saida taji dadin hakan da kikai masu nagode Rama Saade ce kadai a cikin ku takewa mahaifana haka a baya yanzu kuma naga ta daina hakan itama. Amma ance shi alheri ko sau daya kaiwa mutum bazai taba mantawa da shi ba a rayuwan shi. Nai murmushi nace daddy kakanina ne fa kuma iyayye na don may nai masu alherin don su saka min albarka har zakai min godiyan yin hakan da nayi albarkan su fa nake nema nima ? Murmushi yayi yace dani ai kin samu kuwa Rahama don Alhaji ya saka maki kwado kwado. Daddy tashi kai wanka ruwa yana jiran ka a ciki tun dazun yace bakya so na kara shakan kamahin matana naji dadi ne bayan kwana biyu an hana ni jin dadi da abata. Murmushi nayi na zare jikina daga nashi na mike ina cewa Allah ya kaican yana hanaka jin dadin abinda kake so ai. Bayan yai wanka ne ya karya bai tsaya ba ya dauki key zuwa ganin Alhajin nashi har mota na raka shi saida ya fice gidan na juya zan shiga ciki. Hindatu ce a tsaye ta dafa bangon gina tana min kallon harara ko ajikina nace a raina sai dai ruwan idon ki ya tsiyayye. Ban bi ta nata ba na shige abina na barta a wurin ta bini harda zagi ni dai na shige abina. A can part din anty na shige har lokacin bata fito ba na juya zuwa daki nawa part din. Ban dade da shiga ba sai ga gajeye ra shigo wurina tana cewa dani hajiya Rahama dama ina jiran ki huta ne muyi magana dake. Nace gajiye lafiya dai ko ? Tace dani bakomai sai zance na da maigadi gashi ya matsa min yana ganin nice tare da ku yaji har yau ba wani zance akan maganan mu. Na nisa nace hakane ai baki ma san wani abu ba wani sabon zance tsakanin Fatima da Hamza driver. Tace ashe kin sani Hajiya nace wanan tafiyan da mukayi ne na fahinci akwai matsala a tsakanin su. Nace ni yanzu Gajiye ba wai naki hakan bane kinga ga naki zancen ya shafe ni kin dai san halin matan gidan nan cewa zasuyi munga wuein ci munzo mun tare wa mutane haka a gida gaba dayan mu Wanan kan zasu fada don fada don basu raina magana su nace ni indai haka bai zama matsala ga maigidan da uwar dakin mu ai suje suyi ta fada kawai. Yanzu ki bari idan daddy ya natsu zan fito mashi da maganan ai muji may zai fada akai don ayita ta kare . Tace bari ta koma kada uwar dakin mu ta falka bata kusa tana fita na koma na kwanta don a gajiye nake a lokacin sosai. ********* ********* ********* Ya shiga gida da sallama ya samu daddy da hajiya zaune suna karyawa tana bashi abinci, a hankali ya shigo da sallaman shi duk suka bishi da kallo don bai saba shigo masu wanan lokacin ba hakan. Sun zauna da shi suka gaisa yake tambayan yadda mahaifin nashi ya kwana da jikin shi hajiya tace da sauki sai dai cikin dare jikin ya dan motsa mai Allah ya taimake mu zumar da wanan yarinyar takawo muna yana nan shi muka samu mukai amfani dashi Alhamdullahi sai ya samu sauki yai barci sosai sai yanzu ya falka shine yake girkawa. Alhaji ya dan gyara zama yana cewa da kyat wanan yarinyar Allah yai mata albarka na dade ina neman zuma na sahihi na kwarai ban samu ba ko wani aka kawo baida kyau yana da dan hadi acikin sa kuma sai mutum ya rantse ai mai kyaune nashi . Yanzun da Alhaji ka gamsu da wanan din da Rahama ta kawo ma ke nan ko ? Yace ana magana zuma ne mai kyau sosai wallahi, Allah dai yaiwa wanan yarinyar Albarka kaita hakkuri da abinka yarinyar nada kirki wallahi sosai. Ga mamakin sai yaji hajiya tace tana da tarbiya kan gaskiya ji jiya su fitsararun ma zaman gwada sa,a mukayi dasu amma ita ina lura da ita tun bata aureka ba bata taba zama dakai a saman kujera in kuna tare. Yace ko a kaina haka take bani zama ta zauna kamar sauran yanzun haka ma ina barci ita ta tayar dani da ga barci nazo naga lafiyan Alhaji yanzu don taga alaman mun barshi yana jin jiki. Yace tagani ne don duk hiran da ake tun lokacin nake jin jikin na motsa min ban dai yi magana bane. Daddy bai dawo gida ba sai da ya shawo kan Alhaji suka koma asibitin aka duba jikin shi sun fito suka hade da wani abokin daddy yake cewa ai idan daddy nason yayi lafiya to ya samu daddawa na ainihi wanda baida surki ya dinga cin miyan shi da kayan yaji sai kuma ya samu rake ya zauna yasha shi sosai insha Allahu jikin zai kara yi mai sauki. Tun da suka dawo ake neman daddawa mai kyau da za aiwa Alhajin amfani dashi basu samu ba. Muna zaune da anty muna hira nace anty na manta na fada maki ai na hada dan kudin dake a wurina na bayar anawa babana gyaran gida dashi. Nan dai nai mata bayanin komai tace kai amma ko kin kyauta wallahi Rama shine baki fada min ba nace sai yanzu abin ya fado min a raina ai wallahi. Mu kai ta hiran akan rashin lafiya ta nake ta bata karfin gwiwa tun tana murmushi har tana daukan magana ina dai yi ne amma dana matsa sai jikin ta yai sanyi ta gamsu da magana ya kara mata karfin gwiwa sosai a ranta. Haka maigidan ya shigo part din ya samay mu tana zaune a three seat ni ina kwance a kasa daidai kafan ta sai hira muke zubawa da dariya a tsakanin mu. Shigowan shi yasa na dan mike zaune, muna gaidashi ya zauna yana cewa may yai maku dadi kuke kwasan dariya haka tundaga waje anajin muryan ku haka ? Kai daddy yara wanan dariyan ne har yakai waje inji anty ke fadin haka cikin dariya. Hira dai muke ni da kaunata abin ya bamu dariya ne shine kaji muna kwasan dariya haka. Yace to nima gani ai sai ayi hiran dani muyi ta dariyan ko dariya ya bamu anty tace gulma ka mukeyi ai ko. Yace dama shine aikin ku ai da kun zauna sai a kirkiro min laifi a za akaina kuma ? Dariya ne yazo muna a lokaci daya tace kila kayi laifin ne kake shakka ko yace bani rasawa fa ni fa kin san yanzu babba ne na wuce mijin mace biyu sai mijin mace hudu. Ni dai ina jin su suna ta fafatawa sai dariya nake masu kawai suna ta faman musu a tsakanin su. Nace anty ga daddy wai yaya zancen Gajiye ne da maigadi ake ciki gashi har yanzu ba a ce komai ba shima ya samu ya kai ga ko daya ne. Anty tace gaskiyan ki Rama tunda gashi shi har yana ikirarin shi kai mata hudu ne sai a taimaka wa mai son yi daya ya samu shima. Daddy yace wai tsaya zancen dama gaskiya ne tace yanzu ba gashi kaji ba sun dade ai su da sasanta kan su ko. Daddy yace to aini ba wanda ya fada min wanan zance tun wancan lokacin da may zai hana ayi tunda raya sunna ne kuma hakan ai taimako ne garesu. Shima Hamza baba yai min magana akan shi wai wanan yarinyar dake wurin ki Rahama yake so. Nace kamar ban san zancen ba wa ke nan ko Fatima dai yace ita mana ita ya ce sun shirya wai a tsakanin su ko. Ko ke baki san da zancen bane dama ? Nace to ni dai naso nagane da mukaje gida amma sai na dauka mutunci ne kawai a tsakanin su hakan. Anty tace ai Fatima mutum ce ya koyi saan mata gata da tsabta kamar Ramana itama gashi bata da yawan surutu. Yanzu zan samu lokaci na gansu sai muyi maganan da ya dace akai ina ga zaifi. Naji dadin jin mincewa daddy sosai a raina don ba wani muhawara ya yarda da zancen. Hajiya ke son daddawa mai kyau Alhaji ake son yiwa amfani dashi an rasa mai kyau na kwarai duk wanda ake samu wai bai masu ba. Nace nako dawo da daddawa daga gida ban sani ba ko zaiyi mashi gardin sai dai a gwada a gani. Na mike ina fadin bari na dauko a gani, nafita na barsu nan ban jima ba sai gani dashi a leda na bashi. Bai jima ya mike ya fice daga wurin mu nima nace da anty zan je na leko su Fatima. Koda na shiga na samu Fatima na sancewa Atika kan ta nace a, a yau kitso za, a sha ke nan tace naga kan nata yayi wani iri ne. Nace gama sai na kwashe mata kafin mu je a wanke muna wani sati nima kan nawa ya fara damuna ai. Muna kitso nace wai Fatima kin tabbatar da zancen ki da Hamza don yanzu daddy yai min magana akan zancen. Tace cikin dan razana don Allah da gaske anty daddy yasan da zancen nan ashe. Nace in dai kin tabbatar da gaskiya kina so to ki fada min sai a san abinda ake ciki. Shiru tayi naci gaba da kitso na har muka gama nace taje tai wanka tazo ta shirya kafin aje islamiya. Daga nan na shige na barsu tunda ba girki muke dashi ba a part din mu don haka na kwanta abina. Barci na samu nayi sosai don ina fashin sallah a lokacin haka yasa na samu nai barci yadda nake so. Ko da nafito yamma yayi sosai a lokacin ban shiga gurin anty ba sai da mukai sallah . Na samu suna kwasan hira da yaran suna ganina sukayo kaina nan muka zube tare da su har wani lokaci. Ina ganin sun fara jin barci na mike na kaisu daki na kwantar dasu tare da masu addu,a. Na dan jima wurin su nafito anty ke cewa dani ai na dauka kin tafi kin kwanta ne ko ? Nace a, a ina can da mutanena ne na samu sunyi barci yanzu da kyat ai. Na ce zanje na kwanta nai mata sai da safe ina shiga wayana yana kuka alaman kira yana shigo min. Na duba daddy ne ke kira na na daga yace kinyi barci ne ko ? Nace a,a yanzu dai nake shirin kwanciyan yace ok gani nan zuwa kada ki rufe kofan ki. Mamaki nake a raina may kuma ya faru daddy zai shigo yanzu sai gashi yazo yana saye cikin kayan barci nasu na maza. Ina tsaye ina son saka riga sai gashi ya shigo dakin na juyo ina kallon shi fuskan shi babu annuri ko kadan yace dani. Ki shirya muje dakina ki kwana a can yau nace daddy dakin ka kuma yace eh haka nace ko baki fahinta bane ? Nace daddy naga banice da girki ba yau din nan yace zaki shirya mu tafi ko zaki tsaya min gardama ne kuma ? Daddy ba hakana bane, naga haka ba kyau ne shiya ni zaki fadawa abin da na sani akai. Nace kayi hakkuri daddy ina ma up ne yanzu haka bana sallah daddy. Wani kallo ya watso min na noke kaina a kasa sai naji ya jawoni zuwa jikin nashi ya rugumay ni yana sauke numfashi. Daga tsaye ya shiga lugwigwita ni har muka kai saman gado duk tsoro da imani ya na cin zuciyana. Sai da ya tabbatar da ya samu natsuwa a gareni ya sake ni yana mayar da numfashi a hankali. Ya dan jima a zaune ya dafe kan shi da hannu daya, ina kwace na kura mai ido baiyi magana ba zuwa can naga ya mike yace dani thanks ya mike ya fice na dade kwance da kyat na mike na rufe kofan part di na ina tunanen ina matar shi don nasan mace yake bukata haka. Har barci ya dauke ni ina tunane may ke faruwa tsakanin daddy da matan nashi ne yau haka a gidan. Washe gari barci na nayi sosai ban fito ba sai shadaya na mike nai wanka na shirya na nufi wurin anty. Ina shiga take cewa dani yau wani irin barci ne haka gida ya hargitse muna da rikici haka ba dadi . May ke faruwa ne anty tace besty ne mana da matar shi suke rikici tun asuba ne ko daren jiya ban sani ba wai ya rufe kofa ya hanata shiga gun shi. Yau kuma da wanan fitinan muka tashi kuma tace ke dai bari Rama na rasa may ya kawo masu wanan rikicin ne haka ? Shiru nayi ina tunanen abinda ya faru a daren jiya tsakanin mu dashi daya zo min a bukace dashi. Ban daice ma anty ga abinda ya faru ba tsakani na da daddy daren jiya don da kunya ma koda ace a wurin wanj ta samu wanan labarin. Ban dade ba na koma wurina, sai gashi ya shigo yace ki shirya zamu bi jirgin yamma zuwa lagos yau din nan. Na mike daga kwance na zauna ban kuma yi magana ba sai nai shiru don fuskan shi babu annuri a cikin sa. Bayan ya fita na mike zuwa wurin anty na sheda mata zancen tafiyan sai take cewa yau zai tafi ke nan ashe ? Nacd haka yace dani tace to sai ki shirya ke nan ko kafin yamma yayi jiki ba sukuni nafice na samu Fatima ina mata bayani tafiya na. Ita ta shirya min kaya don dai ni ban so binshi ba bana son abinda zai taba min karatuna ko kadan. Yadda yace haka akayi don magariba muka bar gida nai wa anty da yara sallama babu wacce na sallama a sauran matan don banga amfanin hakan ba gareni. Don ka dawo basu taba zuwa su gaida kai da zuwa ko su fada ma zasu tafi don haka nima nasa a raina babu wacce zan kara sallama. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE, , , , , , , IDAN KON BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH DON ONLINE NOVEL NE KIN SANI, , , 57 Zaman mu a lagos bazan iya cewa ga irin dadin da nasha ba a gurin daddy don ya nuna min karamci sosai a wanan tafiyan da mu kayi. Banda wani damuwa sai idan ya fita tun shidda na safe baya dawowa sai shidda na yamma daga hakan muna tare bai fita kuma ko ina sai washe gari haka yasa shakuwa sosai ya kara shiga tsakanin mu sosai. Don zamu zauna muyi hira inta zuba shagwaba gareshi abinda ban samu ba a gida yanzu na samu a nan wurin shi da muke mu kadai. Ina ji tankar a ce haka zaman mu zai dore a haka har abada don bani da damuwar komai a hakan da muke anan. Sai nake ji a raina macen da take daga ita sai mijin ta a gida ta more miji don dai ni sai nace ban san dadin aure ba a hakan. Sai da mukai sati uku a lagos mukai haramar dawowa gida kano gurin yan uwa. Matar abokin shi ne tazo har masaukin mu ta dauke ni muka shiga kasuwan lagos inda na narka kudi na na kwaso les da sauran abinda nasan zasuyi saurin shige min a gurin mutane. Na sawo wa yara na kayan masu kyau da tsada da abubuwan da bamu dashi a nan na sayawa Atika kayan yara mata masu kyau a cikin rahusan kudi mai sauki har yaran su Zulfa da hindatu sai da suka samu tsaraba na duk da nasan akwai matsala a gurin karba. Ba karamin alheri na samu ba a wannan tafiya da mukayi da daddy haka yasa na kara fahintar dalilin da yasa matan shi ke son yin tafiya dashi don daddy yana sakarwa mace hannu idan yai tafiya da ita sosai. Kayan mu sun riga mu shigowa arewa don sai bayan kwana biyu muka dawo mu da karfe uku na rana muka sauka garin kano. Duk kyau da tsarin da gidan dadi ke dashi sai dana raina hakan don abinda nagono a tafiyan mu din. Na samu taro sosai a gurin anty babu wani canjin fuska dana samu a gurin ta da murnan ta, ta tare ni. Nai wanka nai sallah ta turo gajiye har part dina ta gabatar min da abinci na kaiwa maigidan. Shima na samu yai wanka a lokacin tare muka ci abincin rana dashi sai kuma wanan lokacin da muke tsaka da cin abincine matan gidan ke shigowa yi mai sannu da zuwa. Babu wacce tai min an dawo lafiya nima ban damu ba da hakan don na riga dana saba da wanan halin wurin su haka ake tafiya. Yar wurin zulfa ce ma take mika min hannu na dan mata wasa daga hannun uwarta ina cewa babby mun samay ku lafiya ? Sai uwar tace kalau muke ba ta kuma tsaya ba tai mashi a huta gajiya tabar falon inda muke zaune muna cin abinci. Kai ya girgiza kawai yace a fili kukan kuna da matsala wallahi ban ga ranan da zaku daina wanan halin kishin tsiyan ba haka ? Kamar nai magana sai dai na daure ban taka shi ba kada na ja zancen da nisa na hade komai a raina muna gamawa dama a gajiye nake na kwashe kayan zuwa ciki sallah nayi tun wurin ina addua barci yake sata na. Barci nayi sosai a kasa saman carpet din sallah har sai gab da magariba ne fatima ta shigo ta tayar dani sai dana tashi take fada min daddy ya shigo ya samu ina barci amma ga kaya nan an shigo min dasu part dina. Ina alwala naji shigowan yaran da murnan su sunzo taro na ina fitowa duk sukayo kaina suna murnan gani na. Sai da na sallamay sallah na sa Fatima jawo jakar dana zuba tsaraban su na ba kowa nashi haka suka koma fun uwarsu da kaya masu yawa a hannayen su. Kusan tare muka shigo da jinior na dauko mai kayan wasan shi ina jin anty na fadin wai ita Rama bata gajiya da lodo maku tsaraba haka ne duk tafiya kamar don ku takeyin shi. Na karaso ina cewa haba anty indan ban masu tsaraba nayo mawa balle kudin uban su ne ai anty. Tace ke kika san wanan Rama idan bake koni mukai tafiyan ba dashi ina zasu samu kaya haka wani magani na miko mata nake mata bayani yadda akace tayi dashi. Bataki ba ko ta zargi wani abu daga gareni tun a gabana naga tace gajiye ta bata ruwan dumi ta fara sha tasha shi sosai muna hira ta soma cewa zatai fitsari kamar yarda mai maganin tace zatayi da kuma barci. Hakan kuwa akayi na ce gajiye ta zauna a dakin da ita na kwashe yaran muka nufi part dina acan muka kwana tare dasu. Da safe ina idar da sallah na fito, zuwa dubata na samu gajiye na kokaein azawa yara abin zuwa school muka gaisa da ita nake tambayan ta yadda suka kwana ? Tace kai ai hajiya jiya batai barci ba ta kwana kewayawa fitasri ne harda gudawa ma tayi. Koda na shiga na samu ta dan samu barci nafito na taya gajiye aiki na koma na shirya yaran don kada su makara zuwa school. A gurguje na shirya suna ficewa nima na shirya na bar gidan zuwa nawa karatu. Na sha fada sosai a gurin course mate dina don suna ta fadin wai ni da nake serious a da can baya yanzu ina wasa da karatuna sosai kuma. Haka na dage da karatu na mayar da hankali na sosai don kada a barni baya ga karatuna sosai. Ban dawo ba sai yamma lis na shigo gidan a gajiye dani part din anty na yada zango na samay ta kwance saman three seat tana jin sallama na ta dago kai tana min sannu da dawowa na zauna ina fadin wassh tace ai dole ne. Nake fada mata sati biyun da nayi na samu an wuce ni sosai a karatuna, take cewa dole ne Rama nima sai da nai magana a kan hakan abune dai da baka da ikon kan ka amma zanyi magana da maigidan insha Allahu ya dinga sanin abinda ya kamata ayi. Take cewa dani dazun kin fita kin barni na dan samu barci wanan maganin dana sha jiya bai barni nayi barci ba sai fitsarin da nake yi. Nace dama haka mutumin mai magani yace min idan maganin ya karbi mutum zai dinga fitsare cutar dake a jikin shi. Tace jiya kan nasha bauli ba kakatawa a gareni Rama har sai da naji tsoro sosai. Amma wanan maganan da ki kayi yanzu ya sa hankalina ya kwanta sosai da jin bayanin hakan. Take cewa ni masu fitinan nan na kullun suka tayar dani daga barci na da na keyi. Cikin mamaki na juyo gareta nake tambaya nace fitina kuma akayi a gidan ne anty ? Tace akan ki ba ai kema kin san cewa da duk ku kai tafiya sai anyi fitina saboda ke a gidan nan. Nace a sanyaye ni kuma anty ? Tace ke mana Rama kin san su zasu iya saka ido akan mutum amma shi mutum bai damuwa da abin da suke ciki da miji ko yaushe. Tai tsuki tana cewa sunce idan kunyi tafiya sai ya kashe maki makuddan kudi masu yawa da baya kashewa mata shi. Tace bari Rama yau naji abin mamaki sosai a gidan nan gurin mutanen nan ashe ba karamin kudi matan nan suke karba gun mutumin nan ba haka. Yau da Allah ya kama su kinji yadda yake masu fallasa ai sai da sukayi dana sani yace daga yau idan ba gaba daya zai ba da abuba ba zai sake ba ko wace mace kudi ba komai lalurar da tazo mai dashi a gurin shi. Ajiyan zuciya na sauke nace anty zato zunubi su a ganin su gun daddy na samu wanan kudin haka nai sayayya dasu ko may ? Tace in ma a gunshi kika karba Rama ina ruwan su da hakan ne wai su udan sun fita dashi wayan san abinda sukeyi a can din. Yanzu ai ya basu amsa don yace kin mai daidai don haka yake son gani idan yabawa mace kudi yasan inda suka shiga ba gobe sai anzo tambayan shi ba alhalin bai san may ake da makudan kudi hakan ba masu yawa . Wai Rama kiji matan nan fa, da kuma namiji munafuki wai ashe har wani kudi yake basu na sayan kayan need din su da bai ba mu anan. Nace cikin mamaki kamar ya anty tace wai na sayan pad da kayan makeup ko da may ye ma don ni takaici ya hana na tsaya na saurare su ma na dawo nan abina don dashi dasu duk haushi suka bani. Tace ni dama nasan karya ne in bashi ba a ina suke samun wanan kudin da sukewa mutane karya haka dashi ? Anty kiyi hakkuri akan wanda kike dashi mai hakkuri yana tare da Allah ai da baki da amanan su ai gashi yau kowa yaji may suke ciki kuma ai sun wa kan su in sheri ne don kowa yaji may suke ciki yanzu ai. Wai ma don ya mayar dani van san ciwon kaina ba Rama sai gashi wai yazo min da maganan su nai banza dashi ya karaci zamqn shi ya ban guri don ni banga abinda zai fada min ba kuma na yarda dashi. Na mike na cewa anty bari na shiga naga mutane na nadan watsa ruwa na fito sherin su dai a kansu zai kare ai. Ina fita na shiga part dina na samu su Fatima zaune suna kallo suna ganina sukai min oyoyo da gani na. Tambayan su nake ko sunci abinci suke cewa dani sun dafa sunci don yanzu suna girki abinda suke so a waje na. Ban tsaya ba na shige dakina na shiga wanka na fito sallah aka fara na shiga yi. Ban daga daga wurin ba har sai da na idar da sallah nai shafa,i da wutiri na mike fatima na kira nace ta fitar da kayan na gani nan muka baje komai na kwashi tsaraba na da anty da sauran na yaran na shiga wurin anty da su. Tana daki anan na zube kayan falo na samay ta a cikin daki ta idar tana addua na shiga gun ta. Ta shafa take cewa har kin fito ne Rama nace eh anty dama tsaraban da na sayo ne na kawo maki ki gani idan sunyi maki. Ban da na yara har da kuma ni Rama abin ai yayi yawa dai ko nace haba anty yawa kuma fa akan ki abu zai min yawa anty ? Aiko da na zama butulu gare ki anty aduniya akwai abinda zan maki wanda zan iya rama abinda ki kai min a duniyan nan ? Kai haba dai ki daina saka wanan a ran ki mana, Rama ai hakan hukuncin Allah ne ba yina bane. Ni fata na yanzu shine Allah yabaki naki rabon a gidan nan nima naga jinin ki a cikin gidan nan kamar kowa. A cikin raina na karba mata da amin amma a fili murmushi kawai nai mata nace kai haba anty muje kiga kayan a falo kada mu bata maki guri nan. Tana fitowa taga kayan take cewa kai kai kai Rama wanan kayan haka duk a lagos kika samo su haka waya na daga na kira Fatima nake cewa duk su kwaso sauran kayan su kawowa anty ta gani. Nai mamaki danaga tana jidan kayan kitchen din da nazo dasu sai bayan ta gama zabe tana ta yabawa da kyaun kayan haka . Take cewa kin san ina da amare har biyu shiyasa na zaba masu ba sai munje saya waje ba daga baya. Amare a ina kuma anty tace gajiye da Fatima mana Rama ai dole nice uwar amaren dai ina ce. Shiru nayi mamaki ya rufe ni na hali irin na anty ko ni da Fatima take guna banyi wanan tunanen ba haka. Amma saboda salihanci irin na anty sai gashi ta ita tayi wanan dabara ganin nayi shiru naji tana fadin Rama kin fasa abinda kaiwa wani a duniya shine rabonka a lahira walau sheran ko hairan don haka don Allah ki barni na samu wanan ladan na alheri dana sawa raina. Wanan shine kadai abinda mutum zaiyiwa wani mai bukata na kasa dashi ya tsira ga ubangijin shi. Don haka gobe zan baki kudin kayan ki sauran list din abinda nake bukata garesu kuma akan su duk kece zaki sawo Rama na saya a gurin ki wanan alkawari ne naiwa raina hakan. Shiru nayi duk imani da tausayin ta ya kamani sosai sai tunane nake wai ita wata irin mutum ce a duniyan nan cikin mata ? Bata fita ko ina tana gida anty time tana bautan Allah da auren ta haka kuma abinta ban taba ganin ya rufe mata ido ba ita a rayuwan ta. Sai naji tana ta faman yaba kyawon les din da na sayo muna tace kuma kayan yara sun matukar burge ta a rayuwan ta. Muna cikin fira sai ga maigidan ya shigo fuskan shi a daure murtuk dashi dagani har wanan lokacin ranshi a bace yake mai. Gaishe shi muke yi daya bayan daya yana amsawa kamar baya son amsawan a lokacin. Tambayan ko kayan may ye wanqn haka yayi take cewa kayan da Rama ta saro a lagos ne mana. Inda nake ya juya yana cewa ke har yaushe kika samu sayan wa yan nan kayan haka cikin mamaki ? Nake cewa dashi da muka tafi da matar Adebayo ne ta kaini na sayo su a can. Yana tafiya yake cewa kada fa ki ce zaki fara shiga Dubai wanan abin dana gani haka fa ? Dariya duk wanda ke falon yasa saboda maganan shi sai anty ke cewa aiko bataje ba sai tai oda kuma su shigo mata yanzu akwai hanyar bussines ai a cikin sauki masu yawa. Ya har falon mukaci gaba da harkokin mu sai dare na koma ni da su Fatima part dina gan kwanta ba karatu na shiga yi ina nazari saukina abinda na koyo da muka tafi chaina dashi ne akayi bana garin. Washe gari ban tsaya ba na loda kaya a mota na fice gidan Allah ya taimakeni tun a mosque da mukaje sallah nai ciniki sosai an kwashe lace din dana fito dasu ranan gaba daya har ana nema don kyaun su. Na dawo gida nagaji mukai kicibis da Zulfa yarta na wasa a haraban filin gidan ina ganin ta na ja burki sai da aka dauke yarinyar na karasa inda nake aje mota na. Na fito ganin Zulfa duk da nine na fito unguwa ya kamata tai min sannu da zuwa a lokacin amma na san bazan samu hakan ba a gareta na daure na gaida ita da gida. Maimakon ta amsa min sai cewa tayi amma tukin naki Rahama ya zama na ganganci zaki shigo kin san akwai yara a gidan zaki kwaso haka a guje nikan ki rufa min asiri kada ki mayar dani baya please ? Mu koma dani dake ba maishi a gidan mun zama daya ke nan a hakan don Allah ki rufa min asiri please. Mamaki ne ko takaici ya rufe ni na tsaya rugumay da takardu a hannuna ina kallon ta nace haba anty mai yai zafi haka kuma da wanan maganan haka ? Aiko da ban taba haihuwa ba nasan zafin yaron don ina da imani a zuciya ban ga dalilin da zan dauki alhakin karamar yarinya irin baby ba haka ? Daga can bayan mu naji ance damu aiko jaririya ce sai a kashe akan kishi tunda mutum na bakin ciki da diyan mutane tunda shi bai haifa ba saboda hassada. In haihuwa banza ne ai mace ta haifi nata mugani mana amma sai kai ai kokarin salwantar ma da wanda Allah ya baka kuma saboda bakin hassada. Murmushi nayi nace sai dai ku sani ni baniwa Allah garaje akan abinda ya boye da haihuwa da rashin shi duk ikone na ubangiji ni ko a hakan da nake nagodewa Allah na kuma ko yaushe ina cikin gode mai ga irin ni,imar da yai min wanda kowa bai taba zaton haka ba a gare ni. Zama mace ta hudu a wurin mijin irin daddy aiko ba hahuwa alhamdullahi don babu abinda na nema na rasa sai dai nagodewa Allah na a hakan. Tunda mijina bai taba banbatani da masu diya agidan ba kuma rasgin haihuwa ba wai ya damay shi bane don ina juya cikin ku ashe ko Alhamdullahi tunda daidai nake ga kason kowa ko ban haifa ba an haifa min kuma ina da iko yadda naso dasu. Ban tsaya jin amsan su ba na shige abina na barsu nan suna ta faman haushi kamar mahaukatan karnu ka. Zan shiga naji hindatu na fadi lalai yarinyar nan wuyan ki ya isa yanka ashe don kina ganin kamar kin kai kowa ne a gidan yanzu. Na juyo nace har akwai may wata kama na kwarai ne can na daban ana ko kuwa taron cushe inda za, a bar mutum yayi zabe ai ba mai zaben ku cikin gidan nan kuma kun san da haka sai dai ku godewa Allah abin ya zama na sadaka ne gaba daya. Na shige abina na barsu nan kamar ran su zai fita wurin jifana da bakar magana ni dai banji ba balle naji zafi suko sunji nawa dana fada masu. Don basu taba zaton nasan cewa ba shine ya nemay su da aure ba bashi su akayi ya aura a dole. Sunji matukar haushin wanan kalamin harda cewa wai a bari maigidan ya dawo ai dole ne a zauna dashi. Har dare ina jiran kira banji komai ba kuma ban ma fito hira ba fun anty don damuwan da ya kamani kan wanan yawan gorin da suke min na rashin haihuwan da banyi ba kuma ban fadawa anty abinda ya faru ba tsakanina dasu. Washe gari cikin kuka nake fadawa Zarah irin gori da habaicin da suke min idan magana ya hadani dasu. Hakkuri ta bani tace kada nasa zancen a raina don Allah bai mata da ko wani bawan shi ba sai take cewa dani na samu miyar kuka koda yaushe na zauna na shashi sosai don yana sa mace samun haihuwa idan bata haihuwa. Tun wanan ranan zan hada kuka yaji daddawa da kayan yaji na zauna na shashi sosai. Kuma ina hadawa da bissimillah kafa dari daya da goma sha uku na shafawa kasan marana. Sai kusan bayan sati daya ranan daddy ya shigo ina zaune saman sallaya muka gaisa yake cewa dani Rahama idan zaki shigo gida ki daina gudu da mota haka don gujewa kaddara. To daddy nace dashi insha Allah bazan yi godu ba har ya fara tafiya sai naji yace amma kuma nai mamaki don ban san lokacin da kika fara tukin ganganci ba haka ? Na ce cikin murmushi daddy ni bani gudu kaima ka sani ka kuma sheda hakan gare ni ai sai dai zan kara tsarewa insha Allahu. Ya ke cewa dani matar Adibayo tace a fada min kayana zuwa tuesday zasu shigo hannuna insha Allahu. Nace ai min godiya wurin ta sosai yake cewa yana gani wani sati zai wuce zuwa Bangkok akwai taron da zasuyi acan din. Nace amma ba dadewa zakayi ba ko daddy naso kafin kai tafiyan asan matsaya akan Gajiye da Fatima yace haka nake planing nima kafin dai na tafi hakan za, ayi insha Allahu don shawara ne mai kyau wanan. Kuyi hakkuri da wanan da kyat na samu na dan rubuta maku shi don har yanzu ina jin jikina wallahi nagode kwarai da kulawan ku gareni yan uwa wanda na bata ma rai ga jina shiru suyi hakkuri don Allah dani halin jiki da jine hakan nagode da fatan zaku fahince ni yan uwa. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE BA A YAFE BA , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA KEDA ALLAH YAR UWA DON ONLINE NOVEL NE, , , 58 Daddy bai bar garin ba sai da ya tabbatar da komai ya ian kama akan zancen auren Fatima da hamza gajiye da maigadin gidan shi. Har dukiyan aure sai da ya biya tare da duk wani abinda ya dace ayi a kan aure na fannin maza yabar garin. Wanan karon daddy bai tafi dako wace mace ba shi kadai yai tafiyan shi batare da ya tayawa kowa ba gashi s n sa rai cewa , Daya daga cikin su ne za, ai wanan tafiyan da ita zuwa waje don haka kowa a cikin shirin tafiya take amma sai ganin shi kawai sukayi yazo sallaman su akan zai tafi. Yakawo kudi yabawa kowa wanda zatai amfani dashi bayan kayan abincin da ya sayo muna, masu yawa ko wani part aka shiga dashi equally, Da ganin irin wanan tafiya tafiya ce mai muhinmanci a gare shi zai tafi ya dauki lokaci acan har sai ya gama shige da ficen abin da ya kaishi kasan zai dawo gida Nigeria. Gashi yanzu bakin kishi ya jawo wa kowa hasara yai tafiya shi kadai suna kallon ba wacce ya tafi da ita. Sana,a ta nake da karatu ba wasa Allah kuma ya taimake ni ina samu sosai a wanan fanni, Ba karamin haushi da takaicina matan daddy ke ji ba saboda wanan tafiya din da akayi bada su ba. Daga karshe sai ga shi ranan Saturday tunda safe sun tayar damu da fitina a tsakanin su akan fadan yar wurin hindatu wai ta dauki baby sai ta yar da ita daga hannun ta, da gangan . Allah ne ya kama su don suna tsaye suna magana a waje kan tafiyan daddy din ita hindatu ke cewa da ita wanan ai sheri ne da makirci kawai irin namaza don ya ga bada ita zai tafi ba. Suna cikin wanan gulman ne sai ihisan ta dauki baby din daga hannun uwarta tana wasa da ita daga gefe. Sai kawai ta sake ta a kasa ta fadi cikin wasa maimakon uwar tai mata magana sai tana dariya ga har bakin yarinya ya fashe tana tsala ihu ita ko zulfa taji haushi takaiwa Ihisan bugu sosai take fitina ya fara a tsakanin su don kowa bai kawar da ido ga danshi. Fada sosai suke wanda wanan halin ba abin mamaki bane a tsakanin su tonon asiri suke cikin daga murya na fito don raka yara na samay su a hakan su gajiye da sauran yan aiki na daga dayan barin suna sauraren su. Kukan da yarinyar keyi ga bakin ta da hanci najini a gurin da ta bugu yasa na kasa wucesu nace da uwar ki duba wanan yarinyar anty bakiga jini yadda yake zuba mata ba ne ? Ta mayar da kallon ta ga yarinyar jini ne sosai yake zuba da sauri na karasa gurin na bude bakin yarinyar take hankalin kowa ya tashi nace da fatima yi sauri dauko min kada a first aids box . Abin ba dadi yadda nake cusa kada a bakin yarinyar ina fitar mata da jini a cikin sa ashe harshen yarinyar ne ya hakori yai mugun datse shi yake fitar da jini. Da kyat na samu jinin ya tsaya nace maza ta kaita asibiti a duba ta zaifi don ai mata alluran T,T . Hankalin mu duk a tashe don ko ita hindatun jikin ta yayi sanyi sosai dole yarinyar na ajikina muka tafi asibiti mu uku hindatun ce take jan motan ina dafe da bakin ta don jinin bai tsaya ba har lokacin. Ba karamin ciwo taji ba ni da kaina nai treating din yarinyar yarda ya dace muka dawo gida. Nikan muna fita mota nai masu Allah ya tsare gaba na shige hanyar part din mu. Na samu anty na falo zaune tace dani har kun dawo Rama yanzu dana fito Gajiye ke fada min abinda ya faru ai. Rama sai nake ganin kin fini saukin kai a wani fannin har yaushe suka gama maki kazafi akan yarinyar nan don kawai su bata ki ga maigidan Allah ya kare kawai bai dauki zancen su ba. Nace ina zama wanan kuma don kan su ai yarinyar taban tausayi ga yarinya a wani hali amma don hauka wai fada sukeyi su. Ai idan kan yara ne su basu kunyar hakan gare su, shiyasa nake jin dadin yadda ki kaiwa yaran nan training ba ruwan su da shiga wurin kowa yanzu balle su dauko min magana ina fama da kaina. Anty idan kasan halin mutum sai kaci maganin zama dashi ai ba sai sun gansu ba balle suce ga abinda sukai masu kuma. Ashe maganan bai kare ba zuwa rana ni dai ina barci sai jin hayaniya nayi ashe yan uwan Zulfa ne suka shigo gidan. Fada sosai akayi tsakanin su da Hindatu ranan inda suke cewa sun fahinci dai so Hindatu takeyi ta kashe yar zulfa din tun tana ciki. Sai ita ma hindatun ta buga waya ba a dauki lokaci ba sai ga nata yan uwan sunzo take gida ya koma kamar gidan wasu yan tasha can . Ban tsaya ba na ja yara har gajiye uwar son jin kwam muka shige na rufo kofan mu muka bar su can suna ta fitina tsakanin su. Ban san waya buga mai waya ba sai gashi ya kira waya a cikin fada yake magana da anty naji tana fadin ni may kake son nayi a kai tunda ba saurare na zasuyi ba. Hajiyan daddy ashe sun shigo gidan ita da mama laraba da sauran yan uwa fitina sosai akayi ranan. Hajiya tazo har kofan mu da kanta zan iya cewa tun shigowa na gidan da sunan aure yaune zuwan ta na biyu gidan tun haihuwar yarinyar da tazo barka sai yau ina ganin kuma maigidan ne ya sa su zuwa gidan. Jin itace ke buga kofa yasa muka fito amma nai warning din yaran da kada wanda ya fito waje daga cikin su. Nan muka shiga gaidasu ina duke a bayan anty muka gaidasu a cikin ladabi anty tace hajiya ashe kin shigo gidan. Tace yo ba dole ba yar nan tunda na fahinci so suke su kashe min da da ran shi ni kuma ba yarda zanyi ba da hakan. Yaro yana tsaye yana nema maku abin rufin asiri amma ku kullun kuna gida sai bakin fitina ba karewa a kan ku ne faraun din zaman kishi ko may ? Hajiya sai hakkuri don ko nai magana ba jina suke ba yanzu Rama ce ma ta kaisu asibiti don ba ko ta kan yarinyar da taji ciwo sukeyi ba don hauka. To kiji fa inji mama Laraba tace ina shekaran jiyan nan ita wanan mara hankali ta hau ta da fitina wai zata taka mata ya da mota kuma da aka bincika ashe zancen ba haka yake ba ma sheri ne kawai irin na kishin hauka. Hajiyan daddy tace bakinji ba nifa Laraba halin yaran ya isheni ace gida kullun cikin matsala kamar akan su aka fara zama da mata hudu a gida. Mama Laraba tace ga kwanaki wai gorin haihuwa ma su kaiwa wanan yarinyar amma yau ki duba itace ta taimaka aka kai yar nan asibiti kuma. Hajiyan daddy tace wanan kishin nasu ai son kaine baka taba jin matsala ya faru ka samay su da gaskiya. Ita wanan ta tashi a gidan su uwarta ce kawai mata a gidan ubanta shi yasa take da gurin fanin sai ta watsa kowa a gidan ta zauna daga ita sai yarta kawai. Mama laraba tace yanzu ashe kin gane abinda na dade ina fahintar dake akan wanan yarinyar duk wani makirci a gidan nan itace mai kulla shi. Ita ko wanan shashan bata da wayo sai ta hau ta zauna bayan tasan cewa ba don Allah take zama da ita ba. Hajiyan daddy tace ni gaba dayan su duk wace ba zata bawa yarona kwanciyan hankali ba a rayuwan shi ashirye nake da ya sallamay ta nagaji da goyawa karya baya haka. Duk wacce bata iya zama da kishi hanya a bude yake gare ta ba zan yarda su tsiyata min yaro ina ji ina gani ba haka. Yanzu ki duba a baya ina jin hauahin wanan yarinyar Saade akan gaskitan ta Zaliha ta hana na fahinci komai a gidan nan don son kai irin nata da yarta ke yar naki da ko wayau bata dashi. Da zulfa na da wayau yau gidan nan wa yakaita kusanci da yaron nan amma wai da ita ake hada baki a cutawa dan uwanta jifa wanan maganan yau babu dadin sauraro ko kadan. Daga inda anty take tace ayi hakkuri hajiya anyi kuskure sai dai a gyara kawai. Cikin bacin rai hajiyan tace idan ma bazasu gyara ba kowa ta fice ta bar mi yarona nagaji da fitan su haka wallahi. Duk wanan maganan da ake tsaye suke daga kofan shiga part din anty sukeyin shi don basu shiga daga ciki ba. Sukai muna sallama suka tafi muka rako su har gurin motan su sai faman fada hajiyan daddy keyi tace don hauka kowa ta kwaso yan uwanta a cika gida kamar gidan danbe kuna zubawa mutane shakiyanci haka yaro nacan gurin nema maku abin rufin asiri sam bazan lamunci wanan halin ba a gidan nan. Mu dai muna tsaye ni dai ban tanka su ba har suka fice hakan ma masu fitan sai da hajiya taga ba kowa a gidan suka ja motar su suka tafi. ********* ********* ********* Tun wanan lokacin na kula da kowa a gidan sha,anin gaban shi yake yi ba mai yi da dan uwa a tsakani wanda nasan na kwana biyu ne kawai mai hali baya fasa halin shi ai. Na dawo school agajiye na shigo gidan na zauna gun anty muna dan hira take cewa dani gaskiya Rama nikan wai yaya za, ayi na samu wanan maganin da kika kawo min na dada sha. Don naji dadin shi kwarai wallahi kin ga na daina jin wanan yawan taunan jikin da sauran su gashi yanzu har nai barcina normal har safe. Nace masha Allahu dama haka ake so kasha magani da zuciya daya batare da ka tsaya kwankwanto a kan sa ba. Nace niko kinga da shakku ma nakawo maki shi wallahi don ban zaci cewa zaki sha ba anty yadda mutumin ya dinga gidada maganin shi yasa na sayo shi gashi kuma da kudi kalilan akan dubu biyu na karbo shi fa. Tace kaji ikon Allah ba ni kan ai yadda zan samay shi yanzu naci gaba da shan shi don yai min dadi sosai wallahi. Waya na ne yai kuka na ciro shi daga hand bag dina da sauri ina kokarin duba wanda ke kirana a lokacin nan. Daddy ne na gaida shi a cikin mutunci tankar yana a gurin ne tare da mu yake tambayana kina gida ne Rama na amsa mai da eh daddy. Yace don Allah kije part din Zulfa ki duba min yarinyar nan bata da lafiya wai inji uwar, don na fadawa doctor yace ai maki magana zaki fahinci komai akai. Ina sauraren shi jikina yai sanyi na dai amsa mai da tau a sanyaye na kashe wayan. Anty ce ke tambaya na may nene ya faru kuma don ganin yanayi na a sanyayye. Nace da ita wai baby ce bata da lafiya naje na duba ta a part din su yanzu doctor yace na duba naga may ke damun ta. Tace to ai sai ki tashi ki tafi tunda yai maki magana kada kiyi laifi kuma gurin shi. Daga part din anty na wuce zuwa wurin yarinyar dan na dubata na gani na shiga part din gabana yana faduwa don yaushe rabo dana shiga gurin su. Sallama na biyu kamar babu kowa a part din sai can dana sake wani sallama naji yar aikin ta ta amsa min. Ta karaso muka gaisa da ita takewa dani lafiya dai ko tambayan ya dan sosa min rai amma na dake ina cewa ina babby din da bata da lafiya din. Tace tana ciki bari na fada masu ta shige ta barni nan a tsaye ta jima bata fito ba daga ciki can sai gata tana cewa dani wai ki jira tana tafe yanzu . Na kusa kai minti talatin ina tsaye a inda nake sai ga ta tafito da yarinyar a kafadar ta tana faman wani ya tsunar fuska dagani dole ne ta fito din. Nace da ita ashe baby ba lafiya kuma haka tace eh gata doctor yace wai na kiraki ban san ko zaki fahinta ba ma yadda take din nan. Murmushi nayi na karasa zuwa inda taja ta zauna saman kujeran dake kusa da kofan fitowan ta dakin. Nakai hannuna a saman jikin yarinyar najishi radau ya gashe mata sosai nace subbahanallahi ai fever yai mata yawa na duba bakin ta da idon ta gabana ya fadi. Miko min ita nan nagani kamar ba zata bani yarinyar ba na dai karbe ta na fara cire mata rigan dake a jikinta a hankali. Take cewa zafin jikin dashi ta kwana haka na bata magani bai sasauta mata ba har yanzu. Nace miki min towel da ruwan sanyi wani kallo ta watso min tace may za, ayi dashi kuma nace cikin daurewa zan goge mata jikin ne ta dan samu relief. Tace a yadda take din nan kuma a daba mata ruwan sanyi a jikin ta nace shine saukin ta a yanzu ai. A, a gaskiya ki barshi ba zan yarda ba a zuba mata ruwa masu sanyi a jiki yadda take din nan a haka ? Aiki baka haifa ba ka tausayawa wanda ya haifa tunda ba a jeji na dauki ta ba ko a jejin ne ma sai da nasha wahalan zuwa ai dauko ta din. Allah ya baki hakkuri nace da ita tare da fadin baby Allah ya baki lafiya ko, na juya na bar part din don yamma yayi sosai lokacin. Ban nufi gurin anty ba na shige wurina na samu ta kawo min kayana da na bari a gurin ta da zan tafi duba yarinyar. Nai wanka da dauro alwala na nufi sallah din lokaci yayi na magariba ina zaune ina lazumi naji an shigo min daki kai tsaye na juyo ina kallon su. Rahama wai kizo jikin baby ya rikice ki gani nace Allah sarki a kaita asibiti don ni ban taba haihuwa ba ban san zafin yaro ba kuma ba aikin na sani ba. Don ma kada a damay ni na jawo wayana na kashe tare da cewa Fatima ta rufo min kofan falona da key. Kallo na take cikin mamaki don tasan lokacin rufewa bai yi ba amma babu yadda zatayi dole ta rufo kofan don ba fuskan tambayana. Yarinya ta mike kamar ta mutu uwar ta sa hannu ga kai tana faman kurma ihu duk gidan ya rude ta kwaso yar rabe rabe zuwa waje. An kira shi ya na neman layina amma wayana a kashe yake bai samay ni ba ya kira anty a rikice yana tambayan ina inane wai bai samay ni ba tace dashi ina ciki yace ta dubani baby jikin ta ya rikice mata sosai sun kirashi suna kuka. Da kanta tafita ta duba yarinyar taga yanayin da take ciki da sauri ta juta zuwa inda nake gashi wai motar uwar ba lafiya ya kwana biyu a ajiye. Part dina ta nufa hankali a tashe tagan shi a rufe tashiga buga kofan dakin sai bayan dan wani lokaci na fito da kaina ina tambayan ko waye ? Jin muryan anty yasa na bude kofan cikin tashin hankali take cewa kizo Rama baby ba lafiya nace anty Allah ya sauwaka amma ba zan tafi ba gaskiya. Cikin mamaki tace saboda may Rama nace don ban taba haihuwa ba kuma ban san zafin da ba ko inda ake dauko shi kuma ban san may nake karantawa ba ni. Ikon Allah yanzu dai don Allah Rama yi hakkuri zo ki duba yarinyar nan don dare yayi ko sosai. Ban ki ta nata ba nabi bayan ta muka tafi daga ni sai dan rigan barcin dake a jikina sai ihu da kuka muka samu sunayi sosai nace wa yar aikin ta dauko min spoon da sauri daga ciki ta juya da gudu ta dauko karban yarinyar nayi na fara bata taimakon gagawa daya dace ai mata nace debo min manja ta kawo min na bude bakin ta na dan dura mata sai ta kara mikewa ta sake wani irin zawo mai wari ta mike da kyat na samu ta sake hakoranta daya cije guri daya da farko. Wani irin ajiyan zuciya ta sauke a hankali nace a miko min ruwa ta miko min na shafa mata a babban yatsan kafatan ta sai ta sake ajiyan zuciya tasaka kuka cikin ban tausayi. Nace da uwar akaita wurin likita ya dubata zaifi ina fadan haka namike ina fadin Allah ya sauwaka ya bata lafiya na wuce abina ban tsaya ba. Duk suka bini da kallon mamaki cikin damuwa dan suna son suyi magana amma naki tsayawa gurin. Cikin kuka Zulfa ke fadin Rahama don Allah zoki duba min ita don nayi kiran doctor mamud yaki zuwa tun dazu nake kiran shi yana cewa na nemay ki. Ban tsaya ba na shige abina wurin anty na fada saman kujera tare da lumshe idanuwa na ina mai jin takaici a raina. An dan jima kadan sai ga anty ta shigo part din tana girgiza kai take cewa kai wanan yarinyar najin jiki wallahi. Allah ya sauwaka nace daga inda nake kwance take cewa wai wayan ki a kashe yake ne halan Rama yanzu daddy ku ya kirani wai bai samay ki ba. Nace na kashe wayan ne anty bana son ya kira ni nan na fada mata abinda ya faru tsakanina da Zulfa tace dani basu da wayau wallahi. Wai gorin cikin nan da suke maki kece zaki bawa kanki komay ? Jahilci fa na cin wa yan nan matan kan bakin kishi mutum ya dinga yiwa Allah izgili hakan yanzu gashi in ba fahintan abinda ke faruwa yayi ba ran shi a hasale yake yana ganin kinki duba mai yar ne shi. Nace anty baki ga irin wullakancin da matar nan tai min ba dana shiga part din ta duba yarinyar almost to thirty mins ina tsaye ina jiran fitowar ta na duba yar nata fa. Ban ci gaba ba sai gashi ya kira anty ga waya yana fadin wai ina, ina ne haka take fada mai gani zaune tare da ita yace taban waya din. Na karba ban ko gaidashi ba ya fara fada inda yake shiga banan yake fita ba harda fadin don ban san zafin yar ba ne yasa zan yi mashi haka yasan maganina ai tunda karatun da ya barni ina yi baiga amfanin shi ba tun yanzu. Raina ya baci ina sauraren shi anty ce ta karbi wayan a hannuna tana fadin haba besty ka kwantar da hankalinka mana ka fahinci maganan. Yace wani fahinta zanyi har zance mata ga abinda nake so ta tsaya tanawa mutane wullakancin banza haka. Bafa wullakanci Rama tayi ba besty uwar yar ne ta nuna bata yarda Rama ta duba mata yarta ba sai dai wani ya dubata can daban. Kamar ya bata yarda ba bayan munyi magana yanzu take cewa surport kawai taba yarinyar tabar gurin ya kuke son tayi da yar data bar mata. Shiru tayi tana sauraren shi don tasan ya hau baya jin komai a lokacin sai ganin laifina kawai yakeyi. Karshe ma kashe wayan shi yayi ya barta da waya a hannun ta tana bin wayan da kallon mamaki don yaki ya fahinta ga maganan. Tace kyale ta da yar ta duk abinda zata fada mai ita ta dade ban dade a zaune ba na bar part din zuwa nawa cike da bacin rai. Tun cikin dare yan uwanta suka shigo suka kwashe su zuwa asibiti na sha zagi a gun su sai cewa suke ban ki yarinyar ta mutu ba ai don nima banda shi mu zama daya ke nan. Ni dai ban kula su ba ban kuma je asibitin ba wanan karon na share su gaba daya haka shima bai kara kira na ba tun wanan lokacin nima haka ban kirashi ba. Kwanan yarinyar biyu aka sallamo su uwar ta dauki gaba dani itama hindatu ba dadi a tsakanin su. Ina karatuna ina hadawa da business dina ban tsaya bin ta kan su ba ban ma da lokacin fitinan su a raina. Abinda dai na sani shine idan ya dawo a hake yake dani a ranshi tunda ya riga ya hau bai jin has ko kadan. Ayi hakkuri da wanan har na danji sauki baida yawa kadan na samu nayi tun jiya nake typing ban iya yi da yawa ba don yanayin jikina. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , , , 59 IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH KAN CIN AMANA DON ONLINE NOVEL NE KIN SANI, , , Wanan yawan gorin da matan daddu suke min ya fara damun rayuwana sosai har na fara tunane a kan shi. Yau ma bayan mun fito da lectures bani sallah don haka na zauna daga wajen massalaci ina jiran fitowan Zarah ban san yadda akayi na zirfaffa ga tunane ba har ta iso girin tana magana dani amma banji ba. Dafa ni tayi tana fadin Rahama may kike tunane ne haka har ina magana bakiji ni ba. Murmushi mai kama da yake nayi mata tare da sauke ajiyan zuciya ina fadin kin fito zarah Allah ya karba. Tace wai tunanen may kike haka ne Rahama kada fa kijawa kanki wani matsala a rayuwan ki. Na sake sauke ajiyan zuciya nace Zarah ni na shiga uku yaushe zan fita a cikin fitinan matan nan na daddy ne wai. Rahama in sun fito min nan sunga Allah ya ketare ni gobe ma wani hanyan ne zasu bullo min dashi. Will you believe cewa yanzun kuma kokari suke su shiga tsakani na da anty ta hanyar yara duk da nasan cewa anty ba dauka zatayi ba amma kuma yau da gobe bai bar komai ba. Gashi sai faman gori suke min wai ni hankaka maida dan wani naki a haka zan kare wurin bautan diyan kishiya, dama kuma don shi aka dauko ni gidan. Kai wanan akwai shegun duniya wallahi so suke by all meas sai sun shiga tsakanin ki da anty Saade. Ina ruwan su da abinda kikewa yaranta ne sunga sun buga ta ko ina baku rabu ba shine suka biyu maku ta hanyar yara su na zuga ko waccen ku akan dole sai sunga wallen ku a tsakanin ku. Kinga wallahi ki bar damuwa da maganganun su Rahama kici gaba da duban yaran tunda duk zugin da suke wa uwar bata taba dauka ba. Haka kema gazawan ki akan su daidai da rana daya wani bada gurbi ne a tsakanin ku. Ki duba fa yadda yaran sukai mugun shakuwa da ke yadda ko uwar da ta haifesu basu shaku da su haka na ba. Don haka wallahi Rahama kada ki yarda shedan ya rude ki ki zafe ki kara jan yaran ajiki suji haushi in sun yi fushi su mutu mana mugani munafukan banza da wufi kawai. Sannan da suke maki gorin haihuwa baki san ranan da Allah ya baki cikin kuma bakin cikin haka zasuyi ki ce na fada maki wataran. Sai kuma idan kin haihu sabon fitina zai fara tun dai idan Allah fara baki da namiiji a gidan zaki ga sai sun fi haka tsanar ki tunda halin su ne hassada. Ke akasarin mata irin haukan da suke ke nan sai su manta da cewa Allah ne mai bayarwa a inda yaso don gani suke kamar da namiji yafi diya mace don hahilci ke har fa gidajen tallakawa da basu da komai suna da wanan bakin kishin tsiyan a rayuwan su. Nisawa nayi nace kai Allah ya kyauta kawai ni wallahi suna ma son rudani yanzu duk gidan ya fice min a rai gaba daya wallahi. Tace ke shifa kishi dama abinda ya kumsa ke nan kima kishiya tai maki itama shine kishin kawai ba komai ba sai dau na wata yafi na wata zafine kawai, amma kishi duk bata son taga kishiya ta fita da gashi ta ko ina. Mun dauki lokaci sosai da ita muna hira daga karshe mukai sallama kowa ya kama gaban shi. Tafe nake sai dai still ina tunanen dan matsalan da muka samu da anty na da safe akan yara, don Nasir yace ba zaici abincin da akka dafa mai ba ya ishe shi shine nace zan dafa mai wani yaje dashi. Sai taimin abinda bata taba min ba akan yaran dan ta rufe idon ta dani da yaron tai muna tas don har cewa tayi aii wanan hanyan lalata yaro ne na dauko ba yau ba tana lura abinda nake wa yaran bai mata dadi a ranta. Nasan ba komai yasa yanzu take min hakan ba sai don maganan da ya dan hada ne da hindatu har take fadin wai ta fahince ni ba son yaran nakeyi ba tunda kowa ya sani tarbiyan lalacewa nakewa yaran anty don su girma su lalace shine na fake da wai ni ina kula mata dasu. Ko da na shigo kamar na shige part dina sai naga rashin dacewan haka koba komai bai kamata na biye mata na manta da halarcin da tai min ba a duniya. Ina shiga na samu tana waya tana fadin aini yanzu kaina ya kawo wuta wallahi wani abin sam bai dace da yaro ba amma sai ace wai abar yaro yayi shi. Hade bacin raina nayi nai sallama don kada taci gaba da magana har naji abin da zai kara bata min rai. Ta dago ta kalleni a lalace ta amsa min nace anty ya gida ta ce lafiya kawai batare da ta tambayeni ya school ba kamar yadda ta saba tambayana a kullun. Ban zauna ba don waya take saurare na fice zuwa nawa bangaren inda na samu Fatima don Atika ta fara zuwa school yanzu. Ina ficewa wace suke wayan tace munafukar ce ta dawo naji ana gaida ke, tace itace mana nima ji nake wallahi kamar na fita batun yarinyar nan don shegen wayon tsiya ne da ita. Gata dai karamar yarinya tashin kauye amma bakin wayo ke ga yarinyar nan in fada maki . Yanzu fa ki duba dukkan mu babu mai wata sana,a agidan nan amma ita wallahi business takeyi sosai ba kama hannun yaro don bata raina sana,a ko kadan . Matar tace bakinji ba ni narasa wai ina wayyon ki ya shiga Saade mutum ya dauki yuka ya dabawa cikin shi don wani dalilin naki can na banza. Ai da kike son haka da ki bari idan zaki mutum sai kibar wasiya cewa idan kin mutu kin yarda ta auri mijin ki, amma in bashi ba yaushe zaki dauko yarinya tsaleliya haka kamar tsada ki aurawa mijin ki ki koma kina kallon taikaici da ranki da lafiyan ki. Tace bari ke dai Nuriya ni sai yanzu danaga abin madon wuce tunane na abin ya ke ci min tuwo a kwarya. Gashi in fada maki kamar auren sadaka yallah don ta kwaso yan uwa ta cika gida dasu tana batun cin nawa yan gida su. Nan dai sukai ta maganan su da matar tana kara sakata hanyar shedan ita kuma tana hawa ta zauna a kai. Kwana biyu sam ba dadi a gidan tsakani na da Anty don ta canza min fuska sosai bata sake min ko kadan . Ban yarda na biye mata ba haka na nake daurewa ina mata magana tana basar dani cikin rashin kulawa. Gajiye ne matake fada min ranan na dawo take cewa wai Rama may ke faruwa ne tsakanin ki da uwar dakin mu ne kwanan nan. Naga ko abincin da take cewa na aje maki ta daina sai ma ta tambaye ni kada na sake na saka maki wai kowa an bashi abinci ki dafa naku idan kuna so. Murmurshi kawai nayi nace gajiye ba komai shedan ne da shedanu ke son shiga tsakanin mu amma ni ba zan yarda ba don ni ba butulu bace. Zata ci gaba nace da ita tabar zancen don anty ta fita bata sallami kowa ba don ta fara fita yanzu. Saboda gaskiya Alhamdullahi maganin nan da na sayo mata na gargajiya ya matukar karbuwan ta sosai ta daina yawan takura yanzu akan ciwo kamar baya. Ko yaran nason suzo guna kiri kiri wani lokaci zata hana su zuwa ko ina masu magana sai naga suna kallon idon ta da alama dai an masu wani warning akaina ne. ********* ********* ********* Wanan halin ya kai min ko ina, tun ina mamakin jayewan anty gare ni har nazo na daina mukaci gaba da tafiya a hakana sai dai ban yarda ya kaimu ga yadda wani zai fahince mu ba sai mutum ya kula sosai zai gane akwai matsala a tsakanin mu da ita. Muna cikin wanan halin daddy ya dawo ya samay mu a hakan da ita a tare muka saba zuwa taron shi sai ga shi wanan karon mun zo daban daban ba a tare yadda muka saba ba din. Bai kawo komai ba sai da dare bayan ya huta ya kira mu yaji wacce zatai girgi a ranan daga cikin mu. Tace amma dai kasan ka share kusan wata biyar ba a gida ba don haka sai mu koma fresh daga yau yace to shikenan babu damuwa. Na riga kowa ficewa a falon don ban tsaya ba tana gama magana ta sai na mike na barsu. Washegari Ina kwance dakina da safe ya shigo dakin don bamu zuwa school ranan karatu nake ban ji shigowan shi ba sai da ya dan ja min kafa na dago na ganshi sai nai yunkurin mikewa zaune ya dakatar dani ta hanyar mayar dani da hannayen shi yai min rufa dashi tare da kura min idanuwan shi cikin nawa. Ba zan jure ido hudu dashi haka ba sai na kawar da idanuwa kasan yace see you kin gama fushin da kikeyi ne ko har yanzu. Nace haba akan may zanyi fushi dakai daddy yace yaushe rabon ki daki bugo min waya in ba fushi kike dani ba ya tambaya. Daddy bani fushi dakai kaine dai baka fahince ni ba kawai amma ni ban fishi da wanda nake a karkashin shi ai. Yace ko fa ta anty ki na bugo sai tace min bakya nan ko baki kusa da ita shiyasa na san kin dau fushi dani. Wani iri naji don daidai da rana daya anty bata taba fada min komai ba akan daddy na cewa a bani wayan shi. Yace to may ke damun ki haka naga duk kin wani fadawa kin ramay kin yi duhu dake ? Murmushi na kakaro nace ba komai daddy kila don ka dade baka ganni bane kawai. Ya mike yana Yana cewa OK ban san ki ba ke nan sai wanan time din ko ? Nace an dawo lafiya yaya gajiyan hanya yace bazan karba ba jiya may yasa ana magana kika fito kika bar mu a falon. Nace ba komai naga dai an gama magana ne yasa nabar wuein don ina da test shiyasa ban tsaya ba yace anyway yadda kika ce shi ke nan amma sai naga kamar ke baki missing dina ba dai. Nace haba daddy baka iya ka gane ai abin siri ne banice dakai ba jiyan da ka gane hakan ai glad yace ya fara tafiya yana fadin zan shiga wurin Alhaji nagan su sai na dawo ke nan. Ashe tare da anty suka fice bata sallamay mu ba sai da nashigo wurinta gajiye ke fada min ai sun fita da maigidan nace Allah sarki kawai. Ban zauna ba nakoma part dina dama na dan zagayo tane kawai kada kuma ta fasaara ni da wata manufar ta kishi nake da ita. Can gidan da sukaje Alhaji yake fada masu ai nakan shigo wani bi idan na tafi makaranta na dan duba su. Yace wanan yarinyar akwaita da kirki sosai kudai ta hakkuri don ba ai zaben tumun dare ba gaskiya don akwai tarbiya da ita. Can ma gidan mahaifin anty ya fada masu cewa na kanzo dubashi har cake na kawo mai wani lokaci. Hakan baiwa anty dadi ba a ranta saida suka fito suna tafiya ta nisa tace kai mutum sai ka barshi inda ka gan shi kawai. Yace may akayi kuma yanzu kike wanan magana kamar an maki wani abu can ? Tace daidai da rana daya Rama bata taba fada min cewa tana zuwa wurin Abba ba sai yanzu da suka fadi naji. Yai murmushi yana tuki yace to yanzu may ye a cikin hakan don ta zo gaida mahaifinki shine wani abin kuma ? Tace wanan ai munafunci ne besty don may da zatazo bata fada min ba koda ta dawo ta fada min taje din. Yace haba besty yanzu may ye kuma laifin wanan yarinyar anan don kawai taje gaida tsufin nan akan dalilin wa tayi ba naki ba ko don wa tasan su ba kan ki ba kibar irin wanan maganan please don ba girman ki hane hakan. In ba tsaban munafunci ba don may zata bata fada min ba anyi magana ga gaskiya zahirinta kuma kace kada a fada aini yanzi na gane mutum kabarshi kawai inda ka ganshi wallahi. Kakai shi yace shi rana zai kai ka kanaji kana gani yace Rahaman ne kuma munafukar ki yau besty ? Ai kai bazaka bari a fadi ba tunda kaga abinda ke maka ni sai ma ince wai kodai tun farko kana son Rama ne da gaske wai ? Mirmushi yayi yace yanzu aiko may ye ma aikin gama ya gama don kaki akeji abin kunyane aji wanan maganan kuma a bakin ki keda kikai ruwa kikai tsaki wurin hada halakata da ita. Gareka yake abin kunya ni yanzu na fahinci komai ko an daina shana ina barci. Yace ai naga alama kan tunda sauki ya samu yanzu sai a tsiro wani halin sabo daba a sanki dashi ba. Sun dawo gida ranta a bace ta fice daga motar shi dai yabi bayanta da kallon mamaki kawai don ta bashi mamaki sosai ta canza a lokaci daya. Dan tsakanin jiya zuwa yau yaga canji sosai a gare ta wanda bai santa da wanan halin ba a baya. Sun dan jima da dawowa na shiga part din da fara,a na a fuska nake cewa ashe kin dawo anty yadda tabani amsa sai banji dadin hakan ba don cewa tayi eh mun dawo yaya akayi. Na daure nace babu komai dama na shigo dazun gajiye tace min bakya nan kin fita tace eh naje gaida Abba nane. Cikin washe baki nace Allah sarki yana lafiya da mutanen gidan tace lafiya suke ina zama sai naga ta saka wayan ta a handbag din ta dake aje a gefe daya tana fadin ni zan shiga ciku na huta nagaji. Nan ta wuce ta barni zaune na dan dauki lokaci na mike na bar part din don ko yaran basu nan a lokacin. Na wuce ina mamakin wanan dabiar da anty ta kirkiro a tsakanin mu wanda ni ainihi ban san takamaimai abinda nayi mata ba yakawo hakan garemu. Haka dai ake zubawa tsakanina da ita har na karbi girki nai komai a part dina don babu fuska ko kadan a wurin antyna. Na gyara komai neat a part din nai abinci lafiyayye na fitar da sabon kula don ban dauki na ta ba. Yana zaune na caba kwalliya na shiga falon na samay shi ya saka jallabiya mai guntun hannun don yanayin zafin da ake ciki a kasan duk da bamu da matsalan haka sosai don akwai AC ko yaushe a gare mu. Na jera abincin yadda ya dace na dawo inda yake na tsuguna inacewa barka da dawo wa daddy ya kuma gajiyan tafiyan ? Yai dan murmushi ya dago yace tafiya kan ai sai dai wani kuma wanan kan ai anyi angama shi ko. Allah ya taimaka nace dashi, tare da gyara zamana ina cewa ga abinci nan na kawo yace sannu da aiki. Bai jima ba ya sauka ya fara cin abincin a hankali sai ga Zulfa da yar ta ta gaidashi bata tsaya ba kodon ina wurin ne tafice abinta. Anty ce ta shigo tana saye da dogon riga baka a jinkin ta zan iya cewa tun gaisawan safe da mukayi sai yanzu na saka ta a idona don tana dakin ta bata fito ba. Gaida shi tayi ya amsa mata da fara, a yake cewa da ita yaran basu dawo bane banga yau sun biyo uwar su ba gaishe ni ? Tace suna can suna assegment ne kasan ai yaro abinda ka saba mai dashi yake amfani yau bata jin zuwa dasu ne kada su bata mata show killa. Nace a,a ba haka na bane anty na shiga sukace min kince kada su fita ko ina shiyasa banzo dasu ba ai. Eh nina ce su zauna ban son kiriniya kuma dai hakan ra,ayina ne kawai shiyasa nai warning din su da hakan. Ta mike tana cewa dashi a huta gajiya tafice abinta nace sai da safe anty tace Allah tashe mu tafice kawai. Tunda ya dukar da kanshi yana cin abinci bai daga ba kuma bai min magana ba nima dai shiru nayi duk abin duniya ya damay ni. Ya gama na kwashe kayan koda na koma sai naga har anty ta rufe kofan part din ta ko sai kofan baya da zaka fita zuwa ta bayan gida da yake ta kofan part dina ne a bude na jawo kofan na rufe tare da mashi key don ba haka muka saba ba a part din. Na shiga nagama shirina nafito nace Fatima ta tashi su rufe kofa kada kuma ta bude don kowa ya rufe tace yau harda su anty sun shige ne ? Nace eh na samu ta shige ko har sun rufe kodana shigo tace amma dai anty wanan matan kwanakin nan tana da wata manufa dake fa ? Mumushi nayi kawai nace da ita yanayi ne kawai kin san akwai lokacin da mutum yakan ji ba dadi da kowa. Tace kai haba dai anty a yadda aka san ku gaskiya dai yanzu akwai wata a kasa dai kawai ni shiyasa ma yanzu na daina zuwa don ko gaida ita naje yi baki yadda take karba min bane wallahi. Koma dai may ye Fatima Allah ya sauwaka kawai don ba abinda yafi karfin ubangiji ai. Nai mata sai da safe ta rufo kofan ni kuma na shige wurin maigidan na samu har ya shige ko na rufo nabi bayan shi. Na samu har yayi wanka dama na hada mai ruwan wanka dana shigo yafito ya shirya ina zaune a bakin gado nayi tagumi da hannu daya. Rama naji yace na amsa da na,am daddy yace may ke faruwa ne wai tsakanin ki da anty ki ne ? Na dago kaina da idanuwa na da suka ciko da hawaye nace daddy wallahi babu komai nima ban san may ke faruwa ba haka dai kawai na wayi gari naga canjin yanayi tsakanina da ita na karasa ina fadin yanzu har yaran ma anty ta hana su mamay ni. Yace kin tabbatar da cewa iyakar abinda kika sani ke nan tsakanin ku nace wallahi Allah daddy ban san naiwa anty wani abuba a iya sani na. Matar da nake dauka a duniya banda wanda yafi min ita in ba iyayyena ba da suka duka suka haife ni akan may zan yarda na saba mata bayan irin halarcin da tai min a rayuwana. Yace yayi kyau to ki kwantar da hankalin ki indai kin sa ba wani abu kikai mata ba wanda yakawo sabani haka a tsakanin ku. Don ina mai jin kunya ace yau wani ya fahinci akwai baraka irin haka a tsakan ku sai ai maku dariya ai. Iyakar gaskiyan ke nan na fada ma yace zanyi bincike nagano gaskiya amma idan kece baki da gaskiya kada kiji mamaki don zan saba maki don ni bani son karami yana raina babba gaskiya. Nace dashi nagode daga haka ya jawoni zuwa jikin shi dama a shirye nake da in tare shi don nasha gyara tun daga jikina har kasa na. Aiko na san ya yaba don gyaran ya tsuma shi fiye da tsanmani na don kamar ya zautu ya nuna min kamar ba gobe duk ya haukace min sai sambatu yake faman sakewa. Ni dai tunda yace dani na bar zancen a hannun shi ban kara kulawa ba ina dai binta sauda kafa ita kuma tana faman share ni haka na muke tafiyan mu. Hanani hurda da yaran nata da batason ina yi bai sa na fita batun yaran ba ina da hurda dasu sai dai a cikin taka tsantsan nake komai don mun riga da mun saba dasu ko Allah ne ya hadani dasu ta sanadin su. Ranan daddy yana shigowa ya hangeta tsaye da kawar ta tayo mata rakiya tun daga nisa ya sheda ko wacece ita. Mamaki yake may yakawo ta gida shi bayan tsawon wanan dadewan don yasa zaman su da anty ba alheri bane don ba mutumiyar arziki bace ita. Har ya fito mota matar tana faman washe baki data gan shi yana fitowa baibi ta kan su ba sai anty ke cewa Falmata na gaishe ka fa besty. Ya juyo fuska a murtuke yana cewa waye hakana sai matar take cewa baka shedeni bane Yusuf naga kamar baka gane ni ba kuma. Yace fuska babu walwala na gane ki mana ba Falmata Bukar nane dana sani a baya tace nice mana naga kamar baka shedani ba dai ne ? Yace na shedaki ai daga haka bai tsaya ba ya wuce zuwa part din shi bai tsaya ta kan su ba kuma. Ashe mutumiyar har yanzu dai halin mijin naki yana nan dai a yadda na san shi wai ni yaushe zai canza ne halan. Kin dai riga da kin san halin shi don haka may ye damuwar ki ga yan mazan yana nan yadda kika san shi dai sai ma abinda ya karu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON HAKA CIN AMANA NE BA, A YAFE BA DON ONLINE NOVEL NE, , , , IDAN KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA DAKE DA ALLAH DON ONLINE NOVEL NE KIN SANI. 60 A daidai wanan lokacin ne na shigo gidan daga school ina gajiye dogon riga ne har kasa nayi rolling da gyalen shi banda fuskana baka ganin komai a jikina. Da fara,a na fito daga motar ina cewa anty sannu da zuwa ta kwashe ni tun daga sama na har kasa ta watsar kamar bada ita nake ba na gaida su. Sai dai ba fuska a garesu gaba dayan su sai na koma wata banbarakwai dani haka naja kafana nashige ciki raina yai matukar baci da yadda sukai min din. Ina shiga na samu yaran sukayo kaina da murnan su nafito wa kowa da tsaraban abinda yakeso suka shiga murna suna jin dadi. Na dan zauna muka taba hira dasu na dan lokaci har lokacin uwar bata shigo ba tana waje da bakuwar ta. Bayan shiga na bakuwar tace da anty Saade amma dai ina ganin ha banza wanan yarinyar ta barki ba da har zaki dauki tsaleliyar budurwa haka kibawa mijin ki. Anty ta nisa tana cewa bari kedai Falmata haka kowa ke fada min niko gaskiya a lokacin hankali na duk ya gushe ne sai ina ganin aiko bayan zan samu mai tallafawa yarana dashi kan sy maigidan yanzu ne fa ta kara murjewa haka da ita ni kaina ai yanzu nasan nayi kasada babba wallahi. Nan da suka dan taba yan maganganun su na mata a tsakanin su basu su jima ba sukai sallama da junan su bakuwar ta wuce ita kuma ta shigo daga ciki sai dai bata ji dadin irin yarda besty ta ya nunawa bakuwar nata halin ko in kula ba haka a fili bayan ya san tun farko tare suke Ta sani sarai ba yaune karon farko da yake nunawa falmata halin rashin mutunci irin haka ba tun a shekarun baya haka yake nuna wa Falmata din halin tsiya bata taba damuwa da abinda yake nuna mata din ba sai ma dai ta nuna ai halin shi ne a hakan bata damuwa sam. Tana shiga ta samu yaran nata faman murna da dan abin da na kawo masu tsaraba wanda hakane dama da wuya na fita ban kawo masu komai ba daga waje. May ye wanan ta tambaya cikin daure fuska jinior ya karaso inda take yana cewa anty ta sawo min cracas da guguru. Ta mika hannu tana fadin ban nan yaron yaki ta kwace da karfi daga hannun shi tana cewa shegu kawai ana zuba maku aguma kuna faman hadiya kullun. Anty tana zaune falon tana faman fada da yaran daddy ya shigo yana tambayan Jinior abinda ya samay shi tace kukan banza yake ji sai Nasir yace daddy mummy ta kwace abinda anty ta sawo muna kullun yanzu idan anty ta sawo muna abu sai mummy ta hana muci. Dago kai yayi ya kalleta inda take zaune sai faman dakilan wayan ta take hankalinta a kwance. Yace Saade zakizo kiji kunyan wanan abin da kike wata rana duk tsawon lokacin da kika dauka da yarinyar nan bata cuta maku ba sai yanzu ne zata cuce ki abin ma har da yara kuma ? A wullakance ta dago tana cewa dashi kishiyace fa Rama kishiya kuma ba abin yarda bace kasani. Ya huce yace falmata falmata ko to ki sani wallahi nina fada maki idan baki rabu da wanan falmatan ba sai ta kashe ki da ranki kina kallo. Falmatan ce zata kashe ni kuma besty akan matarka kake mata wanan mugun shedan wai may boyar Allah nan tai maka ne haka baka kaunar ta tun baya. Yace nina san abinda baki sani ba amma watarana idan Allah ya nuna maki nufinta akan ki. Allah ma ba zai yarda ba kaida yanzu haushinta kake ji don ta tayar dani daga barcin da nake na dauki amanan kaina dana yara na na dankashi ga kishiya tana cuta na. Cuta fa kikace Saade ce Rahama ce zata cuta maki din kuma Rahama fa Saade dan Allah ka barni nayi harkan gaba na kowa tashi ta fishe shi kawai. Ok yayi idan haka kiia zaba wa kan ki amma ni kada ki saka min yara ga shirmay ku ku ruda min su don Allah na rokeki ni dai nasan Rama bazata taba cuta maki ba insha Allahu. Eh tunda son ta ya rufe maka zuciya ai ba zaka taba ganin laifin ta ba idan tayi maka ai zaka gane amma ni na dawo rakiyan ta ko. Ya mike yana cewa yayi Allah ya kyauta kin daiji abinda na fada maki ban son a saka min yara cikin wanan shirmay naku idan ke zaki zubar da girman ki akan ta. Daga haka yaja jiki yabar falon ran shi a bace yana fita ta bishi da kallon takaici don yabi ya wani zauce akan yar karamar yarinya. Da dare na shirya sai part din anty na samu bata falon zaune sai na shiga daki a zaune take tana cin abinci a kasa ga waya a hannun ta tana kwasan dariya tana cewa shiyasa nake son ki mutumiyar. Tana ganina ta canza annurin fuskan ta tace Falmata bari zan kira dan anjima kadan. Wuri na samu na zauna tare da gaida ita ta amsa min da kyat sai dan shiru ya biyo falon kuma ba wanda yai magana a cikin mu. Sai can na daure ina cewa da ita anty dama wurin ki nazo tace ai gani ko sai nai shiru don ban san may zance da ita ba ma. Can dai na daure nace dama anty nazo na roke ki ne don Allah idan har nai maki ba daidai bane ki yafe min don Allah don ni ban san abinda nayi ba anty na daiga kin dauki zafi haka dani ne daga sama na karasa cikin kuka. Tace kinga Rama ni baki min komai ba yanayine kawai ya kawo hakan ko kin manta ke kishiyata ce yanzu kina ganin zaman mu zai ci gaba da dorewa ne cikin amana yadda kike nufi ko may ? Na dago kai da sauri na kalleta cikin mamaki nace subbahanallahi anty kishiya kuma kikace dani. Anty nice kuma kishiyar ki a yau ? Ba kishiya na kike ba Rama yanzu may kike tunda mun hada miji daya dake ai kishi tsakanina dake ya zama dole dama rashin sani ne yakai ni ga hakan da kike gani. Shiru nayi ina sauraren ta don maganan ta ya daure min kai, bata kuma kara magana ba sai ma sharenin da tayi taci gaba da cin abincin ta hankali kwance. Ganin ba zata tanka min ba namike ina cewa don Allah dai kiyi hakkuri koma may nai maki don ni ban san laifina ba gareki. Ta dago kai ta kalleni tace o bakima sani ba ko dama haka duniya ya gada ai kaga mutum a rana ka dauko shi ka sa a innuwa yace kai zai cuta kuma. Ikon Allah nace a fili anty cuta kuma kada Allah ya kawo ranan da zan cuta maki a rayuwana bake ba ma anty koda wani naki ne a duniya. Yaushe kuma ai sai dai kada a kara dama tun farko saida aka jiye min haka amma ban san may ya hau kaina ba a lokacin na nace ni sai kin shigo gidan nan ina gani kamar mafita ne hakan gareni ashe guba na daukowa kaina ban sani ba. Hawaye kasu dumi suka kara zubo min har nakai kofa tace daga yau ma gajiye ban yarda da ita ba don haka idan zata koma wajen ki da zama ne wala,ba,asa ni dai badani ba kuma. Juyowa nayi nace don Allah anty kiyi hakkuri kada ki bari matsalar nan ya fita waje har wani yaji mu yai muna dariya akai. Tace ji na nawa kuma tunda yanzun na fahinci komai an dade ana cutana ni ban fahinta ba sai da masu sona suka wayar min da kai nagane. Anty suka dai cuce mu amma ai wanan ba wayar da kai bane ki dai kara tunane akai kafin ki zurma ciki. Kada fa kiyi min rashin kunya Rama inma mijin ki ya turoki don kizo ki min maganan banza ki koma ki fada mai ko shi yayi kadan wallahi. Ni ban ma san kunyi magana dashi ba akai ni zuwan kaina nayi don naji laifina tace to yanzu ai kinji ko ? Na fice ina kuka daga dakin ita ko ko ajikin ta shedan ya riga yai mata huduba ko ra hau ban tsaya ba dakina na koma na samu su fatima na kallon su hankalin su kwance. Wayana na dauko na kira innata don ita kadai zan iya fara fadawa wanan matsalan dake batun kunno min kai kuma. Bayan inna ta gama saurare na tai salati tace kai amma dai mutum abin tsoro ne wallahi idan tana ganin kinci amanan ta ne ga haka ta manta ita ta hada ki da mijin ta ki bar mata gidan mana sai ki bar mata mijin ta. Nace to inna idan dai naga abin yaci gaba zan bar masu gidan su tunda dama itace ta sakani yin haka dana bata mata gara na barta kowa ya huta. Washe gari tun sa safe sai ga gajiye ta shigo min da kukan ta wai anty tace ta bar mata part din ta dawo gurina da zama ita an samo mata mai aiki sabuwa don yanzu bata yarda da ita ba kada mu hada mata kai mu cuta mata. Hankalina ya tashi sosai naso zuwa wurin ta nai mata magana amma kuma sai na tuna yadda mukayi da ita jiya da dare. Dole na hakkura wanan zance sai daddy dole nan muka zauna da Gajiye da Fatima muna magana akan matsalar. Gajiye ce ke fadin nifa sai ina ganin wanan matar mai yawan zuwa suna shigewa daki ne ta juyawa hajiya kai a lokaci daya haka ? Nace zato mukeyi gajiye tun da bamu san may ya kawo wanan matsalar ba haka sai dai biri yai kama da mutum irin yadda matar tun ganina na farko da ita take dauka na da zafi ko kishiyana ce ita ya tsaya hakanan wallahi. Sai da na tabbatar daddy ya fito zuwa lokacin na saka zullubeben hijabina na nufi gurin shi na samay shi shida hindatu a falon suna karyawa don da alama ma sun gama ko. Gaidasu mayi da kwana sai shan mur hindatu keyi nasan ba komai bane fushi take may kuma ya kawo ni gurin shi don tasan ni bani shiga idan bani ce da girki ba tunda muka taba samun matsala da ita a baya kan hakan. Yau baki shiga school din ne yace dani yana goge bakin shi da tisue daya dauka saman table din. Nace zan shiga dama kai nake jira ka tashi magana nake son muyi da kai yace ok ai gani ko sai na dan kalli inda hindatu take zaune gefen shi. Yace ko maganan ta siri ne ko kai na kada mai alaman eh sai yai murmushi yace hindatu bamu guri don Allah muyi magana yan mintina. Take ta canza fuskan ta har yafi na farko tafara kanan magana ciki ciki yace nace ki bamu guri muyi magana tunda har kikaga ta shigo wanan lokacin ai kin san magana ya kawo ta ko ? Tace nifa ban shiga hakkin mace ba don may za,a shiga min hakkina haka a hana mutum sakewa da mijin shi don Allah dai. Nace kiyi hakkuri anty ba dadewa zanyi ba nima dole ce takama na shigo maku yanzu din ai. Ta wani bata rai tafice daga falon tare da rufo kofan ya dago ya kalleni ya sauke ajiyan zuciya yace ina jin ki may ke faruwa ne wai ? Kuka na fara ina mashi bayani nake cewa ni zan bar gidan tunda na fahinci akaina har wasu zasu shiga matsala irin haka ba zan so na toshewa kowa hanyar samun shi ba ni. Yake cewa dani amma baki da hankali ko bazaki barni na aiwatar da binciken da nakeyi bane zakizo min da wani zance kuma can na daban. Nace daddy anty fa cewa tayi wai na cuce ta da yn uwana da sani na na shigo don na yaudare ta ni may nai mata haka har take wanan hasashen haka a kaina. Koma may ye nace ki barni da ita zamu fahinci juna keda ki ta hakkuri dama haka zama ya gada ai zo mu zauna zo mu saba nace dashi na gode sai na mike tsaye da zumar na fita. Wani irin jiri ne ya kwashe ni sai naga kamar zan kife a wuri da sauri na dafa kujeran shima ashe yagani ya yo kaina ya rike ni yana fadin subbahanallahi kin gani ko zaki jawa kan ki wani matsala kuma can. Hindatu ce ta shigo ta samay mu a hakan da sauri ya sake ni yana fadin ki lalaba kije ki kwanta ki dan huta. Wani kallon banza ta watso muna batai magana ba na samu na mike da kyat na bar falon daki na koma na kwanta sai barci kai nauyi ya dauke ni. Ranan ban shiga school ba koda na tashi na samu miscalled din Zarah yakai shidda a wayana nan dai na kirata muka gaisa take tambaya na ko may ya hanani shigowa yau. Nace dan matsala ne ya ke faruwa sai kuma banjin dadin jikin nawa shine na dan kwanta ashe barci ya dauke ni ban sani ba. Mun kai wani lokaci muna waya tana fada min abinda akayi a ranan muka kuma shiga wani hiran da ita sai da muka gaji na kashe wayan . Wanka na mike na shiga nafito na gyara jikina na nufi inda su Gajiye suke muka zauna muna hiran mu dasu. ********* ********* ********* Yashigo part din daidai lokacin da bakuwar yar aikin anty take dauko mata abincin ta a falon. Gaidashi tayi kallo daya yai mata ya kawar da kai gareta matar ta fice daga falin ya juya gare ta yana kallon ta yace wanan kuma fa daga ina take haka ? Tace sabuwar yar aikina ce yar aiki kuma ya tambaya tace dashi eh yace ina ita gajiye din kuma tace na sallamata na dauko wace na yarda da ita. Rai bace yace kamar yaya kin sallamata ita wanan din kin san ta ne ko kin san halinta ne ? Tace ko ban san ta ba tafi min zama da mai cuta na yace gajiye din ce take cutan ki kuma Saade ? Don Allah mu bar zancen tunda na fada ma komai ba shike nan ba yace bashi ke nan ba kan don ba zan zauna da wanan matar a gida na ba na fada maki. Tunda abuyazo kaina yadda baka so ba yanzu ai dole ka fadi hakana babu inda zata ita nake son zama da ita ba wata bacan. Yace bako a gidan nan ba na fada maki wai may kike nufi danine haka Saade na dai biki da lalama amma naga abin naki sai gaba yakeyi. Sai kayi abinda zakayi dama ai kaji dani zaman dole kake dani tunda ba komai nake tsinanama ba ko ka samu yarinya karama yanzu kana murza. Koma may ye naji don haka sai ki san dabara tun ban shiga rigan arzikin ki ba rayuka sun baci mara tunane kawai. Yafice rai a bace ya barta tabishi da harara tana cewa ni za aiwa burgan maza ko may ? Bai tsaya ba ya fice yaje ya samu mahaifin anty ya labarta mai komai dake faruwa a gidan shi tsakanin mu da anty din. Mahaifin nata ya murmusa yace kaji halin mata ko kamar ba ita bace nan da kukan ta akan a bari ka auri yarinyar nan. Yace ai Abba cewa tayi yanzu kuma wai asiri ne su kai mata abba yace kai mata sai a barsu kawai in bashi ba keda kikai aikin lada dan kankanin lokaci kuma kizo ki zoje ladan naki haka ta hanyar shimay irin nasu na mata. Wana Falmantan takai shuuma babba wallahi ai dole muyi kokarin rabata da ita yace da daddy ya tafi zai zo har gidan da kan shi ya samay ta ai. A ranan kuwa Abba yazo gidan inda yai masauki a falon maigidan a can aka kira yar tashi ta samay shi sun buga wuta sosai saida Abban ya nuna mata bacin ran shi akai ta dan sauko. Sai dai taki yarda sam da zancen canza yar aikin da tayi dole aka hakkura aka barta da wacce take son zama din acewan ta. Nan daddy yasa akirani nazo yake cewa dani don Allah nayi hakkuri da abinda ya faru ina kuka nake kara ba anty hakkuri idan na saba mata ne tace ita ban mata komai ba sai daddy yace babu inda Gajiye zata tafi ta zauna dani don auren ta ya kusa dama shi ke nan sai a wuce wurin. Nan dai muka watse muka barshi da yar shi yana kara dan mata nasiha yake cewa kefa da bakin ki kikace yarinyar nan ta sama maki magani akan matsalan ki kuma yanzu alhamdullahi alama ya nuna kin samu lafiya shine zaki saka mata da wanan halin da kika tsiro da rana tsaka. Ki sani fa da kanki kikai tabin yaron nan akan ya auri yarinyar nan yanzu kuma anyi auren kina samun lada zaki bata zancen ki a dan kan kanin lokaci haka har may akayi ko ga zaman ku in akwai rayuwa bazaki kwadayin kema kiga kin saka wa yarinyar nan ba kada fa ki matan da irin halarcin da kukaiwa junan ku abin gwanin ban sha, awa daku. Jikin ta yai sanyi da kalamin mahaifinta sai dai gaskiya hudubar Falmata ya riga yayi tasiri a zuciyar ta sai dai zata rage wani abu don bin umurni kawai. Da Abba ya fito sunyi mai rakiya hindatu nagani tasan da akwai magana don Abba baya zuwa gidan haka a banza kai tsaye. Can ta samu Zulfa da zancen duk da ba dadine a tsakanin su ba take cewa da ita mutanen ki fa ina ganin zumunta ya watse a tsakanin su don akwai magana koma may ye ai ji zamuyi muna zaune don sai na gano komai ke faruwa din inji Zulfa take fafin hakan. Ranan dana karbi girki har lokaxin bana jin dadin jikina daurewa kawai nakeyi gashi da dare jikina yai wani irin mugun gashewa da zafi amma daddy bai sani ba. Hakana nake daurewa har na gama girki na gashi ba wani daddy tsakanina da anty sai dai dan saukin anin ina gaishe ta ta karba min harda tambayana ya school tanayi. Sai dai ba wani dogon hura a tsakanin mu kamar da can baya bani dau gajiya da zuwa gurin ta gaida ita duk da na fahinci bata son hakan. Matsala kuma yar aikin ta kazama ne ko girki bata iyaba gashi part din duk ya lalacemata kullun sai sunyi fada da daddy ya kasa cin abincin abin ya fara damunta sosai sai rikice ya fara samuwa a tsakanin su take cewa wai ya dai gaji da ita ne kawai yake kirkiro mata matsala a tsakanin su. Ranan suyi rikici sosai har ya daga hannu ya mareta fada sukayi ba dadi a tsakanin su sosai harta jefo zancena a cikin maganan fada sukayi take fadin wallahi sai taga bayana a gidan nan. Ranan kan makiya sun dara don tabar abin fada a garesu hankalina yai matukar dagawa sosai nake cewa da ita nikan anty zanbar gidan don dama kece sillar shiga na a ciki. Nan na barsu nafice falon da aka taru masu ban tsaya ba su gajiye da fatima na bani hakkuri na dauki handbag dina na fice daga gidan ban masan inda zan nufa ba sai can dabara ya fado min na wuce zuwa gidan Amina course mate dina na kuma roketa kada tafadawa ko Zarah ina gurin ta zaune. ZAINAB iDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE WANAN BA A YAFE BA, , , 61 Gajiye ce tsaye a waje cikin tashin hankali tana jiran dawowan maigidan daga masalaci wurin sallah magriba daya fita. Tana ganin shigowan shi ta tare da sauri tafara gaida shi a cikin tashin hankali take fadin Alhaji dama uwar dakin mu ce tun safe kuna wanan rikicin da hajiya ta fita bata dawo ba har yanzu. Ya juyo da sauri yana cewa da ita wa kenan Rahama ko wa tace dashe ita Alhaji yace ina ta tafi har wanan lokacin tace wallahi ban sani ba don bata kai war haka a waje. Yace da ita yaji ya shige ciki kawai ya barta tsaye a gurin dama duk yinin wanan ranan rayuwan shi a bace yake sanadiyar fadan da sukayi da anty din. Yana shiga ya furzu iska daga bakin shi yana fadin a fili ina wsnan yarinyar zata shiga kuma har wanan lokacin haka? Wayan shi ya ciro daga aljihun gaban rigar shi ya shiga kiran layina duk iya kokarin shi bai samu layin ba gaba daya. A Lokacin ne hankalin shi yai mugun tashi azaton shi ko ina gidan Abba ko na mahaifan shi ne sai yai dabaran kiran su da sunan gaisawa dasu amma har ya gama gaisawa da kowan su baiji an sako mai zancen Rahama ba. Haka yasa ya dan shiga cikin damuwa sosai don shi baiga dalilin da zai sa na saka kafa nabar gidan ba don badani akai fitina ba ai suna na ne kawai ta shigo cikin zancen su. Har dare sosai bani ba labarina a gidan dole ya hakkura ya kwanta cike da damuwa gashi anty ce da girki bata shigo gidan ba. Ita ko uwar gaiyyan bata ma san cewa bani gidan ba har lokacin tana can ta dauki fushi da kowa a gidan don tana ganin an mata tozarci a bainan jamaa. Tun da safe ya buga kofan part dina Gajiye ta bude kofan tambayan ta yayi da ta dawo kuwa ? Cikin damuwa tace dashi wallahi bata dawo ba Alhaji ko gida ta tafine dai yace an ya ban tsan manin zata tafi gida don da sun bugo waya ai. Cikin ikon Allah yana komawa part din shi sai ga maigari yakirashi suka gaisa yaji yana tambayan shi muna dai lafiya ko ? Wanan yasa ya kara tabbatarwa da ina cikin garin dai na samu inda na boye je kawai amma ai duk inda nake zai gane. Anty suna gaisawa da Falmata take fada mata abinda ya faru Falmata tace bana fada maki ba wanan yarinyar annobace a gare ki . Don ta riga da ta asirce ki ta ko ina ba ki da sauran motsawa dole ne asama maki makarun abinda tai maki tun kan ki cutu da yawa. Sunyi da ita zata shigo gidan su kara tataunawa zuwa rana don su san abinyi akai a cewar ita falmata din. Sai dai suna gama wayan a bangaren Falma sai ta sauke wani shu,umin murmushi kawai tana magana a zuciyar ta ita kadai. Daddy ya kira Bashir yazo nab yake labarta mai abinda ke faruwa a gidan shi har da barina gidan danayi bai san inda na nufa ba. Nisawa Bashir yayi bayan ya gama sauraren abokin nashi yace watau su dai mata haka halin su yake basu da tabas akan halaiyan su ? Yanzu ita Saade harta manta da irin halarcin alherin data shuka da Allah ya baku rabo tsakanin ka da Rahama aida ankai ga diya biyu a gidan nan da ita. Nan dai suka yanke shawara akan su shiga school tunda sun san a wanan lokacin da nake ga ganiyar gama karatuna babu inda zan tafi na bar karatun nawa ai. Sun shiga school din da tambaya suka isa department din mu inda suka rasa wa zasu tambaya sai ga wata daga cikin dalibai tafito da ganin ta yarece ita don tai kama da kabila suka gaida ita. Nan Bashir yake tambayan ta ko tasan wata Rahama anan department din tace da hausa gaskiya da wuya da nan san abinda take karantawa ne sai lokacin daddy yai magana yace matar aure ne tana yawan shiga CRV assh color tana shekara na shidda ne yanzu. Tace ok nagane ta wata fara kyakyawa mai kamun kai bata da yawan hayaniya sosai kawar Zarah Ko ? Yace ita, Tace nadai ga shigowan Zarah din dazun amma ban san ko ita tana ciki ba don ko tana nan baka ganin ta sai idan sun fito zuwa sallah. Tace dasu tana zuwa ta juya zuwa ciki daddy yai tsuki yace wasu akwaisu da surutun tsiya wallahi wanan dogon bayanin waya tambaye ta ne wai ? Bashir yai dariya yace ai ta taimaka muna koba komai munji wani abu gamay da Rahama din anan suna cikin magana suka hango fitowan ta da Zarah tana saye da hijjab daidai gwiwan ta. Tana ganin daddy tai mamakin may ya kawo shi kuma gashi yau bata ga na fito ba ko ba lafiya ne dai yazo complain. Suka gaisa sai yaji tana cewa ince ko lafiya daddy yau banga mutumiyar nawa ta fito ba nayi kiran layin ta har ba iya ka ban samay ta ba tun jiya. Ganin wanan yarinyar ta farko taki tafiya takuma tsare su da idanuwa yasa shi cewa lafiya kalau wallahi dama mun zo ne mu ganki jin haka yasa lydia barin wajen tai masu sallama zata tafi bashir yace ta dakata ya bata dubu biyu ta wuce tana masu godiya. Bayan tafiyan ta Bashir yace doctor Zarah dama kawar ki muka zo nema a nan don tun jiya tabar gida bamu san inda ta shiga ba kuma. Munyi zaton kuna tare ne sai gashi kuma munji kina fadin ke ma kina nemanta ne yanzu ? Cikin faduwan gaba Zarah tace bata gida ina ta tafi kuma ? Daddy ne yai magana wanan karon yace ko akwai wata kawar ta da kika sani ko zata tafi can gurin ta anan garin ? Tace wai da wuya wallahi don Rahama bata faye shiga mutane ba in dai ba wacce ban sani ba ne amma kuma an tambaya can gida kauye ko tana can. Yace da wuya don munyi waya dasu suma suna tambayan lafiyan ta dazun da safe kin ga bata can ke nan. Nan dai tai masu alkawarin cewa zata taimaka ta bincika duk inda ta san na sani tagani ko Allah zai sa a dace. Sukai mata sallama suka tafi kasa zama tayi anty Amina tana ganin ta take tambayan ta ko lafiya ? Tace anty kawatace ke cikin dan matsala yanzu mijin ta yazo nan ya wuce Allah ya sauwaka tace tabar ta bata kara magana ba. Koda ta dawo gida ta samu na gyara mata ko ina na gidan har girki nayi mata don daga ita sai kaunar ta ne zaune kuma duk suna fita zuwa makaranta yaran ta da mijin ta basu garin suna can Enugu zaune inda mijin ta ke aiki karatu ya tsayar da ita a kano sai ta samu hutu take zuwa. Ina zaune a falo ta shigo gida da yamma kamar yadda muke dawowa a wahale tace kai kai kai lalai yau gidan nan yasan yayi bakuwa kan. Nagaida ita muka zauna ina tambayan ta abinda akayi tai min bayani can tace Rahama maigidan ki fa yazo neman ki a school yau shida abokin shi. Kawar ki ma naga ta shiga damuwa don bata ma zauna ba nace Allah sarki nasan Zarah tafi da haka wallahi. Nan mukai magana sosai da ita kan matsalan abinda ke faruwa dani take cewa ni yanzu Rahama banga abin tashi ba anan ? Tunda dai mijinki bai maki komai ba matsala dai da kishiya ce don may zaki biyewa rudin shedan ki baro dakin ki ? Nace anty Amina gaskiya barina gidan shine alheri gara dai na bar mata mijin ta a zauna lafiya tunda kinga matan nan tai min halarcin da ba kowa ce mace ne zata iya yiwa bawa shi ba. In dai nice zan kawo mata matsalan farin cikin ta gara dai na barsu kowa ma ya hutu tace a naki tunanen ba ina zaki kai son mijin ki a zuciyar ki ko shi yaya kike son yayi da ran shi a rashin ki ? Gashi kwana daya har ya fara yawon neman ki a gari haka ni idan zakibi ta nawa kiyi hakkuri ki koma dakin ki ki share kowa taita haukan ta ita kadai. Don ko batace ba dama Allah yayi akwai aure a tsakanin ki da shi tun farko ki daina wani tunanen wai don ita tasa ya aure ki ta dawo kuma tana cuta maki haka ? Dole fa sai kin nuna mata kema din mace ce tunda kikaga ta fara wanan halin idan ba kunyi fito na fito ba ba zaku taba zaman lafiya ba yadda kike so da ita. Don ko yaushe magana ya tashi cewa zatayi ai a dalilin ta ki ka aure mata miji gashi mata fara zargin kun dade tare dashi tunda tana bakin ciki ya nuna yana son ki haka. Watau ita so tayi ki ta zaman takura tana juyaki yadda ranta yaso ki zauna baki da incin kan ki ko kadan sai yadda tayi dake ke nan ? Nace ba hakana bane Anty da farko fa zaman mu gwanin ban sha, awa ne don ko makara nayi ban tafi gurin maigidan ba zokiga yadda take bata ranta akan hakan yaran ta kuma tana matukar son yadda muke muamula dasu . Shigowan wanan kawar nata ne a rayuwan ta ya kawo muna duk wanan matsalan da muke ciki da ita a yanzu din. Tace kai haba Rahama in har son Allah da Annabine ai babu wacce ta isa ta shiga tsakanin ku irin yadda kuke da ita din nan. An dai tarar da hali dama akwai wata a kasa kece dai da kike zaune da ita Allah ma,aiki kike ganin ba wani abu a zuciyar ta amma kawa ruwan ta ta tofa ciki kawai akwai hali dama can. Mun dai tattauna sosai da ita tana kara koya min dabaran da kuma yadda zan zauna a cikin kishiyoyi na zamani . ********* ********* ********* Horn ake a kofan get maigadi ya taso ya duba yana ganin motan matar da maigidan yai mashi kashedi ne akan kada ya kara bude mata get idan tazo gidan . Tana ganin shi gashi sai faman horn take ya bude mata amma yaki dole tafito daga motan ta cikin hasala ta nufi kofan tana fadin kai wani irin dan rainin wayo ne kana ganin kana kuma jin ana hirn bazaka bude wa mutum kofa ba ? Yace na jiki na kuma ganki sai dai umurni ne aka bani akan bazaki kara shigowa gidan nan ba tace wani dan kazan uba ne ya haka wanan umurnin a kaina haka. Yake cewa da ita maigidan ne yabani wanan umurnin a kan ki don haka kibar wurin nan kagin na kira maki yan sanda. Tace har ni akewa barazanar kiran yan sanda wayan ta ta ciro takira Saade take fada mata abinda maigadin yai mata take ran Saade yai matukar baci sai gata tafito a fusace daga cikin gidan. Ta nufi get din tana fadin malam musa rainin wayo ne yau kuma akaina ko may ko kana nufin kabi bayan Gajiye ne kaima ? Yace hajiya ba hakana bane maigidan ne ya umurce ni da yin hakan kuma yace idan ta shigo gidan nan a bakin aikina wallahi. Can ta fita suka ga juna da ita sun jima har maigidan ya dawo ya samay su a wurin ya shige ya barsu yasan malam musa ya fake aikin shi ke nan. Da yamma anty ta shirya takai karan daddy da kukanta gurin mahaifinta ya daga waya ya kira daddy din yazo ya samay su anan. Bai dauki lokaci ba ya iso aka kirata tafito nan takawo maganan da tazo dashi ra kara maimaitawa a gaban Abba da daddy din. Daddy yace tabas shiyaba malam musa maigadin shi wanan umurni don Falmata ba matar arziki bace. Yace tun baya sun taba samun wanan rikicin akan ta tun kafin suyi aure da kyat ya samu ya rabasu. Sai gashi kuma yanzu ta sake dawowa cikin rayuwan su da manufanta akan su inda ta dawo da tsigar tarwatsa mai farin cikin gidan shi ga bakii daya. Yace Abba na rasa ko Saade wata irin yarinya ce ita da bata da fahinta ko kadan wanan falmatan sam bata kaunar ta da alheri amma ta kasa fahintar hakan ita. Gashi ta cusa mata mugun halin banza a rayuwan ta har takai ga zubar da mutuncin ta ga abikiyar zaman ta da suke zaman lafiya a tsakanin su. Yanzu hakka Abba Rahama bata gidana yau kusan kwana biyar ke nan na tafi duk inda nake zaton zata tafi ban samay ta ba can. Nasan kuma tayi hakane don ta nisanta kanta da mu don irin maganganun da taji Saade ta furta a kanta ranan. Abba yace subbahanallahi yanzu ina yarinyar mutane ta shiga ba a sani ba shine kai kuma bakazo ka fada min ba a bincika ko zaa ganta. Ya juya gurin Anty yana cewa kin gani kinga iri abinda kika jawo wa yarinyar mutane da kika dauko amana yanzu may gari ya waya akan wanan hadin ? Kina ganin wanan yarinyar zata kara ganin ki da daraja a idanunta ko may tun da kin zubar da kimar ki a gareta ko ? Ta dago kai cikin nadama tana cewa ni wallahii Abba ban ma san bata gidan ba tsawon wanan lokacin haka ? Yace ina zaki sani kin dauki mugun abu kin sa a ranki wai ke kishi baki ji kunyar fadar cewa baki san yarinyar nan bata gidan nan ba tsawon lokaci haka ? Har kina nufin kin manta da irin dawainiyar da yarinyar nan tayi na jinyar ki ko may ke yanzu kina ganin ita wanan da kika dauki amanan kan ki kika mikawa zata iya maki abinda wanan yarinyar tai maki a rayuwa ni nasan akwai abinda mijin ki ya sani yake boyewa akan wanan kawar taki amma ke hauka ya hanaki ganewa tai maki hudubar shedan kin hau kai kin zauna. To ki sani mudfin kikace bazaki bi umurnin mijin ki ki zauna lafiya da kowa ba zamu raba gari dake baki fatan mu rabu lafiya dake ke nan . Hawaye ne ya zubo mata take cewa don Allah Abba kayi hakkuri insha Allahu zan gyara ba zan kara wanan rayuwan ba Abba . Yace yanzu ai zabi a gareki duk inda kika san yarinyar mutane ta shiga maza ki nemota a garin nan don ba zaki maidani mutumin banza ba. Abamu yarinya don darajana amma yanzu kizo ki tsiro wa mutane shegan taka irin haka ? Nan dai suka dawo gida har lokacin ba wani shiri a tsakanin su kowa najin dan uwa a ran shi. Tana fita bata tsaya ba ta shige part din ta kawai ya bita da kallon takaici shima ya shige nashi wurin. Yana shiga wayan Zarah na shigo mai ya dauka da sauri bayan sun gaisa take tambayan shi babu wani labari dai har yanzu ko ? Yace wallahi Zarah ba labarin komai don har garin su na tafi amma bataje can ba ina dai sa rai da tana nan cikin garin akwai inda ta boye kawai. Sukai sallama ta kashe wayan tana kashewa kirana na shigo mata da saurin ta ta dauka tana cewa Rahama kina inane haka ? Rahama ina kika shiga duk kin dagawa mutane hankali don Allah ina kike yanzu wai ? Nai murmushi nace haba Zarah baki ko tsayawa ki tambaye ni zaki shiga tambayana haka ina nan inda nake mana. Munyi magana da ita nake fada mata tazo gidan anty Amina ta samay ni don Allah kada ta fadawa kowa ko ita akwai maganan da nake son muyi ne shiyasa nakirata. Bata bata lokaci ba sai gata gidan dariya muka shiga yi mata tace amma anty Amina baki kyauta min ba yanzu ashe Rahama na gurin ki baki fada minn ba ? Tace alkawari na dauka akai don haka babu yadda zan fada maki hakan kin ga na karya alkawari ko ? Harara ta watsa min tace to yanzu ke may kike anan da kika bar dakin ki ? Nace abinda kikaga inayi mana tace wallahi kin dai ji kunya Allah kuwa Rahama yanzu akan kishiya zaki bar dakin ki da mijin ki ? Kin bar mutumi bawan Allah duk ya haukacewa mutane an rasa gane kan shi duk ya tsayar da aiyukan shi akan ki. Nace yadai so ne amma ai bani kadai bace mace gare shi ke gara na bar mashi matan shi ko za a zauna lafiya yafi min. Kin dai san daddy ba zai taba sakin ki ba batawa kan ki lokaci kawai kikeyi anan in zaki koma dakin ki ki koma tafi maki. Anty Amina tace abinda nake dafada mata ke nan kullun wallahi tunda tazo gidan nan kishiyar may can kowa tashi ta fisheshi mana ba shike nan ba amma ita taki yarda. Munyi magana dasu sosai amma basu shawo kaina ba daga karshe anty ke cewa dama kiran da mukai maki test muke son yi shine tace ke zaki iya koba abin yi yanzu dau dan duba min ita please ko maganan ku zaizo daya da nata. Da sauri ta dago kai tana kallon inda nake tace ku fada min dan Allah may ke gudana ne wai ? Yanzu dai dubata mugani please da sauri ta mike zuwa inda nake ta jawo hannuna ta dan rike kamar mai nazari can ta dago tace two months da kwanaki Rama ? Na runtse idona a hankali ta jawoni da murna a jikin ta tace Allah mun gode ma yan bakin ciki kunyi kunya wallahi. Bude bakin ki mu gani na bude mata duk wani abinda ya dace sai da tai min duk da nima na san dashi. Yan zu may ye abin yi ta tambaya tana kallon anty Amina don taji may zatace da ita din . Kunga wanan matsalan bai san dashi ba nace ba wanda yasani kuma dawowan shi daga chaina ne nasan na samu cikin nan don ga lissafina haka din ne. Mun dauki lokaci tai muna sallama don dare yayi a lokacin ta tafi tun a hanya ta kira daddy din wanda ke zaune tare da Zulfa a falon shi. Bayan sun gaisa ne take fada mai cewa daddy yanzu daga wurin Rahama nake tana kuma lafiya a inganttacen wuri. Mikewa yayi ya ma manta a gaban Zulfa yake yake cewa tana garin nan ke nan tace tana nan daddy a gidan wata kawar mu take zaune. Sunyi magana sosai sukai sallama yake cewa da ita gobe zai shigo ya samay ta yaji komai. Ranan yayi barci kwanciyan hankali don yasan ban bata ba ke nan sai dai har lokacin anty tana bashi mamaki sosai. Nayi kyau na kara murjewa dani dan dan cikin dake ajikina kyauna ya kara baiyyana duk da ba komai ne nake iya ci ba sosai. Muna zaune da Anty Amina a falon ta mukaji an dana bell din gidan hakan yasa muka san anyi baki ke nan. Ta tashi taje ta duba na jawo hijjab dina na saka hankalina yana gun tv ina canza Chanel sai kamshin turaren daddy ya daki hancina. Da sauri na dago kaina mukai arba da shi yana tsaye saye da coth baki ya kura min ido baya ko kiftawa. Inda Zarah take na kalla cikin bacin rai sai ta ware min hannayen ta alaman ina ruwan ta ita. Bissimillah zauna mana Alhaji inji anty Amina take cewa dashi hakan ya samu wuri ya zauna suka fara gaisawa dashi. Can ya juyo inda nake yace Rama yaya akayi kika zo nan bada sani ba kika zauna shiru nayi mashi kamar badani yake magana ba. Yace bakiji may nake fadi bane halan dake shiru kowa yayi a falon can anty Amina ta mike ta shige tare da kiran Zarah tabi bayan ta. Tashi yayi ya dawo inda nake zaune yana batun rugumay ni nace cikin wani irin murya dont dear touch me , kaje kaji da matan ka please ? Murmushi yayi yace kina hauka ke nan kema kin shiga shirmay sauran ke nan tunda har kika bari shedan ya shiga zuciyar ki ya samu wurin zama. Ba wani shedan sai gaskiya kayi min abinda suke so a zauna lafiya bazanyi sillar shiga hakkin kowa ba a rayuwana in wargaza mata farin cikin ta bayan irin halarcin da tai min a baya. Ke kika san wanan amma ita wacce kiie son musguna min akanta bata ma san kinayi ba har yanzu. Yin haka shi zai kara tabbatar da hasashen ta a kan ki harta dauka gaskiyane abinda take zargi gareki. Ni ban taba zuwa gurin boka ko malami ba don na cutawa wani balle in kai ta ai mata sheri. Wanan ba magana bane ki tashi mu koma gida don banga amfanin zaman ki ba anan yanzu. Kaine baka gani ba ni kan nagani ba sai angani ba zaa ce ga aibuna kuma a gidan gida dai ne na bar masu abinsu na kuma bar masu mijin su a zauna lafiya. Murmushi yayi ya mayar da abin ma wasa gareshi duk yadda yaso na sauka naki yarda haka ya tashi ya barni a gidan bai tsaya ba sai wurin Abban anty ya sheda mai halin da ake ciki dani. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 62 Duk yadda daddy ya dauki abin da sauki sai yaga ya fara wuce lissafin shi don haka gidan Abban anty yaje ya fada mai komai washe gari da yamma sai gasu a gidan anty Amina tare. Duk nauyi da kunyan Abban ne ya kama ni sosai dan zaman da mukayi dasu don sulhu sai na kama yi ma su kuka ina rokon Abban da suyi hakkuri su bar ni don Allah amma ni bazan koma gidan daddy ba kuma na barshi har abada. Ran daddy yai matukar baci sosai Abba din ne yai abin manya yace dani to Rahama in banda abinki ai ba zamuyi maki dole ba ko ? Ni da na dauka a matsayin uba nake gare ki a garin nan tunda a dalilin ya ta kika zo nan kuma ke din kin dauki ni tankar mahaifi a gurin ki. Ashe abin ke ba haka yake ba gun ki tunda har zaki iya samun matsala ki ketare ni kizo wani wajen ki boye kin tayarwa mijin ki da hankali haka ? Sai a tunane na yadda nake daukan ki yarinyar mai kaifin hankali na dauka ko a bayan raina bazaki taba watsar da iyalina ba ki guje mu. Ko kin dauke ni mahaifin kishiyar ki ke nan kuma ba uba da nake ganin na zamo maki ba in baki sani ba yau ki sani ga mijin ki nan shi sheda ne. Iyayyen ki don ni suka bada ke gun Yusufa batare da sun yi wani shakkan yin haka ba ga auren ku amma sai gashi matsala ya faru kin ketare ni kin zo wani guri na daban kin zauna. Cikin kuka nace don Allah Abba ka yafe ni kayi hakkuri nayi kuskuren yin hakan da nayi a lokacin tunanen haka baizo min ba a raina. Kuma a yadda anty ta nuna min Abba ko gurin ka na tafi ina ganin zata nuna min don ta nake zaune da kai. Yace na fahince ki Rahama amma idan har kin dauke ni Uba ina son yanzu ki tashi ki koma gurina duk abinda zamuyi muyi shi a can din a gidana. Haka kawai zaki min nasan kin dauke ni a matsayin mahaifi a gareki yanzu shiru nayi ina kuka a hankali. Yace in banda abinki Rahama kin taba ganin inda akaiwa mutum dole idan kin ce kinayi sai na mayar dake idan kuma bakyayi babu dole ga zama ai. Tunda sun kasa rike min ke akan amanan da muka basu basai su bani abina ba na rike ki amana ni don mahaifa basu gazawa da dan su ko yaya yake kuwa. Wanan kasan da Abba ya tula min yasa na kasa ketare zancen shi na ce Abba kayafe ni na amince da nakoma gurin ka amma kuma ina tsoron abinda anty zata ce idan taji ina wurin ka kuma. Wanan ma da akayi da yardan ta da amincewan ta tace na cuce ta balle yanzu taji cewa na koma hannun ka zata dauka ina son in mata wani sabon makirci ne kuma again. Anty Amina tace ni a ganina da kikoma gidan Abba din da zama kiyi hakkuri ki koma dakin ki tunda Abba yazo da kan shi Rahama ko don condition din da kike ciki kina bukatan bedrest da kwanciyan hankali. Da sauri daddy ya dago yana cewa bata da lafiya ne ko may tace to kusan hakane don tana dauke da lalura na karauwa a jikin ta a yadda na auna ta tana da bukatan samun hutu sosai don tana fama da stress tare da ita wanda nasan wanan tashin hankalin ne ke bara zana da ita. Yace cikin wani murya na mamaki Rahama ciki ne tare da ke ban sani ba ko may ? Tace dashi shidin ne da ita, Abba ka barta ta koma dakin ta kada ai fushin manya don Allah. Murmushi Abba yayi yace kagani ko Allah ya azurta ku da alheri amma fitinan matar ka ya hana ku kwantar da hankalin ku, ku fahinci hakan gareta. Abban yace Rahama na amsa da naam abba ? Kiyi hakkuri tunda ga wanan lalurar ya gitta a tsakanin ku ki koma dakin ki ku reni cikin jikin ki da mijin ki. Ki share komai akan Saade ni dai na haifi saade kin sani wanan halin da ta dauko ba nata bane aron shi tayi. Don haka nasan zata sauko da yardan Allah don Addua bai bar komai ba ga bawa don haka may kikace kin amince zakibi mijin ki ko zaki koma gidana da zama ? Shiru nayi shiko daddy duk ya kashe ni da ido yana son jin zabin da na yi a raina a gaban kowa. Na bude bakina da kyat nace daddy tunda komawan shi kake so a gareni na amince zan koma dakina insha Allahu. Yace Allah yai maki albarka Allah ya baki zuria masu albarka da zasuyi maki biyayya fiye da wanda kikewa iyayyen ki. Wani kuka ne ya zomin ba kakautawa dole na mike na shiga daki na hado yan kaya na dama daga na jikina sai dogon rigan dana saka a hand bag dina don canzawa kawai. Mukaiwa Anty Amina sallama Abba da daddy suna ta mata godiya muka bargidan sai da muka kai Abba din gida wanda har muka kai gida nasiha yake ta muna dukkan mu mun sauke shi yake cewa zai nemay ni nan da kwana biyu zai yi magana dani. Tunda muka bar Abba nake ta kuka sai huci daddy keyi bai min magana ba mun dauki titin gidan mu naji ya miko hannun shi zuwa saman cikina naji ya shafa a hankali. Yace a fili Allah na gode ma daka azurtani da karuwa da wadda nake so a rayuwana ya Allah ka bamu mai albarka da tarbiya imani irin na addinin musulunci. Kuka na kara sakawa sosai bai dai min magana ba muna gab da shiga gida ne na dakatar dashi da fadin don Allah daddy ina mai rokon ka da ka boye zancen cikin nan ga kowa don gujewa baki da fitina tsakanina da matan ka ? Baice dani uffan ba ya danna horn maigadi ya fito da sauri ya bude muna get muka shige a lokacin magariba ya kusa bai bude motar ba sai cewan da yayi dani ya kamata ki daina wanan kukan haka don banga dalilin yin shi ba. Sai da ya tabbatar da na daina ya bude min mota na fito ashe Hindatu da Zulfa suna tsaye suka ga fitowana ban tsaya ta kan su ba na shige abina ciki. Gajiye da Fatima na zaune har Atika sai ganina sukayi daga sama na shigo gidan zubur suka mike Gajiye na fadin Alhamdullahi uwar dakin mu ta dawo kenan insha Allahu. Fatima ko fadawa tayi jikina ta fashe da kuka tana cewa anty kin wuce kin barmu cikin wanan matan hankalin mu a tashe. Daga baya na mukaji muryan shi yana cewa Fatima saketa taje daki karbi hand bag dinta kibita dashi dakin. Ban tsaya sauraren komai ba na wuce har ya fara tafiya naji yana cewa Gajiye don Allah ki kula min da ita sosai kada ki bari tana aikin komai don tana bukatan hutu tare da ita. Tace angama Alhaji insha Allahu, yafice suka bi bayana zuwa dakin duk maitar son kallon Fatima ranan sai na samu tv a kashe haka yasa na gane suna zaman takura ne suma a gidan. Na dan zauna can na mike na shiga wanka na fito na tayar da sallah na dade zaune a gurin ina adduoi shiigowan Gajiye ne ya sani dakatawa ta samu wuri a kasa ta zauna tana gaidani. Tace hajiya Rahama kin boye haka da yawa hankalin maigida yai matukar tashi sai faman fada yake da kowa a gidan nan an rasa gane kan shi dan kwana biyun nan. Bayan tafiyan ki sun kara tafka wani fitinan da hajiya Saade sosai a kan ki har yana mata ikirarin indan kin bar gidan nan itama ta tabbatar da tabar shi ke nan . Tace dasu hindatu kuma anyi shi ba dadi a safiyan jiya don ina ganin ta kawo mai zancen ki ne yai mata tas a kan ki. Nace Gajiye kyale su kawai dama don su cuta min yasa matar nan tai min haka ina zaman zamana hankalina a kwamce ta sani yin wanan auren yanzu kuma ta dawo tana zargina haka ? Gajiye tace duk ki bar wanan tunanen hakana yanzu ki rugumi mijin ki kiba banza ajiyan kowa tunda Allah ya nuna maki ai ba yau ta fara ba tun auren ki dashi suke wanan rikicin haka dashi. Nace Gajiye kina nufin anty ta dade tana nuna min wanan halin a tare da ita tace wallahi Allah ko don shi ya zama namijin gaske ne sosai. Ni ina ganin a zaton ta ba zaiyi rawan kafa dake ba haka yadda yakeyi ta dauka dai ta aura mashi ke ne kita mata bauta ita da diyanta kada ki gushe a garesu. Nace koma may ye Gajiye ni da zuciya daya nake zaune da anty idan ita ta dauke ni da zuciya biyu ne na barta da Allah don Allah ba azzaluumin kowa bane ai. Ba zan taba nuna mata wani mugun hali ba na kishi don itace sillar mayar dani haka a duniya da bata jawoni ba da ai yanzu ina kauye sai yadda Allah yayi dani. Dama dai Allah ya riga da ya zana akwai aure a tsakanin ku kuma ta dalilin ta zaku hadu dashi kawai. Amma hajiya ta furfura fiye da tsanmanin ki Rahama don tun tafiyan ki bata taba laiko mu ba shiyan nan balle taji halin da muke ciki. Yaran dai ne ina ganin sato jiki suke sama sama su shigo su tambaye ki ko kina nan da ance bakyanan zasu juya da sauri su fice sukoma inda suka fito. Murmushi nayi nace wanan ai daukan alhaki ne bayan ita ta hada ni da yaran kuma zatace yanzu zata raba mu tsakanin mu ni yaran ta basu min komai ba don haka ba zan daina kulasu ba har ta sauko. Gajiye bata gama maganan ta ba sai ko ga yaran sun shigo dakin nawa suna lekawa suka gane ni jinior ne maimakon ya tsaya sai ya juya da gudu yabar dakin sai gasu gaba dayan su su uku sun shigo da murnan su duk suka fada min a jikina. Mun baje sai faman surutu muke yi dasu daddy ya shigo ya samay mu a haka da gani yaji dadin yadda ya samay mu din, nan ya zauna dasu suna hira sai ga yar aikin anty ta shigo tana cewa maman ku tace na kira ku. Ganin daddy baisa ta gaidashi ba sai yaran suka make sukaki tashi yace kice suna zuwa suna tare dani anan. Mun kai wani lokaci a wurin tare dashi dasu ya tashi ya fice dasu daga dakin nawa naji wani irin ba dadi muna zaman mu lafiya shedan ya shigo muna a rayuwan mu. ********* ********* ********* Duk da anty tasan na dawo bata shigo ba part din ina son shiga school sai da nagama shiri na tsab na shirya na nufi ban garen ta. Tana daga cikin daki sai yar aikin ta ke zaune a falo ga falon ya wani ya mutse man da gani bata da niyar gaida ni nima ban kula ta ba na nufi kofan dakin ta. Sai naji matar nacewa tana kwance ne tace kowa ya shigo na fada mai ta kwanta wama zai shigo din in bani ba na fada a raina nasan kuma don ni tabar wanan sakon haka. Sallama na fara yi har kusan sau uku sannan ta karba min da waye wai please nace nice anty na karasa shiga tana daga kwance da wayya hannun ta nace ina kwana anty tace lafiya kawai. Nace na tafi school adawo lafiya har nakai kofa ra sake cewa dani kinga dama kin dawo daga barna min suna Rama kisa duniya ta zage ni kan gaskiya na ko may ? Tsam na ja na tsaya nace cikin yar sirirayar murya kiyi hakkuri anty idan na bata maki amma ni ban bar gidan nan da sunan ki ba na bari ne kan abinda naga yafi sauki gare mu. Yanzu da kika dawo waya biki can inda kika tafi din ban dai yi magana ba itama bata sake furta komai ba naja kafana na fice daga dakin kawai. Ina fita naji ta kira Saliha matar ta amsa tace bana nace kada ki bari kowa ya shigo min daki ba na kwanta ina hutawa. Wallahi Na fada mata bata tsaya ba ta shigo dakin kai tsaye tace ba dole ta shigo ba tasan mugun kullin da tayo min zai kare a kan ta ai. Murmushi kawai nayi na karasa fita bayan na gama jin maganan su a wajen gidan kuma na hade da mutumiyar tawa Hindatu uwar mita da anyi ance . Gurin da mota na yake na nufa yana aje a wanke min shi sai shaki yakeyi tun daga nesa na bude shi kafin na karaso gurin. Kai amma dai hanne wasu matan basu san takaici ba kayi yaji ba wanda ya bika dangin miji ka kwashi kafa kadawo gidan sidau daga kai sai mijin ka an daiyi harasa kawai wallahi. Wai ma hanne ni sai ina ganin dangin miji sun gaji da bata iri ne a gidan su kulun sai ci ana juyewa a masai babu wani shedan zama ana raya sunan ma, aikin Allah a gani. To ba dole a dawo ba an saba da shan jan miya yanzu ba a iya zaman kauye kare ya nuna mutum. Dole miji na zuwa a kwasa a dawo ragai ragai an gaji da kwasan kuka kulun da dawa. Har na dan wuce ta sai na dawo baya daidai inda suke tare da hanne din yar aikin ta nace cikin murmushi. Ashe kai yaji miji ya dauki kafan shi ya bika baka aiko ba baka turo ka takurawa dangin miji ba isa ne. Kauye kuma suna suka tara don wasu sai dai su fadi sunan nasu amma abin kunya bai bari su taka kauyen . Shikuma nunawa duniya kana kwana da miji ai kauyancine mijin dai shi zai nuna ka isa gareshi har yana rawan kafa. Barin sheda kuma abune daga Allah don da wasu sun tara shedan dayawa yadda suke so kullun. Shan kuka da dawa kuma sai naga kamar abincine ba haram ba don yafi shan giya da zina. To wakike nufi da mazina ci ko may shan giya din nace magana ce da amsar ta ai ko laifine kuma ? Aiko tayo kaina a, a hindatu babu gaskiya don a gabana kuka fara babu ruwan ki da miji ya bita balle gori ya biyo baya naga nan ake yaji gidan nan bai rawan kafa irin haka ? Zulfa ce da tun safiyan jiya suke da matsala tsakanin su take bata amsa tace in kasan abin fada baka san amsan da zai dawo maka ba ai ? Nace na dai gode anty Zulfa in tsoho baiji kunyan hawan jaki ba, shiko haki bazaiji kunyar kada tsoho ba ashe kin zube min wallahi hindatu bazan sake jin naitin ki ko kunyar ki ba agidan nan dani dake shege ka fasa a gidan nan. Na juya nasa kai na wuce abina inajin Zulfa na fadin kin kai ga yadda kike so ai yanzu girman ki da kimar ki ya gama zubewa ke nan. Mace kice ke kowa kina bakin cikin kiga ya rabi miji sai ke kada halan ke kadai aka halitta mashi da ya aura ne wai ? Na ta da mota na na bar gidan abina ban tsaya binta nasu ba don sun kaurai da fada a tsakanin su ba mai jin has a cikin su . Ina isa school Zarah ta tare ni da dariyar shakiyanci nai banza da ita bamu zauna ba muka shiga pratical ba wasa sai two muka fito sallah. Nan muka dan samu lokacin kebewa muka dan taba hira wanda duk hiran namu akan matsalar mune da abokkan zama na mukeyi. Mun gama break muka koma cikin asibiti ba mu fito ba sai karfe shidda dai dai muka fito koda na iso gida a gajiye. Sashe na nanufa kai tsaye inda na samu su Fatima sun gama hada komai don ranan nice zanyi girki a gidan. Komai ya kammala yadda nake so sai bayan da nai sallah na shirya tsab a cikin wani English wear dina mai ruwan pink da baki sai dai bakin yafi yawa a jikun kayan sosai. Kayan abinci na dauka zuwa part din shi har na gama jera komai na dan shiga daga ciki na gyara dakin sama sama har ban dakin sai da na gyara na wanke tsab ina shirin fitowa ne ya shigo dakin don ya kimtsa. Yace ashe kina ciki na dauka kin fita ne ai nace dakin nake gyarawa yanzu yake cewa baki dai jin komai a jikin ki ko ? Lafiya kalau nake bana jinn komai tare da ni sai dai yawan jiri dake damuna sometime idan na mike tsaye nake yawan ji. Yace you see ya kamata muje checkup a duba may ke yawan damuwar ki haka ne wai ? Nace daddy ko ban tafi ba zan iya curing din kaina anan gida da sauri naji yace dani no no no gobe ki shirya mu tafi gun likita ban jaba nace Allah ya kaimu kawai. Falo muka dawo tare ya zauna cin abinci tare ina daga gefen shi a zaune a lokacin ne matan gidan daya bayan daya suke shigowa gaida maigida. Duk wacce ta shigo taga irin zaman da mukayi da daddy yau saman kujere daya na harde kafana daya saman kujera kusa dashi dayan na a kasan kujera gashi gaf da juna muke zaune. Sai mai shi ta hade fuskan ta take suke nuna bacin ran su har anty na a haka ta samay mu zaune dashi. Bata tsaya ba ta juya ta fita daga falon wanda dama da gangan na zauna hakan a kusa dashi don kawai na nuna masu lokaci yayi da zasu fahinci nima fa na iya komai ladabin kurage nake masu kawai. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA SABODA ONLINE NOVEL NE WANAN, , , , , 63 Bamu wani jima ba muka kwanta ranan nasha fada da nasiha sosai a gurin daddu har takai na fara kuka don jikina yai sanyi sosai ga nasihan shi. Ban yi mamakin yadda ta gudanar dani ba a ranan don halin maza ne nuna gwaninta su a gun mace. Washe gari muka tafi asibiti yan maganin da dama nake sha su likita yaso bani nace already dama ina amfani da su ai. Sai da yaji likita yace wanan ba komai bane haka wasu mata suke fama kafin ciki ya zauna a jikin su da kyau hankalin daddy ya kwanta. Tun wanan ranan nake kokarin ganin na kiyayye kowa a gidan dagani sai su Fatima da gajiye muke al, amarin mu. A cikin wanan halin Allah ya kawo muna mama altine ko da tazo bani gidan ina school dana dawo ne Gajiye ke sanar dani zuwan mama din. Sai da nai sallah isha,i na shiga gaida mama din da fara, anta ta tare ni nima din haka a falo na samay ta muka gaisa na tambaye ta duk mutanen gida tace suna lafiya Rukaiyya ma ta haihu na biyu. Naji dadi sosai muna cikin hira jinior na kwance a jikina yana wasan shi Nasir na gefe na a kwance sai ga uwar ta fito daga dakin ta. Na gaida ita irin yadda ta karba min yasa mama ta kalle ni yaran ta kalla tace dasu ban hanaku zama jikin mutum ba ashe ? Cikin rashin sanin may ke wakana mama tace cikin dariya kai amma Saade akwaiki da wani magana kuma . Rahama da yaran nan ai sai Allah shifa yaro kamar dabba yake inda yaga ido a nan yake ko yaushe, da basu tafi gurin wani sun mamay shi ba fuska suka gani. Sai cewa anty tayi a, a mama bana son irin haka yanzu kowa ya tsaya matsayin shi yara dai nawa ne aiko ? Gyara dai zancen ki Saade yara naki ne kin haife su ne kawai amma aida Rahama suka bude idanuwan su ko ? Kai mama don Allah ki bar wanan zancen idan ta samu nata zata bude ido da su ai. Ikon Allah inji mama Altine tace kanki daya kuwa yau Saade nifa tun zuwa na naga canji sosai a yanayin ki. Muna murnan kin samu lafiya kuma sai sabon yanayi ya shigo gaskiya banji dadin jin wanan zancen ba dakika yi yanzu. Ina yarinyar nan tun bata san duniya ba Allah ya hada ku tare har talai kin sadaukar da sonta a kan ki. Anty tace ada ke nan mama ni yanzu ai an shani na warke ko na fahinci waye dan adam ka gan shi a rana kakai shi innuwa yanzu ba may kara yaudara na kuma. To Allah ya kyauta da magana ke nan a gidan naku don naga alaman haka tun zuwa ban ga Gajiye a nan ba tun da tazo taimin sannu da zuwa sai wanan bakar matan nake gani tundazu gata bata da ko marmari kamar muguwa. Mikewa nayi nace mama a huta gajiya zan koma sai da safe ina mikewa yaran ma suka mike wai zasu bini amma fafir uwar ta rufe ido ta hana su a gaban mama dani. Bayan fita na mama take mata magana take cewa haba Saade ban san ki da wanan mugun rayuwan ba. Tace mama ai dole ne ya kawo hakan nan dai takawo wa mama dalilin ta mama dai tana sauraren ta har ta gama maganan ta. Tace amma kinyi kuskure wallahi Saade yau ina kwakwalwanki ya shiga da tunanen ki da har kike wa yarinyar da kika raina da hannun ki kika bata tarbiyan da kike so tayi koda a bayan ranki ne ? Wanan bakin tuhumar da zargi ai wahalal da kanki kikeyi da zubarwa kanki daraja a gun yar kankanuwar yarinyar da take jin ki fiye da kowa a duniya. Dake nan mama yanzu ai Rama ta wuce sani na don ta samu wanda suka fini ke kike daukan ta a yarinya mama. Yarinya ce zatai kokatin rabani da mijina ta na kokarin ganin sai na koma baya gun mijina daga taimako sai abu ya koma tsiya kuma ? Eh lalai kin ko samu matsala babba don dai ni ko ga wani ban taba tunanen haka ba a gareki balle wanan yarinyar Rahama. Duk yadda mama taso ta kwantar mata da hankali anty taku fahinta hakan sai dai ta nuna mata bacin ran yadda take saka har da yara a cikin kishin mu . Ganin bata da niyar yarda yasa mama tace da safe zata bar gidan idan Allah ya kaimu don bazata zauna tana ganin wanan irin cin fuskan ba haka da anty ke min. Daddy ya shigo gaida mama ya samu mama na fada da anty din, yake cewa mama gaya mata dai na rasa inda halin Saade ya boye har ta amince wanan yarinyar ta kai ta ga wanan zubar da mutunci. Da sauri anty ta dakatar dashi tace kaga idan zakai maganan ka kayi amma ka daina sako Falmata a zancen ka kadai hanata shigo maka gida kan matarka ko kuma ta bari ba sai ka barta hakana ba. Nan suka fara sa insa a gaban mama din dashi hankalin mama yai matukar tashi tana jin yadda anty ke mugun aiban ta ni abin ba dadi ko kadan. Da kyat anty ta samu ta sashi ya fita tun fitan shi bara sake magana da anty ba ta mike zuwa dakin da take sauka a ciki. Ina shiga daki na kuka na zauna nayi sai da na gaji na share hawaye na ni kadai a dakin don nasan tunda har mama tai magana anty bataji ba abin yayi nisa ke nan. Tun da safe sai ga mama har part dina inda ta samu na shirya zan fita ina saye da lapcoat a jikina da cup din tea ina dan kurbawa Gajiye da Fatima suna zaune suna kallo don har sun gama duk abinda zasuyi ko. Muna ganin ta shigo ne duk muka mike muna gaida ita ta zauna sai mukai shiru na dan wani lokaci. Can ta ambaci sunana tace Rahama abinda nake so dake shine kici gaba da hakkuri don shi ramin karya kurare ne bai dorewa don na fahinci an riga da an zuga Saade don haka ni yanzu sai dai ke da kuke tare a nan na kara baki hakkuri kawai. Nace mama babu komai dama haka zama ya gada zo mu zauna zo mu saba watarana kai da mai shi. Tace jiya abinda tayi a gaban minin ku banji dadin shi ba ko kadan ni tsorona kada wanan shuumar ta cuta mata ta inda ba a sani ba. Gashi ta kawo mata wanan munafukar ta zauna da ita a gidgida Allah kadai yasan irin abinda suke gunguma mata a tsakanin su. Gajiye tace nima abinda nake tsoro ke nan wallahi amma ita hajiya taki ganewa nace insha Allahu zan saka ido don ni ba zan yarda na biye mata ba haka. Nan dai mukai sallama da mama din bata kara kwana ba ta bargarin ko anty din ta saduda amma ko a jikin ta don ta shiga tarko ko . ********* ********* ********* Falmata tagama duk shirin da take son yi a kan anty don haka ta shirya fara aiwatar da nufin ta gareta. Ina dawowa daga school da yamma don yau ban tsaya an karasa dani ba don bana jin dadi tun safe . A daidai kofan mu naga mai Napep ya sauke yar aikin anty tafito da wani irin katon jarka irin na mangyada ko manja din nan. Da kyat ta ciciba zuwa cikin gidan ina mamaki ko may ye a cikin jarkan haka ta dauko mai nauyi ta dai shige dashi wurin su kai tsaye. Ban shiga ba don na rage shiga yanzu sai da dare bayan na gama magariba kafin ishai na dan lekata don jikina ya dan sake min lokacin. Ina shiga na samu matar ta tsiya wanan abinda ta shigo gidan dashi da yamma ta mikawa anty shi. Ta amsa zata fara sha na shigo falon nakai kallo na ga abin bakikirin da shi haka ta kurba tana bata fuska na gaida ita naga bata ji dadin shigowa na ba na gan ta a hakan. Ni dai na gaida ita na juya abina ina mamaki ko may ye wanan abin da anty ke kinkima ma cikin ta oho ? Muna samun hutu daddy yai tafiya dani sai da mukai wata daya da sati biyu muka dawo nayi kyau sosai gashi da mun dawo bukin Gajiye da Fatima za, ayi shi. A lokaci duk wanda yasan ciki zai gane ina dauke da ciki a jikina sai dai su matan gidan gaba daya idon su ya rufe basu gane ba. Sai ranan da mama Laraba ta shigo ta zo akan maganan auren son shi ya kirata tazo maigidan don bai abu har yanzu bada ita ba. A falin na samay su zaune suna hira na shigo gaida ita tana ganina tace a, a ikon Allah abu ko yayi kyau sosai wallahi ashe na dade rabon da na ganki sarakuwa na ashe abin arziki ya samu haka har ya nuna ban sani ba ? Da sauri gaba dayan su suka mayar da hankalin su a kaina cikine zaune a jikina kuwa dagwas dashi dan wata shidda da kwana ki har ya dan turo dayake na farko ne a gare ni baiyi wani girma ba sosai. Gaba daya falon yai shiru na durkusa har kasa ina gaida mama tace a, a haba tashi tashi kina wanan matsayin inake ina durkusa kada ki haiho min da igiya a wuya. Daddy yai murmushi yace fada mata dai mama don Rama bata jin magana wallahi haka nake fama da ita kan kula da kan ta. Nai dan murmushi na dago na dan sakar mai harara irin na masoya nace kai daddy duk wanan kokarin da nake kuma sai an kai kara na gun mama kuma ? Yace wani kokari kin dai ji abinda mama tace don Allah ki kula Rahama ni ina maganin hutu zan daukar maki ki daina shiga asibiti har ki haihu. Humm, umm inji Hindatu lalai abu yazo ga masuyi ke nan shi cikin ma har wani abin ado ne dashi kuma ashe. Zulfa tace ai ba ayi ba yanzu za, ayi ashe mugani ashe an samu karuwa ake faman boyon shi gare mu to Allah ya ingata. Amin inji daddy da mama ni dai kaina yana kasa Anty na daki a nade don jikin ta ya dawo ba dadi yanzu amma haka take nukurkusa dashi. Daga bakin yar aikin ta da sukai gulma da hanne ta samu labarin cikin jikina sai ga mama kuma da zata tafi ta shigo tana mata murna ashe an samu alheri ne Allah ya raba mu lafiya. Amin kawai tace wa mama din don jin maganan take kamar zata shude a lokacin ranta ta rasa may ke mata dadi. Ranan kan gidan kamar an aiki masu da mugin labari ko wani part zancen cikin suke suna mamakin yadda basu gane ba sai da mama tazo sukaji a bakin ta. Bukin saura sati uku ayi shi jikin anty ya tsanan ta mata ina shiga gaida ita duk da ba fuska a gareta amma haka nake shiga gaida ita na dan zauna na dan lokaci. Gashi ina son na taimaka mata amma babu daman yin haka a gare ni ganin bata da lafiya yasa mai aikinta yin abinda taga dama sosai ta fito da kalar ta a fili. Yaran basu da shakat ko su walla su da gidan uban su yakai har ta fara dukan yaran da sun danyi ba daidai ba. Haka yasa na rufe ido ranan da na samu ta daki Amira uwar na kwance babu daman magana nan na rufe ido nai mata tas nace idan ba zaki iya hakkuri dasu ba sai ki tafi. Har nagama na zaci anty zatace don may nai mata haka amma sai banji tace dani komai ba naja yaran nai masu wanka nabasu abinci a part dina sukaci sai barci. Zakaji tana kiran saliha saliha amma sai ta kyale ta hakana har tagaji ta barta tace bata zuwa ita tagaji wallahi. Haka muka wuce muka barta a cikin matsala muka nufi kauye wurin buki satin mu daya amma ina buga mata waya akai akai naji lafiyan jikin ta. Na samu na shawo kan mama Altine taje ta duba anty bata ki ba ta shirya muka zo tare yadda muka barta daga ita har yaran mun samu abin ma karuwa yayi sosai. Sai da nai kuka yadda na samu yaran sun lalace na samo wata yar aiki diyar lami kawar mama altine da Innata. Gajiye a cikin gidan zata zauna a boys quarters inda akaba su tace basai na dauko mai aiki ba zata kula dani haka na amma dole na nemo wata da zamu zauna dindindin a part din tare dani. Mama Altine sai kuka take cikin tashin hankali dole aka je asibiti da ita ba laifi ta dan samu sauki kwana biyu. Yanzu muna dan samun saukin a zaman mu gashi cikina ya gama fitowa fili sosai kowa kuma yasan da akwai shi. Bayan kaman sati uku har na walwale ga jigilan bukin da nasha ina barci cikin dare naji ana buga kofan mu sosai da karfi. Na yunkura na tashi da kyat kaina babu ko dan kwali na fito dasauri muka hade da Aisha da na dauko take cewa anty tun dazun ake buga muna kofa da karfi haka. Sai da na tambaya da waye naji muryan mama Altine ne na bude da sauri nace mama lafiya dai ko ? Tace ina fa lafiya Rahama jikin antyn naki ne ya tashi wallahi abin ba dadi ita kuma wanan shedaniyar nayi ta da ita tace wai bazata fito ba dare yayi gashi ni kadai ne a shiyan sai ita. Da sauri na kwasa sai dakin yadda na samu anty zaka dauka ma ta mutu ne wallahi na fashe da kukan tashin hankali sosai. Na kamo ta ban ko damu da nauyin da nayi ba na fara bata taimakon gagawa wanda ko asibiti muka tafi shi za, a fara bata a can din. Allah ya taimake ni ta nisa da karfi na rugomay ta ajikina ina wani irin kuka mai tsuma rai sosai. Can dabara ya fado min nace mama ta miko min wayan anty dake aje gefe na kira maigidan yana ganin kiran karfe biyu da mintuna ya dauka a cikin tashin hankali nake fada mai halinda take ciki. Ai ko minti biyu bai dauka ba sai gashi dakin yana ganin ta yace yaushe abin yai tsanani haka mama tace wallahi lafiya muka kwanta da ita don har ta sha magananin ta fa kafin mu kwanta din. Asibiti aka nufa cikin daren nan dole da ita take aka bata gado naso na bisu amma daddy ya rufe idon shi ya hana ni yaran na tayar muka nufi dakin mu da su hakana. Na rufe dakin anty na wuce da keys din wuri na ranan dai haka gari ya waye muna tunda safe har na shirya da abin karyawa na nufi asibitin da take. A cikin tashin hankali muka samay su sai bincike ake a kanta daga karshe zuwa karfe daya likitocin suka gano wani magani take sha yai mata wanan illar haka ajikin ta sosai don har ya fara bata mata kayan cikin ta ko. Maganin da take sha likitoci ke son suyi bincike akai an kwaso sin duba amma duk basu da wani illa sai abin ya daurewa mutane kai sosai. Can anata magana mama tace akwai wani wanda naga wanan yar aikin natsiyaya mata safe da yamma koshi za, a duba a gani ne. Cikin mamaki daddy yace wani irin magani ne wanan nace lalai nima naga tana yawan shan shi don nasha ganin ta dashi da dadewa. Daddu yace a je a dauko tare muka tafi mun samu Saliha tana kwance ta kure volume din tv tana kallon raye raye. Cikin fada daddy yace what noses is this a gida na wanan abin ke faruwa haka kuma mai shiya na kwance rai a hannun Allah ke kina nan kina holewar ki. Part din na shiga dubawa inda Allah ya taimakeni na hango jarkan maganin can an boye shi cikin wani lungu na tsiyaya a wani gora Saliha na kallo na zamu fita take cewa dani Rahama bani key din dakin hajiya zan gyara ne. Nace abar gyaran sai ta dawo ayi amma ba yanzu ba kan muka fice daga gidan da maganin muna hanya daddy sai kallon maganin yake yana mamaki shi. Yace yaya ma za, ayi mutum mai hankali ya dirkawa cikin shi wanan mugun abin haka ne wai ? Nace ni kwata kwata ban yarda da wanan maganin ba ma daddy wallahi amma dai bari a bincika a gani kawai. Sun shiga dashi a cikin dakin bincike mun kuma samu taji dama numfashin ta ya dawo normal yanzu ko. Nan dai muka zauna likitoci na shigowa duba ta akai akai bayan fitan babban likita ne nace mama kinji waban matar wai na bata dan makulin dakin anty zatai gyara a ciki . Mama tace injin baki bata ba dai nace gasu a jakkana ai nifa mama ban yarda da mutanen na ba don zasu iya cuta mata gaskiya tace Allah dai ya kyauta ke dai Rahama. Doctors suka taru inda suka kira maigidan tare ya shiga dani mun samay su a zaune bayan gaisawa ne suke tambayan wanan maganin da aka kawo daga ina aka bata shi ne wai ? Yace bai sani ba sai babban likita yace to a gaskiya masu binciken mu sun yi bincike sosai a kan shi sun gano cewa an hada sanadarai ne masu matukar cutar da dan adam a cikin sa.. Don haka maganin ya cutar da ita fiye da tsanmanin kowa don ma anyi mamakin yadda mutum zai sha shi ya kai har war hakan nan bai mutum ba. Dole sai an binciko mai hada shi kafin ya cutawa sauran al,umma daga baya don yanzu Allah kadai yasan wanda aka cutawa dashi hakana. An bar maganan ga sai an nemo wanda ya bata shi dole kafin ai wani abu akai da haka aka mike kowa ya fice office din. Muna fita nace daddy Saliha itace ta farko da zamu fara tuhuma don ita ce ke daukowa tasan inda ake karbo shi dole. Nasan kuma zata iya gudu idan ta fahinci akwai matsala da sauri yace bari ya bugawa maigadi waya ya tsare ta karta gudu. Sunyi magana da mai gadi yace yanzu kuwa yaga wanan matar da ka hana zuwa tazo sunyi magana ta shiga gida sai ya hango ta tafe da sauri yace gata nan zata fito da kaya Alhaji yace tsare ta har in zo yanzu. Bamu bata loiaci ba ya dauke ni police station ya tsaya yai reporting aka bashi yan sanda da mota muka nufi gidan. Kafin saliha ta karaso get din yasa sakata da key ya rufe ya kada aljihun shi tana zuwa tace dashi bude min na fita yace ba ko gidan nan ba. Wayan ta yai kara ta dauka take cewa gata nan bakin get maigadi ya rufe kofan da ita ai a ciki ta wayan akace da ita ke bazakiyi yadda zaki fito ba ki mashi masifa dole ya bude maki ai. Tun daga nesa muka hango wata bakar kamri a kofab gidan sai dai maishi na hango motar daddy yaja tashi motar yai gaba abinsa. Tare da yan sanda muka shigo Saliha na ganin an bude kofan ta yunkura zata fice aka cafketa. Ciki na wuce ban bisu ba nasa mai gadi ya dauko min jakkar data cika taf da kayan anty ta sace zata gudu dasu. Gajiye ce ta zazzage duk kayan ne masu muhinmanci ta kwasa na anty zata gudu da su dama. Tun nan nasan akwai magana kaddara bai kiran mutum yace baya zuwa ke nan don anty takimu tace mu muggaine ta jawo muggan gaskiya a jikin ta sun cuta mata. Falon yai kaca kaca duk ta bincike mata kaya dagani kuma ba ranan bane tafara diban kayan uwar dakin nata. Da farko Saliha taso tasa taurin kai, taki fadin inda take daukowa Anty maganin sai da ta taji matsi ne take fadin ai wurin wani maimagani ne take zuwa karban mata maganin. Yan sanda sun tabaye ta wakai anty gurin ta nuna ita bata sani ba ita dai ana turata ta karbo ne. Tana cikin handcuffs aka tasa ta a gaba sai gidan wani mutum shi kadai ne a gidan bai ma tare da mace yaso ya musa amma daya ji matsin yan sanda tambaya na fito mashi ta ko ina take ya amsa da lalai wirin shi take karba mai maganin anyi ciniki akan dubu dari biyu da hamsin da ita. Inda yace da farko shi yaso ya taimaka mata ne sai daga baya wacce ta kawota ta dawo daga baya da wani bukata ta nun ka mai kudi masu yawa tace tana son ya dinga saka guba da zaiwa matar illa a cikin ruwan sanyi yace shi da farko yaso yaki amma daga baya da ya fahinci matar yar duniyace dole ya amince yake mata yadda take so don in ma baiyi ba wani zatakaiwa yai mata aikin. An tambaye shi damay damay yake hadawa aciki ya lissafo wasu itatuwa masu cutawa yace sai yake dan zuba kayan yaji don ya kawar da kamshin iccen garesu. Tambaya sosai akai mai inda yai masu bayani yadda suka gamsu yake cewa shi gidan matar ne bai sani ba sai dai yya masu kwatancen ta da motar ta tare da basu lambar wayan ta. Shima aka hada dashi aka rufe tare da saliha da tai bayani kan irin cutar uwar dakin nasu da suka dade sunayi wacce wata matace ta sata akan yin haka din gareta. Don ta sha ji matar na cewa sai taga bayan Saade don da ita zata fara kawar da sauran ba abu bane mai wuya a gareta. Sunan matar aka tambaya tace hajiya taoe kiran ta da shi amma taji Saade na kiranta da Falmata ne. Falmata daddy ya nanata sunan yace dama nasan za, a rina ai don Falmata bata bin Saade haka ga banza. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 65 Nidai a bangare na ba wani shirin suna nake ba sai zarah ne ma tazo min da zancen abinda zamu yiwa kawayen mu idan sunzo kudi na bata da buhun shinkafa da sauran abubuwa sauran da babu zata je ta saya ne can. Don ni ba wasu kawaye ne dani ba can sosai ashe abin ba hakana bane ance wanda yariga ka kwana yana riga ka tashi ita Zarah ta san kwanan wasan. Ranan daren suna sai ga sakon kaya wanan matar mai aikin anty ta shigo dashi wai anty ce tace a kawo min kayan baby ne masu kyau sai turamay zanuwa guda goma. Nan gardama ya fara wasu suka ce wai a mayar mata a dauki kauan baby din kawai wasu kuma sukace wai duka za, a mayar mata dasu ai abinda ba don Allah akeyin shi ba azo ana maka gori daga baya. Duk sai da na bari sin gama zancen su nace bazan mayar ba kada fa ku manta Allah ne ya kaini ga wanan matsayin ta sanadin alherin wanan boyar Allah. Don may baza mu jinkirtawa hukuncin Allah ba kaddarane fa yana a kan kowa duk wanda Allah yaso da jarabta. Nidai Rahama bazan taba manta halarci ba a rayuwana komai tai min da nai hakkuri ban rama ba bagashi Allah ya nuna mata gaskiyan abin ba. Don haka cin fuska baida kyau ni ba chof and clean your mouth bane bazan taba mantawa da halarcin ta ba a kaina don tazo ta canza daga baya. Attu tace kin yi gaskiya nima ba zan so ace amayar mata da kayan nan na tunda ba marasa godiya muke ba. Mama da Attu ne suka tafi wurin ta sukai mata godiya inda suke fada mata cewa ai dare yayi ne shiyasa ni ban samu shigowa ba wurin ta. Washegari tun da safe gidan ya fara cika inda bakin arziki masu zuwa taya mu murna kamar yadda idan an haihu akeyi a ko ina ranan suna. Tun safen nan Zarah tafara zuwa da masa da ta dauko daga gidan Anty Amina da miyar shi sai abin sha da ta shigo dashi. A lokacin ina daki muna magana da Attu da mama sai ga Zarah din yake fada min abinda ta kawo nake cewa da Gajiye ta aika a kowani shiya da masan ina lake da yaran anty na da suke tare dani tun safe. An kai kowa ta karba ba wani fitina a hakan da sukayi haka yasa duk abinda aka kawo zance ta aika masu dashi zuwa goma na rana bakina suka iso garin. Sam banyi tsanmanin zuwa su ba sai gasu da yawa su ashe bus daddy ya tura masu dashi ban sani ba. Nan na shiga murna da ganin su na ma rasa waye zan tarba a cikin su don murna can bayan Larai na hango mama Laure tana kalle kallen shiyan nawa cikin damuwa da sauri na karasa gareta ina murna da zuwan ta sai dai ba wani fuska sosai dariyan yake take min kawai. Har da amaryan babana ashe akazo nan guri ya kaure da murnan ganin su nasa Fatima ta bude masu dayan dakin da bamu amfani dashi duk da akwai komai a cikin sa nan suka shiga da kayan su. Maman Altine ma tazo don duba jikin Anty data dawo daga waje sai da sukaci suka sha ne mama amaryan babana tasa Fatima ta kirani. Nan take min bayanin abubuwan da sukazo min dashi nayi mamaki kokarin da iyayyena sukai min haka. Zuwa karfe daya yan gari suka fara shigowa sai da hankalina ya daga don ganin yawan taron da akai min. Ana tsaka da shagalin taron suna ne mukaji hayaniya ya kaure wai ashe hindatu ce ke fitina don may za, a yanka shanu da raguna biyu aikowa da ta haihu rago daya ya yanka mashi. Daddy baiyi magana ba sai yan uwan shi ne suka tanka mata don Aisha ce tace da ita idan ci gaba yazo wa mutum ana son ya canza lokacin haihuwan ki daban wanan daban. Shi ya bata haushi nan suka raba gari a tsakanin su har yakai yan uwanta sun so su saka baki fitinan yai nisa sai da daddy yafito da kan shi ya tsawata masu suka bari. Lokacin da kawayena suka fara zuwa sai wiri ya rude da gulma a yan garin mu suna mamaki wa yan nan matan yan gayu wai ace kawayena ne su. Gashi duk wacce zata shigo da ledan ta na gift zatazo min duk wanan jigilan da nake bai hanani yawan zuwa duba lafiyan anty ba ina kuma shiga na bata magani idan time yayi. Walima sosai mai gyara harka ta hada min inda aka gaiyyato malami yazo yaiwa mata wa,azi akan zamantakewan aure a wurin da hakkin iyayye da yayan su kuma. Nan ma anci ansha anyi photuna aka kuma watse lafiya ranan yan garin mu suka so komawa amma yamma yayi nace su bari su kwana da safe akaisu kasuwa sai su tafi. Sunyi amanna da shawara na haka suka baje akaci gaba da sha, ani dasu sai dare kawaye na kowa ya kama gaban shi nan aka shiga gyaran wurin dan a samu wurin kwanciya. Ni dai har akaci aka sude banga ko mutum daya ba daga ban garen matan gida banyi wani dogon mamaki ba don nasan za, arina dama da hakan. Muna daki ne zaune ni da su Rukkaiya da Suwaiba daddy ya shigo part din bayan ya gaisa da mutane a ya nufi dakina din. Sun gaisa da yan uwa na kuma gabatar mai dasu tunda sunayen su yake ji sai yake tambayan su mazajen su ? Sun fice sun bamu guri mu gana dashi nan yake tambayana muna dai lafiya ko ban tare da wani matsalar komai ko ? Nace lafiya muke sai yake tambayana may za, abawa yan gatin mu idan zasu koma, ne yace wancan karon da anty ki mukai shawara, sai nace ko yanzu ma da ita zaka kara shawara daddy aita inda aka hau tanan ake sauka . Yafice zuwa dakin anty ban san yaya sukayi ba sai yake cewa dani ta na fada mai kawai abinda ya dace nan na fahinci akwai matsala ke nan nace dashi yabasu turamay da dubu biyar din su ashirin da biyu ne dama sukazo har kanne na maza da akazo min dasu su biyu. Washegari sai ga Anty Aisha da kyautan tukwaicin ta kawo masu nan aka shiga murna naba mama Laure da amaryan baba suwaiba da Rukaiyya zanuwa a boye kada sauran ran su ya baci. Rukaiyya na dankawa duk wanda yagani yai magana sai tace kayan sako ne zatakaiwa wata don nasan idan ba ita na bawa ba wani zai iya bude ledan yace ya gani a hannunta. Wuce wan su yasa naji wani irin kewan su ya kamani sun so tafiya dani gida amma daddy bai yarda ba yace ba al, adan gidan shi ne hakan ba sai dai duk wanda zaizo ya zauna dani yana iya zuwa. Don hakane aka barmin Attu da mama Abu matar maigari su zauna dani a dakina kamar yadda ya umurta din. Yan suna duk wanda yazo yaga yadda anty ta soye sai a koma gefe a dinga tsegumin hakan . Tun washegarin suna ban zauna ba ina kokarin kula da anty duk da ba wani karfi jikina ke dashi ba sosai amma haka nake daurewa ina bata kulawa mama Altine ma bata koma ba tana gidan tare da ita. ********* ********* ********* Dan hutun sati biyu kawai na samu nafara fita makaranta don saura wata shidda in kammala karatuna. Ban zuwa da yaron sai dai yanzu dole nakan dawo karfe biyu in bashi nono in koma don abin ya taru yai min yawa akaina. Ba girki nake ba shiyasa na samu saukin fitinan matan gidan don ba ruwa da zancen kowan su sai dai mu hade wani lokaci a compound din gidan kowa ya wuce. Ranan sai ga maigidan ya kira mu a falo don har anty saida ta halarci wurin nice na shigo a karshe ina dauke da baba a kafada na. Ina shigowa duk suka mayar da kallon su akaina sallama nai masu na samu wuri zan zauna naji daddy yace miki min shi nan mu gaisa. Yana karban shi yake cewa babana yaya naga kana ramaywa kuma kaida kafito da girman ka yanzu naga ya fada kuma ? Humm, umm ikon Allah dai bai karewa a duniya muna dai ganin mamaki kan agidan nan yaya za, ayi dama yaro yai kiba ido yai mai yawa haka. An haifi dan gwal sai wani faman tarairaya shi ake kamar shine farau din zuwa gidan nan kafin wasu hindatu uwar rashin mutunci ke maganan. Daddy yai murmushi ya kaiwa yaron kiss a fuskan shi yace bashi bane farau sai dai ki sani wanan babana ne sai dai kuyi hakkuri don ba mai wasa da alamarin mahaifin shi. Tanan kuma aka bullo muna ai magana ace tsohon gida ne ba mai bakin takanwa akan tsohon gida. Ina jin su nai shiru ina duban wayana dake a hannu na sai naji daddy yace bana son abin jawo magana please. Yace na kira kune don ina son kowa takawo min sunayen mutum uku da zasu sauke farali a ban nan isha Allahu in an hada ya tashi mutum goma sha nawa mutum biyar sun kama sha bakwai haka nai casting din plan dina. Gaba daya falon kowa yai shiru baka jin motsin kowan mu sai can daddy ya soma wasa da yaron dake hannun shi. Zulfa ce takawar da shirun da cewa amma yayana mutum uku dadai ka kara muna ko daya ne ko ? Ni ba mashi ba yadda duk kan mu muna da bukata muma ai banji an anbace mu ba daga tafiyan ko ana nifin har mu ke nan wai ? Baidai yi magana ba sai anty ne tace shin kowan mu kujera uku daidai komai sai lokacin yace Saade so kike na wata yafi na wata yawa ne komay ? Ke kuma dake fadin gar kukuna da bukatan zuwa ai idan zaki koma ne sai ki shirya ki dauki kujera daya daga ciki ko. Zulfa idan har baki gode da ukun dana baku ba kina bukatan kari zaki iya karawa da kudin ki ai zaki iya ko ? Nan kowan su ke magana mikewa nayi don agajiye nake nace mun gode daddy Allah ya saka da alherisa yasa badi afi hakan . Yace Amin Rama nagode na nufeshi zan karbi yaron yace barshi zan kawo shi idan nagama ganin shi. Ina ruwan dan baka saba ba na kauye ya samu burodi toshine may son kin nuna ke wai ta kirki baki korafi ba akai tunda ba a saba ganin kyautan kujera ba. Hindatu ce ke wanan maganan nace da ita cikin sakin fuska shiyasa ai nake godiya wanda ya saba ma naga ai ya karba bai mayar ba. Aikin banza ke nan ashe da so kike nace ban so ki kara da naki kikaiwa mutanen kauye ko ? Nace shi aikin Allah da tallaka da mai kudi duk daya suke a wurin ubangiji ko ba a bani kujaran ki na karaba nagode da wanda aka bani tunda ban saba gani ba gashi yau Allah yakaini ga gani da raina. Ina fadin haka na barsu a falon kowa ranta bai mata dadi ba don kowa da abinda ke damun shi ina tafe ina mamakin haleya irin na wasu. Ta yaya za ai ma alheri mai tarin yawa haka amma ace mutum wai bai gode ba har ya tsaya korafi haka ? Jama, a duniya mai na kashewa matan daddy ne dukkan su uku suke hattara na haka ne don nasan kowan su zargin ta ya shafe ni. Ni may zan masu a rayuna nayi fari a gun su yanzu ma ayi muna abin arziki nayi godiya yazama kuma laifi don har anty na bataji dadin kalman godiyan danai amfani dashi ba a gurin. Bayan na dawo daki na kwanta sai kuma tunanen yanzu wa zan bawa wanan kujeran kuma na san dai Inna ta da Babana suna daga ciki insha Allahu to dayan kujeran fa kuma ? Maigari a, a ina Attu dai ko mijin ta kakana namiji don ban ko kawo zancen wani ba a fanin mahaifina don ba damuwa sukayi ba damu a baya. Dan dama yanzu da sukaga baba nada dan rufin asiri suna dan sha, ani dashi don bukatan abin hannushi. Can kuma na koma tunane watau daddy yana da wadata hakane ashe da har zaiyi kyautan kujerun makka har haka da yawa. Sam bai nuna yana da zarafi hakan don shi ba mutum bane mai son yawan karyan duniya mutumin da hayaniya ma aikine a gareshi bai da ko yawan abokai haka agari. Idan harkaji yace wani abokina ne to tabbatar wani harkan business ne ya hadashi damai shi din. A hankali na lumshe idanuwa na ina kwance rairai ina kallon sama banji shigowan shi ba sai kafana danaji anja min. Na bude idanuwa na daddy ne a tsaye saman kaina rugumay da yaron yace tunanen may kikeyi haka a kwance ? Murmushi nayi na yunkura zaune ya miko min yaron nakarbe shi ina gyara mai kwanciya don yaton barci yake yi daya shigo dashi. Nace daddy mun fa gode yace da akai may kuma again ? Nace makkan daka ba yan uwan mu mana yace godiyan bai isa ba ke nan har yanzu ina son mutum wanda idan an mai alheri ya sani ba wanda zakaiwa alheri yai maka korafi ba naji dadin godiyan ki Rahama don haka mutum hudu zaki bani daga bangaren ki. Da sauri na dago kaina nace mutum hudu daddy yace haka nace Allah nagode ma na fadi a fili nace mahaifana da kakanin na nake son suje daddy. Yace wasu daga ciki ke nan nai saurin cewa Attu da mijin ta mana ai banda wasu kakan nin da suka fi min su a duniya don ni dasu na bude idona. Anya Rahama baki son kai ba anan don banji ki sa kowa daga bangaren mahaifin ki ba sannan kuma in ga kara aiki hada da maigari su tafi ko ? Nasan maigari ya cancanci hakan agare ni amma kuma aida girma na ya gani ga wayanda sukai wahala dani kuma ma suke a cikin yi har yanzu din. Daddy dai bai min magana ba yabar dakin washegari da safe bayan nai wanka na shirya naje part din anty don na gaida ita tun daga kofan shiga dakin ta nake jin muryan ta daga daki tana magana sama sama. Akan may zakace komai daidai da Rama zaka dinga min idan da nasan wanan auren cin amana zai koma min tsakani da kai da ban hada shi ba wallahi. Duk irin rawan kafan da kake akan yarinyar nan duk ina kau da kaina naga abin yanzu yana son ya wuce wuri kuma hakana . Saade wai may yasa kika canza gaba daya ne hakana please halin da ban sanki dashi ba a baya yanzu shine kike kirkirowa kan ki. Tace dole ne na nuna maka abinda ka dauko yi min abaya akan sauran matan ka nai magana ka daina shine yanzu ka dawo da yin shi akan Rama. Ke Saade ya ishe ki haka na gane ke baki san ana tausaya maki ba baki tausayawa rayuwan ki balle na wani. Na fahinci baki kaunan a zauna lafiya har may naiwa Rama wanda ke ko ku ban maku shi ba a gidan nan. Ko ku daban kuke gare ta da zan mata abu a kasa da ku nagane abin naki akwai son kai sosai a cikin shi. Kamar yadda kike da iyagiya uku akan ki nawa haka itama take daure dashi a kanta don haka bazan wullakanta kowa ba don wani yaji dadin rayuwan shi. Abinda na bayar ke nan wa kowa don haka in zaki bani list din ki ki bani idan kuma bazaki bayar ba duk daya a waje na. Ke yanzu ba abin kunya bane agare ki ace kina wanan bakin kishin akan yarinya karama da kika tayar da hannun ki duk kin bi kin sakawa kan ki fitina haka kan abu daya. Maimakon in shiga sai kawai naja kafana na juya na fice daga gidan ba tare dana bari sun san naji maganan su ba. Sai dai na tafi da tunane da mamakin anty a raina wai shin haka kishi yake yasa mutum ko yana cikin wani hali bai tunane bai tunanen makomar shi, sai yayi wanan halin . Ko dana dawo gida haka kawai sai na fara jin nima dan tsanar ta a raina kamar yadda yanzu nasan kishi yasa bata kauna na ko kadan sai dai dariyan hakori kawai. Zama nayi da Attu da mama na fada masu komai sai da suka gama jina suka ce dani dama tana da zazzafan kishi ne sosai rashin hada miji da itane yasa bazaki gane ba. Ba wai bata son ki bane kishine kawai ke cin ta kada ki biyewa rudin shedan yataru ya ruda ku gaba daya har kukai ga abin kunya duniya a karshe ke zata zaga ace tai maki halarci yanzu kina son ki butulce mata kuma. Ki bita da halinta sai a zauna lafiya yawan son mijin ta ne yake sata yin hakan ba komai ba sai dai mu bazamu ce kada kibi mijin ki ba don kada ranta ya baci. Ai itama musulmace tasan abin da sharia ya tana da akan aure in ba so take ya karkata a kanta ita kadai ba ya tashi da shanyayyen bari gobe kiyama. Na nisa ina cewa ni abinda yake damuna bayan wanan shine duk kan su da babu mai kaunata a cikin su. Attu tace shine kishi ai yadda basu kaunar ki hakane ma basu kaunar junan su kowa kan shi ya sani a fagen kishi ai. Nan dai sukai ta bani musalai ina zaune ina sauraren su daga karshe nai masu sallama na shige dakina na kwanta. Waahegari ma kamar na wuce abina sai dai na daure na shiga muka gaisa da ita sunan mun shirya ne amma ba kamar da can baya ba muke da ita. Don wani lokaci sai ta dinga daure min fuska wani sain kuma zata sake kamar ba ita bace muyi hiran mu lafiya. Yau ma fuskanta a gimtse yake babu walwala don haka sai ban tsaya ko tambayan ta komai ba nima nasha toka nai mata sai na dawo nafice. Bina tayi da kallo bayan na fita tana fadin mutum abin tsoro ne wallahi yanzu yariyar na tana ganin daidai muke da ita ke nan. A, a ta fara gajiya ne da halin ki tunda ke baki daukan girman ki da Allah ya baki ai ba haka take ba idan ta shigo nan take zama sai ma kin korata wani lokaci. Mama wai may yasa baki son ayi zancen gaskiya ne akan Rahama yarinyar nan baki san halinta bane sanin baya kikai mata. Mama Altine tace ina ko zan sani tundake da yanzu kuka hada miji da ita kin fini sanin ko ita wa cece ai. Yarinyar nan kina bani mamaki gaba daya yanzu halaiyar ki duk ya sake abinda bakiyi a bayane kika tsirowa rayuwan ki. Wanda ke daki yana fama da kan shi ina shi ina wani tsiro tsirkin kishi kuma kwance a daki. Au mama har ke ma gori zakiyi min ke nan ko ba mamaki ko shi wanda nake zaune agidan don shi ai abinda yake nufi ke nan dani banda moriya ya samu inda yake morewa yanzu. Aiko kin kyauta tunda kin samo mai inda zaiji dadi sai dai kuma ga shedan nason hanaki cin riban abin . Ki kawar da idon ki shiyafi maki ki koma fa Allah wanan abinda kika dauko bashi ne mafita ba a gare ki koda kina da lafiyan ma. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE KIN SANI, , , , , , 66 Kamar yadda na furta sunayen daba bayar ke nan sai dai Inna tai min magana dole aka janye tafiyan ta maigidan ta maigari ya tafi don kara. A bangaren anty abin zaiba mutum mamaki don babu dan gidan su ko daya data bayar sai kawayen ta na kut da kut tabada. Acewan ta wai ai yan uwan ta sun tafi dakyat na katsalandan na rufe ido na ce mata amma gaskiya anty idan haki bada sunan mama Altine ba a tafiyan nan baki kyauta ba. Wani kallo nake a suwa ta watso min amma nadake nace bawai nai maki karan bani bane anty ganin dacewan hakan nayi gareki . Don idan baki hakan ba daga baya abin zaizo ya damay ki, nake gani, bude bakin ta sai cewa tayi aiko ke idan ga halarci zaki iya bayar wa a naki bangaren ai. Nace idan nai maki haka ban kyauta ba na shiga hakkin zumuncin ku zan iya haddasa maku wani abu a tsakanin ku daba haka ba da zance wani nawa ya fasa ita ta tafi din. Shiru tayi batai magana ba nima naci gaba da ba yaro nono ina kallon waya na, sai can naji ta nisa tana ce Rama na gode wallahi sam banyi tunanen yin hakan ba sai yanzu da kikai magana. Nace nagode anty tace damay fa kuma nace da kikai amfani da shawara na duk da ban kai ba ban isa ba amma na tunar dake kuma kika dauka. Tace kai Rama ke nan ni fa yanzu sai kinyi hakkuri dani don ban san may ke damuna ba wani lokacin. Wani lokaci idan nai wani abin sai daga baya naga radhin dacewan shi yanzu badon kin bani wanan shawaran ba sam ban kawo mama ba ga zancen wallahi. Na mike tsaye ina mika mata yaron da ya gama shan nono ina cewa je gun maman ka na huta nima. Ta karbe shi tana cewa dani kai wanan baban fa karfi yake ji yanzu zakiga yana wani dan zabure zabure haka dashi. Dariya nai masu na ce kai amma baba idan ka wujijiga min anty na yau sai na daki kan nan naka kana ganin bata da lafiya. Tace aiko da yau kun hade da uban shi don ni da kaina zan buga mai waya na sheda mai kin dakar mai tsoho haka kawai. A raina nace yau kan yan arzikin suna akan anty nake cewa wai ni anty wani shiri ake yine akan fitan yaran nan daga primary ne ? Kai Rama har wani shiri kuma za ayi don zasu gama karatun pramary nace ai kin san haka ake yanzu wa yara ai masu buki na fadawa yan uwa don yaro yaji dadi ya kara hazaka. Tace to ai shiri na hannun ki yanzu ke uwar su nina isa nace ga abinda za, ayi Nasir yace dani ban yi daidai ba naki yafi gareshi. Nace haba anty shi Nasir din nawa za aiwa wanan shedan kuma anty tace aikin san shi hukuma ne sai lalashi. Saura sati biyu fitan yaran a makaranta don haka kamar yadda uqar tace tabar min shiri a hannuna na nayi komai ban kara tuntuban taba sai aiwatar da komai nake a kaina a cikin jikina kuma. Sai ana saura kwana biyu na dinga yawon kai gaiyyata gun yan uwa da abokan arziki wasu kuma ina kiran su a waya ina sheda masu zancen. Na buga kalanda, books da robobi sai abinci dana ba Zarah ta bayar ai muna saida dare na shiga wurin anty na sanar da ita cewa gobene fa taton yayye yaran da za, ayi a makaran tar su. Tace ai ita shaf ta manta da komai sai yanzu danazo mata da zancen ta tuna take tambaya na may zata taimaka muna dashi nace mun gode mun gama shirin mu ko. Washe gari tunda safe mun shirya zuwa wuein taron, a bangaren Hindatu ma tayi shiri sai dai batai tunanen nima na shiryawa yaran irin haka ba. Taro yakai taro muka iso wurin can muka samu wani rufa muka yada zango a cikin sa da mutanen mu suma hindatu runfar dake kallon inda muke take zaune da mutanen ta. Kusan late Zulfa ta iso don duk mun gaiyyace ta zuwa taron duk da a cikin murane muke amma sai da kowan mu ta nuna wanin halin kishi a bainan jama,a. Kulolin da Zarah ta iso muna dashi ne ya dauki hankalin kowa a wurin sai da aka gabatar da komai na kan yayye yaran inda munyi nasara yaran namu na cikin wa yanda suka samu kyauta sosai a ranan cikin dalibai sai dai babu yar wurin hindu a cikin kyauta ko daya na kokari da aka bata. Nan aka shiga raba abubuwa sosai muka burge mutane muna raba kalanda da books mai dauke da hotunan yaran aa cikin sa. Hankalin Hindatu yai matukar tashi sosai Zulfa ta baro rufan Hindatu bayan ta dan zauna tadawo rufar da muke a zaune a gurin. Ina ga yan uwan Anty sun manta da zulfa na furin nan suka shiga zuga anty wai ta sake min ina mata gaba akan sha, anin yaranta yanzu Allah kadai yasan nawa na karba a gun mahaifin su naci riba dashi kan wanan sha, anin haka. Nan ta hau ta zauna kan maganan su muna aha, anin mu dadi dadi sai naga ta fuske min tun a wurin na rasa gane kanta. Photo ma da zamuyi da kyat tazo ta shiga akayi da ita ana gamawa tabar wurin ta ki zama a karasa komai da ita. Bayan wucewan ta ne Zulfa tace dani Rahama zan so nai dan magana dake kafin a watse wurin nan ko kina da lokaci nace ina dashi anty. Muka kebe da ita tace da fatan zaki fahince ni don ba gulma bane ko zuga zan fada maki shi abu in kanayi tsakani da Allah to kayi shi kai tsaye. Yanzu ina zaune a bayana nake jin abinda ake fadi gamay dake kan wanan abinda kika shiryawa yaran nan duk da kinyi don Allah ne amma an zuga antyn ki ance kudi masu yawa awajan maigidan kinci riba dashi. Baki ganin tabar wurin rai a bace don haka nasan akwai wata a kasa nan gaba kan wanan matsalan. Nace wallahi wallahi anty Zulfa ban karbi ko kwandala agun daddy ba bai ma san da zancen ba sai daren jiya nake fada mai komai akan bukin da za, ayi din. Tace ni dai na fada maki abinda naji kuma naga ta dauka ban san may yasa take daukan zancen mutane ba haka suna ruda ta. Mun dawo gida a gajiye har a lokacin ba wani fuska a gin anty gareni nima sai na share ta kamar ban fahince ta ba. Washegari ina falo zaune da dare wanda har lokacin ban karasa walwalewa daga gajiyan jiya sai ga wayan daddy yashigo min nazo falo yana nema na. Ban je da baba ba nan na barshi wurin Aisha a goye suna kallo da Atika na fice part din. Nai mamakin ganin kowa zaune a falon shiko yana zaune ya saka laptop din shi a gaban shi yana aiki a cikin sa hankalin sa a kwance. Na gaida su na samu wuri na zauna saman kujera ni da ban damu da zama sama ba don girmama su sai gani yau na dane kujera na zauna daran. Kusan minti shidda zuwa bakwai ya dago kai yace damu ummhum kin shigo Rahama dama ke muke jiran zuwan ki. Yace don Allah hindatu ina son ki fada nawa na baki akan bukin yaran nan da akayi a jiya gidan nan ? Tai shiru can ta dago tace dubu hamsin ka bani dana fada ma a tsiwace take maganan wai ita ancuce ta. Yace ok Rahama don Allah ke kuma ina son ki fada nawa na baki da kukai naku a part din ku don ance kece maigudanar da sha,anin ? Nace cikin mamaki daddy aini baka ban ko kwandala ba don ban ma tambaye ka komai ba na dai fada ma gobe zan muyi graduation din yaran kawai na kare primary kace dani Allah ya bada sa,a kawai. Yace good cikin murmushi to ke musali kamar nawa kika kashe a sha, anin bukin da kukayi na yaran ? Nace cikin bazan iya tunawa ba na kashe yakai 100 don adashe na kwasa da nakeyi na sana, ata. Yace to Saade ina fatan kina jin mu ko, kema kuma hindatu yanzu kinji abinda Rahama din ta fada akan yaran kishiyar ta ta kashe kudi haka batare da ta tambaye ni komai ba. Balle ke da yarki ce kuma kikace kina son kudi kan sha, anin na baki. Yace Saade yanzu don Allah baki ji kunya ba wanda yai maka irin wanan abin haka har kake zargin yaci riba dakai ne ? Koma da ace ni din nabada kudin ai tayi kokari ko tunda nan kaf nasan babu wace zata iya yin haka a yanzu kai tsaye. Ai dama ba komai zan fahinta ba kuma don Rama taiwa yaran wanan don kan ta tayi ai ba don niba tunda dama tayi ne don yabo takuma samu ai tunda akwai makirci a cikin abin. Kaiyya Saade Allah ya kyauta kawai sai addua abin naki don haka yanzu korafi da hasashe ya kare ko ? Yana fadin haka na mike sai naji yace no ina zaki dakata na baki kudin ki ai tunda don yabo ake ganin kinyi badon Allah kikayi ba. Ina daga tsaye nace nibadon a biyani ba nai masu don ban iya bitan abinda akai min don Allah da zama tare nayi kawai. Zulfa ne tai magana tace don Allah dai yaya abar zancen nan tunda ba tayi bane da wani manufa don Allah tayi. Kai koma da wani manufane don taci riba bai kamata ace an mata haka ba gaskiya. Toow wata sabuwa ke nan anyi wani sabon kulli ke nan ban sani ba ashe a gidan nan yau kece mai yabon Rama kuma ? Ai ba yabo bane sai gaskiya mutum da girman shi ya zauna yana kanan magana da bai dace ba abu zabban kunya haka. Ni dai na sa kaina na fice kawai ban tsaya sauraren ta ba balle raina ya kara baci don masan idan na tsaya bada amsa abin bazaiyi kyau ba a wurin. Mamaki da takaici ne suka rufe min zuciya na nan dai sukai kaca kaca a gaban sauran da ita yana kira mata da taji kunya wallahi. Zulfa ce tace wallahi naji lokacin da Asamau ke fada maki haka a gabana kukayi shi don tsananin gulma kun manta da cewa ma ina wurin . Sosai ya nuna mata bacin ranshi daga ita har hindatu yana fadin shi wallahi sun ishe shi don korafin su ya kai mai intaha yanzu. ********* ********* ********* Wanan abinda anty taii min akan yaranta sai gaba daya ta zube min naji kawai na jaye daga harkan ta naci gaba da harkokina a gidan. Hakan nayi kuwa don gaba daya sai nake hatkokina ban shiga sha, anin ta ko kadan yaran ma da zasu fara karatun secondary bata fada min ba sai a wajen su ne nake jin hakan. Ban damu ba sai dai a kulllun ina mata fatan alheri da samun lafita idan gari ya waye zan shiga na gaida ita daga haka kuma sai gobe idan kuma na shiga. Yaron ma da nake aika mata na daina ita kuma bata tambaya ba koda gaida ita naje bata taba tambaya na ina yaron yake? Miji dai ne bai nuna min komai a bangaren shi sai ma abinda yai gaba a tsakanin mu a kullun yana alfahari da zama dani nima hakan ina alfahari da hakan gareni. Yana son dan shi sosai wanda hakan ya kara ja min bakin jini a wurin su inda suke cewa harda yaran gida wai na asirce shi akan shi. Ni dai nasan ban yi komai ba akan hakan don haka hankalina yake a kwance ban sa damuwan haka ba a raina. Gashi gaf nake da kammala karatu na haka yasa ban ma mayar da lokaci na ba ga kowa gaba daya duk da ba dadin hakan nake ji ba a raina. Inda na gode ma Allah na nemi madogara da kaina ba sai na tsaya an bani ba da na wahala a rayuwa na yanzu. Nashigo gaida ita da safe mun gaisa nai mata sai na dawo take cewa dani Rama nace naam anty na dawo na tsaya ina sauraren ta. Tace Abba ne yake tambaya na ke ko har shima yanzu kin daina zuwa gaida shi tunda kan mage ya waye ankai ga matsaya. Murmushi nayi nace anty ai ban fushi da Abba ni kawai dai naga kamar baki son ina zuwa gaida shine da nakeyi amma idan babu matsala zan shiga na gaidashi din. Tace ni ba rokoki nayi ba don kije gaidashi din don dai naga ya tambayane kwana biyu shiyasa nai magana. Nace anty koma kin roke ni aiba matsala bane don Abba kamar mahaifina na dauke shi. Tace gara da kikace kama din don da mahaifinki ne Rama bazaki taba yarda ki aure min miji kizo kina kokarin jefa ni a matsala haka ba ? Nace anty aure kikace ba zaman banza nake da daddy ba kuma auren ma aikece kika sakani yi auren dashi don haka yanzu koma may ye ni bana kuka dakowa sai ke . Ni dai a zamana dake anty ban taba cuta maki ba akan daddy kuma bazan taba cuta maki ba a zaman mu don ban mata da irin halarcin da kikai min ba a rayuwana. Duk abinda ke gudana kuma yanzu a tsakanin mu alkalin mu Allah don shine shedan komai a tsakanin mu. Ke Rama nifa bawai nasa ki auri Besty bane don ki shigo ki kwace min miji ko ki sa rayuwana a matsala nayi ne don ki dinga tallafawa rayuwana da na yarana. Amma shine har kika buge yau da haihuwa kina ganin ke kin kai matsayin da har akan ki besty zai rufe ido yana ci min fuska akan ki. Anty wanan matsalar ku ce dashi ada can nakanji na bar maki mijin ki don irin wanan halaiyar da kike nuna min a yanzu. Sai dai a yanzu bazan iya barin daddy ba sai idan shi da kan shi ya bude baki yace na bar gidan nan digo baxan kara ba zan bar maki gidan ki har ma da dan dana haifa dashi. Anty nabiki nabiki don mu sasanta a tsakanin mu amma abin yakiya a tsakanin mu aure dai nakeyi a gidan nan ba zaman banza ba kuma ke ce sanafin shi don Allah na roke ki da kada rashin mutunci mai tsanani ya biyo baya a tsakanin mu. Ina fadin haka ban tsaya ba na fice daga part din don raina ya riga da ya baci yanzu na fahinci anty dama amfani tayi dani don wani bukatan ta kawai. Ashe ba don Allah ta sani yin wanan auren ba dama don wani bukatan zuciyar rane ta sakani ban iya wuce ba school gidan mahaifinta naje. Bayan mun gaisa dashi yake tambayana anty din nace Abba dama nazo da magana ne akan anty din nan dai na fada mai duk yadda mukayi da safen nan da ita. Kai ya girgiza cikin takaici yace dani Rahama al, amarin yar uwarki sai addua yanzu kawai don ni sai nake ganin ko akwai wani abinda Saade taiwa Allah ne a baya wanda ya sa ya baiyyanawa duniya halinta a yanzu. Nai mai godiya bayan yagama min nasiha kamar yadda ya dace duk uba na kwarai, yaiwa yar shi nai mashi godiya na bar gidan. Tun ranan gaba daya ba dadi a tsakanin mu daddy ya gaji ya kawo ido yasa muna yadda na share alamarinta yai mashi dadi sosai don shine kwanciyan hankalin mu gaba daya. Bana jin dadin hakan amma ya zama dole muyi zaman yar tsama din don kwanciyan hankalin mu tunda yanzu ba boyo kowa ya gama fahinta halin da muke ciki da ita din. Allah ya taimake ni nagama karatuna lafiya na kuma samu sakamako mai kyau na alfahari dashi ga duk wanda yai karatu koda ba irin namu ba mai tsawon shekaru haka mai yawa. Ranan da na karbo takardan ban shiga part dina ba sai da nakaiwa anty ta gani ba laifi na samu yan arzikin na kusa tai min murna. Ta miko min takardan na karba nace a hankali da ita anty na gode da ba don ke ba yau ba zan kai ga wanan nasaran ba don Allah duk abinda nai maki kiyi hakkuri dani ki yafe min haka Allah ya kaddara da rayuwan mu. Amma ni bazan taba mantawa da irin alherin da kikai min ba a rayuwana don kece silar zamana a wanan matsayin da nake ciki ayau. Ko bayan raina anty bazan taba mantawa da irin halarcin ki ba a gareni don Allah anty ki yafe min ki bari nai maki biyayya irin wanda na saba maki a baya. Shiru naji tayi batai magana ba nima ahirun nayi ganin bazatai magana ba yasa na mike na dauki hand bag dina zan bar wurin tace dani. Rama nasan kina hakkuri dani sai dai gaskiya har yanzu zuciya na ya kasa yarda da alamarinki na ba bu soyayya a tsakanin ki da Besty ba abaya sai nake ganin kamar rufa ido ne kukai min dake dashi a yadda kuke yanzu. Nace ban taba cin amanan kowa ba a rayuwana kuma koda nayi ke kin sani anty zan rokeki ki yafe min akan abinda nai maki din. A zamana dake ban taba jin digon son mijin ki ba ko daidai da rana daya kai asalima ni koda kika aura min daddy ba wai ina son shi bane anty kema kin sani. Nayi ne a bisa ga kwarin gwiwan da kike bani a lokacin wanda ban san cewa da wata manufa ahskan ba a likavin a ran ki. Tace banda wani manufa a lokacin a kanki Rama don a lokacin sai nake ganin kamar kece zaki share min matsala ta ban san ba aiwa Allah shishigi ga alamarin shi ba yanzu gashi nayi abin ya koma min a ciki kuma . Nace idan kin dauke shi a haka anty ni har gobe a shirye nake da nai maki biyayya akan bukatun ki indai bai sabawa Allah ba. Tai murmushi mai kama da ansa ta a dole tace kaiyya dai Rama ai an bata goma daya bai gyaru ba ne yanzu fa a matsayin kishiya na kike wace mijina kuma ke ji da bukatanta gareshi. Don may Rama ba zanji zafin ki ba akan haka ko yaushe ganinki nake kamar kina sace min farin cikina ne a kullun kina mayarwa a kan ki. Yanzu idan nace zan bar maki mijin ki anty zaki soni kamar yadda kike kauna ta a baya can yadda muke dake. Tace Allah dai ya gyara kawai Rama ki roka muna Allah abinda yafi zama alheri a rayuwan mu yafi zancen barin gida a gare ki nace to shike nan zan ci gaba da rokon ubangiji don dama ina yi sai dai na kara kawai. Na koma wurina cike da tunanen wanan halin da muke ciki ance karshen kiyayya soyayyane to shin haka karshe so yakke ne ko kuwa namu ne yazo da akasi haka wai ? Wata zuciya ne tace dani ba haka bane naku ya hade da kishine shiya jawo maku matsala a tsakanin ku. Kishi ita anty tafi kowa kishi ke nan ake nufi ko kuwa dai a kaina ne kishin ta yafi yawan zafafa ne wai. Daddy ya dawo bayan kwanaki nakai mai takardabn nawa ya gani ya samin albarka yace yanzu saura services ke nan kuma ko nace haka ne daddy. Yace a ina zakiyi services din naki ke nan ? Sai nai shiru yace bakiji bane nace dashi anan kano ke nan tunda ina da goyo zan nema anan din. Yace a, a, a Abuja zakiyi tunda ina da gida can babu kowa a cikin sa kinga sai ki je ki can kiyi idan lokaci yayi. Nasan akwai wani sabon rikici ga iyalin shi sai dai naja bakina nai shiru kawai har ALLAH ya kaimu lokacin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE HAKAN BA ONLINE NOVEL NE, , , 67 Abin ya dan yi dama a tsakanin mu sai dai yaranta sun shiga rudu a hakan yau ace su yi min magana gobe ace dasu su fita harka na bata kwarai bace ni. Amira da yake mace ce kuma ta fara girma sai ta fara bin akidar uwar ta a kaina duk kuwa da shakuwan dake a tsakanin mu da farko. Nasan za, a rina saboda ko diya mace akwaita da saurin daukan akidar uwar ta fiye da na da namiji sosai. Mazan daine ba ruwan su zasu zo koda kuwa baba yana barci su ce sunzo ganin shi ne bani hana su idan idon shi biyu zasu dauke shima su tafi part din su dashi ne ban saka komai a raina. Sai ranan Jinior ke cewa dani little mum wallahi Amira dukan baba take idan na dauke shi kiyi mata magana ta bari. Banji dadi ba a raina sai dai a fili cewa nayi da ita haba Amira keda dan kanin ki kuma zaki doke shi may wanan yaton ya sani da za, a doke shi. Ashe ta kwasa ta fadawa uwarta wai na kamata ina zaginta akan baba nan uwar ta hau ta zauna sai abinda ta rage a bakin ta. Har tana cewa ita bataga wani da a gidan nan ba da za,a haifa wanda yafi diyanta ni har wani haihuwa nayi kodon naga shi ne na haifa da cikina zan tsiro mata da wani tsirko akan dana. Ni a baya may ye ban wa diyan ta ba wa yai min magana ai babu muguntan da ba nai masu ta sani kuma take kawar da idon ta. Nasir dake zaune a gefe yana ta cin abincin shi tun fara maganan sai ji nayi yace haba mummy maimakon ki mata fada ta daina zakice kuma wai ta doke shi. Nasir idan baka rufe min baki ba anan yanzu ranka zai matukar baci a gurin nan wawa mara tunane kawai. Mikewa yaron yayi yabar abincin ya fice daga falon nata ran shi a bace a raina nace namiji ke nan dama yaya halin yan mazan yake ko a banza. Yaton nafita na mike ina cewa anty kiyi hakkuri ni dai nasan ban ci mata mutunci ba akan dan uwan ta don bazan raba su ba dukan dai da akace tana mashi ne nace ta daina banyi wayo ba tukun. Lalai yanzu Rama bakya jin nauyi da kunya ace kina fada wai akan danki kan yan uwan shi rabawa tunda ba tare aka haife su ba ai dole a raba su. In ba shi wanan shashan da bai san ciwon kan shi ba har yanzu ita Amira ai da take da wayo kinga ta gane komai ko. Allah ya kyauta nace na bar falon cike da mamakin son kai irin na anty ita daya dace ace tayi magana akan abinda yarinyar keyi dabai dace ba wai kuma ita ke goyon bayan karya akan hakan. Ni a tunane na kishin anty a kaina zai tsaya kawai ba zai kai ga dan dana haifa a gidan idan har zatayi dubi ga irin yadda naita dawainiya da nata yaran a baya can. Amma sai gashi ita da kanta ke bada daman ai wa karamin yaro na goye wanan abin haka. Wasu kishin su na hana su tunanen ranan haduwan su da Allah, yana da kyau duk abinda mutum zaiyi ya dinga tuna makomar shi ga ubangijin shi. Kamata yayi zancen ya tsaya a iya ni da ita kawai amma yanzu na lura har Amira yarta ta shigo acikin al, amarin namu wanda hakan bai dace ba a yadda maigidan burin shi ko yaushe yaga hadin kai ga zurian shi. Ni kan tun wanan ranan bana yarda a shiga min da yaro wurin su indai ba tare dani zan shiga dashi ba kuma ko nashiga din dashi yana manne a jikina koda kuwa yannen maza sun dauke shi ne idan zan fita zan karbe shi mu fice tare. Ance riga kafi yafi magani ina hakane kada wani abu yazo ya samu yaton wirin sakaci na abin yazo bai muna kyau ba nida su baki daya. Na kan dai ta tunane a raina dacewa watau ita kishiya sunan ta kishiya dai da kowa kishi ya hada ka sai idon ka ya rufe ka aikata komai a kan ta. Yau wai ni Rahama ce ke gudun barwa matar da tafi kowa sona a duniya dana dana haifa da cikina don gujewa cutarwa daga gareta. Gashi kullun idan muna waya dan muna waya da Innata maganan ta gare ni shine yarinya kiyi hakkuri. Kin auri namiji mai mata da iyali da yawa sai kin kara hakkuri da kowa dashi da iyalin nashi, kada ya kasance kullun ki zama mai matsala a cikin su ki bari ai maki yafi ace kece mai yi din. Idan kin zama jaruma akan duk wani abinda zai bullo daga garesu ba sai kin ce zaki dauki fansa akan komai ba Allah na gani kuma shi mijin naku ai yasan komai don duk namijin da ya tara iyali yasan halin kowace daga cikin su da halin kowa suke zama dashi. Ke dai ki masu biyayya don nasan ki dashi shi biyayyan ki akan su shine zai kara maki daraja da martaba a garesu wata rana. Kin zama kamar walkiya acikin su yanzu don idon kowan su yana akan ki motsinki da takon ki a idanuwan su yake don haka ki daure ki cinye jerabawan dake a gaban ki. Kada kiyi wasa da ibadan ki dan ganin samun duniyan da kikayi addua yazo gaba da komai a tare da ke. Da fatan zaki zamo wa mijinki cikin matan aljanna sai an daure ake samun wanan matsayin a wurin ubangiji Allah ya tsare ya kare ku ke da zurian ki baki daya. Nace amin inna a sanyayye haka na wuni sukuku ranan da mukai waya da innata sai faman sakawa da warwarewa nake a raina ina neman mafita akaina. Ga dai daulan duniya da hutu a gidan daddy amma kishin matan shi ya hanani mike kafa inci shi da dadin rai kullun garin Allah zai waye da sabon fitinan da zai bullo kai. Da wuya a wayi gatin Alah ba ace ga abinda Rahama taiwa wani ba agidan yanzu ma dan dama dama zulfa don ita bata faye shiga harka na ba agidan. ********* ********* ********* Maigidan ya dawo daga tafiyan shi anty ta fara girki sai zulfa tayi hindatu ce yau zatayi kwanan ta na karshe a girkin. Don haka a washegari ni zan karbi girki ke nan ban wuni a gida ba na tafi wirin kitso da kumshi na gyara jikina tsab da yamma Aisha ta tayani na gyara part dina don gobe muna da aikin yi in Allah ya kaimu. Tunda na dawo daga gyaran jiki babu wacce ta ganni a cikin gidan don ban fito ba karfe uku muka dora girki don tuwo nake son yi don nasan shi yafi son ci sai dai bai samun hakan ne sosai. Mun gama na kwashe a kula bayan na daure a ledoji na rufe miya sai da yamma zan hada amma komai yana a tanade. Karfe hudu da rabi na dauki kayan gyara na nufi part din maigidan na fara gyarawa komai sai dana gyara shi tsab a part din na fito na koma wurina. Na hada miya ban bar kitchen din ba sai da na kammala hada komai na kwashe miyan agushi a kula na rufe. Wanka naiwa baba itama Aisha nace taje tai wanka har Atika mun fito muka saka kamshi a part din zakace ko anan maigidan zai zauna. Wanka nayi na gyara jikina tsab da yarona English wear na saka a jikina don dare yayi na tsaya a gaban mirro na kalli kaina naga nafito yadda nake so ga kasa na yasha gyara dana durawa cikina tun yamman jiya nake faman tsuma kaina. A ka idana bana shiga wurin daddy sai na tabbatar da matan shi sun gama shiga wurin shi gaida shi sannan zan shirya in tafi. Yanzu ma natabatar da sun gama shiga na dauki kayan abinci zan fice yaron ya sa min kuka don ya iya kiuya yanzu sosai dan kwanan biyun da baba fita muna tare a gida dashi na dauke shi na goya yana kuka muka fice zuwa kaima daddy abinci. Sai dai nayi rashin saa na samu hindatu a falin suna magana da shi na jera abincin tare da yi mai sannu da dawowa a lokacin. Na hada komai yadda ya dace ina duke a gurin anty ta shigo falon suka gaisa dashi yaron na kuka a bayana yace dani miko shi mana nan ga uwarshi ko zaiyi shiru idan ya ganta. Tace a, a barshi nima ba zama zanyi ba nazo ne kawai na gaida kai ai yace kama mata shi mana ta gama abinda takeyi ko. Ban da lokacin wanan gaskiya zan je na huta ne tace ta juya tafice daga falin hindatu ma ta mike tana mashi sai da safe nagama hada komai na sauke yaron na fara bashi nono. Ya sauko ya zauna yana cin abincin shi hankali kwance can dai kaina yana sade akan yaron dake shan nono yana ajiyan zuciya don kukan da yayi. Daddy sai abincin shi yake ci hankali a kwance don ba karamin abinci yake ci ba, can ya dago kai yace dani kin ko ci abincin nan ke ? Nace sai wanan yayi barci nake son na zauna naci yace wai may yasa kin san kina shayarwa kike wasa da cin abinci haka har yanzu Rahama ? Yana magana yana bude bowl din dana saka mai gassasan nama acikin sa ya jawo zuwa gaban shi yace duk kin wani bushe min a idona da gani bakya son cin abinci may ke damun kine wai haka Rahama ? Ba komai daddy kila shayarwa ne kawai yace ban yarda ba still dai kuna da matsala da antyn ki a gidan nan don yanzu ma na fahinta akwai matsala don ta kama maki yaro amma a gabana Saade takiya. Nace wanan ba komai bane ai daddy yanzu ba gashi na kama shi yayi shiru ba ya daina kukan da yake dama kiuyane dashi kawai. Yace kada ki boye min Rahama don ni nan nasan komai ke gudana a tsakanin ku wanan dalilin yasa nake son dauke ki a kusa da ita ko zaku samu sasauci a tsakanin ku. Nace daddy wanan maganan na tafiyana Abuja shi zai kara haifar da wani sabon kiyayya a tsakani na dasu. Ya dago kai daga duken da yake yana yagan naman gasshen dake gaban shi yace dani Rahama shin waya aje ku a gidan nan dake dasu ina duk a karkashi na kuke dai ko ? Don haka ina da ikon zantar da hukuncin da duk naga dama akan ku hukuncin dana yanke kenan shi kuma za,a zartar yadda nake so din. Shiru nayi ina cin gaba da bawa yarona nono yana ta faman sauke ajiyan zuciya, daddy ya lura da cewa ban ji dadin da hukuncin daya yanke ba amma shine kawai yake gani mafita a gare shi a halin yanzu. Ya gama cin abincin shi na dauke kulolin a falin na fita dasu daga nan na shirya ni da dana muka dawo wurin shi. A shirye nake dama da taron shi don haka ba mu samu wani matsala ba sai faman gumzar dayake kwasa kawai a lokacin saboda gamsuwan da yayi. Washe gari har lokacin ban wani sake jikina ba don ina faman tunanen sabon fitinan da zai bullo muna muna zaman lafiyan kadaran kadaham da junan mu. Dan kali da kwai na soya mai sai ferfesun kifi da nai mashi tare da hada mai abin sha zuwa rana kafin na gama hada abincin rana don kada yaji yunwa don idan yana kano ba aiki yake zuwa ba nan. Ina son mai karatu ta sani cewa manufa wanan labarin kamar ishara ce a gare mu mata ba wai don nishadi bane kawai muke bin labarin a, a don dai isar da wani sako ne wanda ke dawainiya da alumma a yau. Shi aure wani babban alamari ne a rayuwan mu bawai munauin shi bane don kawai burin mu don da yawan mu sai muna daukan aure kamar wani manufa ne na cin ma burin rayuwan mu. Don haka nake son mai karatu da tafahinta duk da nasan ansani din amma zan kara tunatarwa akan hakan. Aure mun san ibada ne don raya sunna ma, aikin Allah kamar yadda ya umurce mu damuyi shi don kawar da sha, awa akan mu. Aure akan yi shi ne don son jin dadin zama tare sai dai kada mu manta da cewa aure zama ne nazo mu zauna zo mu saba . A cikin wanan auren da mukeyi ne zai zaman to rabin fannin addinin mu yana a cikin shi don haka duk abinda zamu shuka mutabbatar da mun shuka alheri a cikin sa . Don haka ya kamata musan cewa akwai wani babban alamari mai wahala a cikin aure. Zaki iya fahintar cewa wasu ma auratan basu mu, amula a tsakanin su yadda addini ya shimfida munayin sa Wasu ma auratan basu wa junan su biyayya domin basu ba wa junan su hakkin daya dace dasu sai ba muyi wa juna adalici a tsakani musanman mata masu kishiya. Wanan kishin da muke sakawa aran mu da zaran mukaji za ai muna kishiya shike kawo wasu matsaloli a gidajen mu a yau ke da za, a sama a shirye amarya zata samay ki hakan ma amaryan da nata shirin yanzu take shigowa gidan. Sai dai mu sani duk wace ta rike Allah bazata taba tabewa ba a rayuwan ta idan muka koyi cusa dabia ta jarunta hakkuri da juriya, bata tsigar cin mutunci ba ko yaudara ga abokan zaman mu don haka zai kawo gyaruwan a gida jen mu . Amma ina dadin ke babba baki da kwanciyan hankali hakan ma amaryan babu shi ko kadan a tare da ita wanan zai sa maigida aikata abinda baida niyar aikatawa akan mu shifa hakkuri a rayuwa baibar komai ba a duniya. Sai dai ba a son hakkuri yai yawa wanda zai iya cutar dake tun farko ke da aka sama zaki ja girman ki a gun amarya don ida baki bada kafa da nuna son kaiba babu yadda za, a samu kafar raina maki wayon ki a gidan ki. Ba komai yasa na tsaya yin bayanin nan ba sai kawai don masu yi min magana ga yadda ya kamata novel din ya kasance aciki. Muna bada labari ne ta inda ke uwargida ko amarya kike da matsala sai mu dan yi koyi idan zai yuyu mu gyara barnan da muke a gidajen mu tare da abokan zaman mu. Dafatan za, a fahinci sako na bada kowa kuma nake wanan maganan ba sai dai don mu fahinci inda sakon yake nufa don kowa na da nashi illar daga mazan har matan a yau. Manufa shine baii yuyuwa ace komai yazo yadda muke son ashi a ran mu dole tunda hanya ne na fadakarwa mu samu gyara da akasin shi a labarin. Zaku ga a nan ba wai zama da kishiyann ne damuwa ba a,a kishin mu shine yanzui kadda kiga kishiya tana walwala ko kadan da mijin ki . Idan kun lura ita Saadatu tana son shuka alheri amma kuma shedan ya shiga zuciyarta ya hanata barin ta ci riban abinda ta shuka ta kasa gane cewa tsayuwa daa kafun ta da imanin ta na farko akan Rahama shine zai kaita ga kyakyawan karshe a tsakan kowan su saboda zugin yan uwa da abokanai na barkatai da take dauka. ********* ********* ********* Bayan wata biyu sai abubuwa kara lalacewa yake muna ba wani jittuwa a tsakan kowa a gidan yanzu kowa tashi tafishe shi. An kira masu shirin shiga camp dasu zo suyi register a inda ya dace haka yasa nabi umurnin daddy na cika da inda yake so nayi din. Sai dai tunda na cika nake a cikin fargaba da tashin hankali don duk lokacin dana runtsa idanuna don na dan samu barci sai na samu kaina da tunanen irin fitinan da tafiya zai jawo a gidan gun matan daddy. Babu yadda banyi da daddy ba akan ya barni a kano nai bautar kasa na anan amma yace ya riga da ya yanke hukunci ko a ranshi. Ranan muna waya na sanar dashi da an kiramu wurin screning ana son ganin mu yace dani na shirya a gobe zai turo da Hamza ya dauke ni kuma nazo da Aisha da Atika idan zan zo. Tunda mukai wanan maganan hankalina ya kara dagawa na rasa yadda zan tunkari anty da zancen zuwa na Abuja tunda tasan ko a kano zan iya yin shi. Nasan tunda ansa acan daddy yake kamar hadin bakine mukayi dashi za, a dauka shi ke nan nida mijina amma kuma babu daman mu sake mutum yayi yadda ran shi ke so don gudun afkawa cikin tashin hankali da anyi ance. Don haka da dare banyi barci ba na dukufa wurin rokon Allah daya jarabce ni da shiga cikin wanan rayuwan ya bani kwarin gwiwa tare da fitar dani da karfin mulkin shi. Gashi daddy yace duk wani abin da nasan ina bukata na tabbatar da na dauko shi idan zan taho don idan munzo munzo ke nan da zama abinda ya fada min kenan da mukai wayan dashi. Zuciya na tana fada min zamu samu matsala da anty kan wanan tafiyan da zanyi sai dai babu yadda na iya dole ya kama nayi shi din. Tun a cikin darwn nan mun gama shirin mu don duk wani abinda ya dace mu dauka mun shirya shi yadda muke bukatan tafiya dashi din. Na fito zuwa part din anty jiki ba karfi da kyat nake iya daga kafana na shiga dakin ta da sallama tai mamakin ganina da safe haka tunda ba school zan shiga ba. Kamar yadda na saba gaida ita haka ma yau na gaida ita tace dani yau da wuri haka kika shigo nace eh anty dama nazo ne na fada maki jiya sako ya shigo min ana neman mu Abuja yau din nan don zuwa screening din shiga cam da zamuyi. Tace tau wata sabuwar zance kuma? A Abujan ne zakiyi screening din kuma Rama ? Nace eh can suka tura muyi don kin san yanayin karatun nawa shiyasa akai musayan mu dana can ? Tace ina ko zan sani in ba yanzu da kike fada min ba kuma yaune tafiyan ban sani ba Rama sai da kika shirya zan sani ? Nace ban shirya ba anty shine nazo na fada maki don ki sani don da dare ne aka aiko muna da sakon na sani nima. Tace yayi kyau sai dai zan gargade ki da abu daya zuwa biyu shine ki sani inma hada baki kukayi da mijin ki don kije can ki zauna zan sani ne Rama. Kada kuma ki dauka wai zaki inda maigidan yake kice zaki tsiro da wani sabon sallo a zaman mu don bazan taba lamunce maki hakan ba abinda ya kaiki zakiyi ki dawo inda kowa yake zaune. Nace insha Allahu anty kamar wata uwata ba kishiya ba take min magana tace daga karshe humm wai ni za aiwa loko bayan kun gama shirin shi dashi zakice wai jiya aka turo maki may kuke nufi dayin hakan da zakuyi muna wai ? Nace anty nidai ban san wani magana ba bayan wanan kuma ba zan taba cin amanan ki ba a rayuwana kamar yadda nake fada maki kullun. In ma zaki iya Rama aiga hanya nan don kin san halin kowa anan ai kila ma ni nawa mai sauki ne don zan iya lamuntar wani abin a kan ki. Bata sake magana ba tabarni a zaune a inda nake sai da na mike don kaina nace zan je in shirya ke nan anty tace Allah ya tsare nace amin. Ina dawowa dakina na kira Inna ta na sheda mata zancen tafiyan nawa, tace dani ita antyn naki yaya kukayi da ita akan zancen tafiyan nan dai na kwashe komai na fada mata. Tace nasan za, a rina dama ai don za suyi zaton kun hada bakine ki samay shi a can su ku barsu a nan kano din. Tace ni dai zan gargadeki da abu daya shine ki rike Allah ga duk alamuran ki don alamarin naku sai addua kawai saboda abin naku ya baci sai gyaran ubangiji. Kada ki fidda rai da cewa bazaku taba dawowa daidai ba a tsakanin ku don wanan jerabawa ne kuke gani dake da su baki daya. Ubangiji mai yin ikon shi a duk lokacin da yaso akan bawan shi ne idan ya tashi juye alamarin sai kin yi mamakin hakan a gare ku. Idan kinyi la, akari da irin rayuwan da kukayi a baya da wanan baiwar Allah zakiga alheri ne tsantsan ta a tsakanin ku. Nace Inna nikan sai nake ganin dama da wani manufa tai min hakan bawai din ta soni tsakani da Allah bane. Tace a, a yarinya kada ki saurin manta halarcin da wanan baiwar Allah tai maki a baya can ba abin a manta dashi bane kai tsaye don harkan kishi ya hada ku. Zau yiyu ubangiji yai maku hakane don ya gwada karfin imanin ku baki dayan ku zai yiyu ace kuma wani abune daga cikin hikimar ubangiji ya gwada ku a hakan. Nace Inna ni wallahi duk na sare da halin wanan matar a yanzu kamar ba ita bace mukai zama na amana a baya tare da ita inajin ta kamar ita ta haifeni ma. Yarinya kin taba ganin wani mutum da ya samu nasara a rayuwan shi batare da Allah ya jarabe shi ba a wani tsigar. Kada ki mamaki a tsakanin ku dama akwai wata a kasan wanin ku ba mamaki wani laifi wanin ku yai ma Allah bai sani ba aka harabe ku da hakan a tsakanin ku saboda ku gane ba aiwa Allah shishigi ga alamarin shi. Don haka dake da ita duk babu wanda yasan dalilin yin haka akan ku sai aita addua akan alamarin don Allah ya yafe muna. Ko kuma ba hakan bane anyi gwajin imanin ku ne aga mai raunin imani daga cikin ku din . Baji rasa ci da sha ba kina cikin daular ubangiji sai ki godewa Allah tunda wanan ne kawai taku matsalar. Munyi sallama da Inna bayan ta kara min kwarin gwiwa akan tafiyan nawa nai mata sai mun isa zan kirata muyi magana ta fadawa baba maigari da tafiya yazo muna a bazata ne kuma dasu Aisha zan tafi can din. Daga haka Hamza ya kwada muna sallama wai mu fito da kayan mu maigida yace kada muyi rana a hanyan mu. Sai dana shirya na fitar da duk wani abin da zai lalace harda abinci duk nabawa gajiye shi na shiga sauran part din nai masu sallama na barsu da mamakin hakan nakoma na ssallami anty muka kama hanyan mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA A YAFE BA SABODA ONLINE NOVEL NE...... 68 Sai bayan tafiyan mu ne anty ta samu labarin ai harda su Aisha na tafi ranta yai matukar baci da jin hakan da tayi don sai take ganin na munafunce tane da hakan. Ni kuma ina shakku da tsoron fada mata ne tace dama plan ne muka hada don kawai mu yaudare ta mu tafi Abujan. Ta shiga kiran wayan tana fadawa su mama da yan uwa abinda take hasashen mun aikata ni da maigidan take cewa ai ba dole sai Abuja zan iya sevices ba akwai jahohi da dama a kasan. Mama laraba kan da ta kirata fada tai mata tace ke Saade wai may ke damun kine haka da kike tsiro da matsala haka a rayuwan ki. Yanzu koda ace ma ba akan wani dalili yatafi da ita can din ba ai abin farin cikine hakan a gareki. Ina hankalin ki da tunanen ki suke shiga ne yanzu duk kin dauki kishin duniya da tashin hsnkali kin sakawa yar mutane akai. Kiji tsoron haduwan ki da Allah fa akan wanan bakin kishin da kika sawa zuciyar ki yanzu. Kin abin arziki kowa yans saka maki albarka ga hakan har wasu na son koyi da hali irin naki zaki bari shedan ya dinga rudin ki kuma ? Ina ji maki tsoron ranan da yarinyar nan zata bijere maki akan irin biyayyan da take maki abin ba zai maki dadi ba don ko an kusa wallahi, Kwanaki fa yaron nan naki ke fadawa mahaifin shi yadda kukayi akan dan wurin Rahama da Amira yanzu ke baki jin nauyi da kunyan haka. Shekarun ki da ilimin ki basuyi maki rana ba ko kadan wallahi indai wanan hakin kika dauka. Tace mama ba haka na bane ni bani son munafunci ne ga alamari tace ke dakata na fada maki gaskiya ba matar shi bace ya tafi da ita da yaje can yana hurda da wasu matan na banza fa kuna zube a gida dukkan ku hudun. Jikin ta yai sanyi tace nagode mama tace ki godewa Allah Allah yasa kuma ni kadai kika fadawa wanan maganan kada ai maki dariya wallahi. Sukai sallama ta hada da mata nasiha da lalashi tace tagode suka kashe wayan ranan tasha kuka sosai tana nazarin maganan mama din. Tafe muke a motan tun muna dan hira jefi jefi har mukai shiru gaba dayan mu nikan sai tunanen magana ta da Inna ta na yau nake a raina. Don ba karamin tasirin maganan yai min ba a zuciya na sai dai ina ganin a yadda muke din nan abu ne mai wuya mu shirya yadda take nufi din. Mun isa abuja bayan karfe uku da yake Hamza ya san hanya bamu sha wani wahala ba don gidan da ya ce ya sake din ba wanda na sani bane a baya don yace wancan uguwar baida tsaro sosai. Koda muka isa yana gida a lokacin yana dakon zuwan mu garin mun shiga gidan mun samay shi a falo zaune yana amfani da laptop din shi. Ya dago kai a cikin murmushi yana muna sannu da zuwa ya mike ya nufo kofan da muke shigowa yana son karban dan shi da nake rugimay dashi a kafada na yana barci. Nan Hamza dasu Aisha sukai ta shigo muna da kayan mu daga ciki yake cewa da Aisha kai kayan naku wancan dakin ya nuna mata dakin dake bangaren hagu ta nufa da kayan. Bamu dade da zama ba sai ga hamza ya shigo da ya tsaya kakabe mota a waje yace barin zo mu fita ka samo maku abinda zakuci ko. Tare suka fita lokacin ne nabi gidan da kallon mamaki muka zagaya gidane babba mai kyau yaji komai na zamani dakuna sun kai guda shidda a gidan wuri daban daban ga katon kitchen maigirma da komai a cikin shi zaka ce already akwai mace a cikin gidan ne dama. Sun dawo da take away niki niki da drinks da kaji gassasu a cikin sa masu yawa sai kamshi ke tashi mukaci muka sha dama kafin su dawo munyi sallah a dakin da aka shiga muna da kaya. Nan ida na idar da sallah na kira wayan anty don in sheda mata mun sauka lafiya sai dai wayan har ya gaji ya katse ba a dauka ba. Maigidan yaso hamza ya huta amma yace ranan zai koma kano dole ya sallamay shi ya wuce ranan. Sai bayan tafiyan Hamza ne daddy ya leko dakin da muke zaune yace zo mana Rahama nafito nabi bayan shi. Yace naso ki duba tsarin gidan sai kiga yadda ya dace da tsarin ki shi dai wajcan dakin dana sa yaran su sa kayan ku shi zai zama nasu su biyu sai ke ki zabi wanda zai zama naki already ni nawa ga shi can daga karshen lungun barin dama daga ciki. Nace to yau zamu zauna a nan don mun gaji zuwa gobe sai na duba idan na huta yace ba matsala ga hakan don kunyi tafiya. Da dare ma sauran abincin da mukaci da rana ya rage amma sai da daddy yafita ta sawo muna dan abin tabawa. Ranan nai barcin dadi kamar ace haka rayuwan zai dore muna daga mu sai shi a cikin kulawa da ya dace babu idon kowa a kan mu. Washegari ban yarda a sayo abin karyawa ba ni nafita da kaina muka hada abin karyawa tunda safe ya fita gidan yace na duba abinda nake bukata sai muyi waya dashi a sayo muna. Bayan fitan shi nai wanka na shirya nafito don duba gidan da kyau kafin in fita na kara kiran layin anty sai da wayan ya dauki lokaci sannan aka daga cikin murya mara dadin yanayi tai min sallama na fara gaida ita ta amsa min ba daidadi nace jiya na kira in fada maki mun sauka lafiya baki kusa ina gani na fada mata hakan. Tace ina daga falo wayan nawa yana daki ne nace yaya yaran duk da ita da mukai tafiya bata tambayi lafiyan nawa yaron ba. Tace suna lafiya nace dama na kira ne mu gaisa tace ta gode ina kokarin kashe wayan naji tace dama ashe harda su Aisha ne zaki tafiyan ban sani ba ? Na dan yi shiru can dai nace eh don kin san ai dole inzo da wanda zai kama min yaro tunda kamf zan shiga kuma ba a zuwa da yaro. Tace amma ai ya kamata na san da hakan ba wai naji daga sama ba kin tafi dasu nace ayi hakkuri anty nayi kuskure ta tabe bakin ta kamar ina a gaban ta tace wanan kuma matsalarki ce hakan ai don ban da daraja a idanun ki yanzu. Tunda kina ganin mun zama daya abinda nake sallo dashi kema dashi kikeyi yanzu miji ko ? Haba dai anty don Allah ki bar wanan magana bai dace ba kuskure ne nayi don Allah kiyi hakkuri please. Sai naji ta kashe waya tana tsuki na kalli wayan nace nikan dai na shiga uku da anty mata ko may nayi banyi daidai ba a rayuwan ta nifa naje sallaman ta amma bata tsaya munyi maganan kirki ba da ita tashiga gasa min magana. Bamu zauna ba ranan muka shiga gyara gida daki na mun gyara mun gyara gidan ko ina don har Atika dake jigila da baba idan yai barci tana fitowa ta kama muna wani aikin muyi tare da ita. Gidan ya dauki kyali ga kamahin girki na tashi mai nuna alaman mace ta shigo gidan ke nan a ranan, don gidan dake da mace a ciki daban yake da inda babu mace cikin sa. Daddy ya dawo gida da yamma ya samu gidan ya canza kala komai a gyara shi yadda ya dace ayi shi a inda mace take gida sabanin da babu mace a cikin sa tunda ya tare a gidan. Nai mashi sannu da zuwa ya zauna a daya daga kujerun falon yana nuna gajiya a tare dashi ya mike kafafuwan shi ya mayar da kan shi bayan makatin kujera tare da lumshe idanuwan shi yana shakan kamshin girkin dake tashi. A hankali na tako dauke da cup da goran ruwa mara sanyi sosai a hannuna na duka a hankali na aje cup din da goran ruwan. Takalman dake kafan shi na fara cire mai sai ya dago kanshi daya sagale ga kujeran ya bude idanun shi a hankali tare da sauke su a kaina. Ta kalma na cire tare da zare mai safan dake a kafan shi sai naji ya sauke ajiyan zuciya nace sannu da dawowa daddy ya aiki ya hanya ? Alhamdullahi yace dani na dauki cup din ja tsiyaya mai ruwa na mika mashi ya karba tare da kwankwadewa ina rike da goran ruwan a hannuna har lokacin. Nace dashi akara zubawa ne ? Yace No I, am ok nagode ya sauke ajiyan zuciya nace idan ka huta ruwan wanka yana jiran ka a bayi sai yace ok nagode. Bai dade ba ya mike ya shiga dakin shi ko da na bi bayan shi yana tsaye a tsakiyan dakin yana bin dakin da kallon yadda yasha gyara haka. Na karaso ina cewa dashi ko na taimaka mane da cire kayan daddy naga kamar yau kasha aiki sosai ? Ya sauke murmushi a fuskan shi yace ai kullun haka nake da wanan aikin kin san abinda mutum ke nema baya gajiya da yin shi. Na taimaka mai da cire kayan ya shiga bayi ni kuma nafita zuwa karasa aiyuka na dake gabana a lokacin kada dare yayi ban gama ba. Koda yafito yana saye da rigar jallabiya na maza mai dogon hannu na tsaya daga ga gefen shi nace daddy abincin ranan kafa yana nan. Ya juyo yana kallo na tare da kokarin nade hanayen rigar nashi dogon rigar bubu ne a jikina har kasa kayan sun min kyau sosai ajikina, yace ai da baku sa min ba tunda bana dawowa sai yamma lis haka. Yau ma don kuna gidan yasa na dawo don na huta hakana, yace yau dai kin wuni ke nan a cikin aiki wanan gyara haka ai yai maki yawa gaskiya. Nasa Kabiru ya samo maki yar aiki da zata dinga taimaka maki da aiyukan gida sai ki samu hutawa haka wa ranki don Allah. Murmushi nayi nace godiya nake daddyn mu sai dai tai min gyaran gida da sauran aiki amma banda girki gaskiya don ni tun a kan Saliha na sasuda da zancen yan aiki a raina. Na kawar da zancen da cewa dashi kunyi waya da Hamza jiya ya isa lafiya ko ? Yace wallahi ban samu kiran shi ba sai gashi shi ya kirani yana fada min ya isa da karfe goma sha daya na dare. Nace maza dai basu damu da tafiyan dare ba su nikan ina zan iya tafiya a cikin dare haka na ? Yace antyn ki ma ta kirani dazun da yamman nan ina hanya nace Allah sarki suna lafiya ko nayi kewan su Nasir wallahi jiya jiyan nan. Yace suma ai dole suyi kewan ku anty ki dai ce ke fadan da ta saba dani wai may nake nufi da tafiyan dana shirya maki ? Da sauri na dago ina kalon shi don son jin amsan daya bata din? Yace nace da ita ai ba wurina kika zo aikin ki ya kawo ki kai Zulfa ce dai ma nake ganin batai min wani korafi ba akan hakan sosai don ta basar da maganan ita. Nace a sanyaye nima ta kirani tai min korafi wai nazo da Aisha da Atika ban fada mata zanzo dasu ba. Yace to may take nufi da ba za, a zo dasu ba watake son ya kama maki yaron ko idan an barsu a can duba maki su zatayi ? Nace sai hakkuri alamari amma ai yanzu da sauki don ta rage wani abin ai yana tafiya yace kadama ta rage ita zai dama ai. Yace ni zan karasa masallaci can kasa kada a fara sallah badani ba don wurin akwai nisa da nan kadan nai mashi adawo lafiya ya fice. Na kwalawa Aisha kira ta amsa tafito dauke da baba a hannun ta nace don Allah aje wanan sarkin kiuyan ki sa muna turaren wuta kamshi ya dauki gidan. Daga haka na wuce zuwa dakin dana gyara a matsayin nawa na fara shirin yin sallah don lokaci ya gaba to sosai na magariba. ********* ********* ********* Ranan monday na shirya zuwa camp ban tafi da baba maigidan ne ma da kan shi ya sauke ni inda na samu har dalibai ire iren mu sun fara taruwa a wurin sosai. Bai tafi ba sai da yai min komai ya tabbatar banda matsala yai min sallama ya tafi yake cewa idan na gama na kirashi yazo ya dauke ni tunda ban san gari ba anan. Har yamma muna wurin muna tashi na kira daddy don na samu ni har angama min komai nawa yanzu posting zan jira fitowan shi. Daddy ya iso muka kama hanya sai gida a yadda nai tunanen zan samu yaron ya jigaita sai na samay shi hankali a kwance don dama ya saba da su Aisha ko ga madara da idan yai kuka zata bashi yasha. Nima ranan nagaji sosai ban tsaya ba nafara tafiya ne naji Aisha tace dani Anty an fa kawo yar aikin dazun da kika fita. Da sauri na juyo nace da ita tou har an kawo ta tana ina tace tana dakin mu tare da Atika nace bari nai wanka idan nai sallah sai na fito mu gaisa da ita. Na shige ban zauna ba na fada ban daki na watsa ruwa a jikina ina fitowa wanka ne waya na ya dauki kara na karasa da sauri na dauka kada ya tsunke. Gajiye ce ke kirana a lokacin don haka nai murmushi muka shiga gaisawa na tambaye ta mijin ta tace dani yana lafiya tace wallahi hajiya gidan sai ya koma ba dadi da baku nan . Kun tafi kun barni ni kadai sai matan gidan masu ji da kan su babu dadi wallahi hajiya. Nace kai Gajiye baga anty nan ba ki dinga shiga kuna dan gaisawa mana ai zaki ji dan saukin kadaicin naki. Tace wa ni hajiya don Allah rufa min asiri matar dake zargina may zan mata nayi fari a gurin ta ko ke ai hakkurin ki ne yasa kuke tare har yanzu. Nace to yaya zanyi Gajiye ai binta ya zama min dole kada nazama butulu gareta nice fa mai laifi ni da na aure mata mijin ta yanzu. Kinga kuwa ai ba zan yarda ace a kaina aka samu matsala ba haka da ita sai dai tai tayi wata rana zata gane gaskiya da kan ta. Tace humm hajiya Rahama jiya fa bayan tafiyan ku bakiga haukan da akasha gidan nan ba malam musa da kanshi ke fada min yaga anata gungu gungu a gidan yasan kuma akan tafiyan naki ne. Nace ai yanzu kan su ake ji ni kan Allah yai min gyadan dogo na samu na dan tsere na kwana biyu sai suci kan su kuma yanzu ai. Mun dan dauki lokaci muna hira bayan mun gama na kashe wayan ne na tayar da sallah don nasan an fara sallah a wani wurin don yanayin sallah garin ba daya ba da namu can kano. Sai da nagama komai nafito falo jin nafito sai ga su Aisha da Atika da yar aikin mu ashe yarinyar gwari ce yar budurwa zata kai Aisha ko ta girmayta sai dai gajera ne ba a gane shekarun ta sosai. Ta zube kasa tana gaida ni na amsa mata tare da tambayan ta anzo lafiya tace lafiya ma nace yaya sunan ki tace Helen take amma ana kiran ta da Lami ne nace yayi. Nace da ita don Allah ina son ki rike ni amana kamar yadda muma zamu zauna dake amana anan tace yes ma. Nace aikin ki a nan shine zaki dinga muna shara da wanke wanke da sauran yan aiyuka amma banda girki tace ok ma nagode. Nan dai tana batin wurin daddy ya dawo daga masallaci ya zauna anan falo inda ya samay ni a zaune. Yana cewa na dauko mai system din shi a daki na mike naje na dauko mai na kawo mai na samu ya zauna a gaban abinci zai fara cin don mun shirya maikomai dama. Kai a gaskiya sai ince dole ne wasu mata suke kishi don zama da miji ke kadai akwai dadi don ban san haka ba sai yanzu da muke zaune daga ni sai daddy da yarana kawai sai yadda naso dashi ya koma mun kamar wani narkake dashi sai yadda nake so a gidan . Ai ko ba komai dai na morewa rayuwana na kwana biyu ga hakan kafin na koma ga turke na mai cabo cikin zama da kishiyoyi. Ranan muna zaune da dare baba yana gefen shi yana aiki sai ga wayan shi na ringin sai kusan zai katse ne ya dauka ashe hindatu ce takirashi. Jin muryan yaron dake wasa mai kama da kuka a kusa dashi yasa tana daukan waya tace dashi indai cutane ai sai ka matsa don cin amana mu ba aje damu ba sai a dauki wace ake ganin tafi mu daraja don son kai kawai. You are very stupid yace da ita abinda ya jawo hankalin mu ke nan na dago kai da sauri ina kallon shi yace don rashin mutunci sai ki kira wayana kina min maganan banza don rashin hankali nazo da ita ke ma ai sai kizo din mara hankali kawai. Ido na tsura mai dana fahinci da wata daga cikin matan shine yake waya sai na kawar da kaina gefe daya ina duba tv dake aiki a falon. Ya gama yaja tsuki bai min magana ba nima ban yi ba nasan dai maganan dayace bai wuce akaina ake mai korafi ba don jin abinda ya fadi. Satin mu biyu daddy ya shirya ya tafi kano ranan da ya sauka sai da akai fitina tsakanin Zulfa da hindatu kan rabon abinda yaje dashi. Itako anty na dama jiran shi take da ta karbi girki ba komai tai magana a kan shi ba sai zance na data nuna bacin ran ta akan dauke ni da yayi ya tafi dani Abuja da sunan wai na tafi aiki . Ranan dai sunyi ba dadi inda yace da ita yanzu ke bakiji kunya ba ace wai ke , ke wanan korafin don rashin godiyan Allah gareki. Tace may ye na rashin godiyan Allah din ga haka kishiya fa ka dauka kake tare da ita ka bari a nan wai ni tsuhuwa ko may kake nufi dayin hakan ? Nasan da yardan ka don ka cuta min ka bata kwarin gwiwan zuwa Abuja don yin bautar kasa may nene ba ayi a kano da akeyin shi a Abuja kawai. Yace ke Saade na kaishi din sai may kema tunda Rahama ta tafi kema sai ki shirya aiki tafi ko tunda ta zama maki abin gasa yanzu. Nan dai ya mata kaca kaca kin san halin maza akan abinda suke so ba a taba gane kan su sai su borewa mutum. Ba anty kadai ba kusan kowa yai mai wanan korafin dan tafiya na Abuja yace suma sai su shirya suje bautar kasan sai a zauna lafiya . Ita Zulfa diploma tayi ita ko hindatu NCE ne da ita ta tsaya a nan sai anty da tare sukai bautan kasan su dashi a lokaci daya. Wanan borewan da yayi dole sukai shiru da zancen amma yasha kara agun magabata amsa daya yake basu shi bautar kasa Rahama taje yi a can dole sai ai shiru ba bakin magana kuma don kowa yasan da bautar kasan da akeyi. Kwanan shi goma sha biyu ya dawo garin inda ya samu na shiryawa dawowan nashi kamar zan tari wani bako ta ko ina na shirya mai. Ranan kamar ba gun wasu matan daddy yafito ba cab don bamu ragawa junan mu ba sai da muka bar juna don kan mu waahegari ma bai barni ba sai daya debi rabon shi a gare ni. Na hada mai break fast mai dadi yaci ya fita ban fito ba na kwanta don akwai gajiya sosai a tare dani sai sha biyu da rabi na falka nai wanka na shirya na fiti falo ko ina tsab helen ta gyara shi ba wani makusa a gidan. Bayan na karya ne nace Atika ta dauki min waya na ina budewa naga sakon da aka turo min na posting din mu da akayi. Inda aka turani babban asibitin dake garin Abuja don aiki dasu naji dadi sosai da gakan don nasan zan karu sosai ga wanan ci gaban dana samu. Da murna na kira daddy ina fada mashi inda aka turani bautar kasan abinda ban sani ba daddy ne ashe ya shiga yafita na samu aka turani wurin. Jin yadda nake farin ciki bayan mun gama wayan ya kalli wayan nashi yai murmushi yace Allah sarki waban yarinyar akwai sauran kurciya a kanta dai har yanzu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA, A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , , 69 Bayan komai nawa na bautan kasan ya kammala nagama daga MBBS zuwa housemanship dina wanda komai a cikin gata akai min shi shine sai kuma ga posting ya biyo baya inda aka tura ne asibiti gashi kuma maigidan ya matukar tausaya min ga hakan. Don yasan ba wani gata ke gare ni ba ta ko ina iyayyena basu tare a guri daya ban tare da mahaifina haka ma yan uwan haihuwa na muke da su. Matar da nake jin sauki a gunta ta dauke ni kamar kowa nawa yanzu kishi yasa mun raba hannun riga da ita . Ya zama wajibi ya tallafawa rayuwan wanan yarinyar don sun tauye ta shida Saade a rayuwan ta. Ni kaina na san an an min gata don sai jefi jefi nake fita zuwa camp a lokacin don execuse a wurin dake nuna ni matar aure ce mai karamin goyo tare dani. Komai yanzu idan akwai kudi zai sai wa mutum gata a wurin jama, a don ni kaina na san an gwada min galihu so sai a wanan fannin. Mun yi waya da Zarah take fada min suma sun gama har anyi posting fin su ko tana a cikin kano bata fita ba. Bayan mun dan taba hira na dan bata labarin sabon rayuwan da nake ciki tai dariya tace ai maza sun fi mu wayo Rahama gaskiya daddy yana son ki sosai tunda har yai maki wanan hanyan. Yanzu matsala zai dinga shigo maku sai kiyi ta hakkuri kada ki yarda a shiga tsakanin ku don korafi zai mai yawa idan kuma ke a fannin ki bai samun kwanciyan hankali ba abin mamaki bane kiga canji daga gare shi don mace shuumace. Nace haka dai Inna ta take fada min kullun mukai waya insha Allahu zan zamo mai hakkuri da juriya daga duk wani kalubalin da zan gani a zama nan tare da shi. Mun gama waya dashi na kira anty nake fada mata mun gama zaman camp har an yi posting din mu ko. Banji tai min wani farincikin hakan ba nima dama ban yi tsan manin hakan ba a wurin ta don ba sabon abu bane gare ta. Sai dai rashi na a gidan ta fara shiga wani hali sai take ganin ashe ba karamin amfani zamana yake mata ba a gidan don gashi dan rashi na da tayi na kwana biyu abubuwa na son jagule mata ko ta fanin yara abin yana son yafi karfin ta yanzu. Gashi idan ba yar aikin ta ta dan samu zama da ita ba babu wanda zatai magana dashi haka zata wuni zur ita kadai a part din yara suna makaranta. Sai yanzu ta san ba karamin rana Rahama take dashi ba a gurin ta bata kara tabbatar da hakan ba sai ranan da ta wuni ba lafiya duk gidan ba wanda yazo gaida ita haka ta wuni zur a kwance ita kadai don mai aikin ta irin matan nan ne masu kama da doleye sai dai ta wuni tana aiki ba magana . Gajiye dai kan shigo su gaisa da safe daga haka kuma sai wani safiyan idan ta shigo gashi ita kanta ba dadin girkin mai aikin take ji ba da nake gari ne wani lokaci idan yaran sunce suna son cin abu kaza zatace kuje ku fadawa little mum tai maku. Yanzu ko little mum tayi nisa dasu yaran sun dawo daga school Amira ta dawo da ciwon kai haka ta samu uwar ba lafiya babu mai kama wani tun yarinyar na ciwon kai har ta koma mata maleria ta rasa yarda zatayi ta tura Nasir ya kira Gajiye ya samu wai Gajiye bata nan ta fita unguwa. Abu ya taru yai mata yawa gata a kwance ita babu moriya nan ta tuna halaiya irin na Rahama da ace tana nan ne yau suke haka ita da yarta da yanzu tana nan tana fadi tashi a kan su sannu yana zuwa yana dawowa garesu da kulawa yadda ya dace a kan su. Rahama ko batace ba idan taga abinda ya dace ita da kan ta zatayi mata shi batare da ta sani ba za, a aikata shi. Yanzu ne tasan ta rabu da wani babban bangare na rayunwanta yarinya mai matukar alheri a gareta da taimakawa ko sau daya bata taba nufinta da sherin da ada take ganin kamar abinda take mata da wani manufa take mata shi. Son kai kawai yasa ta ta tsani yar mutanen da tasan kimarta da darajan ta, sam Rahama bata gajiya da kyautata mata dan bata taba gajiya da laluran ta dana yaran ta akanta. Abinda taiwa Rahama kan graduation din yaran ta ne ya fado mata a rai ta sani sarai Rahama zata iya masu fiye da abinda tai masu a lokacin in har tana dashi amma ta rufe ido saboda tasha zuga tai mata cin mutunci. Hakan da tayi bai hana taci gaba da kyautata mata ba da yaran ta amma ita da guda daya da Allah yabawa Rahama a gidan taki jinin ta bude ido taga yaton a idon ta tana jin haushi da takaicin yaron kamar ta shake shi. Tun tana yi a boye har ta bari yarinyar ta fahinci hakan da takewa gudan jinin ta duk abinda take gwadawa yaron bai hana yarinyar taci gaba da so nata diyan ba tsakani da Allah. Ta gyara kwanciyar ta wasu hawaye masu dumi suka biyo idon ta tace ni Saade wai yaushe na koma haka ne Allah ina rokon ka daka rage min wanan zafin kishin haka a raina. Ta lumshe idanuwan ta kalamin Rahama ne ke dawo mata a rai da take cewa ba zantaba cutan ki ba anty a rayuwa idan ban soki ba bazan ki ba ko wanii naki don kece silar farin cikina a yau. Amma sai take ganin a lokacin dadin baki ne irin na yaudara kawai take mata baya ta gama cuta mata mijinta da take matukar so yau yana kokarin nuna ma duniya akwai mazauni Rahama a zuciyar shi. Yau gashi da ranta tana ji tana gani daga karshe Rahama ta barta kuma tana can tare da mijin zaman ta lafiya ta barsu nan suci kansu a tsakanin su. Yau da Rahama tana gari da yanzu daga ita har yarinyar sun san abin yi ko gashi bata da wani dabara a hakan. Idan bako tayi da zaran Rahama ta sani ta shiga da wainiya da shi ke nan har sai ya wuce idan babba ne zata saya mai sunan shi kaikoma saan tane zata girmama duk wanda yazo gareta ta dauke shi kuma da mutunci. Amma yanzu da bata nan ranan ma da tai baki Hindatu na ganin su tai kamar zata buge su da mota tazo ta wuce su kamar bata gan su ba ma tayi tashige abinta. Nan take ta tuna da daddin Rahama a gareta tace da Rahama ce da murna zata tare su tana haba haba dasu tana farin ciki da zuwan su harsu tafi. Tana cikin wanan tunanen ne abin ikon Allah taji wayan ta na ringing har ya katse bata iya dagawa ba can kuma kira ya kara shigo mata da kyat ta iya daukan wayan sunan Rahama tagani a screen din wayan yanuna mata da Rama. Ta dauka cikin dauri jin Sallaman ta kawai mun fara gaisawa na katse da cewa anty may ya faru baki jin dadi ne ta dan kakaro murmushi da kyat tace hakane Rama. Nace subbahanallahi kin ko sha magani tace nasha sai dai bai barni ba ciwon har yanzu, ya salam nace anty kije asibiti mana a dubaki . Tace dare ya somayi Rama nace haba anty ina Nasir abashi waya muyi magana dashi tace yafita baidawo ba. Nace bani Amira anty, tace wallahi tunda yamma ta dawo ba lafiya ita ma tana can kwance jiki ya gashe mata hankali yai matukar tashi nace anty shine kuke zaune a gida haka. Kashe wayan nayi take na kira wayan Hamza na fada mai cikin tashin hankali da ya je gida ya dauki anty da Amira zuwa asibiti don Allah. Bai bata lokaci ba ya isa gidan da shiga ya nufi wurinta inda ya fada mata nice na turo shi ya kaita asibiti. Bataki ta shirya ita da yarinyar suka tafi asibiti inda likita yai mata fada may yasa tabar Amira har jikin yai mata nisa haka ? Nan dai akai masu allurai da magani da ita da yar Hamza ya dawo dasu gida mai gidan bai nan yai tafiya kasar Sudan a lokaci wayan shi kuma baya shiga. Ina sallah ishai ya bugo waya gaisawa kawai mukayi nake fada mai zancen rashin lafiyan anty amma sunje asibiti an basu magani sun sha. Nan nake fada mashi cewa harda Amira bata da lafiya yace bari ya kirata yaji yanzu mukai sallama ya kashe wayan . Tana kwance ya kira layin ta sun gaisa yake cewa yanzu Rahama ke fada min keda Amira duk ba lafiya to yaya jikin tace Alhamdullahi mun samu lafiya Rahama ta turo hamza ya kaimu asibiti ai. Yace yanzu ke idan da batai wanan dabaran ba haka zaku zauna da ciwo a gida yana cin ku sai yai nisa kuma ki sa mutane a wani hali. Fada yayi sosai bata dai ce dashi komai ba yai mata Allah kar lafiya sukai sallama ya kashe wayan tai tsuki tana cewa kaman ya damu da mutane yanzu. Kafin ya kira ai saida ya fara kiranta nasan shine take fada mai bamu da lafiya ya bugo min yanzu yana wani fadan karya haka. Ban kwanta ba sai da nai mata yaya jikin da Allah ya bata lafiya mukai sallama na kashe wayan tana mai bani tausayi a raina. Da safe ma tun da na idar da sallah na kirata muka gaisa na tambaye ta jikin ta tace taji sauki harta samu barci jiya sosai. Nace a bani Amira don Allah mu gaisa sai da aka dauki lokaci duk wayan na a kunne aka kaiwa Amira nai mata yaya jikin tace da sauki nace ta karya da wuri tasha magani. Ta dai amsa min kamar bata so ban damu ba nai mata Allah kara sauki nace ta gaida yan uwan ta tace zasu ji. Haka na wuni akai akai ina mata ya jikin har dai nagane kamar tagaji da jina na daina kiran nata hakana tunda ta samu lafiya yanzu. ********* ********* ********* Muna zaune a falo gaba dayan mu har helen da kan zauna a tare damu idan ta gama aikin ta don ban matsa mata kada na zo na cutawa yar mutane gata ko banza ba musulma bace. Karatu muke da Atika da ke assignment din ta don ta fara karatu yanzu har Aisha takan je wurin daukan lesson idan ina up. Mamakin yadda yarinyar take da saurin daukan karatu nake gashi dai daga sama ta fara amma tana iya hada kalmomi yanzu da kan ta. Sai nake gani da yanzu tana kauye a haka wanan basiran nata zai tafi ga banza bata amfana dashi ba sai tallan koko kawai da uwayen su ke sanaan yi kullun safe. Wanda saura yan uwan su shi suke yi yanzu a kauyen babu karatu a tare dasu wanda ko a dakin su ne zai amfane su nan gaba. Rokon Allah nake a zuciya na akan zurian da Allah zai bani nan gaba su ma Allah ya basu hazaka akan karatu na addini dana bokon baki daya. Mun gama sai muka dan shiga hiran dasu Aisha da helen keyi wai sun fita sun ga wata mace ta raba sadaka da kan ta a hanya kuma kudi yan dubu take bayarwa. Nace injin dai baku tsaya karba ba don kun san yanzu duniya ta baci zakkaga mutum da fuska kamar na Annabi ne shi amma yana da wata manufa a tare dashi a zuciyar shi. Sallaman daddy ne mukaji a tsakiyan falon bai fada min zai dawo ba a ranan sai fanin shi mukayi kawai ya dawo a ranan a kuma wanan lokacin. Atika ta mike da murnan ta haka ma sauran suna mashi sannu da zuwa shima da murna ya amsa masu taron da suke mashi din. Duk da ina da kwaliya a jikina don bani zama hakana don bai gari don ban san ko wa zai shigo min ba ya samay ni babu shiri a tare dani. Kallon shi nake daga inda nake zaune ina jin wani iri sin daddy yana ratsa min jikina har zuwa cikin zuciya na gashi ban iya tashi na tare shi ba sai faman binshi da kallo nake daga inda nake zaune. Inda baba yake zaune a kasa yana ta wasa da kayan wasan shi ya nufa ya duka ya dauki yaron yana cabewa a sama sai washe baki yaton keyi don yanzu yasan mahaifin shi sosai. Ko dan muna mu kadai ne sabanin dacan da sai an dauki lokaci bai ganshi ba, ko kuma don yaron yanzu ya kara wayo ne ban sani ba. Har ya karaso inda nake zaune dauke da yaron yadan lakoto min hanci yana fadin irin taron da zan samu ke nan kuma yau ? Nai dan murmushi nace to ganin ba zata nai maka mana daddy shine bazaka sanar damu kana tafe ba na shirya maka ? Murmushi yayi yasa hannun shi daya ya dago fuskana dashi muka hada ido yai murmushi yace bani son ki wahal da kanki ne wurin cewa zaki shirya abin taro na dan nafi son kina hutawa a koda yaushe. Yace yanzu baga kina zaune ba kina hutunki hankali a kwance da na sanar dake samun ki zanyi kin sha aiki duk kin gaji. Na dan dago kai na kalle shi nai murmushi tare da cewa aiko yanzu daddy ba zan huta ba tunda abincin da mukayi nasan ba irin cimar ka bane da dare. May kuka dafa ya tambaya cikin son ji nace dafa duka ne da vegetables a cikin sa kawai yace ke bakin ci ba Rama ? Nace a sanyaye naci don nice ma ke son ci na zauna na dafa muna shi din da daren nan yace to nima shi din zanci in har akwai saura idan kuma babu sai nasha tea na kwanta kawai. Nace balle ma akwaishi bamu cinye ba duka ya samu wuri ya zauna tare da gajiya a jikin shi nace Aisha zo karbi yaron nan ya huta please. Yace haba barshi Aisha nayi missing din babana da yawa mu gana nace dake nagaji da daukan babana ne halan. Murmushin jin dadi nayi don inajin dadin yadda daddy ke nunawa yaton so da kauna tankar shine din mahaifin nashi ba suna yaci ba. Sai na tuna da lokacin da yaso sakawa yar wurin Zulfa sunan mama laraba amma taki ta saka sunan da take so ga yar nata wanda nasan hakan yaci mai rai kyalewa kawai yayi a ranshi. Mikewa nayi na dauko mai ruwa da cup na kawo mai tare da tsiyaya mashi ruwan bai sha ba sai daya dan fara ba yaron ruwan tukun yako sha sosai ashe dama yaron najin kishi ban sani ba. Yace kai Rahama kina ko kula min da uba wanan shan ruwa haka kamar tun safe bai sha komai ba yana jin kishi. Atika tace daddy haka baba yake da son ruwa fa shi ruwa baya usan sa yace ai ko a dinga bashi nace dashi ya miko sauran wanda yaron yasha yai burtsatsi a ciki. Yace haba Rahama baki son muyi zuminci ne da uban nawa nan gaba zuba min kawai ki gani dan Allah. Na zuba mai ruwan cikin sauran wanda yaron ya rage ya zuke gaba daya na kara mai yadan yi wasa da yaton ya miko shi yace zai rage kayan jikin shi yaii wanka. Ya mike na mikawa Atika da ta saura a falon yaton nace kaishi wurin anty Aisha tai mai shirin kwanciya kafin nazo tare muka shiga dakin dashi. Saida na hada mai ruwa bayan ya shiga wanka na tsaya na kara gyara dakin tare da kwashe kayan da ya cire na ciro mai riga mai saukin sawa na dora a saman gado na fita zuwa hada mai abinci kafin ya fito daga wankan . Tare muka zauna bayan yafito yaja cin abinci muna hira akan tafiyan nashi inda yace dani yaje duban wasu kaya ma adanai ne a can sudan kuma sunyi nasaran samun kayan a can din da suka je. Nai farin ciki sosai dajin wanan labarin inda na taya shi murna mun kuma koma hiran a kan ciwon anty nan ya nuna min bacin ranshi na akan may zata zauna da yarinya a gida ba lafiya hakana. Nan dai mukai hiran mu daga karshe muka mike zuwa ciki don na fahinci yana son hutu a tare dashi duk da nasan idan mun shiga din bawai kwanciyan zaiyi ba sai ya samu natsuwa a tare dani. Washe gari ban tsaya ba na shirya mai abin karyawa don kada na makara har ruwan wanka sai dana hada mai kafin nabar gidan. Bai tashi ba don gajiyan da yake dashi sai sha daya yafito a cikin shirin shi inda ya zauna ya karya ya mike ya shiga store din mu ya dan duba abinda bamu dashi a ciki yafito ya fice a gidan. Da wuri na dawo gida dan ina son shirya ma daddy abinci lafiyayye don dawowan shi. Bendi sa na jawo na ce da Aisha ta wanke min kafin nafito na shiga dakina nai sallah tare da sauya kayan jikina nafito na dora girki inayi muna hira da yaran har komai ya kammala min yadda nake son shi. Sai dana kusan gamawa ne ya shigo gidan inda yaton shi na na Abuja Sani ya biyo bayan shi da kayan amfanin gida a ledoji niki niki. Sannu da zuwa muke faman yi mashi ya amsa muna nan yazauna sukai magana da sani na dan lokaci yai muna sallama yatafi. Ban zauna ba sai da nakawo mai abinsha yasha sai kuma ga kiran waya ya shigo mai ya dauki lokaci yana wayan ina zaune daga gefen shi ba dai sauraren shi nake ba amma kuma sai na fahinci kan business din shi ne yake wayan. Neman kudi akwai wahala nace a raina don mutum baida lokacin kan shi kullun busy mutum yake naganin yaya zaiyi ya hada ya zama mai kudi. A yadda na fahinta yanzu kamar daddy yayi watsi ma da aikin shi na filaye da yake a Abujan yafi bada karfi a fanin business din shi nake gani. Don kamar yafi mai muhinmanci da kawo mai kudi duk dai shi ba mutum bane da ke zama da mace yana fada mai sirin shi kamar wasu mazan can. Da hannu ya nuna min wasu kayan da Sani ya zube a falo a gabana na fahinci yana nufin na bude nagani ne ai kuwa na mike na jawo kayan kaya ne ciki da gani tsaraba ne muka samu a ciki. Lafaya ne da kuma atamfofi irin na matan Sudan masu kyau da tsada sai kayan yaran shi suma zubin na yaran sudan ne. Nai mamaki kwarai don daddy ba ma, abucin yo muna tsarabq bane idan ya tafi tafiya na fahinci hakane tun ban shiga gidan da sunan aure ba a gareshi. Don dan dama idan yai tafiya da mace zai bata kudi yace tai tsaraba idan taga dama amma shi baya sayowa ko da yara tsaraba idan yai tafiya. Sai na fahinci duk yadda akayi akwai matsala ne gayin haka a gareshi haka yasa ya daina sayo kayan tsaraba a bangaren shi don kwanciyan hankalin shi. Nace ai mu sun goga muna tsiya yau sai gashi zamana a nan tare dashi ya sayo muna tsaraba sai abin yabani mamaki sosai. Kayan sun min kyau jira jake ya gama waya naji ba asin kan kayan nan dai na diga daga kayan ina yaba kyawon su a raina don har baba sai da ya samu tsaraban har hula da takalma da su falmara irin na yayan larabawan sudan din. Yana gama wayan kuma aka sake kiran shi ashe Zulface tana mashi sannu da dawowa har take tambayan shi yaushe zai shigo kano ne ? Yace da ita sai na huta ko akwai matsala ne tace ai ba a rasa ba don so nike kazo sai a zauna tsakani da matan ka fada masu motar daka aje don zuwa makarantar yara na kowa da kowa ne bai na diyan su ba kawai don sai a wuce abar min ya ba a dauke ta ba. Yace haba Zulfa har yaushe na dawo da za, a tare ni da wani korafi haka tace na sani abin ne ya soma isa na wallahi shiyasa nai magana. Yace to sai ajirani nazo naji matsala may yake kawo hakan ne kuma sukai sallama ba tare daya fada mata ranan da zai shigo ba din. Ya kashe yana cewa kai bisimillahi zasu soma ke nan ace mata ba zaman lafiya kullun da sabon fitinan da za, a tsiro ma a gida don bakin fitinar tsiya. Lokacin nai magana nace daddy ai kaji abinda ta fada tunda ko kaji tai magana akwai abinda akayi mata ne kan hakan. Yakamata a duba agani inda matsalan yake don a gyara fitina ba dadi wallahi ni dai yanzu Allah ya rufa min asiri na dan ketare wanan tunkuna kagin mu koma kuma a dasa inda aka tsaya a baya. Yace ku koma ina kina ganin akwai inda zaki koma ne kuma can sai dai idan ni na bar garin nan da zama ko zaku koma can yanzu yadda na san dadin zama da mace una zan iya zama kuma ni kadai. Nace to amma daddy kasan hakan ba mai yuyuwa bane tunda bani kadai bace muna da yawa dole ne kuma a raba zuwa nan din watarana don bazan tabbata nan ni kadai ba. Yace a naki tsarin ke nan amma ni kan ai nasan abinda zai min kyau ba sai wani ya tsara min ga yadda zan yi ba agidana. Kawar da zancen nayi ta hanyan tambayan shi cewa daddy naga kaya gasu da kyau kuma sosai yace bakece da zan tafi kikace sai kunga tsaraban Niger ba ? Naso na sayo maki sarka sai dai ance na bari idan na tafi Dubai anfi samun na kwarai a can . Godiya nafara yi sai kuma nake cewa kayan sun hau a yadda muke idan kowan mu ya cire guda guda ina ga uku zasu saura. Yace ban yo tsaraba da wani ba amma idan kinga zaki basu ba laifi ga hakan duk fitina da akayi ke kika jawo shi. Nace ba matsala ai hakki ne akan ka dadi nan na zaba na ware namu yana dai kallona nace Amira ma ya kamata ace ta samu a ciki tunda sun hau. Yanzu aigaki gasu sauran biyun yace sai ke ki dauka don dama ni ake na sayo su duk don ban son zancen na wance yafi kyau da haske nace ba komai ba dai ka sayo ba ladan ka naga Allah ai. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE, , , , , , , 70 Satin daddy uku da dawowa daga sudan ya shirya zai tafi kano sai dai kafin lokacin sai da yasha korafi a wurin matan shi na can kan rashin zuwan shi gida da baiyi ba. Banyi mamakin rashin ganin bai dauki wani kaya ba daga nan daga shi sai wayan shi da laptop din shi kawai ya tafi nai mai rakiya har kofan sai da naga dagawan shi na bar kofan nakoma ciki a raina sai ina jin ba dadi ba ina ruwan saboda miji dadi. Nan ya yafi ya barmu da kewan shi nasan ko na kirashi ba zan samay shi ba a lokacin don haka naci gaba da harkokina kawai. Kamar yadda a kwanaki yai muna zuwan bazata suma yau din dai sai ganin shi sukayi ya dawo garin kawai bai sanar dasu zuwan shi ba. Ya samu matan duk basu gida gaba dayan su duk dako rana yayi a gurin mai gadi yake jin lokacin da kowa ya fita daga gidan. Su dake hake da zuwan shi su mai korafi sai gashi abin ya juya su yanzu yake jiran dawowan su yaji da izinin wa suka fita daga gidan ne. Antyna ce tafara dawowa daga unguwa wai ta tafi gidan Hannatu kawar ta ne don sun kwana biyu basu gaisa ba da ita shine yau ta dan leka ta. Tana dosowa gidan taga motar shi a haraban gidan tace a,a shi wanan ya dawo ne babu ko sanarwa haka yai ma mutane bazata. Nan dai ta karasa daga ciki tana mamaki sai fada takeyi tana fadin kai akwai dai muna funci a duniya shine Rama ta kasa kirana ta sanar dani don kawai kulin sheri. Tana zama ta jawo wayan ta nan taga miscall dina har sau biyu dana kirata bata sani ba ashe wayan yana a sillent ne. Tace muna funci may yasa tun jiya bata fada min da zuwan shi ba ai munyi waya da yamma da ita amma bata sanar dani yau zai shigo ba ai. Kai maikishiya dai bata mutuwar Allah inji hausawa duk dai ban tsira ba ke nan daga kazafin ta din. Kamar yadda ta dawo haka ma sauran suka dawo zuwa yamma sun tar da bako a gidan haka suka dinga shiga daya bayan daya suna gaida shi da zuwa ko wace kuma sai ya tambayeta hujjanta na fita bada izinin shi ba da sukayi. Haka ya rufe masu baki akan korafin da suke son yi mashi kan zancen dake cin su arai kowa taja bakin ta tai shiru da hakan. Ba fuska ga korafin da kowa ta shirya mai don gudun kada su daukowa kan su fitinan da zai jawo masu matsala a tsakanin su. Nan dai ya zauna bai fita ba har dare sai da anty ta shirya abincin shi sai abin ya zama mata banbarakwai don bata saba kaiwa ba, bata kuma saba kwaso kayan idan ya gama ci ba. Sai abubuwan yanzu ya koma mata sabo don jikinta baya son wahala a cikin shi saboda lalabashi takeyi da tayi abu mai wahala yanzu zata kwanta ne. Wanan abin ya dan sata tuna da Rahama da yanzu tana garin itace zata kai kuma ta kwaso duk da rashin dadin ran da babu a tsakanin su bai sa ta daina taimaka mata ba itace ta gyara part din yadda ya dace amma yanzu gashi dole ita da kanta ke komai don bata farawa ta tura yar aiki tace tai mata wani abin a gurin maigidan. Sai washe gari ya tafi gidan su, gaida mahaifan shi inda mahaifin shi ke tambayan lafityan mu har lokacin dan dattijon na fama da kan shi da jiki ga tsufa ga ciwo. Daddy yai murmushi yace suna gaida ku Alhaji mahaifin nashi yace da alama wanan dabaran da kayi yayi tasiri a yadda jikin ka ya nuna a yanzu. Murmushi daddy yayi ya dan shafi fuskan shi yace gaskiya ne Alhaji nima a yanzu hankalina yafi kwanciya don duk korafin da za, ai min zan iya hade shi saboda haka shine kwanciyan hankalina. In ko ba haka ba da nufina na kara gyara wanan tsohon gidan nawa sai ita Rahama din ta koma cikin shi da zama. Saboda may zakai haka ka raba masu gida muryan Hajiyan shi ce dake shigowa kuma maganan da suke a kunnen ta. Tace ba a aure su aka auro su ni yanzu ba zan yarda ba su kashe min kai ga banza don duk abinda ake ciki a gidan ina da labatin shi sarai. Har may kaiwa wanan yarinyar wanda su bakai masu shi ba ita har wani dadi taji don sun samay ta karamar yarinya kuma dai tana da biyayya ai da yar bariki ka kwaso masu duk wanan tsiyan bazasu yi shi ba haka don basuga wurin yi ba. Yarinyar dai ta san ya kamata shi ya kawo haka inda yan zamani ne ai ba zata tsaya dubaiyyan komai ba akan su sai dai a rikice gaba daya agidan. Kaga sunyiwa kan su ke nan idan rashin mutuncin yaran zamanin nan ai sun fi kowa iya wa don abinda yaran yanzu zasuyi sai ya daure maka kai kai babba. Yanzun dai wanan hukuncin da ka yanke shine daidai dama sun saba cin kan su sai suyi tayi ai tunda shine aikin su. Alhaji yace ni Saade ma tafi bani mamaki wallahi yarinya ana murna da halinki na dattako sai ki kwaso shirmay kuma ki saka a cikin harkan. Dama halinta ne kune baku ganewa don shiru shirun mutum mugune tanayi tana nokewa kamar batayi ba. Sun dauki lokaci yana hira da mahaifan nashi daga karshe yai masu sallama ya bar gidan tare da basu alheri irin yadda ya saba basu kullun idan ya dawo. Gidan Bashir ya wuce daga nan don sunyi waya zasu hadu dama dashi din bashir na ganin shi yace kai mutumina anya ba wani injin Rahama ta turaka ba wanan irin fresh haka may ye sirin hakan ne wai ? Murmushin shi yayi kawai yace da bashir din ka faye gulma wallahi kowa ya gani yai shiru sai kaine mai magana. Ai kaima kasan ko may ye sirin shine kwanciyan hankali banda wani zullumi a yanzu da zan shigo gidana dashi. Sai dai a tare ni ana haba haba dani kamar wani dan baby karami ba a yarda raina ya baci ko a fada min bakar magana da zai sa raina baci. Wallahi bashir yanzu na kara fahintar halin yarinyar nan sosai dan zaman da mukayi da ita din nan mu kadai a can. Saade bata san tayi sakaci babba ba sai da ta zubarda mutuncin ta akan yarinyar da ta yarda da imanin ta har tai shaawan hada taraiyan mu da ita sai daga baya kuma wai abin ya koma mata ciki kuma. Banda wani matsalan da zance gashi akan wanan yarinyar don hakkirin yarinyar ya baci sosai fiye da tsanmanin ka. Yace to dama ai abinda muke fata ke nan a samu gayin haka Alhamdullahi kuma tunda an samu din gashi a zahiri kuma mun gani ai. Don wallahi gaba daya ka canza kayi wani fresh dakai Allah ko, daddy yace ai hindatu naga tana so magana amma bataga fuskan hakan ba sai cewa take wai indai an cuce su Allah yana gani. Bashir may na ajewa Rahama wanda su nan ban aje masu shi ba ban taba ba yarinyar nan wani abinda ban basu ba a rayuwana yanzu haka tsaraban da tace na sayo mata na Sudan nasa matar kamal ta sayo mata saids ta raba shi tace akawo masu har Amira sai da taba daga ciki. Yace kaga ma na manta ban basu ba balle kuma naji may za a ce akan kayan don nasan sai sunyi korafin shi kan. A daiyi hakkuri mace ko daya ce sai hakkuri da halinta balle kai daka cika sunnan ma,aikin Allah kai hudu gaba daya. Yace aiko nasan na cika sunna don ina ji a jikina wallahi mata halin su sai su wallahi bashir wani lokaci har nakan ji na barsu na huta gaba dayan su zaifi min alheri wallahi. A, a kada kai haka please ai sai duniya ta zage ka ma gayin hakan don ba za, a ga laifin su ba sai naka don nasu boyewa zaiyi. Kuma in kai haka ai dole wasu kuma zaka auro tunda ka saba zama da mata kuma duk halin su daya ne kana ganin su nan. Nan dai sukai hira daga karshe ma suka fice zuwa unguwa basu dawo ba sai dare ta sauke bashir ya nufi gidan shi. Nan dai ya samu an hada mai komai yai wanka ya zauna don yaci abinci Zulfa ta fara shigowa ya mika mata key yace ta kwaso mai kaya a motan shi a baya tana fita hindatu na shigowa falon. Sun gaisa take cewa dashi yau ya fita ya shige gari haka, sai da ya dan kurbi ruwa ne yake tambayan ta idan na zauna gidan wani abu zakiyi min ne ? Tace ko ban maka komai ai muma muna son ganin ka ko tunda an jaye muna kai sai lokacin da muka gan ka yanzu a garin nan. Dama abinda kike so na zauna ke nan a gida kina fada min idan kin isa ai kema mace ce sai ki jayeni yadda aka jani din ko ? Tace inda kana jayuwa min da na ja din don nafi kowa son yin haka amma muna ji muna gani ana son a fifita wacce tazo bayan mu da karfi da yaji haka ? Kafin ya bata amsa sai ga zulfa da kaya tashigo falon ta zube su a gefen kujera kamar hafin baki sai ga anty tai sallama ta shigo itama idon ta akan kayan da ta gani a gefen shi. Sai da ta kai zaune tafara gaida shi ya amsa mata da yaya aiki ya gida tace Alhamdullahi yace ga kayan nan naku ne sai na Amira guda daga ciki sauran na yara ne ku duba ku gani kamar da sunaye a cikin sa. Da sauri hindatu takai hannu tafara duba kayan tai daidai da wanda aka rubutawa Zulfa a jikin ledan tace wanan Zulfa naga an rubuta mana ? Sai taa shiga daga sauran da karfi ta dawo akan wanda aka rubutawa zulfa din ta rike tana cewa ni wanan din nake so ai. Zulfa tace wallahi kinyi kadan don da suna na yazo ko ban so ko shi nake so balle kuma kallan yai daidai da jikina baki. Tace wallahi baki isa ba yace miko min nan ta miko mashi yace kwaso sauran mun sauran nan ta miko mashi ya duba sunayen yana mika masu kayan. Sina shiga hannun anty ta sheda rubuta na take ranta ya baci sai da ta bari sun gama haukan su tace da shi wai Rama ne ma ta zaba muna kayan ? Yace eh itace tace ai a kawo maku din don natane ta aiko maku dashi take wurin yai tsit ba wanda ya sake magana kuma daga cikin su. Sai tace yanzu Ramane kuma zata zaba muna kaya ko may hakan ke nufi wai ? Yace amma kinji abindana fada maki ai cewa na ta ne ta aiko maku dashi ko da wani magana ne kuma bayan hakan ? Zulfa tace aiko mun gode na dade ina son wanan kayan wallahi amma Rahama ta kyauta kuwa. Zakai wanka ne yanzu ko sai anjima ta tambaye shi don kawar da zancen don ranta yai matukar baci ga hakan da taji. Yace ko abinci banci ba ai kin gani kuma ita dai zulfa ta hada nata dana yarta tana fadin ai muna godiya ta fice daga falon. Hindatu kamar bazata tashi ba itama ta dauki nata dana yarta tabar falon cikin fushi tafice a fusace ta barsu nan. Shiru falon yayi kamar babu kowa a cikin sa ya jawo abinci ya fara ci sai dai yaji yai yawa loma biyu yayi yace wanan yajin fa haka bayan kin san yaji bai bani bashi a cikina ? Tace yayi yajine miyan ni ban maci naji ba ai balle naji yajin shi yace yayi kyau ya ture abincin gefe ya jawo laptop din shi yana dubawa. Tai dan jim a wurin can ta mike zata fice batare data dauki kayan da aka basu ba yadan dago kai yana kallonta, yace su kayan da kika bari a nan fa ? Tace dashi ban ga abinda zanyi dasu bane don ban rako ko wace mace ba zuwa duniya yace sai ki dauki na yarinyar ba matsala ai idan kinyi hakan don dama nasan zakiyi hakan tun can. Ita dai ne da bata da zuciya har yanzu bata san matsayin ta a gare ki ba take sauran bin ki har tana wani jadda min wanan ne na anty na don zasuyi mata kyau sosai kuma sun fi laushi. Yanzu bakiji kunya ba agaban wa tan nan kika nuna bakin cikin ki akan Rahama abinda su ya kamata ace sun nuna wai sai ke data san darajan ki da kimarki ne zaki nuna hakan. Kamar zatai magana bayan ya gama maganan shi sai kuma taja bakin ta tai shiru kawai tafice batare da ta dauka ba. Ya bita da kallo har ta bace mai ga gani yaja tsuki yaci gaba da yin abinda yakeyi a laptop din nashi. Koda ta koma part din ta babu irin tunanen da batayi ba akarshe sai ma ta tura Amira wai ta dauko kayan a falon baban su don ko tsaya ta duba dama batayi ba don haushi da takaicin da taji. Amira tazo daukan kayan daddy yace gasu nan ta kwasa a saman kujera yace idan kinje ki turo min Soja yazo ina neman shi. Nan dai yarinyar tafita tana murna tana shiga tace mummy amma kayan nan suna da kyau wallahi kuma kalan nan ya matukar burge ni. Tace aje su nan don Allah sai yaran suka shiga daukan nasu suna farin ciki da samun kayan. Nan Amira ke fadawa Nasir sakon daddy bai tsaya ba ya tashi yafice yaje gun amsa kiran da akai mai din. Sun dan taba hira yaron ke tambayan mu yace muna gaidasu Nasir yace daddy idan anyi hutu ina son zuwa wurin small mum amma mummy mu tace wai bazan tafi ba yace ka bari idan anyi hutun sai na turo a dauke ka ko ? Yaron yaji dadin ya fara murna can kuma yace ina son inga baba nasan yanzu ya kara girma sosai kilama yana tafiya ? Sosai daddy yaji dadi a ran shi yadda dan shi ke son dan uwan shi do ko yaushe a cikin tambayan shi yake idan sunyi waya dashi. Nan dai suka juya hiran kan karatun su inda ya fadawa uban abinda suke bukata yace gobe zai bada kudi sai a sayo masu in Allah ya kaimu. Sun dan taba hira yace yaje ya kwanta gobe akwai school har yaron yakai kofa yace daddy kada ka fadawa mummy batun tafiya na don zata hanane idan taji. Yai murmushi yace bazan fada mata ba ai sai dai taga kawai mun tafi ba shike nan ba yace hakane daddy. Bayan yaron ya koma take tambayan shi kiran da uban ke mashi yace ya tambayeni ne abinda muke so a saya muna sai tai shiru kawai batare data kara magana ba. ********* ********* ********* Ni dai na fahinci tun zuwan daddy idan na kira anty da kyat take amsa min tana min magana a cikin basarwa sai dai ban fahinci komai ba ga hakan. Komai yana gudana kamar yadda ko wani gidan maaurata yake gudana, duk da ba a wuri daya muke zaune ba a rasa dan abinda kaje ya dawo a tsakani. Wani lokaci zanga abin bacin rai don kirkiri a gabana wata zatai mai waya da tana da bukatan kudi haka zai tura masu ina kallo niko dake nan zaune tare dashi ba wai kudin yake bamu ba. Sai dai babu abinda na rasa a gidan don ko kayan kwalliya haka zai sayo muna su pad da sauran abubuwan bukatu na mace dana gida. Ina gani sai dai hakkuri da haka din don na fahinci shi idan bakai ka tambaye shi kudi ba bai iya fitarwa yaba mace su haka kawai. Gashi su suna can suna zaton ni ina nan ina jin dadin rayuwana ne tare da maigida su suna can anbarsu abinda basu sani ba suma dake can sun fini samun daga gare shi. Kwance nake na mike a saman dogon kujeran dake falon tunda na dawo jikina nake jin ba dadi sosai. Atika da tadawo daga school ta debo abinci a plate tazo inda nake tana ci take naji wani irin tashin zuciya ya kamani. Da sauri na mike na bar falon don ma kafin na shiga ban dakin har na fara amai ko dan yadda naji yazo min a lokaci guda. Sai da na watsa ruwa na fito na saka wani dogon riga a jikina falon na dawo na kwanta duk jikina ya mutu min da nauyi. Hiran su suke amma na kasa saka masu baki yadda na sabayi ko yaushe sai ma idanuwa na dana lumshe kawai ina jin jikina ya sake min. Yamma lis yashigo gidan kamar yadda ya saba wani lokaci don yawan goslow da ake dashi. Sai sannu da zuwa suke mai ina kwance da kyat na iya bude baki nai mashi sannu da zuwa ya samu kujeran dake daga gefe na ya zauna. Hira yake da Atika don abokiyar hiran shi ne a wanan lokacin idan ya dawo gida, sai dai duk maganan da suke idona yana a rufe don ban jin dadi. Jin shirun da nai masu ne bayan gaisuwan da mukayi ban ce dashi uffan yasa shi dagowa yana kallona yace yaya akayine nagan ki a kwance a wanan lokacin haka ? Na dan gyara kwanciyana ina fuskantar shi inacewa dashi yau ban jin dadin jikin ne ina ga zazzabine ke son sata na dai. Wani aman ne ya kara zo min a lokacin na mike da sauri na nufi dakina tunda nai wanan amai din jikin nawa ya kara sakewa. Da kyat nai sallah daga haka na haye gado na kwanta tare da dunkulewa wuri daya, take kowa yasan bani da lafiya yaso muje asibiti amma nace ya bari harda safe idan na fita zan sa a dubani can. Sai cikin dare zazzabi yaso ya hanani barci dole nasha paracetamol na dan samu saida a jikina da safe da kyat na lalaba na shiga asibitin. Na dan yi treatment din kaina cikin ikin Allah kuma sai na samu sauki sosai daga haka na fita batun ciwon koda ya dawo ya samu na samu sauki bayan wayan da nasha daga gareshi yana tambayan lafiya na. Naci gaba da abubuwana normal sai bayan kamar sati kuma sai na fahinci duk dare sai zazzabi ya rufe ni da kyat zanga safiya ya waye min sai kuma na mike tangaram dani. Abindai yai yawa gashi ban son daddy ya fahinci hakan sai mukurkusa nake ni kadai ban fadawa kowa ban da lafiya ba. Amma kana ganina zaka san na fada sosai na ramay harda dan wuya nayi don wahala. Kwance nake don yau da wuri na dawo gidan don jikin yakiya min sai da na dawo nasha magani daga inda nake kwance bayan na dan ji sauki kiran layin zarah nayi don mun kwana biyu bamu gaisa ba da ita. Mun gaisa muka dan tambayi lafiyan juna kwana biyu nake cewa wallahi Zarah ban da lafiya duk kwanakin na sai dare yayi zazzabi yake rufe ni sosai. Abinda ya fito bakinta shine kinyi test kuwa Rahama nace wallahi Zarah tsoro nake ji ina son yi amma ban san result din da zai bani ba. Tace baki da hankaline Rahama maye a ciki da zakice wai kina wani jin tsoro to wallahi ni raina ya bani ciki kika samu. Gabana naji ya fadi don abinda nake gudu ke nan dama nace kiwa Allah ki rufa min asiri duka duka baba watan shi fa goma sha uku yanzu Zarah. Tace to may ye na wani tsoro cikin banza ne da da uban shi, wallahi kiyi test ki san abinda kike ciki kada kizo ki halaka kan ki da wasu drugs can na daban. A sanyaye nace da ita naji zanyi Zarah amma don Allah maganan ya tsaya dagani sai ke don Allah ban son ko daddy ya sani tace an gama amma don Allah kiyi test din nace naji zanyi. Sai bayan na gama komaine na shiga daki na auna kaina abinda dai nake gudu din ne ya faru don ya nuna min positive akwai ciki ke nan tare dani. Wani irin faduwan gaba ne yazo min a take hankalina yai matukar tashi sosai sai ga wasu hawaye na sulalo min a idona. Tsoro farfgaba da tausayin yarona ya kamani nace na shiga uku ni Rahama yaro da baiko kai lokacin yaye ba ace kuma ciki gare ni. Ni yaya zanyi da maganan mutane kuma akaina yanzu tundai kishiyoyina musan man ma anty ya zama dole naja bakina nai shiru nasan mafita da cikin nan tun kagin ya baiyana a hanani wani yunkuri akan shi. Haka na lalaba na kwanta tunda safe sai ga kiran Zarah tana tambayana yaya kinyi kuwa Rahama don jiya ban iya barci ba ina tunanen ki. A sanyaye nace da ita wallahi Zarah nayi yabani positive tace bagashi nan ba zaki tsaya Allah yai maki sani kuma ki cuci kanki a banza. Nace zarah nina shiga uku yaya zanyi da ciki ga goyo kada yaro na yazo ya cutu ni gaskiya zan san yadda zanyi wallahi ko. Tace kai ke kan Rahama sai ina gani akanki yar fari ta kare wallahi cikin da ake nema da kudi ke Allah ya baki shine zaki sakaci dashi. To wallahi ahir din ki don idan kikace zaki wani yun kurin barar da cikin nan kin san ba karamin fitina zakuyi da mijin ki ba ke ma kin sani dai. Nace Zarah ni yaya zanyi ga ciki ga goyo ga kuma wanan aikin da ba hutu a gare shi nakin dai na shiga uku wallahi zarah. Tace waiko Rahama kan ki daya kuwa kike fadin wanan maganan haka ko harkin manta da irin gorin da ake maki a baya har ana kiran ki da wai ke juya ce baki haihuwa. Tace ni dai abinda zan fada maki shine kiyi hakkuri don ba aiwa Allah shishigi ga alamarin shi don baki san ko wani irin da ubangiji ya aiko maki ba da har kike wani ikirarin zubar dashi. Idan kinyi hakkuri har kwana nawane kin haife abinki kamar yadda kikace kikama bakin ki sai dai a ganki dashi kawai kowa yasha mamaki ba shi ke nan ba. Nace naji Zarah na kuma gode da kulawan ki akaina Allah ya raba mu lafiya tace amin koke fa zakibi ki tayar wa kanki da hankali bayan kin san cewa akwai illa ga mai karamin ciki idan tana saka damuwa a ranta. Koda muka gama waya da Zarah ni hankalina bai kwanta ba sai sakawa nake ina warwalewa ni kadai a raina ban fita ba ranan don weekend ne ba zuwa ko ina ranan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , 71 A cikin rashin walwala nake duk kwanakin nan don damuwa akan cikin dake a jikina ga tausayin yaron da nake goyo dake kamani. Nayi sakaci da ban yi saurin gane hakan ba da wuri sai da abu ya zauna sosai a jikina don yanzu ni kaina ba zan iya cewa ga adadin watannin cikin ba sai na duba don ba al, ada nake ba da nake goyon. Sai ma da daddy yai tafiya ne kafin ya dawo na danga jini na kwana uku kuma ya dauke take na tuna tun wanan lokacin ban sake ganin komai ba kuma har wanan lokacin. Bakina naja na tsuki na tsurawa sauratan Allah ido sai dai idan na kalli baba sai yaton ya bani tausayi dole na hado mai magani wanda nasan zai gina mashi jikin shi na kuma dinga sa Aisha tana bashi abinci inganttace mai kara bashi lafiya. Alhamdullahi don sai ma naga ya kara min kuzari sosai fiye da da can baya da yake rashin walwala sosai haka zan faki udon mutane na rugumashi in ta kuka don sai ina ganin zan iya rashi ne. Ina kwance da yaron dayai filo da jikina muna barci a falo don ban fita ba yau ina up, mafalki nake ko mai don muryan Nasir danaji a kunnuwa yana fadin little mum. Na bude idanuwa na da kyat na sauke su akan yaran dake tsaye a kaina har su hudu cikin mamaki da murnan ganin su ne ya kamani a lokaci guda na mike ina fadin Nasir kune ko mafalki nakeyi ne wai na jawo jinior zuwa jikina. Muryan daddy ne naji yana fadin ke yanzu baki da wani aiki sai barci mun shigo muna sallama amma barci ya dauke ki haka ji yadda kika kwanta da yaron nan idan ya fado fa. Shi da kan shi ya gyarawa yaron kwanciya na juya wurin yaran da har sun zauna ina masu sannu da zuwa yaran mata sai bin gidan da kallo sukeyi tako ina. Sai ga Atika ta fito tana ganin su taji dadi tace Lah Amira kune kuka zo ashe Amira din tabi Atika da wani irin kallon mamaki. Nasan ba komai bane sai mamakin yadda ta canza a dan lokaci kankani haka zaman birni dama kai baka sanin ka sake sai dai wani ya gane maka hakan. Jin hayaniya yasa Aisha da helen fitowa su ma sannu da zuwa suke masu ba bata lokaci sai ta juya kitchen ta dauki masu ruwa da abin sha takawo masu. Nan dai na zauna dasu ina tambayan su mutanen gida Nasir ya kasa hakkuri ya mike zuwa inda muke ya dauki yaron a kafadan shi. Take yaron ya bude idanuwan shi yana kallon dan uwan shi kamar ya sheda shi sai ya danyi murmushi ya lafe a jikin dan uwan nashi yana sauke nunfashi. Ya shedani nace haka yake dama idan yaga maza ya kama bin su ke nan yana son su dauke shi abinci Aisha ta kara kawo masu Amira ce ta fara bude kulan naga ta kurawa abincin ido kawai. Munan dai zaune tare da su daddy ya shige dakin shi ban ko samu bin shi ba nai mai sannu da zuwa da kyat na mike na bi bayan shi dakin nabar yaran nan zaune suna cin abinci. Ina shiga na samu zai shiga wanka nace sannu da zuwa yace ai na zaci murnan ganin yaran ki bazai bari yau na samu taro ba. Nace abin ne ya bani mamaki don banyi tsanmanin zuwan su ba din yace dama ina sun supraise dinki ne yasa ban fada maki cewa anan zasuyi hutu ba ai. Nace daddy nagode yace da akai mai kuma nace daka kawo min yaran nan don sada zumunci a tsakanin mu ina kewan su wallahi sosai. Yace to ai gaki gasu yau sai kewa ya kare yana fadin haka ya shige bathroom ya rufo kofan duk da ba wanda zai shigo dakin don bani yarda kowa ya shiga dama dakin saboda sirin mu ne. Na juyawa nayi na fita zuwa falin na samu yarsn sun gama cin abinci nace yanzu abinda za, ayi shine na nunawa kowa dakin shi ko inda zaku zauna musha hutun mu. Nace kai Nasir dakai da Jinior daki daya zaku zauna Aisha kaisu dakin can na kusa da hanyan fita tunda ku maza ne. Nasir yace dakyau little mum shiyasa nake son ki wallahi ko yaushe ina son mummy ta raba min daki da wanan amma taki sai tace waini yaro ne. Nace to aini yau gashi na raba maku dakin ko sai ka zauna can abinka daga kai sai Jinior kawai Amira kuma zaku zauna dakin dake kusa dana su Aisha ina fatan tsarin yayi maku daidai sukace yayi mum. Bayan kowa ya shiga nashi dakin ne sun yaba da kyau da tsari din dakunan don ko ina akwai gado da mirro da kuma drower aciki duk da ba kowa amma a gyara suke don helen na gyara su akai akai. Daddy bai fito ba sai da zai tafi sallah inda yasa Nasir da Jinior a gaba suka tafi wurin sallah tare dashi. Da dare gaba daya muna falin sai faman hira ake kwasa wasu na kallo daddy ya fito daga dakin shi nasan abinci yake so na mike na shirya mai table yadda ya dace ayi. Nan ya zauna ya soma cin abincin bai dade da zama ba yaji kukan baba yace a miko mashi shi inda yake nan suka zauna suna ci tare. Daga inda Amira take zaune naga ta kura masu ido tana kallon su, nasan ba komai take kallo ba sai yadda daddy keyi da yaron take kallo kawai. Bai jima ba ya mike ya bar mu don yanzu gida ya cika ba halin zama yadda ya saba yi muna da muke mu kadai a gidan. Ban dauki lokaci ba nai masu sallama na wuce na samu daddy can har ya kwanta don yana da gajiya a jikin shi na tafiyan da sukayi din. Ranan dai shi kan shi bai fahinci komai ba a gareni don bani da lakka ko kuzari a tare dani don haka maneji kawai mukayi muka kwanta asuba ta gari. Da safe mun tashi na hada break fast a gurguje nayi komai tun kan yaran su fito muka bar gidan kowa ya kama gaban shi. Bayan fitan mu da dan wani lokaci yaran suka fara fitowa daya bayan daya suna karyawa Amira ce kusan fitowan karshe ida take fada da Ihisan wai ta kwashe madara ta bar mata kadan. Sai Aisha tace bari na karo maki ai akwaishi ba iyakan shi ke nan ba ta karfi roban taje ta zubo mata madara mai yawa a store takawo mata. Amira ta kalli madaran tace yana da yawa ke nan ashe shine aka zuba muna dan kadan a roba muda kayan uban mu ? Kafin Aisha tai magana jinior tace sai fada anty ta cika muna roban nan har baki sannan madaran da aka bari ai a gida ba haka kike sakawa ba da yawa. Tace wallahi Jinior zan gwagware ka yanzun nan da kai nake magana ko may idan can bana sha ai anan yanzu inda ake saya sai nasha yadda raina ke so tunda nasan karowa za ai muna. Sai bayan na dawo ne ina dakina zaune a saman abin sallah Aisha ta shigo dakin tana gaidani da dawowa na tambaye ta babu dai matsalan komai akan bakin mu ko ? Tace ba komai wallahi nan muka wuni dasu muna hira a falo sai dai Amirace ma nake ganin za, a samu matsala nan take fada min abinda ya faru da bana gidan. Murmushi nayi bayan nagama sauraren ta nace kyale ta Aisha kada ki taba mata magana akan komai da zatayi ko ta fada a gidan nan ai gidan ubanta ne itama dashi take takama da hakan. Tunda naji take taken Amira da zuwan ta sai na san yadda zan zauna da ita don mu rabu lafiya ba matsalan komai ga zuwan su. Sosai nake basu kulawan da ya dace ba abinda yafi burge su a gidan kamar irin kayan motsa jikin da ke a wani daki inda daddy kanyi asubancin shiga yana motsa jikin shi a ciki. Ko yaushe suna ciki wai suna motsa jikin su don suna daukan abin kamat kayan wasa a garesu ni kuma bana hana su yin komai. Ranan da wuri na dawo gida don ina son da yamma inda zaga gari dasu don yanzu ina fita da kaina da mota cikin gari. Bayan kowa ya shirya ne muka fito don zuwa wurare suga garin da idon su tun wurin shiga mota taso ta samuna rikici wai ita sai gaba zata zauna tare dani. Dana fahinci may take nufi sai nace a,a ai ku duk mata ne don haka Nasir da Jinior zasu zauna a gaba Nasir da bai magana yaji dadi yace ilove you mum. Tunda muka fita ana hira a mota tai shiru tana kallon ko ina ba wanda yabi ta kanta muna tafe muna hira ina nuna masu wurare a garin. Daga nan mukaje wani park dasu nan na koma gefe sukai yadda suke so a gurin da zamu dawo muka biya Sahad store dasu ssayayya ssosai mukayi muka dawo gida duk jikina ba dadii karfin hali ne kawai nake don yaran. Amma hakan bai boyu ba a gareni don sai da nakai kwance na danyi zazzabin kwana biyu na mike. Kwana biyu dda jin sauki na kuma na kwashi yaran har asibitin mu muka shiga nakai Nasir yaga barack din sojoji yakara jin dadi sosai a ranshi. Bayan mun dawo gida ne na huta sai na tuna da wani kayan unders dana sayowa Amira a hand bag dina na mike na nufi dakin da take don nakai mata kayan. Waya take babu tantama nasan da mahaifiyar ta take wayan tana cewa mummy bakiga yadda ta koma bane sai sayayya take muna kamar bada kudi ba wallahi. A daidai lokacin nai sallama a dakin kuma naji abinda ta fada nace ai waya kikeyi ashe ga wanan kayan naki a handbag dina na gani ashe ban saka leda ba damuka fito. A yatsine tace dani kawai ok ta karba na fito daga dakin batare da saka komai a raina ba, abinda ban sani ba kullun cikin waya take da uwar tana fada mata abinda akayi da wanda tagani anan din. Ashe da daddy zai wuto da Nasir sun yi gardama da ita tace bata yarda ba shikuma yace sai ya gani shine tai dabaran turo Amira tace sai dai idan dukka yaran zasu tafi yace aishi yafi buukatan hakan don tasan idan da Nasir kawai akazo bazataji komai ba gare shi. Satin su uku tare damu uban ya shirya su suka koma gida ba don yaran sun so ba don ko ita Amira din taji dadin wanan zuwan da sukai min din. Ranan da suka koma gida tun ranan ta fara tsiyayawa uwarta labarin irin abinda suka gano a can din. Nasir dake zaune ranshi ba dadi yace kai munafunci baiyi ba wallahi yanzu ke duk irin abinda akai muna na gata har kinga wurin gulma anan ? Ranta uwar ya baci tace dashi rufe min baki mara tunane kawai da baian ciwon kan shi ba an barmu anan cikin wahala ana can anajin dadi. Yace yaushe ma daddy din ya zauna a gida wanda idan ya fita sai yamma yake dawowa gidan kuma in badon inta little mum takai mu yawo ba yaushe daddy ke da lokacin mu ma. Bayan kwana biyu da karban girkin ta sai da sukayi ba dadi da Saaden kkan abinda yara sukace mata a kaina. Nan ya rufe idon shi yai mata tas yace wallahi sai dai tayi hakkuri in bata gode ma abinda yake mata ba tana ina yi gaba shi yagaji da fitinan ta kullun. Yace ashe dama kin tura yar kice don taje tai CID a can to kinji abinda ranki ya baci duk irin kokarin da akaiwa yaran ki amma baki gode ba yace ni na riga na aje zancen ki ko wallahi ba yau ba tunda baki da tunane. Ya kuma samu Amira da Ihisan yai masu tas yace masu munafukai ai sunyiwa kan su don ba zasu kara zuwa ko ina ba. Yaran sunyi kuka sosai sun kuma yi da sun sani da basu fadawa iyayyen nasu komai ba da suka gani acan Amira harda karya ta hada wuriin fadin zancen ta. ********* ********* ********* An bugo min cewa mahaifina baida lafiya hakan ne yasa na shirya zuwa gida don a yadda aka bugo min ma sai nake ganin kamar baida raine. Tare da daddy muka tafi lokacin cikina yana da wata hudu a jikina amma ba a ganewa don in ba kayan aiki ke a jikina ba to kuwa baka rabani da hijjabi ajiki na. Da dare muka sauka ban shiga wurin kowa ba tunda ni da nai tafiya ba wance tazo taro na sai duk suka share ni kamar ba zuwa nayi ba. Sai washe gari da safe har mun shirya zuwa kauyen mu naga ba zan iiya share anty ba hakana ko banza nice kasa gareta ai. Na shiga wurin ta mu gaisa tunda nai sallama tana karyawa ta dago kai muka hada ido gabanta yai wanii irin mugun faduwa don gaba daya na sake mata na canza kamar ba Raman da taa saani ba nata a baya. Komai nawa ya koma na wayyayin mata ba sakin fuska nima a idona na gaida ita ta amsa min a gadarance. Nai mata yaya gida cikin rashin damu yarona yana tafiya yana saye da dogon wando da riga mai dogon hannu da takalman shi masu tsada sai kamshi yakeyi gashi fari kwal dashi sai gashin kanshi mai zubin na fulani. Ina rike da hannun shi ban sake shi ba don kada yai mata wani abin kuma nace zan shiga gida don baba ne baida lafiya mukazo. Allah ya sauwa tace dani muka fice tabini da kallon harara takke ta dauko wayan ta ta buga wa yar uwar cin mushen ta tace wai Rahana kin koga abinda nagani kuwa ? Nan dai take bata labari tace wallahi ki matse mata kada ki bata kafa kikuma fada mata ta tuna da asalin ta kada ta manta daa bazanki take rawa har yanzu. Falon daddy na shiga iinda tun kan na karasa kamshina ya sanar dana ciki ina tafe falon suna ciki da matan shi duk su biyun a lokacin sai dai kamar magana sukeyi dashi. Baba na ganin mahaifin shi ya fisge a hannuna ya nufi wurin shi ya dane jikin uban yana fadin daddy cikin gwalancin yara take uban ya gane mai yake nufi. Nai masu sallama tare da gaishe suy ban damu da ko su karba min ba sai dai alama ya nuna sunyi mutuwar zaune a wurin. Na juya nace cikin dan hausan na daya koma na yan Abuja yanzu daddy mun shirya muna son mu tafi ke nan. Yace a, a Rahama ina tare zamu tafi ki dan bani minti biyar na fito please don ina son in shiga na dduba shi kinn san damun koma ni tafiya zanyi nace ok sai ka fito ina waje. Har na juya naji hindatu tace da daya layan wuya inda an haihu da yawa aiko mijin bamu gani ma saui dai labari a haka dai za, a dawama da da daya kamar laya. Kamar na wuce sai na juyo nace nagode maa Allah Allah yasa mashi albarka amma kila gado nayi na haihuwan da dasyan yadda naga wasu sunyi. Ke wallahi kama kan ki kada kiga an rike maki maciji kina wasa da bindin shi bakifi kowa ba don kkowa ma yasan hanyan bin miji idann ya tashi ba sai an hada da yaudara ba da cin amana. Bin miji ai isane duuk waccee ta shirya tazo mu tafi don ni nayi gaba , a, a Rahama kudai tsaya kuyi abinku amma kada ki sani a ciki. Nace Anty Zulfa da wanda yai magana ai nakeyi ba dake ba daga haka nafice abina na barta nan tana kumfar baki a falon. Bai dade ba sai gashi ya fito muka dauki hanya shi ke jan mu nii dashi ne a gaba yaran suna baya. Sai da muka kusa fita garin kano naji yace watau ku mata halinku daya wurin hauka keda kikazo duba mara lafiya ina ke ina tsayawa hauka haka. Nace cikin bacin rai daddy abin matan nan ya isheni ne wallahi mace haka da bakin son fita ko yaushe daga zuwa na jiya jiya zata hauni da balai wallahi a shirye nake da kowan su don nagaji da hakkuri hakana. Bai kara magana ba muka dauki hanyar kaauyen mu a can ya barmu zamuyi kwana biyu mu dawo mu wuce mun samu jikin baba din yayi sauki sosai. Yai masu goma na arziki yai muna sallama ya dawo ya barmu a can zamu ga yan uwa kowa sai fadin canzawan mu yakeyi. Nai mamaki kwarai yadda innata ta fahinci ina da ciki ajikina haka da sauri abinda kowa bai gane ba sai ita don sai najii tace dani. Amma tun kan ki yaye yaton nan kika samu ciki ko gabana ya fadi nadago klai nace hakanane inna tace Allah ya inganta ya rabaku lafiya nace amin. Wanan katon na kwana a giidan mun mun sha hira da mahaifina kamar bashi ba munci mun sha daga nauin abincin kauye da muka dade bamu samu ba. Amarya baba ta haihu sai haba haba take dani ta rasa inda zata sani ranan don daukaka da na samu ta haihu tana goyon diya mace itama. A yadda na fahinta ciwon sugar ne ya kama mahaifina sai dai ban tabbatar ba na dai ce idan na koma sai su shigo asibitin mu a auna ashi a gani. Bai so zuwaa amma da kyat na samu ya amince da zaizo naa saya mai kayan abinci na masu sugar nace ya fara ci mu ganii. Kwanaan mu biyu hamza yazo ya dauke mu mun sha gata sosai a gida muka dawo kano da yamma na samu gida ya rikice don matan daddy sunce sai suma yaje dasu Abuja din don basu yarda ba case din daa na samu anayi ke nan don tun a mota Hamza ya fara kyankyasa min labarin halin da ake ciki. Yace daddy ya haukace masu donn yace idan sukai tsiya ko kin gama ma bazaki dawo ba a raina nace dama hakan ne ai don nasan da wuya asibintin da nake su sake ni. Ban bi ta kan kowa ba na shige part dina da mutane na gajiye tanata faman dawainiya damu cikin rashin gajiya don harda helen mukazo garin. Sai washe gari da rana na shirya tsab zan tafi na gaida iyayyen mijina da yan uwan shi, kafinn in fita na leka anty a part din ta mun gaisa ta tambayi mai jiki nace ya samu sauki. Nace zan tafi na leko su Hajiya har furin Abba zan shiga don kada taji naje yazama min matsala kuma a tsakanin mu duk da yanzu ban gudun shi idona ya bude ko. Na juya nakai kofa tace dani Rahama sai na dakata don jin yadda ta kirani sunan da ya dade banji shi a bakin ta ba haka yasa na fahinci tana da magana mai girma ke nan. Najuyo ina fuskantar ta batare dana koma na zauna ba tace ke yanzu kina ganin wanan cin amanan da kuka dauko yi muna keda maigidan shinee daidai komay ? Bafa ke kadai bace matar shi yaran nan da suka dawo sun fada min duk abinda kike a can ban yarda ba sosai sai yanzu da idona ya gane min nagani. Nace ashe dama ba hutun arziki su kaje min ba leken asiri ne yakaisu ke nan ? Tace aiko sunyi bai baci ba don dukiyan uban su ne suke ci bana wani ba kuma don ke baki da hasara da daya ke gareki a gidaan shi yasa kiika sa uban su gaba da wawaso ko ? Murmushi nayi nace dayan ma na gode da Allah yabani nima na kada nawa a cikin naku kinga suyi zumunci da yan uwan shi don nabar tarihi nima. Au lallai naga kuwa kije abuja kada ki manta cewa duk abinda kike takama yanzu dashi nice dai din nan silar shi. Nace ban taba manta halarci ba komai kankantar shi damani shiya nake shanye duk wani dacin da kike zuba min don ni ba butulu bace. Yaushe kuma? Butulci yafi wanan da kike min kuma ai ya baci nai maki rana kin min dare kina son rabani da miji ki kuma rabashi da diyan shi. Nace cikin girgiza kai Anty tare na ganku har diyan ku don haka ni Rahama ban taba tunanen wanan kalman ba a raina don ni ba azzaluma bace kuma nasan ya kamata ako ina. Wuyan ki ya isa yanka komai yanzu zaki iya fada min ai don kina ganin kin kai, ddon kina takama miji yana a hannun ki. Nace cikin dan murmushi kamar maganan bai zafe ni ba babu inda nake don har gobe a karkashin ki nake. Don nabu abinda nake maki a baya wanda na fasa yin shi ayanzu, na fannin biyayya sai wanda naga baki ra, ayin shi nake dainawa don haka girman ki da kimarki yana zaune daram a zuciya na ko yaushe. Miji kuma ni a suwa da ya zama nawa in samu mutm da iyalin shi ince zan shige gaban su ni har yaushe na shigo cikin ku ne ma ? Tace Zamu zuba tunda abinda kika zaba ke nan nace mu zuba alherin nan da kika saba yi min ina maki Allah ya kare mu daga sherin shedan. Ban tsaya sauraren ta ba na juya na fara tafiya sai naji tace takamar ki dai da dayan da kika jefa a cikin mu shine kadaran ki waike kin haifi namiji ko ? Akara haihuwan mu gani iin haihuwan ya zama banza ke nan a gidan kowa ta kwaso sharan ta tace sai anan zata juye shi a cika muna gida da diya barkatai. Maganan yaci min rai sai kuma na tuna da abindake ciki na a yanzu wanda kowa bai san dashi ba sai ni da Zarah da ubangijin mu kawai. Nai murmushi nakai hannuna ga cikina take ko naji cikin ya wani dan harbawa don tun ranan da mukai tafiyan nan mai nisa naji ya fara dan min motsi kadan kadan. Ina fita mukai kicibis da Zulfa tace ashe kun dawo nace eh anty ya baby traana lafiya tace dani sai dai Rahama gaskiya ki mayar da hankalin ki akan abinda ke shirin faruwa a gidan nan bawai nai magana bane don wani abu a, a ni kawai dai nasan kowa kan shi ya sani. Nace naa gode sai na dawo tace a dawo lafiya na samu yara na jirana a waje nan muka samu Jinior da Nasir sukace zasu bimu nace dasu mu tafi. Duk da nasan fita dasu zai kawoo matsala gidan su daddy muka fara kai gaisuwa naji dadin yadda Hajiyan dadi ta karbe ni tana kuma yi min nasiha akan hakkuri da jama,a tace duk abindda zanji nayi hakkuri naci gaba da biyayyana don mai hakkuri yana dafa dutse yaci. Shima Alhajin shi yai min nasiha akan rayuwa mai kama da wa,azi kan zaman takewa naji dadin fadan su a gare ni sai gidan mama laraba don ba nisa da gidan su daddy din. Abban anty nakai mai shadda da turare da zuma ya nuna jin dadin shi da ganin mu sosaii yai min fatan alheri da saka min albarka tare da kara rokona nai hakuri da yar shi. Har gidan Aisha da Fatima muka shiga daga can muka wuce zuwa gidan Zarah can muka bata lokacin mu gurin hira tare muka fito zuwa gidan Anty Amina da hajiyan harka na sada zumunta. Mun shigo gida tun a get maigadi kewa Nasir kabi hajiya uwarka bata sani ba har anyi tashin hankali tsakanin ta da Alhaji a gidan nan. Nace ai a gaban Amira muka tafi don haka ansan fitan mu dasu muna shiga gidan ba a dade ba sai na ji ihun yaran yana tashi sai dai ina ganin jinior ne ta samu gamin shi. Ban shiga bada hakkuri ba sai fatan Allah ya sauwaka nayi na shareta ina jiran tazo tai min magana kan fitan da nayi dasu din amma sai naji shiru kwanan mu shidda ran na bakwai tunda safe muka bar garin. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , , 72 A wahale muka isa don gaba daya na ragwabe a motar da kyat naga an kai don tun ina jurewa har yakai bana iya jurewa sai dai daddy yana ganin kamar gajiye ne kawai ke damuna. Tun shiga na daki ban fito ba na watsa ruwa a jikina na kwanta ranan ko wurin daddy ban samu zuwa ba a dakina na kwana. Washegari har ya fita na kasa tashi sai bayan fitan shi ne kawata tazo gidan tai treatment din na har na danji sauki. Ban samu kaina ba sai yamma jikin ya dan sake min na fito falo wurin mutane sai dai duk da haka a kwance nake. Dadi ya dawo daga office mukai mai sannu da zuwa sai su Aisha suka mike ina kokarin mikewa zaune ne naji yace dani wai ke duk gajiyan hanya ne haka ko kuma kewan antyn ki ne ke damun ki ? Murmushi nayi nace ai anty na wanan karon ba mu kwasa da dadi ba da ita don ta fada min magana na fada mata sai daga baya abin ke min ciwo da na biye mata har muka kai ga haka da ita. Yace abinda kuke son kai gayi ke nan ni na kasa fahintar may nene matsalan ku ga wanan halin da kuka tsiro yi. Shiru nayi har ya gama fadan shi ya bar falin inda ni dai banga laifina ba don duk yadda ake ai nayi wa anty halarci. Satin mu daya da dawo daddy ya shirya yabar kasan zuwa Spain don wani businesses da suke hassashen yi na karafuna a can. Tun da daddy ya tafi na samu sakewa a gidan don dama a takure nake dashi don ina jin kunyan yadda zai gane cewa akwai ciki a jikina tun kan na yaye goyona. Tun tafiyan daddy ba mai jin motsin kowa tsakanina da su anty nace a raina watan sai idan yana gatin me dama matsala yake yanzu da bai kasan shiru babu ruwan wani da wani. Sannu a hankali nake bussines dina inda nake saro kayan da zasu shiga na tura dasu kano wurin Zarah da mai kayan harka da yake mata na shiga wurin ta nan danan zakaji tace min a karo wasu sun shige ta turo min da kudina. Rana wirin yawon shige shigen, Hindatu sai gata gidan mai kayan harka wata kawar ta takaita wurin ta bayan sun dada ta wurin iya hada mace. Ta shiga Mai gyaran harka tagane ta amma ita ba san ta sanni ba na ta sake tana fada mata komai akaina tace. Wallahi wata hatsabibiyar kishiya muka samu gata yarinyar karama kuma yar kauye ce amma shigowan ta gidan gaba daya ta kwace muna miji. So nake yadda ake yabaki din nan ki hadani don Allah yadda mai gidan zai rikice akaina ya bar wacan gajar yarinyar yaji ba kowa a gaban shi sai ni cikin mu hudu. Wallahi ni ban ki ace duk sufice su barni da gani sai shi ba a rayuwan mu na tsani kishiya a rayuwa na gashi kuma Allah ya bani su har mu hudu ne kuma ina son mijina don ban iya rabuwa dashi. Sai da maigyaran harka ta gama saurarenta tace ai ba haka yakamata kice ba kedai kawai abaki abinda idan kuna tare yaji ba wata bayan ke. Tace haka nake so ashe dai ke yar hannu ce sosai kinga daga haka ai zan samu kanshi ya tunkudo waccan shigiyar data koma Abuja da zama ta dawo gida ni in dane. Yarinya kamar hatsabibiya ba duk abinda nayi mata tankar taki nake zubawa akan ta shigiya ko gezau sai naga kamar aiki zaici amma kwana biyu sai abu ya koma fiye da farko. Tace da ita su bata kwana biyu su dawo idan ta gama mata hadi duk da kudin da ta tsala masu amma haka hindatu ta lale ta biyata kudin ta kai tsaye. Suna fita wayana dake gefe na yai kara na daga da kyat don a kwance nake tun safe da yake yau ban fita aikin sai da dare. Ina dauka muka gaisa tace Rahama kin san may nace a, a tace wallahi yanzu wanan kishiyar taki tazo guna yau. Nan dai take fada min yadda sukayi da irin zagin da ta dinga min sai dariya nake nace kai Allah na gode ma wallahi Allah ka kara rufa min asiri dama nan suna yawan jifana duk kan su Allah ne dai ke kareni wallahi don ba imani ne dasu ba akan mijin su. Tace ni dai yanzu na bata kwana biyu ta dawo idan kuma ta dawo zan mayar mata da kudin ta ne don ba zan iya mata komai ba. Nace a, a hajiya kadai ki haka don Allah kefa akasuwa kike don haka na rokeki da duk abinda kika san na amfanine tsakanin miji da mata ki bata ni a gareni babu komai wallahi ai zaman lafiya zai sa a tsakanin su Allah kuma yasa ta gane gaskiya. Waiko kina da hankali kuwa Rahama kishiya har kike fadin nabawa abin amfani taji dadi da miji ko may ? Nace yo hajiya sai may jikinta daban nawa daban ai bashine zaisa tafini ba kema ai zakiji tsoron Allah ya tambaye ki akan yi mata kissa da kikayi idan baki bata mai kyau ba. Tace kai lalai ma Rahama halinki daban ne wallahi da zasu gane natabbatar ba karamin zaman lafiya zakuyi dasu ba amma kishi ya rufe masu idanuwan su. Mun dan kai wani lokaci da ita muna hira daga karshe mukai sallama da ita tabarni ina tunanen irin hakin na kushiyoyina naga maganan maigyaran harka gaskiya ne datace na kar mikewa na nemi tsarin jikina da na yarona. Haka na wuni da zancen lafazin hindatu akaina nasan Allah ne ke tsare ni bawai iyawa na ko wani abin ba da na keyi. Sai dare na shirya nai masu sallama nafice zuwa asibiti inda zanyi night duty dina tun shigana na shiga na shiga aiyukana na manta da zancen wata hindatu can a raina don aiki da yai muna yawa a gany don matsalan mata da yai yawa yanzu. Sosai nake kula da kaina ban wasa da duk abinda zai kawo min kuzari ajikina na masu ciki tunda na sani ba sai wani ya fada min ba. Ranan na shiga wurin aikin mu nan nasamu sauran likitoci mata yan uwa na suna hiran aka rayuwan duniya kowa tana fadin nata matsalolin. Ina sauraren su banyi magana ba sai da sukaji ni bance kala ba sai wata hadiza ke cewa dani ke kan doctor Rahama kin huta ke kadai ce a gun mijin ki kin huta da matsalan rayuwa. Murmushi kawai nai mata nace a ganin ki ke nan doctor hadiza ni jinku kawai nake don nafi ku matsala idan da zakuji sai kice ashe ke naki dan mali ne. Tace kajiki da wani zance matar dake zaune daga ita sai mijinta ke har may kika sani akan halin wani zaman takewa haka ? Nace doctor hadiza nice ta hudu a gun mijin mu ba yadda kike tunane bane din a lokaci daya suke hada baki wurin cewa what nace hakane namike ina tattara takatdin dana gama dubawa na wata mace da aka kawo a cikin dare ciki ne idan ta samu sai yaki zama a jikin ta har sai yafita asamu lafiya. Nafice duk suka bini da kallon mamaki dayar tace kai ina ban yarda ba wallahi ta dai fadi ne kawai don muce itama din ai tana da nata matsalan. Amma mai kishiyoyi ne zata zauna haka ko yaushe hankali a kwance bata cikin wani damuwa ko kadan. Basu yarda ba nima ban kara masu bayani komai ba muka bar zancen a haka a tsakanin mu bandai masu bayani ba. Sai kuma kamar sati uku na shigo na samu abokiyar aikina tana waya cikin tashin hankali sai na fahinci da mahaifiyar ta take wayan. Tana fada mata rikicin da suke da mijin ta da kushiyar ta har takai gayin kuka nasan uwar tace ta nemi tsarin jikin ta ne sai naji tace mama nida ke nan a ina zan samu wanan ? Sai dai ke ki sama min don Allah dai mama daga ni har yaran da zaran Nafisa ta shigo garin nan bamu da sauran kwamciyan hankali har sai ta bar garin nan zamu zauna lafiya dashi. Har ta karasa wayan bata daina kukan da takeyi ba nai ajiyan zuciya nace da ita kiyi hakkuri hakana don Allah. Shi alamarin namiji sai idan kana sakawa a ranka ne zai damay ka tunda har kin san inda matsalar take maku da zaran matar shi ta shigo gari ki rungumi yaran ki kifita zancen su har lokacin da ta tafi ya dawo maku. Idan yaga kina damuwa da alamarin maimakon kiga sauki sai dai kiga ma yana kara tula maki haushe ga hakan yadda ranki zai kara baci ga banza. Mafita dai daya ke nan mama ta fada maki shine kidai tsare jikin ki dana yaran ki don kariya daga duk wani manufa nata akanki. Don idan kin fahinta sai kiga bayin kan shi bane hakan shuumanci ne irin namu na mata take kara ingiza shi akai don ranki ya dinga baci kawai idan tazo garin. Tace doctor Rahama don baki da kishiya ce yasa kike fadin haka wallahi a yanzu nayi dana sanin auren Abdul a rayuwa na. Haba dai don Allah kice astangafurullah mutun da kuka haihu har biyu dashi zaki tsaya fadin haka kuma akan shi. Tace doctor kishiya fa ba abin yarda bace walkahi nasani nace mata don ma sai nace ni nafiki sani don ni nan da kike ganina kishiya tai sanadiyar aure da mijin mu na zama ta hudu amma kuma yanzu nice babban makiyiyyarta a duniya don halin kishi kawai. Da sauri ta dago kai tana kallona a cikin mamaki nace kwarai kuwa nan nafara bata labarina har zuwa wanda hajiyan harka ta jiyo min din ga hindatu. Nisawa tayi bayan tagama saurare na tace amma kan matsalar ki yafi nawa gaskiya ni ina zan iya zama cikin mata uku na zama ta hudu ai sai su caza min kaina dayan ma yaya na gama da ita balle har na zama ta hudu. Nan dai muka yanke shawara tare zamu tura wa mahaifiyanta kudi ta taimaka muna yadda tace daga kasan bargu na kayanji. ********* ********* ********* Ranan dai nace bari na kira anty mu gaisa don kwana biyu ban kira ba bata kirani ba kuma dama dai nice mai kira din ba ita ba. Ga mamakina sai bata dade ba ta dauki wayan na fara gaida ita tare da tambayanta lafiyan yaranta. Mun dauki lokaci muna dan hira wanda duk akan yaran ta ne mukayi shi normal ba wani matsala a ranan haka yasa bayan mun gama wayan naiwa Allah godiya kan hakan. Tun wanan lokacin nakan dan kira wayan ta mu gaisa tunda ta rage yawan daure min da takeyi a baya gashi har zata tambayi lafiyan baba wani lokacin abinda a baya batayi. Abinda ban sani ba yanzu ta fahinci zama dani ba karamin rana ne gareta ba don barina yasa ta fahinci cewa ni ba kishi nake da ita ba sai taimako amma ta biyewa son zuciya tana musguna min haka. Gashi tsakanin su duk da miji baigida kullun da irin matsalan da zai bullo a tsakanin su sai iyayye sunzo sun shiga ga maganan. Don raini dama sun riga da sun raina tako tun baya wanda ba komai yaja mata haka ba sai son kai da suka fahinci tun farko tana dashi ashe ? Ga gori dan abu kadan zasu rufe idon su suyi mata gori akaina kuma su zageta fes shikuma mijin dake goya mata baya yanzu yafita zancen ta . Shiyasa taga ta shirya da Rahama kila zai kawo mata saukin zaman doya da manjan da ke tsakanin su tunda dama shine matsalan nasu. Haka yasa take kokatin ganin ta taushi zuciyar ta akan kishina da take ji a zuciyar ta ko za,ta samu sauki a rayunta. Ban dai yarda na sake sosai da ita ba kamar baya don bana fada mata komai na sirin daya shafe ni yadda muke da ita a baya can. Koda yaran ne suka bulstiye mata zata kirani ta fada min nai masu magana kuma suji tundai ma Amira dake yawan dauko mata magana a gidan yanzu. Nakan wa yarinyar magans maikama da Nasiha a cikin hikima kuma ta fahinci magana na ta bar abinda takeyi din. Cikin jikina ya girma yanzu sosai don har ya fito watan shi bakwai da kwanaki haka nake ta fama dashi ni kadai nake kunshe da abina ba wanda ya san da shi bani ma fatan wani yazo daga fannin daddy har ya fahici hakan. Shima muna waya dashi amma ban taba sanar dashi komai ba akancikin don haka baisan dashi ba tare dani sai dai nasan ranan da zai gani da akwai rikici kan gaskiya ban damu ba an dai riga da anyi din ko. Ya bugo waya zai dawo cikin wani sati don watan shi uku acan da kwanaki kenan baya kasan sai da yaga komai da suke so ya kammalu masu shine zai dawo gida. Naso bashi sakon kayan baby amma kuma may zance dashi ga hakan sai kawai nashiru sai yazo ya ganewa idon shi zai san yadda yayi ai da hakan. Anty da kanta ke kokarin sanar dashi shiryawan mu da ni da ita sai dai idan tai magana a waya yayi murmushi don yasan tuban mata na mazuru ne dan abu kadan zai sa ta koma wa halinta tunda ya fahinci abin a jini yake muna. Sai dai ya fahinci tunda muke ni baitaba jin nai mai wani korafi mara dadi akan kowacen su ba bani kuma sukan su gaban shi koda kuwa sun bata min rai na. ********* ********* ********* Da yamma ya dawo ya iso gida da biyar da wani abu lokacin ina daki ina kara shirya duk da dogon riga ne a jikina light blue na daura dan kwalin shi a kaina sai cikin daya turo a jikin rigan yai tsiri dashi. Nafito da fara, a na don na manta da baisan da zancen cikin ba ni da murna na samu yaran gidan suna taron shi nace daga kofan da nake fitowa din da daddy oyoyo. Ido ya zuba min bai iya karba oyoyon danai mashi ba a lokacin sai idon da ya zuba min har na karso inda yake tsaye sagale da corth din rigan shi a kafadan shi. Da hannu ya daga yace dani dakata Rahama da sauri naja wuri daya na tsaya kamar yadda yace min din. Kallona yake cikin mamaki idon shi akan cikin nawa, yace Rahama ciki ne dake komay nake gani haka ajukin ki ne wai ? Murmushi nayi nace kai wallahi har naji tsoro na dauka wani abune wallahi, ina karsowa inda yake a tsaye sai su Aisha suka fara sulalewa falon. Ya kara kallo na yace yaushe har kikai ciki a gidan nan har ya girma haka ban sani ba Rahama ? Nace daddy wani ciki kuma kai mutum bai kiba sai kace ciki kuma humm naji yace kawai tare da kara bina da kallon mamaki ? Boye min kuma kikeyi ko may Rahama da har ciki zai zauna a jikin ki yakai haka ni uban cikin ban sani ba saboda may zaki boye min wanan irin maganan da ba karami ba haka. Na rugumay shi ina sauke ajiyan zuciyan ganin shi ya dan dafa bayana tare da kai hannun shi ga cikin take kuwa dan cikin yai wani bul bul daga cikin riga. Yace tabbas kuwa cikine dake Rahama, don gashi naji motsin shi yanzu ai. Na sake shi ina fadin daddy sannu da hanya yaya aiki yaya jama, a kuma da sanyi ? Yana dai tsaye yana kallona daga inda yake bai motsa ba yace abin ya daure min kai wallahi yadda har mace zatai ciki yai girma haka ace wai ban sani ba don may zakiyi min hakane wai ? Zama nayi don banda jimirin tsayuwa mai yawa yanzu da kyat na kai zaune ya kara kallona a cikin mamaki. Ganin baida niyar zama nace ka zauna mana daddy ka huta tukun kafin muyi wani magana dakai ko. Yace dani barni a nan tunda banda wani amfani a gunki har zaki iya boye min alherin da ubangiji yai min haka banyi mai godiya ba. Nace afuwa yallabai tuba nake nayi kuskure amma may zan fada ma tunda lokacin da zaka gani yayi ko . Kallon mamaki ya sake min daga haka bai sake magana ba sai ya fara tafiya zuwa part din shi ran shi a bace mai. Bin bayan shi nayi da kallo daga gurin da nake zaune na sauke ajiyan zuciya bayan naga shigewan shi ciki. Ban iya tashi ba don tashi wuya yake min sai da na dauki lokaci mai tsawo na mike nabi bayan shi zuwa dakin. Na samu har ya fito daga wanka ya saka dogon riga mai laushi a jukin shi ko jin nashigo bai sa shi ya juyo inda nake tsaye ba. Daga inda nake tsaye nake cewa dashi abinci na falo yana jiran ka ya dan juyo tare da zuba min idanuwan shi a kan cikina. Yace ba yanzu zanci ba sai nayi sallah zan zauna naci abincin nace daddy ko ruwa baka sha ba fa tunda ka dawo yace No ki barshi a koshe nake ai. Sai banji dadin yadda ya daure din ba na juya don barin dakin cikin jan kafa na da kyat don bani da wani lakkan kwarai yanzu. Muryan daddy naji yace Rahama may ye dalilin ki na boye min cikin dake a jikin ki, kika ki fada min kina da ciki tsawon lokaci haka ? May kuma kike nufi da hakan da kikai min kika hana na godewa ubangijina da ya azurta ni da samun karuwa a gidana ? Shiru nayi ba amsa ya dago yana kallo na ido da ido da sauri na dukar da kaina a kasa cikin jin nauyin shi na rasa may zance dashi din. Ya sake cewa ba dake nake bane baki jini bane ki may tambayan ki nayi akan wani dalili kikai min hakan ? A sanyaye nace daddy ni bana nufin komai ga yin hakan da nayi a gare ka na dau yi shiru ne don ban san yadda zan fada ma ba a lokacin ganin ina shayar da yaro dan wata goma bai isa yaye ba. Amma ni bayan wanan bani da wani manufa akan hakan kuma nayi haka ne don gujewa maganganun mutane akan hakan. Nace amma don Allah kayi hakkuri tunda ranka ya baci ga yin hakan da nayi din ba da wani manufa naki fadawa kowa ba ni. Yace ashe baki da hankali ban sani ba Rahama cikine zaki boye har yakai tsawon wanan lokacin kina nukurkusa dashi a jikin ki batare da wani naki ya sani ba ? Ko kuma kin dauke ni ban san abinda nakeyi bane saboda wani hujja can naki na banza mara dalili, Ko waye baisan hikimar ubangiji ba idan ya tashi yin ikon shi akan mutum zaki dauki ciki har yakai wanan matsayin kina fama dashi a tare dake kin yi gum idan kika cutu ga hakan da kikayi laifin wa kike tsanmanin za, a gani ga yin hakan. Shiru nayi mai har ya gama fadan shi nace don Allah daddu kayi hakkuri nasan nayi kuskure babba nima. Bai min magana ba sai saka kai yayi ya fita daga dakin kawai na dade a wurin da nake a tsaye a cikin damuwa daga baya nabi bayan shi na fito daga dakin nima. A falo na samay shi zaune yana waya na samu wuri na zauna sai faman wayan shi yake ya nuna baima san ina wurin ba sai baba ne da yazo yana dan jana da hira nake bashi amsa kawai cikin gwalancin shi na yara. Sai da akai kiran sallah na mike na shiga dakina nai sallah ban fito ba don a gida yai sallah shima na idar da isha,i da shafa,i da wuturi na kara dan gyara jikina na fito falon na zauna. Tun kan na kai zaune yace dani mikon min abinci nan naci a nan na mike zuwa wurin da abincin yake a table na dauko zuwa inda yake na jera su a gaban shi. Sai da nagama har ya fara ci na samu wuri a gefen shi na zauna ban dai yi magana ba har lokacin don nasan nayi laifi babba. Cin abincin shi yake hankali a kwance da gani abincin yai mai dadinci don ya dade yane kewan abincin gida irin haka. Nan dai na zauna ina amfani da waya na ban bi ta kan shi ba sai can batare da ya kalle ni ba yace dani wata nawa ne cikin naki yanzu yake ? Shiru nayi tare da dakatar da abinda nakeyi da wayan na dago kai ina kallon shi sai kuma nai saurin dukar da kan nawa a sanyaye nace dashi takwas da kwana ki ke nan yanzu. Amma gaskiya rashin hankalin ki yai yawa wallahi ashe da sai dai kawai naji haihuwan ki idan na dawo ke nan da ban dawo ba a yanzu ? Shiru nayi shima ci gaba yayi da cin abinci shi har ya gama ya jawo roban da na aje mai ruwan wanke hannuwan shi yafara wanke wa sai naji ya ce dani. Amma ki sani wallahi, idan kin sake maimata min irin haka bazaki ji dadin matakin da zan dauka akan ki ba nan gaba. Saboda wani hujjan ki can na bazan mara gamsuwa zakiyi kokarin cutawa kanki dana tare dake irin haka ? Abinda yasa kuwa zan bar wanan maganan a yanzu don kawai yanzu na dawo kasan bazan yarda na shiga yan uwa na da bacin rai ba haka. Na rasa ke wani irin tunane ne akan ki duk wanda zaiyi magana yaje yayi mana abin kunya ne halan gare ki da da uban shi ki cuta muna haka ? Na sake cewa don Allah daddy kayi hakkuri nayi kuskure na sani nima ka yafe min don Allah yace naji amma gaskiya banji dadin hakan ba wallahi. Nasan banda gaskiya don haka na lafe ban kara yin wani magana ba nai shiru har ya gama na kwashe kayan abincin zuwa kitchen. Ko da ya shiga sai da na dauki loiaci na samay shi har ya kwanta a lokacin ko nima kwanciya nayi sai naji ya dan sauke ajiyan zuciya tare da juyowa yana fuskantar inda nake kwance yace. Ni ban ma san ta ina zan fara gwada babyn nawa ba wanan girman da cikin nan yayi haka duk da nasan ba laifina bane ga hakan. Yana kewar matan shi dole ya manta da bacin rai da ya tarar a gidan ya biya bukatan shi sai dai ba yadda yaso yi din ba. Washegari gaba daya jikina ya dipge min hakana na daure na fito na shirya mai abin karya tare da namu gaba daya da taimakon Aisha na samu na gama komai na jera mai bai dade ba yafito daga dakin ya ci ya fice daga gidan. Bayan fitan shi wanka nayi na samu wuri na kwanta sai barcin wahala ya kwashe ni ban falkaba sai gab da sallah azahar na tashi inda na samu har Aisha ta hada abincin rana . Naji dadin hakan don ta taimaka min kwarai da gaske saboda koda idona biyu ma bazan iya komai ba yadda nake jin jikina din. Bai dawo gida ba sai bayan karfe biyar na yamma nan ya zauna yaci abincin kafin ya tashi sai ga yaron shi sani nan garin ya na shigowa da kayayyakin abinci nau,i, nau,i. Komai na amfanin gida sai da ya sayo muna yakuma ce na duba idan da akwai wani abinda nake so wanda ba a sayo ba din a ciki don kada na tashi nace komai an sayo. A dan kwana biyun da daddy ya dawo ya fahinci bana cin komai sai kunu na koko da nakan zauna nasha sai na koshi, . Duk lokacin daya shigo zai ganni da cup a hannu yace may ye wanan sai nace dashi koko ne nake sha ranan dai yace dani wai Rahama ban gane wanan yawan shan kunun da kike ko yaushe ba ko so kike kijawa kan ki wani matsala ne kuma? May na rasa a gidan nan da zaki zauna dare da rana baki da aiki sai shan koko akai akai haka sale salin kija min zagi ko ki haifi da da rama ace ba, a baki kulawa ko may ? Na dago kai daga inda nake zaune ina fitar da zufa na dan kalle shi a hankali nace daddy ba wai don wani abu nake yawan shan koko ba kawai shine zan sha na zauna lafiya. Yace to na fada maki bana so ki dinga hada tea ko dan abinci mara nauyi mana kina ci bana son yawan shan kokon nan ni. Don ba zan yarda ki cutar min da abinda ke acikin ki ba in ke baki damu da kan ki bane haka ? Mamaki ne ya kamani kaman wanda bai san lalurar ciki ba ko may yanzu ne ma nake dan iya shan kunun a baya sai ruwan bakin liptop nake sha kawai ai. Yagama fadan shi ya shige daki banyi magana ba may ma zance ina a wanan stage din har zai tsaya min fada irin haka. Tun wanan lokacin idan zan sha sai dai na shige can dakina nasha na fito waje kamar ban sha komai ba. Sai da yai sati uku ya shirya zuwa kano inda kafin nan ya sha korafi sosai a gun matan shi inda kafin nan yasha korafi sunyi fada sosai har a waya sai suke ganin ya makale ne a guri na kawai muna jin dadin mu a Abuja. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 74 Subbahanallahi kowa da abinda yake fadi akan wanan matsalan wasu suga laifina wasu kuma gaba dayan mu suke zagi wasu kuma ita hindatun ce suke zagi. Alokaci daya abin duniya ya taru yai min yawa akai ni kadai duk da ba a gari daya muke ba haka bai sa na tsira ba daga zargin mutanen duniya. Tun faruwan wanan abin gaba daya ya sauya ya koma wani zaki mafadaci da kowa a gidan shi haka yasa kowa ya shiga hankalin shi dashi. Ni da a kullun nake kusa dashi abin ya shafe ni don ya dauki zafi da kowa bai magana na tsawon lokaci da kowa sai idan shi yaga daman yin hakan zai dan zauna dasu mama a falo su danyi hira kafin ya fita. Waya ko ko yaushe hindatu cikin bugowa take tun ban fahinci ita bace har nazo na gane cewa itace take yawan bugo mai wayan ako wani lokaci. Na dai san baifi ban hakkuri takeyi ba haka muke mata sai mun bata da gangan sai mu dawo daga baya kuma muna bin muna ban hakkuri da dodofa a dawo damu yanzu wanan abin ina ranan shi ? Lokacin da take cin mutunci ta manta cewa ba a hannunta auren yake ba kuma iya hakkuri dai daddy yana dashi akan iyalin shi don ba duk maza bane zasu iya hakkurin da yake kullun ya dawo gida daga wurin neman hakkin shi da irin fitinan da zai samu na jiran shi a cikin iyalin shi. Don ma yana namijin duniya ne ya san yadda zaibi da ko wace mace a zauna lafiya da ita. Yau ba fita kasancewa weekend ne yana gida yana barci har goma da wani abu na safe nima barci na nayi sosai na tashi nai wanka na shirya nafito ganin rana ya soma yi bai karya ba. Sai na fita zuwa dakin shi na samay shi har lokacin kwance yana barci kada na damay shi yasa na juya zan bar dakin. Rahama naji yace nace naam daddy na juyo zuwa inda yake a kwance tsakiyan gado, na karaso gap dashi nace dashi antashi lafiya yace Alhamdullahi yaya ku ka kwana nace lafiya kalau, yace kin shigo kuma zaki fita mana ? Nace eh daddy dama naga rana yayi ne shine nazo na duba naga baka karya ba har yanzu sai kuma na samu kana barci shine zan fita. Yace yanzu nake son na tashi dama nai wanka aina dan huta yau don dama ina da gajiya nace haka na gani shiyasa zan fita na barka ka huta din. Yace ai kin barni na huta din don ba a damay ni ba yace barin yi wanka na fito na ce bari hada ma ruwan wankan kafin ka tashi. Yace barshi kawai a yadda kike din nan ai gwara ki huta barshi kawai zan hada idan na shiga ai. Nai murmushi nace ai zan iya hada ruwa ba wani aiki bane ai yace gashi kinyi kyau yau kamar ba mai tsohon ciki ba dake. Na dan mai kallon mai wata irin tsiga nace daddy yau kuma zolaya ce abin yadda na koma wata bushuma dani haka kamar wata uwar mata komai ya bude min haka dani ? Yace yana dagowa kece ke ganin haka ni dai ban gani ba nace gadai masu kamar kwarai can a kano suda basuyi nauyi ba ka barsu. Ya mike zaune yana cewa ai ba sai kin gwada min su ba keda ke gabana yanzu nake magana ba wa yanda basu kusa dani ba. Cikin ya hanaki daukan dawainiyan kato kama nane ko may da zakice wai duk kin koma wata kala dake to ni dai ban gani ba ke kika fada yanzu don ni wata yar shar nake gani a gabana cikin bai sa kin jagule ba tunda bai hanaki yi min kwaliya in gani ba. Nace cikin jin kunya kai haba dai daddy ina kwalliya a nan haka kamar wata bosa dani. Dariya yai min ya mike tsaye yace barin shiga wankan ko su mama bamu gaisa ba yau dasu don ban fita ba. Sai ya kamoni zuwa jikin shi yace ko za a taimaka min ne na dan yamutsa wanan kwalliyan da akai min ? Da sauri na dago kai na na kalle shi nace don Allah daddy rufa min asiri yadda nake din nan ina zan iya daukan double share jiya da yau haka. Yace kai wanan dai akwai ragguwa wallahi ko ba cikin ma ai haka zakice dani niko gani da bukata ga mace nace ai Allah yabaka su yadda zaka shanye kwadan ka. Murmushi yayi yace baki ganewa ne ke don haka abar zancen tunda ba a bari na kara more weekend dina. Ya shige bandaki ni kuma na juya na fice daga dakin kafin yafito a falo na samu su mama zaune na gaida su nan mama ke cewa nace yau ko asubanci dan nan yayi ya fita ne bamu gaisa ba da shi. Nace ya na nan mama bai fita yanzu naje na tadashi ya karya rana yayi bai karya ba yau weekend ne bai zuwa aiki sai in ya kama yakan fita irin ranan yau din. Tace bari ai maza na kokari wallahi mutum ba hutu ko yaushe kamar agogo wurin neman na kai ace kuma wanda ke gida a zaune shine mai fitina haka. Nasan inda maganan ta ya dosa sai nai saurin kawar da zancen don ban son aci gaba da yin shi ba dadi magana daya kullun. Nace mama kun karya kuwa ko akwai abinda za, a kara makune wanda kuke son ci ayi maku shi yanzu. Tace a, a a haba dai ai Alhamdullahi munci mun sha mun gode wallahi ni zaman nan ma baka aikin komai har ya soma isata wallahi. Ka saba da yi wanan yi wancan a gidan ka nan ko kana zaune wuri daya ba baki ba fari sai kallo tv da cin abinci kawai shine aikin mutum. Nai murmushi nakai zaune ina fadin to mama Allah ya kaiki ga hutu danki ya kawo karfi ai sai a godewa Allah dama haka ko wata uwa ke fatan gani ga zurianta hutu daga tsatonta. Muna ta hira dasu suna bani dariya daddy ya fito yau kanan kaya ya saka a jikin shi ida ya nuna dan tunbin girma daya fara ajewa a jikin shi. Nan ya karaso suka fara gaisawa dasu mama nacce akawo abincin nan ne ko a table zakaci yace batin tafi can naci yacewa Attu tsohuwa yau sai ki shirya muje yawo ko naga baki saba zama wuri daya ba haka. Tace rufa min asiri barni anan wanan gari naku ai sai ku dake cikin sa nikan ai in kaga fitana a gidan nan gida zan koma. Yace a, a kada muyi haka dake mana idan kin koma dan tsohon mijin ki ya tambaye ki labarin abuja may zakice dashi kuma ? Yau kan zan fita daku kuga gari son ita wanan yanzu sai a hankali tayi nauyi da yawa balle ta kaiku wani wuri. Attu dai ra nace babu inda zata nace aiba ke kadai bace ga mama gashi kije kiga gari don Allah ko ki koma mijin ki yaga an wayar dake sai akasa dariya daddy ya mike nufi gurin da abinci yake. Yana tsaka da cin abinci mukaji wayan shi yai kara mu dai inda ya barmu ana hira sai ji mukayi yana fada yace na fada maku kada a fita min da ya ta gidana don rayuka zasu baci idan an fita da ita gidan nan ki bar min yata a gida na. Maganan da yake da karfi a cikin fada yasa muka mayar da hankalin mu gareshi falon yai tsit kamar ba kowa acikin sa. Ya gama wayan ya taso sai mama kecewa Ihisan ce take son tafiya da its ko yace itace mama ina zata min da yarinya wanan gidan nasu da ba kwabo ban yarda ba wallahi aiba da ita tazo ba. Sai Atyu ne tace dashi ayi hakkuri Alhaji abin abin a sannu bacin rai ne yakai ga hakan da anyi hakkuri baki daya da ba akai ga wanan barna ba don Allah kai namijine ayi hakkuri dai ko ita matar naka ka barta dakin ta inda gyara ta zauna yafi sauki. Yace ai Attu bar wanan yarinyar bata san arziki ba ina hakkuri don darajan mahaifinta amma ita duk bata san da hakan ba . Uwarta kuma ta biyewa son zuciyar yar ta bata iya kwaba mata sai yadda take so zasuyi yanzu gata ga yar nata zance ya kare. Wasu uwanyen haka suke dama basu san su kwaba wa yaron abinda yake ba daidai ba balle ita da ta saba zama ita kadai gun mijinta kunga yanzu yarta na auren mai mata dole ne su dinga ganin ana cuta masu su basu ganin nasu laifin ko kadan. Mama laraba ce ke wanan magana ni dai ban yi magana ba don tun ranan da na bashi hakkuri yai cikinada fada kamar zai cinye ni danya ban kara magana ba kan zancen. Ya juyo inda nake nai shiru cikin damuwa yace ina yaran nan suke su duba min store may kuke bukata a sayo maku zan kira sani yazo ya samay ni yanzu. Nace ina ganin nama da kifi za, a sayo don akwai komai yace su dai duba akaro bana son wani abu ya kare ba sayo wani ba. Aisha na kira tazo ta fadi abubuwan da za, a karo muna can naji yana waya da Hamza yace aje a sayo kayan abinci nasan suma zai saya masu ne don akwaishi da kokarin kulawa da abin abincin gidan shi sosai. Tun fitan shi bai dawo ba sai hudu da rabi nafito falo na zauna ba kowa falon ban dade da zama ba. Sai ga mama tafito falon tace ashe kin fito Rahama nace eh mama sannun ku da zama tace bari ke dai takai zaune tana cewa dani. Har yanzu yaron nan baidawo bane ni har ranan da ba aiki ma bai zama a gida ya dan huta ne wai ? Nace cikin murmushi mama ai wani lokaci sai dare yake dawowa shi ko yaushe aikine gareshi kin san dan kasuwa baida hutu ko kadan. Tace bakaji ba suko sauran na ganin kina nan dashi ne kuna holewan ku ashema har gara can in yana can yana dan zama a gida aganshi. Nace mama haka abin yake ai zatone kawai irin na dan Adam amma danan da can duk daya ne tace ai basu ganewa ne. Amma dan banbancin kadan ne kawai mama ni fa duk abinda zace su ta fada duk mai zuwa tazo ai ga wurin nan tunda ba saman kaina mace zata zauna ba tana wurinta ina wurina. Tace da sauri na raba ki yar nan hakan dai yafi nisa da nisa amma matan nan bar su kawai inda kika gan su ba dadi garesu ba don bakiga yadda sukayi ba ranan da zamu zo ko ? Nace mama ni abin yana daure min kai ma wallahi zamane dai na kazo nazo sai a zauna afahinci juna a zauna lafiya bashi ke nan ba. Tace ke kika san wanan ai kinga ita zulfa yanzu tagane mai goya masu bayan ta san gaskiya kin ga ta kama kan ta da wuya aji sunan ta yanzu ga wani matsalan. Muna nan zaune ina gyara hular rigar dake a jikina sai gashi ya shigo gidan da sallaman shi. Nan muka shiga gaidashi ya samu wuri ya zauna yace kun gani sai yanzu ko mama haka nake wallahi banda wani lokacin kaina ko kadan yanzu ma wanan meeting din da mukayi ban san dashi ba sai bayan fitana. Ai maganan da muke yi da Rahama ke nan nace su wa yan can suna can suna ganin kana nan like da ita ne ko wani lokaci kuna tare kamar wani dadi kuke ji anan din. Yace mama sun san komai hali ne dai irin na mata su sani su take ai ina tafiya da ko wacen su sun san abinda ke wakana ai. Nace ga abinci can a table yana jiran ka tun dazun yace kai Rahama bar abincin nan bana jin cin komai yanzu hutu kawai nake so nagaji sosai wallahi. Mikewa yayi zuwa dakin shi mama tace ikon Allah abincin ma mutum bai zama yaci don kan shi wanan neman kudi da wahala yake wallahi. Wanda bai sani ba sai aga ai masu kudi dadin su kawai suke ji ba wani wahala a tare dasu irin haka nace mama ai neman na kai wahala ne dashi. Na kai wani lokaci na mike na samay shi a dakin na dauka zan samay shi a kwance amma sai na samay shi ya saka laptop din shi a gaba yana aiki a ciki. A hankali na karasa inda yake zaune na zauna daga bakin gafon nace a sanyaye daddy na dauka hutun kake ashe aki ka tsiro yi kuma. Ya dago ya dan kalle ni yace ina fa hutu Rahama abinda ya kaini spain ne ya fito shine kikaga mun wuni yau muna aiki kan sa haka. Nace Allah ya taimaka ya bada saa yace amin yace wallahi naso weekend din nan mu dan shiga mu samo kayan haihuwan ki tunda ban samu saye a waje ba yadda na saba. Nace kada ka damu daddy Allah dai ya sauke makani lafiya shine a gaba ai ba za, a rasa wanda za ai amfani dashi ba a wurina don na dan saya ko. Ya dago tare da sauke idon shi a kaina yace amna in ke baki so kin san shi baby hakkina ne na saya mai kaya da kudina ko ? Shiru nayi yace ki shirya ki daure ki ku tafi da Aisha ko wata kawar ki ku dan zabo nayiwa matar Abdulkarim waya da zasu dawo ta sayo muna acan dama ina tunanen kagin su dawo din ko kin haihu ne. Nace ai da, yace kin daiji magana na ke nan ki shirya ku tafi ya jawo briefcase din shi dake gefe kudi masu yawa ya fitar ya aje min a gabana yace idan basu isa ba sai ki fada min na kara maki. Kallon yawan kudi nakeyi ina mamaki may zan saya haka da wanan kudin masu yawa har yana fadin wai idan basu isa ba saina fada mai ya kara. Nace ni daddy may zan saya da wanan kudin bayan kace ka bada sauti a sayo muna a waje kuma ya dago idanuwa shi da wahala yasa sukai ja yacehaba Rahama wai bakiga abinda nakeyi bane na fa riga na fada maki yadda nake so. Shiru nayi can na mika hannu na dauki kudin daya zube min a gefenshi tare da cewa nagode Allah ya saka da alherin sa . Don dai nasan ba wai ya bani wanan kudin masu yawa bane kan sayen kayan haihuwa kawai sai dai alherine zuwa gare ni tsakanina da shi. Koda na koma daki na zauna na kirga sai naga har dubu dari biyar cur din su nace cikin mamaki ikon Allah wanan kyautan na daddy da yawa yake gashi kuma ya hanani yin ko magana a gaban shi. Yadda yace hakan mukayi don Faiza kawata da muka hadu wurin aiki muna shiri da ita, na dauka washegari muka tafi shopping din tare itace ta zabo kaya masu kyau na baby mu ka dawo gida niki niki dasu. A dakina Aisha ta zube kayan don ko ita saida na sayawa duk wanda ke gidan abinda zai amfane shi din. Ban dade da dawowa ba ya shigo ina zaune a kasa na saka kayan a gaba muna kallo sai gashi ya shigo dakin idanuwan shi akan kayan. Yace har an sayo kayan ke nan nace eh daddy yabi kayan da kallo ya sauke idon shi ga wasu set din rigunan yara unicef dake hade wuri daya har guda uku ya dan taba yace kai amma kayan nada kyau wanan kaya haka nasan an biyo ni kudi ko ? Da sauri nace a, a daddy kadai biyoni don ga canji ka nan ko rabi ban kashe ba ma wallahi yace kinyiwa baby na keta ke nan ashe ke nan nida nace ki saya aita saka mata ko shi shine zaki ma mai shi keta Rahama. Daddy duk wanan uban kayanay zanyi dashi haka sunyi yawa wallahi yace yanzu saura naki ke nan aban zaki saya ko a ina ? Nace cikin bata rai daddy ni daka barshi ina da kaya yace hakkin kine fa Rahama don may zaki tauye ni haka ne wai ? Kina son na zamo cikin mazan dake tauye hakkin matan su ne ko iyalin su wanan ne fa kadai abinda zan maku har kuji dadin zama dani cikin ko wani irin hali nake don Allah ki bari. Ni ban iya yiwa mace alhetu ba idan ba ita ta bukata ba don ban saba da yin hakan ba a rayuwana amma ke kuma ba tambaya kike ba idan an maki kuma ki kama korafi. Nafa san may nake a gaba dayan ku kada ki dauka neman kudine kawai a gabana haka. Ayi hakkuri yallabai kasan ni yar tallakawa ne kuma yar kauye yace baki saba da riya ba ke nan ko , ? Nace ba haka nake nufi ba daddy gani nayi dai kamar zan takura ma ne kawai da yin hakka yai dan murmushi ya lakoto kumatuna kadan yace Rahama ina ganin har yanzu baki san waye mijin ki ba ko ? Nace na sani mana daddy na gashi a gaba na kuma ubana mijina na ko ba kaine ba yace to idan kin sani da baki fadi hakan ba yau. Ko bani auren ki ni may kashe maki kudi ne balle yau ni mijin ki ne kuma mai kaunar ki don haka kibar min haka please ? Zuria fa zamu tara ni dake mun ma tara din don may zaki dinga mayar da kanki baya ne wai ? Ke fa Rahama matar manya ce ba matar yara ba shiyasa nake son ki gane shigar ki fitar ki wani kimane da daukaka na a idon jama,a. Nace angama daddy haka nake so dake amma baki bari kinji dadi ba balle na tare dake suma suji dadin ki. Har ya kai kofa ya juyo yace zan shiga kano idan zan dawo akwai yaran da zan dawo maki dasu nan don karatun su daga ciki akwai ihisan don haka ki sani ba sai sunzo ba ki gan su. Nace daddy kana ganin iyayyen su zasu yarda da wanan hukuncin daka yanke kuwa akan diyan su kafa san yadda nake dadu duk da sun san bazan taba cuta masu ba amma abune mai wuya hakan ya kasance ai. Babu ruwan ki ni keda gida na yadda nake so zan tsara abina ba ra, ayin wani zanbi ba. Yaficr ya barni a zaune a gurin a hankali na jingina jikina da gado . Ina tunanen wanan sabon fitina da daddy ke son kuma dauko min ba a gama wani ba zai jawo min wani again. Ranan da daddy ya wuce zuwa kano tunda safe yai muna sallama sai dai kafin ya tafi sai da yajika kowa na gidan da kudi masu yawa. Tun da ya tafi na koma daki ban fito ba ina ciki kumshe barci nake a cikin barcin na fara jin canjin yanayi na falka da wani irin ciwon mara mai rikitarwa. Ban daki na shiga tun a can na fahinci labour yazo min ke na gaba na ya fadi sosai na fito na fara tana dar duk wani abinda zan bukata a tare dani. Naso na gwada haihuwa ni kadai sai dai kuma yaya zanyi ga yan tsofin da aka kawo min don irin haka amma may zance dasu bazan iya ba gaskiya. Zarah na kira ta dauki waya ta fara surutun ta nace ke wallahi yau yau ne fa don abin boye nason fita fili. Tace da magana ke nan nace wallahi tace yanzu yaya za, ayi nace shinr na kiraki ai muji nan dai ta fara min bayanin yadda ya dace nayi. Amma ina bazan iya ba na daga waya na kira Faiza sai ko gata bata bata lokaci ba na sha wuya wanan katon don ba irin haihuwan baba bane da nagani da sauki. Da taimakon Allah Allah ya kawo min sauki na sullubo katon da baki dashi kamar uban shi komai na daddy yaton nadashi a jikin shi shima. Sai sannu Faiza ke min har ta gama gyara mu tace barin fadawa tsofin nan naki kada suga ba ai masu daidai ba nace kyalesu tukun har mu kimtsa. Sai da ta gama komai na kira Aisha da waya nace ta fadawa su mama na haihu ashe tare suke a falo tace kin haihu anty gaba daya suka dauka ta haihu fa ? Wanan wani irin haihuwa ne a sauki haka sai gasu koda suka shigo Faiza na tsaye tana gyara yaron da taiwa wanka ta nade shi a showel. Sai faman mamaki sukeyi nan suka shigo da murnan su suna fafin Alhamdullahi Allah abin godiya Allah ya raya muna. May aka samu mama tana tambaya Faiza tace kin samu maigida mama sai dai bakine ba kamar dana ba cewa baba. Tace gida ya biyo dama gidan su bakake ne koshi wanan farin ai satowa yayi wurin uwar shi amma ai komai na gidan su ne. Waya na dake gefe yai kara na dauka daddy ne ina dauka nai mai sallama yace hayaniyar may kuke haka ne wai nace dashi suna gaisawa da babyn kane da ya kore ka ya fito. Yace what tsaya don Allah wai da gaske kin haihu ne nace ga mama na mikawa mama din waya ta karba tana fadin sai kaji an haihu bayan ka ko ? Yace yanzu shi nake ji tace aikuwa gamu nan da mai kama da kai sak wallahi kamar ma har ya baci wallahi Allah yasa dai yayo halin ka. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 75 Zaune daddy yake a falon shi yayin da ya kira wayan Zulfa na zaune a gefen tana hada mai abinci don ranan a gunta ya sauka. Jin maganan da yake ta fahinci nice na haihu duk da taji wani iri a ranta amma a fili cewa tayi dashi Rahama ce ta haihu ? Yace itace wai lafiya na barta fa sai gashi yanzu na kira tana cewa ta haihu Zulfa tace ikon Allah ai yafi da nan may muka samu ne ? Yace yaro ta haifa, Masha Allahu Allah ya raya muna ta fada tace ashe shiga Abuja ya kama mu ke nan satin nan suna ? Bai bata amsa ba yace barin fadawa su hajiya yanzu nan ya shiga buga waya yana shedawa mutane zancen. Mun gama waya da shi nace Faiza ta kira min layin Anty ta kira bugu daya biyu gana uku ta dauka gaida ita na farayi bayan sallama. A ranta sai tana dauka wani kilibibi ne yasa na kira layin nata don naga daddy ya shigo kano ranan. Nace ya kwana biyu tace Alhamdullahi ya kuke nan ya su mama kuma nace gasu suna gaida ke nace anty kin yi bako fa yau. Tace bako kuma azaton ta dai zancen mijin ta ne nake mata harta fara tanadin amsan da zata bani lokacin. Sai nace da ita na haihu yanzu ga baby yana gaida uwar shi, tace au haihuwa kikayi ne Rama ke nan bayan tafiyan mijin ki kika haihu ko ? Nace yanzun nan na haihu ai bayan shi ma sosai na sauka tace to Allah ta raya nace amin mukai sallama na kashe waya na kit. Murmushi na sauke don nayi arziki an min magana mai dadi a lokacin sai dai bata tambaya ba ko may na haifa din. Na kira Zarah inna ta da duk wani wanda ya dace ya san da haihuwan ta bangare na, Faiza bata dade sosai ba ta koma gidan ta don yamma ya soma a lokacin. Kashe waya na nayi don ina bukatan hutu sosai a lokacin don haka na kashe waya ranan da wuri nai barci na bar su mama da dawainiyar yaron da sauran alamuran gida. Daddy sai bayan ya gama abinda yake ya shiga gun anty yace da ita kin ji Rahama ta haihu baya na ko ? A getsire tace dashi eh ta bugo min waya dazun tana sanar dani Allah ya raya akan sunna yace da ita amin ya fita don ya lura da yadda ta daure fuska tun zuwa shi. Don haka baiba da wani kafan da zata tsiyaye mashi abinda ke kwance a zuciyar ta ba. Ranan barci na nayi hankali kwance don ban falka ba sai da asuba na kara gyara kwanciya na na tusa wani sabon barci sai da mama dake kwance gefe ta gama abinda takeyi ta tayar dani nai wanka misalin shidda da rabi na safe na tashi. Ina fitowa kuma na samu ta hada min tea mai kauri tace na sha kafin na shafa mai ya turiri haka na daure na shanye shi duka. Sai na gyara jikina sai faman zufa nakeyi kwaliya nayi sosai Aisha na shigowa nace ta dan shiga makwabtan mu ta fada masu duk da ba wani hurda nake da su ba amma ya dace nabasu hakkin makwabtakan da ya rataya a kan mu tsakanin mu da su. Aiko zuwa rana sai gasu suna shigowa gidan ganin baby ikon Allah kamar kada yaron ya sha iskan duniya sai gashi ya fara haske. Yadda duk ya dace a kula da maijego hakana mama laraba take kula dani sosai ita kuma Attu tana dawainiya da jariri da kan ta. Naji dadin kasancewan su tare damu sosai don ba karamin kula suke bamu ba dagani har baby din yadda ya dace ayi a aladan hausawa. Duk da ba sabo nayi da mutane ba sosai amma suna shigowa jefi jefi yin barka zaman bariki ke nan wani ko don ya shigo yaga yanayin gidan ka zai shigo tunda daman shiga ya samu gare su gashi kuma na aika masu da haihuwan dama. Saboda haihuwan da nayi yasa daddy yai kwana biyu sai ya juyo Abuja ranan da zai dawo kwatsam ya fadawa anty cewa zai tafi da Nasir da jinior Abuja don akwai makarantan da yai masu register a can tare kuma da ihisan zasu tafi. Take tace dashi bata yarda da hakan ba yace ba yardan ki nake nema ba umurni na bayar a shirya su in da abinda za a shirya masu su tafi. Take ranta ya baci taso saka tsauri sai da taga ba gudu ba ja da bayane ta nemi hajiyan shi da kuka take fada mashi zancen tafiya da yaran da yazo mata dashi. Hajiya tace haba Saade ina shi ya haifi ditan shi kuma ba wai ya dauke su daga gareki bane gaba daya karatu ingantattace yake nema masu. Wai may yasa kuke hakane please kin fa san inda za, a kaisu ba wai wuri bane na mugunta ina kin san halin Rahama akan yaran ki in banda so da kauna ba wani abu a tsakanin su. Yarinyar da tun bata mallaki hankalinta ba take a hannun ki don yanzu kishi ya hada ku tare idon ki zai rufe har ki manta da irin amanan da ke tsakanin ki da yarinyar nan. Yanzu ne baki kaunar hurdan ki da wanan yarinyar ko may ? Ko har kin manta da irin mutinci da yardan dake tsakanin ki da wanan yarinyar a baya yanzu zaki rufe ido ki nuna baki san halin wanan yarinyar ba ? Ko har kin manta saboda kishi yardane fa yasa har kika amince kika zabo ta da tazo ta rike maki zurian ki koda bayan ki kika aminta da ta zauna da mijin ki don yarda da tarbiya da kika bata da hannun ki ? Wanda har muke ganin a lokacin hakan bai dace ba sai bayan shigowan ta muka gane cewa bakiwa kan ku zaben tumun dare ba. Sai yanzu ne kuma zaki dawo ki nunawa mutane cewa alharin da kika shuka dama bada zuciya daya kika aikata hakan ba da wata manufa kika aikata hakan gare ku ? Sai kuka yazowa anty tace hajiya da wata manufa kuma fa kikace tace eh man da wata manufa mana in bashi ba may ya rufe maki ido haka har kika manta da makomar ku ga Allah. Yarinya na faman binki kina ta zubar da mutuncin ki da kimar ki ga idon yarinya don ma kin samu yar albarka da tasan ciwon kanta da yar zamani ce da bata san halarci ba may kike zaton zai faru a tsakanin ku. Yaro yau ko kaika haifeshi yaya ka kare dashi balle an baka aman shi riko idan zakiwa kan ki fada kiwa kan ki ki kama mutuncin ki zaifi maki alheri kin ji na fada maki. Anty sai kuka take sharba don nasihan hajiya yai matukar shiganta sosai sai dai har lokacin gani take anci amanan ta. Daddy yana gama shirin shi sallama kawai yai mata ya kwashi yaranta Amira kawai ya bar mata don ta taimakawa uwarta da wani abin. Kuma yasan cewa zuwanta a halin yanzu wani sabon fitina zata kara haddasawa a tsakani wanda zaita kawo rikici a tsakanin mu ko yaushe. ********* ********* ********* Muna zaune sai ganin su mukayi ya iso da yaran kowa yayi mamakin ganin su sai dai ni da dama ya fadawa cewa yaran zasu dawo nan da karatun su. Su mama sun dauka hutu sukazo sai da suka gansu da jakkunan kayan su ne suka fahinci da akwai magana. Ihisan taki sake jikin ta sai shan toka yarinyar keyi duk wanda yai magana a hasale zata bashi amsa. Ashe ba karamin rikici akayi ba da yaje ya dauko yarinyar a gurin uwar ta sai da mahaifin hindatu yazo yasa baki ya wuto da yarinyar din. Ina dakina kwance daddy ya shigo dakin idanuwan shi a kan mu ya dan rankwafo inda nake yace barka da arziki nace barkan mu daddy kuna lafiya ya baby din yake kuma ? Na juya inda yaron yake kwance a cikin showel nace gashinan kwance gurin yaron ya duka ya dauko shi ya dade dashi yana mashi addua kafin ya aje shi yana fadin Alah ya raya muna Aliyu haidar acikin amincin shi. Na lumshe ido nasan sunan da yaron yaci ke nan in ban manta ba sunan mahaifin anty ke nan ya sakawa yaron ni dai amin nace tare da fatan Allah yasa yaron ya biyo asalin mai sunan na gaskiya sahabi kuma suriki ga mazon rahama. Ya dago bayan ya aje yaron yace dani ga yaran nan sunzo ke nan anan zasu zauna sai hutu zasu dinga zuwa gun uwayen su suna ganin su. Nace Allah ya taya mu riko yace dani amin sai ayi hakkuri duk da kin saba dasu yanzu akwai dan canji ga baya sai an kai zuciya nesa ga wasu abubu na su. Nace ba komai in sha Allahu zaa kiyayye da yardan ubangiji da ai na kowa ne bana mutum guda bane dama. Yace ya gode yafice daga dakin nafito falo don in basu masaukin da zasu zauna saboda akwai baki a gidan. Dakin da suka taba zama nan na sake ba su Nasir sunji dadin hakan sosai don na fahinci suna son dakin tun lokacin da nace dasu shine daidai da samari kofan shigowa su kuma suna ganin sun kai samari din yanzu. Ihisan ce da nace ta zauna da su Aisha ta kawo min gardama wai ba zata zauna da su ba do bata zama da yan aiki. Nace to kiyi hakkuri ku zauna idan su mama sun koma sai ki kama daki daya daga cikin dakunan bashi ke nan ba duk da nasan tai karama da zama daki ita kadai . Aiko tace ita bata san haka ba sai dai na bata nata dakin ko ta zauna a falo nan mama ta saka baki tai cikin ta da fada har uban ya fito ya samu ana wanan rikicin haka. Yake tambayan may ye mama ta fada mai komai dake faruwa yace idan hakane su su Aisha su koma daki daya da helen sai a gyara mata wancan din da helen ke ciki. Duk da raina ya baci sai ban nuna komai ba ga haka nasa suka gyara mata takoma ciki aka zauna lafiya duk da nasan yaran zasu takura zama da kafira a daki daya. Washe gari da safebayan nai wanka na shirya ina zaune ina cin abinci mama na daga gefe na tana gyaran wani ganye a roba da zata hada muna na kunun kanwa tace dani. Rahama nace naam mama tare da dago kaina tace abinda nake so dake shine kikara hakkuri akan zaman yaran nan a tare dake. Musanman ma wanan yarinyar da kike gani tunda kikaga ta fara tsiyataku irin haka tasha hudubar shedan sosai a kan ki ne. Don haka don Allah Rahama na rokeki da kikai zuciyar ki nisa akan zaman yaran nan dake don wani babban rikici ne ya dauko maki kuma anan. Kin san maza su basu gane haka sai in abu ya faru dasu ne hankalin kan kawo wuta cewa sunyi kuskure wani ma ko ya gane bai gyarawa don suna takama iko a hannun su yake. Nace in sha Allahu mama zan fake don nima na fahinci yarinyar tazo da wani manufa akaina tun zuwan ta na lura da hakan gareta. Tun da aka gyarawa yarinyar daki bata fitowa falo sai idan ta fito cin abinci tana gamawa kuma zata koma daki ta zauna ita kadai. Ban damu ba sai harkokina na suna nake don ban tsaya binta kanta ba tukun nakama shaanina kawai muka barta yadda ta ware kanta gare mu. Monday ya kaisu makaranta nai arziki harda Atika ya hada ya mayar can duk ko da tsadan makarantan amma yai min wanan karar haka. Shiyasa nake son daddy sosai wurin irin wanan halin nashi na karanci ga dan kowa don nima haka yai min a baya. Saura kwana uku suna Zarah da maigyaran harka suka iso Abuja da tarin abin arzikin su washe gari basu zauna ba suka fara shirye shiryen abinda zasuyi na sunan komai da yakamata ace anty ce tai min sai ga abokan arziki sunyi tsaye sun fitar dani kunya da taimakon Faiza kawata komai ya kammala masu don su ba wai sanin garin sukayi ba. Da yamma yan suna daga kano suka iso yan kauyen mu da kuma yan uwan daddy maza da mata gida ya cika da baki tako ina jama, a ne a gidan. Nai mamaki yadda mutane sukazo min haka Suwaibana bata samu zuwa ba don ance tana jinyar mijinta Jatau baida lafiya sosai. Ta ban tausayi yadda ake min labarin suna fama a can gashi basu da mai taimaka masu duk da yake a kwance ya tsuke bakin aljihun shi tam bai sayen ko magani dashi suna matukar wahala sosai. Nace da Rukkaiya shine aka rasa wanda zai bugo waya ya fada min halin da take ciki ga yara ga lalurar miji da wani zataji kuma ? Ranan suna daddy ya baiyanawa jama, a sunan yaro Aliyu sai ranan suna anty Zulfau ta iso tare da wasu yan uwanta su hudu. Ta girgiza kwarai da ganin irin daular duniyan da muke ciki a zaune take mood din ta ya sauya tun kan ma ta shiga gidan. Abokan tafiyan ta na kara zugata wai dankari kune aka bari ashe a can kuna gafin gida ga inda arziki yake nan jibge. An mayar daku wa yanda basu iya cin duniya ba ke nan an kawo wace ta iya ci an ajeta ana itace matar gaban mota an mayar daku tsofi da karfi da yaji. Naji isowar su amma sai banga sun shigo gidan ba nake tambaya akecewa suna waje tukun basu shigo ciki ko. Can sai gasu sun shigo ina saye cikin wani dogon rigan din kin Dubai da gyalen shi iri daya masu ruwan kore da milki a jikin su. Sannu da zuwa nake masu a take yadda suka amsa min a wullakance sai na fahinci da akwai magana a tare dasu. Nan dai aka cika su da abin motsa baki kala kala a gaban su sai faman bin gidan da kallo sukeyi suna mayde baki. Can buki yayi buki a kace ana nema na a waje nafito lokacin na sauya kayan dake jikina zuwa wani hadaden lece maron colour. Nace ance ana magana dani ko wake nema na Zulfa tace dani nice nace gani anty kina son wani abune ko may ? Tace eh k dakin maigidan nake nema dama nace to sai tambayan yai min wani banbarakwai nace sai dai a rofe kofan nashi yake don jama, a. Tace to aban key din nace a, a anty ga dai daki can na gyara maku don zuwan ku shida kan shi ya rufe kofan da zaifita don jama, a da sukai yawa a gidan. Tace ban gane ba may kike nufi nace ba komai sai dai ki bari idan ya dawo sai ya bude maki ki shiga ko ? Tace ikon Allah dakin mijin ma Rahama hanani shiga zakiyi ko may ikon naki da mulkin har ya kai can ban sani ba ashe ? Nai murmushi babu bacin rai nace ban kai can ba amma sai dai kiyi hakkuri don Allah don key yana a hannun shi ya fita dashi. Ta juyo fuuu ta wuce dakin da suka sauka sai bin mu da idanuwa mutane ke yi don anji may muke a wurin. Gun mama taje da fadan ta sai da suka gama sauraren ta mama Rakiya tace da ita haba Zulfa may yakaiki wanan maganan kuma haka a bainar jama, a keda kikazo abin arziki kuma ? Ki bari mana idan mijin naku ya dawo sai ki tafi amma ko nice yanzu ya rufe kofan shi bazan baki key ba tunda baa nan kike zaune ba tare damu. Tace kuma wai su mama sun goya mata baya ai mata cin mutunci nan dai suka taru sukai mata fada ashe komawanta daki takira shi a waya ta kwashi karya da gaskiya ta fada mai. Anci an sha anyi shagali harda walima akayi wa, azi wa mata aka dan raba abinda aka sayowa jama, a a wurin. Yan asibitin mu sun min kara sosai don sunzo wurin sunan harda wanda ma ban zaci zasu zo wurin ba sun zo tayani murna sun kuma koma da abin arziki a hannun su. Sai dare ya dawo gida lokacin yan gari sun rage sai mu da bakin mu yasu yasun mu muka rage a gidan. Muna dakina dasu Zarah mun baje sai hiran sunan mukeyi sai ga ihisan wai nazo daddy yana kirana. Na saka hijjab dina na fita don nasan daddy yana dakin shi a lokacin ban kawo komai a raina ba nai sallama na shiga dakin sai ganin Zulfa nayi a zaune cikin rashi damuwa nace da ita ashe kina nan anty ya gajiya. Sai naji bata amsa min ba na gaidashi da dawowa ya amsa min tare da cewa wai may ke faruwa ne yanzu Zulfa ta samay ni da wani zance koma ince tun ina can ta buga min waya lokacin muna meeting ban jiba sosai. Cikin mamaki na juya gareta ina cewa may akayi kuma ban fahinta ba ni yace dakata Rahama don na kawo ki nan ke kadai bashi zai jawo kiwa matana cin mutunci ba abainan jama, a haka daga tambaya sai ki rufe ido ki dinga gaya mata maganan banza haka a bainar jama, a. Kin fita ne ko a tsaanin ki ke kadai keda gidan ne da wata bata da ikon zuwa tayi yadda ranta ke so a gidan. Yaushe kika fara halin rashin mutunci irin haka ban sani ba kada na karajin qanan halin a gida don bazan lamunta a wullakanta min mata na ba ko kadan kin sani. Idanuwa na rutse a hankali na mayar da hawayen dake son zubo min a lokacin don ba zan yarda kishi taga bacin raina na bukatan ta ya biya. Nace ayi hakkuri duk da ban san abinda nayi ba amma tayi hakkuri don ni tazo garin nan bazan so tace nai mata wani abin bacin rai ba . Ina fadan haka ban tsaya ba na juya na bar dakin raina a bace a daki nake mayarwa Zarah abinda ya faru tace dama shi ya kawo ta taga ta bata maki sha, ani ba komai hakan bai samu ba ta hadaki da miji yaci maki mutunci a gabanta. Nace ba komai ta dauki bashi in dai ban cuce ta ba bata barin garin nan Allah bai tona mata asiri ba ai a gaban shi. Washe gari ban bi ta kansu ba an hada abin karyawa wanda wasu masuyi na kudi nabawa aikin yi har abinci su suka kawo muna ban fito ba sai rana nafito na gaisa da mutane har ita din Zulfa saida na leka dakin da suke na gaida ita da bakin ta. Sai wani kallon banza suke min anty na bata zo ba amma taimin aike na abinda zata bamu wanda kayan baby ne da nawa masu kyau da tsada ta aiko muna dashi tace tunda yaro yaci sunan mahaifinta Aliyu. Sai washe gari yan suna suka shiga kasuwa da gari bayan sun huta sunyo sayayya sosai a kasuwan. Sun dawo suka fara shirin tafiya tun basu tafi ba na fara kewan su a gidan sako sosai na shiryawa iyayyena da yan uwa na da basu samu zuwa ba misanman ma Suwaiba na dake cikin wani hali na ban tausayi. Sun shirya tsab da safe zasu wuce ina kallon yadda Zulfa ke nuna min ita fa matace kuma tana da iko da gidan mijin ta sau yadda taso. Ban kula ba ban damu ba daga ita har mijin daya share ni a gaban bakina duk da banda Zarah da maigyaran harka ba wanda yasan halin da nake ciki a gidan. Zaune muke muna hiran mu a dakina duk da dare yayi har wasu sun fara barci a gidan sai sama sama muka dinga jin hayaniya na tashi. Bamu damu damu saurara ba da farko sai dai da muke jin muryan daddy yana tashi muka kashe kunnuwan mu wurin saurare. Fada ne sosai tsakanin daddy da Zulfa ke tashi yana fadin wallahi idan har baki fito min da kayana ba sai ran ki yai matukar baci. Ko allura na bai taba bacewa ba a gidan nan sai yanzu zan nemi abu in rasa shi nidawa ke dakin bayan nidake ke kwana a ciki. Daga inda hajiyan harka take kishingide ta mike zaune tana cewa lalai Rahama kin cika yar halak wallahi. Fadane fa ake a gidan nan nace matsalar suce hajiya ni ba abinda ya damay ni da sha, anin su su suka sani. Muryan mama Laraba yasa muka kara saurarawa tace bakiji ne Zulfa tun farko dakika zo may muka fada maki ranan da kikaiwa yarinyar nan wullakanci a gaban kowa don tace kawai key baya hannuta yana hannun maigidan. Nan fa faban bakinta kika rufe ido kina mata cin mutunci son ran ki ashe ke da wani manufa kika sa sai a bude maki dakin duk da hanakin da mukayi. Tace mama aiba ni kadai keda key din ba sherine kawai aka kulla min don a bata min suna kawai wallahi amma ni ina ruwana da kayan shi. Yace kina nufin Rahama ce ta shigo ta daukar min abu bayan sun dade a wurin bata dauka ba sai yanzu. Mama tace kai amma Zulfa baki biyo nono ba wallahi sai dai a yabe mu da fada amma ba mugun hali ba dan hannu. Ta juya rai a bace inda mama take tace mama may kike nufi kema satan zaki dafa min ko may ? Yace rashin kunya zaki mata yanzu ko may tace ba rashin kunya sai gaskiya tunda dai dama kowa yasan yanzu mama don anga Rahama na nan sai wani shishige mata akeyi don ana zaton itace mai shi. Ihsan da suke dakin ta ta kumaji plan din su ta fito tace a a anty ba ruwa little mum ga maganan ku naafaji hiran ku ranan da kike basu labarin kinga white gold a dakin daddy masu yawa. Akace ki diba sai yanzun kuma zakice wai ba ke bace tai salati tace yanzu ihisan ni zakiwa sheri abin naki har yakai can ashe ? Nan dai duk gidan yai tsit ana sauraren fitinar su sai dai ba wanda ya fito sai sauraren su da akeyi kawai a sauran dakunan kamar yadda muma muke sauraren su din a inda muke zaune. Duk yadda daddy ya buga taki fito mai da kayan shi su mama sukace ya kyaleta Allah ya tona asirin mai shi bai so ba haka ya yarda yabar zancen rai bace mai. Ni dai a bangare na Allah ya fitar min da hakkin kazafin da taimin ya hau kai ba tare daya bincika ba gashi abinda ya wakana a tsakanin su yanzu. Washe gari tunda safe suka bar garin tare da sauran bakin da suka zo sai gidan ya koma muna tsit iyamu aka bari dasu mama kawai agidan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BZ ONLINE NOVEL NE, , , , 76 Tun tafiyan bakin mu su Aisha suka gyara min gida ko ina ya rage daga ni sai yara dasu mama da zasu zauna har zuwa lokacin da zanyi arbain kafin su wuce. Har wanan lokacin iyakana da daddy ina kwana ko shi daga kofa zan tsaya na gaida dashi na bar dakin wani lokaci ma a falo zamu hade ko ina barci zai fice daga gidan sai in yadawo nai mai sannu da zuwa daga inda nake. Ban bin shi baya balle na daukowa kaina magana ko wani sabon fitina, nayi hakane don na kama kaina akan komai dama sati biyu aka bani a wurin bautar kasa na don haka lokaci kawai nake jira na koma. Banda matsala da yaran da ya kawo min sosai Jinior dai ne da Ihisan keda dan matsala kuma basu wuni a gida in sun fita tun safe acan zasu wuni sai shidda na yamma zasu iso gida. Ina ganin shiru ya dan damay shi ne ko yaya ban sani ba dama can shi dai ba gwanin zama bane ai hira dashi don ko yaushe zaka samay shi busy ne. Na kan yi mamakin yadda yakan samu lokaci a baya yana hira da hindatu ko don yawan nacin ta ne tafi mu nacewa ban sani ba. Case din shi da Zulf sai da iyayye suka sa masu baki daya je gida tafito mai da dutsen shi don yasan cewa ita ta dauke su. Tasha fada sosai a gurin iyayyen su sai datace ba itace ta dauko da hannun ta ba Rafia ce kaunar ta data shiga dakin tana ciki ta dauka aka kuma bincika haka din ne sannan ta samu sasauci a gurin shi. ********* ********* ********* Tun bayan haihuwa na ban faye fitowa falo ba ina dakina ko barci ko wani abin tunda bana sallah a lokacin. Ina kwance a dakina don tun yamma dana dan leka su mama a falo na dawo daki kafin magariba ban sake fitowa ba har tara da wani abu na dare. Yanayin rayuwa ta tun haihuwa na gaba daya ya sake min bana son yawan hayaniya haka kuma bana yawan zama cikin mutane sosai. Dama da yara nafi sakewa ko a baya ban faye shiga cikin manya ba ina zama ana suraitai don nakan rasa may zan fada wani lokacin . Kwance nake sai dai ba barci nakeyi ba idona kawai na rufe na dora tsintsiyar hannuna a fuskana. Idanuwa dake rufe bai hanani sanin ya shigo dakin nawa ba don kamshin turaren shi dana shaka a lokacin . A hankali na bude idanuwa na da suke rufe da farko yana saye da hannuwan shi duka biyu a cikin aljihun wandon shi dake jikin shi. Yana ganin na bude idanuwa sai ya karasa takowa zuwa inda nake kwance tare da kura min idanuwan shi duka biyu a inda nake kwancen. "Rahama, Na amsa da naam ba tare da ko na motsa jikina ba daga yadda ya samay ni a kwance din da farko saman gado. May kike nufi ne da yin hakan da kika dauko yi a gidan nan yanzu bayan kin san duk wanda ke gidan nan a katshin ki yake zama sai ki shige daki ki bar mutane a falo suna zama. Na fahinci tun ranan da akai maganan nan da Zulfau kika dauki bakin rai kika sawa zuciyar ki haka kada kice ko ban fahinci may kike nufi bane fa ? Kin daina kulani kin daina kula duk wani wanda ke gidan nan yanzu kamar yadda kikeyi a baya can ? Wasu kwalla ne masu zafi suka silalo a idanuwana, na tuna yadda ya rufe idon shi yai min tas ranan akan gaskiya na a gaban matar shi. Idan kuwa ban kama kaina na tsaya a matsayina ba ai wata rana zan iya kai kaina inda Allah bai kaini ba wurin karanbani na. Lafiyan ki ana magana baki bani amsa ba sai ki kama zubar min da hawaye haka kamar wacee akaiwa wani abu daga magana kawai. A hankali na iya bude bakina da kyat nace don Allah daddy ka barni a matsayi na a dakina wanda ka bani agidan nake zaune bana son shiga hakkin da banawa ba ni kadai a gidan mutane. Yace haka kikace ko nace hakan aka fada min ai koka mantane ranan abinda ka fada min a gaban matar ka akan na tsaya a matsayina kuma banfi kowa iko da gidan ba. Yace wanan ne hujjan ki dama na sani sai dai kina da aiki idan kikace ke baki mantuwa da sabani idan anyi. Ba rashin mantuwa bane sai tunatar dani wani matsayin da nake ciki wanda naso na manta shi a baya can. Yace cikin kada kan shi ok yayi kyau tunda haka kikace ba matsala yasa kai ya fita na bishi da kallo har yabace min da gani na share kwallan fuskana tare da gyara kwanciya na. Ina kwancen ban daga ba sai gashi ya sake shigowa dakin a karo na biyu wanan lokacin ya sauya kayan dake jikin shi zuwa rigar barci. Take kuma ganin shi yasa gabana ya soma halbawa a hankali, da kyat na tatara natsuwa na wuri daya har ya karaso inda nake kwance. Muryan shi naji yana fadin Rahama kin ban matukar mamaki da kalaman da kika fada min a yanzu kafin na fita. Bayan aure na dake sai nake daukan zan samu natsuwa da kwanciyan hankali a gare ki ganin irin tarbiyan dake gare ki. Sai kuma irin yadda rashin kwanciyan hankali ya yawaita a tsakanin ki da abokan zaman ki daya biyo baya musanman ma Saade da Allah kadai yasan sirin ku a baya sai ga sabani yazo yana yawan shiga a tsakanin ku kuma. Wanan dalilin yasa naga gara na raba ku ko za, a samu zaman lafiya da kowan ku shine dalilin da nai dubaran dauko ki zuwa nan garin na kawo ki inda babu kowa naki ko nawa sai abokan arzikin da Allah ya hada mu dasu anan. Duk da hakan da nayi Rahama ke nan na kasa sama muna farin ciki gayin haka don gashi har yakai a gaban iyayyen mu kina son su fahinci akwai wani matsala a tsakani dake a yadda kike yi din nan. Kina nufin ko nuna masu ni na kasa sama maki farin ciki da kwanciyar hankalin da mutane suke hasashen kina a cikin sa a nan din. Jin yayi shiru yasa nace dashi, daddy ni bakai min komai ba fa kuma ba wai nayi wani abu bane a sani kawai dai na kama kaina ne ga tunin da akai min a matsayina. Yace tuni akan may yanzu ke kinga yadace a yadda zulfa ta gaya min anyi na tsaya nagoyi bayan ki batare da na dauki mataki ba ai sai ace dani gaskiya ne nafi karkata akan ki kamar yarda ake fadi din. Nace aini da kai mun san fadi ne kawai amma may akai min wanda su ba ai masu shi ba sai dai suce ina nan garin a tare da kai ni kuma ban hana kowa zuwa ba ai tunda suma gidan mijin su ne nan din. Murmushi yayi yace keda bakin ki don bacin rai kike fadin wai wata tazo ku zauna da ita anan din ? Nace in Allah yayi akwai wacce zata zo mu zauna dani dakai ai duk bamu isa mu hana ba daddy . Daddy Allah ne fa mai tsarawa bawan sa rayuwan da zai yi a duniya ba wai tsarin bawa bane duk mai zama tazo mu zauna mana. Don ka ne nake ganin wa yan nan abubuwan daddy baka tsaya bincike ba ka rufe idanuwan ka ka sauke min masifa akaina yadda kake so don kawai ka gyarawa matar ka rai. Dariya magana na ya bashi yace idan na san yadda ake tsayawa gyarawa mace rai ai kin fi kowa sanin hakan gare ni ke dai kice matsalana daukan mataki batare da na tsaya bincike ba kawai. Nace ni ko may ye yanzu ai ya wuce sai dai ka sani Allah ya na tare da mai gaskiya ko yaushe banga dalilin da da hannun ka ka rufe kofan ka ba da zata zo ita tace na bude mata dakin dan na kowa ne. Yace yanzu dai komai ya wuce ai Allah ya wanke ki banga abin tsayawa bata rai ba anan tunda zancen ya wuce. Nace ai kaine duk wani sanadin fitina na dasu ina son in tabbatar ma daddy zan jure ko wani irin hali da zan shiga dasu akan ka nakuma jure hakan na zama jaruma a wurin su, don na tabbatar masu da kai kan ka cewa ni zama nake da kowan ku tsakani da Allah. Insha Allahu daddy bazaka taba danasanin aure na da kayi ba indai ta wurina matsala zai fito har mu saba maka. A hankali ya karasa takowa inda nake yakai zaune tare da min kiss a goshina yace nagode da kika kara tabbatar min da hakan da bakin ki Rahama. Na dade da sanin kina gujewa bacin zuciyan wasu ki hade shi a ran ki ni kaina nazo nayi nadaman yadda nai maki gama yadda Allah yai saurin nuna min kuskuren abinda nayi da wuri. Wani sanyi naji ya lulubeni a lokaci daya atake kuma hawayen nadama suka soma zubo min don nasan nayi kuskuren daukan zafin da nayi da kowa bayan Allah ya wanke ni ga maganan ko. Yace ina son daga yau ki saki ranki da kowa ki koma normal batare da su mama sun fahinci akwai matsala a tsakanin mu ba. Nace in sha Allahu ya wuce zanyi yadda kace tunda haka kake so amma ni kawai dama dan hutawa nake kafin na koma bakin aikina. Yace ai ban ki hutun ba nima ina son hakan amma a rika dan kula mutane aba kowa hakkin shi don Allah. Ya fice daga dakin bayan mun samu fahintar junan mu nace a raina dama ance matan yanzu a dakin su suke yaji ba sai wani yaji ba. Gashi mun samu matsala kuma mun shirya a tsakanin mu batare da tsofin dake gidan sun fahince mu ba. Tun washe gari na dan fara shiga mutane in dan zauna sai dai ban jin dadi sosai saboda dana zauna zan fara barci a gurin. Har sai nake tunanen ko dai wani ciwo ne ya shigeni haka na barci na san dai dana haihu duk wani treatment din daya dace aimin a asibiti Faiza tai min shi a gida. Ashe ba haka bane gajiya ne kawai yake sani barcin bayan kwana biyu sai na murmure har na fara zuwa gun aikina yadda ya dace don saura wata daya da kwanaki mu gama bautar kasan namu ko . Haka yasa na dage sosai ga aiyukana na gidan mijina dana wurin bauta ma kasa don kada na samu matsala a ko wani ban gare. Daddy yakan yi kwana goma zuwa sha daya ko sha biyu sai ya leka kano yai kusan kwanakin da yayi muna ya dawo. Har nai arbain wanda yazo daidai kuma da gama bautan kasa na a asibitin da nakewa aiki din. Sun karbi takatdun mu mu hudu sunce zasu iya neman mu anty time idan bukatan hakan ya taso garesu. An bamu kyaututuka na yabo kamar kada a rabu muka barsu suna jin kewar mu sai kuma gida gasu mama na shirin komawa gida don yanzu hankalin su ya koma gida sosai sun gaji da zama wuri daya. Daddy yaban kudi masu yawa mukaje dasu sukai sayayya saura kwana uku su tafi sai shirin tafiyan su akeyi don shi zai mayar dasu gida da kan shi. Naso zuwa amma daddy ya hana yace na bari idan sallah yazo sai mu tafi can muyi sallah tunda ya gabato su ma don azumi suke son komawa dakunan su. Ranan da zasu tafi kusan duk mun nuna damuwan mu don bamu son su tafi saboda suna da dadin zama sosai. Bayan tafiyan su sai gidan ya koma muna shiru kamar ba kowa dama ance bako Rahama ne ga wuri. Shirun da gidan yayi yasa muna shirin kwanciya ranan saiga Ihisan cikin kayan barcin ta take cewa wai ita bazata iya kwana dakin ta ba tsoro take ji. Nace a, a Ihisan in banda abinki ai ba yau kika fara kwana dakin ba kuma kefa kika matsa da abaki wanan dakin ke shi kike so. Don haka kiyi hakkuri ki koma dakin ki ki kwanta kiyi addua Allah zai tsare ki tace itafa atabau sai dai in Atika zata zo su dinga kwana a tare. Atika tace wa ni wallahi bazan tafi ba keda kike fada a school din mu cewa ba baban mu daya mu yan aikin gidan ku ne anty mu ta karbewa mamakin miji shine mukewa mutane sallon banza kika sa akai min dariya. Wani iri naji ba dadi a raina amma na daure nace haba Atika don kawai tace ki tayata kwana shine zaki mata sheri haka ? Tace wallahi anty ba sheri bane ai mama Laraba ce tai muna sharia da muka dawo gida tace kuma nayi hakkuri kada na fada maki. To ai yanzu gashi duk da anbaki hakkuri kin fada naji tace ai haushi naji wallahi ni ba zan tafi ba na juya inda Ihisan take da alama dai tsoro take ji din nakoma lalashin Atika din tace muje amma kinci arzikin anty wallahi nace nagode. Na juya wurin Ihisan nace da ita haba ihisan ai ba sai kin tozarta dan uwan ki ba zakiji dadi kowa ma ai yasan cin arziki mukazo gidan ku shi mutum rana gare shi da kike ganin shi don akwai ranan da zai taimaka maka. Tace Iam sorry mummy bazan sake ba ai mamanace tace dama idan sun min tsiya na fada masu hakana amma na bari tun ranan da grandma tai min fadan hakan. Nace good girl haka ake son yaro ya dauki fadan manya dama ki bari kinji a zauna lafiya da mai kudi da tallaka ai duk Allah yayi shi ko. Suka wuce zuwa dakin nace kada a manta ayi addua dai idan za a kwanta suka insha Allahu. Bayan tafiyan su mamakine fal a zuciyana yadda mace zata zaunar da karamar yarinya haka tana koya mata kissa da kisisina Allah kadai yasan irin hudubar da taiwa yarinya da zatazo ko idan sunyi waya. Don haka zan bi yarinyar sannu a hankali na fahinci komai da take kullawa agidan don idan nai sakaci zata iya min wani kulli da ba zan iya fitar da kaina a ciki ba wata rana. Sai da na samu kebewa da Atika nai mata fada mai kama da jan kunne akan ta sani ba daya suke ba da Ihisan don kada wata rana taga tayi abu tace ita ma zatayi sosai naja mata kunne Alhamdullahi kuma yarinyar ta fahinci maface ni sosai. ********* ********* ********* Bayan daddy ya isa gida ya kai su mama Laraba gidan ta inda anan Attu zata kwana sai washegari yasa akaita gida. Ya isa gidan shi ya samu iyalin shi lafiya anty ce da girki bayan sun gaisa ne take tambayan shi su mama yace da ita ai tare suka dawo ya sauke su gida ne. Tace a a na dauka ai tare da Rahaman zasu dawo gaba daya tunda ta gama abinda ya kaita can din ko ? Yace cikin mamaki ta dawo ina kuma tace ban gane ta dawo ina ba, ba anan take ba dama ko a can zatai ta zama kuma ? Yace dama kunyi da ita cewa idan ta gama zata dawo nan ne ? Tace da kai dai mukayi haka da zata tafi yace to a can zata zauna don aiki zata fara badadewa ba da zaran danta yayi kwari. Nan ta bishi da kallon mamaki tace au Rahaman aiki zatayi ita ke nan yace eh ba shine burinta ba ko haka zatai tsawon shekaru bakwai ya tafi a banza bata more mai ba wa alumma ? Abin mamaki baya karewa kullun a gidan nan tace daga karshe yayi ashe nike wautana anan ina murnan zasu dawo gida. Yace ai da nan da can duk daya ne a garesu ko may ake a can wanda ba ayi anan din waya ne kullun kuna gaisawa idan kun ga dama to sai may kuma ? Bata iya magana ba don mamakin daya bata yawani zare a lokaci daya kamar bashi kamar wani bako ya koma mata sam yanzu ba kamar wanda ta sani ba a baya. Mai dubaiyya da son jin bukatunta amma yanzu shi da kan shi ma ke kirkiro mata matsala. Don tunda ya tafi da yara karatu can ta fara kawo wutan gane cewa akwai magana gaba don haka ta mike tsam ta bar falon ta barshi yana cin abinci. Ya bita da kallo sai dai yana jiran ta tunda duk itace ta jawo mai yin haka ai ta dauko fitina ta saka a ranta bata zaman lafiya dashi kwata kwata yanzu haka ma abokan zamar ta kamar wacce asiri ke aiki a kanta har yanzu. Shiru shiru yana jiran ta sake maganan ya bata amsa daidai da maganan ta amma sai yaji shiru bata kara yin maganan ba again. Abinda bai sani ba ranan ta kwana tana tunane kan maganan sai daga karshe ne ta dai yanke shawaran ta hakkura tasawa kanta saida kawai akan zancen Rahama. Don dai koma may ye dai ai itace silarshi tana ta bada kai ana mata dariya a tsakanin su ga yaranta can har biyu gunta amma bata ji wani korafi ko kadan ba daga yaran har yanzu ko sunyi waya dasu lafiya lau take jin su. Hakkuri da nadaman abubuwa yazo mata a rai a lokaci daya ta mike ta roki Allah da ya sanyaya mata zafin Rama da take yawan ji a zuciyar ta koda yaushe. Tasan yarinyar bazata iya cewa ga wani abinda ta taba mata ba na cutar wa amma yakai yanzu saboda halin da take gwada mata har ta fara mayar mata da amsan magana mai zafi. Shine dalilin da taja bakinta tai shiru ta dai san halin mijin su fiye da kowa hutsune bai jin mutunci idan idon shi ya rufe. Kowa kuma haka yakewa don may karamar yarinyar da ta raina zata fita sanin maganin zama da mijin su lafiya aiko wacce mace na kishin mijinta ta san kuma Rama na da kishin ita ma tunda mace ce amma ta iya dannewa ta boye sai itace bazata iya boye nata ba. Aike da kira ya ishe shi a gidan su Hindatu har takai ranan an datse a gidan mahaifan shi nan Alhaji shi ya sa baki yace sai yaje ya duba matar nashi tunda yanzu ta gane kuren ta. Baiso ba haka ya daure ya tafi da yamma shi da Bashir daya dauka don ya raka shi gidan ya ganta amma ran shi baiso haka ba. Sun isa gidan suka aika a sanar da zuwan su hindatu naji ta fada daki tafara dauko kwallin da aka bata ta shafa tare da wani powder da turare duk tayi yadda aka umurce tayi ta yafa taiwa uwarta sallama ta fita uwar nacewa kinyi yadda akace kiyi ko kin dai san irin kudin da muka kashe a gurin nan. Tace kada ki damu mama nayi komai yin fatan dai mu dace kawai idan ya ganni din. A lokacin saura wata daya ta gama idda da takeyi tana fita ta samay su zaune a falo ta gaidasu a cikin wani irin ladabin shagu. Ya dago kai da kyat yana amsa mata yana kallonta yaji wani irin shock a ilahirin jikin shi gaba daya yaga ta sauya mashi ta koma kamar wata hawai niya mai rikida ako wani lokaci. Tai mashi kyau ta koma kamar wata yar shila a ganin shi, wani irin sonta da kaunarta yana fisgan shi. Cikin washe baki yace da ita idon ki ke nan daga magana kadan sai ki fushi ki dawo gida. Take ta gane cewa tarkon ta ya kama kurciyar da take hako nan ta shiga juya shi yadda take so har sukai mata sallama suka tafi Bashir dai yana kallon ikon Allah. Sai da suka kama hanya yaji daddy ya sauke ajiyan zuciya da karfi yace yaya akayi ne mutumina ? Yace kaina ne naji yai min wani irin sarawa wallahi muna barin wurin nan kamar kar hindatu tafito gaba daya sai na nemi natsuwana na rasa. Yanzu kuma mun bar wurin naji kaina yana sara min ba dadi wallahi nan dai Bashir ya nisa yace dashi nifa kada nai magana nayi laifi kuma ? Yace kamar ya kayi laifi kawai kafadi maganan ka mana kai tsaye ? Yace abinda zan fada ne da nauyi akwai kuma kamshin gaskiya a cikin sa yace kafadi maganan ka mana kai tsaye ka tsaya kana wani kwanaye kwanaye haka dakai ? Bashir ya nisa yace anya Hindatu bata gama da kaiba yadda naga ka zabura daka gantaka kuma sukurkuce a lokaci daya ga wani kamshi wani irin mugun turaren gargajita danaji tanayi. Daddy yace kai amma akwai ka da wani magana yanzu nine hindatu zataiwa magani kake gani ya kamani ? Bashir yace kai kafi karfin sherin mace ne ko may wallahi ka fada tarkon mata kace nace da kai wata rana bai yi magana ba sai murmushin da yayi yace kai akwai da wani zance wallahi hindatu fa matatace ka sani. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 77 Idan daddy ya tafi baya wuce kwanakin da na fada a baya sai gashi wanan tafiya har ya gwauta kwana ashirin da biyu a kano. Baya kiran mu kamar yadda ya saba kiran mu a baya idan yana can sai jefi jefi zai dan kira sama sama yaji lafiyan mu. Sai dai abinda na dan kula dashi shine yawan kiran Ihisan da takanyi musanman ma da dare naso na dan gane wani abu amma sai kuma nai tunanen kila rashin uwar ta a gidan yanzu yasa yake yawan kula ta din. Ranan sai gashi ya dawo sai dai ya fada ya dan yi baki kadan mun tare shi da murnan ganin shi sai dai ba wani walwala sosai a tare dashi sai na dauka duk gajiya ne hakan kawai ya kama shi. Sai da yai wanka ya huta bai dade ba yafito ya fita daga gidan ina mai tayin abinci yace dani barshi kawai bana jin cin abinci yanzu. Ga watan Azumi saura yan kwanaki a lokacin sai kuma ba hankalin maigidan wuri daya don da gani akwai abinda yasa a gaban shi. Ni dai ban tsananta wa kaina sai nasan may yake ciki ba ina dai kokarin wurin ganin na sauke duk wani nauyin da ya dace ai mashi. Wani abinda na lura dashi kuma shine duk dare sai mun kwanta za, a kira shi da waya zai dauki lokaci yana waya. Lokacin ne na fara shan jinin jikina da gane cewa da mace yake waya sai na nemi walwala a tare dani na rasa amma duk da hakan bani nuna komai a fili na bar abin a raina kawai. Ana azumi saura kwana ukku lokaci duk kwanan shi shidda da dawowa yace zai koma kano a gobe banyi mamaki ba ko zaton wani abu tunda nasan cewa gida ne can kuma akwai iyali. Sai da ya shirya yafito yana waya naga shirin wucewa yakeyi nace daddy sai ya juyo yana kallo na naji yace da wanda yake wayan minti biyu ya kashe ya kara juyowa inda nakke yace dani umm,humm ? Na dan kwantar da murya nace daddy dama naga kafin ka dawo za a tashi da azumi shine nace baka sai muna abin taron azumin ba. Yace ban fahince ki ba may kike nufi da hakan nace wai da nace kayan shan ruwa kodon yaran nan ko ? Yace Rahama yaushe kika fara wanan halin har ni zakice wai ban sayo maku wani abu ba ko may kike nufi da wanan maganan naki ? Ko kin taba min magana akan na sayo maku abu a gidan nan bani ke sayowa ba in naga dacewan hakan ? A sanyaye nace don Allah daddy kayi hakkuri nayii kuskure dama don naga wancan karon ka dan jiima baka dawo bane yasa nai magana yanzu din. Yace o,wo yai min wani irin kallon sama da kasa kamar wanda ke hake dani dama yana jirace na tanka mai. Nace Allah ya tsare aje lafiya adawo lafiya yace amin kamar a hasale ya juya ya wuce abin shi batare da ko juyowa ba again. Mamaki ya kamani nakai zaune a kujeran dake kusa dani ban san abinda yasa daddy yanzu magana ba magana ba sai ya hauni da masifa sosai. Aisha ce takawo min Haidar da ke kuka na karbe shi sai ga baba ya biyo su ya kwanta a jikina nan na sauke ajiyan zuciya na gyara ina fitar da nono nabawa yaron. Ina shayar da yaeon ina tunane ga baba da ke tsaye rabin jikin shi kwance a jikina ya damay ni da tabe tabe a fuskana. Nace a sanyaye don haushi nakeji a raina bari mana baba yaton bai bari ba nakai mai duka akai abinda bana yi duka sai dai inwa yaro fada. Take yaton ya fara kuka sai kuma yabani tausayi bashi ya bata min rai ba na fashe haushin uban shi a kan shi. Na jawo shi da hannu daya ina lalashin shi har na samu yai shiru Aisha taji kukan shi ta fito tana tambayan may ya samay shi kuma ? Nace baijin magana ne na dan duke shi shine kikaji ya bare baki haka yana damun mutane da kukan banzan shi. Nan dai taja yaron suka fice suka barni ina tune a zaune sai naga ni may ma yakaini yi mai magana bayan nasan yadda muke a yanzu dashi. Sai zuwa sha biyu har lokacin banajin dadin yadda muka rabu ya tafi dani a hasale sai na yanke shawaran kiran shi na bashi hakkuri. Kira daya biyu ga hudu ya daga yace cikin muryan shi mai nuna har yanzu baya jin dadin ranshi da fadin. Yaya akayi kuma na dake nace ba komai sannu da hanya kawai dama zan maka sai kuma na baka hakkuri bisa ga saba makan danayi da zu a yafe min don Allah nayi kuskure na sani. Yace is ok sai anjima ssi ya kashe wayan kit bin wayan nayi da kallon mamaki may naiwa daddy ne haka nake tambayan kaina ? Abinda ban sani ba ashe bani kadai ke fuskantar wanan halin ba kowan mu ya rasa gane kan shi tun zuwan shi gidan su hindatu abubuwa suka jagule baki daya a kan shi. Wanan zuwan da yayi yazo a tsayar da maganan komawan ta gidan shi har ya iso gida baida walwala ba isa gidan shi ba sai da yaje gidan su hindatu ya zube tsaraban da ya sawo masu a hanya. Ya samu iyayyen shi da zance sai dai hajiya ta nuna bata yarda ba taso abar hindatu a hakkura hakana a hakkura kawai. Amma yadda daddy ya dage sai hankalin su ya tashi Alhaji yai gyaran muryan yace kinga ayi hakkuri tunda shike da abin shi don haka barshi ya gyara auren shi a zauna lafiya. Dole hajiyan ta hakkura sai dai bataso hakan ba Alhaji ya tura manya aje a gyara zancen sai ga masu zuwa sun dawo da sabuwar magana kuma. Wai iyayyen hindatu da ita kanta sunce in har zai amincr idan ta koma ya maida ita Abuja da zama ita ma ta amince da zata dawo. Nan hajiya ta hau fada tace sam ba zai yuyu ba anan ma gaban kowa yaya aka kare da ita balle ta bisu can inda babu idon kowa sai su yasu yasun su. Amma daddy na zuwa yace may zai hana ya amince da nan da can ai duk gidan shine shike da iko akan komai don haka ai wanan ba matsala bane ai. Hajiya tace yanzu da hankalinka Alhaji karami kake wanan magan kafa san halin yarinyar nan sarai bawai ta canza bane . Yace kai hajiya ita hindatu wani haline da ita kawai ni keda gidana ai zan san yadda zanyi indon wanan ne ai ba wani matsala akan shi. Tace a, a fa yar mutane dake can zaune kalau cikin rufin asirinta kada taje ta tayarwa yar mutane da hankali kuma ? Hajiya ita da Rahama din ai duk ni aje su ko may zai kawo wani fitina kuma yanzu tunda kowa yasan kowa dama . Hajiya bata dai gane komai ba don ya dage daya amince da atafi din shi ba matsalar komai ga yin hakan tace to shike nan ai may daki shiyasan inda ruwa ke mai yoyo. An mayar da aure ko su anty dake garin basu da labari sai ji da sukayi ga bakin shi yake fada masu batace dashi kalla ba don ta fahinci irin rawan kafan da yake duk aanan lokaci ta san kuma ruwa baya tsami banza ai. Bayan kwana biyar sai gashi ya dawo lokacin Azumi nada kwana biyu da dauka bai nuna min komai ba mun tare shi cikin mutunci. Sai bayan an sha ruwa yana zaune da yaran suna hira na shigo falon bayan na idar da sallah nai mashi sannu da shan ruwa na juya zan wuce yace dani gobe ina son duk wani kayan daki a fitar sai za a saka sabo ne . Na juyo da mamaki don naga kayan ai basu komai ba amma kuma sai na share don kada na daukowa kaina magana nace Allah ya kaimu kawai. Sun gama ya sallami yaran yai shirin kwanci sai dana fahinci cewa yadan dade da shigewa na shirya naje dakin. Na mulke jikina da ture masu kamshi don kawar da karnin nonon da nake shayarwa a lokacin. Har na shiga na kwanta yana waya bai gama ba har barci ya dauke ni ya gama bai tayardani ba sai da muka tashi don yin sahur. Washegari tin safe muka tashi da aikin kwashe kayan da ya umurce mu dayi bamu jima da kwashewa baaka fara shigo da wasu iri dirka dirkan kujeru masu kyau da girma. Ma aikata suka gyara komai sai dai dakina da dayan dakin dake facin din na ihisan komai nashi iri daya ne da nawa kala ne kawai aka banbanta masu sai biyu zuwa uku suka gama lokacin ina kitchen mun fara hada abin buda baki ko. Munyi mamakin ganin hakan amma naja bakina nai shiru ban tsaya magana ba don jin ko yaya hakan din. Sai dare sosai ya dawo har yaran sun shige ko dakun nan su don azumi ne kowa ya gaji ba wani dogon hira. Ko ni har na shige na kashe wutan falon ya dawo gidan jin motsin dawiwan shi yasa na fito ya na zaune yana cin abincin da ya samu an jera mai na buda baki. Nai mai sannu da zuwa ina kokarin juyawa naji ya kira sunana na dakatar da tafiyan dana fara yi tare da juyowa gare shi. Yace zoki samu wuri ki zauna ina son nayi magana dake ne samun wuri nayi na zauna sai dai ba gaf dashi ba. Yace Rahama ina son yin wani magana dake ne sai dai ina fatan zaki fahince duk da nasan ba wani bakon abu bane sosai a gare ki. Gabana ne ya soma harbawa don ban san wani magana bane wanan wanda ba bako na bane haka ? Maganan da zanyi bawai ya sabawa sharia bane ko da wata manufa zanyi sai dai daurowan hakan . Na tattara natsuwana ina sauraren abinda zai fada min din a yadda yake maganan shi mai kama da roko kuma da gadara yasa nasan akwai wata a kasa. Jin nayi shiru yasa ya dago kai ya dan kalle ni yace dani kina jina kuwa nace inaji kai nake saurare ai . Yadda nai magana yasa yasan a shirye nake ke nan da inji abinda zai fada din a lokacin. Ba wani magana bane sai dai kiyi hakkuri a yadda na tsara zaman mu a baya yanzu an samu akasin hakan don Hindatu zata dawo nan garin ku zauna tare. Dam dam naji gabana ya fadi shike nan ni nawa ya samay ni inko hakane gara kawai na barsu na koma kano komai ya fanjama fanjan. Kinji abinda na fada aiki nace kwarai kuwa ai wanan ba matsala bane don gidan ka ne danan da can sai dai ni zan barku na koma kano na zauna tunda dama na gama abinda ya kawo ni garin ina ga zaifi maku dadi hakan ma don ku sakata ku wala ba sai na tsaya a tsakanin ku ba. Yace aiko kina nan bazaki hanamu sakata ba kamar yadda itama bazata hanaki sakata ba din. Don haka gara na koma inda na saba yafi min zama a cikin ku mu kadai dagani sai ku a garin mutane. Yace wanan kuma maganan ki ne kin dai ji tsarin danayi yanzu a gidana nace naji don haka zuwa jibi zata iso don mun mai da auren mu da ita. Nace ai naga alaman an maida aure tunda take son zuwa takurawa wacce ka sayo ba auro ta kayi ba kamar kowa dama dani tafita yanzu kuma ta dawo dani a ranta. Yace wanan kuma tunanen ki ne hakan ni dau gidana ne kuma yadda nake so zan tsara kowa na da hakki a gare ni . Idan zaki fahince ni ki kwantar da hankali don babu abinda zai faru tunda ita ba bakuwar ki bace. Ni dai na fada maki abinda ake ciki in zakiyi hakkuri ku zauna lafiya dan ba wanda ya kawo wani a cikin ku nina kawo kowan ku kowa kuma da halin shi zan zauna dashi. Na mike nace wanan sai kuma a yaudari wata ba ni ba Allah ya baku zaman lafiya dama tare na samay ku ai koda na shigo don haka kunfi kusa. May ya kawo zancen yaudara anan dukkan ku ai mata nane babu wacce zan tsaya yaudara daga cikin ku. Banyi tsamanin jin haka daga gareki ba a yadda na tsamoki da farko daga cikin ku na kawo ki nan don yanzu nace wata zata zo ku zauna shine zai zama matsala. Na juyo tare da tsayawa nace tun farko ai saida na baka shawaran yin haka amma kace dani ba tsarin ka ba ke nan haka kaga dama. Sai yanzu din ta kullo ni arai zata zo tace zata shiga min rayuwa ban sa akai ba balle a kar min . Kuma kafin ma ta taso ni na isa gida ko sai tayi da wata amma badai Rahama ba dai kan. Inda nasan wanan shirin kake kwana da kwanaki aida baka bata lokacin ka ba gurin shiri da kafada min tuni da angama ai. Na juya na wuce zuwa dakina ban kara tsayawa sauraren shi ba ina shiga nafara hada kayana dake cikin wardrobe. Tsab nagama shirins tunda dare na rufo kofana tare da hayewa gado wurin yara na da Aisha dake kwance gefen su. Barci ya kaurace min a idona sai faman tunane nakeyi don na tabbatar da wanj manufa hindatu ta zabi biyoni Abuja wanan karon wanda manufan bai wuce kalman daukan fansa ba akaina. Tunda dama tana cewa a dalilin shegen dana akai mata saki don haka sai ta rama abinda nai mata koda zata tafi tsirara ne. Abubuwan da daddy ke min duk kwana kin na dama nasha jinin jikina da akwai wata akasa gashi kuwa yau naji da kunnuwa na. Kai namiji sai a barshi kawai idan ya tashi munafuncin shi sai dabara da wayo ya bace mashi wai yau daddy ne da bakin shi yake ce min da hindatu zamu zauna gidan nan. Matar da bata maida fitina bakin komai ba aida in zauna da ita gara nakoma can in ma dafani anty zatayi yafi da hindatu ta shigo min da balai gida. Wai ma sai bayan da ya gama komai shine yanzu ya mayar dani sakarai yazo fada min abinda ta zaba don ta dawo mai. Ba wani dadi naji ba koda nike ni kadai din balle ace an karo min sabon fitina akaina. Ni wanan rayuwan auren da may yai kamane wai kullun sabon fitina da kanana kanan rashin fahinta ke zo muna. Ni dai arabu yafi min komai sauki da wanan zaman danger da muke da kishiyoyi wi da mijin ma haka wi. Da yake barci barawo ne sai da yai dabaran satana cikin wanan halin da nake ciki da asuba ranan shi da kan shi ya tashe ni inta dasu Aisha suyi sahur acikin waya. Ban fito don sahur ba dama ni ban damu da yin sahur din ba kullun balle yau da raina yake a bace. Ruwan sanyi kawai nake da bukatan sha na koma na kwanta nafito falin din in dauki ruwa a kitchen nan nagan shi zaune yana shan tea suna sahur shida Nasir don yaron akwai shi da kokarin Ibada sosai. Ban ko kalli inda suke ba na wuce zuwa kitchen kai tsaye sai Nasir din ke cewa dani kin tashi mummy nace eh Nasir ba tare da na tsaya ba na wuce abina uban yabini da kallo kawai. Ganin yaron ya bini da kallo yasa yai murmushi yace yau mummy ka fushi take kyale ta yaron yace but why daddy yace wa yaron nothing cikin daga kafadan shi. Sai can yace wai bata son dawowan maman Ihisan nan gari haba daddy a gidan nan wanan matar zata dawo ta zauba da mu haba haba gidan zai zama badadi ke nan daddy . Wani tsawa ya dakawa yaron yana fada dashi Nasir har yaushe kasan irin wanan magana ina ruwanka da harka. Yaron ya ja bakin shi yai shiru haka ya mike ya bar uban zaune a falo ya bi bayan yaron da kallon mamaki da takaici. Kafin karfe bakwai na shirya tsab na shirya yaran nawa kuma tare da Aisha da Atika sai helen da nake tunanen yadda zanyi da ita don dole na sallamay ta koma gida. Muryana da Aisha ya tsinkayo daga dakin shi lokacin da nake cewa da ita kuyi sauri ku shirya bana son muyi tafiyan rana don kun san azumi ne ga helen ta dage da kukan ta wai sai ta bini a fadawa wacce ta kawo min ita tare zamu tafi. Ban fi minti biyar ba da shiga ya shigo dakin da sallaman shi ya bi kayana dake a tsakiyan dakin cikin troler dina da kallo. Ya juyo inda nake yana murmushi yana cewa wai ke da gaske tafiya zakiyi ne kike nufi Rahama don dan wanan magana ? Ban juyo na kalle shi ba sai takarduna da nake cusawa a wani jakkana ganin ban juyo ba yace dani ki zauna muyi magana ban jiyo ba still sai ya karaso inda nake a tsaye din ya kamo hannuwa na duka biyo na dago idanuwa da suke cike da bacin rai na sauke a kan shi. Ganin yanayi na yasa ya fahinci a cike nake da bacin rai tun daren jiya sai yaji baiji dadin yadda a lokaci daya na sauya ba akan may zan sawa kaina damuwa dayawa haka don kawai wata zata zo mu zauna a tare. Amma a fili sai cewa yayi Rahama kin bani mamaki wallahi ban taba tsanmanin wanan matakin ba a gare ki don kawai wata zata zo shine abin bata rai gareki alhalin kin san dama bake kadai bane gareni. Kiyi hakkuri ki kwantar da hankalin ki yanzu ai in kin wuce sai tace tsoron ta kike yi har kin gudu ko kina kishi da zuwan nata nan. Na dago idanuwa na na sauke akan shi akamar zanyi magana sai na zare hannaye na daga gare shi a raina nace kai namiji dai bai da tunane shi yanzu har ya matan irin rikicin dake tsakanin mu da ita ne a baya inda bamu haduwa wuri daya ba ai fitina ba. Balle yau ace wai har shi da kan shi zaiyi sha, awan tara mu a gida daya irin wanan wani irin gululun bakin ciki ya tokare min zuciya na naji ko ganin shi bana son yi a idona tare da dana sanin zama dashi. Zama nayi idanuwa na suka fara fitar da hawaye n takaici zama yayi a kusa dani ya kamoni zuwa jikin shi na fisge da karfi nace kada ka soma ka tabani wallahi na gaji da yaudara irin naka. Baka kauna ba ka sona zaman dole kake dani na sani ba yau ba don gashi yau ka nuna afili da kan ka ka dauko min tashin hankali har dakina gara na koma gida inda akasan darajana da kima ta. Yace kamar yaya na dauko maki fitina har dakinki a kanki zata zauna idan tazo ko may kike tunane haka da zuwan ta din ina kowa da halin shi zai zauna. Nace haba daddy kabarni don Allah na yi abinda zai fisheni kadai riga da ka zabi wacce kake da muradi a kanta ba sai ku sha zaman ku ba. Bina yayi da kallo ganin na mike na ci gaba da shiri na ya dan dade a tsaye yana kallona sai ya juya ya fita har nagama shirina komai da yake nawa na dauka. Waya na ke ringing na dauka a zatona ko Faiza ce da naiwa magana ta samo min mota sai naga bakuwar nomba ce na dauka da sallama a bakina. Ina mamakin waye kuma ke kirana da safe hakane wai ban dai kai karshen tunane na ba naji muryan namiji yana karba min sallaman nawa. Mun gaisa dashi ya kira sunana yace Rahama nasan baki gane mai magana ba ko nace eh hakanane. Yace to yayan ki Bashir ne abokin mijin ki nace au yaya kaine ya kwana biyu ya iyalin ka yace suna lafiya sai nai shiru. Can yace Rahama yaya akayi haka kuma daga jin hindatu zata shigo wurin ku ku zauna sai kuma ki rikicewa abokin nawa keda ake yabo kuma Rahama zaki bari har wata hindu can ta bayar dake. Rahama duk fa wani hannkurin da kike a gidan nan kowa dake tare da ku ya sani don Allah daga yau ki dauri ki zama MARUCIN KAN DUTSE A GIDAN MIJIN KI FITAR KI SAI AN DAURE. Nasiha sosai yai min masu ratsa jiki har yake ce min duk abinda na gani don Allah na daure na bar komai ga Allah yace dama haka take bukata a gareki ai . Wanda yayi kaka abu don kaji haushi ka sani shine kuma har zaka bari ya fahinci ka raza da shirin shi don Allah narokeki da ki daure ki zauna dakin ki yi hakkuri yanzu idan kikai fushi kika tafi dariya za ai maki wallahi kin dai san halin ku na mata da tsegumi ba banza Hindatu ta bar mijin ku ba nina sani don ni ke ganin abinda akeyi. Wanan kuma ba komai bane don kece zaki shawo hankalin komai da zata so aiwatar wa don kara gurbata mashi da rayuwan shi. Shiru nayi ina sauraren shi sai hawayen da ke zubo min yace don Allah Rahama kiyi hakkuri don tafiyan ki ya tayar da hankalin mijin ku sosai wallahi shi da kan shi ya kirani yake fada min halin da kuke ciki tun jiya daya fada maki. Shi hakkuri wuta gare shi amna a karshe dadin shi yawa gare shi idan ka daure don haka ki janye wanan maganan tafiya don Allah Rahama. Cikin muryan kuka nace da ka barni na basu wuri yaya bashir tunda banda amfani a gare shi. Wa ya fada maki Rahama keko keda amfani a garshi shima ya sani ai don ko sha anin Saade idan da baki hakkuri ai da ba a kai haka ba ko. Muna gama waya da bashir sai kuma ga mama Laraba ta kirani nace itama an kai karan nawa wurinta ke nan shike nan ni nawa ya samay ni dada. Mun gaisa ta shiga lalashina ta na bani magana fada sosai tai min tare da lurar dani illar abinda nake son yi din takuma kara fahintar dani yadda zan zauna da hindatun idan tazo tunda na riga na san halin ta nai mata godiya na share hawaye na dole in zauna kada na zamo wacce bata jin maganan manyan ta. Aisha na kira don ta dauki yaron da ya gama shan nono take cewa dani an fasa tafiyan ne anty nace da ita eh kawai ta dauki yaton tace anty kiyi hakkuri don Allah koma may ye Allah nagani ai. Ban fito ba shima bai shigo ba da rana nafito inda zamu hada abin buda baki tare da yaran muna kitchen din naji dawowan shi ban damu da naje gaida shi ba yadda nake matukar jin zafin shi ranan. Shima dakin shi ya shige bai damu da yazo inda muke ba don bats kan mu yakeyi ba ma a lokacin dawowan matar shi nan yake ta faman shiryawa kawai a ganina. Ina aiki ina tunanen yadda zan zauna dasu mutumin ma da ya ajeka ba wai ya damu da damuwar ka bane a yadda nasan hindatu zanga rayuwa kala kala a wurin ta sai dai ya zama wajibi nima dole na fito da nawa gwanin ta don nuna mata jiya ba yau bane fa. Mun gama komai na shirya mai inda zai yi buda bakin shi na shige daki nsi wanka na shirya ina jiran lokacin sgan ruwa yayi sai tunane nake gobe iwar haka muguwar bakuwar mu ta iso gidan ko nace a fili ubangiji Allah ya haushe ni kan duk wani kulli da zatazo min dashi a gidan nan. Sai da na idar da sallah na dan sha tea kawai a dakina don shi nake iya sha a lokacin don raina ba dadi har lokacin a haka na wuni a gidan dashi. Nafito a cikin kwalliya na yana zaune yana waya yana hango fitowa na ya katse wayan da yakeyi din cikin nuna rashin damuwa na isa inda yake zaune na gaidashi da shan ruwa shima ya amsa min a sake. Na juya zan wuce sai naji yace dani ina kuma zaki baki ban abinci ba juyowa nayi ina dan kallon shi kawai. Nace zan koma daki ne naga ai komai na aje a gurin ba sai na tsaya ba yace wa kike son ya zuba min to ? Kamar nace ya jira matar shi tazo ta zuba mai mana saidai nai shiru kada ya gane kishin nawa yakai haka da yawa. Sai dai nace dashi naga kamar baka tashi ci bane yanzu kana waya kada na takura maku ne ai. Yace waya kikaga inayi yanzu zo ki zuba min naci yunwa nakeji dama banci komai ba bayan ruwan da nasha dazun. Ban musa ba na juya nakoma na fara hada mai abinda zai ci din a cikin plate. Ya jawo zuwa gaban shi ya fara ci sai na dan so mikewa yace ina kuma zaki kin san dai ba haka kika saba yi min ba ko. Ban musa ba na samu wuri na zauna a gefe ina amfani da wayan dake a hannu na sai cin abincin shi yake hankalin shi a kwance. Ya gama yake cewa hada min ruwa na watsa ko zanji jikina ya dan sake min ban motsa don banda nayir tashi a lokacin sai da ya kara fafin bakiji bane sai na mike kawai ba tare da nai magana ba na wuce , uwa dakin. Na shiga dakin ke na sai ga wayan anty ya shigo min ina hada ruwan wankan muke waya mun gaisa take tambayana ashe kuma Hindatu a wurin ku zats zauna wanan karon ? Nai murmushi nace haka yace anty tace to akai zuciya nesa dai don kin san halinta ba bakuwar ki bace kikuma kula sosai don kin san makircin ta. Kagin nai magana sai gashi ya shigo dakin lokavin har na gama hada msi komai da zaiyi amfani dashi a bandaki din. Nace da anty tayi hakkuri zan kira nan da minti goma sai na kashe wayan na juyo zan fita daga dakin sai naji yai caraf ya rike ni ta bayan shi tare da juyo ni ina fuskantar shi. Yai murmushi yace ke naga alamar ki idan na biye maki gaba zamuci gaba dayi har bakuwar taki ta samay mu a haka cikin wanan halin. Mutum ance yayi hakkuri ba sai ya hakkura ba ya barwa Allah alamarin sa anfi son mutum ya dinga hakkuri da duk abinda yazo mai na kaddara. Na dago idanuwa da suka rine zanyi magana yace ya isa haka please bana son jin wani magana akan zancen nan abar komai ya wuce please. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , 78 Washegari Ina tsaye a kitchen ina duba kayan amfanin mu sai naga komai akwai sai kaayan miya da muke amfani dashi fresh ne ya dan kare. Na dan kai lokaci a tsaye ina nazari abinda zamuyi anjima na shan ruwa ina nan a tsaye ne sai ga Aisha ta samay ni a kitchen din. Tace tun jiya nake tunanen kayan miyan bazasu ishe mu ba yau sai dai idan na za ai miya ba sabo nace ai yazama dole Aisha tunda yaran sin fi son mai miya nagani. Motsi mukaji na alaman an bude kofan gidaan an shigo cikin gidan sai dai bamuji sallama ba kuma. Aisha ce ta fita ta gani don yaran suna makaranta a lokacin heleen kuma ta na baya tana wankin kayan ta. Sai gata ta dawo tana cewa dani Anty maman Ihisan ce fa da wata bakuwa suka shigo naji gabana ya fadi ras nace innalillahi wa inna alaihin rajiun a cikin zuciya na na karasa da Allahuma ajirni fi musibuti wa, akalilli hairan min ha. Take naji natsuwa yazo min a lokaci daya na daure na fito daga kitchen din daidai lokacin da yai daidai da shigowan maigidan shima. Fuskan shi asake yake fadin ashe har kun iso ko tace wallahi ko kasan sammako mukayi don mu iso da wuri dama. Sannu da zuwa nake mata amma sai tai kamar batajini ba tai wani sharewa na juya wurin shi ina mashi sannu da dawowa ya amsa min hankalin shi na kan su. Na juya zan wuce naji yace ina kuma zaki Rahama ga baki anyi na waiwayo ina kallon su kafin nai magana naji tace bakuwa dai nikan aiba bakuwa bace a gidan nan. Murmushi nayi kawai na sa kai zan wuce yace ina tambayan ki zaki wuce kuma mana ? Sallah zan shiga nayi lokaci ya gabato na bashi amsa da hakan na fara tafiya abina batare da na tsaya ba yace idan kin idar da sallah ki samay ni a falo na shige abina ina jin suna dararakun su nace lokacin ki ne mata. Alwalan na shiga na dauro na fito na shimfida abin sallah nafara gabatar da Nafila sai na kawo azahar nayi ban tashi ba na zauna ina rokon ubangijina da yai min kariya akan hindatu dama ko wani mai kina. Can bayan wani dan lokaci naji muryan shi yana kiran sunana daga kofa sai dana dan dauki lokaci na fito falon ya zaune itama din tana zaune a gefen shi bakuwar ina tsanmani tana daki ne. Na iso wurin naji yace kin shiga kin zauna kuma bayan na fada maki idan kin idar ina jiranki a falo nace ai gani yanzu na idar da sallah dama. Na samu wuri na zauna a daya daga cikin kujeran dake falon ban dago kai na kalli gurin da suke a zaune ba kamar zata shige mai jiki. Ya dan juyo yana kallona nai kamar banga yanayi ba don ba zan ba da fuskan da zata zo min da zafi ba don nasan a shirye ta tako garin da ganin yadda take wani fisge fisge. Hindatu tace dear ya sauke ajiyan zuciya ya dan waigo inda nake yace Rahama nace naam daddy yace magana nake son yi daku tun yanzu kafin yaran nan su dawo daga school. Ai muna jin ka tace dashi yace ba wai na hada ku nan bane don aita min rigima ko tashin hankali ba a gida na kawo kowan ku nan ne don mu zauna tare mu tsira tare bana son jin fitina ko hayani daga kowan ku a gidan nan in ba haka ba ran mai shi zai baci. Sai kuma zancen yara yarana kun san bana son banbamci kowa ya rike min su kamar duk ku kuka haife su da cikin ku. Ina ga sauran bayani kan kwana wanan ya rage a tsakanin ku kuka san yadda zaku raba abin ku dai. Sai tace ai wanan ba matsala inkaji fitina dama an dauko shine kowa ai yasan halin kowa a cikin mu banga abinda za, a tsaya kuma fadi ba yanzu. Kwana kuma yadda muke a baya can gida haka zamuyi ko yanzu two two days kowa yayi ya fita ba shike nan ba. Na juya nace shike nan zan iya tafiya kagama ko yace shike nan abinda zan fadi dama bana son jin komai a gidan nan . Na mike na barsu zaune tun kan na shige naga takai kwance a jikin shi yace a, a baki da hankaline hindatu Azumi fa mukeyi. A raina nace duk abinda kika zo dashi dai gida kika zo don yanzu ba Rahaman da bace wanan da kike fadawa son ran ki. Juyowa nayi na kira Aisha tazo daki ta samay ni dama tunda naji cewa zata dawo nan nasa suka dawo dakin dake kusa danawa hannun mu daya dasu. Ta shigo tana dauke da Haidar daya tashi daga barci nace kai har ka falka ke nan wanan barcin dai baikai ko ina ba. Ta zauna nace da ita dama ina son kara ja maki kunne ne akan zaman matar nan damu na dai fada maki har helen don babu ruwan ku da harkan ta. Tace anty na sani kuma Atika ma naja mata kunne tun jiya har helen din yanzu ma na fadawa helen din tazo. Nace shike nan ba wani abu bane dama tace abinci fa nace yadda naga wanan matar tazo Aisha bari muga gudin ta tukun don kada muyi tace kuma waya samu. Bata fita ba nan ta zauna abinta muna hira helen ma ta shigo tace dani anty naga dare ya fara abinci fa sai dai naga wanan matar a kitchen tana bude bude nace yi zaman ki mu gani. Can muka fara jin kamahin girki na tashi a gidan sai da nai sallah la, asar na fito daga daki na samay ta tafito daga kitchen din nake cewa ashekina ciki bata ko kalli inda nake ba tace eh kawai ta shige. Na koma daki abina ban jima da shiga ba yaran suka shigo gida sai ga su sun samu bakuwa a gidan Ihisan kan da murnan ta ta fada a jikin uwarta. Tace wa yaran ku halan kunyi bakin ciki da ganina ne naga kunyi wani cirko cirko kuna kallona kamar kun ga bakuwa. Jinior baiko bi ta ianta bw sai cewa yake ina little mum din mu take helen da ta kwaso shayi ta daka mata tsawa tace ke yar aiki kizo ki kwashi kayan nan ki wanke. Sai yarinyar tace anty bata bari na wanke masu kaya ita ke wankewa ko Aisha tace to ni ba antyn bace maza zoki kwashe su. Kamar nasan sunayi sai gani na fito daga daki naga helen tana wanke kayan abincin namu nace da ita helen yaya haka bana hanaki ba ashe ? Tace wanan bakuwar anty ce tace na wanke mata na fada mata tace sai na wanke kafin in magana sai najita daga baya na tana fadin eh nice nan nasa ta wanke muna su. Nace amma ni bani bari ta wanke muna kayan ibadan mu don ba musulma bace ko kin manta watan azumi muke watan ibada ne. Na manta kin san bani azumi ne sai yanzu danaji daga bakin ki dai na tuna kallon mamaki nai mata kawai nace helen bar kayan na wanke su shige dakin ki. Sai cewa tayi dama nasan akwai tsiya akan yaran nan dake don dama naji komai gamay dasu to ki sani duk wace tazo cin arzikin mu ba zan barta ba. Sai lokacin na juyo nace da ita wasu ko wasu kan ai kina ganin su dole ki barsu inda kika gansu din. Tace haka kika ce ko nace kwarai kuwa ai kema kina da ya da ar aiki sai ki saka su don ban saka naki ba. Na wuce abina na barta a tsaye ta fara haushin ta data saba don ba yau ne farkon ganin ta ba a gare ni nasan ta nasan halin ta tun a baya. Ina shiga daki sai ga Nasir da Jinior Nasir ke cewa dani little mum wai may wanan matar tazo yine a gidan nan yaushe ne kuma zata koma ta barmu please da zuwan ta tafara wa mutane fada a gida haka. ********* ********* ********* An sha ruwa kowa yana dakin shi gidan ya koma shiru ranan daga hindatu sai daddy ne a zaune a falon ga abinci dafa duka data dafa ya saka a gaban shi tun cibi daya daya diba ya hade shi da kyat bai sake iya kara na biyu ba. Don yaji da kaurin kuna dake tashi ga abincin ga ba magi ko mai naiji ba wai shi may azumi zai yi buda baki dashi. Sai faman surutu take zuba mai yana dai amsawa da kyat da eh a, a don biye mata kada ranta ya baci. Na fito daga dakina dauke da Haidar na samay su zaune a hakan na gayar dashi da shan ruwa ya amsa da fara,ar shi yanawa haidar wasa. Ban saukr yaron ba na juya abina na wuce zuwa kitchen don Nasir ne ya fito dani nai mashi abinda zaici ba zai iya cin wanan abincin ba. Miya na hada dole a cikin daren nan na zuba shinkafa a rice cooker na dafa masu shine yaran gaba daya sukaci suka kwanta niko na sha tea kawai. Washegari abinci ne tule an barta dashi a kitchen ta fara fada da masifa don taga tunkuyar da naiwa yaran abinci da shi. Ta kwasa fuu taje ta fadawa maigidan harda zancen helen da yadda mukayi a jiya din sai da ta fada mai komai. Ina jiran yai min magana sai banji yayi ba haka ta zubar da abinci mai yawa tunda ba almajiri ko wani mabukacin da zata iya ba anan. Yau da zata dora ina dakina tun safe barci nake kwasa abina can baba ya tayar dani da kuka nasan yunwa yake ji na fito indan dama mai cooker orth yasha ko zai muna shiru. Na samu ta fito daga kitchen tace yauwa dama naso fitowan ki yanzu. Don naji naga jiya kun hada kai da yara sunki cin abincin dana dafa yau dafa dukan taliya zan masu sai naga shegen da zaice baici kuma. Murmushi nayi mata kawai na shige abina tabiyoni kamar tana zargina har na dora abinda zanyi nagama na fita na dawo falo na zauna nakira Aisha ta kawo yaron. Sai da Aisha ta fito da yaron har sun zauna nace ta fifita mai yai sanyi a bashi sai naji tace amma wanan da kika damawa yaronki kin dai san na baban su ne ko idan ya kare fa ? Nace sai ya sawo wani dama ai dan shi ne yasha ba dan wani ba kuma tare suke sha da uban dama. Ai bashi kadai ya haifa ba ba zan yarda da son kai din nan ba kowa ma ai shi ya haife shi ba wanda ya tsinto a bola cikin su . Kin ga sai ki dama kowa yasha tunda ko banza gaki a kitchen ai ko abu mai sauki kankana. Rahama wuyan ki fa na lura tun jiya ya fara kauri to bari kiji bakin cikin ki da tashin hankalin ki za a katse maki jin dadin rayuwan ki anzo an gwamatse ku to sai dai ki mutu. Nace kai ji wani magana kuma nan wanan kuma ai sai Allah dayayini ya isa ya katse min jin dadi ba mutum banza ba irin ki. Ranta yai mugun baci tace nine banzan zan gwada maki wallahi ni hindatu ba banza bace a gidan nan sai na lahira yafiki jin dadi angaji an koma kauye inda akafi wayo dama kwashe kwashen Saade ne yakaimu ga haka itama din kin mata halin ku na yan adam kin rabata da mijin ta. Nace koke baki fi karfin hakan ba a gare ni nace dadin abin dai ina da asali ba cirani nazo yi ba garin mutane balle ace ba a san sunan kauyen mu ba. Aiko sai zagi ta uwa ta uba kamar ba azumi takeyi ba nace ni bani zagin ki don nasan hukuncin zagi ga Allah kuma ina ibadana ke kinyi kadan ki rusa min ibadana. Haka muka sha ruwa tana rusa muna fitina har magariba kowa ya shige muka barta a wurin. Tun dawowan shi gidan ya fahinci akwai matsala don maigadi ke cewa dashi tun waje oga bakuwar nan fa tana da masifa tana matsawa uwar dakin mu yau fitina suka wuni yi. Yace dashi sharf ita ma bakuwar matatace kamar yadda uwar dakin naka take matana don haka mind your self ya wuce shi fuu yana bashi hakkuri. Ran shi a bace yafito daga dakin shi bayan ya sauya kayan jikin shi zuwa na shan iska yana zama sai ga Jinior ya fito yana cewa daddy I can't eat this food. Ya dakawa yaron tsawa ya juya rai a bace ya fice daga falon sai gata tafito ta zauna a gefen shi bata dade da zama ba Nasir ya fito zai fita daga gidan uban ya hango shi. Yace ina zaka yanzu da daren nan soja yaron ya tsaya ya dan juyo yace zan fita na samo wani abu a waje ne don bama iya cin abincin nan gaskiya. Ya juya gareta yace hindatu wani irin abinci kika dafa ne yaran sun kasa ci tai wani irin shuumin dariya tace sun kasa ci ko makirci dai. Dafa dukan taliya ne nayi masu shine za, ace sun kasa ci ni duk iskancin yaro dashi da wanda ke turo shi ai ina iya shi wallahi. Kafin yai magana sai ga Ihisan ta fito tace mama nifa bana iya cin wanan abincin ya yi yaji da yawa ba haka little mum ke muna abinci ba ko Aisha. Yace you see, Ita kuma wanan din waya kulla mata makirci da tazo da wanan maganan bafa yau ba ina maki wanan complain din kan abinci akwai komai amma ai abinci ba test ba komai. Tace a hasale yadda na iya nakeyi bakuma wanda zai sani nayi abinda ban tashi yi ba ehe, Ina sawa yarona parmpers naji yana kirana na fito da yaton a hannu na a zatona fadan dazun ne zai yi magana a kan shi. Sai da nai mai barka da shan ruwa na samu wuri na zauna ina sauraren shi inji may zaice dani. Yace ga danki can daki yanzu ya fito zai fita na tambaye shi ina zai tafi wai zaije ya samo abinda zaici baya iya cin wanda aka dafa masu. Nace subbahanallahi Nasir a Abuja da daren nan ina zaka haka karami dakai yace gasu nan har jinior shiyazo ya fara samu na sai ihisan kuma sai ki sama masu abinda zasuci yanzu. Dama haka kike so yar iska shine plan din da kika shiryawa yaran tun ian nazo nai murmushi na sabala dana a kafada nace basu saba cin kazanta ba tun wurin uwar su yanzu ko ba yadda za, ayi su iya cin jagwalgwalen ki sai a koma kitchen a koyi girki don an wuce wurin. Ke ke ke hindatu may na fada maki tun farko bana son irin wanan jidalin kikace min bazakiyi ba yau kwanan ki nawa da zuwa da har zaki fara muna fitina haka tun jiya kike complain ke anyi maki abukaza. Yanzu ina dawowa aka tare ni tun waje kun wuni kuna jidali a gidan nan bayana wallahi duk ina kwasan ku ku koma kano gaba dayan ku ko. Na ce yafi nono fari a wurina ai can ma gida ne ba wani matsala ko can tace karya ne munafuka don ki min bakin ciki ko to ba inda zan tafi nazo ke nan zama daram. Nace gaki ga gidan ai na shige gurin yara suna kwance kowa a cikin damuwa na zauna bakin gado Nasir ya dago kai yana kallona yace little mum barka da shan ruwa nace kunci abinci sai sukai shiru nace tambayan ku nake kun yi shiru mana. Wallahi mum abincin ba dadi kuma yana wani wari wari nace yanzun may zakuci, da kuka zauna daki bakuyi magana ba ? Jinior yace naje gun daddy ya koro ni nace kaima da gangan yanzu dai ba wanan ba ku tashi muje kitchen muga may zamu dafa mai sauki. Da saurin su suka mike muka fito daga dakin nan muka wuce zuwa kitchen tare da yaran cikin sauki na hada masu abinci mai sauki sai gasu sun fito suna dariya harda ihisan na zubawa na kira Aisha ta dauki namu zuwa part din mu. Nan suka zauna wurin uban nasu suka zauna suna hira suna cin abinci cikin jin dadi da walwala har suka gama suka dan yi hira suka mike zuwa dakin su. Ni dai muna dakina da Aisha, da Atika sai helen dake biye damu nadauko ta ba dama na kore ta cikin mu kuma. Anan da yake barcin azumi ne har barci ya kwashe su ban tada su ba na barsu nan sai asuba muka falka don yin sahur na riga na tanadar masu abin buda baki na dauka nakaiwa yaran nasu sai dana tabbatar da sun tashi sun shiga brush na bar dakin nasu. Ban kwanta ba na shiga dan zirgazirga kafin ai kiran sallah na gama na zauna saida nai sallah na tayar da yaran suma sukayi suka fara shirin zuwa school. Barci na nayi sosai koda na tashi na samu Aisha ta gama duk wani abinda ya dace ayi shi. Wanka na fada ban damu da son zuwa gaida daddy ba don nasan baya gidan a lokacin don goma da wani abu a lokacin. Gidan tsit sai kace ba kowa a cikin sa kowa na dakin shi yana barcin azumi a lokacin wanka nayi na fito don sama ma yaran da basu azumi abinda zasu ci. Ina kitchen ina karainiya naji kamar motsi a falon ban tsaya juyowa ba naci gaba da abinda nakeyi a kitchen din. Can dai na sake jin motsi sai na dan leka hindatu ce naga tafito kamar daga backyard din mu da alaman rashin gaskiya a tare da ita. Na lafe don karta san ina kitchen din a lokacin da sauri ta shige dakin ta tana waige waigen bayan ta. A hankali naci gaba da aiki ba tare da na damu da abinda nagani a gare ta ba don zargi ta nakeyi kawai nagama na kwashe a kula ina fito daidai ta sake fito sai naga ta dan kadu tace ashe kin tashi nace da ita eh har ta fara tafiya take cewa tun dazun kike nan ne ? Nace yanzu na fito in samawa yaran nan abinda zasu dan ci tace oho yayi sai ta juya ta koma dakin ta nikan na wuce zuwa dakina . Ance zance baizo maka sai kana tsaka da sallah shedan ya dinga rudin ka da zantutuka barkatai a zuciyar ka. Irin hakane yazo min kan na duba backyard dinan naga may matar nan take boye min Aisha nasawa kira tashigo nace ta matso kusa da inda nake zaune saman sallayana. Cikin rada nai mata bayanin abinda nake son tai min tace ba matsala ta fice daga dakin. Takai min ti ashirin sai gata ta dawo dakin take cewa dani naga ni anty a razane nace wai da gaske tace Allah ko. Nan muka bar zancen har zuwa dare nasan Aisha zata iya aiwatar da komai yadda ya dace. Mun fito muka dora girkin abinda za ai buda baki a ranan tunda mu zamuyi duty . Yi wana dora wancan sauke wanan har muka kamala komai da za aci na jera shi inda muke zama ai buda baki. Tunda nake aikin nake ganin tafita takoma haka taitayi nace da Aisha ta saka ido idan naje sallah akan matar nan . Bayan kiran sallah saiga yaran sun fito sun taru a falo nan mukai buda baki na tura yarta tace tazo tasha ruwa. Sai gata tafito dakin tana ganin yadda muka taru ana raha kowa na farin ciki yana shan fruit da drinks din dana hada a wurin. Sai ta bata rai ta juya zata wuce bata zauna ba nace bissimillah mana ga abin buda baki nan an aje tace barshi kawai har anjima ta juya ta koma dakin ta. Mun gama muka shiga sallah amma Atika na gurun ta kasa ta tsare sai gata tafito tana tambayan Atika ke baki zuwa sallah ne kowa ya tafi tace sai anty Aisha tafito zan shiga taso yiwa yarinyar jan ido sai taga bazata gusa ba nan da can dole ta barta an bata mata plain din ta. Sai bayan sallah ya shigo gidan ina daki Atika tazo ta kirani wai nazo daddy ya dawo ban dade ba na fito nai mashi sannu da zuwa ya karba ya shige dakin shi don ya sauya kayan jikin shi zuwa masu sauki. Ruwa na hada mai yai wanka ya fito falo ina daki tare da yaran ban fito wurin su ba don naji muryan su a falon tare. Ihisan ce ta shigo take fada min daddy yana kirana falo na karaso ina kara gaidashi da shan ruwa tana zaune gaf dashi tana tsiya ruwan juice din abarba a cup. Ya dago ya kalle ni lokacin da nake zama saman kujera yace kin shige daki kin zauna da yara bayan kin san cewa nafito kuma . Nace na dauka ba wani abinda kake bukata don na aje ma komai da zaka bukata wurin. Yace baki zoba waye zai zuba min abincin nacu sai na dan kalli inda take zaune ina nufin bagata ba a wurin ta zuba mai. Nadai sauko na zuba mai komai yadda ya dace na fara kwashe sauran zan shige dasu kitchen tace ina kuma zaki dasu ni ban ci ba ? Nace ba tare na zuba maku dashi ba na mu yana can sama table ajiye nai saurin kwashewa na bar wurin da kayan zuwa kitchen tabishi da kallo ko zaiyi magana. Na riga da na shirya amsan bata a lokacin koda zaiyi magana kan hakan sai baiyi ba din har nakai na aje. Na fito naso nq shige sai naji a jikina ni daddy yake kallo sai dai naki yarda na dago na kalle su. Yace Rahama daidai na dan juya na amsa naam daddy yace yaran ki sun ci abinci ko ? Sunci tun dazun daddy yanzu fruits salad suke sha kafin su kwanta yace yayi kyau. Na fahinci daddy yana da wata manufa akaina ranan don haka naki bada fuska yadda zai samay ni da sauki hakana. Yana gamawa na fara kwashe kayan hindatu dake zaune ta cika fan don ko magana batayi ranta ya baci dani. Ban koma wurin su ba na shige daki abina na samu yaran sun watse sai Aisha ke gyara wurin da suka bata. Wanka nayi na shirya na haye gadona na mimike abina ina waya da zarah sai dana gama Aisha ke cewa dani anty na dauko fa nace abune aciki tace wallahi helen nasa ta ciro yana can mun boye shi a wani gyrin mun mai fitsari a razane nace Aisha kina da hankali idan wani ayan Allah ne fa ? Tace a, a wani abune kamar tsoka da gashi an sosoka mai allura a jikin shi kamar mutum mutumi. Nace wa iyazu billahi injin kun jefar tace helen ta fita dashi can bayan gida sai da muka wargaza shi gaba daya muka fitar dashi takardan dake ciki muka boye kawai. Muna nan muna magana akan zancen daddy ya shigo dakin sai Aisha ta gaidashi tafice daga dakin ta bar mu a ciki nida shi. Kallona yake ni kuma naki dago kai mu hada idanuwan mu ni dashi yace humm kawai tare da karasowa inda nake. Rahama wai har yanzu fushin ne kike baki daina ba ko may ? Nace fushi ni bani fushi da kowa ai da ina fushi aida ba haka ba ba yanzu nafito wurinka ba can fallo inda kuke zama daine banayi har a soka min magana tunda ni banje na takurawa mutum ba. Yace naso ace tun kan hindatu tazo ta fahinci halin da muke ciki kin daina wanan fushin haka na don Allah ki sake jikin ki ki bar wanan fushin hakana. Nace na huce indai nice yace koke fa in ba haka ba ko yaran ki abin zai iya shafa ai. Ya juya yana fadin ina jiran ki a dakina ban tanka shi ba ya fice daga dakin nabishi da harara kawai har ya fice. Har sha daya da wani abu ban je gun shi ba sai ga wayan shi ya shigo min na dauka lokacin har na soma barci. Yace wai kin manta da nine anan komay may ke damun ki ne haka wai Rahama may kike son bullowa dashi ne a tsakanin mu ? Ina ce mun riga mun yi magana kin ce komai ya wuce yaya kike son nayi da raina ne please. Ban yi magana ba sai mikewa da nayi na gyara shiri na fice daga dakin inda na samu yana kwance ban bata lokaci ba na kwanta nima. Ya sauke ajiyan zuciya tare da birginowa inda nake a kwance yakai hannun shi a jikina. Abin mamaki ranan duk yadda daddy yaso yakai a gare ni sai ya kasa duk kokarin shi a kaina abin yaki sai ya koma tankar mace a guna. Ya koma yana sauke nunfashi gefe daya tare da wani irin tartso zufa a jikin shi ni dai ina kwance lamo nima mamakin hakan nakeyi yau a gare mu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , , 79 Wanan matsalan da ya faru tsakani na da daddy sai ban dauke shi komai ba a raina ko banza ma acikin watan mai arbarka muke watan kara kusantar bawa ga ubangijin shi. Ban sa abin a raina ba don ban dauke shi wani babban matsala bane a wurina sai na samu daman yin ibaduna yadda nake so. Yau shine karo na uku da abu daya ke ta maimaita kan shi sai ya kusan kaiwa gare ni sai wasa ya canza sallo aiki. A bu daya dake ci min rai shine rashin walwalan da naga daddy baya ciki a yan kwanakin nan. Don zai zauna yayi tagumi da gani akwai abinda yake tunane a ranshi tun abin na damuna har na fitar da damun a raina tunda bai fada min komai ba. Na fito falo daga dakina don in danyi hira da yaran dake gida yau weekend ba su zuwa school a gida zamu wuni tare dasu don haka nakan yi na zauna da su na wani dan lokaci muna hira a tsakanin mu. Hiran mu muke kwasa ga tv na aikin shi sai faman dariya muke a tsakanin mu banji sallaman shi ba sai ganin shi mukayi a tsakiyan falon ya shigo gidan. Nan yaran har ni muka shiga yi mashi sannu da zuwa ya samu daya daga cikin kujerun falon ya zauna akai tare da dafe goshin shi da hannuwan shi. Sai duk muka bishi da kallo Nasir ne ya fara mikewa zai shige sai daddy ya bude idanuwan shi da sukai ja yace No zauna abinka mana kuyi hiran ku. Yaron ya koma ya zauna inda ya tashi sauran ma sai suka zauna baiyi magana duk zaman da yayi sai lumshe idanuwan shi da yayi. Nace dashi daddy yau lafiya kake kuwa naga ka dawo wanan lokacin ya dan bude idon shi ya sauke su gare ni yace inaga dai azumi ne yasa min jin ciwon kai yau don ni ban faye saurin yin ciwo ba haka. Sannu muka fara yi mashi yana amsawa can ya dan dago yace Nasir ina Ihisan take banganta ba nan cikin ku. Kafin Nasir yai magana sai jinior yace da uban tunda mum din ta tazo ai ta daina zama tare damu ko school muka tafi sai ta dinga muna abinda taga dama yanzu ma saboda ita late mukeyi zuwa schoool da safe. Daddy yace may yasa baku fada min ba tunda ta fara hakan yace kira min ita dakin nasu sai yaron ya mike tafi gun kiran ta. Tare da uwarta suka fito falon inda uwar kecewa dashi kadawo ashe yace eh kawai ya juya kan ihisan yana cewa may yasa kowa na falo a na hira kika shige daki ke ? Yanzu nake jin duk kwanakin nan bakya fitowa da wuri sai kin sa yan uwan ki yin late a school daga yau kada na sake jin haka daga gareki. Sai uwar take cewa wata sabuwa yau kuma Ihisan ce akaiwa kulli bani ba babu dai yadda zakuyi damu gani nan bari nan wallahi. Yace ke dakata wani irin magana ne wanan kuma haka sokike abarta tana cutawa yan uwan ta kullun ta sa su makara ko may aida ba haka takeyi a baya tare suke fitowa su wuce. Inda nake tajuyo tace yanzu Rahama baki ji kunyan fadin wanan maganan ba wa karamar yarinya zakiwa hadi wurin ubanta. Murmushi nayi nace da ita cikin dariya Allah sarki Rahama mai dadin suna yanzu kuma nice na fada mai don ina bakin ciki da Ihisan ko may ? In ba bakin cikin ba may zai sa ki mata hadi gun ubanta hira banda kilibibi may kike koyawa yaran suyi in ba gulma ba. Wai hindatu may yasa baki da tunane ne ina ruwan Rahama a cikin wanan zancen yanzu da ita ake zuwa school din ko may wai ? Ta juya gun Nasir tace kune kilababbun da kuke cewa haka ko zaku hanata zama da uwarta ne ko may yan bakin ciki da sukai gadon mugun abu a gurin uwar su. O my god wai may nene haka kike yi hindatu na fa fada maki bana sin irin haka so kike karnaiwa ihisan fada ko may idan tayi ba daidai ba ? Wanan cin amanan nata da kukaitayi don bana nan yanzu nazo babu wanda zai saka min ya a gaba da mugun manufa in yarda don da baifi da ba Ihisan dai ba yadda zakuyi da ita don ta zamay maku kashin bakin tunkuya ta Allah bata ku ba ta juya ta wuce fuu zuwa ciki. Yarinyar ta samu wuri ta zauna a takure yayin da falin yai tsit bayan wucewan ta ciki sai Nasir ne yace dani mum yau ki muna wanan miyar bindin saniyar da kafan shi mana please ? Nace Nasir an barka a tasha sai dai ka fadawa maman ihisan tai maku don yau itace da girki sai yaran suka bata rai yace ni yau shi nake son ci wallahi. Nace bari banda gobe sai nai maka duk abinda kake so sai uban yace saboda may baza ki masu ba tunda shi suke so sai nai shiru nasan yin zai iya jawo man matsala gun matar shi. Yaran suka ce daddy yace ki muna shi inji jinior nace kaida baka azumi ina ruwan ka da abin shan ruwa na masu azumi ne kawai wanan. Aisha tashi ki ciro min ki dan saka a ruwa ya sake kafin na taso kin san wuyan dahuwa ne dashi. Ihisan ce ta mike zuwa dakin su nasan ko ta fadawa uwar ne sai gani nayi ta fito ta shiga kitchen din a lokaci sha daya na rana lokacin yin abin buda baki baiyi ba. Amma haka ra babake kitchen sin wai tana aiki nikan ganin ta shiga banyi yun kurin tashi zuwa abinda zanyi ba din. Ba ita ta gama ba sai bayan uku da wani abu na rana na shiga na dora masu girkin sai gata tafito daga daki tana shiga naji tace may aka dorawa wuta haka kuma ? Bayan wanan uban abincin dana dafa sai an kara dora wani kuma again wanan ai ya zama barna ko ? Nace abinda diyan masu gida ke so shine zan dafa masu tace haka za a kare wurin yiwa diyan kishiya bauta babu gode balle na gode. Gyara dai maganan ki ko kin manta nima ina da masu ci a ciki ne da zakice hakan. A dai bari su girma kamar kowa mu gani ba wanan ya ta tsitsai din ba da ba a san da su ba a gidan. Nace a wwurin ki ne yake amma agun wanda ya yanka masu rago yasan dasu kin san ance mai karami watarana shi keda babba insha Allahu. Magana take so yai nisa na fahince ta sai na sharer ta naci gaba da aikina sai naga yaa dace na hada tuwon farar shinkafa aci dashi ba bata lokaci na dora na fara aikin shi sai dai ba yawa sosai. Da muka sha ruwa shi muka ci muka bar faten doyan da tai muna wanda har ya yi karfi ko don yin shi da akai da wuri. Koda daddy ya shigo ya samu yaran a falo suna cin abincin su a zaton shi shi aka girka a gidan saida ya gama ya fito ya zauna cin abinci ya na budewa faten ya tare shi a fuskan shi take ranshi ya baci. Da karfi ya kwala mata kira don kwance take tun shan ruwan ta jikin ta yai mata nauyi ta mike ta fito kai babu dan kwali ba wani kwalliyan da tayi. Tans zuwa yace may ye wanan saboda Allah yanzu hindu abinda zanci ke nan a gida na a matsayina na wanda yai azumi kko may ? Tace may kuma yayi don Allah kai mutum baima gwanita ka gode mai yace may ye abin gwaninta anan a faten doya ke kullun ba zaki iya yiwa mutane abincin kwarai ba don kiuya kawai kada ki motsa jikin ki komay ya kawo haka. Ni gaskiya ba zan lamunci hakan ba wanan ai cutawa ne gare mu may aka rasa a gidan nan da baza a girka muna abincin kwarai ba ? Ni shi na iya kuma shi nayi ba zan wahal da kaina ba don a yabe ni ko wani abu mutum na fama da azumi yai aiki ya gaji a kawo mai wani korafi can kuma ? Ya ce yayi kyau za a ko jimu a gidan nan dake idan wanan abincin zaki dinga girka muna tace iin hakane sai dai naiwa mama waya akawo min wata yar aikin don ba zan iya wanan wahakan ba gaskiya. Yace yanzu dabara ya rage gareki ai idan tazo sai ta girka iya bakin ki don ba zan auro mace ba tace bata iya min girkin da zanci. Ya kwalawa jinior kira yace kira min mummy ku a dakin ta yaron yazo kirana ina ba haidar nono na ce gani tafe yaron bai gama shan nono ba na mikawa Atika shi na fita. A zaune na samay su yadda na ga zaman su yau yasa nasan akwai matsala ke nan na karso ina mai barka da shan ruwa ya karba min a dakile yace ina abincin da naga kinyi ? Na kai idona kan faten dake gaban shi fari nace nabawa yaran yace babu ko kadan a bani nai dan shiru can nace akwai shi yace a bani don Allah ? Na juya na koma daki na dauko mai cikin wanda za suyi sahur dashi na kawo mai har miyan da komai. Na aje ban tsaya ba zan wuce tace indai kili bibi abin yi ne sai mu zuba mu gani dama sherin da kike son kulla min ke na yasa kikai wani girki. Ban iya sheri ba ni da bakin maigidan naiwa yaran girki ki wacce ta fada baki bata fada maki daidai bane dazun yadda akayi. Tace wakike nufin ta fada min nace wacce kika hana karban abinci ai tazo ta karba taci duk da kin hanata ci din. Ya isa haka please yana kai loma abincin a bakin shi daga haka bai kara cewa komai ba yaci gaba da cin abincin shi na juya zan wuce yace jinan. Sai na juyo yace ku saurare ni daga yau girki a hade za, a dinga yin shi ban yarda a kara raba tunkuya ba a gidan nan ba. A zato ita zata fara korafin saboda may amma sai naji tace ya dai fi don bazan iya wahakan ba kaitan banza abincin ba haka. Nace baida matsala ta fadi haka ni may zance na bada kaina duk da nasan mune zamu cuto ba zatai komai ba ita na sani. Tun wanan rana muke komai a gidan tana daki kwance da yar ta sai in an sha ruwa sune farkon diba ni dai bance komai ba a kan hakan da yai muna din. ********* ********* ********* Nidai ranan ina barci bayan na falkane Aishs ke cewa dani wai sun fita shida hindatu din. Ban kawo komai ba sai da suka dawone naga anata shigowa da kaya irin na raba ma dangi din nan da karshen azumi. Aikina nake banbi ta kansu ba sai da dare ne ya kiramu nazo na zauna yake cewa kayan da za, a bawa mutane na sallah ne sai kiyu list din wa yanda kike sin abawa a part din ki. Nace ayya angode don na riga da na saya ko har an kai masu ko ina fadan haka namike na bar wurin ban tsaya ba yabi bayana da kallo kawai. Na koma daki ina mamakin hali irin na daddy ni may ya dauke nine wai zuwan hindatu fitan su karo na uku ke nan a gidan tare. Na farko wai sun fita zuwa gidan wani abokin shi a bakin matar mutumin nake jin labari sai na biyu wai sunje sayaya ne a wani plaza na gida. Sai kuma yau da sukai min wanan rainin wayon babu ko shawara haka kawai don an mayar dani yar tallakawa wai nai list din wanda za aiwa alheri a part dina don muna tallakawa ko may ? Ban fita ba duk da ni keda girki har ya gama abinda yake ya kwanta sai washe gari ina zaune ina shafa mai ya shigo dakin. Ban juyo ba nai mai ina kwana yace wai Rahama may yasa baki son a zauna lafiya ne ke yanzu yadda kikai min jiya kin kyauta ke nan. Ni dai banyi magana ba sai shiri na nakeyi kawai yace badake nake magana ba ne kin kyale ni ? Nace kaje ka karawa wacce ta sayo din takaiwa yan uwan ta can ni duk da tallakace bani daukan wullakanci kishiya idan ta mai da kai yadda take so ni ba zata mai dani ba don ba zaman ta nakeyi ba anan balle tace zata zabawa yan uwana abinda taga ya dace dasu watau gana kauye ko ? To kubar abunku nagode Allah ya kara arziki da budi gaba na juya zuwa wardrobe na fara fitar da kayan da zan sa ajikina. Yace yanzu nagane nufin ki Rahama watau don muje da hindatu ta tayani zaba shine bakin cikin ki ko ? Na juyo nace bakin ciki bakin ciki akan may fa akan ka fita da matarka ko may ai ba yau ka fara fita da ita ba ko a kano ya damay ni sai yau zan damu ko may. Ni dai nasan ban wa kishiya shishigi ba balle ni ai mina ga bara kudi ka bamu kace kowa ya saiwa yan uwan shi kayan sallah sai yanzu ne ita tasan hanyar yaudara ko may ? Sai yai shiru ba abinda yake tunane sai yasan haka akayi da yai magana nakawo mai wanan shawaran akan kowa ya saiwa nashi da kan shi . Yanzu ko itace ta bada wanan shawaran kan a saye a rabawa mutane kuma gaskiya wanda tace wai namu din baikai wanda yaga ta zaba ba a bangaren ta. Yai magana tace kallan ya burgeta ne sosai kuma zai karbi yan uwan ta sosai don suna son kalan. Yace yanzu dai kina nufin bazaki karba ba nace ba nufi bama bana karba na yafe har ga Allah aba wasu. Yace to shike nan zaki gane kin min wullakanci ga hakan nace aina saba ba yau bane farau din hakan gareni indai wulakancin ka ne. Wani abin ance idan bakai magana ba sai ya zama maka ciwo a zuciyan ka don maganan na da amfani saboda idan kai sa,a za a daina. A bangare na ma maganan yai min rana don ashe wai gajiya sukayi a ranan da harda kayan sallah mu dana yara zasu sayo sai suka gaji suka dawo gida washe gari zasu koma su sayo din. Yin maganan da nayi ne yasa shi dogon nazari duk da ran shi ya baci a yadda nai mai da farko amma daga baya dayai tunane sai yaga rashin dace wan hakan. Don inda gaskiya ne ai kamata yayi ya dauke mu mutafi tare a sayo komai dani ba su ware ni ba yadda sukai min din. Ya kuma tuna a bara yadda akayi saye kowa kudin ta ya bata ta sayo ita da yaran ta da nata. Washe gari koda tai kai zancen zuwa saye sai cewa yayi da ita ya fasa zaiba wa kowa kudin shi ya saya wanda yake so da yaran shi yadda ya saba yi muna. Ranta ya baci tace wanan ba shawaran ka bane na sani kodan jiya matar ja tai fushi taki karban kayan yasa zaka canza shawara a yadda muka tsara da farko. Yace in ma haka din je hakan ne don ba haka na saba yi ba da farko ai tun farko sai da na so kin wanan shawaran naki amma kika kawo min kabbali da ba, adi don haka abar wanan zancen zan bawa kowa kudi yadda na saba ne. Amma idan kai muna haka mu aka kwara ni da zulfa tunda sun fi mu yara ai yace au shine hikimar ki ashe kikai wanan shawaran bafon Allah ba ashe kikayi. Rahama na da gaskiya ke nan ta fahinci abinda yasa kikai masu hakan ke nan ashe tace da yake ta iya yaudara ba dama ai haka yasa ta hada dayin majuju don ta haifi diyan ta samu garabasa . Yace ke wa ta hanaki yin hakan ai kin rigata shiga gidan tace Allah ne bai kawo ba kaima ka sani ai. Yace ashe kin san Allah may yi itama shi din ne ya bata a lokacin da kowa bai zata ba din don haka ban son dogon zance kan maganan na riga na fada maki shawara na don tun farko haka na saba yi maku ai. Ni dai ban san sanda yaiwa yan uwana da iyayye aike ba sai ji nake suna bugo waya suna godiya amma fir naki tambayan shi abinda ya aika masu dashi. Yaje kano gun su Anty kwanan shi goma a can gun su anty ya gama abinda ya kai shi ya dawo Abuja gurin mu da aikin shi. Ranan ya dawo ne ya ban kudina dana yara na har dasu Aisha da Atika da helen dake wurina sai da suka samu, Haka yasa na fahinci kowan mu haka yai mata sai da zan tashi ne ya sake miko min wasu kudin yace wanan na su Nasir ne da jinior don uwar su tace na kawo maki tunda a nan suke gun ki. Mamaki nayi sosai yadda anty ta sauko haka ba kamar ya watan nin da suka wuce ba ashe yaran ne kan yawa fada mata komai a waya shine yasa ta kara sakewa a ranta ta dai fahinci ba wani abu a zuciya na kan ta zugin mutane ne kawai yasa ta rudani dama amma ita har yau ba zata iya cewa ga abinda nai mata ba. Washe gari muka shiga kasuwa da yaran nai masu sayayya sosai yadda ya dace da kowan mu har haidar sai da na dan sayo mai tunda yana dasu dama aje. Naso muje kano muyi sallah a can har daddy ya amin ce sai hidimar tafiya muke yi gaba dayan mu don baifi kwana uku ba ko hudu ai sallah. Komai munyi na tafiya amma ranan yana dawowa sai yazo min da zancen ba tafiya mu kano sai dai zai tafi da Nasir da Jinior suyi sallah a can. Banji dafi ba babu yadda zanyi dole muka hakkura da batun tafiyan na dai san dole akwai matsala ta wani wuri akan haka. Cake na hada lafiyayye da su donut da sauran snacks da zasu tafi dashi nai kuma saa sunyi dadi sosai don sai kamshin vanilla flavor sukeyi na saka a fararen robobi naba yaran sukai wa anty da Alhajin daddy da Abban anty na sallah. Washegari zasu tafi ya kira mu yake sheda muna Sani zai kawo muna naman sallah da sauran abubuwan bukata da zamu bukata na hidimar sallah din ya kuma kawo kudi masu yawa yaba kowan mu yai muna sallama suka tafi. Da yamma sai ga nama mai yawa Sani yazo muna dashi zakace ma Saniya ce suku tum aka yan ka muna an gyara shi tun can iyakar mu dai aikin shi kawai. Muna shirin fara aiki sai ga hindatu ta fito tana wani ya tsunar fuska tace ke Rahama a raba naman nan biyu a bani nawa nan ? Nasan tsiya take ji don haka nace kamar ya a raba biyu adai kasa a cirewa kowa ku dauki kasan ku tunda ba mu kadai ne da hakkin shi ba. Wasa wasa muka fara rikici kan hakan ta dauki waya ta kira maigidan cikin masifa lokacin yana falo can ma ana wani rikicin tsakanin anty da zulfa kan abin sallah din. Sai da ya gama sauraren ta yace kisa wayan nan a handsfree muyi maga taji, ta dauka ya goyi bayan ta ne sai tace a fusace yace ki saurare shi kiji abinda zai fada nace ai gani tsaye ina jin ku. Yace Hindatu ta ansa ya kira nawa sunan nima na karba yace a kasa abakowa dake gidan har maigadi tunda abin naku tsiya ne, yace ai gaskiya ta fada abinda aka saya don anfanin bukin salla zai kawo fitina kuma wai may ke damun kan kune haka please da wani kuke son naji ne wai haka ? Tace haka zakace yace may kike son nace nama kuka rasa a gidan ko may da wanan zai kawo maku fitina haka don baku da tunane na gane abin naku hadin bakine don kawai kuci min mutunci ku hanani kwanciyan hankali. Ta juya a hasale tana fadin keda keda tsiyar nama sau ki hada da namu duk ku cinye ina ruwan dan baka saba ba da ganin hakan. Nace ni dake yanzu ai sai a banbanta wanda ya nuna zalamar shi ba ki dai kwaruwan mu kan. Duk da ta wuce tsaye nayi aka kasa shi daidai sai kason mu ni da ita yafi na sauran yawa nace Aisha ta kai mata nata. Can ta koroto da naman tace muje mu kara mu da ya zamawa bakon gani a gare mu tadawo min dashi nace ta saka a freeze ta aje mata. Nan suka shiga gyaran shirgin naman da yake yaran na da hazaka zuwa goman dare har sun gama komai suka saka a wani katon roba mai marfi suka kawo dakina. Da dare sai ga anty ta bugo min waya tana min godiya wai taga yara sun zo da abin arziki nai murmushi kamar tana gabana nace haba dai anty ai wanan ba komai bane ni ina zan iya abinda akai min. Tace to adai ta hakkuri don kin san zaman hindu wurin ku ba alheri bane da biyu ta zabi zama can din yaran nan sun fada min irin zaman da kuke acan din kina ma da kokari Rama in nice ai da na bar mata gidan na dawo inda nafi karfi. Nace a raina yanzu kuma haka ke son dawowa tsakanin mu bayan ta riga taba da kafa an muna dariya ta jima tana min hiran rikicin su da Zulfa tace tana ganin hadin baki sukayi akan hakan. Nace anty ni dai nasan ban na shiga hakkin kowa shiga nawa ne dai ba zan dauka ba tace to a kara hakkuri mukai sallama ta kashe wayan ta bar ni da mamakin ta. Washe garin sallah koda goma yayi duk mun gama komai na abincin da zamuci tunda ba wasu zamu aikawa ba sai makwabtan mu da ba musulmai ba na sawa abinci da soyayyen nama da abin sha na aika masu dashi. Natura Aisha ta fada mata an gama abinci yana saman dining idan sun tashi ci bata ki ba ta turo yar ta ta diban mata itama ihisan din nan falo ta zauna taci nata. Ranan da daddy zai dawo sai gashi yazo mata da wata yar aiki sai dai bai dawo da yaran ba zasu tsaya can suyi hutu a wurin uwar su ne. Dawowan daddy babu abin da ya canza a tsakanin don har yanzu baya iya aiwatar da komai idan muna tare dashi sai dai idan da sauran matan shi yake zai iya gudanar da komai normal yadda ya saba. Tun abin baya damun mu har ya fara yi min magana sai gashi wai laifina zai gani kan haka wai ni ban ma damu da halin da muke ciki ba ni dashi din. Na idar da sallah asuba na zauna a wurin na fara tunane may ke kawo muna wanan matsalar ne haka tsakani na dashi don gashi har mun fara samun matsalan zama kan hakan dashi. Na kira Zarah abokiyar shawara na nake fada mata halin da muke ciki ban ko kai karshen magana na ba ta katse ni da fadi cikin tashin hankali Rahama kina ko da hankali kuwa ? Kina cikin wanan babban matsalan haka kika zauna tsawon lokaci mai tsawo haka abuna damun ki. Nace Zarah ni may kike so nayi ne wai tace kin ko san abinda ke damun ku daga ke harshi bafa karamin abu bane wanan don asiri ne da akeyi tsakanin na miji da mace da hausawa ke kira da dan baka. Ba zai taba samun natsuwa dake ba sai idan wanan asirin ya bar aiki a tsakanin ku tunda da sunan ku akayi shi amma dai anyi shuuman mata anan don yanzu ba zamu cewa ga wacce tai maki wanan abin ba tunda kina da kishiyoyi da yawa. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A TAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 80 Tun bayan waya na da Zarah sai hankalina ya fara tashi don ba karamin tsoro kalamin ta ya bani ba. Ni lafiyana shine yafi min komai a rayuwa na in dai zasu barni da lafiya ina iya bar masu mijin su a zauna lafiya. Amma ta ina zan fara wana san yai muna wanan shamakin a tsakanin mu ni dashi don duk kishiya kishiya ce dai. Amma wa zan zarga a wanan matsalan shin hindatu dake nan zaune tare da mune ko kuwa wa yanda ke gida ne sukai min hakan wai ? Nan dai na zauna ina ta faman tunane wanda har na gama ban iya gane komai va daga ciki abinda dai na yake da ga karshe shine zan dukuma nafi da kaimi wurin kai kuka na ga Allah dayai min tsari akan duk mai bina da wani mugun manufa. May na tare masu da har yai zafi haka sukai muna wanan mugun asirin da sai jahili zai iya shi. Sannu a hankali na fara rama a tsaye gashi bayan zarah aminiyata ban iya fadawa kowa wanan zancen don da kunya aji shi a bakina haka. Muna cikin wanan halin ne ranan sai ga massage ya shigo a email dina asibitin da nai bautan kasa suna neman mu muzo interview wurin su. Murna farin ciki duk ya kamani a lokaci daya daddy kawai nake jira ya dawo na fada mai naji may zai ce akan zancen. Koda ya dawo nice da girki ranan don haka na tsara kwalliya na dana bata lokaci wurin yin shi ga lafiyayyen abincin dana girka don shi a ranan. Bai shigo ba sai yamma lis ya dawo gidan ina dakina ina bawa yarona nono naji muryan shi Atika na mikawa yaton bai koshi ba ya dan sa kuka nace fice dashi zuwa dakin ku don Allah, Tana fitowa dashi uban yaji kukan shi yace kai Atika ya akayi ne yake kuka kawo shi nan ta mikawa uban yoron ta nacewa wai bai koshi da nono bane shine yake kuka. Daddy yace ita nonon nata na sayarwa ne ko may zatayi dashi da bazata bashi ba ya sha ya koshi da kyau. Daga kofa ina fitowa nace cikin wani murya najan ra, ayi nace wallahi daddy ya faye tsotso shi bai koshi da nono. Ya dago yana kallo na na tabbatar shigan tai mashi kyau don ni kaina na sani saboda kayan ya fitar min da kurciyana a fili. Yai murmushi yace nawa za, a sayar muna a bashi ya sha ya koshi yadda yake so na sake cewa daddy don Allah barshi yanzu Aisha zata kara mai da abincin shi yasha. Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature. Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi. Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace. Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai. Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi. Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ? In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba. Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon. Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi. Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ? Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi. Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ? Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ? Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho. Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace. Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi. Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu. Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe. Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service. Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku. Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani. Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi. Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai. Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din. Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake. Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin. Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba. Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi. Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure. Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon. Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun. Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na. Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai. Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai. Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace . Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu. Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ? Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan. Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ? Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu. Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin. Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa. Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai. Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka. Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita. Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi. Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi. Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba. Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani. Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin. Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan. Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan. To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan. Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai. Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani. Don ni da farko banyi zaton wanan matsalar babba ne haka ba sai yanzu dana fahinci abin kamar ba mai karewa bane muna tunda yana iya amfani da yan uwa na ashe nice dai muke da wanan matsala din tsakanin mu. Haka naci kuka na da tunanena nafito na koma na kwanta ban farka ba ga dan barcin dana samu sai bakwai na safe ashe hindatu nace ta kasa ta tsare taga fitowana daga dakin don haka take min wanan dabian kullun nake da girki. Haka na daure na ci gaba da alamura na kamar kullun sai dai daddy yazo karyawa da safe sai naga ya kura min ido ban yarda mun hada ido dashi ba sai naji yace Rahama na amsa a sanyaye ban dago na kalle shi ba. Naci gaba da abinda nakeyi yai shiru yana nazari na nazo wucewa ya riko hannuwa na abinda yasa ni dagowa na kalleshi ke nan yace dani. Sai naga idon ki kamar kin yi kuka a daren jiya ko? Ban tanka mashi ba sai kokarin wucewa da nake son ya sake ni nayi kawai nake da hannuna dake rike da nashi din. Tambaya na ya sake yi na sunkuyar da kai na kasa wani irin abu nakeji a zuciyana kuka kawai nake da bukatan yi a lokacin ko zanji sanyi. Ya sake ni ban tsaya ba na shige dakina na rufo yakai minti talatin sai gashi dakin ya shigo yazo ya tsaya kaina ya dan jima a tsaye ba tare da yai magana ba. Sai zuwa can yace nasan kina cutuwa Rahama nima abin ya fara fin karfina don ni kadai nasan halin da nake ciki a zuciyana. Nace ni bashi ke damuna ba gida nake son zuwa kawai na kwana biyu ko zan huta sai naji yai murmushi yace cikin wata murya Rahama kina nufin kije gida ki fada masu matsalar da muke ciki ko may ? Muryan shi ya ban matukat tausayi a yadda yai magana yace kina ganin idan sunji wanan matsalar da muke ciki zasu barki ki zauna dani ne haka Rahama ? Ban sake magana ba sai kukan da nakeyi shima din bai min magana ba yana dai tsaye a wurin kawai can naji ya sa kai ya fice daga dakin a gurin Aisha nake jin wai daddy ya fita. Mikewa nayi na shiga bandaki nai wanka tare da dauro alwala na sallah raka,a biyu nakai kuka na ga Allah. Nan na zauna naci gaba da lazumi da jero adduoi sai tunanen abubuwa da dama dayazo min a raina na zamantakewa na a gidan daddy wanda a kullun da irin matsalar da nake fuskan ta a gidan. Nake tunane shin haka sauran mata masu kishiya suke zaune a gidanjesu dama ake ganin kamar wani dadi mace ke ji idan anga tafito tana tunkaho a waje. Ni kan gaskiya da muguwar rawa gwanma kin tashi da a illanta min rayuwana kan kishi gara kowa ya kama gaban shi a huta hakana. Don in anci gaba da haka watarana inaji ina gani akan rayuwana za, a koma wama ya sani ko ana hakan nice dai ban gane hakan gare ni. Da kyat na iya tashi na shirya na fito don duba girkin da Aisha ta riga ta dora muna ba laifi na samu taimin shi yadda nake so sai dan abinda baza, a rasa ba kawai nayi. *** *** *** Tun bayan fitan shi daga gidan abin duniya ya damu zuciyar shi ya rasa wa zai fadawa wanan magana sai bashir ya fado mashi a rai don ya fishi sanin irin matsalolin hakan nan. Sun gaisa sunyi komai yace Bashir wallahi akwai matsala bashir din yace subbahanallahi matsala kuma Gentle yace wallahi babba kuwa. Nan dai yake koro mai komai har yagama yi mai bayani Bashir din ya nisa yace lalai babban matsala ne wanan. Yace sai dai gaskiya ko ka yarda ko kada ka yarda zan fada ma gaskiya wanan abin sihiri ne wanda mata keyi a tsakanin su. Sai dai banyi tsanmanin yanzu wayewar kai din nan ashe an saura yin irin shi abune mai wuyan sha, ani sosai don dole sai ka nemi makarun shi. Yace a ina zan nema Bashir kafa san ni ba wai na iya irin abubuwan nan bane a rayuwana asalima naki jinin alamari da sihiri shiyasa ma ban yarda da shi ba ni. Yace to shike nan tunda baka yarda ba Allah ya sauwaka ko yace kamar ya ban yarda ba ai magana nake fada ma yanzu kan ai dole na yarda tunda ya faru dani. Sunyi magana yace idan ta shigo kano akwai inda zasu tafi tare dashi aji ko may yakawo hakan sukai sallama ya kashe wayan. Monday tunda safe na shirya don zuwa inda ake neman mu wurin interview din da za, ayi ban tafi da haidar ba gida na barshi gun Aisha na dauki mota na fita. Koda na isa na samu wa yanda aka neme mu tare sun hallara a wurin ko na shiga don gaisawa da mutanen arzikin mu. Ban dade da zuwa ba aka kirani na shiga ba wani tambaya sosai akai min ba don sun riga da sun san mu dama don haka bamu sha wani wuya ba sun dai karbi takardun mu kawai. Sai bayan mun dawo ne Aisha ke fada min ai akan fitina daddy sunyi fada da maman Ihisan nan dai ta labarta min komai. Sai da na huta nafito falon don bata ma san dawowa na ba gidan sai ganina tayi falo zaune muna kallo. Sai naji tace an dawo ta zubar dama an saba ana mazuru ana shaho may zai sa a iya zama gida tunda an riga da ansaba hurda da wasu maza. Take naji raina ya baci sosai sai dai Allah ya taimake ni ban tankata ba tunda na gane hassada ne abin nata ba komai ba. Sati biyu sai ga shi anturo muzo mu karbi appointment letter din mu ya fito ban bata lokaci ba na tafi na karbo inda sabon wata zamu fara aiki dasu din . Wanan dalilin yasa na matsawa daddy kan son zuwa gida na dubo su yaso ya hana amma da na matsa yace mu shirya idan zai shiga ya sauke mu. Take na fara shirin tafiya tsaraba sosai na hada tunda safe muka kama hanyan kano tare da shi. Banzo da yaran ba don suna school dagani sai Aisha da baba da haidar mukazo kawai anty tai mamakin ganin mu don bata san zan shigo ba. Duk da halin da nake ciki amma ita a idon ta taga na mata kyau ne sosai na sake na zama wata classic lady dani. Ban dade ba a gurin ta na fita zuwa part dina inda na samu duk yayi kura dayake dare ne inda zamu kwanta muka dan gyara tunda safe muka shiga gyaran wuri da taimakon gajiye muka gyara ya zama neat. Nan take min hira wai yanzu ai anty ta karaya sosai tana son janta a dawo irin da can baya amma ita gaskiya tana tsoron hakana don wanda ya zarge ka a baya bayan yasan halinka amma ya rufe ido yai ma sheri ita bazata zauna da ita ba. Tace takan dai dan taimaka mata wani lokaci can ba, a rasa ba sai da nai kwana biyu a kano na shirya muka wuce gida. Mun isa da wuri don haka kafin wani lokaci akasan da zuwan mu nan yan uwa da abokan arziki suka dinga shigowa taron mu sai dai naje washe gari Allah yaiwa Jatau mijin Suwaiba na rasuwa muka tashi da wanan tashin hankalin kuma a gare mu. Koda naje gidan abin ba dadi ruwa ma babu shi a gidan ko kadan nasa akira masu ruwa suka cika duk wani kayan dake gidan take na bada kudi aka sayo masu abinci sai dai suwaiba ke cewa dani ai rabawa akeyi kowa yai nasa nace ba matsala tabar masu sai a kawo mata nata. Ban samu zama ba don kwana uku a gidanta muke wuni sai dare nake dawowa gida don haka ban samu kebewa da Innata ba. Sai ranan da aika sadakan uku bandawo ba saida na wadata Suwaiba da duk wani abin bukata suma kishiyoyin nata nai masu nasu irin alherin gwargwadon hali na dawo gida ban kai dare baranan gidan . Da dare muna zaune muna hira da Aisha uwarta ta kirata bayan fitan ta ne Inba ta ke cewa dani wai niko yarinya lafiya kuke kuwa don naji ance wanan hatsabibiyar kishiyar taki takoma can inda kike da zama yanzu ? Nace a sanyaye lafiya muke inna sai dai dan abinda ba a rasa ba can kuma ba kullun bane tace to Allah ya kyauta a daita hakkuri da jama, a don Allah. Nace insha Allahu Inna sai na boye mata don ban san yadda zan iya fada mata komai dake faruwa ba a tsakanina da daddy din. Sai wurin Attu ne da naje cikin hikima irin nasu na manya take tambaya na na sake jiki sosai ina fada mata matsalar dake damuwar mu tsakani na da daddy din. Take naji yar tsohuwar ta saka min salalami tana tafa hannayen ta tace yar nan tun yaushe hakan ke faruwa na fada mata tace to kin fadawa uwar ki da kikazo nace haba attu ko nasha giyar wake yaya zan iya fadawa inna wanan maganan kuma. Ko ke dai daurowa tayi da har na koma bazaki ji shi ba a bakina ba tace ki koma ina cikin wanan irin laluran haka na ai banga ta zama ba . Dole ne na bazama wurin masana a walwale maki wanan sihirin don idan ba walwale shi ba ku ba zaman lafiya ko zaman aure a tsakanin ku tunda akwai cutawa ga hakan. Wunin da banyi ba ke nan don Attu ta fita tabar mu don haka na wuce uguwar mu na gaida mama Altine da matan babana. Gidan mama Altine na fara shiga duk da mun hadu a gidan Suwaiba da ita amma tana ganina ta shiga ina taka saka dani ta shimfida tabar muka zauna ni da yaran ta kawo ruwan randan kasan ta mai tsabta muka sha. Tace Rahama har na fara zargin ko don irin halin da uwar dakin naki ta tsiro dashi yasa kike ja baya dani kuma yanzu. Nace ni kan yaya zanyi na gujeki mama aisai butulu ke mantawa da uwar shi irin halarcin da kikai min duniya ko uwata data haifeni ai ya tsaya nan. Tace to na gode Rahama nan muka shiga hira tace zata dafawa yaran abinci suci nace barsu mama kada ki wahalar da kanki mama kinga abincin su nan biscuit tace yaran birni ke nan. Mun sha hira da mama amma ko ta dauki halin da anty take min sai na kawar da zancen nace da ita ai yanzu an daina dama rudin shedan ne kawai. Sai bayan la,asar na bar gidan na shiga gidan mu tsatsaye na gaidasu mama tsufa ya taso mata kanta yai wani farin gashi gashi a dankare mata ba gyara hakoranta na gaba sun zube. Tabani tausayi sosai nace da ita idan na koma zan sa ai mata hakoran roba tunda dai batai tsufan da zata rasa hakora ba haka na san dai daya ya fadi wurin fadan su da amaryan ta a baya amma sauran biyun fa ? Nakawo alheri nai masu nace zan dawo don in gana da babana naga jikin nashi yadda yake yanzu. Sai gap da magariba nakoma gida inda na samu har Attu tazo nema har sau biyu ban dawo ba sai ta bar sako da magariba zata dawo mu fita. Na samu yaran sunyi barci koda tazo ban zauna ba muka fice tare zuwa inda zamu nida ita sai kanina Audi da ya raka mu zuwa unguwar da zamu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A TAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 80 Tun bayan waya na da Zarah sai hankalina ya fara tashi don ba karamin tsoro kalamin ta ya bani ba. Ni lafiyana shine yafi min komai a rayuwa na in dai zasu barni da lafiya ina iya bar masu mijin su a zauna lafiya. Amma ta ina zan fara wana san yai muna wanan shamakin a tsakanin mu ni dashi don duk kishiya kishiya ce dai. Amma wa zan zarga a wanan matsalan shin hindatu dake nan zaune tare da mune ko kuwa wa yanda ke gida ne sukai min hakan wai ? Nan dai na zauna ina ta faman tunane wanda har na gama ban iya gane komai va daga ciki abinda dai na yake da ga karshe shine zan dukuma nafi da kaimi wurin kai kuka na ga Allah dayai min tsari akan duk mai bina da wani mugun manufa. May na tare masu da har yai zafi haka sukai muna wanan mugun asirin da sai jahili zai iya shi. Sannu a hankali na fara rama a tsaye gashi bayan zarah aminiyata ban iya fadawa kowa wanan zancen don da kunya aji shi a bakina haka. Muna cikin wanan halin ne ranan sai ga massage ya shigo a email dina asibitin da nai bautan kasa suna neman mu muzo interview wurin su. Murna farin ciki duk ya kamani a lokaci daya daddy kawai nake jira ya dawo na fada mai naji may zai ce akan zancen. Koda ya dawo nice da girki ranan don haka na tsara kwalliya na dana bata lokaci wurin yin shi ga lafiyayyen abincin dana girka don shi a ranan. Bai shigo ba sai yamma lis ya dawo gidan ina dakina ina bawa yarona nono naji muryan shi Atika na mikawa yaton bai koshi ba ya dan sa kuka nace fice dashi zuwa dakin ku don Allah, Tana fitowa dashi uban yaji kukan shi yace kai Atika ya akayi ne yake kuka kawo shi nan ta mikawa uban yoron ta nacewa wai bai koshi da nono bane shine yake kuka. Daddy yace ita nonon nata na sayarwa ne ko may zatayi dashi da bazata bashi ba ya sha ya koshi da kyau. Daga kofa ina fitowa nace cikin wani murya najan ra, ayi nace wallahi daddy ya faye tsotso shi bai koshi da nono. Ya dago yana kallo na na tabbatar shigan tai mashi kyau don ni kaina na sani saboda kayan ya fitar min da kurciyana a fili. Yai murmushi yace nawa za, a sayar muna a bashi ya sha ya koshi yadda yake so na sake cewa daddy don Allah barshi yanzu Aisha zata kara mai da abincin shi yasha. Wallahi Rahama kiji tsoron Allah in baki son Allah ya kama ki da laifin daukan alhakin wanan yaro yaro dan wata shidda da kai ace bai sha nono ya koshi ba sai wani abinci can na bature. Ban so ba namika hannu ina karban yaron a wurin shi nace jishi dan Allah sai dan banzan tsotso dashi aikai ka baci da ci wallahi. Komawa mukayi daga ni har shi muna dan hira yaron na shan nono yace ina yaran nace sun fita wasan ball sukace. Yace kai yaran basa ji wallahi nace to maza ne ba a raba su da irin haka tunda ba mata bane sai dai a saka ido ga muamulan su kawai. Sai dai haka din amma ba kwar ba dai kan don an wuce wurin kwaliyan da ba biyan kudin sabulu ai aikin banza ne yin shi. Gaba daya muka juya inda take tsaye tana magana cikin tafiya zuwa kofan baya shi dai na dauka bai fahinci maganan ta ba amma ni sai na fara zargin anya ba daga hindatu muke samun matsala ba kuwa ? In ba shi ba yaya tasan abinda ke tsakanin mu ni dai na san daddy ba zai taba fada mata komai ba a tsakanin mu duk yadda suke kuwa don shi ba namijin dake zama yai maganan wata matar shi da wata ba. Tafe take tana waka mai kama da habaici kamar an dauke ta an rada a kasa ta fadi kasa tim a tsakiyan falon. Ba karamin buguwa tayi ba ga wanan faduwan shine yace innalillahi may ye haka ya akai haka kuma sannu tashi. Bai mike ba yana zaune inda muke yana cewa may kika taka kuma haka ya kada ke wanan faduwan haka ai sau ki karye ko ? Allah ai ba azzalumin bawa bane don shi ba ai mai gadara in daukan alhaki abin yine kadan mutum ya fara gani a rayuwan shi. Ina fadin haka na mike na bar wurin ban mata sannu ba ta mike da kunya ta nufi dakin ta tana cewa ban san shege yaron da ya zubar da ruwa ba a saman ties din nan kuma ? Bai jima ba ya tafi sallah sai bayan ya dawo ne na fito don bashi abinci mun zauna yana ta latsar wayan shi har na zuba mai abincin na aje a gaban shi ya kalli abincin yace duk ni zan cinye wanan Rama ? Kada fa nai kiba kizo kice dani na tsufa maki nan gaba ki fara dan kwanaye kwanaye kuma kina baki son zama da tsoho. Nai dan dariya mai kama da murmushi nace ai tunda bance ma tsoho ba da farko yanzu ma bazance ba don ni din ma yanzu ai ba yarinya bace. Muna cikin hiran sai ga ta fito daga daki tace dear kasan na fadi a gaban ka amma ko ka shiga ka dubani kaga ya jikin nawa gashi yanzu duk jikin nawa ciwo yake min wallahi. Yace ki sha magani mana tace ni asibiti nake son zuwa aduba min kafana don ciwo yake min yace amma ba yau ba kan don dare ya yi yanzu. Ta wani bata rai bataso haka ba taso ne ta tasa shi a gaba sukama hanya zuwa asibi a cikin daren nan ta nuna man iyakana dashi sai bai biye mata ba yace tasha magani agani zuwa gobe. Sai da ta wuce nace dama ina son ka huta na fada ma an turo min da sako ana neman mu ranan monday wurin interview asibitin da mukai service. Yace a, a shine baki fada min ba Rahama wanan ai ba karamin magana bane yanzu zanyi waya da MD naji yaya ake process din abin naku. Nan a wurin ya kira sukai dan magana yace ba matsala na shigo kawai ranan monday din za a duba ai ina da kwazo sosai sun sani. Mutum zai iya fahinta yanayin mu a lokacin yadda muke daukin junan mu sai dai ba dama komai don engine bai aiki a kaina ko kadan dan wasan da ma yakanyi da farko idan yayi yanzu sai gari ya waye mai ba lafiya a jikin shi. Mutum zai gane yana cikin damuwa don sai matsala ya faru zaka san idan mutum yana kaunar ka baka sanin zurfin kaunar sai idan matsala ya gitta a tsakanin ku zaka gane zurfin kaunarva gare ka kasan yadda mutum ya damu da kai. Hakane yanzu a kullun bakin daddy bai gajiya da kwantar min da hankali yana bani hakkuri kan matsalan dake faruwa damu din. Nakan yi murmushin yake nace haba daddy bakomai mana ai matsala ne kowa yasan ta sai yace Rahama nasan ina cuta maki sosai sai dai hakkurin ki bai bari a fahinci muna da matsala ni dake. Don da watace da yanzu duniya ta fahinci halin da muke ciki ko ansan muna da matsala wurin wanan fannin. Wanan kwantar min da hankalin da yake yasa ban dauku matsalan nakaishi can kasan zuciya na ba sai ma kara kaimin da nayi wurin kyautata mai fiye da koda yaushe yadda wani ba zai iya fahinta ba. Ina shiga dakin shi kullun nake da duty na kwana a ciki indai ba mun dan samu matsala bane nai fushi dashi. Don a dakina nake yaji bana fita bana kai kara gun kowa yadda naga sunayi ban taba kai karan shi a wani ba duk zaman mu dashi na aure. Yau ma na shirya tsab nabi bayan shi zuwa dakin hindatu da ban san may yasa idan ina duty zata dauki lokaci zaune afalo wani lokaci sai na shige zata bar falon. Yau ma tana ganin na shige ta mike ta fada dakinta ta jawo wani roba fari can kasan kayan ta inda ta boye ta dauko wani abu mai kama da baka ta hada shi yadda takeyi kullun. Ina shiga dakin ya fito daga wanka yana tsaye yana fesa turare a jikin shi na shigo dakin da sallama na. Jin sallama na yasa shi dan juyowa gare ni yana murmushi yace har yaran sun kwanta ke nan nace sunyi barci tun dazun ai. Karban turaren nayi naci gaba da fesa mashi sai bina da kallo yake yana murmushi da kada kai kawai. Nace daddy lafiya ko naga sai wani kallo kake min ko yau injin ta samu service ne ban sani ba daidai da nake mayar da turaren a mazaunin shi yace . Da haka zai kasance gare mu yau din aida nafi kowa farin ciki ko yaushe burina da fatana naga wanan matsalan ya tafi a gare mu. Yace Rahama ni har yau na kasa kai karshen fahintar ki nace namay fa daddy ? Yace baki ganewa ke kina da wani baiwa da ba kowa ne Allah keyiwa shi ba ke kanki baki sanin kina dashi sai dai na tare dake ya sanar maki da hakan. Nace daddy wani irin baiwa ce wanan kuwa dani ban san da shi ba haka sai kai ka san shi a gare ni ? Ya murmusa yana nufar gado yace ba yanzu zan fada maki shi ba sai nan gaba idan komai ya daidaita tsakanin mu. Sai ya zauna a bakin gadon yace Rahama ina tausaya maki ina cutar dake a shekarun ki baki cancanci wanan hukuncin ba haka a wanan lokacin. Rama ba zan iya boye maki ba ina tausaya maki matuka kuma don abin nawa a kwai son kai a cikin sa na kasa sama muna mafita a matsalar mu idan wani yaji haka tsawon lokacin da muka dauka a matsalan nan sai a ga na faye zama mai son kaina da yawa. Nace haba daddy saboda may zakace haka kuma ai komai mukkadari ne daga ubangiji mutum bai dorawa kan shi lalura ai. Yace nasan haka Rahama amma irin hakkurin da kikayi a dan tsakankanin nan ba kowa ne zai iya daure wanan irin matsalar ba haka. Gashi ke kinyiwa wanan matsalar kankantar dauka da ace shekarun ki ya haura hakane nasan ba matsala zaki iya jure hakan har lokacin da Allah zai kawo muna mafita. Nace ni ban damu ba daddy Allah dai ya bamu lafiya yace kwsnan zan tafi wani guri da nake kyautata zaton kila a shawon kan matsalan a can idan na tafi. Nace daddy ban son kasawa kan ka tunane akan wanan matsalar saukin abin ma bani kadai bace a gun ka kana iya zuwa wani wajen wata kila acan ka dan samu kadace kayi. Ni dai burina na zama mai cin wanan jerabawan da ubangiji ya aiko muna dashi bana zamo cikin masu kasa daurewa da kaddara ba. Murmushi yayi gami da girgiza kan shi yace hakane amma wani lokaci abubuwa da dama sukan zowa bawa da sanadi don ai a gunki ne kawai wanan matsalan yake faruwa dani. Nace dani da sauran duk a hannun ubangijin mu muke shi kadai ne kuma yasan dalilin yi hakan a gare mu don haka ka cire wanan damuwan a zuciyan ka kawai mu koma ga Allah ya kawo muna saukin alamarin. Haka mukai ta hiran matsalar yana kankamay dani yana wasa da gashin kaina da yasha relexzer ya kwanta baya har barci yazo ya dauke mu bamu sani ba kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai kan maganan. Ina jin saukan numfashin shi alamar barci ne ya dan dauke mu na lalaba na mike daga saman gadon na shiga ban daki can na darji kuka na don na fahinci shima daddy yasan akwai matsala a wani wuri kamar yadda zarah ta fada min ranan. To wa naiwa laifi yai min wanan mumunan hukuncin haka da sai mara imani zaiyiwa dan uwan shi haka a rayuwan zaman duniyan nan na dan lokaci kalilan. Gashi na kasa fadawa inna ta matsalar da nake ciki kada hankalinta ya tashi na rasa wanda zan fadawa bayan Zarah da itama da kyat na iya fada mata komai. Inna ce ya kamata na fadawa kuma ina jin nauyi da kunyan fadar irin magana haka a tsakanin mu ta yaya ma zan iyace mata wai miji baya iya kwanciya dani. Don ni da farko banyi zaton wanan matsalar babba ne haka ba sai yanzu dana fahinci abin kamar ba mai karewa bane muna tunda yana iya amfani da yan uwa na ashe nice dai muke da wanan matsala din tsakanin mu. Haka naci kuka na da tunanena nafito na koma na kwanta ban farka ba ga dan barcin dana samu sai bakwai na safe ashe hindatu nace ta kasa ta tsare taga fitowana daga dakin don haka take min wanan dabian kullun nake da girki. Haka na daure na ci gaba da alamura na kamar kullun sai dai daddy yazo karyawa da safe sai naga ya kura min ido ban yarda mun hada ido dashi ba sai naji yace Rahama na amsa a sanyaye ban dago na kalle shi ba. Naci gaba da abinda nakeyi yai shiru yana nazari na nazo wucewa ya riko hannuwa na abinda yasa ni dagowa na kalleshi ke nan yace dani. Sai naga idon ki kamar kin yi kuka a daren jiya ko? Ban tanka mashi ba sai kokarin wucewa da nake son ya sake ni nayi kawai nake da hannuna dake rike da nashi din. Tambaya na ya sake yi na sunkuyar da kai na kasa wani irin abu nakeji a zuciyana kuka kawai nake da bukatan yi a lokacin ko zanji sanyi. Ya sake ni ban tsaya ba na shige dakina na rufo yakai minti talatin sai gashi dakin ya shigo yazo ya tsaya kaina ya dan jima a tsaye ba tare da yai magana ba. Sai zuwa can yace nasan kina cutuwa Rahama nima abin ya fara fin karfina don ni kadai nasan halin da nake ciki a zuciyana. Nace ni bashi ke damuna ba gida nake son zuwa kawai na kwana biyu ko zan huta sai naji yai murmushi yace cikin wata murya Rahama kina nufin kije gida ki fada masu matsalar da muke ciki ko may ? Muryan shi ya ban matukat tausayi a yadda yai magana yace kina ganin idan sunji wanan matsalar da muke ciki zasu barki ki zauna dani ne haka Rahama ? Ban sake magana ba sai kukan da nakeyi shima din bai min magana ba yana dai tsaye a wurin kawai can naji ya sa kai ya fice daga dakin a gurin Aisha nake jin wai daddy ya fita. Mikewa nayi na shiga bandaki nai wanka tare da dauro alwala na sallah raka,a biyu nakai kuka na ga Allah. Nan na zauna naci gaba da lazumi da jero adduoi sai tunanen abubuwa da dama dayazo min a raina na zamantakewa na a gidan daddy wanda a kullun da irin matsalar da nake fuskan ta a gidan. Nake tunane shin haka sauran mata masu kishiya suke zaune a gidanjesu dama ake ganin kamar wani dadi mace ke ji idan anga tafito tana tunkaho a waje. Ni kan gaskiya da muguwar rawa gwanma kin tashi da a illanta min rayuwana kan kishi gara kowa ya kama gaban shi a huta hakana. Don in anci gaba da haka watarana inaji ina gani akan rayuwana za, a koma wama ya sani ko ana hakan nice dai ban gane hakan gare ni. Da kyat na iya tashi na shirya na fito don duba girkin da Aisha ta riga ta dora muna ba laifi na samu taimin shi yadda nake so sai dan abinda baza, a rasa ba kawai nayi. *** *** *** Tun bayan fitan shi daga gidan abin duniya ya damu zuciyar shi ya rasa wa zai fadawa wanan magana sai bashir ya fado mashi a rai don ya fishi sanin irin matsalolin hakan nan. Sun gaisa sunyi komai yace Bashir wallahi akwai matsala bashir din yace subbahanallahi matsala kuma Gentle yace wallahi babba kuwa. Nan dai yake koro mai komai har yagama yi mai bayani Bashir din ya nisa yace lalai babban matsala ne wanan. Yace sai dai gaskiya ko ka yarda ko kada ka yarda zan fada ma gaskiya wanan abin sihiri ne wanda mata keyi a tsakanin su. Sai dai banyi tsanmanin yanzu wayewar kai din nan ashe an saura yin irin shi abune mai wuyan sha, ani sosai don dole sai ka nemi makarun shi. Yace a ina zan nema Bashir kafa san ni ba wai na iya irin abubuwan nan bane a rayuwana asalima naki jinin alamari da sihiri shiyasa ma ban yarda da shi ba ni. Yace to shike nan tunda baka yarda ba Allah ya sauwaka ko yace kamar ya ban yarda ba ai magana nake fada ma yanzu kan ai dole na yarda tunda ya faru dani. Sunyi magana yace idan ta shigo kano akwai inda zasu tafi tare dashi aji ko may yakawo hakan sukai sallama ya kashe wayan. Monday tunda safe na shirya don zuwa inda ake neman mu wurin interview din da za, ayi ban tafi da haidar ba gida na barshi gun Aisha na dauki mota na fita. Koda na isa na samu wa yanda aka neme mu tare sun hallara a wurin ko na shiga don gaisawa da mutanen arzikin mu. Ban dade da zuwa ba aka kirani na shiga ba wani tambaya sosai akai min ba don sun riga da sun san mu dama don haka bamu sha wani wuya ba sun dai karbi takardun mu kawai. Sai bayan mun dawo ne Aisha ke fada min ai akan fitina daddy sunyi fada da maman Ihisan nan dai ta labarta min komai. Sai da na huta nafito falon don bata ma san dawowa na ba gidan sai ganina tayi falo zaune muna kallo. Sai naji tace an dawo ta zubar dama an saba ana mazuru ana shaho may zai sa a iya zama gida tunda an riga da ansaba hurda da wasu maza. Take naji raina ya baci sosai sai dai Allah ya taimake ni ban tankata ba tunda na gane hassada ne abin nata ba komai ba. Sati biyu sai ga shi anturo muzo mu karbi appointment letter din mu ya fito ban bata lokaci ba na tafi na karbo inda sabon wata zamu fara aiki dasu din . Wanan dalilin yasa na matsawa daddy kan son zuwa gida na dubo su yaso ya hana amma da na matsa yace mu shirya idan zai shiga ya sauke mu. Take na fara shirin tafiya tsaraba sosai na hada tunda safe muka kama hanyan kano tare da shi. Banzo da yaran ba don suna school dagani sai Aisha da baba da haidar mukazo kawai anty tai mamakin ganin mu don bata san zan shigo ba. Duk da halin da nake ciki amma ita a idon ta taga na mata kyau ne sosai na sake na zama wata classic lady dani. Ban dade ba a gurin ta na fita zuwa part dina inda na samu duk yayi kura dayake dare ne inda zamu kwanta muka dan gyara tunda safe muka shiga gyaran wuri da taimakon gajiye muka gyara ya zama neat. Nan take min hira wai yanzu ai anty ta karaya sosai tana son janta a dawo irin da can baya amma ita gaskiya tana tsoron hakana don wanda ya zarge ka a baya bayan yasan halinka amma ya rufe ido yai ma sheri ita bazata zauna da ita ba. Tace takan dai dan taimaka mata wani lokaci can ba, a rasa ba sai da nai kwana biyu a kano na shirya muka wuce gida. Mun isa da wuri don haka kafin wani lokaci akasan da zuwan mu nan yan uwa da abokan arziki suka dinga shigowa taron mu sai dai naje washe gari Allah yaiwa Jatau mijin Suwaiba na rasuwa muka tashi da wanan tashin hankalin kuma a gare mu. Koda naje gidan abin ba dadi ruwa ma babu shi a gidan ko kadan nasa akira masu ruwa suka cika duk wani kayan dake gidan take na bada kudi aka sayo masu abinci sai dai suwaiba ke cewa dani ai rabawa akeyi kowa yai nasa nace ba matsala tabar masu sai a kawo mata nata. Ban samu zama ba don kwana uku a gidanta muke wuni sai dare nake dawowa gida don haka ban samu kebewa da Innata ba. Sai ranan da aika sadakan uku bandawo ba saida na wadata Suwaiba da duk wani abin bukata suma kishiyoyin nata nai masu nasu irin alherin gwargwadon hali na dawo gida ban kai dare baranan gidan . Da dare muna zaune muna hira da Aisha uwarta ta kirata bayan fitan ta ne Inba ta ke cewa dani wai niko yarinya lafiya kuke kuwa don naji ance wanan hatsabibiyar kishiyar taki takoma can inda kike da zama yanzu ? Nace a sanyaye lafiya muke inna sai dai dan abinda ba a rasa ba can kuma ba kullun bane tace to Allah ya kyauta a daita hakkuri da jama, a don Allah. Nace insha Allahu Inna sai na boye mata don ban san yadda zan iya fada mata komai dake faruwa ba a tsakanina da daddy din. Sai wurin Attu ne da naje cikin hikima irin nasu na manya take tambaya na na sake jiki sosai ina fada mata matsalar dake damuwar mu tsakani na da daddy din. Take naji yar tsohuwar ta saka min salalami tana tafa hannayen ta tace yar nan tun yaushe hakan ke faruwa na fada mata tace to kin fadawa uwar ki da kikazo nace haba attu ko nasha giyar wake yaya zan iya fadawa inna wanan maganan kuma. Ko ke dai daurowa tayi da har na koma bazaki ji shi ba a bakina ba tace ki koma ina cikin wanan irin laluran haka na ai banga ta zama ba . Dole ne na bazama wurin masana a walwale maki wanan sihirin don idan ba walwale shi ba ku ba zaman lafiya ko zaman aure a tsakanin ku tunda akwai cutawa ga hakan. Wunin da banyi ba ke nan don Attu ta fita tabar mu don haka na wuce uguwar mu na gaida mama Altine da matan babana. Gidan mama Altine na fara shiga duk da mun hadu a gidan Suwaiba da ita amma tana ganina ta shiga ina taka saka dani ta shimfida tabar muka zauna ni da yaran ta kawo ruwan randan kasan ta mai tsabta muka sha. Tace Rahama har na fara zargin ko don irin halin da uwar dakin naki ta tsiro dashi yasa kike ja baya dani kuma yanzu. Nace ni kan yaya zanyi na gujeki mama aisai butulu ke mantawa da uwar shi irin halarcin da kikai min duniya ko uwata data haifeni ai ya tsaya nan. Tace to na gode Rahama nan muka shiga hira tace zata dafawa yaran abinci suci nace barsu mama kada ki wahalar da kanki mama kinga abincin su nan biscuit tace yaran birni ke nan. Mun sha hira da mama amma ko ta dauki halin da anty take min sai na kawar da zancen nace da ita ai yanzu an daina dama rudin shedan ne kawai. Sai bayan la,asar na bar gidan na shiga gidan mu tsatsaye na gaidasu mama tsufa ya taso mata kanta yai wani farin gashi gashi a dankare mata ba gyara hakoranta na gaba sun zube. Tabani tausayi sosai nace da ita idan na koma zan sa ai mata hakoran roba tunda dai batai tsufan da zata rasa hakora ba haka na san dai daya ya fadi wurin fadan su da amaryan ta a baya amma sauran biyun fa ? Nakawo alheri nai masu nace zan dawo don in gana da babana naga jikin nashi yadda yake yanzu. Sai gap da magariba nakoma gida inda na samu har Attu tazo nema har sau biyu ban dawo ba sai ta bar sako da magariba zata dawo mu fita. Na samu yaran sunyi barci koda tazo ban zauna ba muka fice tare zuwa inda zamu nida ita sai kanina Audi da ya raka mu zuwa unguwar da zamu. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , , , 81 Kusan wuri uku Attu ta tafi dani duk maganan su daya ne kamar hadin baki kishiya ce tai min aiki ta yadda mijina ba zai iya saduwa dani ba. Sai in an karya wanan abin da tai min wasu suyi misalin kamannin mai shi wani kuma yace daga cikin kishiyoyina ne sukai muna aikin. Dama irin abubuwan da ake kullawa akaina da diyan da na haifa bayan na dawo gida sai barci ya gagare ni wasu kwallan bakin ciki da tausayin kaina suka zubo min. May wa yan nan yaran sukayi da har za, a saka dasu cikin harkan mu haka su dai tsaya a kaina nida nai karanbanin shiga rayuwan mijin su. Ina kwance wurin ashe inna batai barci ba sai naji tace dani yarinya kada ki sa damuwa a ranki abu ya zamo maki biyu fa don kinga shi harka kishi dama idan baka hadu da mai imani ba da tsoron Allah haka ne yake kasan cewa dama. Nace ina niba kaina nake jiwa ba sai yaran nan da suna su ya shigo ciki duk da bawai na yarda da hakan bane har cikin raina amma nasan zasu iya don har yau babu daya daga cikin su data taba kallon dana da sunan so ko tace zata dauke shi. Suma din hakan sukeyi idan suna goyo ba mai yarda kishiya ta taba danta kinga wanan ba zai damay ni ba amma ace an hada da asiri shine illar ai. Tace wanan aiba bakon abu bane dama ba yau aka fara yin shi ba a duniya magana daya anan shine kafin ku koma sai a samu tsari abawa yaran dake ma sai kusha. Gabana naji ya soma faduwa abinda ban so ban kauna naki jinin naji aikin sihiri yau gashi ya hau kaina in har ina son kaina da lafiya dole ne kuma nayi din don rigar zamani ne muke ciki dole ka nema kasaka kaima a zauna lafiya. Bandaiyi wa kowa sheri da yardan ubangiji haka kuma ina fatan duk wace ta nufe ni dashi ya koma kanta. Sai naji Innata tace dani aiki godewa Allah da yake kare ki in bashiba dama shiga irin wanan wurin kai tsaye ai kasada ne babba sai mutum ya shirya yakan shiga. Amma ke in ma don Attu da ta dan kaiki kafin tarewan ki ba ai haka zaki shiga masu kara zube amma kinga da yake Allah yana son ki sai yake kare ki daga kaidin su. Nace yanzu ni inna gaskiya hankalina ya daga sosai in da zai sauwaka min da zaifi min sauki wallahi a zauna lafiya. Tace akul na karajin wanan mugun shawaran a bakin ki akwai may yine in ba Allah ba da sukeyi ba Allah ne ke tsare muna ke ba. Kedai ki dage ga ibadan ki roki ubangijin ki sauki ga komai Allah yana tare da bayin sa ko yaushe suma din masu yi Allah ya shirye su su daina su gane gaskiya nace Amin . Satin mu daya yadda aka bani sai ga daddy da kan shi wanan karon yazo dauka na nasan ba komai yasa yazo ba yazo yaji ko na fada a gida halin da muke ciki. Amma sai yaga an tare shi da mutunci ba wanda ya nuna mai yasan da wani abu muna batun fitowa ne ya so ganawa da maigari. Bai boye mai komai ba na halin da muke ciki maigari ya nuna bai san maganan ba don ban fada masu komai ba. Yace ai baba Rahama yarinyace mai kaifin tunane da sanin ya kamata duk tsawon lokacin nan ban tsanmani ta fadawa wani wanan matsalan ba. Maigari yace hakan yana da kyau boye sirin ka ga jama, a don yanzu duniya ba abin yarda bane sam. Yanzu gashi kazo a makare da akwai inda zamu dan tafi dakai nan gaba damu ne kadan a kwa wurin wani amin na da zamu mutumin masunci ne yana da wanan makarin ina ganin insha Allahu. Ni dai muna jiran ace mu fito sai mukaji wai sun fita da baba maigari haka yasa na samu daman fita da sauri naje naga Suwaiba da Rukaiyya inda muka dawo tare da ita Rukaiyya din don taga tshin mu. Sun kai awa uku suka dawo saida sukai sallah akace mu fito mu wuce nai sallama da mutane yan uwa da abokan arziki muka kama hanya zuwa ********* ********* ********* Mun iso kano bayan sallah la, asar nayi mamaki kwarai dana samu anty ta aje muna abinci don tasan da zuwan mu lokacin . Har part dina ta bayar da abincin aka kawo muna saida mukai sallah muka zauna mukaci abincin na hada dan tsaraban da zan basu na aika masu dashi suka aiko min da godiya. Sai da nai sallah magariba da ishai na shiga wurin anty mu gaisa take cewa dani ai har tana batun zuwa gaida mu ashe na taso sai naji nauyi da kunya ya rufe ni don ba haka na saba yi mata ba idan na dawo da baya. Nace mun dawo Abba baya jin dadin jikin shi ne yana fama da zawayin hakaro tace kai haban nawa banawa bana yana son aci naman layya dashi ke nan ashe. Na zauna tana tambayana mutanen gida nace suna lafiya tace miko min baban nawa na ganshi injin dai kina kula min da tsohon nan Rahama don bana wasa da lamarin shi. Nai murmushi nace anty nima ai Abba nane bana wasa da zancen shi sai dai bavan nan namu ya faye cine anty. Tace kajiki da wani zancen banza akwai wanda bai ci ne a duniya Rahama kina sin muyi fada dake ne ko kibar min tsoho yaci son ranshi kamar kowa. Nace ban ma samu zuwa gaida Abba din ba da nazo tai murmushi tace a to kila shi ma aban yabi sahun mu ne yanzu ana ja da baya dashi. Naji kunyar maganan ta nace kai haba anty dawa kuma nake ja da baya ni babu komai wallahi don dai ban kusa ne kawai. Tace a dai bar zancen Allah ya dai ya sauwaka kawai tace kwana ki da yaran ki suka zo sallah suke fada min irin rigimar da kuke kwasa da dayan uwar tasu. Murmushi nayi nace kai maman Ihisan ai halinta sai ita bayan haka ban kara komai ba ga zancen duk yadda taso taji wani abu ga zaman namu ban yarda taji komai a wurina ba. Mun dan taba hira na mike nace zanje naba yaran magani kafin suyi barci tace ta Allah tashe mu lafiya nace Amin anty na fita zuwa part dina. Nai mamaki kwarai a yadda naga wanan sauyin gun Anty haka kamar ba ita bace zanzo gayarwa tana daure min fuska kamar bata son amsawa a baya. Washe gari ban samu fita ba don nagaji da yawon da muka sha a gida da mukaje sai washe gari muka tafi gaida mutane har gidan su daddy da Abban anty saida na zagaya don washe gari zamu koma Abuja da safe. Na shiga tun dare naiwa Anty sallama take bani hakkuri na hakkura da yara da sauran jama a nace nagode anty tace a kuma yafe mu don Allah dai Rahama. Nai murmushi nace kai haba dai anty may kuma ya kawo wanan magana hakan ni baki min komai ba wallahi. Tace umm, umm Rahama ki dai yi hakkuri ga abubuwan da suka faru don Allah abar komai ya wuce haka na nace anty wallahi baki min komai ba Allah dai ya yafe muna baki daya tace amin ta kawo tsaraban data hada min sai da nai mamaki sosai wallahi. Mun isa Abuja da rana sosai koda muka shiga gidan yai tsit kamar ba kowa cikin sa ga ko ina kamar ba a shara nai mamaki ko ina helen data bar wuri haka ba gyara. Mun shiga min huta a dakina Aisha ta mike ta fita zuwa dakin su lokacin na samu na mike nafara gyaran wuri nima sai dai ina mamaki ina helen taje hakane wai ? Ga matar gidan ban ganta ba koma na ganta ba halin na tambaye ta nasha bakar magana gun ta don ba karamin aikin ta bane yin hakan. Can sai ga Aisha ta shigo take cewa dani anty kamar fa helen bata gidan nan don banga kayan ta ba gaskiya. Nace kamar ya bakiga kayan ta ba tace wallahi ba komai nata a dakin nan sai wanan shegen bujen da kika hanata sakawa tun zuwan ta. Kafin naii magana sai ga daddy ya shigo yana gyara hannun rigat shi doguwa dake jikin shi, yana fadin shi zai fita sai Aisha ta mike tabar dakin. Nace daddy na dawo banga helen ba kuma Aisha tace dani babu kayan ta ma a gidan gaba daya ta kwashe kayan ta. Yace yaya akai haka kin bata kudin watan tane da zata tafi ? Nace nima shine yaban mamaki ai wallahi yace ki tambaya mana kiji ko ina ta tafi aji kada yarinyar mutane ta bata ko wani abu ya samay ta ai zargin ki kuma. Yai min sallama ya tafi sai dai duk abinda nakeyi zuciya na fan yake da tunanen yarinyar a raina sai da yamma yaran suka dawo suka samu mun dawo. Da murnan su suka zo taron mu har dakina Nasir sai daukan kannen shi yake yana murna da fanin su sai washe mai baki suke suma suna farin ciki da ganin shi don sun saba dashi sosai dama. Jinior yace wallahi mummy naji dadin dawowan ku na matsu ki dawo dafa taliya ba dadi kullun muke zuwa school watarana ma ba komai muke zuwa hakana. Nace helen batai maku ne ni ban ganta ba ma dana dawo ko ina ta shiga ban sani ba tun dazun nake neman ta. Wai mummy baki sani ba shi da Atika suna hada baki wurin cewa ai maman Ihisan ta koreta sai data mamareta ta kore ta kuma a cikin dare ta watsa mata kayan ta waje tace ta wuce tana ta rokon ta amma bataji ba a gidan neabours din mu ta kwana. Nace what duka da kora akan may zata kora min ita tunda ba zaman ta takeyi ba agidan nan ? Atika ta marairaice tace Anty don ma baki gani ba wallahi ranan helen ta bani tausayi sosai wallahi danace tai hakkuri tace wai saura ni sai na bar gidan nan tunda ba gidan ubana bane . Raina yai matukar baci sosai nace innalillahi wa inna alaihin rajiun yanzu wani irin rashin imani ne haka ka kori yarinya diya mace a cikin dare. Jinior yace wallahi mum harda Ihisan tana ta zagin helen tana ce mata wai barauniya munafuka muguwa. Basu dade da dawowa ba baban su ma ya dawo ashe dama yaje ya dan sayo kayan bukata ne irin dagin abin breakfast. Ban mai magana ba sai da ya dawo da dare yana zaune ya fara cin abinci nazo falon na gaida shi yake cewa dani ya gajiyan tafiya nace Alhamdullahi. Sai na samu wuri na zauna yana cin abinci kamar da kyat ita ko hamshakiyar tana zaune ta hakince ko kallon inda nake batayi ba balle na samu sannu da zuwa. Da zamu tafi har kofan dakinta nake ina sallaman ta tai min Allah ya kai lafiya amma yanzu na dawo ta kasa yi min sannu da zuwa. Can ya dago kai ya dan dube ni don yasan ba dabia na bane zama a wurin su idan suna tare irin hakan ko can a kano din har nan Abuja din kuma banai masu hakan. Yace yaya dai kakata don wata raba haka yakance dani idan yaso zolayana wai na haifi baban shi da surukin shi sai na dan gyara zama nace dama magana nazo muyi dakai da ita. Yace wa hindatu nace ita nazo ne ka tambayan min ita dalilin ta na korar min yarinyar dana dauko amana san nan kuma korar yarinya diya mace a cikin dare koma may tayi ai a sahirta mata harda safe ko a bari na dawo. Yace subbahanallahi a cikin dare fa hindatu kika kori yarinyar mutane may tai maki dakika kore masu diya hindatu ? Shiru tayi kamar ba da ita yake magana ba sai da ya kara maimaitawa da karfi tace na kore ta don ba zan iya zama da barauniya ba. Yace may ta satar maki haka da har kika yankewa yarinyar mutane wanan danyen hukuncin babu tausayawa ko kadan a zuciyar ki hindatu ? Sai tai shiru yace bayani nake so daga gare ki kafin naje neman diyan mutane inda ta shiga kuma ki sani wallahi idan yarinyar nan ta fada wani hali wallahi ki kuka da kanki don Abuja kin sani ba karamin gari bane. Tace to don may bayan na kirga nama kowa ga yadda zan saka guda guda shine ita zata zo ta tsamay biyu ta cinye. Yace wa,iyazu billahi Hindatu agidan nawa aka koma kidayan nama kuma yaushe aka fara hakan ban sani ba a gidan nan ? Tai shiru ya koma kaina yace Rahama yaushe kuka fara kidaya nama kuna sakawa yara guda guda ga abincin su ? Nace ni ban san lokacin da aka fara masu haka ba ni dai nasan zubawa muke masu yadda ya dace ? Kai ya fara kadawa yana kiran kalman innalillahi cikin takaici yace hindatu ina zaki da alhakin yaran nan da kika dauka haka har ki kori diyar mutane akan nama nama fa a gida na ? Sai ya kira jinior da karfi saiga yaron yazo da gudun shi bayan ya amsa yace daddy gani yace zauna yaron ya samu wuri ya zauna daddy yace jinior fada min ya akayi helen ta bar gidan nan. Sai yaron ya dago kai ya kalli hindatu sai yai shiru uban yace tambayan ka nakeyi kayi shiru sai ya sake kallom ta yace a, a a dama maman ihisan bata sani bane ashe ihinsan ce ta kara nama. Sai sai tace kai muna fukin Allah wace ihisan ta kara nama din yace banaji da kike koran helen tace maki itace ta kara ba biyu ba bata iya cin tsoka daya a abinci sai kikace tai maki shiru dama kingaji da zaman ta a gidan da ita ake maki munafunci sai kikai ta marinta kika watsa mata kaya waje tana baki hakkuri ihisan ta shure ta tace ta fice a gidan nan bakwa son ganin ta. Daddy ya dafe kai yace kai kai hindatu wallahi baki da imani ko kadan a ran ki har dukan diyar mutane kikayi bayan kora kuma ? Tace nagane kana son kaga laifina don wanan yar kafiran da aka aje muna gida saboda wace ta ajeta tafi kowa ko may ? Yace rufe min bakinki idiot stupid mara hankali da tunane kawai baki da imani don bake kika haifi yar ba zaki mata haka ina ruwan ki da addinin ta tunda ba gidan ki take zaune ba. Nan yai mata kaca kaca itama din bata kyale ba ranshi yai matukar tashi yace wallahi shi halinta ya kai mai ko ina yace yakike so nayi dake hindatu ? A can idan na barki dasu ba zaman lafiya a nan din ma ba kwanciyan hankali wai ke wata kalar macece da bata tsoron Allah shin don ke kadai ne akayini don may in har ni kike so to ki zauna lafiya da duk wanda nake tare dashi mana. Tace kana da gaskiyan ka ba laifin ka bane anje gida an kaika gurin malaima sun maka asiri idon ka ya rufe baka ganin kowa da kima sai ita. Yace kamar yadda ke kika saba kaini idan kin je gidan ko haka kike ganin kowa ma sanan shi ke nan shiga boka da malam mutun ya daiji tsoron Allah tunda rayuwan mu ba a hannun mu yake ba mutuwa na iya riskan ka ko yaushe. Ya mike a fusace ya fita bayan fitan shi sai kuma ya sake dawowa ya dauki keys din motar shi ban dai san ina zai tafi ba a lokacin. Muna nan zaune sai zagi da cin mutunci takeyi nace ni banda lokacin ki don yanzu ba shi ke gabana ba yar mutane da kika salwantar ne a gabana. Tace na salwantar sai kisa nima ya salwantar dani tunda sai abinda kikace. Nace kika ce dai ke da kika san yadda ake sa mutum ya yayi abinda bai ashi yi ba ki daiyi ki gama gani nan bari nan takalmin kaza. Tace komai shuumanci ki Rahama wallahi ni Hindatu nafiki sheri nace niko na sani nakuma fi kowa sanin hakan tunda ba imani gareki ba kan komai. Ranan gamuwa da ubangiji yana tafe ranan da babu yafiya ga bawa sai aikin da ya shukawa a zaman shi na duniya. Sai ki tayi tunda baki da aikin yi ni kinga inda na nufa don ina da abin yi a gabana yar mutane da kika salwantar don bakin kishin ki shike gabana ba hauka ba. Sannu mai abinyi ai ban san kina danayi ba sai da kika fada karatun ma da kike wa mutane sallo dashi mun san komai kudi ya bayar kikaci. Nace to ke abada kudi mana kici ashe na isa tunda har za a iya kashe kudi a kaina a samo min abin yi ba in zauna zama sa ido da hassada da bakin ciki ba. Aiko kamar na yaba mata bargon balai nan ta kara harzuka tayo kaina da masifa da jidali inda take shiga banan take fita ba. Ina shiga daki na kara lalabar wayan matar da nake ba kudin watan helen don tun da yamma nake kiranta waya na ringing ba a dauka sai nai saa ta dauka wanan karon. Maganan data fara min bayan ta dauka shine haba doctor Rahama yanzu abinda kukaiwa yar mutane kun kyauta ke nan ku kori yarinya a cikin dare haka ? Badon tai dabaran shiga gurin makwabtan ku ta kwana ba yaya kuke son yarinyar nan tayi a cikin daren nan. Nan na shiga bata hakkuri tace gaskiya abinda yasa bazan boye maki ba shine don tun zuwan ta wurinki bamu taba samun matsala dake ba. Yanzu kuma da wanan abin ya faru ta fada muna cewa baki gari kishiyarki ce tai mata haka gaskiya da munyi karan ku an dauki mataki kan dukan da akai mata tunda ba duka acikin dokar mu. Hakkuri na shiga bata tace dani na bari suyi shawara suji yadda za, a yi zan iya kiranta washe gari naji yadda suka yanke akan maganan. Tai min sallama na kashe wayan ina jin kunar rai ga yadda hindatu tasa na ke rokon su da suyi hakkuri akan laifin da bani nayi ba. Daddy sai goma da wani abu ya dawo gidan har lokacin ranshi yana a bace yazo dakina yana ce wa dani naje nayi reporting ne a nan area din ko za a ganta nace ta ta koma can inda ake dauko su ashe. Yace an ganta ke nan nace dashi eh tana can har munyi magana dasu sun nuna min bacin ran su sosai sunce badon ba a taba samun matsala ba damu da sunyi kara kan dukan da akai mata. Yace yes suna da right din da zasuyi kara mana tunda ita waya taba dukan mata ya amma tana iya dukan diyan wasu kan laifin da ba nasu ba. Dukkan ku bazan lamunci duka ba a gidan nan akan ko wani yaro wallahi sannan ku sani gaba daya yaran nan amana suke a gare ku duk wanda yaci aman dan wani sai Allah yaci nashi. Ya sa kai ya fita daga dakin ranshi a bace na sauke ajiyan zuciya bayan fitan shi don na gane nufin shi ajan yaran shi ne da yaji ana saka masu naman miya sai an kidaya yake wanan fadan ko gani yake duk haka mukeyi dani da ita cin aman yaran nashi mukeyi ke nan a bayan shi. Tana shiga daki ta kira wayan uwar ta tana cewa da ita wallahi mama wanan shegiyar Rahamar shuumace ki duba fa yanzu gaba daya ma na rasa gane kan dear yau ma fa a gaban ta yai min cin mutunci akan yarinyar nan dana kora. Mama sai kudi muke kashewa amma kamar bama yi ni wallahi ina bakin ciki na bude ido naga wanan yar iskan a gidan nan yarinya kamar manya nayi kamar ba ayi. Kiduba fa shi wanan mutumin fa cewa yayi bata dawowa gidan nan in ma har ta dawo ba ita ba kwanciyan hankali da maigidan amma ji yadda ta dawo ko gezau babu a gare ta. Uwar tace waini kan dai ko baki abinda akace kiyi ne dakyau Hindatu abin akwai ban mamaki a cikin sa fa. Na ga dai in ba wanan bakan da akace ba banga abinda kikace ya kamasu ko shi ai ba haka yadda muka so ba yayi tunda ni a zatona suna tare har yanzu suna hurda kece dai baki ganewa. Tace shi ne ai mama amma gaskiya zan maida hankali sosai ga duk abinda akace nayi na dinga yin shi daidai da dadi da rage a ciki. Washe gari na karbi girki sai dai duk abinda nake yi hankalina yana kan wanan danyen hukunci da aka yankewa yar mutane ta sanadi ya zama dole yanzu na maida hankali akan duk yaran don Allah kadai yasan abinda ake masu a bayana kuma a hana su fadi. Don yadda jinior yayi a gaban uban shi ya nuna anyi warning din su sosai akan maganan shiyasa yaji tsoron yin magana a gabanta don a daki sun mayar min da komai yadda akayi din. Bayan na gama na kwashe nai yadda muke da abincin na shiga don nai wanka na gyara jikina don aikin da nasha. A yanzu ban da wani buri a raina idan ba na samun sauki ga lalurar dake tsakanina da daddy ba don bani ba koshi dake da wasu matan yana samun sasauci a ranshi ya dan damu da matsalan sosai. Don da zamu dawo ina zaune a gaban mota yake cewa dani Rahama may yasa da kika je gida kika kasa fadawa su baba halin da muke ciki ni dake. Na juyo da sauri na dan kalleshi sai tunkin shi yake hankali a kwance nai shiru ban ba shi amsan tambayan shi ba. Yace na dauka zaki fada ai koshiyasa kika matsa min kina son zuwa gida ki duba su ashe ni zato ne kawai nake sai nai mamaki da naji baba maigari yace baki fada masu komai ba. Na juyo da sauri nace kafada mashi fa kace ya gyada kai yace kwarai kuwa banda kunya dana fada masu ko ? Nace a, a ni bance ba amma naga maganar tana da nauyi fada ne a gaban manya shiyasa kawai nai mamaki. Dama ban tsanmani din zaki iya fada ba kawai dai zatone nakeyi shiyasa ma na yanke shawaran zuwa daukan ku da kaina don na samu nayi gaisuwa na kuma samu mu kebe dashi baba maigari din. Kinga kuma Alhamdullahi zuwan nawa yai min rana don yasan irin matsalar tamu shine har ya kaini wani kauye gaba daku. Nace ni fa ban faye yarda da irin abubuwan nan ba shiyasa na sa Allah gaba da roko na fadi hakane don kada ya kawo komai a ran shi gamay da irin haka. Yace ni dai yanzu burina shine Allah yasa mu dace don kowa da irin nashi saan ai idan Allah ya kawo karshen abin sai kiga komai yazo da sauki. Idan mun je akwai abubuwan da aka bamu wanda zan maki bayani a can don a tare zamuyi ni dake sai dai idan mun isa. Ina wanan tunane don ban san ko may za muyi a taren ba da yace gashi yau nice da girki bai min bayanin komai ba har wanan lokacin. Ina tare da gajiya don haka a gurin da nai sallah nan barci ya dauke ni ban ma san dawowan shi ba gidan har ya dawo yaci abinci ina barci na a kasa saman sallaya. Sai da ya gama yai komai ya kara shigowa dakin har lokacin ina kwance a wurin ban falka ba daga barcin. Jin motsin shi yasa na falka daga barcin da nakeyi har ya kai kofa nace daddy kadawo ashe ? Yace kin falka ke nan tun dazu nazo kinata barci yanzu ma har zan shige na lekoki nagani ko kin tashi. Na kai dubana ga agogon bangon dake dakin ya nuna min goma da wani abu na dare yace may yasa kike ta waban barcin haka tun dazun ? Nace gajiyan tafiya ne ke tambayana kawai daga idar da sallah na kwanta ina tasbihi sai barcin ya dauke ni. Yace kina dai tunane barci ya daukeki ko, ki yi hakkuri Rahama Allah zai kawo muna dauki mu koma kamar yadda muke da yardan ubangiji. Nace wanka fa yace yayi tunda ya dawo in dai kin gama sai kizo ki samay ni mu fara abinda na fada maki a mota jiya da zamu dawo . ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 82 Ba yan na gama shiri na ne na shigo dakin yana zaune a saman dogon kujeran dake dakin yana zaune ya mike kafan shi daya a sama. Dayan kuma ya sako shi a kasa ga laptop a gaban shi yana dube dube a cikin sa hankalin shi ya matukar daukuwa ga abinda yake yi. Na zagayo ta gaban shi na dan zaune tare da mashi sannu da aiki ya amsa min ba tare da ya dago ba. Yace dani dauko min wancan jakar dana dawo dashi jiya na mike na dauko jakar na kawo mai tare da dan rusunnawa na bashi. Ya karba yana sauke ajiyan zuciya tare da dan dube dube a cikin jakar tashi yana ciro wani abu a cikin leda. A hankali nakai hannuna ga kafan shi na fara dan matsa mai kafan dake saman kujera a hankali naji ya sake sauke ajiyan zuciya karo na biyu. Yake cewa dani baki gajiya Rahama duk da ba komai nake iya tsinana maki ba sai faman kokarin taimaka min kike yi ko yaushe. Nace ai wanan kaddara ne yana kuma iya faruwa akan kowa tunda bada son rai hakan ke faruwa ba. Yace na sani amma ki kara hakkuri Rahama ki sani ni na fiki bacin ran wanan abinda ke wakana a tsakanin mu tunda ba haka muke ba da dake a baya sai naga kamar nine sanafdin komai. Ina tsoron kada hakkurin ki ya zo ya kare wata rana ki nuna min gazawarki Rahama har wani yaji may ke tsakanin mu. Nace haba daddy ni fa musulmace nasan kaddara kuma bakaine sanadi ba tunda abin dani dakai duk ya shafe mu. Don haka ni nayi imani duk abinda faruwa da bawa da sanin ubamgijin shine kaga Allah ne mai tsarowa bayin shi jarabawa don gwajin imanin su. Dadi da wuya ai duk daga Allah suke ban taba zargi ko zaton wani ba akan wanan matsalan ni na barwa Allah komai. Don haka daddy ka daina cewa kaine sanadin hakan a gare ni tunda na aure ka ya zama wajibi a gare ni da in rungumi kaddaran ko wani irin hali akan auren mu, haka kuma zan jure duk wani kaddaran da zai shigo muna in zama jaruma walau dadi walau wuya. Ni tsakani da Allah nake zama da kai da iyalin ka don haka ba zan taba yin dana sanin auren ka ba koda kuwa akan kane haka yake faruwa din don bani iya mance halarcin da kai min kake ma cikin yi min din. Rike yake da ledan da ya dauko a jakkar shi ya aje ledan ya dan rungumoni izuwa jikin shi yana dan sauke ajiyan zuciya a hankali mai nuna alamar zuciyar shi na cun kushe da damuwa da wani abu. Yacd Rahama na godewa Allah da Saade da ta yarde min na mallakeki a matsayin mata a gareni. Mun dan dauki lokaci a haka rugumay da juna yayin da idanuwa suke fitar da hawayen tauayin kan mu. Ya sake ni tare da dauko wanan ledan yana budewa yace dani ki saurara kiji yadda zakiyi amfani da wanan maganin. Yace kinga wanan zamu dinga wanka da shine dani dake, wanan kuma ya dauko dayan yace hayaki zamunayi a tare idan zamu kwanta sai dai yana da matsala shi don ance kada ya zuba koda kadan ne a kasa. Da sauri na dago ina kallon shi yace eh ai a tare zamuyi dake don haka sai mu fake amfani dashi. Sauran dayan da ya rage ya dauko yana cewa wanan kuma da kike gani sha zamuyi da ruwa tsami irin na kamun koko da ake dama kunu dashi. Na dago again na kalleshi yace kada ki damu na tanadi komai yadda bazamu wahala ba sai dana samo komai kafin mu zo. Don haka sai ki tashi yanzu ki soma hada muna yadda aka bukace mu da muyi mu saurari hukuncin ubangiji. Ban zauna ba namike na shiga ban daki na hada muna ruwan wanka na fara shiga nayi shima ya shiga bayan mun fito na jona borner mukai hayaki sai na dauko cup na zona hada wanan nasha din muka sha. Muna gamawa muka kwanta a rugumay da junan mu sai safe tunda ba wani abinyi kuma. Kwana uku akace muyi amfani dashi don haka washe gari ma mukai amfani dashi kwanan karshe da zan fita sai mukayi da safe. Shike nan kwana uku muka gama sai jiran sarautar ubangijin mu duk da haka ba wai na daina wanda Attu ta karbo min bane ina abina yadda da duk aka umurce ni da yi kuma ina wa yara na suma kalar ta su da aka bamu ai masu amfani da shi. Daga haka na ci gaba da harkoki na don Monday mai zuwa zan fara shiga wurin aiki wanda daga ni sai maigidan muka san da zancen aikin nawa don abu bai kan kama ba bana karan banin fadawa mutane sai ya zama gaskiya. Naje har gidan matar data kawo min helen muka shirya da ita don yarinyar ta amince zata dawo wurina da zama. Haka yasa suka amince suka bani ita na dawo da ita gida ranan hindatu kamar zata cinye ni danya don ganin na dawo da yarinyar. Ana saura kwana biyu na fara fita aiki na karbi girkin gidan nai komai yadda na saba yi daga gyaran gida zuwa girki da gyaran dakin maigida kafin wanu lokaci har na gama komai na shiga wanka inda na samu Aisha ta gyara min yaran suma. Kamar yadda ya saba dawowa gidan ya shigo tun hawa step din da zai kawo mutun cikin gidan kamshi ya fara taron shi. Yashigo da fara, an shi yana shakan kamshin turaren dana sa Aisha ta turare gidan dashi wanda da takeyi wai hindatu tace da ita za ai wa mutane hayaki sihiri a fakaice an labe da kamshin gida. Tazo tana fada min cewa wai ga abinda hindatu ke fadi dataga tana turaren gidan ta ko ina. Nace kyale ta wanan ita ya shafa gani take abinda takeyi shi kowa yakeyi a gidan shiyasa take fadin hakan a zaton ta turaren asiri ne muke yi ke nan. Koda ya shigo gidan ya samu Aisha da yaran zaune a falo ya dauki haidar yana mashi wasa baba ma yazo ya rigumay shi haka ma jinior suna jin dadin dawowan shi. Yace wa Nasir ya karbi key ya dauko masu leda a mota ya shigo dashi da sauri Nasir din ya fita sai gashi da ledojin a hannun shi ya shigo falon dasu. Daidai lokacin da Hindatu ta fito daga dakin ta don jin dawowan shi gidan ganin yaron ya shigo da ledojin yasa hankalinta ya koma gare shi. Yana kokarin mikawa uban tace kai kawo nan sai uban ya juya yana kallonta yace ki barsu mana nasu ne suna sayawa ai tace ko nasu ne ai zan ga may ye a ciki ko. Daga inda nake nace wanan kuma sai ki bari idan an shigo dashi ranan girkin ki don yau ba hurumin ki bane yin hakan. Kallona take cikin mamaki yaron kan dama bai son bata ledan sai ya nufo ni dashi aka barta tsaye banbarakwai tana zaran ido. Tace ke har kin isa ki hanani taba abinda mijin mu ya sayo don wani hujjan ki can na yan kauye. Nace ashe baida dadi kikeyi hanka don haka a gunki naga hujjan yan kauye nima na koya. Nagane nufinki ke watau ki shige min gaba akan komai a gida da wurin miji ko nagane shine manufan ki. Murmushi nayi nace wanan dai yau bazaki taba ba sai abinda muka baki kamar yadda kike muna muma idan ya kawo wa yaran shi abu na juya inda yake yana surutu da yaran shi kamar baima san munayi ba. Nace sannu da dawowa ya aiki da jama a ? Ya dan dago yana kallona yace kun gama fitinan ke nan ko ku bakujin kunya fada kullun a gaban yaran ku sai yaushe zaku girma ku daina wanan halin haka ? Ledan nake budewa ban yi magana ba na fara fitar da abinda ya sayo masu chefs ne da corns da su biscuits sai kaza gassasa guda uku masu zafi sosai na mr big. Tana tsaye har lokacin tana kallona nace Atika dauko plate a kitchen ta mike da sauri ta tafi sai gata da plate guda hudu a hannun ta na fara yanyanawa na kasa wa yaran guda biyu na bar muna daya mu uku nida ita dashi shima na kasa muna shi daidai. Nace karbi jinior ba maman Ihisan ta dauki nata ka kawo muna namu nan ni da daddy na shiga raba masu sauran kayan yadda ya dace. Na zata zatai fushi taki karba tunda ban raba yadda take muna ba don kaza daya take dauka ita kadai da yarta haka ma sauran tarkacen sai abinda ta bamu zamu gani. Nace ma Aisha ta saka muna namu a ovon kada yai sanyi har daddy ya fito wanka sai muci namu sun gama ci daidai lokacin sallah ya gabato mazan suka shiga alwala kafin mahaifin su ya fito su tafi sallah. Shiri na nayi sosai na fito falo na zauna ina jiran dawowan su nan muke da sauran yan matan muna hira saiga Ihisan ta fito tana cewa dani. Little mum wanan sauran chefs din ya rage ki bani nace ai duka na raba maku sai dai na Baba zan kara maki don banga yaci sosai ba. Shi din na dauko na bata tace thanks mum ta juya ta tafi abinta tun a nan ta fara ci tana wucewa Aisha tace bata saba idan an kawo uwarta ta kwashe mata ba nace ai uban ta ya sayo shine nufin ta sai ga su sundawo daga sallah still akwai leda a hannun jinior shi dai daddy baya gajiya da saiwa yaran shi abu kudi daine baya yarda ya basu a hannun su haka ma bai bari wani ya basu kudi su kashe da kan su. Nan ya zauna yaci abincin shi yaran na basy wurin cin abinda suka sawo a bakin massalacin da suka tafi sallah da mahaifin su. Mun dan taba hira a wurin duk ba wani hira bane can sai akan yaran shine akai magana inda yake cewa yana son a saka baba a makaran ta. Nace tun yanzu yace to uwar shi ne tai magana nace anty yace ita mana yana da wata uwa da zata bada umurni hakane in ba ita ba ? Jiya muna waya take fada min ya kamata asa shi makaranta hakana da taji muryan shi nace Allah ya bada saa yace amin. Ni dai ban so a sa shi ba a wanan lokacin naso sai ya dan kara girma amma yanzu may zance tunda ta nuna concern din ta gare shi. Alama ya kara nuna tai matukar saukowa ke nan yanzu a yadda muke da don da zamu dawo harda kayayyakin sawa ta saya masu dana dinki tai masu tare da yaranta wai na zuwa sallah jumma,a ne. Na kwashe kaya don lokacin har ya mike zai shige don nasan ba kwanciya zaiyi ba zai shiga interneat ne yai aiki a laptop din shi wanda haka ya zama mai kamar jiki kullun kafin ya kwanta sai yayi wanan halin. Ban shiga wurin shi ba sai da na gyara tsab kamar kullun na samu har yaran sunyi barci na tada Aisha ta kashe wuta tare da rufe kofa na nufi dakin bayan na kashe komai na wuta na falon. Na samay shi zaune kamar yadda nai tunane din ya dago dayaji shigowa na yana cewa yaran sunyi barci ne ko ? Nace tun dazun suka kwanta sunyi barci ko na dan yi abin da zanyi adakin na samu wuri na kwanta. Sai da ya gama ya tashi ya dan shiga ban daki bai jima ba ya fito daga ban dakin ya shirya ya hawo gadon lokacin har barci ya fara dauka na ko. Ya dan rugumoni zuwa jikin shi sai na bude idanuwa yake cewa Rahama naga yanzu kema kin fara iya fitina bana son wanan fitinan da kuke a gaban yara suna jin ku suna kallon ku hakan baidace ba gaskiya kamar kuna koyawa yaran wani hali ne na daban wallahi. Nace in sha Allahu za, a gyara amma itama ai mata magana abu ba abu ba zata dauke shi da zafi kamar ko da yaushe a jirace take dani. Yace kuke dai jirace da juna nidai nace a bari bana son irin hakan da kuke yi a gaban yaran don girma suke suna ganin abinda kuke yi. Shiru nayi ban yi magana ba yakai hannun shi a kan jikina ya fara dan taba ni nasan ba komai zai iya ba sai kawai na lumshe idanuwa na inajin abinda yake min. Naji yace dani Rahama na amsa da naam yace juyo yau kiga baby ki abinda yakeyi na dan juyo don ganin abinda yake nuna min din da sauri na kawar da kaina gare shi. Ranan dai komai ya wakana a tsakanin mu sai dai da gani yana da sauran matsala yadda da ya gama naji yana maida numfashi sai fadin yake Alhamdullahi Allah ya karba adduan mu yau. A raina nace a hakan cikin wanan irin wahalan ba zan iya cewa ga abinda ya kawo muna sanadi ba sai dai nace Allah ne ya yanke muna wanan wahalar kawai. Karfin hali irin na maza da safe ma sai da daddy ya sake nema na abinda ya wakana daren jiya shi ya kara faruwa dashi nan na barshi a kwance na fita wurin yara na. Na samu Haidar yai kuka sosai don Aisha tace tun da asuba ya falka yake wanan kuka da sauri na isa wurin su na karbe shi. Yai kuka sosai sai ajitan zuciya yake sakewa don kukan da yasha din na zauna na fara bashi nono da kyat na samu ya kama nonon ya fara tsotso yana sauke ajiyan zuciya irin na yara. Bai jima ba barci ya dauke shi sai da yai nisa na cire mai nonon na shimfide shi na shiga nai wanka nafito zuwa kitchen. Abin ya zama kamar sabo gun daddy don kafin na fita girki duk da baya jin dadi jikin shi amna sai da na dan wahala gun shi. ********* ********* ********* Monday na shirya najawa Aisha kunne sosai kan hindatu kada ta kula da ita su zauna a dakin su idan sun gama girki. Daddy da kan shi ranan ya kaimu tare da yaran har baba da za, a saka a schoool din a bisa umurnin anty da ta bayar a kan shi. Ni suka fara saukewa suka wuce hindatu koda muka bar gidan bata fito ba a lokacin tana dakin ta tana barci na dai fadawa Aisha ta fada mata na tafi gun aiki. Ta fito tana karyawa ne Aisha ke fada mata anty tace idan kin fito na fada maki ta wuce wurin ai baki tashi ba. Tace aiki aikin may kuma tace ni dai haka tace na fada maki idan kin fito tace ashe akwai tsiya ko a gidan nan. Wa take nufi zai dinga zama mata gadin gida ita tana zuwa gun aiki kai lallai namiji muna fuki ne wallahi. Yanzu shi abin da suka kulla ke nan dama ban sani ba sai kawai naji zancen daga sama kawai wai an fita gun aiki. Ni bazan dauki wanan tsiyan ba wallahi ya dawo naji ai ba ita kadai tai karatu ba da za, ace wai wani aiki za, a fita. Za, a dai fake ga sabara a halbi barewa kawai da sunan aiki ba wanda za, a daukowa cuta a lakakawa muna zaman zaman mu. Ita dai Aisha ta wuce tabarta tana faman fada don ba sa,ar ta bace balle ta tsaya bata amsa kan maganan ta. Ta kasa hakkuri ta dauko waya ta kira daddy inda take shiga ba nan take fita ba yace cikin tsawa kan ki daya kuwa Hindatu ? May ya kawo wanan magana haka da kikeyi ba dadin jin ni dai ke auren Rahama da yarda na kuma ta fara aiki ba gaban kan ta tayi ba. Tace ai dole ka yarda tunda angama dakai sai abinda tace dakai takeyi yace ita Rahama din tace ita mana. Yace ashe takai mace ke nan a wurina tunda sai abinda ta sani nake yi a rayuwana yana fadin haka ya kashe wayan shi don bai iya sauraren haukan da take mai lokacin. Na samu karbuwa sosai a gun aikin anbamu office din mu kowa yasan inda zai zauna an kaini fannin mata don dama a kan su nai karatuna watau ganycology. Ranan wa yanda muka saba dasu cikin likitocin suke ta muna murna da samun aikin da mukayi tare da su. Matar farko dana fara karban matsalarta tana fama da bleeding na tsawon kwanaki ban sha wani wahala ba na gano case din ta bayan na tura ta ai mata wasu awo daya dace ayi kafin na gane case din ta din. Na bata gado itace pecent dina na farko don haka ta samu kulawa sosai a wurina don nai mata abinda ya dace ta samu har inga yadda case din zai tsaya wanda ba komai ke damun ta ba sai peibros dake damun akasarin mata a yanzu idan jinin bai tsaya ba dole muyi mata aikin shi. Don matar ta riga da ta manyanta ta haura shekara arbain ko da haihuwa dole ne a cire mata mahaifan ta don kada ya zama mata cancer nan gaba. A gajiye daddy yazo ya samay ni yana zaune cikin motar shi na karaso wurin da yake ya bude min na shiga na zauna yake cewa dani a gaida doctor Rahama da aiki. Nai dan murmushi nace dashi ina zare rigar likitan dake saye a jikina daga sama kai daddy abin kuma yar zolaya ce kuma yau ? Yace to naga baku da hutu ne da zaran kun saka wanan rigar da kike cirewa kamar imanin ku ya gushe kuke zama. Dariya nayi kawai muka fara hanya sai da muka fita daga haraban asibitin na sauke ajiyan zuciya nace dashi daddy ya amsa da naam nace nagode nagode ubangiji ya bar kauna ya kara rufa asiri yace da akai may kuma wanan irin adduan da godiya haka ? Nace badon Allah da kai da anty ba da ba zan kai ga wanan matsayin da Allah ya kaini ba a yau nasan Allah ya nufa da zan zamo haka din to amma kuma kunr sanadin hakan gare ni ai. Yai dan murmushi ya shiga round about din da zai kai mu kwanan unguwar mu yace ki dau godewa Allah din da kika fara fada don shine ya hukunci hakan a gare ki. Ban taba tsanmanin matana zata taba aiki ba a duniya amma sai gashi ke karatun ki ya zamo dole na barki ki fita ki taimakawa alumma dashi. Nai dan murmushi nace kamar kasan case din farko dana fara karo dashi abin akwai ban tauayi sosai ga matar wallahi. Yace ai ku likitoci kuna fama da case iri iri balle ma ku dake fannin mata ai abin naku sai nake ga kamar yanzu yafi matsala sosai. Mun kusa kai gida yace Rahama na amsa mashi yace ina son ki saurare ni da kysu kiji may zan fada maki. Sai na mayar da hankalina sosai a gareshi yace ba hundatu ba duk wani wanda zai yi magana akan aikin da kika soma yi bana son ki biyewa mashi har ku bata min rai. Yana fadin haka nasan akwai magana a kasa ke nan don haka ya zama wajibi a gare ni da nai taka tsantsan dakowa don dama nasan dole sai an samu wanan matsala tunda cikin matan shi babu mai aiki kuma duk sunyi karatu gwargwadon hali. Aiko ko da muka shigo gidan taji yara na muna sannu da zuwa tana daki sai yar aikin ta kawai na gani a waje don matar babu ruwan ta da saka kanta ga harkan kowa ba kamar hanne da tai zama da ita bace a baya wanan ta girmay wa hanne sosai tasan ciwon kanta. Ni dai na shiga daki naji fitina ya barke a tsakanin su inda nake jin muryoyin su yana tashi. Ban fito ba amma ina jin komai tunda gida daya ne tana fada wai banfi kowa ba da zai barni ina fita wurin aiki. Sai ga Aisha ta shigo dakin nan take labarta min maganganun da tayi da bana nan. Nace kyaleta sai dai kare ya mutu da haushin kura don nagaba yayi gaba ko na baya sai labari. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 83 Ranan sunyi fada sosai a tsakanin su ina jin yadda take surfa min zagi daga dakina amma ban taka masu ba tunda badani take masifan ba. Saboda yara na fito falo don na duba su don tunda na dawo ina dakina ina hutawa saida nai sallah na fito inda suke na duba su. Muna zaune tare dasu suna min hiran baba yadda ya kwashe a makaranta karon shi na farko. Munyi dariya sosai muna cikin dariya ne sai gata ta fito daga dakin ta a hasale take don har lokacin tana jin masifa a tare da ita. Wa za,a gwadawa boko ni da naga alhudahuda sarkin karatu ana gwada min yin karatu mace bata fu mu balle a fifitata a gare mu sai a san wanda za za, a bari gadin gida. Ni dai ban kulata ba taci gaba da cewa in asiri ne ai gida mutum yazo mu zuba kafan wando daya da mutum mu gani a gidan nan. Kamar nace da ita ai munzuba ba yau ba tunda wani dadi naji a wurin ku tun shigowa na gidan kowa da irin nata surfan a kaina ai. Amma saboda maganan da mukayi dashi a mota naja bakina nai shiru ban taka mata har tayi ta gaji ta shige ciki. Case dai har yakai gun iyayye ban san yaya akayi ba kwana biyu naga sun shirya a tsakanin su nace miji da mata ke nan tsakanin su sai Allah. Naci gaba da zuwa aikina hankali kwance sallah babba na gaba towa don yazo gab a lokaci sai shirye shiryen sallah ake ko ina. Haka ne muma a gidan mu sai faman shirin sallah mukeyi ba babba ba yaro kowa na zumudin zuwan wanan lokacin kamar yadda ko wani musulmi ke fatan ganin shekara ta zagayo irin hakan. Ranan ya dawo yake fada muna mu shirya ranan laraba zamu tafi kano sallah gaba dayan mu gidan nai saa ina up a lokacin da tafiyan zai kama ke nan. Don har mu tafi mu dawo ina da dan lokaci a wanan season din na bukin sallah da za, a yi din. Nan kowa ya shiga shiri ni dai a raina ban so ba don nasan babu abinda zamu je yi sai fitina a tsakanin mu a can. Amma da yake babu yadda zan yi dole na hakkura na shirya ba tare da na nuna komai ba a fili. Ranan da zamu tafi lokaci da da duk wani musulmi idan ka gan shi busy yake ba kama hannun yaro ga kowa. Tafiyan da zamuyi ranan ya kama nice keda girki don haka nai muna abincin da zamuci a mota don yara. Mun fito har lokacin hindatu bata fito ba sai na zauna gaban motan don ganin nice mai girki sai bayan wani lokaci tafito tana shan kamshi. Gaban motar inda nake zaune tazo ta tsaya a kaina ni dai bance da ita komai ba sai shine bayan ya gama rufe ko ina na gidan ya karaso gare mu. Yace a, a ya baki shiga ba ke yake cewa da ita tai mai wani irin kallo tace a ina kake son na zauna yace ba wuri ne a motan halan ? Tace a saman kanta kake son na hau na zauna ko may ko baka gani ne kai ? Yace ya salam hindatu may yasa kike son rigima ne ke ko yaushe ina kin san komai kuma kusan kece kika kawo wanan matsala mai girki ce zata zauna a gaba indan irin tafiyan nan ya kama . Tace nan ai ba kano bane ko kuma ai acan din ne nai magana ba a abuja don haka sai kasan yadda zakayi. Ya dan kallo inda nake zaune na rungumay haidar a jikina yana shan nono muka hada ido naga yanayin shi ya shiga rudani sosai. Tsam na daga yaron daga jikina na fito daga motan na bude gidan baya na shiga tare da rufo kofan da nake daga gefen shi. Ta sauke ajiyan zuciya cikin fisgan jikin ta takai zaune sai ya zagaya ya zauna mazaunin driver don shi da kan shi zai ja motar da muke ciki inda Hamza yazo zai kwashi yara da yan aikin mu. Sai daya zauna ya juyo inda take zaune yace koma baya ki zauna ke ma, tace saboda may ? Yace haka nace ko baki ji bane ba matar da zata juyani yadda ranta ke so wallahi kin ji na fada maki. Bata fita ba tai zaune ya jiwo idanuwan shi sun canza kala yace ba dake nake magana ba kina bata muna lokaci haka ? Taja tsuki ta fice daga motan ranta a bace ta dawo inda nake zaune a baya ta zauna tare da jawo ganbun motar da karfin tsiya ta rufe gwaram. Ya kada kai tare da kutawa ya fara jan motan sannu aa hankaki muke fita garin har lokacin ba wanda yai magana sai dai idan zai tsaya ya sai wani abu ya fita daga motan kuma komai daban daban yake sayowa kowan mu baya hadawa. Ba mu isa kano ba sai uku na rana don haka kowan mu a gajiye yake duk da haka ban wuce part dina ba sai da na fara zuwa mu gaisa da anty. Ina ganin ta gabana yai mugun faduwa nace anty lafiya kike kuwa tai dan murmushi tace Rama ina ko naga lafiya yau na kai sati biyu ina fama da jiki sosai amma yanzu Alhamdullahi na samu sauki ai. Nai mata sannu tare da tambayan mutanen gida tace duk suna lafiya ban jima ba na mike zuwa nawa sasshen don na dan huta. Na samu gajiye a falo tazo taron mu muka gaisa nai mata yaya gida ta kawo abincin da tai muna don taron mu nan na bar su Aisha suna ci na shige ciki don na rage kayan jikina. Nai wanka nai sallah na sauya kayan jikina zuwa dogon riga na fito falon don na danci abincin da akkai muna. Gajiye ta sake dawowa nan muka zauna muna ta zabga hira da ita nacee gaskiya Gajiye banji dadin ganin anty ba ga kwanaki da muka zo tayi kyau sosai amma yanzu duk taa ramay wallahi. Tace bari hajiya ai yanzu ma taji sauki ke nan idan da ga satin da ya wuce ne ai abin ba kyau taji jiki sosai wallahi. Nace Allah ubangiji ya bata lafiya tace amin na zauna naci abincin sai dai ba wani mai yawa ba sosai ba don raina ba dadi tun fitinan mu na safe. A bakin Gajiye nake ji irin yawan fitinan dake faruwa a nan din inda take fada min komai nace kai kishi dai baiyi ba wallahi gashi kuma a jinin mu yake. Ban fito ba sai bayan ishai don mun dan tsaya yan gyare gyare a shiyan don wuri ba mutum raggage ne sosai ba kamar yadda idan akwai mutum yake tsab ba. Na samu anty zaune da yaran ta sun kewaye ta sai faman zuba mata hira suke Nasir yana kwance a three seater ya daga kafan shi daya ya tokare bango dashi. Ina shigowa bayan nai mata sannu tare da mata mun samay su lafiya sai na juya wurin jinior daya manne ma jikin nata. Nace kai kuma big man may ye haka baka ganin bata jin dadi kawani manne mata haka kamar zaka koma ciki da kai ? Ta dan shafo kan yaron tai murmushi tace kai haba Rama yaro yaga uwar shi kice kuma kada ya manne min nace yana nan yana aikin shi zuba ko. Tai dariya tace yana bani labarin fitinar uwar su ne kai wanan bata bari a zauna lafiya ki dai ta hakkuri da kowa Rama nagode kwarai wallahi yaro sai hakkuri kokai uwar shi balle yana ganin baka haife shi ba. Murmushi nayi na dan dukar da kaina nace anty aiko ba wani matsala a bangaresu wallahi don suna da dadin zama gashi suna maida hankalin su sosai ga karatu. Tace kai Rama ai in kan yaran nan ne baki taba bari a fadi don Allah Rama yadda kika rike min su amana ko bayan raina ki rike min su haka don yaro sai hakkuri . Nace haba anty tare da abinki zaku raka har tsufa insha Allahu Allah dai ya baki lafiya tace kai Rahama ho tsufa yanzu ganin tsufa ai sai dace. Tace da ace ba a gunki suke ba hankali baya taba kwanciya da zaman su can da wata amma kinga yanzu ko da banji komai a wurin su baa hankalina a kwance yake don ko a nan suke ya tsaya haka balle ni yaushe nake ta yaro ma can . Kin ganshi harda wani sallo yazo min wai shi a can mummy su bata bari su kwanta sai sunyi wanka da dare sai sunyi kaza da kaza don iyayi. Dariya nayi kawai tace ubangiji ya raya maki naki zurian su taso tare da yan uwan su kunya naji ban iya cewa amin ba a fili a gaban ta. Sai kuma muka dauko hiran aikina take cewa dani kwanaki waban da ta maida kowa irin ta ai ta bugo tana fada muna wai ga abinda yai maki ya barki kina aiki mu muna gida. Don haka sai mu hada mai kai tace idan ita ta manta aini bazan taba mantawa ba ina aikina amma saboda su dole na aje nabi ra, ayin su. Sau nawa yana bamu kudin jari tunda sunce su sana,a zasuyi amma kudin ya kare har dubai ta fara zuwa ban san ya akayi ba kuma ta daina. Ita kanta yasha bata kudi fiye da kowan mu idan sunyi tafiya amma sai a rasa ina kudin ke shigewa haka ? Yanzu dai naji akan aikin ki wai suma sai ya nema masu aiki yace ya basu right kowa ya nema kema bashi ya nema maki ba ai. Nai murmushi nace anty ni bani bakin ciki da aikin kowa wallahi tunda ba a jikina kudin zaifito ba balle. Ranan munyi hira sosai har dare ya soma nai mata saida safe na koma wuri na inda dama a gajiye nake na samu har yaran sun kwanta muka rufe part din sai safe. Da safe na fara raba dan tsaraban da nazo dashi na aikawa Zulfa abinda nazo masu dashi ita da yarta nai mamaki da tace a dawo min dashi sun gode don ba halinta bane. Ashe tasha zugi sun hada kai kan zancen aiki akan lalai suma sai ya nema masu aikin yi kamar yadda nakeyi haushin hakane yasa tace a dawo min da kayana. Ban damu ba na karbi abina na ci gaba da aikawa masu so suka karba da godiya da murna da fatan alheri. Kagin a fara kiciniyar aikin sallah na shirya da yamma zuwa gaida iyayyen daddy da sauran mutane kada nazo ban samu zuwa da wuri ba nai laifi gin hajiyan daddy din don tana son a bata girma sosai a rayuwan ta. Na samay su zaune a falo na gaidasu taja yan jikokinta a jiki tana masu wasa tace dani Rahama ga yaran kamar sun saba dani mana basu da kiuya ko kadan. Muna gidan sai ga daddy yai mamakin ganin mu yace nan kuka zo ashe nace eh muka gaidashi Alhajin shi yace shi yasa nake son yar tawa ai akwaita da hankali. Kaga ta kawo muna yara mu gan su gasu har suna batun kwace min mata na don tun shigowan su suke manne da ita sai shigowan ka suka yo gun ka. Murmushi yayi Alhaji yace yaya jikin ita Saade yayi sauki ko ? Yace ta samu sauki ina son idan an gama sallah na fita da ita waje don sai nake ganin wanan ciwon nata ne ke son dawo mata kuma. Subbahanallahi Allah dai yasa ba shi bane don bani son wanan mugun cutan yace kagab ta nan Alhaji dama zuwan da muka taba yi lagos ta sayo mata wani maganin gargajiye shi tai amfani dashi tun lokacin ya lafa. Yanzu kuma ai Rahama batayi karan banin zuwa bata wani magani ba kuma can tunda ta riga ta zarga ta inji hajiyan daddy ke fadin hakan. Alhajin yace haba saboda may ai tsakani da Allah ta ke mata taimako ai bai gajiya ga bawa idan ya tashi yi. Nace ai a lagos ne mun shiga kasuwa naga maimaganin yana talla nai mai magana yabani yanzu ma ban gane wurin ai don an dade. Allah dai ya bata lafiya inji Alhaji ya fadi cikin damuwa da abin sai hajiyan tace dama ina son ganin ku gashi Allah ya kawo ku yau. Tace ba komai bane sai zancen sauran matan ka akan aiki da yar uwar su keyi su ka hana su korafi yai yawa daga iyayyen su don Allah suma ka sama masu aikin a bar wanan zancen hakana inda hali. Yace hajiya ni banaki bane ai tun farko idan baki manta ba sai da na basu baki sukace Sana,a za suyi su naba kowa jari don uin sanaan don dama ni ba aikin nake so ba gare su. Hajiya macr mai hankali da sanin ya kamata ake bari ta fita aiki ba wacce zata fita ba kimtsi ba sanin ya kamata ba don nasan kan aikin nan zamu iya samun matsala dasu watarana. Tace na daice ka sama masu aikin kowa ya huta don uwar ita hindu har waya ta bugo min tana son yi min tijara ranan. Don haka kaji abinda na fada ma yace itama bani na sama mata ba ai don haka kowan su ya gwada saan shi ya nemawa kan shi don ni yanzu ban ma san ta idan zan fita neman wani aiki ba can. Kada ki manta da halinsu hajiya sai na samo kuma suce ai bashi suke so ba zan daibawa kowa baki ta fara idan ta samu din shike nan ko ? Ni dai ina duke ban dago kaina ba a inda nake ina sauraren su ban jima ba namike nace zan je na gaida Abban anty dasu Zarah. Sai dare muka dawo gidan a gajiye na dawo din haka ko wurin anty ban samu shiga ba ranan mukai wanka bayan munci abinci sai barci. Ranan jajibur ma ba sauki a gidan fitina ne akan wai an yanka sa sai yabawa maigadi mijin Gajiye kafafuna da kai don ya san raba shi gareshi fitina ne. Aiko suka ce dawa Allah ya hada su bada shi ba don gajiye na yar uwana zai masu haka aiba su kadai bane mabukata akwai masu so da yawa a gari . Shine ya kawo masu fitina akayi kaca kaca a tsakanin su nikan ban fito ba sai labari nake ji don muna ciki muna aikin sallah saboda su Aisha bazasu iya min yadda nake so ba idan na barsu. Sai da mama Laraba ta shigo gidan ba shiri ta tsawata masu suka daina wanan fitinan da suka sa a ran su. Bayan tagama dasu ne ta shigo wurin mu take cewa jiya na shiga barka ance kin shigo baki samay ni ba ai nace eh mama tace harda tsaraba haka maiyawa Rahama mun gode Allah ya raya maki yan diyan ki ya tsare muna su nace amin mama don yanzu mun saba saboda dan zaman da mukayi da ita. Na dibar mata nama mai yawa nace taje ta kara don ya yanka masu sa ita da sauran yan uwanta taita godiya tana cewa ke gashi kin bani naman da saboda kai da kafa wasu ke ta masifa a gidan. Na dai yi dan murmushi kawai tare da tambayanta su anty Fatima yar ta yar Farida tace suna can uguwar su mai nisa shiyasa bata ganin mutane ai yanzu tunda suka koma can din. Tace bari ta shiga taga jikin anty nai mata sai anjima ta tafi ta dan jima wurinta suna hira kan matsalolin gidan ta tafi daga baya. Washe gari sallah muka tashi mun gama aiyukan mu don tun dare muka hada komai shiyasa muka samu saukin aiki ranan sallah. Daddy ya shigo da kanshi har part din nawa yana saye cikin wani shadda gezena sai maiko take faman yi fara tare da yaran shi maza yayi don fita sallah idi. Ya samu na shirya yaran ya dauki haidar bayan mun gaisa mun mashi barka da sallah. Suka fice gidan aiko yana fita da yaran ya samu Nasir da jinior na jiran shi ya fito saiga hindatu ta rako wata kaunarta da aka aiko gunta. Ta ce lalaima don bata san da kayan ba sai yau da ta gani a jikin su munafunci dai baya karewa a gidan nan su diya matan sai a kaisu a bola a yar mu gani. Bai kulata ba ja yaran shi suka fice don kada su makara basu samu sallah idin ba a ranan. Dun kai awa biyu a waje ashe saida ya biya dasu gidan mahaifanshi da wasu yan uwa yai masu barka da sallah ya dawo gida. Part din anty ya fara shiga yai mata barka da sallah tana ganin haidar a kafadan shi yai barci tace a, a babana daga massalacin kuma kai barci ta mika hannu ya miko matashi ta shinfide shi a wurinta. Ya dan jima ya fito ya shiga wurin Zulfa da hindatu nice ta karshen zuwa ya dubani nai mai barka da sallah ina tambayan yaran yace haidar yayi barci suna gurin uwar su ta shimfide shi can. Naji dadin jin haka don alama ya nuna ba karamin saukowa anty tayi ba sosai ya dan zauna kamar yadda ya zauna suka gausa da kowa ya fito. Haka akaita aikin sallah ban sha wahala ba don ga gajiye da Aisha da helen da Atika su ne karfin aiki sai fama da wayan mutane nakeyi masuyi min barka da sallah. Sai wani lokaci aka kawo min yaran Amira tai masu wanka wai sun bata jikin su da maikon nama. Muna cikin magana naji hayaniya ya kaure wai ashe kan girki ne hindatu tace ita zatai girki ranan zulfa tace bata isa ba ai can suke zaune da miji don haka ba ruwanta da girkin kano. Sun jima suna fitina shiya shiga tsakanin su ya raba fitinan yace baza tayi ba dani da ita ba maigirki a garin nan sai idan mun koma can don haka bai son wani fitina kuma. Tai masifa babu kunya gajiye na mayar min nace babu gwani ke nan a garesu don basu bar kan su ba ma balle wani shetin daine aka kullawa a tare. Dare yayi na shiga gun anty na gaida ita sai na samu ta kwanta naga wata yar dattijuwa tazo wai gwagon ta ne muka gaisa da ita na karasa gun anty nace anty yaya dai tace dan nama biyu fa naci shine jikin nawa ya koma min ba dadi wallahi. Nai mata sannu na dan dade a wurin ta nai mata Allah ya sauwaka na tafi don yara saboda na bar haidar baiyi barci ba a lokacin. Washe gari sai dana karya naje gaida ta tana zaune a kasa ga cup din tea a gaban ta bata sha ba sai sanyi yakeyi . Nace anty kisha mana kada yai sanyi tace bari Rama bana jin dadin komai jikin nan nawa sam ba dadi wallahi da kyat na samu tasha tasha magani. Na jima na barta don ta dan huta na wuce wurin daddy na gaidashi suna tare da Zulfa na gaidasu a tare ya amsa min itama dai ba laifi ta dan amsa a dakile. Yake cewa dani yana son mu shiga gurin su baba kafin mu koma sai dai bai san lokaci ba amma mu zauna a shiri dai. Naji dadin jin hakan nai mai sallama na fita daga wurin su din na zagaya inda su Aisha ke aiki a gurin gajiye na dan zauna tare dasu. Yinin ranan dai haka naji bana jin farin ciki a tare dani haka dai nake daurewa ban yi magana ba da kowa. Zarah ta shigo mun dade muna hira shiya mantar dani komai da nake ciki a gidan mun sha hira ta tafi. Da dare na leka anty ban dade ba na dawo don kaina yana min ciwo a lokacin na kwanta sai barci ya dauke ni har suka gama suma suka shigo suka kwanta. Can cikin dare naji ana dukan kofana da karfi na falka kusan tare muka fito falon da Aisha dake barci a dakin su. Nace waye yace bude Rahama nine na bude da sauri don jin muryan daddy da nayi ina budewa nace daddy lafiya dai ko a wanan lokacin. Yace Saade ce jikin ya tsananta mata sosai ina son muje asibiti yanzu da sauri na koma na dauko hijjab dina don dan rigar barci ne a jikina dama. Na bi bayan shi da sauri muka nufi dakin tun a kofa kanajin kugin ta tana nishi ina shiga naga halin da take ciki take jikina ya mutu don abin ba kyau . Nai mata sannu ta dago kai da kyat tace dani Rahama kin tashi kinga jikin ya tashi kuma again tun da safe haka nake yanzu ne ya zama worst haka kuma. Nai mata sannu ta karba tace dani Rahama don Allah ki ta hakkuri da diyan ki gasu nan zan bar maki amana a hannunki da fatan zaki yafe min. Hawaye suka zubo min nace haba dai anty don Allah ki bar wanan magana duk zafin ciwo ne daddy yace ku kamata muje gun mota da sauri. Dagota da zamuyi sai ta rike min hannuwa na gam tana son yin magana ba baki kuma gareta bayan maganan da tayi din. Innalillahi kawai nake kira nace daddy kama muna ita don Allah daddy ka yafe ma anty don tana cikin wani stage yanzu mawuyaci ya juyo da sauri yana kallon mu ya karaso ya rike ta kafin wani lokaci tafara dan shakuwa tana murmushi ga magana abakinta amma baya fita batafi minti biyu ba Allah ya karbi abinshi. Salatin da na saka ne yasa shi kara razana ya ruvumay ta ajikin shi yana fadin Saade na yafe maki na dan taba hannun tanaji ina ba motsi rai yai halinshi a saukake ta cika a dakin ta. Wani iri kuka ne yazo min da ban san na iya irin shi ba ma nace yau nawa ya samay ni anty kin tafi kin barni da babban nauyi a kaina haka ni Rahama na shiga ukku. Tsawa daddy ya daka min yace ke bari kuka mana kila dogon suma tayi nace ba suma bane daddy she has gone salati ya fara yana fadin yanzu Saade kin tafi kin barmu da yaran nan ke nan. Ai take wuri ya rude da kuka na tashin hankali amma har wani lokaci har wasu makwabta sun shigo gidan. Sai dai daga Zulfa har hindatu babu wacce ta leko sai da asuba ya kula da hakan don mu a wutin gawar nata muka kwana har safe. Yaje ya dinga dukan kofan su da karfi yace to sai ku fito marasa imani ita nata ya kare sai ku jira naku kuna jinabinda ya samay ni amma mugun hali ya hana ku fitowa tun dare. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 84 Kafin gari ya karasa wayewa gidan mu ya cika da jama,a yan uwa da abokan arziki sun cika gidan don anyi sanarwa a massalataiya anji. Mama Altine da wasu daga cikin iyayye na sun iso tunda safen nan don asubanci sukayo don su samu zanaidar ta. Muna zaune cikin tausayi da tashin hankali kakai mata komai daya dace aiwa mamaci aka dauko anty muna ji muna gani za a kaita gidan ta na gaskiya gida ya sake rudewa da kuka. Yaran suna manne dani suna kuka aka fice da ita zuwa gidan gaskiya inda kowa dole ya halarce shi idan lokaci yayi. Nidai har aka wuce da ita banga giccin daya daga cikin matan daddy ba a wurin aka wuce da ita mutane akabita da adduan alheri tare da fatan dacewa da rahaman ubangiji. Rigan barcin dake a jikina dashi na wuni ranan sai hijjab din dana saka gashi duk inda nasa kafana yara suna biye dani. Mutane basu da tsoron Allah don ranan yan uwanta suka fara wani shawara can akan abin duniya. Dakina nake zaune washe gari ranan su Inna sunzo da kishiyoyinta da wasu yan uwa na da suka zo muna gaisuwa. Kuka nake sosai cikin tashin hankali suna lalashina da kyat na bude baki nace Zarah dole ne nai kuka . Zarah anty ta tafi ta barni da babban nauyi a kaina zarah yaya zanyi da wanan nauyin haka dole ne nai kuka anty ta wuce tabar mu a daidai lokacin da muke bukatan ta a tare da mu. Tace haba Rahama kiyi imani mana duk mai rai yana tare da wanan balle yaran nan tun tana a raye kusan kece komai nasu sunan ta haife su ne kawai ita. Kin san halin su sun san naki matsala daya ce ita wanan yarinyar da keda akidar kishi a zuciyar ta amma nasan itama zata sauko idan girma ya kara shigan ta. Kuka nake sosai har su inna suka saka baki da sauran mutanen dake dakin da kyat na dan tsagaita kukan nawa da nake yi. Ranan da akai uku kuma ranan abin ya dawo muna sabo don anyi kuka sosai na rashin wanan boyar Allah mai mutunci da karamci a tare da ita. Ta samu sheda na alheri a gun mutane wanda kowa ke fatan samu ga jama,a a bayan shi. Sai dai matsala daya shine irin yadda yan uwan anty suka nuna zalaman su a fili don muna ji muna gani suka shiga yanyana kayan da ta bari cikin rashin tunanen ta bar baya a duniya. Ba wanda yai tunanen cewa akwai yara ta bari dama daddy ya gargade mu akan mu sa masu ido ga duk wani abinda zasuyi ga dan zaman su damu a rabu lafiya. Shiyan na bari don bakin cikin yadda suke harkokin su a cikin nuna rashin da sukayi sun manta da anfi bukatan ganin mai kaya bisa ga abinda ta bari a duniya. Idan kaga daddy zaiba mutum tausayi don ya ramay yai baki ya koma wani silent dashi gwanin ban tausayi. Sai da zasu tafi ne wata sister din anty ta samay shi wai tana son ta dauki Amira ta zauna a wurin ta yai dan murmushi yace asiya sai dai kuyi hakkuri amma Amira tare da yan uwan ta zata zauna. Don ni banda akidar barin diyana a wani wurin don haka ai hakkuri da wanan zancen kawai a barta a cikin yan uwanta. Sun danyi magana akan wasu kaya nata yace yanzu shi ba wanan ke a gaban shi ba adaiyi hakkuri har nan gaba idan an natsu. Su tafi don basu so haka ba sun so daukan ita Amira din ta zauna a wurin su amma fir yaki yarda da tsarin su. Mama Altine da wanan gwagon nata suka bari a dakin anty kowa ya watse ubangiji yasa anty ta huta Allah yasa Aljannan fiddausi ne makomar ta acan itakan ta tafi da sheda mai kyau da kowa ke fatan samu ga jama, a. Sai gidan ya koma shiru an barmu mu kadai yasu yasun mu yaran suka ce su ba zasu kwana a part din ba a wurina suka dawo har Amira din. Ba a daina zuwa muna gaisuwa ba don mutane suna shigowa jefi jefi kwanan ta biyar da rasuwa nace da yaran su shirya muje muyiwa Abba mahaifinta gaisuwa a gidan shi. Mota biyu muka tafi dashi har mama dasu gajiye duk muka tafi gaida Abba din yaji dadin zuwan mu yai mata addua tare da fatan Allah yasa albarka ga abinda ta bari a duniya. Nan yai mun nasiha mai ratsa jiki sosai yake fada min girma da nauyi da kuma dadin dake ga rikon maraya in anyi hakkuri yace abin akwai wuya sai an daure gaskiya. Kuka nake ina sauraren shi daga karshe ya juya kan yaran suma yai masu nasiha tare da ja masu kunne kan jita jita da biyayya. Mun shiga cikin gidan suma mun masu gaisuwa muka fito don su ko ajikin su sai harkokin su kawai suke a gidan kamar ba abinda ya samay su ma. Mun tafi gidan iyayyen daddy daga can su ma sun muna yadda ya dace babba yayi sun kuma kara jajan ta muna kan mutuwan. Alhaji yace danj tau Rahama sai dai mu kara baki hakkuri don yanzu wani nauyi ne maigirma ya samay ki rikon maraya sai kayi hakkuri. Don shi uban nasu yace tare zasu koma dake har ita wanan din don muso ta zauna nan wurin mu amna yace can yake son ta koma don karatu don haka aita hakkuri dakowa ma don zaki ta ganin abubuwa harda ma wanda baki taba tsanmani ba. Kuka nake yi yai min nasiha haka ma ita hajiyan shi bamu dade ba muka dawo gida don mutanen da ke shigowa yin gaisuwa. Don su wa yan can ba ruwan su harda mutuwa kamar kishin shi ma suke don ba abinda ya damay su sai harkokin su sukeyi kawai. Muna shiga get hindatu ta rako kawarta sai dariya suke kwasa tun daga nesa muna hangen su sai mama Altine tace ikon Allah watau dai wanda ya mutu shiya mutu a zamanin nan . Ki duba fa gidan iyayyen nata sai harkokin su sukeyi kamar ba a mutu masu ba shiyasa a kullun ita marigayiya take wanan korafin na rashin kaunan ta da basuyi. Mun shigo kamar ma bata gan mu ba mudai bamu kula su ba muka shige wurin mu idan na shiga part din na anty sai naga wurin ya koma min wani iri kamar ba shine da mai shi take raye va komai na alatu akwai a cikin sa. Yanzu ko masu kwasan ganima sun dauke wasu abubuwan amfani da dama a part din acewan su ai yaran basu komai dashi. Ina zama jinior yazo ya zauna a saman jikina yace dani yanzu little mum wai ba zamu sake ganin maman mu ba inji Amira. Na dan shafi kan shi nace zaku ganta mana idan kun tuna ta sai kuyi mata addua don shine take bukata a gare mu. Nan nake koya masu irin adduan daya dace ai mata da ita dama sauran musulmai da suka riga mu gidan gaskiya. Ranan da akai bakwai wasu sun dan shigo muna mun kumayi sadaka da abinda ya sauwaka a gare mu. Nasan zamu koma sai nasa su fara shiryawa kowa ya dauki abinda yake bukata don idan mun tafi zuwan mu aikine kuma. Sai dai tun rasuwan bamu samu zama da daddy ba koda yaushe ka shiga wurin shi yana tare da jama, a a tare dashi. Da dare ya nemay mu muka halarta a falon nashi yana zaune yai zaman dirsha a kasan saman center carpet ya mike kafafunan shi tare da harde su wuri daya. Farar jallabiya mai dogon hannu ne a jikin shi ya balle aninaiyar gaban rigan ya ramay sosai yai baki. Ina goye da haidar a bayana don yana fama da zazzabi duk yinin ranan shiyasa bai yarda da kowa ya dauke shi sai ni ko Aisha daya saba da ita. Nai sallama ban tsaya gaida su ba na samu wuri na zauna sanan nace daddy mun wuni lafiya ya ya karin hakkuri kuma ya ce Alhamdullahi Rahama. Ya jikin na haidar yaji sauki ko nace eh yasha magani shine jikin yai mai sanyi yace Allah ya sauwaka kaji haidar ko kewan diyar kane gashi baka ma santa ba kai. Duk maganan nan ba wacce tace dani yaron baida lafiya ne daga cikin su sai kowa tai shiru nace a raina cin tuwon kishiya ai ranko ne. Shiru ya ratsa falon bayan ya daina magana sai can ya dan gyara zaman shi yace ba komai yasa na kira ku ba sai muyi magana akan rashin yar uwar ku da mukayi. Dafatan ubangijin Allah ya rahama mata ina kuma rokon ku da ku gafarta mata a dan zaman da ubangiji ya nufata mukayi da ita. Sai dai mutuwa hanyar kowace idan tamu tazo ya bamu muma cikawa da kyau da imani don ita Saade ta godewa Allah ta mutu a dakin ta a kuma hannu na da Rahama da gwagon ta cikin mutunci da rahama. Allah yasa ta huta yasa Aljanna ne makomarta na fadi cikin wani yanayi na damuwa yace amin sai zulfa ma tace amin can kasan makoshin ta. Yai dan murmushi yace to Zulfa yanzu girma da ragaman wanan gidan ya dawo a hannun ki da fatan zakiyi koyi da abinda ita marigayiyar tayi watau hakkuri. Sai tace hum, umm Allah dai ya kyauta kawai amma ni ina zan iya wanan yace to shike nan yanzu dai ya saura gare ki ai. Hindatu tace ance wai Allah ya kauda ranan yabo to shine nan yau nakeji kuma yanzu ita Saaden ne ake yabo haka kuma a bayan ta. Yace ada bana yabon ta ke nan kike nufi ko may tace ni dai ai magana nayi wani girma can girman da za,a taru a kashe mutum da ran shi ko may ? Hindatu komay mutum zai yi ya tuna da mutuwar shi itama da tafi ba wai da son ranta ta tafi ba don idan bakiji tsoron wanan isharan da ubangiji yai muna ba agidan nan yanzu banga lokacin da zakiji ba kiyi hankali. Yau fa sati daya da rashin yar uwarku amna kike wanan maganan haka kamar wacce bata da imani a zuciyar ta. Tace yanzu kuma may ye nawa a nan da za, a lake min a wuya banci ba bansha ba a dora min nawa akai. Yace yayi cikin kada kan shi yace sai batun tafiyan mu don zamu koma idan ba don wanan lalurar ba da tuni mun dade da komawa sai gashj Allah yayi nashi ikon a kan mu. Shiru ya biyo baya can yace yanzun dai ina sauraren ku naji naku tsarin tukun na kafin na fadi nawa. May za, a tsara kuma bayan dama kowa yasan inda yake tun farko sai zulfa tace may kike nufi da hakan badai kina nufin ni kadai zaku tafi ku bari cikin wanan tangamaymayn gidan ba ni kadai. To idan ba zaki zauna ba ai sai ki san yadda za a yi nidai ban zama nan kin sani wallahi dani akazo tare kuma zamu koma do ba zan yarda ba da wani shawara can. Nan suka fara sa insa a tsakanin su kowa na fada wa dan uwa bakar magana nikan haidar dake bayana a goye ya motsa don jin hayaniyar su, sai na mike na fara dan jijiga shi. Zulfa tace munafuka da ba aiki kikace zakiyi ba a ina kike son zama ki aikin dama badai can din ba tunda babu mai daukan ki da wani dan karamin kwalin ki can masu degree ma yaya suka kare bare ke mai NCE din. Ai gara ni mai NCE din dake mai kwalin bugi ko kina nugin ban san yadda kika samay shi bane da dodofa da bin malamai office office don aci. Yace cikin tsawa kai ya isheni haka please ku barni naji da abinda ke gaba na da wanan fitinan naku na banza da kukewa mutane. Daddy zan tafi na shimfide yaron nan kwanciya yake so na fadi hakan ai dole kice haka tunda mu an mayar damu mutanen banza watau ke maganar bata shafe ki ba ke nan ko ? Hindatu ce tace danu haka cikin watso min wata uwar harara mai nuna tsana, nai murmushi nace niko ta shafa tunda baki fini ba agidan idan yace na zauna sai na zauna din maye a cikin zaman tunda nasan zaman shi zanyi ko anan din ke zaman ya dama tunda ba alheri a zuciyar ki. Tace ke munafuka ke har zaki ce wani baida alheri bakiji kunyar fadin hakan ba mun fasan komai wallahi adai bar kaza cikin gashin ta kawai. An mayar da yara marayu yanzu an dawo ana wani nuna son su a bayan fage ta Allah dai bata mutum ba indan anyi wa wani an take lafiya wani kan wallahi sai dai a tafi tare . Nace to wata sabuwa ke nan to na barki ga Allah yabi min hakkina a kan ki kan wanan kazafin da kika laka min banji bangani ba da daren nan. Yace Rahama ban son na kara jin bakin ki a wurin nan ki min shiru kinji na fada maki kafin ran ki ya baci yanzu. Naja bakina nai shiru ina jin wani irin bakin ciki a zuciya na may wanan matar ke nufi da maganan ta tana nufin ni na kashe anty ko may ? Yace yanzu tunda abin naku ya zama haka nasan abinda zanyi don haka ku bani wuri ke zulfa ki bari zan roki mama ta zauna ita da gwago dakin Saade in yaso ku zaku dinga zuwa wata uku uku ku dawo ita wanan da ke aiki sai ta zauna can da duk wacce tazo. Aiko hindatu ta hau balai tace bazata yarda da wanan hukuncin ba don ita wallahi zama Abuja daram gare ta ba mai dawowa da ita nan tunda Rahama ba fina tayi ba ai. Aiki bai zama dole ba a gareta don muma ba yi mukeyi ba balle yace idan aiki bai zama dole ba rikon yarana da takeyi ya zama dole yanzu a kanta ai ko dole ta zauna min dasu can suyi karatu. Nikan yaro ya matsa min da kuka nai masu sai da safe tunda naji hukuncin daya yanke na bar falon kawai raina yana min kuna sososai ga kalamin hindatu a gareni amma taci bashi ai. Na shiga na shimfede yaron nasan idan bamu tafi ga gobe ba zuwa jibi zamu tafine sai dai ban san yadda zata kaya ba dai ne. Mun shirya tsab ban san yadda akayi ba sai dai da zamu fito naga da hindatu zamuyi tafiya amma yarta ba lafiya sosai a ranan. Sai naji tana fadin wai a motar mu Ihisan zata zauna tunda bata jin dadi kada taje can bata kusa jikin ya matsa mata a wani motan. Har na zauna nafito daga motan yace ke kuma ana butun tafiya ina zaki kuma nace zan koma wancan motar ne ku tafi kawai don ban san yadda zan zauna a matseni ba ga yara tare dani. Yace wa zai matse ki kuma nace naji ana za a kara wata mana yace idan bazatabi yan uwan ta ba ai sai ta zauna don ba yaron da zai shigo nan bayan kananan nan. Tace Lalai samun wuri ya juyo wurin da nake tsaye yace shiga mu tafi don Allah rana yana muna naiwa su mama sai wani lokacin muka barsu a tsaye suna daga muna hannu ita dai zulfa bata ko leko ba ma. Tafiya muke kamar na kuramay har mukai nisa ba wanda kewa wani magana nasan dai a kule take dani nace ban zama da yarta a mota daya. Niko a shirye nake da duk wani balain ta a lokacin don haka nake jiran ta tanka min nima nai mata tas. Haka muka iso gidan mun samu maigadi yana jiran isowar mu mun riga yaran isowa don haka kagi su iso naba jinior key ya bude min part dina na shiga dayarana. Sai da na zauna suka iso gidan hayaniyar su yasani gane cewa suma sun iso ke nan a lokacin. Dakina suka nufo gaba dayan su lokacin ina cirewa Baba rigar jikin shi daya bata da ruwan lemon da uban ya basu a mota da muna hanya. Nai masu sannu da zuwa ban ga Amira ba nake tambayan ta sukace tana falo zaune nace ita bazata shigo bane ? Jinior ya fita ya kirata sai gasu tare sun shigo dakin na ce kowa ya shigo kin zauna a falo Amira tace wai kanta ne ke ciwo. Na dago da sauri ina kallonta sai na fahinci kuka tayi don alama ya nuna a idon ta nace to shiga ki wanka sai kisha magani kafin a kawo abinci ki ci. Tace ina zatai wankan nace shiga ga bandaki nan mana kiyi ko ta mike kamar bata so ta shige ban daki nace a raina akwai aiki dai kan gaskiya. Munyi wanka minyi sallah sai ga Nasir sun dawo da uban da ledojin abin ciye ciye tare da shi. Nace muje falo a zauna a ci nan muka fito dukkan mu falon kowa ya dauki take away din shi sun fara ci ke nan ina bawa yarana sai ga hindatu ta fito tana cewa kai nasir naga kaimin ba miya a ciki mana da yawa yaron yai sauri yace bani na zuba ba haka aka bamu nima tace. Haka aka baka yaya wana da kuke ci yafi wanda kai muna din miya a cikin sa nace kai Nasir dauki ga nawa nan mika mata idan yafi shi miya din sai suci. Ta dan gware wanda tafito dashi din a wullakance a gurin ta dauki nawa din ta wuce dashi dakin ta nace ki dai ji dashi in kaya ne. Tana wuce wa Amira tace ashe haka take har yanzu ta shiga bata dade ba Ihisan ta fito falon tace little mun kina da maganin ciwon ciki ki bani don Allah. Nace da yarinyar yaya jikin har yanzu bai fada maki bane ko may tace cikin ya mutse fuska takai zaune tare da dan kwantawa tace dani ya dawo min a ciki nan gefen tana nuna min a raina nace Allah ya ceta inba afendix bane ke damun ki. Nace bari na dauko maki pain reliever ki sha mu gani don uwar bata kusa ne nai mata magana da tana kusa bama zan ko kalleta ba wallahi don taji haushi. Nasan ko yanzu yarinyar ta dai zo ne bada son ran uwar ba ta shigo wurina don ciwo ya isheta. Ta dan zauna na dauko na bata tasha tamike ta wuce zuwa ciki mukaci gaba da harkokin mu a wurin ba wanda ya koma kan su. Ni da Amira da Aisha muka kwana dakina can cikin dare naji ana dukan kofa na falka muryan daddy ne ki kira wai na bude kofa. Na mike da kyat na bude kofan ina hamma nace dashi lafiya dai ko yace Ihisance ba lafiya jikin ya matsa mata soai sai birgima take wai cikin ta ya damay ta. Nace Allah ya sauwaka kawai ina batun juyawa yace tace maganin da kika bata dazun ne ta dan samu yai mata sauki yanzu kuma ya tashi mata. Nace sai dai da safe kakaita asibiti a dubata don ina ganin kamar sai nai shiru yace muje mana ki gani yadda take ko ? Nace wa ni daddy haba dai Allah dai ya bata lafiya da safe sai a shiga asibiti da ita yace ke Rahama ban son wanan haukan fa . Nace amma daddy ciwon da baifi na da ba ai naga dana ya fara ciwo kana gani ko kallo bai ishi hindatu ba sai nice ban san ciwon kaina ba ko may ? Yace nace kije ki duba min ya ko ? Kamar nace oho ya sai nai shiru nace ina zuwa na jawo kofa ban ko saka hijjab ba nabi bayan shi muka tafi dakin. Yarinyar na kwance a kasa ta ta kugi muka shiga dakin uwar da yar aikinta na saman kan ta kamar za suyi kuka. Na karasa ina cewa ihisan ya kike ji ne yanzu ta nuna min cikin ta da hannun ta na kai hannuna ina dan latsa cikin nata a hankali nakai daidai inda nake tuhuma din tai wani dan kara ta rike min hannu na. Nace ina ga kamar dai tau kila dai nan ne ke damun ta kawai amma gobe a kaita wurin likita dai ya dubata. Yanzu barin bata dan taimako ta samu tayi barci ko zataji dama uban yace kina ganin may kin dauko magana kuma kin toge gareshi. Nace a, a ba wani abu bane a bari har goben dai a gani ke fada min naji may kike tuhuma gareta nace a hankali apendix ne nake gani take dashi. Sai uwar tace Allah dai ya sauwaka a bari gobe dai aje gun likita ya gani muji may likita zai fada akai. Na mike nace sai da safe a bari gobe a kaita gin likita din yace ban fa son hauka ita Rahama din ba likita bace da batasan abinda ke damun ta ba ? Nace a, a fa a dai bari goben likita ya duba muna ita agani zai fi sauki ni kaga ban sanni ba yace oh god Rahama dauko abinda kikace zai sa tasamu barcin kafin gobe din. Nace da an barshi dai har gobe sai a tafi yace wai magana na zakibi ko wani shirmay can ban ki ba na fita naje na hado allura da magani nazo nai mata. Uwar tai wani zuwa ta kafeni da idanuwan ta kamar tana son hanin abinda zan wa yar nata da idon ta a raina nace kiji dashi kunci albarkacin daddy wallahi. Cikin yardan ubangiji sai ko ya dan fara lafa mata sannu a hankali tai wani gyatsa sai uwar tace kagani ba ulcer ne ba komai ba Ihisan bata son cin abinci wallahi. Yace ke raba ni don Alah da hauka danballa kawai ni dai ina ganin maganin yai mata aiki na fito na bar masu dakin na koma dakina. Da safe ta samu barci sosai muna karyawa uwar ta fito ta hadawa yarinyar tea takai mata bance da ita ko yaya jikin ihisan din ba na kyale ta. Zuwa goma uban yafito daga dakin shi a cikin shirin shi muka shiga gaidashi da kwana ya amsa yace dani baki shirya ba nace zuwa ina daddy yace asibitin mana ? Kafin nai magana naji ashe tana waje tace ai don ba yarta bace ko dubata tayi taga yadda take nidai da ta dama aina shirya. Murmushi nayi nace ai kowa nashi ya sani ashe ban sani ba sai yanzu da kika fada na sani ai don ke naga kina hakan ai don haka kowa yasan zafin nashi. Yace kada ku kawo min shi da safen nan ran ku ya baci yanzu ki tashi mu tafi nace ban yi wanka ba baba ma haka ya tashi baijin dadi yau allura nake son in ya falka nai mai in nayi mashi wanka . Yai tsuki yace tashirya ita ihisan din mu tafi uwartace tayi wanka tun dazun kai muke jira yace ku samay ni a waje ina jiran ku. Yafice ta shiga daki tayar da diyan suka fito ba wanda yai masu a dawo lafiya suka fice gidan nasan ranta ya baci sosai. Sai da suka fara tafiya ba wanda yai magana sai can tace wallahi matarka nason shige min hanci tai hankali dani. Yace sai ki face ta ai tunda tana son shiga maki hanci din waya fara bake ba baida dadi kikayi kin manta cewa ke ma zai iya faruwa a kanki ko idan zakiwa kan ki fada kiwa kan ki fada zama tare baice haka ba. Babu wacce zan saka akan wata cikin ku kun san da hakan amma kun kasa ba kan ku lafiya tun ina iya lankwasa Rahama kan hakan gashi yanzu itama harta iya. Tace ai dama nasan bazaka taba ganin laifinta ba nice dai mai laifin kullun ba ita ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 85 Suna ganin likita ya dan dubata tare da tambayoyi sai maganan mu yazo daya yace yana ganin duwatsun ciki ne ke damun ta. Amma suje suyi hoto a gani ya rubuta masu takarda zuwa wurin yin hoto din suna hanya tace Allah dai yasa ba hakan bane masu bakin mugun fata ga mutane kawai. Haushi da takaici ya rufe shi bai samu cewa da ita komai ba sunyi angama komai ya mayarwa likita da takardan nan dai ya tabbatar masu da zancen da na soma yi masu tun a gida. Ya kuma fada masu sai anyi mata aiki dole ancire mata shine samun saukin ta kawai. Haka suka dawo gida jiki a mace masu ina dakina na dan kwanta na samu hutu don haka ban san dawowan su ba gidan. Sai bayan nai sallah na fito falo wurin yaran na dan zauna dasu don har yanzu a cikin damuwa suke ban dade da zama ba sai ga Ihisan din ta fito daga dakin su tazo inda muke. Duk yarinyar ta ramay ta fada sosai don ciwon ya buge ta tana zuwa takai kwance nan kowa ya mayar da hankalin shi gareta. Nice na fara cewa da ita Ihisan ya jikin naki tace a hankali da sauki mummy nace an dai ga likitan ko sai ta tabe bakin ta tamai da kanta saman kujera tace thesame result kuka bada ke da shi ai. Nace ai dama na sani Allah ya sauwaka tace amin a sanyaye nan sauran yan uwan suka shiga gaida ita da jiki banda Amira da sai da taja aji wurin gaida ita din. Don babu gittuwa ko kadan a tsakanin su zaman su a wuri daya fitina da gaddama sukan tayi ba mai son wani ya fishi. Jinior ne ya shigo falon yake cewa dani little mun kaina na min ciwo tun dazun nace subbahanallahi shine bakai magana ba jinior na jawo shi zuwa jikina ina dan taba kan nashi a hankali. Sai Amira tace dashi zo nan may yasa tun dazun kaki fadi gashi daddy ya tafi asibiti kai wasu shine baka bishi ba. Shiru nayi na kyale yaron yaje wurin ta din naga may zatai mai don ina lura da ita irin yadda take wani kula da yaran Ala dole itace keda nauyin kula da su din yanzu. Wanda nasan ba huduban kowa bane sai na yan uwan uwarsu da kawayen ta da sukai mata a wurin zaman makoki. Yaron dai bai tafi ba yai kwance saman jikina ta dako mai wani tsawa tana fadin bada kai nake yi ba ne dan abu kaza kawai. Idona ya rufe nace da ita Amira kina da hankali kuwa kada na sake jin kin zagi dan uwan ki da wanan mugun kalamin ranki zai baci. Wani kallo ta watso min irin na raini abin ya bani mamaki sosai amma sai na daure na share ta kamar ban gan ta ba na mike na je don na daukowa yaron magani ya sha. Kafin na dawo na samu har ta kaiwa yaron rankwashi aka tana mai fada shi kuma ya turo baki yana ramawa. Nace haba Amira wai may yasa bakyaji ne ki rabu dashi mana kinga baida lafiya ko. Sai Jinior din yace ban mata komai ba take duka na akai wai na daina karban abu a gurin ki zaki kashe mu ne bakya son mu nace bana yi shine take dukana. Na juya gunta hannu a sagale dauke da maganin dana dauko nace Amira nice zan kashe ku ko wa da zan kashe ku aida na kashe ku tun a baya ina kika samo wanan magana irin haka babu dadi ji kuma ? Nace ki daina wanan irin halin har kina fadawa yan uwan ki baida kyau idan wani yaji zai maki wani fassara na jahilai ne. Na zauna na bare maganin nabawa yaron tana zaune tana cicika tana batsewa ban dade a wurin ba na shige daki sai ga jinior ya biyo ni dakin nan ya kwata a saman gadona sai barci ban fito ba ina dakin a zaune ina tunanen wanan hali na Amira yadda zamu kwasa nan gaba da ita a hakan da take min. Tsawon wani lokaci sai ga daddy ya shigo dakin na dago daga kwance ina mai sannu da zuwa bai karba sai naji yace dani. Rahama baki da tausayi ne ko baki da imani ne har yaushe uwar yaran nan ta rasu da zaki fara saka yara gaba ds fitina haka ? Bari kiji bake ba duk mai son mu zauna lafiya a gidan nan wallahi ya guji batawa yaran nan rai in bashi ko waye zan iya saba mai a kansu. Ke yanzu baki kunyan ace tun yanzu har kin fara daukan alhakin yaran nan haka ba dama mutane sun fada min haka amma naki yarda da maganan su . Don ina zaton zaki dubu irin halarcin da uwarsu tai masu ki kwatanta ki rike min su amana kamar yadda tai maki a rayuwanta. Tun daya fara magana sai kallon mamaki nake mai don na kasa yin magana dashi don mamaki daya kamani. Ban ma san jinior ya falka ba sai naji yace daga bayana daddy kaga Amira ta dake ni ko don kawai nace wa little mum ta bani magani kaina yana ciwo shine tace wai na daina karban abu a gun mum zata kashe mu ance duk abinda ta bamu kada mu karba wai. Shine don nace da ita banyi ta dinga rankwasa na a kai kuma kan yana min ciwo da mum tazo na fada mata shine tace Amira ta daina halin nan ba kyau ita bazata taba cuta muna ba Amira ta daina idan anji za, a dauketa a jahila. Bayan mu ta wuto sai ta fara kuka tana fada wai mum tace mata jahila da kukan ta zai kara min ciwon kai na dawo nan na kwanta. Ya dago kai ya dan kalle ni yaga na sadda kaina kasa cikin damuwa sai jikin shi yai sanyi yace da yaron yanzu kan ya bar ciwon ko yanayi har yanzu ? Yaron yace dashi ya daina mum taban magani na sha shine nai barci yanzu naji muryan ka na tashi in fada ma Amira ta doke ni kuma kaina na min ciwo. Yace da yaron ka bari zan ganta nai mata magana bazata kara dukan ka ba a gidan nan daga yau, yaron yace dashi na gode daddy. Ya juya ya fita daga dakin wasu kwallan bacin rai suka silalo daga idanuwa na ba wani irin nadama dana sani takaici da kuma tausayin kaina ne ya rufe ni a lokaci daya na rasa cikin wanan dana lissafo wanda yafi min girma a cikin sa. Zama nayi a wurin na darji kuka na mai isata sai da Aisha suka shigo da haidar ne dakin na tsagaita ta miko min yaron tana fadin anty kinji Amira. Ashe haka take da munafunci wai fa sai da taji motar baban su ya shigo ta fara kuka, shi kuma yana shigowa ya samu tana kuka ya fara fadin may akai maki wa ya taba ki tace wai little mun ce daga magana kawai ta dinga zagina tana min fada bata ko karasa ba ya juyo zuwa wurin ki Ihisan na ganin haka ta mike zuwa dakin su nasan uwarta zatabawa labari a dakin. Nace Aisha babu komai akwai Allah yana gani ai idan cuta masu nakeyi kudai ku kama kan ku da diyan shi don Allah ki kuma jawa Atika kune ko yaushe. Tace ai ina mata fada kullun anty nima na fahinci kamar za, a samu matsala da ita tun zuwan ta naga yadda take nuna muna. Tun wanan lokacin na kama kaina sosai da yaran bani shiga harkan su sai ya zama dole duk da dai su diya mazan basu nuna min komai muna normal yadda muke dasu a baya. Bana fita falo kamar baya dana dawo ina dakina sai yaran kuma suka tsiro bina dakina suna taruwa a can muna hira dasu in ka debe ita Amiran dakan zauna a dakin su ita kadai. Yau ma zaune nake na barbaje a saman gadona ina aiki a system dina baba da jinior suna kwance daga gefe na shi baba barci yake shi kuma jinior ya samu wayana yana game a cikin sa sai Nasir dake kwance saman dogon kujera shi kadai Aisha Atika da helen na kasa zaune suna zuba hiran su. Sai ga daddy ya shigo dakin yana saye a cikin kananan kaya a jikin shi kayan sun mashi kyau sosai a jikin shi. Nan yaran suka shiga gaida shi yana amsawa suka fara mikewa suna barin dakin daya bayan daya. Ina zaune a inda nake na dan dago kaina na kalle shi saudaya na mayar da kaina ga abinda nakeyi ga system din wurin aikina. Sai da yaran suka gama fita daga dakin ya dan kara takowa zuwa tsakar dakin yana cewa dani Rahama maganan da nai maki akan Amira yasa kika tsiro da wasu halaye a gidan nan. Kin fa sani yaran nan dole ne na dinga saka ido ga damuwan su ana tsawatawa don kada suga uwar su bata gida an fita batun su ko ana cuta masu mussanman ma ita Amira din dake da wayau a cikin su. Jin abin da yake fadi bai sa na daina abinda nake ba naci gaba da aikina kawai yake cewa ba dake nake magana ba ne kinyi shiru. Nace ba shiru nayi ba daddy ni dai nasan ko uwar yaran nan tana a raye ba zan taba cuta masu ba balle yanzu da bata da rai ace kuma na ni Rahama ce mai cuta masu kuma. Yace dole ne na dinga yi ina tunatar dake a kan hakan din kada suga ba ai masu daidai a gidan nan. Nace ni ai bance wani abu ba ko laifi ne nai mata don ta daki dan uwan ta na tsawata mata ta fada maka na kuma daina in dai nice duk abinda zatayi ko zasuyi iyakata ido dasu yanzu a zauna lafiya. Yace wanan kuma magana ne don a wurin ki suke ai yanzu ina na samu wa yan nan din ba a gunki ba na gansu yanzu. Nace bazan hana su yi komai ba a wurina idan kuma suna son abu har in ina dashi zan basu bazan taba hana su shi ba. Fada daine na daina yi masu balle ya zama min laifi kuma a gidan nan ina fadan haka na dukar da kaina naci gaba da abinda nakeyi. Don na fahinci akan yaran nan idan ban kai zuciyana nesa ba zamu samu matsala sosai dashi a zaman mu kan yaran. Kamar zai yi magana sai ya juya ya fita na dago na bi bayan shi da kallo take wasu hawaye suka dan silalo min daga idona. Da sauri na mayar dasu a inda suka fito don idan na biyewa abinda ake shuka min ruwan idona zasu kare ga banza a gun kuka. ********* ********* ********* Tun wanan ranan na kama kaina sai dai duk wani abinda ya dace mace taiwa miji da yaran ina masu ban daina ba har yanzu ina yi. Sai dai ita Amira din ce ta tsiro da wani sabon sallon wullakanci ga su Atika zata shige bandaki tai shiru a ciki sai ta sa yar uwa makara. Ko kuma ta zauna taki shiryawa da wuri sai sun makara idan sunje makaranta su sha duka kan latte. Ranan Atika ta samay ni da kukan ta take fada min cewa ga irin abinda Amira ke mata daga karshe dai hakkuri na bata tare da ja mata kunne nake cewa daga yau ta bar dakin ta dawo dakina mu zauna tare ta barsu can da su Aisha a dakin. Aiko Amira na ganin haka idan ta fito sai dai ta samu tayi wanka ta shirya sai ta shiga nuna fushi a hakan kuma. Ranan dai zasu tafi makaranta sai suka saka Atika gaba da gori da zagi har takai ga bada amsa sai ta kwashe ta da mari kawai. Sun dawo sai ga Atika tashigo daki duk ta ramay tayi wata zurum da ita wai Amira ta mare ta ta fada min duk yadda sukayi da ita din hakkuri na bata na sha alwashin canza mata makaranta na dinga biya da kudina zancen gori ya wuce hakana. Washe gari da zasu tafi bata bisu ba don na hanata ban fada wa kowa ba na dauke ta sai wani makaran ta dake kusa da asibitin mu na kaita can nai mata registration a nan tun rana aka bamu uniform da littafan ta don akwai yarinyar da hakkuri. Tun da suka ga haka suka dauki fushi ita da Ihisan sukayi suka gaji shi daddy bai sani ba sai ranan da zaitafi kano ya fito da safe ya ganta a cikin wani uniform. Yake tambaya ya haka kuma sai Jinior ke fadin ai an canza mata makaranta ne don su Amira da ihisan suna dukanta a hanya idan zamu school ko zamu dawo. Yace ke Amira duka fa shine aka canza mata school ban sani ba kamar zaiyi magana sai kuma yai shiru ya sallami yaran yana shiga mota na fito a cikin shirina yaga Atika ta bude mota na ta shiga yana dai kallon mu suna magana da Hindatu kus kus kus a gaban mota na dan tsaya daga nesa na kara yi mai Allah ya tsare hanya na juya na shiga mota na riga su fita daga gidan. Abin da na fara hankalta dashi shine yawan zuwa kano da yake a wanan lokaci da yake nasan dai wata kila wani business ne yake a can yanzu don shi dan ujula ne. Ashe ni abinda ban sani ba wai aure daddy ke nema a kano din tun rasuwan anty da wata daya aka fara zancen tun bai mayar da hankali ba har yazo ya mai da kai ga zancen. Mun kai asibiti na samu alheri na jira na wai mun samu takardan zuwa kara karatu mu kananan likitoci har mu goma kuma ina daga cikin su. Nai murna don ko ba komai zan dai dan daga nabar wurin na kwana biyu ai. Sai dai abinda nake ji shine daddy don nasan da wuya ya yarda da hakan ba karamin kwasa zamuyi ba akan zancen. Ban fadawa kowa ba na dunkule maganan a raina har ya dawo sai daya dawo da kwana biyu na na tun kare shi da zancen karatun dana samu din. Shiru yayi kamar bai jini ba ya kyale ni nagaji da zama na mike nabar wirin dama nasan za a rina dashi kan tafiya wanda ba komai zai kara sawa ya hanani ba sai zancen yaran shi dake wurina. Wanda rikon ba dadi nake ji ba gareshi da yaran don wani lokaci sai sunyi kamar sun hade min kai sai daga baya Nasir ya zamay ya dawo hanya ya dinga zagin Amira din sai na hana shi. A bakin gajiye na fara jin zancen auren daddy din don sunyi fada sosai da Zulfa da yaje akan maganan a nan Gajiye ta samu labarin har take fada min. Muna gama waya da ita na kira Zarah a rikice ina fada mata abinda naji tace aure fa Rahama nace bari ke dai Zarah. Take hankalin Zarah yai mugun tashi zakace itace ake son yiwa kishiya din ba ni ba nace da ita haba nifa ban damu ba Zarah tunda ba a kaina zan zauna ba take cewa Rahama ai dole in damu don ko wayan nan na gidan yaya kika kare dasu balle wata can don ko ita da sunan ki zata shigo gidan. Tunda hakkurin ki yasa ana ganin cewa kece star din gidan ba wanan shegiyar kyamusassan ba dake juya shi son ran ta. Ina ganin ranan ba ni kadai naji zancen ba don naga sun kwasa da shi da hindatu a bakin ta naji sunan matar tana cewa ka rasa wacce zaka auro sai Raliya ? Raliya da take yar duniya na karshe kowa ya sani yace idan na kwaso ta in a kanki zata zauna sai na gani ba a aure ke aka auro ki. Ina jin haka naja bakina nai shiru ban nuna komai ba ga zance nai kamar ma ban sani ba sai dai ana cikin wanan rikicin ne kuma na fahinci na samu ciki. Naso na zubar sai dai wanan ba a boye yazo min ba don bana son kamshi ko kadan rana yana sa turare amai yazo min na shiga bathroom din shi nai ta sharara aman. Koda na gama na dago yana tsaye a bayana ya kura min ido nai kamar ban ganshi ba na wuce shi nazo na zauna a bakin gado. Yace Rahama na dago kai na kalleshi yace may ke damun ki dama naga duk kwanakin nan kina wani rama a tsaye kin wani fada sai farin da kikayi. Na ce a wahalce lafiya ta kalau yace bai yarda ba dole na auna kaina ya gani ban so ba amma dole na auna di yana tsaye yana kallona har na gama. Can ya nuna min postive akwai ciki ke nan wata biyu da kwanaki sai naga yai murmushi yana cewa wanan karon ba boye Allah ya kama min ke. Cikin ya sako min barci da kasala sai son shan maltina mai sanyi koda yaushe haka yasa na kasa boye cikin ga kowa. Sannu a hankali nake lalabashi zancen zuwa karo karatuna har lokacin bai yarda ba da zancen ranan da nai magana yake cewa dani yanzu wanan din dana yarda kikayi baki gode ba ke nan Rahama ? Shine har zaki tsiro min da zancen zuwa wani kasan bako nan kasar ba yin wani karatu can ni ba namijin tace bane balle duk lokacin da kikaga dama ki tsiro da abinda ranki ke so. Na marairaice nace idan na bata maka rai daddy kayi hakkuri ba wai dan in bata maka rai na tsiro a gun aiki ne aka bamu wanan daman na zuwa kara karatun. Ka sani dole dama aikin mu sai da hakan ko yaushe don samun ci ga ba amma tunda baka so har na bata ma rai don Allah kayi hakkuri dani. Bai min magana ba har na gaji da zama na mike zan fice daga dakin yace ina kike son zuwa a haka kina wanan wahala da karamin ciki a jikin ki ? Nace dashi daddy Allah ne ya bani wanan daman ai akwai wa yanda na sama suna so amma basu samu ba ni na samu da zuwa na shiyasa kaji na matsa ma da zancen. Yake cewa dani idan haka ne ki bari zanyi shawara shi yasa nake son kara aure tunda naga ke ba batuna kikeyi ba yanzu daga zancen yaran ki, sai na aikin ki shike gaban ki kawai. Nace haba daddy nice ban kula da kai kuma kaima kasan ai nafi ba da muhinmanci a kan ka sama ga komai daka lissafa yanzu. Murmushi naga yayi kawai don ban nuna komai ba ga kalman auren da ya furta din zai kara ina zan nuna ni dake lalashi a barni naje gun kishin banza na bata zancen nawa. Kishiya ce dai yai niyar karawa ba fasawa zaiyi ba don ni ban ma da bakin cewa wai zanyi wani magana a kan karin auren nashi. Haka nai ta hakkuri ina danne zuciyana kan zance gani ina fama da kaina ciki ya sakani a gaba da fitina komai nacu in ba dan maltinan nan ba sai na amaye shi. Ranan daki ya isheni da zama na dawo falo a cikin yara na zauna muna hira ina kwance na sa dan dabino ga bakina don kada miyau ya taru min a bakina da yawa. Daddy ya shigo ya samay mu a hakan suka shiga gaidashi yake cewa nan kuma yau kuka fito nace wallahi dakin naji yana min kamshin turare shine na fito. Yace wanan cikin yazo da nashi kalar daban naga na yaran nan ba haka kikayi ba a lokacin nasu cikin. Daga baya tace ciki ciki fa ciki kega Rahama din ko may ta tuna sai ta sauke hannu data dafe kirjin ta dashi ta nufi dakin ta da sauri. Kowa falon kallon mamakin yadda ta razana yake mata sai muka bita da kallo na dago kai nabi daddy da kallo mai nuna kagani ko . Ya girgiza kan shi kawai ya nufi dakin shi cikin mamakin ta ashe zancen bai kare ba sai bayan kwana biyu sukai rikici dashi. Tace ita sam bata yarda da zancen cikin dake a jikina ba don ba daddy yai min ba sai dai in nasan inda na samo shi. Yace cikin mamaki ban fahinci may kike nufi ba fa ciki ba nawa ko may kike fadi banji ba dakyau. Idon ta ya rufe tace eh nace ciki ba naka bane yaushe rabon ka da Rahama da zata kwaso ciki tace nakane harka yarda don idon ka ya rufe da son haihuwa ne zaka rungumi cikin shege data kwaso maka. Kau kau taji mari masu zafi har biyu ya sauka mata a fuska yace da ita stupid idiot munafuka kawai kin zaci kowa macucine irin ki idan bani nai mata cikin ba uba wa yai mata cikin ? Kila kin san sherin da kikayi ne na bazatai ciki dani ba yasa kika fadi hakan babu kunya a gabana don baki da mutunci. Har lokacin tana dafe da kumatunta inda ta sha mari don bata taba zaton haka ba a gareshi irin yadda ta daure shi tana ganin sai abinda tace yake aikatawa a ganin ta sai yadda ta juya shi yanzu. Sai gashi taga bazata daga gareshi take kuma gaban ta ya fadu wani tunane yazo mata tace a ranta kodai ya gane dan bakan da tai mashi tsakanin shi da Rahama ne ? Yaushe har tai sakacin da wanan abin ya karye bata sani ba bayan duk ranan girkin Rahama sai ta haka shi don kada komai ya kasance a tsakanin su. A dadafe taja kafanta zuwa dakin ta ta fada saman gadon ta wani kuka ne yazo mata a lokaci daya ta jawo wayan ta tana kiran mahaifiyarta cikin tashin hankali tana kuka. Uwar na dauka tace mama na shiga uku na lalace zulfa da ciki ga kuma Rahama da wani ciki ga shi wani auren zai kara mama wai may ke faruwa ne dani haka a lokaci daya sai ta sake wani kuka mai ban tausayi. Uwar tace kiyi shiru mana muyi magana na fahinta kina ta faman kuka haka may zan gane har mu san mafita gare mu. Dole ta tsagaita kukan nata take fadawa uwar a tsanake abinda ke faruwa da ita a gidan sai uwar tace da ita amma hindatu kin kai sakariya wallahi. Yanzu duk kudin da na kashe kina nufin na kashe su abanza har kika bari wanan shegiyar yarinyar ta sake kumsa wani ciki a gidan nan ke ki na zaune da ya daya tilo kina mata hakon gida ita da mijinta suna fita neman na kansu. Tace mama na shiga uku na halaka wallahi ga zancen auren nan ba fasawa zaiyi ba don ko wani sati yanzu sai ya shigo kano da wuya ta tsalake sati bai shiga kano ba gun bazawarar tashi. Uwar tace ni abin ma duk ya daure min kai wallahi ban san ta ina zan fara ba ma wallahi duk bakin sakacinki ne ya jawo muna ganin wanan balain son mijin kike kawai a baki kina nufin a haka har zaki samu ki mallakeshi ke kadai yadda kike so. Mun samu waccan ta tafi muna murna yanzu saura ita wanan hatsabibiyar yarinyar mai kama da shuuma ashe ita. Don Allah ayi hakkuri dani bazaku dinga jina ba don matsalar waya da nake dashi sai jefi jefi har zuwa lokacin da Allah zai kawo min mafita na samu waya. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 86 Abubuwa sun daurewa kowa kai a lokaci daya wai daddy zai auro banker mai aikin a bankin manoma na kasa. Matar wata yar bariki ce don ba yarinya bace sun taba soyayya da ita don unguwar su daya dashi unguwar iyayyen shi ke nan. Ita da kanta tai nai tayi bayan rasuwan anty da wasu kwanaki tace tana son ta maye gurbin anty idan ya amince a gidan shi. Gani take yanzu tafi karfin shi irin yadda ta waye tai kudi yadda yake jin labarinta a gurin Bashir, don haka koda ta bukaci hakan sai ya ce ta bari zaiyi tunane akai. Amma yawan turo mashi da sako da nuna kulawan ta yasa ya fara mayar da hankalin shi gareta. Hindatu ta shiga matsanacin damuwa sosai a lokaci daya abu ya taru yai mata yawa a ranta ga kishiyoyi da ciki ga kuma zancen auren da miji zai kara yi. Sai hauka take ta saci lanban Raliya a wayan shi ta kirata sukai cin mutunci sosai da ita abin ba dadi tsakanin su don sun zagi junan su sosai. Haka ma Zulfa suke fama da ita acan ba dadi kishi suke nunawa sosai a tsakanin su. Ranan suna hira da daddy kan abinda hindatu tai mata sai Raliyan ke cewa yanzu saura ita dayar matar taka naji nata kalar kishin a kaina su wa yan nan naji nasu ko. Daddy yai murmushi yace wai kina nufin Rahama ko wa tace sunan ta ke nan ashe yace da baki sani ba ashe ? Tace ni ina zan sani tunda ba ruwa na dasu sune suka damu dani da sun sani su kwantar da hankalin su don ni basu gabana sam. Yace indai Rahama ce kuwa ban tsan mani zaki taba jin bakin taba ga wanan zancen don ni kaina har yau banga wani canjin fuska ba a gunta kan wanan zancen. Tace man kabar cika baki akan mace yadda sauran sukai min ko ita nasan zata aiwatar da nata don haka itama ina jiranta inji nata kalan kishin a kaina. Bayan sun gama waya ne take tunane ko dai a cikin matan shi yafi so na ne da gaske kamar yadda take ji din tunda gashi da bakin shi taji ya yabe ni cewa ba na kishin ta in ba so ba may zai sa ya yabeni ni kadai haka dole ne ta fahinci waye wanan yarinyar da kyau ta san ta inda zata fito min da nata halin. ********* ********* ********* Kwana biyu bana jin dadi haka nake ta faman nukurkusa gashi ba dadi tsakanina da hindatu zaman kawai muke na doya da manja ba ruwanta da ni nima haka ba ruwa na da ita irin mugun kishin nan muke gudanarwa a gidan na kowa tashi ta fishe shi. Daddy ya dawo da rana don sudan yaje yai sati biyu a can yana dawowa ya samay ni cikin wanan halin na rashin lafiya sosai ya dauke ni sai asibiti don a dubani duk dana fada mai ina treatment a gida. Bai yarda ba sai da mukaje asibitin namu ya kaini an dubani anmin duk abinda ya dace ai min din don doctor Fatima muka samu tana ta min sheri. Muna hanyan mu na dawowa gida wayan shi yai kara har ya katse bai daga ba ni dai ina lafe a seat din da nake abu ya damay ni. Can aka kara kira ya dauka yana cewa hanya nake ina driving nakai Rahama asibiti ne ba lafiya nadawo na samay ta a kwance. Ko cewa tayi ya bani mu gaisa sai naga ya miko min wayan na gane may yake nufi na karba gabana sai faduwa yakeyi. Muryan ta kawai da naji sai da gabana ya kara faduwa sosai da sallama muka fara take tambayana ya jikin ance banda lafiya nace Alhamdullahi tace Allah ya sauwaka nace da ita amin. Nagode nace tace babu komai wanan baby yana baki wahala da yawa naga ko yaushe baki jin dadi murmushi nayi mata kawai nace haka yazo min wanan karon kuma. Tace Allah ya sauwaka nace amin nagode mukai sallama na mika mai wayan sukaci gaba da hiran su har muka kai gida nafita na barshi yana wayan shi. Duk da naji wani iri a raina ban dai nuna mai komai ba a fili na dake ne kawai na ciki na ciki a raina. Shi ya biyo ni da maganin lokacin har na kwanta don barci nake ji Alluran da akai min ya fara aiki a jikina ya kawo min maganin da aka bani har dakin nawa don dana rude a mota na bar mashi shi. Ina kwance yake cewa dani kisha maganin kafin kiyi barci na ce ai zan sha kawai na gyara kwanciya na yace dani tashi mana kisha nai shiru kamar banji shi ba. Murmushi yayi ta gane raina ne ya baci ya juya ya fita sai gashi ya dawo da goran ruwa mara sanyi ya kawo min. Yana fadin tashi ga ruwa kisha maganin na mike da kyat shi ya bara min ya hada min yadda aka zana min yabani na sha ina sha na koma na kwanta abina ya fita daga dakin. Bayan fitan shi ne Aisha ta shigo da Haidar wai yana kuka na ce ta miko min shi ta bani abincin shi in bashi. Yaron sai kuka yake na rugumay shi a jikina nasan nono yake so ni kuma so nake ma na yayye shi daga nonon. Kuka yake sosai dole na bashi nonon ya sha san nan aka samu lafiya dashi har yai barci a jikina tare mukai barcin dashi har tsawon wani lokaci. Dawowan yaran ne yasa muka falka nan suka cika ni da surutu dole na tashi na biye masu muka shiga yadda muka saba duk da ina jin jiki sosai. Na samu maganin da nasha yai min aiki sai dai bakina ne babu dadi ko kadan a lokacin amma dole na biye masu do ba barina zasuyi ba na huta daga mai kawo kara sai mai neman abu guna haka nake fama da lalurar su koda yaushe idan suna gidan. Na samu naji sauki na dan fara fita gashi zance tafiya mu sai karasowa yake amma har lokacin ban san may nake ciki ba ni da tafiyan ko zai barni na tafi ban sani ba. Kwana biyu naji zancen auren shi ba wani motsi haka yasa na dauka kila sun watse ne ni dai ba tambaya zanyi ba balle naji may ake ciki. Abban Anty baida lafiya wanan dalilin yasa muka shiga kano muka duba shi na zagaya dangin ta dasu suka gansu nan na barsu na shiga kauyen mu a gurguje ban kwana ba na gaida su. Nake fada masu zancen tafiya na da zanyu zuwa karo ilimi a kasan turawa sunyi murna sosai da jin haka sai dai maigari ne ke tambayana yaran a ina zasu zauna su nace dashi shine dai ban sani ba amma dai duk yadda za, ayi zanyi naga anyi yadda ya dace sunyi min nasihohi yadda ya dace akan auren da sukaji yana batun karawa din. Ina ta ce keta kara kwantar min da hankali kan zancen auren ta tausa na da kada na yarda na nuna komai na barsu suci kan su tace dani. Kin dai san ba fasawa zaiyi va tunda ya riga da ya saba da zama da mata hudu ko da bai auri wanan din ba wata zai auro maku kuma dole ku zauna da ita din don dole tunda ra ayin shine kuma zaman shi kukeyi din. Kedai karamace a cikin su duk ita ma wanan din da zai auro din ance ta girmay maku ga shekaru dukkan ku. Don haka keda kike karamar su ki zama may hangen nesa a kan su kece zaki zamo may sanin ya kamata kada kice zaki ja da hukuncin ubangiji akan abinda ya halasta akan mazasuyi wanan dama ne da Allah ya basu akan may mu mata baza mu dinga daurewa ga hakan ba mu tsaya a matsayin mu na mata akan su. Kada ki yarda ki zubar da kimar ki a idon wace zata shigo din wurin nuna kishin ki a fili harta samu daman da zata shigo dake a ran ta. Haka shine ke kawo baraka a rasa samun zaman lafiya a tsakanin abokan zama gida ya koma kamar gidan da babu tauhidi ha cikin sa. Tunda inna ta fara min wanan nasihan kaina yana kasa ina hawaye don nasihan nata ya ratsa min jikina sosai don gaskiya inna take fada min ba karya a cikin sa. Nace inna na gode insha Allahu zaki samay ni yadda kike so da yardan ubangiji ba zaki ji wani abin assha ba daga gare ni. Mun rabu lafiya dasu duk da a gurguje naje ji nake kamar kada na barsu a ranan mukai masu sallama na barsu lafiya muka dawo kano washe gari muka kama hanyan Abuja ni da yaran da driver daya kawo mu gidan. Mun iso duk na wahala a hanyya saboda warin petur din motan da yake hawa min kai wanka nayi kawai na samu wuri na kwanta sai barci. Daddy baya garin yaje calabar wurin wani aiki don haka nake da isasshen hutu nai barci sosai sai dana falka ne na iske miscalled din shi har uku a wayana. Wanka na yi nai sallah magariba da isha, i na fito ko zan dan iya cin abinci na samu Aisha ce ta girka masu abinda zasuci don ita matar gidan ko kallo bamu isheta ba ma. Na zauna naci sosai don jelof din yai min dadi ai inda naci nan na kwanta sai barci don duk jikina yana min ciwo sosai. Mun kai kwana hudu da dawowa ya dawo garin yana zaune da yara sun kewaye shi na fito daga dakina nazo yi mashi sannu da zuwa dutyn yamma zanyi a ranan don haka ban zauba ba na wuce zuwa shiryawa. Karfe uku bai min a gidan ba nai masu sallama na tafi aikin mu a kwai dadi akwai wahala don idan duty ya zagoyo kan mutum tun dai na dare shine matsala babba a gin mace. Tun daddy na fadan hakan har ya gaji ya kyale ni tunda yasan haka aikin ya gada dama. Ga tafiya yazo sai shiri nake don ya yarda da tafiyan nawa kwatsam sai naji zancen wai auren daddy da Raliya za a daura a karshen watan da muke cikin sa. Haukan kishi kan na gane shi a gun matan daddy don sai da ta zare masu yai muna kaca kaca hardani da ban fitar da nawa a fili ba ya hada yai muna tas ranan. Yace duk wacce bata iya zama hanya a bude yake mata zata iya tafiyan ta idan bata iyawa. Nidai ina zaune shiru banyi magana ba har ya gama na mike na shiga dakina na kwanta raina ya baci amma ina gudun in magana in bata batun tafiya na don ni buri na shine naga dai na samu tafiya karo ilimina don shine mafita a gare ni. Don shi na fahinci ba mace a gaban shi in zaka zauna ka biye mashi babu abin da zaka tsinta banda bacin rai da takaici kawai . Wanan auren kamar wanda zai auro budurwa yake jin shi don yadda naga yake rawan kafa akan shi. Sai kuma kyalewan da nayi wai bai mashi dadi ba nan kuma ya samay ni daki ina kwance na dawo aiki na gaji ban dai fara barci ba a lokacin. Yai tsaye a kaina yana cewa wai ke may kike nufi ne naga ana magana har yau banji may kikace ba kan maganan koke baki da wani shiri ne akan hakan. Na dago cikin natsuwa nace dashi daddy ni yanzu may zance kuma aure daine kayi niyar yin Allah kuma ya halasta maka yin shi ni wacece da zance wani abu ga hakan. Ba a aure ni aka auro ni don may zan tsaya ina tayar da jijiya kan abinda bai shafe ni ba ta shigo mana Allah ya kawar da shedan a tsakanin mu kawai. Shiru yayi yana kallina sai can yace naji amma idan kina da wani magana you are free to talk about it. Nace ni da ke shirin tafiya daddy har wani shiri zanyi kan hakan sai dai idan Allah ta dawo damu lafiya in naga ina son wani abin sai nayi. Yace haka kika ce nace shine kawai magana na ubangji ya bamu hakkuri da junar mu kawai yace yayi Allah yasa mu dace nace amin. Duk yadda yaso yaji bakina kan maganan ban yarda na furta komai ba shine yake wa tantama anya kuwa ma ina son shi kuwa kowa ya tayar da hankali amma ni ko gezau bai taba jin na furta kalman komai ba da anyi magana na kawo mai nawa hujjan ya rasa bakin magana. Su kan an yi lissafi har sai da yai mamaki may ye wanan haukan haka da suka lissafo mai duk da sabbin kujeru ne a gidan amma sai da hindatu ta lussafo wai a sake wasu kayan gidan dana kitchen. Ya fada masu gidan ta daban zata zauna amma hakan bai sa ta yarda ba da shi don dai a zauna lafiya yace yaji za, a sake wasu. Nan kuma suka bullo da cewa basu yarda da zancen zama wuri daban ba ai yaudara ne wanan ta dai zo inda kowa yake a zauna ana ganin komai. Nan yace wanan kuma tsarin shi ne va nasu ba don haka yadda yake so ke nan haka kuma za, ayi din ba zai kawo ta nan ba inda muke. Ni dai nawa dasu ido sai daga baya ana gap da daura aure wai hindatu tana neman shiri da amarya akan su hade min kai. Take cewa wai dama ita ba komai takewa rigima ba sai don kada ta shigo tai masu irin yadda nai masu don yanzu in bani ba daddy baijin kowa a ranshi. Harda fadawa amarya wallahi ta shirya sosai don mu yan kauye a shirye muke wai har gida naje na shiryo a kan ta don kawai zancen ya ruguje. Da yake mu mata hankalin mu kadan ne in anzo ga maganan kishi sai ta yarda da shirin su ta hau ta zauna a kai cewan da sukai mata wayon tsiya ne dani shiyasa ba aji na furta komai ba. Ranan ina kwance sai ga waya da bakon nomba na dauka da sallama na ba ko gaisuwa sai naji ance dani Rahama ko nace eh. To na kira ne na fada maki aure da yusuf ba fashi a tsakanin mu don dani ya dace bada ku ba don banga wata dafa cikin ku data dace ace tana matsayin matar shi ba. In kyau kike takama dashi nafiki in kurciya kike takama dashi nafiki in kuma dan aikin likitan da baikai yakawo bane kin san nafiki don ni yanzu kiris ya rage na zama manager. Zataci gaba nace to Allah ya taimaka ni bani takama da komai sai Allah da manzon shi dama ba sai kin fadi ba dake din ya dace don ni bakowa bace sai boyar Allah mai tsoron shi kuma diyar tallakawan kauye don haka kiyi hakkuri idan ma wani abin kikaji nayi maki har kike wanan magana. Tace ke rufa min baki munafuka kawai kina wani simi simi kamar ta kwarai dake sai dai ki mashi shida kika shanye amma bani ba. Kashe wayan nayi don ban iya ci gaba da sauraren wanan kalamin nata Aisha na daga gefe na duk abinda take fadi tanaji tace dani anty amma matar nan bata da hankali ne ko ? Nace da hankalinta Aisha hakan wai shine kishi ni bata gabana don nasan inda na aje ta tun farko matsalana daya shine shi daddy din ya nuna min wani abu. Amma tunda bai nuna min ba kin ga may zai damay ni da haukan ta bakina kawai take son ji kuma batajin shi indai nice. Ban nuna mai komai ba don ban fada mai ba ita da bakin ta da hira yai mata dadi take fada mai ai ta kirani ta zageni don taji abinda nake shiryawa a kan ta. Sai ranshi ya baci ya kashe wayan dip tai kiran duniya yaki dauka na shigo dakin bayan sun gama wayan. Yabini da ido a zaton shi zan fito mai da zancen sai yaga har nagama yi mai komai daya dace na samu wuri na kwanta bance dashi komai ba. Bayan na kwanta sai naji yace dani Rahama na amsa da naam yace Raliya ta kiraki ne sai nai murmushi kawai bance dashi komai ba. Yace tambayan ki nayi ta kiraki ko bata kiraki ba kuma yaya kukayi da ita din data kiraki din. Nace ta kirani daddy yace yaya kukayi nace kawai magana ta fada min nace da ita kuma nagode shike nan. Bazaki fada min abinda ta fada ba ke nan nace daddy ba komai bane ai sai neman baki a yadda na dauki maganan don tace ga abinda nai mata kuma. Sai naji ya rungumoni yana sauke ajitan zuciya yace ba zan dauki wanan halin ba na fada mata tun farko kuma wallahi sai ta fada min da maganan ya fito harta samu nombanki ta kiraki. Nace daddy indon ta nice kada ka dauki maganan da zafi abinda aka fada mata akaina ne tai amfani dashi ba tare da ta gani ba. Yai shiru ya fara bin lafiyan jikina ni ba ma wani dadin kimai nake ji ba har yayi ya gama mukai barci. Washegari tayi kira harta gaji yaki daukan wayan abu wasa wasa taga zance nadon baci a tsakanin su haka yasa ta shirya taje gidan mahaifan shi takai karan shi gun su hajiya. Nan hajiyan da ake jikawa ko yaushe ta kirashi tana fada dashi wai zai watsa masu kasa a ido sai da yaga lokaci ya gabato shine zai masu hakan. Yace hajiya idan ba ta fada min wanda ya fada mata maganan nan ba wallahi sai dai mu watse sai ta fada min wanda ya bata nomban Rahama da har zata kira min mata taci mata mutunci. Ahaka take son na sata cikin iyalina gashi tun bata shigo ba sun fara fitina dakowa gaea dai ayi hakkuri kowa ya hakkura ba zan daukowa kaina wani fitina ba bayan wanda nake ciki. Jikin su duk yai sanyi nan hajiyan ta tursasa ta sai da taga da gaske zata rashi ne tace itafa hindatu ce ta kirata ta fada mata kuma ta bata nomban don ta gwada Rahama din ta gani. Sai bayan sunyi wayan ne amsan data bani ya sa na fara fahintar ko dai shiri ne kawai sukai min gashi yanzu zata ja min tsiya . Hajiyan tace kin san halin shi idan ya hau don haka kikirashi ki fada mai komai a fahinci juna don kada su ja maki tsiya. Dole tai mai text akan zata fada mai komai ya dauki wayan ta kirashi tafada mai duk yadda sukayi da hindatun a waya. Tsuki ya ja ya kashe wayan batare da yai mata magana ba hankalin ta ya kara tashi sosai dashi duk kuma yana mata ne don ta shiga hankalin ta dama don shima ya kamu da son ta. Ina daki da dare ranan yace nazo fali yana nwman mu na mike dakyat na fita zuwa falon na samu hindatu a zaune ya daure fuskan shi ba rahama a gare shi. Gabana ya fadi na samu wuri na zauna na gaidasu ya amsa min da kyat gabana ya fadi don ban san may nayi ba kuma. Can yace hindatu ta amsa a bashe dashi yace may kika fadawa Raliya gamay da Rahama ? Tace may ta fada maka nace da ita yace abinda kika fadi yanzu zuwa gidan da yarinyar nan tayi duba jikin mahaifin marigayiya shine kikace wai taje gida yin shiri kan auren mu. Tace ita Raliyan ta fada ma na fada mata hakan yace in kina mussune na kirata ta maimaita da bakin ta. Tace in tace na fada na fada din karya nai mata wani abin taje yi in ba shi ba can din ko may ye bamu sani ba kaine dai da idon ka ya rufe baka gane wa tunda ana yaudaran ka. Take ranshi ya kara bacu yace munafuka algunguma wacce bata kaunan alheri dani kina zaton kowa irin kine ko may ? Kin dauka duk wani shetin dakike yi ban sani bane kina ganin kin shiga tsakani da Rahama babu moriya atsakanin mu shiyasa da tai ciki kike cewa cikin shege ta kwaso min tunda kin san sherin da kikayi a tsakanin mu ko ? Nace cikin shege kuma ubangiji Allah ya tsare ni daga zina ko banda aure balle da aure na ya daga min hannu yace yi min shiru wanan munafukan may ye bazata iya yi ba kike gani. To bari kuji wallahi ba wacce zata kawo min rashin kwanciyan hankali ga iyalina na kyaleta koma wacece a cikin ku. Don haka wanan shirin naki baici ba sai ki sake kulla wani tunda nasan ba fasawa zakiyi ba don halinkine sheri a jinin ki yake na sani. Ki sani dake da Raliya har ma da ita Rahaman da kuka saka a gaba duk wanda yace sheri da munafunci zai kawo min yana gidana zaman lafiya idan na sake kama mutum zai dauki mumunan mataki akan mai shi. Nan ta shiga yan koke koke wai Raliya nadon kulla mata sheri don ta shigo gidan shine zatai mata kazafi ? Yace kazafi waya bata nomban data kira Rahama din dashi abindai baiyi dadi ba a tsakanin su. Nan na barsu na shiga dakina raina a bace na rasa may naiwa wanan matar a duniya tasani gaba haka da kiyayyan ta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 87 Bayan komai ya daidai Raliya ta, ta aiko mutane gun shi a bashi hakkuri gatsau mukaji wai an daura aure ranan Jumma, a da shi da ita. Ni banga wani abin tashin hankali ba tunda mun san da zancen dama amma su o,o kan anyi masifa wai bai fada masu zasu daura aure ba ranan. Nidai ina ji na fada daki ja dauro alwala nai nafila na roki ubangiji ya haushe ni kan duk wani mai kina har ma da mai sona din Don yanzu yan uwan daddy sun kasu kashi biyu don irin abin duniyan da Raliya ke narka masu ya rufe masu ido sosai don ba karamin dukiya take kashe masu ba wurin neman son ta gare su. Sai faman zagin mu akeyi wai yanzu ya samu mata data dace dashi mu duk dama ba wacce ta dace da zubin shi gata yar gayu ga ilimi ga wayewa da arziki. Maganganu dai ba dadi akan mu kamar yadda idan za aiwa mace kishiya take jin su haka muka din ga jin zagi daga dangin miji masu kwadayi. Amira da murnan ta har party ta hada wai baban su yayi aure ance a gun matar zata koma su sha dadi a wurin ta. Ni dai ina sauraren dawowan shi garin inji ya kwashi yaran ya mayar gun ta kamar yadda naji suna fadi din. Ranan da daddy ya dawo duk muna gida ba wanda yasan cewa zai dawo ranan amma duk da haka ina cikin shiri na kamar kullun duk da banjin dadi amma ina da kwaliya a jikina. Dogon riga ne dinkin Dubai mai duwatsu a gaba da kasan rigan sai dan kwalin shi dana daura akaina. Kwance nake saman three seat ina shan iska yaran nata zuba min hira sai hindatu da ke zaune kamar an fito da ita tana waya kusa da yarta. Yana shigowa suka mike da murna suna mashi sannu da zuwa sai ganin mace nayi a bayan shi suna shigowa tare don ni ban ma san ta ba dama. Na mike da kyat zaune ina mai sannu da zuwa sai naji yana bisimillah shigo mana ga wuri ki zauna hindatu dake shirin gaidashi sai gaisuwan ya makale mata a bakin ta. Yace da Jinior dake makale dashi da baba Jinior fa sabuwar mummy tazo gaida ku ko kuje ku gaisa sai Jinior din yaki yace a, a baba nikan ban santa ba gadai mummy na nan little mum ban son wanan sabuwar mum din. Murmushi yayi ya dan kali inda take tana kokarin zama nasan yaji nauyin maganan da yaron yayi mai ne. Yace ksi kai Jinior kaine fa mijin nata kake fadin baka son ta kuma yaron yace ban son ta little mum nake so daddy sai yayo kaina. Duk muna zaune muna kallon su sai bin mu da kallo takeyi da gidan da muke ciki zaune. Baba da Haider sukayo kaina suka fada a jikina nace jinior go and greet her she is your mum too. Magana na baisa yaron zuwa ba sai cewa da yayi ban yi banyi she is not my mum na daka masu tsawa nace jeku gaida ta Aisha ta kawar da shirun da ta fara gaida ita sai sauran ma suka shiga gaida ita din. Nace Aisha dauko abin sha a kawo masu sai tace cikin wani ya mutse fuskaka No a barshi a koshe nake ni. Yace may ye ma, anan hakan may kika ci da zakice bazaki sha ruwan ba ance a dauko maki sai tai shiru. Bayan sun sha ruwan ta dan kurba kadan ta aje cup din a saman tire din ta dukar da kanta duk annurin fuskan ta ya gushe mata. Ashe abinda ya bata mata rai shine ganin da tai min tana takama da fari da gashi na shago sai taga inda na gaskiyan yake. Yaran suka fara sulalewa suna barin falon daya bayan daya ya saura sai mu kadai a falon daddy ne ya fara magana da cewa ina son duk ku ukun ku bani hankalin ku a nan. Ya koma inda take da fuskan shi yace Raliya yau dai ga ki Allah ya kawo ki a cikin iyalina da sunan zama kema don haka wa yan nan sune matana ga hindatu ga Rahama da fatan zaku rike junan ku amna a zauna lafiya. Falon yai shiru na wani dan lokaci can ya kara kurba ruwan lemon dake gaban shi bayan ya aje ne yace ko akwai may magana daga cikin ku in babu zan kai Raliya gidanta da zata zauna a nan. Ba nisa sosai da nan din kusan unguwa daya ne da mu nan din da inda zata zauna ita din ko akwai may magana na sake tambayan ku ? Shiru nayi ina kallon wayana don hankalina ma baya a kan su ko kadan ina abinda nake da wayan nawa tun fara maganan shi damu. Cikin firgici na dago kaina don jin ya ambaci sunana da sauri na amsa da naam yace bakiji bane nace ba magana kina ta faman kallon waya a hannun ki. Nace a sanyaye ba komai Allah ya bamu hakkurin zama da junan mu bisa amana da gaskiya yace Amin tare da dan furzo iska daga bakin shi. Mikewa yayi daga zaune yana fadin oyo muje na kai ki gida ko kada yamma ya kara yi muna anan din sai na dawo yace tare da fara hanya ta mike tabi bayan shi bataiwa kowa magana ba a cikin mu ta mike tabi bayan shi suka fice daga gidan duk muka bisu da kallon ikon Allah. Akan wanan tsohuwar yake wanan rawan kafan haka wa mutane wanan aiko marigayiya ta girma balle mu don dai tana da dan karamin jiki ne kawai ba a ganewa. Ni dai ban tanka ta ba sai ma Aisha da nake kira tazo ta kwashe cups din da suka sha ruwa dashi a falon. Sai faman tsuki take zubawa bandai tsunka ba ina daga kwance karshe ma mikewa nayi zuwa dakina suna ta zunduma zagi ita da zulfa da ta kira a waya. A raina nace nima haka suke zunduma min zagi na halittana yadda ransu yaso amma ni banga abin kushewa ba don shi ya gani yace yanayi ai ********* ********* ********* Duk wani rawan kafa da kika san namiji nayi idan ya kara aure shi daddy keyi abin ma zaban kunya gareshi amma shikan ko a jikin shi ma. Baya shigowa gidan sai goma da wani abu na safe idan ya dan zauna zai mike yace ya fita sai hindatu tace zaka dai koma gun amaryan ka dai. Ni damuwana shine inda zan bar yarana na tafi karatu don dai ba zan iya barin su gun hindatu ba gaskiya mutumin da bai iya kula da kansa ba shine zai iya kula da dan wani. Ina kwance daki tunda na dawo ban fita ba na kunna A C yana sauko min da sanyi a jikina idanuwa suna a lumshe kamar ina barci a lokacin. Ya shigo dakin dauke da wasu takardu a hannun shi kafa da ke mike ya dan ja yatsun su sai na bude idanuwa na na sauke su a gareshi. Yace barcin marance kike ko mai zaune na mike ina fadin ba barci nakeyi ba na dai kwanta ne kawai. Miko min takardun yayi na karba tare da dubawa pasphot ne na Aisha da jinior da baba da haidar a cikin ledan komai na tafiyan su an shirya masu. Ban san sanda na sake murmushi ba a fuskana nace masha Allah daddy kamar kasan abinda ke damuna a raina duk kwanakin nan ke nan. Yace na sani mana tunda zurfin ciki baya barin kiyi magana amma ni nasan dole ne ai ya damay ki a ranki. Na dago kai nai mashi godiya tare da cewa su sauran a nan gida zasu zauna ko may ? Yace na gama magana a kan su idan nan din baiyi masu ba zasu koma Kano har ki dawo wurin Zulfa ko hajiya na ina hakan yayi maki daidai. Nace eh yai min nagode nace sai dai doctor Fati ta roke ni na bar mata Atika a gidan ta ta zauna har na dawo. Ya dago da sauri ya kalle ni tare da cewa umm,umm don ita bani na haifeta ba za ai wanan shawaran ban sani ba ko may kada kice ki canza mata makarantan da kikayi bai damay ni ba a baya ido kawai na sa maki tunda ke baki iya fada min abinda ya faru har kika kai ga yin hakan gareta. Don ki nuna min ke ma yanzu wuyan ki yayi kauri kina iya samun kudin da zaki dauki nauyin su batare da ni ba. Ki dai tuna zaman yaran nan a wurin ki sai da amincewa na don in ba amince ba babu dan da zai zo ya zauna min a gida hakana na kyaleshi. Don naga kawai suna bukatan taimako ne kema haka zaman ki dasu akwai karuwa a gareshi yasa na barki ban maki magana ba. A sanyaye nace kayi hakuri daddy amma ni banyi haka da wata manufa ba sai gujewa bacin rai kawai don yadda yaran suka dauko yi mata zai iya haifar da fitina watarana shiyasa na canza mata makaranta din ba wani abuba. Yace naki ke nan idan kinyi laifin anyi magana saiu kice zakiiba mutum hakkuri akai to ni babin sson mace tace zatta shige min gaba a gidana kinji na fada maki. Shiru nayi har ya gama ya fita ban yi magana ba ya juya da bacin rai yabar min dakin na sauke ajiyan zuciya tare da binn bayan shi da kallo. Wani sabon surfa da Amira ta tsiro shine weekend sai tace a gidan amaryan daddy zatayi ni dai banyi magana ba iyakata ido sai ta dawo tana wani jiji da kai a gidan har da kokarin sake magana. Ba wanda yasan da zancen tafiya na sai da tafiya yazo gap ne aka sani saura sati mu bar kasan lokacin amarya takai wata daya a gidan. Na fahinci kamar har yanzu aikin ta yana kano zuwa take tana dawowa nan Abuja din amma dai bamuji a bakin maigidan ba. Gashi idan zata dawo sai ranan da ya dace ace nice da girki take dawowa garin sai dai naga da yamma ya shirya yace zai tafi gidan Raliya tana gari. Abin naci min rai amma naga kwana nawa ya rage na daga na basu wuri suci kan su aa tsakaniin su don haka na danne zuciyana nai shiru. Munje kano nai sallama da mutane muka dawo daren da zamu wuce naga tashin hankali gun hindatu ba ita kadai ba har da sauran matan daddy sai da sukai korafi wai yana kashe min kudi kamar ni kadai ce matar shi. Nasan ba plan din kowa bane na hindatu ce ita tanemi sauran da wanan magana ban bi ta kan su ba nikan sai Nasir da yasha kuka wai ba zan barshi ba in tafi. Daddy da kan shi yai min magana yaushe ne zan kai Atika din gidan doctor Fati ta zauna nace aii na jaye maganan yace bayan kkun kiitsa kuma ga yadda zakuyi zakice kun fasa nima naga hakan zaifi son barin ta a nan akwai matsala don haka kikirata ki sheda mata maganan yana nan. Nai mai godiya na kirata na fada mata taita murna nace masoya na asali ke nan sai bare yai maka abin alherin da baka zata ba ma a duniya. Na gama da wanan matsalan dake damuna na Atika yanzu banda sauran kunci a tare dani sai shiri na nakeyi na tafiya yawancin kayana duk dama na loda nakaiwa iyayyena da yan uwa na agida abu kadan na bari a dakina. Helen ma na mayar da ita gun wacce tabani ita amma akwai wata yar wajen aikin mu data karbi yarinyar kuma a hannun su. Washegari kukan da Nasir keyi ya sa hankalina yai mugun dagawa don zance bann taba ganin yana kuka haka ba sai naji jikina yai sanyi nace na fasa tafiyan kawai zan zauna. Na samu daddy da magaban aiko ya hauni da masifa yace akan Nasir zakice kin fasa tafiya kin san nawa aka kashe kan wanan tafiyan naki da yanzu zaki zo min da maganan rubish. In dai don Nasir ne ki bari nan da wata daya zan mai komai sai ya biyo ki bashi ke nan ba haka muka kama hanya ni ko sallama da abokan zama ma banyi ba don ba fuskan yin haka a garesu yadda muke. Jirgin lagos muka shiga mun kwana daya muka daga wani abokin daddy ne yai ta dawainiya damu don da yace dashu zamuyi tafiyan amma daga baya sai cewa yayi ba zai samu zuwa ba zaizo daga baya. Nasan matsala daga matan shi haka ban damu ba muka wuce abin mu tunda bukatana ya biya. Mun sauka lafiya a kasan na Germany inda aka tura ni karatun don an watsa mu ne ba wuri daya aka aje mu ba da sauran kowa da inda aka kaishi. Gida dan madaidaici aka kama muna har karatun yara sai da akai muna komai a kan shi na fara fita gun aikina na fitan da damuwan komai a raina na rungumi karatuna gadan gadan. Aisha zamu bari a gida ita da Haidar tai aiyukan gida daya dace ni da jinior da baba kuma mu fice wuein neman ilimi da ya kawo mu kasan. Idan mun dawo ni zan koya masu karatun addini sai wani lokaci mu watse sai kuma gobe haka rayuwan mu a can yaci gaba da gudana gwanin ban sha, awa damu. Watan mu hudu a kasan amma babu daddy habu dalilin shi sai dai can ba a rasa ba yakan dan bugo waya yaji lafiyan mu yadan yi hira da yaran sai ya kashe. Naso saka damuwa ga hakan amma nabawa kaina magana na mayar da hankalina ga abinda zai fishe. Ranan na dawo ina zaune da yarana a falo muna hiran mu a cikin raha da jin dadi sai ganin an turo kofa mukayi kawai. Gaba daya hankalin mu ya koma a kofan yana saye cikin kayan sanyi muka bishi da ido abin mamaki babu yaro ko daya da yai daukun ganin shi a lokacin balle suje su taro shi kamar an masu nasiha a hakan. Sai Aisha ce tai mai sannu da zuwa nikan kallon kallon muke dashi don watan mu bakwai ke nan yanzu da zuwa sai gashi ya ziyarce mu yau. Roku roku nake don cikin jikina yana ganuwan haihuwa a lokacin da kyat na iya bude bakina nai mashi sannu da zuwa. Yace Aisha kece baki fushi dani ke nan don naga sauran duk fushi suke dani ga alama ? Ban yi magana ba ya samu wuri ya zauna ya mika hannu baba yazo sai yaron ya noke ya nufo ni inda nake. Yace Jinior harda kkai fushi kake da daddy yaron baiyi magana ba yai shiru nace dasu oya a gaida daddy cikin harshen turanci. A sanyaye suka fara gaidashi sai dai basuje inda yake zaune ba komai na sha Aisha ta kawo mai sai dai ya kasa sha. Nan ya fara magana cikin karfin hali irin na maza wai nasa yaran sunyi banza dashi in ban hura masu kunne da kalaman banza ba akan may zasuyi mai haka. Nidai shiru nayi har ya karaci fadan shi ya mike yana tambayan Aisha dakina ta nuna mai ya shiga na mike da kyat nabi bayan shi. Sannu da zuwa na sake mai tare da tambayan mutanen gida ya amsa min a bashe da suna lafiya kawai. Falon nadawo wurin yaran don shi ya shiga wanka nai masu fada kan abinda sukayi ma uban nasu duk sukai min shiru. Ya fito ya samu wuri ya zauna lokacin muna kitchen muna hada mai abincin da zaici don bamu damu da girka abinci ba don mun saba da abincin can. Ban fito ba ina jin shi yana hira da yaran sai da muka gama komai na jera na shiga wanka lokavin sallah yayi mukai sallah. Sai bayan mu idar ne na samu zama a falon wurin su na sake gaidashi tare da tambayan kowa a gida. Yace duk suna lafiya haka muka zauna ba wani sakewa kowa da abinda zuciyar shi ke saka mai a lokacin. Sai dare mun kwanta ne yake cewa wai banyi murna da ganin shi ba gashinan har na fara sawa yaran shi kiyayyan shi a ransu. Raina yai mugun baci nace haba daddy ya kamata kai min adalci hakana please har fa nan makwabtar kasan nan kake da matar ka amma ka kasa zuwa ka ganmu don kana gudun bacin ran matarka ga yin hakan. May kaji nace maka ina ganin sam baisan nasan sun fito honey moon ba da ita sai da yaji na fadi sai ya fara yan kamay kamay da fada irin na maza idan basu da gaskiya. Wai dama yasan shi nakewa ni kasa nawa ya fita dani ina amarya nace nasan da hakan kuma ni hakan ba komai ba ne a guna ai. Don bakaji nai magana ba sai yanzu da kakawo wanan magana don haka a barni naji da abinda ke gabana ni ba kishi ya damay ni ba fatana naga na rabu da cijin dake jikina lafiya. Duk abinda mutum zaiyi ni ba ruwana don nasan akwai Allah yana ganin komai yace dana san bacin ran da zanzo na samu ke nan da banbar abinda nake nazo dubaku ba ai. Nace aini ba don ni kazo ba kadai zo watakila don yaran ka ne ko wani harkan gaban ka tunda nan din wurin zuwan ka ne dama. Shiru yayi bai sake magana ba muka kwana a hakan don a tunanen shi tunda yaji nai magana yasan raina ya baci sosai don shi kan shi yasa baida gaskiya. Banyi wani dokin ganin shi ba yadda ya tsanmata don a dadafe muke zaman da yai muna kwana biyu. Satin shi daya ya shirya zai koma sai gashi haihuwa yazo min da daren nan ana washegari ya wuce dole ya tsaya na sauka lafiya dana babba dashi na haifo mashi kamarsu dashi har ya baci sosai ga wani girma da yaron yazo dashi. Wanan karon Aisha ce mai karban jegon ita ke mun komai daga ni har yaron bamu da matsakan komai . Nan ya bugo waya gida yana sheda masu haihuwan nawa abu ga kishin mata sai aka juye zancen wai dama yasan lokacin haihuwa na yayi yasa ya tafi gun mu. Dako dadi suke ji yayi banza damu don kowa yasan bai je ba tun tafiyan mu hakan na masu dadi yadda yai watsi damu can. Duk da ba wani zaman dadi ne a tsakanin su ukun ba fitinane ko yaushe a tsakanin su ba sassauci ga komai yadda muka barsu haka ake. Don Raliya tai masu tazara sosai ga komai sunki kwantar da hankalin su su fahinci ta fisu iya zama da namiji sosai. Ashe bayan wucewan mu Amira can ta tare gidan ta ba dadi ko yaushe sai sun kwasa dole ya tattaro ta ya maidata kano don hindatu tace bata zama da ita tunda ta guje ta da farko. Shiko Nasir yanzu bai zama gida sai dare zasu ganshi tun uban bai farga ba har ya gane haka gudun kada yaron ya lalace mai ya mayar dashi Kano gidan kakannin shi da zama. Sai aka bar hindatu da yarta kawai a gidan sai masu aikin su gaba daya ya kasa hada kan gidan nashi yadda yaso komai na batun tabarbare mai. Zulfa ta haifi da namiji itama bayan mu tsakanin mu da ita wata daya ne da kwanaki sai da yaga komai ya koma min normal ya kara sati ya shirya bayan ya radawa yaron suna da Abdulrahaman. Ya koma gida Nigeria inda yaci gaba da harkokin shi na yau da kullun sati uku nayi na koma karatuna don ba wani hutu sai renon yaron ya koma hannun Aisha. Munyi waya da zulfa nai mata barka itama din tai min nai mamaki da ta kirani tana min barka da haihuwa. Na tambaye ta kowa tace suna lafiya tun wanan lokacin takan dan kira waya mu gaisa nima dana ga haka nakan kirata mu gaisa sai dai ban yarda muyi wani hira mai tsawo. Wani rana mama laraba na kira mun gaisa take cewa dani gaskiya Rahama banji dadi da kika bar kasan nan kika bar yaron nan yana shirin lalacewa ba. Gabana ne ya fadi nace wa tace Nasir mana nan dai take min bayanin komai a kan shi banji dadi ba ranan na rufe ido na fadawa daddy magana son raina kan watsi da iyalin shi da yake kokari yi ya tare gun mace daya kuma na roke shi da ya turo min yaron do dawowa na ba yanzu ba koda na gama zan kara jonawa ne naci gaba don dawowan ma ya fita min a rai. Banda kewar iyayyena banda damuwa ga kowa yanzu da sannu sannu na dawo da Atika da Nasir a waje don ina samun kudi sosai yana shigo mun tunda ba komai nake dasu ba a can komai da mukeyi daddy ne yake biya a katkashin shi. Kulawan da bamu samu daga gareshi ne kawai matsala wanan kuma haka maza suke da giyar aure idan ta rude su. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NR, , , 88 Alhamdullahi zance komai nawa yanzu ya kammala a gare ni sai hamdala da godiya ga ubangiji a gare ni. Naje da niyan yin shekara daya da watanni sai gashi zan yi shekara uku a can da watan ni lokacin zan zama babba likita cikakkiya idan na dawo sai course da zandinga zuwa yi don ci gaba na. Saan dana samu shine wanan auren da daddy ya kara komai baya gaban shi sai amarya da lalurar ta sune yasa a gaban shi. Duk da bana gida ina da labarin komai a kunne na don duk abinda ake ciki yana dawowa gare ni ina jin komai a inda nake. Wanan dalilin yasa na kara neman hanyan cigaban karatuna a can nai zamana da yara na matsala shine Amira da ta dauko wani hanya na makirci tasawa kanta. Nai alkawari a raina idan na dawo zan jata a jiki na ga rayuwan ta bai salwanta ba don bata da kunya ga makirci da son wullakanci sosai. Zamana a can ya matukar tsonewa amaryan daddy ido sosai sai dai duk samo kan shi da tayi bai sa ya yarda da ta dinga kawo kushe ga matan shi ba don haka yake shi idan ba an hadu da halin maza a kai ba. Sai ta nemi hadin kan sauran don burinta kawai taga ban dawo kasan da auren daddy ba don tafi hindatu iya makirci gun kishiya. Saboda ita hindatu tana hadawa da hauka ga alamarin ta don datayi sheri rawan kan ta zai sa ta tona kanta akan abinda tayi din. Ita ko wanan akwai wayo da ilimi a gare ta sai tai masu sheri ta dawo ana zagi da ita kamar ba itace tayi ba. Haka take faman cuta masu amma basu ganewa dama ita zulfa ba wai ta yarda da ita bane don ta san ta tasan komai nata tun baya. Ta gwanmace da tai hurda da ita gara dai ta daure ta jani a jiki yafi mata alheri ga yin hakan dasu. Tana yawan kira na tun ina dari dari da ita sai dai har nazo na sake jiki da ita zan kirata ko ta kirani mu dauki lokaci muna hiran mu da ita . Sai dai bana yarda ta dauko min zancen abinda ya shafi gidan namu na rikici idan ta fara nakanyi dariya nace Anty Zulfa a dai ta hakkuri wata rana sai labari insha Allahu. Da sannu har na fara saro kaya dubai ina turo mata tana sayarwa don kayan da nasan zasu shiga nakan shiga na saro na turo dashi ita da hajiyan harka. Cikin ikon Allah sai gashi ta fara dagowa ita ma ta samu abinyi yanzu don tana samu sosai a wanan fannin sana an namu. Wanan ne kuma ya kawo wani sabon tsegumi a gidan har ya kai matar daddy ta fara zuga shi kan wai ina nake samun kudi nake facali haka. Tunda yace shi yana ma dadewa bai muna aiken wani abu ba ji fa duk da yaran shi na a wurina amma bai sa ya mayar da hankali ya kula damu yadda ya dace yayi. Gulma yasa hindatu ke fadawa zulfa ai shegiyan nan ta kusa dawowa tunda naji Raliya na fadin sai tayi abinda zaisa ya dawo da ita kasan nan tunda batafi kowa bane ai. Suna gama waya ta kirani take sheda min yadda sukayi tace na fada makine don ki san abinyi kuma don Allah kada sunana yafito ciki Rahama. Haka yasa na shirya ma maganan ina jiran ya runkare ni na bashi amsa don likacin nayi nisa ga karatuna sosai ga yan yara na duk sun tasa sun girma gwanin sha, awa dasu ga duk wanda ya gan su. Kwana biyu shiru banji yai min magana ba sai kamar bayan sati uku ya bugo waya naji yace dani ke nifa ina son ku dawo gida hakana fa. Don zaman ku acan ya fara isa ta hakana, a raina nace anzo wurin ke nan nace haba daddy kwana nawa ya saura na karasa karatun . Hakkurin da kayi na taimaka min nazo ai bai kai wanda zaka yi yanzu ba so nayi na samu yaran nan su hada karatun sun tunda sun kusan gamawa nagani. Yace kin dai ji na fada maki ku shirya zan shigo ku dawo gida hakana ban son zaman nan cen da kukeyi. Amma dai ai ba zaman banza nake ba ko abinda zai amfane ni nakeyi a can kuma da yardan ka nazo nan din ba wai a cikin rashin yarda bane nazo. Ni na yarda da farko amma yanzu ban amince ba zan shigo ku dawo gida hakana cikin yan uwa. Daddy waban maganan kane ko dai na wani na tambaye shi da hakan, aiko take ya hasala dani yace kamar yaya magana na ne ko na wani wa ke aurar min ke da zai min zaben akan matana? Nace a gaskiya i iya dan sanin da nai maka nasan abinda zaka iya nasan wanda baka iyawa amma wanan maganan daji ra, ayin wani ne a kaina. Don may shi bai kaunar cigaba na ko kadan yasa ya tursasa maka wanan ra, ayin a kaina don ya shiga tsakanin mu saboda yasan ba abu bane da zai yuyu kai tsaye. Saura shekara da wata bakwai na kammala karatuna duk hakkurin da kayi da rashin mu a gidan sai yanzu ne wanu magana zai bullo kuma daga baya ? Kin dai ji na fada maki idan zaki shirya kafin nazo to idan kuma baki tashi shiryawa ba ni zanzo na kwashi diya na nadawo dasu gida. Nace Allah ya kawo ka lafiya Allah dai na tare da mai gaskiya ko yaushe ya kashe wayan ba tare da yai min magana ba. Zarah na kira nake fada mata komai har yadda mukayi da zulfa data kyankyasa min zancen tun farko kafin ya kirani. Tace Rahama tunda har Allah yasa kinji sai kin jajirce akan haka kada ki tsaya sanyi aimaki sakiyar da ba ruwa abinda kowa ke neman wanan daman ke Allah ya baki shine za, ai maki sheri don haka wallahi kada ki yarda da zancen dawowan nan sai kin kammala nuna mashi kema kin iya. In yaran ne ya kwaso su su mana ai sun samu na samu a can kice ya hada harda na goyen ya dawo dasu gida din mana ki gani idan zai kwaso su din. Dama gidan shi akwai zaman lafiya ne nasan zai iya kwaso su yakawo wa matan shi amma gida ba dadin yau balle na gobe ya kasa tsawata wa matan shi shine zai ce zai maki hakan. Ta min maganganu sosai da suka kara min kwarin gwiwa naji ko kadan bana jin shayin komai a kan maganan idan yazo din. ********* ********* ********* Ya shirya yai sallama da iyalin shi akan zai dawo damu idan ya tafi take aka soma gulma da dariyan keta akan dawowan nawa bashiri. Har suna fadin yanzu suga wanda zanwa wani sallon tsiya tunda karatun ma nawa ban hada ba balle na dawo na samu wani cigaba a nan da nake tsanmanin zama nan gaba. Ya iso da dare ban nuna mai komai ba na tare shi a cikin mutunci da girmamawa sai washe gari bayan ya karya yaran sun fita zuwa makaranta ne yake tambayana shi baiga kamar na mun shirya tafiya ba bayan ya fada min zaizo mu koma tare dashi. Nace komawa ina kuma daddy yace ke Rahama kada ki mayar dani mutumin banza fa na fada maki zancen komawan ku gida kina son mai dani karamin yaro. Nace daddy kayi hakkuri amma ni babu inda zan tafi sai na kammala karatuna nan da watanin masu zuwa insha Allahu. Yace ok good yayi kyau kila zaman kanki kikeyi ban sani ba yanzu ? Nace ba duk zaman kaina nake ba nasan dai da yardan ka nazo wanan karatun ba dakin amincewan ka ba sai bayan nazo ne naga sauyi daga gare ka duk ina hakkuri ina shanyewa don a zauna lafiya. Amma duk hakkuri na hakan bai maka ba daddy sai an turoka ka shiga rayuwa na anga ka tozarta ni hankali zai kwanta. Wakike tsanmanin ya turo ni na dauke ki ke nace koma waye ai ka sani don haka idan do na koma kawai na zauna ana fitina a tsakanin mu ne ni bazan tafi ko ina ba sai na kanmala abinda ya kawo ni nan din tunda ba zaman banza nakeyi ba nan din. Lalai abinda mutane ke fadi yau nagani da ido na tun ba aje ko ina ba kina son ki nuna min kinfi karfina yanzu Rahama. Nace ko daya ni ba zan taba fin karfin ka ba kai ma ka sani rashin adalci ne naga yai min yawa duk abinda ake min ina hakkuri ina hadewa a zauna lafiya baka gani daddy yanzu yakai har sai wata mace ta tursasa maka ra, ayi a kaina kuma kabi don kawai ka gyara mata ran ta taji dadi. Aiko nan ya shiga fada inda yake shiga ba nan yake fita ba harda cewa har may na zama da nake ganin nafi karfin shi a yanzu.? Na tuna a karkashin shi nake kuma in yaga dama karatun da nake takama dashi sai ya ruguza min shi aikin ma ko na gama bazan yi ba don na sani. Sai lokacin nai magana nace daddy nagaji nagaji wallahi na dai yi hakkuri naga alamar ka gaji dani ne kawai ka tsiro min wanan halin ba yau ba don haka a watse kowa ma ya huta tunda abin babu gode balle na gode Duk yadda nake ma kokari baka gani sai ka rufe ido kai min cin mutunci yau har da goranta min in kai kadai kasaura namiji a duniya nabarka daddy daga yau. Yace haka kika ce nace shi yafi muna sauki dani dakai tunda banzo nan ba sai da yardan ka yanzu anzugo ka kazo kana min tujara irin haka ido a rufe nafasan komai tun kan kazo dama ina jiran wanan lokacin. A karshe yace tunda ban tashi ba zai tafi da yaran shi ne shi, nace a sauka lafiya sai dai a hada har da Abdul a tafi don banga abinda za a bar min shi yiba a guna. Ranan Allah dai ya gyara don kamar zai sake ni Aisha da taji hayaniya yai yawa tafito tana bashi hakkuri tana kuka. Yafice ya bar gidan cikin kunan rai da mamakina don bai fadi in fadi a sanin da yai min amma sai gashi ranan mun yi kaca kaca dashi. Washe gari ya kira mama laraba da fada a hasale yake fadin wallahi mama zan saki Rahama na gaji da wullakancin da yarinyar nan take min haka. Salati mama ta saka tace Yusuf kan ka daya kuwa yau kake fadin wanan maganan haka ? Rahama fa kake fadin zaka saka da bakin ka kake fadin wanan mumunan kalamin haka may yarinyar tai maka yai zafi haka ne ? Yarinyar da ta rike ma diyan ka amana ta kuma zauna dakai da zuciya daya da kowa naka tun shigowan ta gidan ka ban tabajin wani abin assha ya shiga tsakanin ku ba haka ? Yace mama hakkuri fa duk lokacin na nakeyi da yarinyar nan tunda na kara aure ta canza min kwata kwata ba dadin ta nake ji ba sam, hakkuri kawai nake da ita kawai. Yanzu may tai maka mama din ta tambaya cikin son jin abinda nai mai yai zafi haka da muni. Yace mama har ni zanzo daukan su mu dawo gida tace dani wai bata zuwa nace idan bata tashi ba zan dawo da yarana gida tace na dauka har Abdul mai shan nono din. Watau ta nuna min yanzu ita idon ta ya bude ko tasan duniya ko may wallahi zan gwada mata ni banga wanan matar ba tukun a rayuwana. Da har zance ga raa, ayina tace dani bazata bi ba sai nata ra, ayin take so yi nagaji wallahi mama tunda ita bata san ana tausaya mata ba ko kadan. Tace baba babaka saurare ni wallahi wallahi idan kayi gigin sakin yarinyar nan kan dan abinda baikai ya kawo ba zakayi dana sani yafi dubu kuma ka sani kai keda hasara ba ita ba. Don ita ta debi rabon ta gareka ko ta haihu da kai ta samu ilimi ta samu karuwa kaiko fa ko rike maka yara nan wani sabon aiki zai zama maka wacce ma ansan uwar su rasuwa tayi sun kasa rike maka su dan dagawan yarinyar nan gidan ka balle wacce suka san uwarsu na raye da ran ta. Wallahi kada ka bari shedan ya rude ka kazo kana da kasani daga baya don shi za, ayi ina laifin wanan yarinyar karatu fa tajeyi amma sai da ta kwashe yaran nan kaf ta tafi dasu can suma su karu. Idan kai ma Rahama kan kara itama tai maka na itace yanzu dabara ya saura gare ka zan kuma fadawa yaya halin da ake ciki ta sani tunda ba zuwan girma da arziki kai masu ba sai ta kashe wayan nata dip. Nan kuma ya shiga damuwa maganganun mama din yana dawo mashi a rai ya ja wani tsuki ya dade zaune inda yake kafin ya mike din . Yara kan na shirya su tsab nagama shirina na dauke Atika da Aisha muka fice na bar mai note da cewa idan ya tashi ya kwashi yaran shi ya tafi dasu kamar yadda yace nima aure ne ban yi na fasa ko shi kadai ya rage namiji a duniya na barshi har abada ke nan. Tashin hankali yana gama karantawa ya kalli yaran dake barci sai da wani zufa ya tartso mashi a goshi. Tun ba aje ko ina ba ga maganan mama yafito mai shi ina zai kai wanan yaron yanzu haka tundai na goye ke bashi tausayi idan ya falka yaya zaiyi dashi yanzu. Sai ko ga yaron ya falka ya fara kuka Nasir ya tayar Allah ya taimake shi yaron ya iya abinda Aisha ke mai tare sukai renon yaran ranan. Hankali a tashe yake nemana ko ina a garin gashi bai san inda zai gannin ba abinka da wayayyen kasa take aka gano inda nake can cikin asibitin da nake karatu. Ban yarda na karbi yaron ba sai da ya jajibo min manyan kasan mu suka saka baki na karbi yaran amma na dage ban zama dashi kuma. Shima sai abin nawa ya fara bashi mamaki yadda na hau fiye dashi a yanzu duk yadda aka so fir naki yarda nace nagama zama dashi ke nan tunda har ya rufe ido yazo min cin mutunci a kasan mutane. Ni kaina nai mamakin kaina yadda na iya rufe ido nai mashi tas haka a kasan mutane batare dana yi dubaiyyan akan baya ba. Ya samu an lalaba na karbi yaran amma bamu shirya ba tsakanin mu don kowan mu ya hau sosai. Bayan tafiyan shi ba wani shiri na canza layin wayana gaba daya na ma canza muna mazauni nabar maigidan shi baki daya. ********* ********* ********* Ya sauka a lagos sai daya huta ya samu natsuwa ya karso Abuja lokacin Raliya tana gari tazo tana jiran zuwan mu ta samu na fada min taga yaya muka dawo. Sai ganin shi tayi shi kadai babu mu take ta nuna bakin cikin ta a fili tace sun dawo kuwa shiru yayi ya shige dakin shi bai tanka ta ba. Bata hakkura ba bayan ya tashi ya fito ta sake tambayan shi da kai kadai naga ka dawo mana yace a tsawace Raliya will you keep quaint please. Nagaji na fahinci kina son mayar dani mutumin banza don kinga ina biye maki kin san kin fadawa mutane kece kika tasani a gaba shine kika bari naje naji kunya ga hakan. To ki sani kafin ma naje Rahama tasan komai da kuke kitsawa a nan keda masheranta yan uwan ki. Kin zubar min da mutunci ga yarinya ta mayar dani mutumin banza mijin tace kawai don komai da kika kitsa min a nan tas naji shi a bakin Rahama a can. Nagaji nagaji wallahi daga yau kada na sake jin wani zance akan wanan yarinyar a gidan nan ko rayuka su baci. Kada ku mayar dani mutumin banza mana haka abinda wanan yarinyar take min ko kadan baki iya min shi ina nan na dauko Amira na kawo maki amma kika kore min ya tabar karatun ta ta koma kano. Kina ganin abin bai min zafi bane ko may yanzu ita kuma wanan dabaki ko zauna da ita ba kin dauki tsanar duniya kin sa a kan ta ba don Allah ya gyara ba da kin kai ga hakon ki akai. Ya fice ya barta nan da mamaki ina naji wanan maganan haka har yakai a kunne na kodai aljanace ni bazanji shi ba a inda nake. Daga karshe taita tunane tace ko hindatuce ta fada min tace ina hindatu ai tafi ta son ma na dawo gida din bazata fada ba to ina naji wanan magan ne wai ? Kwana biyu sun rasa gane kan shi gaba dayan su ya dauki fushi da kowan su da yake ta iya bariki ranan da tai wani zuwa ta nemi shiri dashi. Har kasa ta duka wai tana neman gafara a wurin shi ta marairaice murya tana fadin ita bada wani manufa ta fadi hakan ba ta daiga ya kamata ne ace mun dawo gida hakana tunda ance na gama karatuna shiyasa tai maganan. Bai tanka taba har ta gaji ta mike don shi idan ya tuna da cin mutuncin da nai mai na barshi da yara har gobe abin na bata mai rai. Nikan bayan tafiyan shi naji ba dadi amma naga hakan yafi min sauki ko ba komai zan kara samun natsuwa ga jeraban dake tafe min . Don namiji idan ka biye mai baka taba samun natsuwa a zuciyar ka shi baiji kunyan goranta min ba nima haka yasa na rufe idona na dauki mataki akan abinda suka kulla suyi min din. Ba mai wani contact dina nima bana kiran kowa naci gaba da harkokina na watsar da komai balle namiji irin daddy daya cika mata a gida kowa da nata kalar sallon data iya. Ya neme ni daya sauko don yaji lafiyan yaran shi amma layin bai shiga sai daga baya ya fahinci kila na canza layi ne hakan yasa ina nan akan bakana dashi ke nan ban sauko ba. Niko nasan zanji surutun mutane akaina sosai amma hakan bai damay ni ba don ba zan zauna da kurciyana sunnun namiji ya kashe ni ba a raina. Don ni kadau nasan irin hakkurin da nake a gidan ba a gani saboda hakkuri na sai gani ake nice ke yadda raina yaso ba a san cewa na zamay irin matan da akewa kirari da MARUCIN KAN DUTSE bane. Kafin ya tofo sai an dauki shekaru bai tsiro ba a gani hakan ke sa ana daukan alhakin wasu mata ake ganin suke shanawa a gidan miji don hakkurin su. Hakkuri idan yai yawa yakan baci ga dan adam don wani lokaci yana zama cuta haka yasa na dauku matakin don nuna mai nifa mutunce mai jini a zuciya ba wai ruwa kawai nake sha ba na zauna hakana. Sannu sannu kwana nesa sai gashi na gama karatuna lafiya har Nasir da Atika sun samu kammala nasu karatun. Sun so rike ni a kasan nai aiki dasu amma hakan ba zai yuyu ba don kaucewa zargi irin na mutanen mu don haka na daure nai aiki dasu na wata shidda kafin na karbi komai na yaran mu tattaro mu dawo gida gaba daya. Ranan labara ranan saa muka sauka gida Nageria ni da yaran lokaci har Abdul ma yana tafiya da kafan shi ya fara karatu a can don shekaran shi biyu da dan kai. Sai da muka huta a lagos har kwana uku don nisan tafiyan da muka kwaso muka dan huta anan. Shigan safe mukayi Abuja a gidan da aka tanadar min na sauka na ma, aikatan mu nan na sauka ni da yarana baki dayan mu. Na canza na koma wata matar manya ga aji ga class komai na tara a rayuwana bana shayin kowa kuma a halin yanzu ta fannin kishiya. Sai washe gari na saka layin dana saya na nan gida Nigeria don an min wellcome back. Na fara kiran yan uwa da abokan arziki muna gaisawa dasu don su san na dawo gida a lokacin. Ban san dan gulman daya fadawa daddy cewa muna cikin Abuja ba mun sauka ni da yaran . Yai matukar mamaki sosai don shi dama a hakane ta hake min zaiga yadda zan dawo gidan don yasan dai dole gidan shi zan dawo banda wani wurin zuwa kuma. Sai gashi yana zaune mama laraba ta sake kiran shi tana cewa ashe Allah ya dawo da yaran nan lafiya jiya da dare Rahama ta kirani take fada min sun sauka lafiya sun dai iso lafiya ko ? Wani iri yaji a ranshi amma a fili yace lafiya suka iso mama tai min addua ta kashe wayan sai lokacin ne ya ke tunane may wanan yarinyar take nufi ne wai dani ? Daurewa yayi ya kira bashir din ya fada mai halin da muke ciki na dawo kasan ban nemay shi ba. Bashir yai matukar mamaki sosai yace dama mai hakkuri bai iya fushi ba don haka kaida iyalinka ke hannunta ba fushi zakayi ba da su. Daurewa zakayi kaje kanemayta ku sulhunta a tsakanin ku tun maganan baiyi nisa ba sosai don kaga yanzu fa ba da bane. Rahama na da ilimi tawaye tasan duniya don haka juyata yadda kake nufi tunda ta hau haka kabita ka lalabata kawai a wuce wurin. Ya dauki shawaran abokin nashi don ya nemay ni amma ban daga wayan ba, hakan bai mashi ba sai gashi ya nemi gidan da muke yayi zuwa yakai ukku amma naki yarda ya ganni. Don ko yaushe gidan namu a rufe yake bamu fita ko ina mutum ma bai sanin akwai mutane a ciki don muna bakin shiga don da gidan empty yake ba kowa a cikin sa. Hankalinshi ya tashi gashi ko yaran shi na hanashi ganin su balle yaji dan sanyi a ran shi idan ya gan su din. Ganin baida wani mafita ga matakin da na dauka yasa shi yanke shawaran da zai fishe shi kawai don haka. Kano ya nufa ya je kauyen mu ya sanarwa iyayyena halinda muke ciki ni dashi abin yai matukar basu mamaki sosai. Kin san halin iyayye da rufe ido su ba yarsu laifi nima hakan ne ya kasance da nawa iyayyen don laifina suka gani ga zancen. Tare suka shirya zuwa Abuja da daddy anyi tafiyan ne da maigari da mahaifina da liman da wani abokin babana. Gidan da aka bani babbane akwai dakuna uku da katon falo sai haraban gida da sauran abubuwan rayuwa. Zaune nake da yaran gaba dayan mu a falon mun dawo ke nan daga wurin shan icce cream tare dasu mukaji ana nocking din kofan gidan namu. Nasir yake amsawa da ana zuwa yayi tsawo ya girma ya zama saurayi yana bude kofan gidan sukai tozali dashi mahaifin nashi ne a gaba. Yace daddy you are wellcome cikin harshen turanci tare da cewa sauran da hausan shi daya dan sauya dan yawan turanci a can. Sannun ku da zuwa sai ya dan riko hannun daddy nasu yana fadin daddy we miss you, ya rungumo yaron tare da riko hannun shi yana tambayan shi mummy ku na ciki ko ? Yaron yace tana nan ciki gata can zaune a falo ma a lokacin ina zaune a kasa namike kafuwa na Abdul ya hau kan kafafuwan nawa yana shan icce cream sai jinior dake zaune saman kujera dana kara jikina gap da kaina yana shan ice cream din shi a roba mai dan fadi duk sun zagaye ni muna hira. Sai ganin shi nayi yana shigowa rike da hannun Nasir a nashi ga mutane a bayan shi. Na dago kai naga mutanen da yake tare dasu da sauri na mike ina gyara zamana tare da fadin sannun ku da zuwa baba. Sai dai daga cikin su babu wanda ya amsa min gaisuwan nawa haka yasa na san anzo dani arai sosai don duk sun dauki zafi sosai dani ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 89 Duk na daburce na rasa may zanyi don ganin su da nayi a gidan nawa na dauke yaron dake jikina ina masu sannu da zuwa. Wuri suka samu suka kai zaune take Aisha ta shiga kawo masu abin sha a gaban su suna ta bin mu da kallo. Nasan ba komai bane sai ganin irin yadda dagani har yaran gaba daya duk mun sauya ma ganin su. Don munyi fresh mun kara girma da kyau nayi jiki da fari don canjin yanayi dana samu a can din. Nan na fara gaida su tare da masu sannu da zuwa sai dai basu wani karba min a cikun farin ciki da gani na din. Sai baba maigari ne ke fadin Rahama a she kun dawo nace eh baba wallahi mun dawo yace yaya karatun ya jama, a can da kuma yaran nace dashi Alhamdullahi. Yace sai dai kuma yaya na gan ku a nan ba a gidan mijin ki ba kuma don can naga ya kamata ace kun sauka aiko. Nace eh baba akasi aka samu sai dai kune baku sani ba amma gaskiya a halin yanzu bamu tare da shi don tun ina can muka samu matsala dashi gaskiya baba ba ni da auren daddy a kaina don mun dade da rabuwa dashi akan wasu dalilai. Magana nai masu ditect ba wani farga ba komai a zuciya na sai sune ma naga sun shiga rudani wanan ya kalin wancan suka fara a tsakanin su. Sai shi maigari ne yai karfin halin fadin Alhaji Yusuf wai abinda take fadi gaskiya ne ko may don bamu fahinta ba mu ? Daddy yai dan murmushi tare da girgiza kan shi yace ba gaskiya bane baba asalima ban san inda wanan maganan ya fito mata ba ni. Na dai san mun dan samu matsala da ita tana can tun wanan lokacin kuma bamu sake haduwa ba da ita har yaran sai yau din nan baba ni ba irin mutanen nan bane masu saurin sakin mace akan da matsala kadan. Maigari yace dani Rahama ban taba tsanmanin wanan halin daga gare ki ba kada ki kasancce a cikin irin matan nan da abin duniya oan yi saurin badewa idanuwan su. Nace baba kada kuyi min wanan zaton don bani daga cikin masu wanan irin halaiyan ko kadan. Haba Rahama koma may ya faru a tsakanin ku ai ya kamata ace mun sani ba wai ki bugun gaban kan ki ba ki tare a wani wurin da bamu da masaniyan shi a rayuwan ki. Nai murmushi nace baba ku kwantar da hankalin ku kun san wa kuka haifa ai bazan yi wani abin assha wanda zai taba mutuncin ku a duniya ga idon mutane. Sai lokacin babana yai magana yace na sani Rahama kuma ina shedan ki ga hakan amma ki sani gidan mijin ki yafi maki daraja ga komai. Nasani baba amma kuyi hakkuri fa wanan hukuncin da har kukaga na dauka a kaina don shi abu mafi sauki ga rayuwa na daya dace inyi. Baba ni ke zama da daddy yanzun kuma nace bana yi don Allah kada ku tsaurara min matakan da zuciyana baya iya jure daukan shi ga yin hakan danayi. Baba na roke ku da kuyi hakkuri ku barni na samu natsuwa a rayuwa kan abin da zai fitar dani daga wanan rayuwan da bawan Allah nan yake son jefani a ciki. Amma Rahama daga ke har shi din kun barmu a cikin duhu kan maganan din mu bamu fahinci may kuke fadi ba gar yanzu bamu san may ye matsalan ba. Maimakon nai magana sai hawaye suka fara zubo min shar shar sai duk hankalin su ya tashi wanan abokin na mahaifina da suka zo tare ne yai magana. Yace ni ina ganin da mun bawa wanan yarinyar dan lokaci har ta samu natsuwa sai a san mafita akan zancen don tunda muka ga Rahama har ta bude baki taimuna wanan magana haka yau ya kamata mu bita a sannu. Sai duk sukayi shiru can baba maigari yace gaskiyane nima tunanen da nake ke nan yanzu a raina don haka kai malam Yusuf kayi hakkuri don Allah harta samu natsuwa. Da haka aka bar maganan sukai min sallama ko abinci basu tsaya sunci ba acan ma bayan sun fita basu tsaya ba don a ranan zasu koma gida acewan su. Sun tafi suna cike da mamaki da fargaban abinda ya faru yau din a tsakanin mu don abin ya daure masu kai sosai. A motane suke magana shi wanan mutumin yace ya kamata abi zancen a hankali kamatayi suji ta bakina tunda har na jajirce masu akan hakan don da alama shi mijin baida gaskiya bayan musaawan da yayi bai kawo wani kwararen hujjaba akan maganan ai. Nima dai abinda ya daure min kai ke haka iji maigari yace dole akwai wani matsala tunda tun auren su bata taba kawo muna wani kara ba makamancin haka din. Ni dai tun tafiyan su haka na wuni a hargitse dani don nasha alwashin daukan wa kaina fansa akan abinda daddy ke min din. Daga baya na ba kaina shawara na fitar da zancen a raina na rugunmi yara na na bar zancen wani daddy can. Bayan kamar yan kwanaki na gama hutawa na ina batun fara aiki muka samu waya Abban anty ba lafiya sosai. Ban tsaya ba washe gari na kwashi yaran sai kano muka dira a gidan mama laraba nai muna masauki don bamu je gidan daddy ba. Wurin mama ne nake samun labarin wai an gyarawa amaryan daddy part din anty da ke kusa da nawa din a nan garin yanzu a ciki take zaune. Ban damu ba don batun shi ni ya fice min akai ko mun tafi da dare asibiti mun duba jikin tsoho ba lafiya ko kadan yana jin ance mune cikin karfin hali ya bude idanuwan shi yana dan murmushi ya mikawa Nasir hannu yazo inda yake. Yaje sun gaisa haka yaiwa sauran yaran abin gwanin ban tausayi yace cikin murmushi Rahama naso na zauna dake na taya ki duba yaran nan amma ban tsanmanin hakan ba don ciwon nan da wuya yabarni. Don Allah kici gaba da kokarin da kikeyi a kan su kece da dadin hakan wata rana kin yi kankanta da daukan wanan nauyin a kanki amma kuma gashi cikin ikon Allah kin rike wanan amanan da aka bar maki da kyau ina maki fatan alheri dake da yaran nan a rayuwan ku nan gaba. Kuka na fara haka yasa na bar dakin mun dan jima asibitin sai godiya yan uwan su ke tamin ganin yadda yaran suka koma a lokaci guda bakacewa suna da maraicin uwa a tare dasu don na zamay masu uwa ko a garesu yadda ya dace. Sai dare muka koma gida tun da safe labarin rasuwan Abba ya samay mu ba mu tsaya ba muka garzaya gidan gaba dayan mu. Damu akai komai aka kai daddy masaukin shi daddy bai san da zuwan mu ba sai da yazo yaga Nasir a waje yai matukar mamaki sosai. Bayan sun kebe ne yake tambayan yaron da yaushe suka zo yake fada mai ai da aka bugowa mummy waya shine jiya muka taso har yake labarta mai yadda mukayi da tsohon a daren jiya da muka zo ganin shi. A ran shi yace wanan yarinyar akwaita da bakin wayo sai dai ban san Rahama da riko irin haka ba ai dole ne na sauke girmana nabi yarinyar nan a sannu a zauna lafiya tunda nagane yanzu bani gaban ta . Sun shiga ciki ina waje zaune da wata sister din anty da muke shiri tun banyi aure ba muna hiran mahaifin su ya shigo ciki gaisuwa. Damu ya fara cin karo zaune saman farar kujera mun mai gaisuwa shima kamar babu komai a tsakanin mu ya shiga ciki yai ma sauran yan uwa ta, aziya yafito tun wanan lokacin ban san yaya ya karata ba kuma. Sai dai na nemi yaran ban gansu ba ake ce min sun fita da daddy su ai shiya tafi dasu da zai wuce. Naso sa damuwa amma na danne don ina tsoron mutane su fahinci abin da ke a tsakanin mu dashi a wurin. Tsora kada ya rike yaran ya biyo min ta nan yaci galaba na sai dai yadda nake ji a raina koda zai karbe yaran shi ne zan iya hakkuri dasu din in har ya biyo min ta nan. Mun dawo gidan mama har nai shirin kwanciya bai dawo da yaran ba gida hankalina yana atashe sai mamane ke tambayana wai ko zai dawo dayaran nan kuwa yau. Nace a sanyaye ban sanu ba mama tace barin kirashi naji ina ya tsaya dasu ga dare yayi tana kiran shi ya dauki wayan. Tace kana ina da yara ga dare ya soma baka dawo mata dasu ba har yanzu yace da ita suna nan gida tare dani. Mama tace dawo mata da yaranta hakana su kwanta dare yayi zaiyi magana tace dashi Alhaji karami kada ka soma kace zaka tsoma yara a cikin zancen ku. Kanemi shiri yadda ta dace a gun matarka yafi wanan hanyan dakake son dauka. Yai dariya yace mama ba rike su zanyi ba nima ina son ganin su ne tunda hardasu ta hana min ganin yara na. Tace na fada ma dawo mata dasu yanzu batai magana ba amma nasan abin zai damay ta a rai. Yace gamu tafe mama aishi Abdul din ma da bai sanni ba sosai tundazun fitina yake min shiko takwarana sau fada yake wai wata ta shiga dakin maman su bazan iya rigimar yaran ba gani tafe dasu mama. Tace cikin dariya aika dandana kaima kaji abinda take ji yau dasu ku dai maza nakan rasa ina tunanen ku yakan shiga idan kun tashi tsula tsiyan ku. Tunda mama tace ga shi tafe da yaran na shige ciki abina don bani kaunan ganin shi ma idan na tuna yadda ya rufe ido yazo tsula min tsiya a baya. Dana bita son miji da yanzu bankai wanan matsayin da Allah yakaini gareshi ba da akaso ai min bakin ciki akan shi. Ina cikin wanan tunanen ne naji muryan su sun dawo suna nema na nan Nasir ya shigo dakin dauke da kanin shi a kafadan shi yayi barci ko. Yana shimfideshi sau ga uban a bayan shi dauke da Haidar shima yayi barci a jikin shi sai daya aje shi yace da yaron dake tsaye ya fita. Yaron na fita nai kamar ban ganshi ba adakin sai wani irin kallo yake bina dashi kamar ranan ya fara gani na, naji yace Rahama wai may kike nufi ne damu haka ? Da har zaki zo garin nan kiki sauka a dakin ki kizo nan gidan mamana ki sauka ban fahunci har yanzu inda kika dosa ba fa da auren mu. Najuyo nace dashi abinda kai niyar yi a can kasan da kaje har kake ikirari a akaina nake jiran ka dashi har yanzu. Yace ni banje don yin wani abuba da ina da niyar yin wani abu aida a lokacin nayi ko tunda ba wanda zai hanayi idan natashi yi. Nace ko yanzu ai sai ka tashi don shi nake jira a gare ka kasani kuma ba zan zauna da mutumin da bai son cigabana ba har abada. Yai murmushi tare da cewa nine yau kuma bani kaunan cin gaban ki kike iya fadin haka da bakin ki Rahama ? Kada fa idon ki ya rufe don kinga kin kaiga bukatan ki yau kice ni zaki watsa ma kasa a idona. Nai murmushi nace aika dade da goranta min ko kan hakan koka manta ne na tuna maka yau ne ? Na manta sai kin tuna min kila zan tuna don ni ban iya kawo komai a yanzu. Malam ka ba kan ka lafiya gidan kane dai bazan koma cikin shi ba nagaji da zama da mutanen dake son ganin baya na akoda yaushe. Suwaye ke son ganin bayan naki nace wanda suka zugoka daddy kazo idon ka a rufe kana son ci min mutunci don an zuga ka. Ni ban damu da kowacen su ba duk su uku din amma su duk abinda zasuci min dun duniya ta shine gurin su a kullun. Gida dai ne na bar maku abinku sai a barni na zauna lafiya please ba kare bin damo kuma. Yau nine karan kuma, Rahama ko wa ? Ni ba zan taba muzantaka ba don nasan darajan ka a gare ni kuma ko banza uban diya na kake yanzu don haka kada Allah ya kawo ranan da zan aibanta ka a gaban wani hausace ta kumshi haka nai maka. Yai shiru yana kallo na amma sai nai kamar ban ma san yana tsaye a wurin ba yaja kafan shi ya fita daga dakin ba tare da yai magana ba ko may yasa oho ? Acan falo naji muryan shi suna magana da mama ya dan dauki lokaci a wurinta kafin ya tafi ********* ********* ********* Nasan zai iya dawowa washe gari don haka tunda safe na shirya muka bar garin zuwa kauyen mu ni da yaran. Mama na fadin tun yau zaku tafi nazaci ai sai anyi uku zaku wuce can din nace bari na tafi yau mama don wurin aiki sun fara nema na. Tace to Rahama duk dai abinda zakiyi ki sa tsoron Allah a gaba ki sani auren ki yafi maki komai mutunci a duniya. Ni dai ban ga wani abin assha a agareki ba ko wanan karramawan dz kikayi na zuwa gurina ki sauka da yaran duk yawan fadin garin nan yai min dadi sosai wallahi . Yanzu ni abinda nake so dake shine ki janye wanan fushin da kikeyi ki koma dakin ki ki zauna yafi daraja da kima. Murmushi nayi kawai nace mama da adaiyi hakkuri don hakan shine sauki a gare mu ni dashi mama yaya zan zauna da mutumin da kullun baida ra, ayin kasa sai wanda aka sashi yaiwa mutum may nai wa daddy wanda zai dinga juyani haka akan matan shi. Tace ya fada min komai amma din Allah kiyi hakkuri ki koma dakin ki nace mama ko zan koma da daddy ba zan zauna a gidan nan ba idan har inda muke bai mai ba yana iya canza muna wuri amma ba nan din ba kan na gama zama da Hindatu kuma. Tace umm, umm Rahama hakkuri baibar komai ba a duniya kiyi hakkuri dai a sasanta a tsakanin ku nai dariya na gyara gyalen jikina mukai mata sallama na tafi. Ana sallah muka shiga gida don bamu fito da wuri ba banzo da niyar komawa ba a ranan dama shiyasa Nasir bai biyo mu ba. Bayan tafiyan mu daddy yazo gidan da Bashir sai samu yayi mun tafi yai mamaki duk da ranshi ya baci amma sai mama ke fada mai yadda mukayi da ita kafin na tafi. Bashir ne ya iya magana yace wanan kuma sabon zance ne ita kanta ta sani kamar itace idon gidan nan yanzu kuma tace bazata dawo ciki ba ke nan sun zama masu gida daban daban ke nan. Gaskiya barin Rahama a main house matsala ne don yanzu haka dan barin da tayi din nan mutum bai zuwa ya sha ruwa a gidan nan. Shi dai daddy bai iya magana ba don shiru yayi kawai abin shi abin ya daure may kai ya rasa may nake nufi ne dashi. Sun dauki lokaci da ita suna magana sai fada yake kwasa akan ba zai amince da hakan dana zo dashi ba din. A can gida ma bayan na huta ne maigari ya shigo muka kebe dashi da Inna ta yake min gaisuwan Abba din da kuma tambayana halin da muke ciki ya kuma roke ni da karna baye masu komai don a san mafita ga zancen. Ban boye masu ba duk yadda mukayi na fada masu komai har abubuwan da ake min a baya ina shanyewa duk na labarta masu komai. Yace yanzu shu hakkuri zai kara bani amma za, a dakanci zuwan daddy din aji may ya yanke akan bukata na din. Matan daddy sun samu labarin dawowa na kasan nan itama hindatu ta shiga nata kalar haukan ba hinduba har da Raliya tayi irin nata take cewa dashi. Ashe yar gwal ta shigo kasan shiyasa naga ka wani birkicewa mutane dan kwana biyun nan haka yai mata wani kallon shekeke yace wace yar gwal kuma ? Tace matarka mana Rahama tunda ita gani take tafi kowa a wurin ka yace ashe ke baki sani ba tafi kowa din gani kike kamar ita ke ganin hakan ni nasan tafi kowa din ai shiyasa kikaga na birkice ai din. Nan ta shiga surfa bala,i inda take shiga ba nan take fita ba yai shiru ya kyale ta yagama shirin sa ya fita baiko tsaya karyawa ba shine suka fita zuwa gidan mama da bashir din. Kwanana biyu a gida ina shirin wucewa ne daddy ya yazo garin nan suka samu wuri da maigari aka kira mahaifina yazo kan zancen namu. Duk abindana fadi maigari bai rage mashi komai ba sai ya dukar dakai yace a yi hakkuri amma kowa yasan matsalan mata indan sun fi daya a gida sai hakkuri. Ita Rahama ne bata ganewa nifa nasan abinda nakeyi ba wai ban sani bane komai da nakeyi ina yi ne don zaman lafiyan ta hakan ma da nake duk gani suke ai bayan ta nake ko yaushe. Sannan maganan canza gida ba zan sake mata gida ba anan dai zata zauna inda muke illa iyaka dan gyaran da za, ai mata kawai shine . Yanzu ai tunda tana gari bari a kirata taji da kunnuwan ta sai ayita a kare anan ta koma dakin ta idan kun shirya din tsakanin ku. Ina saye da dogon hijjab dina na shigo da sallama a zauren na samu wuri na zauna tare da gaida mahaifina da kwana. Yace Rahama ai ina gida ina jiran zuwan ki sai ga sako kuma maigari ya turo nazo mijin ki yazo mun zauna dashi babanki maigari ya mashi bayanin komai kamar yadda kukai magana dashi. Sai dai gaskiya akan canza wurin zama yace bai amince da hakan ba yanzu dole inda kike din zaki koma sai dan gyaran da za ai maki. Nai murmushi nace baba nifa dama don ku ne zan koma gidan daddy amma ba don wani abu ba can don nasan in na koma ma halin ba dainawa za, ayi ba mai laifi daban wanda akewa fada daban. Rahama yace yana gyara zaman shi ban so kimun wanan kaken ba haka don kina da wani manufa a ranki dani. Nace ni banda manufar komai a kan ka zama dai ne idan ba za a canza min wuri ba sai a hakkura kawai. Yace wanan kuma dama shine gurin ki kadai ki yunanen don na rabu dake ko bazan iya rayuwa ba ko wani abu Nace ni awa da zan hanaka rayuwa dama ai ba tare dani kake ba da kake rayuwan ka don haka ko yanzu kuma da bamu tare ba wanda ya hana wani jin dadin duniya sai ma ni da aka tauye kawai. Kai haba ya isa haka mana sulhu fa muka zo ba batawa ba bashir yace Rahama don Allah kiyi hakkuri abi wanan maganan a tsanake. Yanzu dai kinji yace bai aminta da zancen raba gida ba don haka ina son kiyi hakkuri da wanan maganan. Nace Bashir ita wacce ya raba damu din ai bata fimu ba ban damay shi bane da da nima ya yarda danawa bukatan Ita da ta damay shi ai ya fifita mata gida ta zauna ita kadai babu tsangwaman yara ko namu gare ta. Yai dan murmyshin yake don jin abinda nace nace aidole kai min dariya tunda na zama abin dariya gareka yanzu don banda wani sauran moriya a gun ka. To bazan iya ba ni ma don babu wacce ta fini balle a dai rabu kowq ya huta shi ke nan ba mai matsawa wani kuma a zauna lafiya yara dai ne zaka iya wucewa da abinka idan ka so hakan. Rahama wai kanki daya kuwa kike wanan magana haka a gaban mu inji mahaifina. Nace Abba ni wallahi mudin ba hada mu za, ayi ba guri daya ba zan ta ba komawa ba gidan nan na kwanmace na zauna ni kadai har bayan raina. Subbahallahi may yasa kikai saurin rantsuwa ne wai inji Bashir nace wallahi iyakar gaskiya na na fada maku in har yace ba zai canza min gida ba to sai dai ya hade mu guri daya duk mu hudun a zauna tare ko kuma ya sauwaka min kawai . Kai ban si ki rantse ba dai adai bi zancen a sannu ko nace ni banda wani magana bayan wanan shike da igiyar aure a kan shi zabi ya rage nashi yanzu. Duk shiru sukayi yadda na zare ban jin kunya kamar ba Rahaman da suka sani ba a baya can shiru shiru dani yanzu girma yazo min na kuma kara wayewa idona ya bude. Shiko daddy haushin iyayyena yake ji a ran shi don yaso ne su fatatake ni na koma kai tsaye bai san na wuce wanan bz agun su ina da daraja da kima sosai sa kwarjini ga idanuwan su kuma dole su duba min abinda zai fitar dani. Nace ni tunda bai yarda ba abari na wuce don gobe zan koma Abuja zan fara shiga aiki ranan monday sai dai zan so na san matsayi a gun shi don ban son ina yawo da hakiin aure a kaina. Haba Rahama ki daina wanan kalamin bai dace dake ba gaskiya iji bashir sai baba na yace Rahama indai har ni na haife ki to ina son kibi mijin ki ki koma dakin ki ki zauna daga yau. Aiko sai na saka masu kuka nace baba dama baku so na shiyasa baku damu da damuwa na ba ni wallahi da in koma haka ba wani kwakwaran magana daga gare shi gara na mutu kowa ma ya huta. Salati suka saka namike na shige ciki na barsu nan nan dai suka taran mashi akan ya barni na zauna inda nake amma yace shi bai amince da hakan ba sam. Yafi son ya hada kan iyalin shi a wuri daya yafi mai suna ciki na barsu na wuce abina ban tsaya ba kowa yai mamakin wanan canzawan nawa niko inayi ne da gangan don samun sauki a kaina. Nayi hakane don mu zauna wuri daya da ita Raliyan dake suraitai a kaina don ta raina kan ta don nasan zaman su wuri daya da hindatu ba karamin kwasa za, ayi ba tunda bata rike girman ta ba gareni. Abune mawuyaci na sani ya yarda na koma wani wuri da zama dama don yafi son ya zauna hade da kowa ban san yaya tayi taci kan shi har ya raba muna gida ba da ita tun farko. Suna hanya ne bashir yace dashi ya kamata kai nazarin maganan yarinyar nan don idan bakayi da gaske ba naga alaman Rahama sai ta kubce maka. Yace na sani Bashir nasan may wanan yarinyar take nufi dani yanzu tana ganin ta zama abinda burin ta ke son zama shine yanzu zata guje ni. Bashir yace sam bakai tunane ba kuwa don har gobe matarka na son ka kawai da abinda kukai mata ne kaida matan ka har taji kimar ka ya zube a gareta. Ya juyo yace kimata ya zube fa kace a wurinta yace kwarai kuwa ba wurinta ba har a wurin iyayyen ta dani ma kaina da muke magana dakai a yanzu din. Haba haba mutumi da girman ka da kimar ka harka bari mace ta baka shawara kuma ka yarda ka hau ba a karatu da aiki ita takeyi ? Tana son ka ta kasa sa zaman lafiya a gidan ka kamar yadda ita Rahaman tai ta hakkuri da komai tana shanyewa yanzu dubi fa yaran ka bazakace ba itace ta haife su ba fa. Amma kana ganin kaf din su akwai wacce zata iya rike maka yaro ko daya ne idan ba ita din ba. Iska ta furzo daga bakin shi tare da numfasawa yace abinda nake duba ke nan yanzu idan har rabuwan zamuyi yaya zanyi da yaran nan nata da na marigayi din dake wurin ta ? Don dai kasan bazan bar mata su ba a wurin ta yace kagani sai yace ina mamaki na gane tauein ran mahaifiyar ra ta kwaso ke nan data barsu a gun mahaifin su taje tai wani aure daban shine itama yanzu zatai koyi dashi ke nan. A, a a fa kada ka kawo wanan tunanen kaidai kaiwa kan ka shawaran abinda zai fisheka kawai don samun mafita idan ita Raliyan son ka take tsakani da Allah may zai sa bazata dawo cikin iyalin naka ta zauna ba ? Kai bashir kaima kasan zamu kwasa da ita kan hakan sai bashir din yace to kuwa a nan zaka gane gaskiyan Rahama din . Yace zan gwada in gani amma dole sai anyi gyara ko kuma na samu wani wajen maigirma da zai wadace mu yace da yafi ma don haka ni zan shigo Abuja naga Rahama muyi magana na tsanaki da ita da yardan ubangiji. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 90 Tunda nai sallama dasu mama na shiga gidan su daddy don n yi sallama dasu nan hajiyan shi ta tsure ni tana min fada sai da ta gama ta tashi ta shiga sai ga Amira ta dan matso kusa dani ta make muryan ta tana fadin. Mummy zan biki mu koma Abuja don Allah na gaji da zama nan hajiya fada gare ta don Allah mummy kice zaki tafi dani Abuja don Allah sai ga hajiyan ta fito da leda a hannun ta. Nace hajiya dama nazo da magana ne don Allah Amira nake son a ra min zan je su zana wani jerabawa ne a can bazata dade ba zata dawo. Hajiyan tace dani anya Rahama zaki iya da wanan miskilan yarinyar Amira da kike gani bata da mutunci wallahi nace hajiya ba damuwa bama wani dadewa zatayi ba ai zata dawo nan. Tace shi uban ya sani ne nace eh munyi magana dashi dama yasan da zancen tace to ai shike nan ni dama ai ba wani abu take min ba anan din banda sani magana. Nan dai ta ce ta hado kayan ta mu tafi da saurin ta ta mike ta shiga hada kayan ta sai gata da katon akwatin ta tafito dashi. Hajiyan tace a, a Amira keda ba dadewa zakiyi ba shine zaki kwashi kaya haka da yawa nace ina ruwan Amira ai ra dawo dasu in bata saka duka ba. Mun bar gidan ke nan mun dauki hanya daddy ya shigo gidan su yace ina Amira bayan sun gaisa sai hajiyan nashi tace , a, a ita Rahama ba tace kasan da tafiyan su ba ta dauki abinta ta wuce da ita ai, wai akwai jerabawa da zasu zana a can ita da yan uwan ta. Yace kai kai wai may Rahama ta dauke ni ne yanzu please yanzu zan buga mata waya ta dawo min da ya ta ban son iskanci da rainin wayo. Kai ban son shashanci inji Alhajin shi ita Rahaman bakuwar kane ko kuwa cutawa yarinyar zatayi a can dama a gun wa take ba wurin ta shakiyanci irin nata yasa ta bar gunta. Yanzu kuma tun ganin su da tayi sun dawo hankalinta yai mugun dagawa kuma ya koma akan su ganin yadda suka sauya gaba dayan su. Kabar mata yarinyar nan a wurinta tun da kai ka kasa cika alkawari ita ta daure ta dauki amanan da aka bar mata a hannun ta kai da baka iya sai kaje can kaji da gaiyyan matan ka suna juya ka yadda suke so. Duk ka sake ka rabu da yarinyar nan Rahama ko bayan raina ne wallahi ban yafe maka ba kaji na fada maka. Take yaji gaban shi yai mugun faduwa yace wanan yarinyar ta gama daure ni ta ko ina bai dade zaune ba ya mike ya bar gidan. Dama ina jiran called din shi kan maganan yai ta kira har sau uku yana katsewa ban dauka ba har muka isa bai kara kirana ba. Ranan momday na fara fita aiki ban samu matsalan komai ba nayi clearing din komai yadda ya dace nayi kafin na fara aikin da na dawo. Yaran kuma na kaisu makarantan da yafi ko wani kyau da kulawa na saka su a nan nike zuwa na kaisu na kwaso su. Ban hurda da kowa ba ruwa na da kuma kowa don gujewa zargi ko surutun mutane a kaina komai namu yana tafiya normal . Ranan mun dawo gida na kwaso yaran na shiga dakina nai wanka na fito falo ina saye da dogon riga iri mai hula baya din nan sai harkokin su sukeyi ina kallon wani program a tv. Nocking din kofa akeyi Jinior ne ya tafiya bude naji yace la ga daddy kano yazo sai naji gabana ya fadi ras. Ya shigo rike da Jinior a hannun shi nan yaran suka shiga yi mashi sannu da zuwa suna gaidashi yana amsa masu tare da kiran sunayen su. Haidar ne da Abdul suka nufo ni suka fada a jikina dama haka sukeyi in sunga wanda basu sani ba yazo balle sunji ance daddy don in sunyi laifi sai muce sai mun kai su wurin daddy ai sai suyi ta kuka don ba waye sukayi da uban ba sosai. Sannu da zuwa nai mashi tare da bashi wuri ya zauna nake cewa dashi a she muna da bako bamu sani ba yace ban fada maki ina tafe bane ina son ku ganni ne kwatsan irin hakan. Mun gaisa muyi mai yaya hanya sai yaran suka shiga watsewa daya bayan daya suka barni dashi a falon. Ya kira suna da cewa Rahama gashi yau na sake dawowa gare ki da kokon bara na da fatan shine zai zamo zuwa na na karshe a wurin ki kaan wanan zancen don ina son muyi magana ta fahinta dake please ? Shiyasa ma kika ga nazo nan din ni kadai batare da kowa ba a cikin masu maganan har shi uban aikin. Shiru nayi ina sauraren shi a lokacin yace don Allah Rahama kada ki boye min komai ki fada min tsakanin ki da aboki na yau dai na sani da kuma shawaran da kika yanke tsakanin ku a yanzu. Tun da na fara magana sai umm, umm yake fadi yanq kada kan shi yana nisawa har na kai karshen magana na. Yace to sannu Rahama da hakkuri shi musulmi bai gajiya da hakkuri sai ki kara yanzu idan aka hada ku ukun a gida daya zaki amince ki zauna ki koma a karkashin shi ki daina daukan nauyin kan ki da nayara dakike yi kike nuna muna kin kai kin isa ke ma. Nai murmushi nace ni bance nakai ba ko na isa kawai dai ina kare mutuncina daga wullakancin ku da kuke ganin abin ku zai rufe min ido na dauki wullakanci ku akaina. Wallahi yaya bashir bazan kara jure wullakancin da daddy yake min a baya ba yanzu ku sani ina zaune sai dai kishiya ra ban abu ko na gani tana min sallo dashi ni ko idan za ai min sai kowa yaji don ina diyar tallaka ko mai son miji. Yai dariya yace kiyi hakkuri insha Allahu duk wanan ya wuce sai dai ina son ki kama bakin ki ki sa muna ido don Allah kuma zan rokeki wani abu kafin komai ya kammala yadda muke so ki daure ba don ni ba don Allah zakiyi Rahama ki bar nan ki koma dakin ki da yaran ki kafin komai yazo daidai. Nace har zuwa yaushe komai zaizo daidai din kake nufi ? Yace insha Allahu ba za, a dauki lokaci ba nan da dan lokaci idan mun samu wurin da yai muna kyau a nan din zaku koma ciki hakan yayi maki ko ? Zaki kuma koma dakin ki don Allah ki bar nan din da kuke zaune don dai ki san mutumi ba zai taba zuwa nan ba wurin ki da sunan aure. Nace kada yazo mana ba sai yasha zaman shi ba in sha nawa in baizo nan ba ai yana iya zuwa wurin wata ba kunya yadawo yara na kallon shi. Wani irin dariya ya kwashe dashi yace kai Rahama yaushe kika koma hakane wai kodai har da karatun kishi kika koyo ne can ? Nace dama aina iya ina dai binku sannu ne don biyayya kuma yanzu naga kamar kuna ganin tsoron ku nake ji ban iya daukan wa kaina incin hakan ? Yace musan kin iya ai har kin wuce wuri tunda har da yaran mun kin hana muga abin sai labe labe kika barmu dashi kawai. Daga karshe muka juya kan hiran karatuna yake cewa gaskiya na godewa Allah abin kamar a mafalki wallahi Allah. Nace a ro ai baku so hakan ba dani ku yace haka dai kikace ko mu wuce ace muna mijin doctor ai dadin mune ko. Da zai tafi ya kawo alheri yabawa yaran nace haba harda wani guzuri kuma yace ai wanan ba komai bane ni dai naji dadin mutuntanin da kikayi ai. Yanzu yaushe ne zaku koma can din ku bar nan don na sani kafin natafi in ma da hali ki gobe ne sai nazo na kai ku da kaina kafin na wuce ai ? Nace kai haba dai kamar wacce ta matsu sai na shirya may be nan da wata ko fiya da hakan dai . Yace a, a don Allah k bar wanan zancen mana ko so kike abokina ya samu hawa jini ai wanan horon ya isa hakana don Allah. Nace horon may kuma sai kace wanda baida wasu matan a tare dashi dai don Allah barni har na shirya a tsanake please ? Ya daure fuska yace to naji amma insha Allahu nan da Saturday mai zuwa zan zo na kaiku gidan da kaina nace da sauri a, a ni bani hurda da Saturday ai don nasan aibun yin abu a wanan ranan sai dai Laraba mai zuwa na sama ko Friday din ta. Yace yadda kikace hakan za, a yi rankishi dade aiko hakan ma mun gode sosai wallahi don zan tafi da kwarin gwiwa ai. Nace amma fa ia sani gidan nan zamana yakeyi ba zan sake shi ba muddin naga baiyi yadda mukai alkawari da kai ba wallahi wallahi sai dai ku wayi gari na dawo nan din kuma bazan taba kara yarda da ku ba har abada. Yace insha Allahu ma zaki samay mu da cika alkawari da yardan ubangiji kada ki damu yi muna dai fatan alheri mu samu mu fita daga tarkon ku na mata tunda haka Allah ya nufe mu da gani a kan ku. Har bakin mota na raka shi ya wuce yana min godiya na koma ciki na zauna sai lokacin hiran mu dashi ke dawo min a raina nai mamaki yadda na amince mai da bukatan shi haka ? Ina fa jin tsoron kada sai na koma daddy yace bai san da zancen ba yazo ya karya alkawari sai gabana ya fadi dam a lokaci guda. Na dauki waya nai dialing din nomban shi kira daya biyu gana uku ya dauka ina jin yana magana yace hello nace yaya Bashir sai kaga na kira ka kuma yace eh wallahi ko kinyi mantuwa ne dai ? Nace kamar ka sani nace wallahi yaya Bashir kada na koma gidan daddy da zama yazo yace baisan da zancen hada mu wuri daya ba daga baya. Na rantse da Allah idan yai min haka sai nayi inpiching din ku a kotu daga kai harshi daga baya kada kuce ban fada maku ba. Yace subbahanallahi Rahama may ya kawo wanan zancen kuma haka kodai kina shawara da watace ban sani ba ? Nace aini ba haka nake ba banda yawan kawaye haka kuma ban sharing din matsalana da kowa sai idan naso na dai kirane kada na koma yaga na koma yace zai min wullakanci kan hakan ba zan dauka ba. Yace kada kiji komai kwantar da hankalinki ashe daddy yana kusa suna tare yana jin may nacewa Bashir din ya kada kan shi kawai. Sai da muka gama wayan yace Bashir yanzu na gane dalilin wasu maza da basu yarda mace tai ilimin zamani bayan secondary. Wai yau Rahamane ta zare haka don Allah yarinyar da ko yatsa aka sa mata a baki bata ciza shi idan ba taso ba amma jita yanzu don Allah. Yace nima abin har tsoro yake bani ai sai da mukai wanan maganan da ita bashir din yace wallahi ba komai bane sannin ciwon kan ta tayi yanzu kawai duk shi ya jawo hakan ba komai. Sai dai gaskiya sai kayi da gaske don akwai magana babba idan sun hadu a wuri daya dadin abin kasan halin kayan naka ka iya zama dakowan su ko. Amma dai ayi a sannu ayi adalci don Allah a tsakani kaga wanan daukan wacce bata girki ka fita da ita don Allah a daina tunda suna da motan su kowa taje gashin kan ta don ba kowa fa zai iya hakkurin abinda yarinyar nan kai mata ba. Yace ni may ne mata illa kishi data saka a ranta kuma duk haka suke ai da bakin kishin junan su yace dashi ai dai ba a taba ji ba sai yau din nan ko ? Nan dai suka tattauna daga karshe suka shiga gari don yin wani harka daya shafe su can. ********* ********* ********* Ban fadawa yaran batun tashin mu ba gidan sai ana saura kwana biyu mu koma can muna falo dasu mun barbaje nace dasu. Tau yau dai saura kwana biyu mubar gidan nan dai sai duk sukayo min ido caaa akaina sai Aisha ce tace dani anty ina zamu koma kuma bayan nan din , ? Na bisu da ido nace daddy yace bai yarda da zaman mu nan ba dole mu koma gida mu zauna can wirin shi. Har suna hada baki wurin cewa inda mama ihisan take nace can din kuwa kai kai inji Nasir yace wallahi ni haka bai min dadi ba nace ina ruwan ka kai da kake namiji baka zama gida kuma kwana nawa ya rage maku ku tafi ku barmu nan din. Kowa ya dinga fadan albarkacin bakin shi nasan dan freedom din da muka samu yanzu akwai matsala idan ance za ai muna abinda akayi a baya zama ba sakata ba wali a can din. Basu so ba haka dai na kwantar masu da hankali muka shirya ba komai muka dauka ba don wacin gadi zamuje yi mugani ga watauna ba san mu dai shiga din ba agani. Dogon motar su na wurin aiki ya turo muna ta kwashe mu da kayan mu zuwa gidan ni da yarana da yan matana ras har su uku don ko wace ta girma yanzu. Mun shiga da sallaman mu babu kowa a falon sai tv dake faman aiki a wurin kawai shi kadai. Ban tsaya ba muka wuce part din mu a rufe yake na dauko ke daga bag dina nabawa Aisha ta bude muna suka fara shiga da kayan da mukazo dasu ciki. Jin motsi yasa ihisan fitowa tare da yar aikin su sai taga muna suka juta da sauri suna fadawa hindatu din tace wa Rahama fa a gidan nan yai daidai Aisha ta fito falon tana jin su. Ta koma tana fada min nace tasan abinda tayi kila kada na dawo yar iska wacce bata tsoron Allah ga alamarinta. Aiko kamar ai aiko mata da sakon kayan ta har muka gama shiga da kayan mu ciki ba wanda ya leko falon cikin su. Dama munzo da abincin mu da zasu ci don haka bamu damu da rashin girka muna komai ba. Sai bayan wani lokaci daddy ya dawo gidan ina zaune na idar da sallah la, asar naji shi da yaran sukan Haidar da Abdul sukayo daki da gudun su da suka gan shi. Ina may nene wai haka ya bude labulen dakin ya shigo yana cewa ikon Allah daddy kuma kuke tsoro. Daga yaron nayi ina kwashe salaya na nace dashi sannu da dawowa fuska a daure yace yauwa kun dawo lafiya. Alhamdullahi na bashi amsa dashi ya nufo yaran suna kokarin shige min a jikina basu son ya dauke su wai . Yai murmushi ta re da kadan kanshi yace baku sanni ba ko maman ku ta hana ku sani na ko ? Ni dai banyi magana ba na bude wardrobe na ciro wani dogon riga nawa Abdul ya rike min kafafuna nace kai tsaya dan Allah ni kada ka kadani kasa kaji. Ya zo ya duka har inda muke ta dauku yaron ya fara kuka zai fita dashi shiko haudar duk yabini ya make shima nace kubi daddy ya sayo maku ice cream ba zaku sha ba yaran suka kada kai nace to kuje gun daddy ya sawo maku biscuit da sweet yanzu zaku dawo da big bros zaku tafi cewa Nasir sai suka yarda suka bishi. Bai jima ba ya fice dasu har jinior da Nasir din suka fita tare yan matan suka dawo guna suka zauna muna hira. Sai gab da magariba suka dawo gidan hindatu na falo taga shigowan shi dasu tace bissimillahi diyan gwal sun dawo ke nan bamu da hutu yanzu gidan nan balle aiyi lokacin mu. Tace ashe kin gane ke nan farin cikin rayuwa na sun dawo duhu ya yaye min banda lokavin kowa yanzu sai su. Aiko tace dawa Allah ya hadata bashi ba kuma don may zai fada mata hakan ai wullakanci ne ba sai ya fadi ba kowa ya sani ai. Aikin banza may ye bamu sani ba mu dama ai mun ssn komai shiyasa aka dawo aka lake wani gurin har a gama shirya maka don a samu a mallake mu wallahi duk abinda mutum ya dauko ya kare a kansa. Munafuncin banza da wofi sai da aka gama ta zubar da bin dangin miji a na rokon su sannan aka dawo muna mu Allah ma dai ya cece mu da ciwo wallahi. Yace cikin wani tsawa ke hindatu ya isheni haka duk kika kara bude baki kika zagar min mata na ki kikai mata sheri yanzu zan dauki mataji a kan ka. Eh lalsi shirin ki na kyau wallahi Rahama amma mu zuba dake a gani wallahi sai anga wanda zai raina kan shi. Ina daki ina jin ta nace ohoni Rahama na dawowa turke na mai cabo dada an fara ke nan kuma amma zan daga mata kafa na iya gudun ta dai. Shi oan shi yai mamakin yadda na kyale ban tan ka ta ba a lokacin don har lokacin ma ni bata sani a idon ta ba haukan ta dai take kwasa. Ina jin komai na na dake a dakin bayan sunyi sallah ya fito da yaran suna zaune falo haidar na kuka jinior ya taba mai biscuit din shi sai ga wayan Raliya ya shigo mashi a lokacin. Ya dauki wayan tana jin kukan yaron tace kana inane haka nake jin kuka yaro kuma ? Yace ina gida zaune daidai fitowa na daga daki in gaidashi tace gidan ka fa ya sake cewa eh a gida nake zaune mana. Tace wake kuka yace Haudar ne da Junior ke rikici haidar sun dawo ne ko may sai raji murya ina cewa kai Jinior baban kwabo ne fa naka zaka sha na kanin ka kuma kyale bros sai na dauko nashi ai kasha kaima. Tace dashi eh lalai na yarda kuwa ashe akwai munafunci ban sani ba haka sai yace muna funcin may sai ta kashe wayan ta. Kallon wayan yayi yai tsuki tare da murmushi yana girgiza kan shi kawai na fahinci komai amma sai nai kamar banji ba naci gaba da magana da yaran na bar wurin ban sake magana ba. Tsaye yake yana waya yace Bashir maganan ka gaskiya wallahi na fara fahintar komai a yau din nan da dawowan Rahama gidan nan. Nan dai yake fada mai komai da yafaru tsakanin shi da Hindatu da Raliya din yace bashir kaji min matan nan yadda taita rokona kan na yarda muyi aure zata kawo min kwanciyan hankali a gidana. Yanzu gashi na fahinci shigowan ta ma yafi tayar min da hankali fiye da baya can don ko tsakanin ta da sauran babu kauna kullun cikin makirci take wa abokan zama. Bashir tace kafara ganewa ke nan yanzu sa masu ido da a tsakanin su da kan su zasu fahinci komai akanin kaga am fara shiryawa ai mata ba a shiga tsakanin su sam barsu suyi tayi da kan su. Ban karbi girki ba sai washe gari nayi girki ba zance komai ba don nasan mai karatu zatace dama ahi nake so eh ko shi din ne ai mutum nake mai jini a jika dole ne nima naso mijina dan yaushe rabo. Bayan komai ya kammala ya dan rugumoni yana cewa Rahama na amsa a dakile yace na rokeki daga wanan karon kada ki kara nisan ta kanki gareni. Dariya ma maganan shi tabani nace nina nisanta kaina gareka ko kai kanisan ta damu don kawai baka dauke mu da daraja ba kayi mun haka don ran matan ka yai dadi. Su sancewa baka damu dani ba, dani da babu duk daya muke a gare ka don kawai ran su yai dadi su san ka wulllakan tani. Yace bar wanan maganan ke bazaki gane bane ko nai maki bayani sai kiga ai da gangan nai maki hakan. Nai murmushi nace ni yanzu aikai nake saurare naji hukuncin da zaka yanke wanda zai kawo fahinta a tsakanin mu kowa ya zauna a matsayin shi. Yace na fahince ki na kuma gane komai yanzu da kike nufi da fatan zaku kara hakkuri da junan ku nace ita Zulfa sai zuwa yaushe ne zata dawo nan garin. Yace sai na shirya nace amma daddy baka ganin ana shiga hakkin ta da yawa duk yaran mu suna nan suna samun ingantaccen karatu ita ko tana can an barsu da nata yaran. Ji nayi ya numfasa yace zan shiryawa dawowan nata nan da yan kwanaki kadan insha Allahu zata dawo amma kin san dole a kwai tsarin daki da zamuyi don nan din dakuna shidda ne kawai a gidan ke kina da biyu hindatu biyu sai nawa dana su Nasirda suke a ciki. Nace hakane yace amma ba matsala ita Ihisan sai ta dawo dakin da yaran ki ke ciki su zauna tare ko ta koma dakin uwarta da zama sai ta zauna a dayan har mu samu daki araina nace anzo wurin. Nan inda mukayi a nan muka bar zancen sai ko ga Zulfa a cikin bazata tazo ni dai na dawo aikin dare na samay ta a gidan. Har dakin da take na shiga nai mata sannu da zuwa na dawo dakina ina cire lab coth dina sai gata a dakin nawa tashigo. Nace a, baku hutaba kun taso tace ina naga hutawa Rahama matar gida tace bani zama a kusa da ita nai murmushi nace haba dai hakan ko zai yuyu. Yanzu bari nazo nace da Aisha dake ciro min kaya a wardrobe Aisha yanzun keda su Amira ku koma dakin can na yar aikin maman Ihisan sai ku gyara wa anty wanan da kuke a cikin sa. Nagama magana sai ga daddy ya dawo daga gun aikin shi yana tambaya suna ina nace magani yaki nema ke nan. Sun gaisa da ita yake cewa kin kai kaya ki dakin ko tace mai dakin tace bata san da wanan zancen ba a falo ma ta barni zaune tun dazun yanzu da zanyi sallah kagin Rahama ta dawo ne yar aikita tace na shiga nan nayi. Ya juta zai fita nace dashi da har nace su Aisha su gyara mata wanan da suke a ciki ai su sai su zauna ina ya tambaya cikin fada da dan harara nace su zauna da ihisan din a can . Yace ba haka na tsara ba babu kuma wanda zai canza min tsari na kan hakan yaran ki su zauna nan kusa dake kina ganin su yafi. Nan dai suka fice a tare ya ga su Aisha sun fara fitar da kaya su yace su maidashi ciki kawai a wancan zata zauna. Shi da kan shi ya shiga dakin ya samu mai aikita a ciki yace mata ke koma gun uwar dakin ko ta mai dake dakunan dake baya nan matana zata zauna ta mike tana cewa tau Alhaji. Ta shiga gun Hindatu ta fada mata sai go gata tafito da saurin ta tana fadin banga wanda zai min wanan ba ni da wurina ace za, a ai min kutse yace gidan ki ko gidana ? Tace gidan kane amma may zai hana ka kaita can inda Rahama ta zauna do sun fi kusa ai da ita yanzu nagani. Yace bake zaki tsara min yadda za yi da gidana ba ya juya gun Zulfa ce ga dakin ki nan zaki zauna gobe a shirya yaran su fara shiga school da yan uwan su. Daga haka ya wuce ance ga kofa aiko ta shiga bakin ta inda take shiga ba nan take fita ba zagi gori ba wanda mu ukun bamu sha ba a ranan gun ta. Nan dai dole aka dawo da tsari sai dai abinda ke daure min kai shine duk wani abinda ke gudana gidan yana kunnen Raliya tasan komai kamar tana zaune a gidan. Sai kuma nazo na fahinci cewa yanzu idan zatazo garin sai ranan da zanyi girki tayi na farko na kyale ta sai gashi tayi na biyu again shine na nuna ban yarda bada hakan. Don ta shigo garin kamar yadda ta saba sai gashi ya dawo ya samay ni a kitchen muna hada abincin dare ya dan tsaya a wurin yaran can ya wuce dakin shi sai ya aiko z kirani naje na samay shi yayi wanka ya sauya kayan jikin shi ko. Ina karasowa yake cewa har kun gama ne nace da dan saura ya juyo da kyau ya fuskance ni nasan yana da magana sai na fuskance shi nima. Yace tau gashi kuma yau Raliya tazo garin kuma kinga dole a can zan kwana gunta ke nan tunda tazo ba nan ba. Nace ok ta shigo ashe yace eh wallahi nima nafito meeting ne na samu called din ta take fada min wai ta shigo. Nace to sannun ta da zuwa yanzu akwai magana ne yace eh nace abinci kada ksa dani a can zan kwana . Ba dai yau ba ko don yanzu after six ra shigo sannan kuma ai ba gaskiya bane tace sai ranan girkina zata dinga shigowa garin nan wancan karon tai min haka na kyale ta to wanan karon ban yarda ba kuma idan kaje ba yafe maku zanyi ba ta bari idan na gama wunina sai ta dauka kaga girkin sai yazo muna daidai ke nan tana fira zulfa ta dauka kuma. Tsaye yayi tana ksllona tare da sauraren magana ina ganin kamar zaiyi magana na juya na fice daga dakin ban tsaya sauraren shi ba. Na koma naci gaba da aikina a kitchen can naji fitan shi yara na mashi sai ya dawo ya fice daga gidan. Sai bayan na gama ne na koma daki don har na gama raina yana a bace ina jiran inga gobe in an matakin dauka a gare su. Muna daki hayya hayya da yaran sai ga Nasir ya shigo bayan ishai yana fadin Mummy dadi yana kira a falo nace daddy fa yaron yace eh. Na mike na nufi falon yana zaune fuskan shi babu alaman annuri a cikin sa nai mai sannu da dawowa yake cewa banga abinci bane nace ya kiraki nace na zata ba nan din zakaci bane ai. Yace don Allah dauko muna abinci muci kafin yaran nan suyi barci don tun dawowan mu tare yake zama da yaran shi maza suci abinci tare da shi sai idan baya garin ne. Na juyo naje na hado mai abinci na kawo masu suka zauna sukaci na shige ciki abina na barshi nan tare dasu suna ci ana hira. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 91 Muna barci da safe dashi a daki wayan shi yai kara ya mika hannu ya dauki wayan yana dauka daga inda nake kwance ina jin muryan ta. Fada take sosai dashi wai har ita zaiwa wullakanci don ya raina mata wayo saboda ya gyara wa matan shi rai. Akan wanan shegiyar mai kama da kwara zaka wullakantani ka barni kaje gunta don ta fini ko may ? Yace ashe kin san inda nake ke nan dama kika zo don ita ma ki wullakan ta tako ? Sai ta kashe wayan yaja tsuki daga inda nake kwance na gyara kwanciya na tare da dauka hannu na kai saman jikin shi na dan rungumoshi kadan sai ya sauke ajiyan zuciya. Yace ashe ba barci kike yi ba ke nan nace kun dai tayar dani da wayan ku yanzu yace baku barin fitina ku ai. Ban san wai may ke kawo wanan son rigiman ba haka a tsakankanin ko yaushe kowa da nata kallan son fitinar ga yar uwar zaman ta. Banyi magana ba sai sauke ajiyan zuciyan da nayi kawai tare da lumshe idanuwa na ko dai ba komai na daukar wa kaina incin wanan son tozarcin da Raliya take son yi min din. Ban fito ba sai wani lokaci don Aisha da Amira suna gida suna iya taimaka min da komai yadda ya dace. Koda na fito Aisha ta kamala har ta sallami yara sun tafi school tana wanke kayan miyan da zatai abincin rana dashi. Sun shigo wurina muna gaisawa dasu ina zaune ina shafa mai muna hiran rigiman yan makaranta haidar da Abdul da dan wurin anty zulfa wai sun gaji basu zuwa school ranan. Sai ga Zulfa tashigo dakin daidai ina saka kaya a jikina tace kin tashi nace eh ina kwana anty tace Alhamdullahi. Yau fa mutanen ki an sha rigima dasu a gidan nan wai ba zasu school ba sun gaji da kyat muka samu suka wuce. Nace yanzu nake tambayan Aisha su take fada min yadda kuka kwasa dasu ai tun ba aje ko ina ba an fara haka kuma ? Tace ashe kuma mutumiyar ki ta shigo gari ne nace wake nan fa tace Raliya mana tsohuwar banza nima a waje na ganta tazo gun mutumiyar ta suna magana. Nace ashe har yanzu suna tare ne ke nan haba ina mamaki yadda komai na gidan nan yake a kunnen ta dama. Matsalar su ne wanan ban dai bin kowa da sheri tace ai sunji kunya dana gansu amma sai nai kamar ma ban gan su ba na wuce abina. Wai ma kin san wani abune maman haidar don haka take kirana kotace dani maman yara don har yaranta a gun mu suke sakewa su wala in suna gida komai tare muke masu tun zuwan su garin. Don yanzu gaba daya Zulfa ta sake dani sai dai ni sese da sese nake da ita ban yarda na sake kamar yadda ita ta sake dani ba sosai. Tace ina mamakin wanan zaman nasu Raliya bata san halin hindatu bane tukun aini na dade da dawowa rakiyar karya da zalunci tun tuni shiyasa take jin haushina kamar ta shake ni take ji. Nace anty ba ke kadaiba ai ita kowa haka take dashi in ba yarta ba a gidan nan shiyasa ban yarda taiwa yara na horon da bataiwa yarta. Tace in anyi magana tace wai ita kadai ke gare ta ai dole ta so ta tunda ita take gani. Nace muma din da muke ganin wasu ai babu wanda bamu so a cikin su balle tace haka tace aike sha kundum din ta . Don lokacin da nazo baya ta gama haukan ta don zuwa na ta mayar dani wawiya wai shine ranan kina wurin aiki take son yin gulmanki dani batasan yanzu ba da bane. Wai yanzu kwana biyu za a ganki da ciki don baki da guri sai ki vika gida da yara kifi kowa samun gado don ko wandin kika shaka sai kinyi ciki ke kamar kinfi kowa iya kwana da miji ne. Dariya nayi nace ita gado ya dama ko ita da zata samu haihuwan irin haka ai yi zatayi har tafi kowa tace balle maganan ta daya biyu zancen gado ne ita. Nace ita ya dama wanan sai ta kasheshi ta kwashi gadon ai tunda shine burin ta ko yaushe. Tace waya san gawan fari tsakanin mi da mai dukiyan wanan Allah kadai ya sani yau ina Saade ta huta da wanan rigima nan mu kullun da baida ranan karewa. Take naji wani daci a raina nace Allah sarki anty ita dai ta dabance wallahi duk irin abubuwan nan bai damay ta ba dama a rayuwan ta barta dai da son diyan ta shine nata. Tace ai basu da kaico sai dai ace uwa uwace kawai don may suka rasa wanda baki masu yanzu wa zai iya wanan abinda kike sai an tona a halin yanzu kan. Murmushi nai mata kawai na kara shirina duk muna hiran take cewa ita wanan mara tunane da akai mata shigo shigo ba zurfi ai sata ta dafa mata a bayan ki data zauna gunta. Da sauri na juyo nace wa Amira tace ita mana cewa tayi idan tazo da kudi wai Amira tana diba kuma in tayi miya sai Amira ta kwashe nama ta cinye. Nace Allah sarki ba dai Amira bz kan da dai ta tsaya ga cewa tana sa rashin kunya da zan yarda amma ba sata ba kan. Tace aiko sun hadu da uban don ya haukace mata sosai a lokacin ya kwashi yar shi ya mayarwa Hajiyan shi itama hajiyan tai masifa sosai a lokacin . Nace niko banji wanan labarin ba tace ina zakiji kuna can waje lokacin ke sheri iri iri fa ta lakawa yarinyar harda cewa tayi tana kawo maza a gida idan ta fita. Nai salati nace ashe abin wanan matar na gaske ne ita bata san daddy akan dan shi baida wasa ba da kowa tace aiko sun hadu dashi don da kyat ta samu ya sauko suka shirya dashi. Ai lokacin ne ta dawo nan dakin marigayiya da zama don yace bai yarda da zaman ta inda take ba don maza na shiga gunta. Nace matsalar su ce don bai shafe mu ba wa yan nan idan ka biyewa halinsu sai ka zauna kullun baka da aiki sai cin naman su kana rage masu nauyi. Shiyasa kikaga banda lokacin irin wanan suraitan a rayuwa na aikin gaba na ya damay ni na fadi hakane don ta bar zancen don naga bata da niyar barin maganan su. Har na shirya muka fito tare da ita falo inda na fara taya Aisha aiki da na sama tanayi ban dauki lokaci ba na dawo muka zauna sai suma yaran sukazo suka zauna inda muke. Amirace take muna hiran film din data kalla muna ta dariya saiga daddy ya fito cikin shirin shi zama yayi ya karya yana yi yana sauraren hiran mu da mukeyi ana dariya. Mamaki yaji sosai a ranshi yau a gidan shine aka zauna haka ana hira harda dariya ba wani fiti a tsakani. Yadaga ido daga inda yake yakai idon shi ga dakin Hindatu dakin ya na a rufe kamar bata cikin gidan. Sai da ya gama ya mike yana goge bakin shi da tissue yake zo inda muke yana cewa ita waban bata ciki ne ko tafita ne ? Sai mukai shiru ba wanda yai magana daga cikin mu sai ya sake maimata tambayan nashi da cewa hindatu ta fita ne ko may ? Sai zulfa tace dashi ina ga tana daga ciki don banji motsin fitan ta ba dakin nata ya nufa ya tura ya shiga tana daga kwance a saman gadon ta. Ta dan dago kai taga mai shigowa dakin sai ta mayar da kanta a saman filon da take kwance ya karoso yana fadin lafiya ke kika dawo daki kika kwanta yan uwan ki na falo suna hira ? Gyara kwanciyar ta tayi tana fadin tau wani sabon magana ke nan kuma wani hira yanzu aka dauko yi a gidan banda labari ni ? Yace wai ke may yasa baki son zaman lafiya kin fi bukatan ko dayau ai fitina dake ne wai daga tambaya zaki jero min wasu maganganu can ? Banga zan iya hiran kulla makirci ba ne shiyasa na dawo daki don nasan ko ina ba a kai indon wanan hadin kan ne da naga anayi a gidan nan. Wsnan ke kika sani don ke ko yaushe baki kaunan zaman salama sai na tashin hankali da anyi ance kawai in bashi ba kowa na waje ke kin dawo nan ki ware kan ki ke kadai kin fita sun kore ki ne ? Ta dab dago a nakashe tace kora fa acikin su kaga wacce nake shayi ne ban dai iyawa ne don ban iya makirci ba ni. Murmushi yayi don jin may tace ya juya zai fita sai tace kirikiri Raliya tazo garin nan akai mata wullakanci ta koma don wata. Yace wullakanci? Wa yai mata wullakanci din ? Tace kaida matar ka yar so mana yace ban san da maganan ba sai yanzu a bakin ki naji dai. Tace amma ai kasan tazo garin nan ka barta ka dawo gun matarka ka kwana don kada ran ta ya baci ko ? Yace oho ashe tazo ne dama ita don ta bata mata rai ita ma ban sani ba sai ki bari ranan girkin ki zance ta dawo daidai lokacin da take zuwa sai ke da ba a so ki barmata naki girki ko ? Tace da sauri ban gane na barmata ba akan may zan bar mata fina tayi ko may ? Yace oho ashe ita tafi tane da zata bar mata girkin nata ko yaushe taga dama tazo garin. Sai dai ita ba, amma ni kan ko tasha giyan wake ne ai bata min haka ban din bata ga wuri ba kai ya girgiza ga shi dai a sannu abubuwa suna baiyyana mashi yana gani da idon shi. Wanda a baya baidamu da ya bincika ko ya luraba yasan may yin hakan da takeyi yake nufi shi kawai mata tazo gari dole a wurin ta zai kwana ke nan bai damu da ya hankalta da hakkin wata yake dannewa ba a ranan . Fita yayi daga dakin don i zuwa yanzu ya fahinci mata da ksidin su ya zama mai dole ya mike ya kara gyara gidan shi da kan shi ba sai an hankaltan dashi ba . Bayan fitan shi ya biya gidan Raliya nan ya samu ta tafi bai kirata ba ya share ta don ya fahinci komai yanzu. Motar da na saya a can ya shigo don haka sabon tsegumi ya taso a gidan kuma don takanas ta kano Raliya tazo har gidan ganin motan da idon ta. Matar da zatai zuwa goma garin bata shigo gida ba amma sai gashi ranan da na fita girki yake cewa da Zulfa da zata karba kada tayi girki Raliya zata shigo garin. Tashigo da yamma sai gata gidan bamu ma san may ya kawo ta ba lokacin muna falo har yaran ina saye cikin shadda maron colour yasha aiki tun daga sama har kasan rigan don zanin ma an mashi aiki na dan je gidan wata nurse din mu da muke shiri da ita ta haihu ranan aikai suna shine muka leka ni da zulfa dasu Aisha. Tana shigowa muna fsli suna cin kayan bukin da muka dawo dashi tana ganin ko wani cas a cikin kwalliya kamar zamu buki sai ta daure fuskan ta. Kaina na duke ina karanta sako a wayana sai ji nayi yaran na mata sannu da zuwa ban dago kai ba son na shagala da karatun abinda nake karantawa. Idon ta akainaa don tun dawowa na bamu hadu da ita ba dama sai yau din nan da ta samay mu a hakan zaune ana ta hira. Sai da ta kusa zaunawa ne ma na dan dago kai na ga ashe itace muna hada ido naga tai saurin kawar da kanta banji komai a raina ba irin yadda a baya nakan ji gaba na ya fadi idan na gan ta tashigo. Nace au sannu da zuwa tace yau ta zauna banga sun gaisa da Zulfa ba ban kuma kula ba sai maga wayana yana kara na dauka Doctor Fati ce tazo ashe tana tambayana ina gida ne nace eh. Ban ko kashe wayan ba sai gasu sun shigo gidan tun a kofa tace one family ke nan doctor kune nan gaba daya da iyalinki kuna harka. Kai lalai in dai wanan kwallitan kukewa ogo zaku ko rikita shi ya daina fita kun gan ku kuwa kamar wasu da zasu dinner dare. Mukai dariya nace kai doctor fati ke dai akwaiki da zolaya kwalliya kan ai sai baiga kallo gamu har hudu a jere ras sai wacce ya zaba. Zulfa tace kai doctor fati kamar kin san dama ina son ganin ki wallahi tace to ai gani tace wanan lace din da mukai magana yana nan na cire maki shi ihu tasa tace da gaske antyn mu ? Tace bake kikace kalar kike so ba ban sayar ba yana nan a aje maki naso idan zata fita ta kai maki a wurin aiki ne. Tace aiko nagode wallahi kin san kuwa har neman shi naje zulfa tace banace zan cire km aki shi ba dama ai kyau alkawari cikawa. Tace dama mota nazo gani naganta ma a waje gashi can su dear na kallo da ogan naku don muna shigowa ya dawo shi ma tace muje naga kayan kafin a zabe su. Mikewa mukayi nan muka bar ta zaune tare da yara muka shige abin mu mun jima a dakin sai gamu mun fito da kayan da ta zaba a leda. Har kofa muka raka ta can muka gansu tsaye suna kuskus a tsakanin su bamu kula su ba muka gaida mijin doctor fati dake jiran ta suka tafi muka juya zuwa cikin gida. Muna shiga Zulfa ke fadin wanan fa gulma tazo yi dama an tsegunta mata zancen motar ki shine tazo gani nace ita ya shafa wanan kuma. Tace bari ki gani yanzu zuwa gobe zakiji sabon rikici ya barke tace wa hindatu ai bata taba bari boni yai barci ita wurin kullin sheri. Ba wanda ya zauna falon cikin mu kowa dakin shi ya nufa don yamma yayi a lokacin can na samu su Aisha suna gwada wasu dogayen rigunan da na zabar masu cikin kayan da suka shigo. Carab na anshe rigar hannun Aisha nace kema kin san tun can na fada maki wanan diyana na sayowa helen kuma jiya akai min waya wai taki zama gun da take tace wurina zata dawo. Aisha ta fara fadin don Allah dai mumm ki bar min wallahi ina son rigan nan tun can nace ai sai da nace dake ki zaba kikaki yanzu ki zo ki dauke mata shi. Kuma ma iyakarki da wanan rigar Aisha a gida kawai don bai fita maki waje kinga tsagar shi yana da yawa a baya sosai. Sai ta turo baki nace ashe baki son cikin wanca da na sayo muna mu biyar masu tsadan nan bakiga na dauko su nan ba. Da sauri ta miko min rigar tana fadin wallahi nikan wacan din nake so a bar mata wanan din na fasa son shi. Atika ne kawai nake ganin dogon rigar nan baiyiwa sai Amira tace ida bai mata ba sai abar min don Allah mum na dauki riganunan ina dubawa sai na jefawa Atila dake kusa dani karamin kuma yana da kyau sai duk yara sukayo kan ta wai zasu kwace ta fado min tana fadin anty boye min don Allah sai duk suka danne ni wai zasu kwace rigan mun shagala muna ta ihuce ihucen mu a dakin ya shigo duk yaran na saman kaina suna son kwace rigar a hannu na don wani lokaci haka mukanyi wanan wasan dasu. Muryan shi mukaji yana fadin kai wanan wasan fa haka zaku jin mata ciwo ne ko may duk suka daga suna numfashi nima dai dariya nake masu nace kyalesu Atika duk wanda ya kwace maki sai na hada maki da nashi ki hada biyu. Suka fice daya bayan daya daga dakin don ganin shi ya shigo dakin sai bayan sun gama fita daga dakin ne yake cewa dani kin shige cikin yara kuna mugun wasa haka kamar wata karamar yarinya dake. Nace ina kokarin jawo dan kwalina daya cire dama may nake ba yarinyar ba kaine dai baka gani yanzu don kaga na tsufa maka. Baki ya dan mayde yace ni zan tafi magariba ya gabato sai dai da safe ke nan don Allah kisa Nasir ya rufe gida idan tara yayi. Nace za a rufe ai insha Allahu har ya fara tafiya yace dazun Raliya ta shigo tace wai duk baku tare ta ba daga ke har Zulfa may yasa zakuyi mata haka Rahama ? Nace ikon Allah so take na goya ta ko may ta shigo nai mata sannu da zuwa da yaya hanya may kuma take so nai mata bayan wanan. Yace har ma kun gaishe ta ashe nace wallahi na gaida ita da zuwa shigowan doctor Fatima ma yasa muka barta falon muka shiga dakin anty ganin kayan da akazo dasu. Yace to ni yanzu ma ina shiri ta bugo tana fada wai tazo matana sun mata wullakanci a gidana. Nace shiya kawota dama tsegumin in bashi ba ai naga har tazo ta koma bata shigowa gidan nan. Yace ni zan tafi nace sai da safe har yakai kofa nace gobe in Allah ya kaimu fa Su Amira zasu tafi sayen form din Jam sai dai dana yace wallahi shi bai son yin karatu a kasan nan. Ya juyo yana kallona tare da fadin sai ina zai tafi baida hankali ne killa kamar Nasir zan sake shi kadai zuwa wani kasa karatu . Baiji da kyau bane idan baiyi ba sai ya zauna gida ba gashi ga gidan yai ta zama mana nace haba daddy yarona fa yanzu yakai big boy ne fa. Tsuki yaja ta sake ce min sai da safe yana tafiya yake fadin idan na dawo na samu bai tafi ba sai na bata mashi rai gobe.. Nace ba a ko bata mai rai tare zamu je ya cika a zauna lafiya gobe din yace ato dadai yafi maku sauki kan. Da kyat na lalashi Nasir da ya bari muje ya cika ya bi umurmin daddy isan ya fara yi a na daga baya sai ka tafi inda kake so lokacin ka dan girma. Zulfa ta shigo ta samay shi yana cika yana batsewa ta samuna baki na samu da kyat na shawo kan shi da nasiha da komai ya yarda dani. Tare din muka tafi dasu suka cika form din don dole Nasir din ya cika saboda ubam yace ba zai kaishi waje karatu ba yanzu sai ida ya kara girma. Koda ya dawo gidan bamu nan mu fita lokacin ashe da wuri ya dawo gidan ba yadda ya saba hantsewa ba idan yana can. Sai da na shiga na dan huta na fito zuwa wuri shi na samay shi kwance rigingine ba barci yakeyi ba daga kofa na tsaya nake cewa dashi . Ina kwana ya dan juyo yana cewa dani har kun dawo nace eh munyi sakkone don mu samu da wuri da rana zan tafi aiki ne in Allah ya kaimu anjima. Har na juya zan fita nace ashe yau da wuri kadawo haka yace eh nadawo bakin hana a barni na huta ba kowa sai zargina yake wai nina saya maki mota. Nace Ya Subbahanallah kuma dai shikuma aka kulla yanzu kuma nace dole suce haka don ina yar matsiyata ko ita da ta sai nata kwanaki wa yai magana ko don ni yanzu na saya shine abin magana don ba a son agan ni da karuwa ko ? Bai dai yi magana ba ns juya na fita raina a bace nace wai may matan nan ke nufi dani ne kodan ya kasance ban iya karyan duniya ba ni da watace aiko da sun sha haushi wallahi don da komai na gani saya zanyi na shigo dashi gidan. Allah bai dora min irin wanan rayuwan na kwasan banza da wofi ba shiyasa har suka samu daman zargina idan sun ga nayi abu. Kwantawa nayi har na fara barci sai ga Aisha tazo wai inzo daddy yana kirana a falon shi take ce min naga Amarya ma tazo duk suna falin zaune nace tau. Sai da na dan bata lokaci na fito falon na samay su zaune suna jiran fitowan nawa na karso da sallama na na samu wuri na zauna kowa sai cika take tana batsewa a cikin su. Yace yauwa kun hadu ko dama ba komai yasa nace kuzo nan ba sai maganan motar Rahama da kuka gani kuke zargin ko nine nan na saya matashi da kudina na munafunce ku. Da sauri na dago kaina nace motar tawa ake zargi kuma hannu ya daga min alamar nai shiru na barshi ya gama sai na kada kai kawai tare da gyara zamana. Yace yanzu gaku ga ta kuji daga bakinta idan nine na saya mata ko na taimaka mata da koda kwandala ga sayen motar nan da tayi. Kafin nai magana sai zulfa tace haba haba dai yaya ai wanan maganan ma haka bai dace ba koda kaine ma ka saya mata motar ai ba laifi bane balle Rahama ai ba wacce za a zarga bane yanzu don an ganta da wani abu a cikin mu. Duk mu nan fa mun san aikin Rahama ban ga dalilin da zai sa mu dorawa kan mu wahala bayan mun an zata iya sayen abin da ma yafi wanan din. Humm umm inji Hindatu ina ruwan karere kina nufin ke nan yanzu Rahama tafi aji ko may kike nufi da maganan ta. In ma bata fi mu aji ba ai yanzu dai kunji ba shi ya saya mata mota ba don haka ya kamata ku bawa kan ku lafiya muyi fatan muma Allah ya bamu abin yiwa kan mu. Haba sai ko sukai cikin ta da masifa ni may zance tun da Allah yai min gata an karba min zancen sai naji Raliya na fadin wa za aiwa burgan aiki ko wa akafi aji ni wallahi kar nake kallon mace don nasan wanan plan din ba yau ba kada ku mai damu kananan yara mana . A raina nace zaki gane shayi ruwa madam don zan gwada maki na fiki iya bariki in shi kike takama. To yan uwa kun bani mamaki sosai wallahi kunce sai na bace ban fada maku uzurina yanzu kuma na fada maku amma hakan baiyi ba saida na samu marasa hakkuri da basu yarda da kaddara ba suna sake min magana yadda ran su ke so. Idan kuna ganin maganan da kukai ta fadi a gamay dani shine adalcin zama ko kuma zaku iya sani yi dole sai ku matsa kuyi tayi . Masu cewa ba zasu sake shiga group dina na ba matsala guban wani zuman wani sai Allah ya kawo masu hakkuri dani da yadda nake dama ko yanzu ina tare dasu sun dade suna hakkuri da rayuwa don sun san ba ni nai kaina ba nima yar adam ce kamar kowa acikin ku. Yadda kuke da uzuri haka nake da uzuri nima amma masu hankali a cikin mu sun san da hakan. Masu fadin kudi suka biya don na zauna ba hutu naita rubata masu labari akan dari uku sunyi kuskure zan iya mutum kudin shi yaje inda za, a dadada mashi ran shi. Ni ina can ina neman waya don na faranta maku rai ku kuna nan kuna ta aibanta ni don rashin hakkuri da son kai irin na wasu. Ina mai karaba wanda suka fahinci matsala na hakkuri ba kullun ne zaku dinga jina ba haka zan ta maneji har sauki yazo muna da fatan zaku fahince ni yan uwa nagode ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 92 Ubangiji Allah ya jikan anty yai mata rahama yasa ta huta yasa aljannan fidausi ne makomarta. Wanan mata bazan taba mantawa da ita ba a rayuwana duk wani rudin shedan da ya shiga a tsakanin mu lokacin dan zaman da mukayi a rayuwan ta bana taba jin zafin ta ko haushin ta. Saboda irin rayuwan da ta gina ma rayuwana a baya wanda har tawa mutuwar tazo ba zan daina amfana da abin da tai min ba. Shiyasa har gobe ina jin jinin ta kamar duk abinda nai masu ban masu wanda ita tai min ha sai dai na kwatanta kawai iya yina. Don abin da yasa nakewa mai karatu wanan bayan shine tun da suka fara cecekucen su zauna nake cikin kamala da sanin ciwon kai tankar ba dani ake wanan badakalar ba. Wanda yadda nake zaune cikin natsu ya jawo daddy mai da hankalin shi a kaina yana kallon yadda nake zaune ba abinda ya damay ni sai ma jan ajin da nake tankar ba da ni ake zancen ba. Don ban biyewa haukan kishi nai wani dogon hayaniya yadda ya tsamaci zanyi ba da farko. Wanan kuma zaki iya tuna training din da anty ta fara kaini na koyon zaman duniya tun farkon zuwa na wurin ta. Banga amfanin shi ba sai yanzu da girma yazo min na san ciwon kaina nake amfani da irin darasin da na koya a wurin. Watau mace ta zamo kamila mai jan aji da natsuwa ba ko yaushe a cikin hayaniya ba da watsar da kai. Raliya da yake mai ilimi ce ta san duniya sai yadda na mayar dasu wasu bi can ya bata mata rai don kishin yanayi na da jan aji ya tsone mata ido. Bata taba sanin na koma classic lady ba sai dan ganin da tai min din nan sau biyu baya dawowa na yasa ta gane cewa akwai aji sosai a gareni. Don na waye nasan duniya na san ciwon kaina komai nawa a natse nake aiwatar dashi ba kamar sauran ba. Take wani zafin kishina ya rufe mata zuciyar ta gashi taga akaina ake fitina amma sai waya nake kallo ina dan murmushi can na nisa nake cewa iya kar maganan ke na dama don ni zan tafi na shirya ina da theater da karfe hudu da zanyi. Na mike tsaye daga inda nake zaune na juya gun hindatu na ce Hindatu idan kina ganin komai daddy ne ke maki a rayuwa har kike zargin haka take muna muna kina hada dan karamin banga a gida don tayar da hankalin mutane to aiki babba na gaban ki kuwa don zaki tabbata cikin wanan halin. Ina fadin haka na juya na fara tafiya ina fadin Allah ya bamu alheri anty Zulfa don Allah ki bar bata bakin ki hakana. Don wanan bazata taba daina halin ta na sheri ba tana tauye rayuwan ta dana wasu ni yanzu banda lokacin bata wa wurin kallon abinda wata keyi naci gaban ta. Aiko ta shiga bakin ta don har na shiga daki na rufe tana faman surfa ruwan balain data saba yi bata ko gajiya ita da fitina shiyasa take kullun cikin bakin rai. Sai bayan na dawo ne da dare Amira ke fada min ai dazun fada kuma ya sarke a tsakanin Raliya da Hindatu kafin ta bar gidan. Kai Allah dai ya sauwaka ita wai bata tunanen yanzu yarta ta girma ne tana ganin abinda takeyi gashi gidan wani zata wata rana. Aisha dake shimfide baba tace ai ihisan din ce tai mata magana shine har ta daina fitinan suka shiga daki. Amira tace ai dai taji kunya a gaban daddy Anty tace mata kece kika fada min shiya sai motan don tun bai aure ta ba yake maku haka ya saya mata abu kuna kallo. Nace ji sheri fa banda motan da daddy ya saya min lokacin don zuwa makaranta yaushe ya taba sai min wani abu ni kadai. Amira tace maman kafin ta rasu ko yaushe maganan ta shine kunyar ki take ji takance gashi an zugata ta kasa fahintar ki yanzu gasu Nasir a wajen ki tankar ke kika haife su don abinda Maman ihisan take masu anan duk yaran na fada mata da yadda kike tarewa ba ki bari tai masu sheri. Shine fa takance ita bata san may zatai maki ta wanke laifin ta ba a gareki . Nace Allah sarki antyna ni bata da laifin komai a wurina ni abinda tai min har na mutu bazan taba saka mata shi ba a rayuwana. ********* ********* ********* Azumi yana gabatowa kowa na shirin zuwan shi munyo odan kaya sosai ni da anty Zulfa inda ta tura kano da sauran wurare don a sayar mata muna daukowa indiya da chaina. Ranan muna cikin daki anty Zulfa muna kallon kayan da aka shigo mata dasu sai shirya kayan su Aisha da Amira da Atika ke faman yi. Zaune nake a saman dogon kujera sai ga Jinior ya shigo yana fadin daddy yana neman mu a falo nida maman baby yadda suke kiran anty Zulfa ke nan. Mun fito yana kishingide a saman center carpet yaran duk sun rufe shi yana biye masu suna son kwatan abu a hannun shi. Sai Hindatu da ke zaune daga gefen shi ta hade rai da alama yaran sun damay ta ke nan da hayaniyar su da sukeyi da uban nasu. Mun zauna tare da gaidashi sai dan wurin Zulfa hanif ya nufo uwarshi yana fadin mama baba ya sayo muna. Tace ai ku kenan kuyi ta faman shan zaki yana biye maku kuma bai daina saya maku kullun sai dankanoma kuke fama dashi. Dan kanoma ko lalacewa ya mai da yara kamar wasu diyan zinare can yai zaune a cikin su yana wasu abubuwan da bai dace ba dasu. A yanzu ko naga ko a baya haka yake da yaran shi kowa yasan halin yaya a kan yaran shi sai dai in yaran na yanzu ne ba a son ya zauna ya fahince su kuma muji. Daddy Jinior tace kana neman mu ko na fadi hakane don kada zancen su yai nisa sosai a wurin don sun dauko sake layi. Ya gyara zaman shi tare da dago Abdul daga jikin shi ya rugumay yaron yana dan buga bayan shi a hankali yace. Kin shirya saurarena ke nan baki biyewa wannan haukan ba don banga dalilin dan magana kadan sai an mayar dashi dogo ya zama na fitina ba ko yaushe. Ayi hakkuri inji Zulfa tace abin hassada ne ba a raina shi a gidan nan in bashi ba yaro kuma ace ana hassada da zama da uban shi. Idan basu mamay ka ba wazasu mama suji sanyi a ran su bayan kai da mu da suka sani nace anty abar zancen don Allah hakana. Mun yi shiru can yace dama ina son fada maku ne ba zai muyi azumi a gidan nan ba don na samu wani wuri a cikin nan maitama ne. Kowan mu yai tsit yana sauraren shi yace gida ne babba da kowan ku zai samu walawa a cikin sa yadda yake so. Part na farko mutum biyu ne zasu zauna cikin sa shima dayan hakane da sauri zulfa tace har Raliya ke nan nan zata dawo da zama ita ma ? Yace ai kinji nace kowan ku sai kunje kunga gidan ke Zulfa zaki zauna tare da Rahama a bangare guda haka ma ita hindatu da Raliya sai su zauna a dayan bangaren. Nace yaran fa daddy ? Yai dan murmushi yace uwar yara inda kike ai dole dake zasu zauna dayan part din yafi girma don akwai extract dakuna har biyu sai shi dan naki akwai dakin shi a kasa shima nawa dakin sama zan zauna. Dama dai ka gama tsarawa ne ko mu fada muna kawai kakeyi yanzu inji hindatu ta fadi haka a hasale. Shi ya bata amsa da fadin eh na tsara komai fada maku nakeyi don umurni nake bayarwa ba wai ra, ayi ba. Shiru mukayi gaba dayan mu sai Zulfa ce tace dashi zuwa yaushe zamu koma sai yake cewa nan da sati mai zuwa insha Allahu. Kunga kafin azumi kun dan saba da wurin ke nan Allah yakai munace tare da fadin Allah ubangiji yasa mu koma a sa, a gabadaya kowa yace amin . Ina kokarin mikewa ne yake cewa ga wuri yayi nisa ban san yadda zakuyi da wa yan nan kayan naku ba ? Don ba abinda zaku dauka a nan din komai na sa an saka maku a can iri daya don ban son wani korafi ya biyo baya kuma. Zulfa tace dashi ai wanan ba matsala bane yaya ko motar company ku ba sai kasa ya kwashe muna ba zuwa kano. Hindatu tace shine ai yace idan kun shirya su wanan baida matsala sai kowa ta fadi inda za a sauke mata nata. Tun daga wanan ranan aka fara shirin komawa sabon gida ba wani hira sai na komawan mu can sabon wurin kowa keyi. Ban zauna ba ni aiki ya sha min kai sosai a lokacin sai ga helen ta dawo ta girma ita ma sosai a lokacin don tunda ba karatu takeyi ba nasan ta kusa aure ke nan A wurin Zulfa nake samun labarin wai anyi fitina dashi da Raliya tace bazata koma ba can inda take zata zauna ita. Tace karshe ma ashe cewa yayi dole ta nemi transfer ta dawo da aikin ta nan Abuja inda kowa yake yanzu dai ban san yadda suka kare ba. Ai bazata so ta dawo nan ba tunda can yafi mata samu nan kuwa kinga idan ta dawo dole kasa zata koma tunda akwai na gaba da ita da yawa. Tace a dama ai galihu ne kawai irin na mutanen mu har takewa mutane sallon wai ita saura kiris takai manager yanzu. Yanzu akai mu gani mana in kaiwa banza ne nasan dai ba karamin kwasa zasuyi ba kan hakan matar da ta saba haka take kamar faransi ba oda ina zata iya zaman gida yadda yake so. Ni dai ina jin ta nasan koni haka akaita zagina a baya ban ma sani ba ko yanzu ai ban debe tsanmani don kishiya sunar ta kishiya ai. Ranan Laraba da ya zagayo ya kwashi yara ya fara kaiwa shi da Sani da motocin mu da duk wanin abinda za, a bukata sai mu da bamu tafi ba mun tsaya sai an kwashe kayan kowa a gaban idon shi. Bayan an gama ya dauke mu shida zulfa a gaba ni da hindatu muna baya sai hadiyan rai takeyi ban san may ya bata mata rai ba a lokacin tundai safe take hakana a gidan. Gida ne babba mai kyau ga tsari shigen ginan mu na na can kano sai dai wanan din ya nuna mai aikin wayewa da akayi na zamani. Mun shiga da addua da godewa Allah yaran ne suke nuna muna ga inda daddy yace namu ne duk komai iri daya ne har ginan wanan dai dakunan da aka kara biyu sune banbancin mu. Amma bayan hakan komai iri daya ne kowan mu zata tashi da dakuna biyu a bangaren ta. Abin yaiwa kowan mu dadi sosai nace Zulfa ta fara zaben inda take so sai bayan ta zaba na farkon ta dauka ni kuma na dauki wanda ke daga ciki ni yafi min sauki ma don hayaniya da ban so sosai idan ina resache. Wata sabuwa Hindatu ce tazo tana fadin kuji min wanan tsohuwar wofi din duk sai muka waiga gunta muna kallon ta sai take cewa wai fa Raliya ke fadin ita bazata zauna part daya dani ba sai dai wai a hada ta da Rahama su zauna wuri daya watau mu tsofin mata ya hade mu wuri guda ke nan. Kuji min tsohuwar banza mai mayar da kanta baya don Allah wai kamar Raliya ke cewa wai mune tsofin mata jifa don Allah. Dariya zulfa tai mata tace haba haba dai ke da mutumiyar taki kuma za a ji kan ku ai bai dace ba haka ku dai sasanta kan ku acan. Tace bari Zulfa matar nan ta bani haushi wallahi bata san ina dakin ha ta bugo mai waya tana wanan maganan. Ai ban bari takai karshe ba nace ke tsohuwar banza wace bata san may takeyi ba wa ye tsohuwar bake ba ke ba a gujeki ba shine ke zaki guji wani. Dariya ta bani sosai har na kasa hadewa sai da na fasa shi nace da ita amarya ce fa maman Ihisan tace kai amma dai ke amaryan may can. Haihuwar ta hudu fa har da bari tace min wanda ma aka sani ke nan fa na boye wayasan su. Tunda shima uban aiki bai san hakan ba sai daga baya don ta boye mai komai da farko akan zancen diyan nata. Nace kai hudu fa kikace tace wallahi Allah ko kuma dasu zata dawo nan gidan wai da sauri Zulfa tace wani gidan ? Tace ai sai kiyi tunda uban aikin ya yarda mu may zamuce na san dai akwai tsiya kan a gidan nan don ban yarda agola sufi min diya na. Dariya sosai muke mata har taji haushin mu tace ai dole kuyi mun dariya tunda baku aka taba. To maman ihisan aiko mu ba a bari ba don gidan gaba daya ne kila tsarin zaman a tare bai mata ba ta bullo ta wanan tsigar kuma. Kuma wallahi dole ta zauna ba tunda ba fin kowa tayi ba ta zo a zauna in kasa akaci a kwaba tare a hade shi. Zulfa ta kallo inda nake tai min signal da idon ta wai nai shiru nace yanzu dai ai gamu gani ko tunda dai namu dama idone mai daki shiyasan in da ruwa ke mai yoyo. Ta dan jima tana ta tonon asiri har ta gaji ta koma wurin ta Amira tace wai mummy ku baku san tana da yara bane dama ? Nace nifa ban san komai bz a kanta kin san ba ta dade ba na tafi germany shiyasa ban ma damu da nasan komai ba akanta. Tace wai danta ya girmay ni nisa ba kusa ba wallahi baki gan shi gudan babba dashi fa ya kusa kai daddy tsayi muka kwashe mata da dariya kawai. Yanzu mun samu hutu da rage fitina don kowa akwai kitchen a part din ta sai daga baya nake ji ranan a wurin sani wai sayen gidan yayi ashe da kudin shi ba haya bane. Nace a raina lalai alamarin daddy ya bunkasa sosai ke nan har ya iya sayen wanan katon gidan haka a garin Abuja don iyalin shi. Saura kwana hudu a tashi da azumi daddy ya shigo muna zaune a falin mu Abdul na saman jikina yana rikici wai sai na goya shi bai son na kowa sai ni. Tun daga main falo yake jin kukan yaron na tashi ya shigo bayan ya sallami bakin shi sun tafi yana fadin. Wai may ya samay shine haka yake kuka daidai ina dukan shi don ya isheni da fitina tun safe yake hakana a gidan anyi lalashin duniya yaki yarda da kowa. Nace fitina yake ji yau haka kawai ya tashi haka yanzu wsi shi sai na goya shi yace to may zai hana ki goya shi din yaro jeka ta goya ka kaji Allah ya taimake ka kai ba wanda ya hana ma bayan ma. Ni wai ban gane ba fa har yanzu naji shiru in dai ba planning kike yi ba Rahama kin dai san bani kaunar wanan abin ko kadan. Murmushi nayi nace Allah dai ne ya tausaya min don wanan dan fitinan idan ina zan iya dashi haka. Take naga ran Zulfa ya baci har ya lalashi yaron ya dauke shi zasu fita baitai magana ba a raina nace kishiya ke nan baki da tabas ai dama sai dai a tafi a rufe kawai na ciki na ciki dama. Ya kai kofa ya juyo yana fadin yau Raliya zasu dawo fa ina fanin don tace dani sun taso dazun. Ita dawa zasu dawo naji kace zasu dawo inji zulfa da sai yanzu tai magana dashi tun da yai min maganan samun ciki a gaban ta. Yace idan tazo ai zaki gani tace aiko gamu gani din Allah ya kawo su lafiya mu sha kallon yan birni. Ya dai fice da yaron abinshi daga falon bai tanka ta ba nima don ta san na fahinci may take nufi sai na share ta na ci gaba da karatun wani takarda dake hannuna. Haka har muka watse don ra san na gane manufanta amma kada abin yai nisa sai naji tace dani ashe yau Rahama kina da baki ke uwar yaya. Nace gaki uwargida ina ni ina wani kwashe kwashe can kedai zata dinga barwa yaran idan zata tafi ai tunda kece uwar gida sarautar mata. Tace a ina uwar gidan take nan kudai da kuke jin lokacin ku ai sai daku gashi yanzu har yana maki tuni kin dade baki haihu ba hakana. Murmushi nayi ba yanzu zan bata amsa ba na kira Aisha nace ta dauki min magani daki na ba baba har Abdul din dake rikici idan an dawo dashi. Bayan ta kawo min maganin ne na matse yaron na bashi yasha sai dan wirin Zulfa hanif yazo wai shima na bashi nace dashi allura dai zan maka sai yaron ya gudu can kuma ya sake dawowa ta nace wai sai na bashi maganin ya sha. Uwar tace wallahi hanif zan doke ka yanzu kuwa dannema ina faman kafa kafa da ku kace a dinkira ma magani lafiyan ka kalau kuma. Nace nima ai ba mahaukaciya bace da zan bashi magani don nasan illar yin hakan fiye da kowa. Bance zaki hashi ba ai shi nake ma fada nace a, a bashi ba dai aiko kana dasu da yawa baka cutawa wani don baidasu yana kafakafa da abinshi. Shiru tayi bata sake magana ba sai kallo mukeyi kowan mu yayi shiru yaron yazo ya lafe saman kafana na dauke shi na aza a saman jikina yai barci. Haidar na ganin haka yasa rikici wai ya tashi tace yaki tashi ai ba uwarka bane kai kadai in kana son dauka zo na dauke ka nan mana. Sai yaron yace baiyi na hawo shi nace kyale mama kaji bari in yai barci sai na sauke shi ka hau kaima. Wani hira ta dauko min da haka muka wayance zancen kowa ya manta da abinda akayi muka basar dama shine kishin ba komai ba. Sai wajajan shida ga Jinior ya shigo yana hakki yace mummy kin san may nace a, a jinior tace wallahi ga matar nan matar nan mai sallon nan ta zo harda wasu yara ana shiga masu da kaya wurin maman Ihisan. Addua na fara a bakina na neman kariya da tsarin ubangiji Allah akan zaman da zamuyi da ita a gidan. Ba wanda ya shiga don dama Allah ya taimake ni yarana basu da irin wanan shige shige na wasu dakuna ba wanda ya tafi inda suke. Ko dakin Zulfa da muke kusa wuri daya basu shiga idan ba ya kama dole ba ka tsare yaran ka wuri daya alheri ne a wanan zamanin da muke ciki don kariyan kai. Yaron ka in yana wanan halin zai iya shiga wani hali baka sani ba haka ma za, a iya zarga mai wani sheri ba tare dz kaika sani ba ko yaron. Shiya ka zamo abokai da diyan ka shine kawai alheri d mafita a wurin ka don yanzu lokaci ya canza kowa nashi ya sani ba kunya a kan hakan. ********* ********* ********* Har suka kwana suka wuni ni dai ban sasu a idona ba daga ita har yaran nata data zo dasu wurin yar sa idon shiyan mune ma nake jin wai yaran ashe duk manya ne dasu. Ni dai na jawa yara na duka kunne kan su iya kan su daga uwar har yaran ba ruwan su da kowan su nasan kuma insha Allahu zasu ji magana na. Balle ma Amira da taki jinin ta kamar yunwar cikin ta bata ko son ai mata zancen Raliya sam taci uwar bari gunta ko. Ban san tana falon ba na shigo a cikin shiri na, nazo na roke shi zan kai yara gun baba daga csn idan an gama masu zamu dan je nakaisu yawo. Ganin ta baisa na fasa abinda ya kawo ne ba kai tsaye na nufi kujeran da yake zaune akai na dan zauna ina cewa sannun ku da hutawa shi kadai ya amsa min nace daddy don Allah ina son zan kai yara gun baba daga can zan dai kaisu su sayo abu yan matan. Gaba daya ke nan zaku fita dasu ko nace eh ba iya tafiya biyu shiyasa nace su shirya mu tafi. Kada ku bari yamma yai maku a waje kin san bana son hakana dai nace nima ina da abinyi idan mun dawo, ba zamu kai har yamma ba ai. Na mike ina fadin mun tafi yace kudin askin yaran fa ko an yafe min ne na barshi nace zasu shigo ai su karba nazo fada ma zamu fita ne dama. Daga haka na sa kai na fice falon ba wanda yaiwa kowa magana a cikin mu ina fita taja tsuki tare da kawar da kanta kishin ya motsa ke nan. Nima hakane dana samay ta a fslon sai da naji nawa kumzllon ya zaburo min daurewa dai nayi na hade shi ya koma inda ya taso. Bayan kamar minti goma sha sai gamu mun fito tare da yaran suna gaba ina bayan su muka shigo falon har lokacin tana nan zaune a falon. Nan suka kewaye shi kowa na fada abinda zaije yi Amira taje gefen kujeran da yake zaune ta lafe a bayan shi tana fadin daddy kudi zaka bamu muje shopping yau. Harara take watsawa sai gani na shigo ina gyara hijjab din dake jikina nace au zama ma kuka yi Aisha dake gabana tana cewa daddy ina wuni yace a, a Aisha duk wanan kwalliyan haka na fita ne ? Tace daddy ai ban yi kwaliya ba tunda da anty zamu fita kasan ita ustaziya ce yace lalai ke kuma fa ? Helen ce ta katse masu hiran su da Aisha da yake mata wasan barkwanci idan yaso don ba kullun yakeyi ba sai idan yana son nishadi. Ya sa hannu a aljihu shi yana ciro kudi yake cewa ku yan mata sai a dan baku mai yawa ko don naga ance yau shopping ne za, a da mummy. Ya mikawa kowa kudin har yan samarin da zasu wurin aski sai da ya basu nasu yadda zasu sayo abu a can Ihisan ce ta shigo daga karshe tana cewa mummy bana ce zan tafi ba. Nace ayya ai na dauka ko kina barci ne tace yanzu nunu ke fada min taga kun fito ai, jinior shine mai alaman rashin kunya irin na yara yace bazamu dake ba ke ma ba kina fita da maman ki ba ki barmu. Kai jinior zan buge bakin nan naka yanzu ashe ba anty bace ko kake mata haka bana hanaka yiwa yannen ka rashin mutunci ba ko . Ya ja baya yana magana ciki ciki na ce mu zamu tafi ihisan karbi kufin ki gun daddy mu tafi muka juta muka barsu a nan yana bata kudin ta. A kofan gida na ga wani sauri zaune kallo daya nai mashi na kawar da kaina ya na charting a wayan shi. Yana ganin yan mata naga ya tsura masu ido yaron bai min ba na tsaya ban fita ba sai da naga kowa ya shiga mota nima na shiga muka wuce A mota na muke tafe duk motar ta dauke mu harda Nasir da bamuyi niyar fita dashi ba a lokacin amma ya nace sai ya bimu ya dauki Haidar da hanif shi kuma jinior yana tare da ni. Mun kaisu gun baba sai da suka dan bata muna lokaci muka samu akai masu muka nufi wani babban store na kaya nan suka shiga kashe dan kudin da aka basu karshe ma sai dana cika masu muka dawo gida tun daga nesa na hango wanan yaron zaune again. Nace wai waye nan zaune tun dazun na ganshi da zamu fita sai ihisan ta ja tsaki daga bayan motta tace dan matar nan ne fa wai shima a gidan nan zai zauna. Sai shegen kallon mata wallahi ni haushima yake bani gashi kamar mugu idan ka gan shi ni wallahi ban san may yasa aka kawo muna su gida ba wallahi. A raina nace akwai matsala kuwa gani da wa yan nan yan mata haka kuma wanan yaron dagani dan zamani ne irin yaran nan ne da ba kwabo. Ga wani shegen aski da yayi a kan shi wandon shi irin yadda hitsararun matasan nan kayi wai sagin nace dasu to ku saurara dakyau wallahi gaba dayan ku kuyi hankali dashi kunga dai bamu san tarbiyan shi ba ko ? Ina shiga ciki da mota naga yan matan su biyu a waje wai suna selfi a cikin huranin gidan sai ihuce ihuce sukeyi abin su. Nace Allah ka cece mu wanan rayuwa haka akwai aiki kuwa gaskiya kowa tasha dogon wandon pencil da matsatsen riga a jikin ta. Da suna muna wani yauki amma muna fitowa sai suka bimu da kallo don basuyi tsanmani akwai zukakan yan mata haka ba a gidan. Kowa ya shiga gida da kayan shi niki niki har ihisan a falon mu muka tsaya da ita ana duba abinda kowa ya sayo a wurin. IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 93 Ganin yaran nan da nayi bai min dadi ba sai dai ba zaka aibanta dan wani ba sai addu,a da fatan alheri ga dan kowa shine adduan ko wace uwa tagari ga ko wani da tagani. Don haka ni dai na dinga kafa kafa da yarana tare da masu adduan neman tsari daga sherin shedan. An tashi da azumi kowa ya dauki niyya sai wa yanda aka sahelce masu yin azumin kamar yara tsofi marasa lafiya da sauran su. Muna ta kokarin hada abinda zamu sha ruwa dashi a part dina ni da yara ko ina ya dauki kamshin girkin da suke tayi kowa da abinda yake son ci idan ya sha ruwa. Zulfa ta shigo tana cewa a, a wanan kamshin yau duk na masu buda bakine haka ko may ? Ina daga kwance nace da ita ai duk hadama ne irin tasu yanzu karshen ta ma da an sha ruwan nan zasu barni da abincin a kitchen. A, a mummy nikan nawa tas zan cinye shi ai daidai cikina na soya muna ma Atika dariya daddy ya shigo falon namu. A, a da alama dai ku azumin bakwa jin shi yau wanan dariyan haka da kuke kwasa kamar an maku bushara. Yaran nan dai mukewa dariya sun hada abinci kamar masu shirin taron baki wai duk na shan ruwa ne haka . Amira ta dauko kula tana fadin daddy yau dz abincina zakai buda baki ko na hada delicious mai dadi, Murmushi yayi kawai nace yau kan kin makara don daddy gun maman Ihisan zai buda bakin shi sai yarinyar tace shitty wallahi na dauka a gun mummy ne ko maman baby da kaci dahuwana. Murmushi yayi yace ku bari idan su mummy naku za suyi girki sai na zauna naci har sai na koshi. Ya juya yana cewa Sani zai shigo maku da kayan shan ruwa don mun makara bamu samun lokacin zuwa kasuwa ba da wuri. Ni dai ban mayi magana ba don ina fama da Abdul mai fitina wai orth din da aka bashi akwai zafi har ya gama ya fita wurin mu. Ba a dauki lokaci ba Sani ya iso gidan da kayan cikin wata mota haka mai girma duk kayan da ya shigo dasu almost a part dina ya tafi. Don suna suna aka bi aka sayawa kowa kayajn shan ruwan har helen d bata sallah sai da aka bata alhakin ganin ido. Ni dai ban san yaya akayi ba don kayan ma da ya shigo dasu lokacin mun gaji nan muka barsu a falo yadda ya tara muna su. Fitinan zancen kayan ne ya tayar da mu tun da safe daga barci muna barcin mu mai dadi na safe na azumi sai ga daddy ya aiko wai mu zo kusan Hindatu ce ta karshen fitowa ranan. Da alama fita zaiyi a lokacin shi ba ma kwanciya zaiyi ba kamar yadda mu muka dan samu hutawa. Bayan duk mun zauna ne yake cewa damu ke Zulfa damay damay sani ya kai maki part din ki jiya ne ? Nan ta shiga lissafo mashi abinda aka kawo mata din ya juya gun hindatu itama ya tambaye ta tace ya kawo min kayan abinci sai kayan tea nawa dana Ihisan yace. Rahama ina jin ki yace dani nace nima kayan abinci ya kawo muna na shiga lisafo mai kamar yadda sauran sukai mai lissafi. Yace ke ina jin ki tace a, nima dai ai shi aka kawo min din yace ki fada yadda kowa ya fada min inji tai shiru yace ke nake sauraro don ban son alamari da zargi da kuma tauye hakki akai. Dole ta lissafa mai kamar yadda mukai lissafi da tagama sai yace good yanzu ina son tambayan ki akwai wani wanda nabawa abinda yafi naki a gidan nan ko na yaran nan. Koko da kikie cewa na bawa matana abinda raina ke so ke na baki kadan ke da diyan ki don bani na haife su ba, . Nawa kike son na rage daga ciki na kara maki tace ai ni ha shi nake nufi ba ni nufina don may akai hakana ba a bawa kowa equal ba. Yace saboda gida nane kuma kudina ne sannan kuma iyalina ne dama ke dashi kika zo ne wai? Ke basuyi bakin ciki akan diyan ki da kika zo dasu ba sai kece mai bakin ciki da su da yaran su komay ? Tace wa zanwa bakin ciki a cikin nan kayan tea da sauran abubuwan bukatu basu fi karfin saye na ba balle don nai magana har ka zaunar dani a gaban matan ka kana son yi min cin mutunci. Yace kin baki cikin kan don in ma na fushine hindatu da akabawa ita da yarta da yar aikin ta kawai zatai fushi bake ba . Humm wai sani in fika agalo da rabon gida yau shine nan to mu haka muka saba a gidan nan inji Zulfau mu wa yan nan kayan basu kai na wanan fitinan ba don wani bai taba karewa ba ba a kawo ma wani ba. Hindatu tace mu din da ba kowa ba a wurin ki gashi bamuyi hassada ba sai ke ce kikayi yanzu indan da kinfi karfin shi da baki bi baya kinyi korafi ba ai. Tace dama kayi niyar wullakantani yasa ka dauko ni ka hada ni da matan ka ba don kaja min wullakanci da raini. To sannu mama uwar matan duniya wai ke Raliya may kike daukan kan ki ne ko wa kike ganin kinfi wani abu a gidan nan wallahi in ma ganin wani abu keka wa kan ki to ki sauke don nan dai bama wacce kika kai balle kifi mu. Tace a haka din Zulfa tace a hakan kuwa da kika gan mu don tsafi guda muke bautawa kin kuma sani kika shigo. Ban daiyi magana ba har lokacin sai tagumi da nayi da hannu na daya mamaki ya kashe ni na wanan zancen don sai naji duk ta karkare zube min a idona gaba daya. Don ni kaya ma duk suna falona ban shiga dasu a ciki ba har wanan lokacin da takai wanan korafin a a gaban shi. Nasan yawan kayan da taga an shiga dashi part din nawa yasa yaranta fada mata ita kuma bata san cewa tsarin shi ba ke nan har yaro na goye sai an saka shi ga lissafin komai haka nima nazo na sama sunayi a gidan. Anty da kun so kuyi shiru ba wai abinda take nufi ke nan ba sai nai murmushi bayan na fadi hakan garesu. Ta wani juyo ta kalle ni a lalace tace ai sai ki fadi abinds nake nufi ke da kika san manufa na din akan maganan danayi. Nace cikin murmushi, kamar yadda daddy ya fadi ne dazun mu bamuyi bakin ciki da yaran ki ba da akabawa dsidai da namu sai ke ne zakiyi bakin ciki don daddy ya ba harda kananan yaran da ba su azumi abin shan ruwa don kina ganun iyayyen su zasu yi amfani dashi ko ? Bayan wanan ba wani abinda kike wa wanan hassdan to bari kiji Raliya kike kowa ma ki tambayi anty hindatu kiji idan ni kayan tea sun damay ni a baya da nake nan tare da ita rabon baba ita nake bawa na shi nace ta kara da nata. Ni fa wanan abin da kike gani basu damay ni ba yanzu haka kafin a kawo wanan din da kike magana wanda ya saya muna na monthly yana na wanda kuma aka bamu gun aiki sunan nan na shigo dasu sai hindatu tace har aban mu daga ciki ba. To shine may sai kifada masu suda ke jira ki kawo masu suna zaune su karba amma ni kin san nafi karfin wanan. Don yadda aka baki nima anbani din sai Zulfa tace da baki fada ba mu din dake zaune tana bamu bawai mun rasa bane ko mun gaza a, a zamantakewa ne na alheri yakawo hakan. Don duk kan mu nan koda kike ganin muna cin kan mu yanzu muna da fahintar junan mu akan haka duk abinda ka samu sai ka tsakura wa dan uwa badon rashi ba ko tsoro muke haka don mu koyawa diyan mu akida na alheri muke wanan rayuwan. Abinda ka samu kaci da wani shine ranon ka gobe kiyama ba wai wanda kavi kai kan ka ba zaka mora don shi ya zama bola ko. Shiru tayi don ta fahinci bazata ci riba ba tace amma dai hindatu ke munafukace ta gaske ina kece kafin na zo kike fada min haka akewa Rahama ko yaushe idan anzo rabo kina son na kwato muna yancin mu. Haba dai yanci fa akaina ko akan wa kika zo kwata ashe ko zaki mutu baki kwato ba in dai nice don nafi karfin ki har abada. Ai ba san da ni kikai damara ma tun tuni da na yi mara ba dake ta yadda kika zo min din don a banbanta tsakanin kasa da tsakuwa a gidan. Kai ya isheni ba shi na kiraku yiba ga hindatu itama ta gefe tana fadin lslai Raliya kin kai katuntumar munafuka a duniya. Kada ki tsanmanin ko na manta yadda mukayi dakw kirana kikayi a waya cewa kin ji ance komai dear kewa Rahama sai ya fifitata da kowa akan komai don tana rike mai yan marayun shi. Idon rikon makircin da takewa yaran ne sai kinyi sanadin da kika rabata da yaran kiga tsiya ita kuma ki hana mata rawan gaban hantsi a gidan nan. Kince sai kin mayar da ita goro abin saye abbabu cikin gidan nan sa ita da banza duk daya zaki mayar da ita . In tana takama da dan karatun likitan da rayi ne nasa ido na gani sai kin yi sanadin da kika sa tabar aikin ma gaba daya a gidan nan da ma aikatar su. Ke dan Allah ya ishe ni haka na munafukan banza munafukan wofi kawai dake da ita kuna tunanen ban san irin makircin da kuke kullawa bane a gidan nan ko may ? Gaba dayan ku nan ba wacce ban san halinta ba don haka ba sai kun fada ba nasan duk makirci da kuke kullawa shiyasa ma na mayar da kowan ku nan naga iya gudun sherin ku din. To bari kuji daga yau kada wacce ta sake samuna akan irin wanan shirmay naku na banza a gidan nan ke ma nayi maki hakane don ki san bani daukan irin wanan halin a gidan nan. Saboda naga kin kasa fahinta na da lalama don haka daga yau bana son jin wani gulma ko sheri ya taso ga dukkan ku a gidan nan in ba haka ba har naji ran mai shi sai ya baci. Babu mai iya korar wata a cikin ku tunda ba wacce ta aje wata anan sai ni don haka mu zuba ga mai irin wanan halin a gidan nan mugani ni da mai shi. Yana fadin haka ya mike yabar mu zaune a falon ban zauna ba na mike na fice daga falin nima zuwa part dina zuciyana tab da tunanen wanan rashin wayo na matar nan. ********* ********* ********* Kamar yadda ya saba muna ko wani azumi hakan ne ma yanzu yai muna kayan azumi dana sallah ya kasa kashi hudu yace kowa ta kwasa ta aikawa iyayyen ta dashi kafin su dauka Raliya ta zubur ta kwashi na gaban Zulfa haba. Zulfa tace dawa Allah ya hada ta bada ita ba zubur ta rike mata hannu tace baki isa ba wallahi idan baki daukan na gaban ki sai ki barshi. Kai kai ban son fitinar tsiya wai ke may yasa baki kama girman ki ne ko yaushe ki zauna kina fitina akan abinda baikai ya kawo ba. Zulfa fara dauka sai hindatu ta dauka Rahama idan ta kwasa ki kwasa sai ita daga yau haka nake son a dinga yi. Itace dai tazo da nata zalaman mutum na wa mutane ssllon shi mai shine amma dan abu kadan ya tsone mashi ido don son banza irin na mutum zulfa ke fadin hakana tana kwasa. Hindatu kan dataga fitinar da yafi karfin nata haukan sai tsuki take ja nace a raina kadan ma kika gani tsohuwar banza kawai. Yara na kira bayan nace na gabana nake so suka zo suka kwashe min nida zulfa ihisan ma ta kwashi na uwarta ta kira yar ta wai mimi tace suzo su kwashe mata nata. Sai ga yarinyar ta shigo da wani matsatsen wando duk surar jikin ta a waje ina kallon daddy ya kawar da kan shi data shigo falon. Kudi ya mikawa kowar mu yace mu aikawa iyayyen mu dashi su sai abin sallah nace mun gode Allah ya kara budi ta hanyan alheri sai kowa ya shiga godiya. Ban son dogon zama irin haka don ba a watsewa lafiya karshe ina ganin ya gama na mike na barsu nan na shige abina. Ina shiga Amira tace humm umm mummy kinga wani wando da yarinyar shiyan nan ta saka tashigo falon ga daddy a zaune kanta ko dan kwali babu. Nace nata kallar wayewan ke na Amira fitar da tsiraici in kinga haka ba a kwabe su da yin hakan bane tun farko. Tace to ai mummy indai wando mu ba a gwada muna wanduna a gidan nan nace iyakar ku kuwa shiyan nan ba dashi. Tai dariya tace kai mummy ai na sani ni mamakin yadda ta shiga falo hakana ga daddy zaune nake ji ai. Ashe bayan fitana da zadu watse sai yace ta tsaya maganan wanan shigar na diyar ta yai mata . Sai tace to may ye kuma a cikin hakan naga a gida suke zaune ba fita tayi haka ba waje dashi nifa yara na sun saba da free life ban faye son takurawa yaro ba a rayuwana. Yace to nan gida nane idan baki son nina takura masu wallahi ki tsawata masu ga abinda sukaga yan uwan su ba suyi min. Don ba zan yarda a kawo min gurbataccen akida ba a gidana ina zaune lafiya da yara na tace dashi wani sabon fitina dai kake so dani kawai. Naga dai da yardan ka nazo da yaran nan don tun farko sai dana fada ma ba zan barsu a kano ba na dawo nan na zauna fakon diyan wasu nawa na can zube. Gwamma duk abinda sukeyi suna gabana yafi min sauki kace ka yarda nazo dadu da aina kowa ne shine yanzu zaka zo min da magana don yarinya tasa wando kawai. Yace ok so kike ajimu kan yaran nan ke nan tunda har na fada maki ban son hakana ke wata irin uwa ce da batasan abinda ya dace ba da yaran nan. Haka ahi wanan yaron nagan shi a kofan gidan makwabta ni bani son iyalina suna jaye jaye ina zaune kalau cikin rufin asirina. Tace kuma dai shima najin ke nan sai nayi ta kullen shi a gida tana koyon akidar mata ba fita ko may don ka gan shi kofan wani gida gidan ya shiga ne ? Shiru yayi don kada zancen yai masu nisa don ya fahinci akan yaran ta zasu fara samun matsala da kowa a gidan. Zulfa ta samay ni muna hira da Amira ina zaune ina mata kalaba a kanta take cewa dani wai Rahama baki fahinci matar nan bako ? Nace wake nan anty tace Raliya mana tsohuwar banza nace kuma dai amma azuciyana cewa nayi ai tafi nan ma. Tace ita fa by all means ta zama uwar gida tana leading din mu take so wai ita a dole tafimu shekaru take nufi ai tasan yara ne mu ta aure shi ta zauna da mu. Nace anty nifa kwata kwata bata gabana wallahi don ni halinta bai min ba bamu zuwa daidai in ba don daddy na yawan taka mata burki ba da kullun sai anji bakin mu da ita a gidan nan. To ya riga yace bai son fitina kinga shiyasa ni ba ruwana da tsabganta daga ita ko har yaran ta ma basu gabana. Tace yau ai naga fitsara kinga yadda yarinyar ta shigo muna haka kerere da ita da wani matsatsen wando can abu ko gaba babu ciki. Dariya maganan ta ya bani sai kuma tace ke ko fa uwar haka take a bushe wallahi ko nono bata dashi sai bussashen kirji haka ta tashi ina kiranta da yar kadangaruwa. Dariya muka kwashe da shi gaba dayan mu falon tace bakiga munafukar nata ba yanzu ta fara dawowa rakiyan ta taga babu ci ga harkan. Da ta dauka karyan arzikin da ake mata ko gaskiya ne shine ta wani shishige mata don ta dauka zata zo da wani kadarine a gidan tafi kowa. Sai gashi taga a binda ba ta zata ba a wurinta mai shine zai tsaya fadan kayan masarufi a gaban kowa haka ? Su dai suka sani kan su ake ji ai dama irin haka ga haka ake karewa wanda ka shigo kuna shiri da shi dashi za, a fara jin kan ku a gidan. Gara ma ka zauna da kowa da zuciya daya idan kishin yazo ayi shi in angama akoma daidai yafi don shi kishi dole mace tayi shi ko wacece kuwa. ********* ********* ********* Wani wayewa jinkai duk Raliya tazo muna dashi amma sai taga ashe kowan mu da take gani da nashi iyawan a gidan. Haka mukai azumin mu mukan fita zuwa sauraren tafsir ni da yara da anty Zulfa da bata bin mu amma daga baya ta tsiri bin mu muna zuwa tare. Idan kuma ina da aiki ita ke zuwa da yaran su sauraro su dawo ranan mun tafi tare da zamu dawo muka tsaya mukai sayayya a wani shago na kayan kwallaman yara don daddy yai tafiya a lokacin mu kadai ne a gida yasu yasun mu. Tun a bakin get muke jiyo hayaniyar su anty tace ba lafiya dajin wanan fitinan mun fiti muka karasa shiga muke jin harsunan su yana tashi sosai. Naso na wuce amma sai naga ihisan a waje zaune tace mummy ku shiga kuyi masu magana ko zasu daina don Allah. Yarinyar ta ban tausayi muna shiga naga daga uwar har yaran suna zagin hindatu itama tana mayarwa. Nace subbahanallahi may ya kawo haka kukuma waya saka bakin ku ga maganan su na manya. Sai wanan fitsararar mimin tace wallahi duk wanda yace zai zagi uwar mu a gidan nan bamu kyale shi. Ku bar ganin don munzo kuce wai zaku wullakanta muna uwa muna kallon ku tun dai ke wai ke a dole ga star a gidan ko ke kikai mata bazan kyale ki ba. Nace wa kike nufi ni ko wa tace ke Rahama dake nake nace tarkasa nifa kikace tace kwarai kuwa take na tuna da kauye ai batai aune ba tako biyu nayi sai gani a gaban ta ji kake kayau kayau nai mata mari biyu masu kyau a fuskan ta. Sai data duka don wahalan da tasha ta dago idon da ya cika da hawaye tace kika mare ni wallahi sai na kashe ki yau a gidan nan. Nace bissimillah gani gaki yarinya karyan iskanci kikeyi baki san Rahama kuwa sai kin shiga track dina zaki raina kan ki. Daga magana zakiyi min rashin kunya zagina na ta fara ta uwa ta uba sai babban nasu tace dani don Allah anty kiyi hakkuri ke Mimi wai baki kyalewa ne hakana. Nace idan bata kyalewa barta ai nine maganin ta nace ke har kin isa ki zageni ai ban san an kawo muna kushiyoyi ba a gidan sai yau da kika fada. Uwar tace don Allah don annabi doctor kiyi hakkuri sai ko ga yarana sun shigo part din Aisha tace ke wallahi ku kama kan ku ko yanzu jikin yarinya yai tsami in kina iskancin ki ki san inda zakiyi shi. Nace Aisha maza ku bar nan ku koma inda kuka fito maza ku koma ciki ba bata lokaci yaran suka juya suna fadin wallahi da yau anyi karamin yaki a gidan nan kuwa. Hindatu tace kun gani kunga inda akasan darajan babba magana daya tai masu sunjuya amma ku da baku san komai ba sai fitsara don wullakanci. Raliya sai faman hakkuri take bani tana kuma zagin yarinyar haka yasa na juya na wuce banyi magana ba. Bayan an sha ruwa muna zaune falon mu sai gata tare da yarinyar sun shigo muka gaisa take cewa dani doctor na zo da mimi ne ta baki hakkuri don Allah tayi kuskure na saka bakinta ga harkan mu harta fada maki bakaken magan ganu irin haka na. Zulfa tace wuribta samu ai yanzu tasan kwaruru ba tsaran wake bane in ba rashin kunya ba ta yaya zaka bude baki ka zagi babba wanda ba sa,an yin ka ba. Uwar ta bani tausayi kuma dai ko ba komai ta nuna yadda ya kamata tace ban san may yakai yaran nan ga maganan mu ba. Shara dai ne da kazanta ba dama a gyara wuri an bata shine nai magana ya zama muna na rigima yanzu in deen yaji wanan magana aini tawa ta samay ni daga ni har su a gidan nan. Sai naji ta bani tausayi sosai nace bama zai ji ba ai tunda anyi ya wuce ta dai bar fadawa babba maganan da yai mata dadi tunda ba haka taga anayi ba a gidan. Tace ai gata bayan marin da kikai mata sai dana kara mata wani don banga abinda ya kaita sa baki ba ga maganan manya ? Na juya wurin ta nace da yarinyar wa sunan ki tace dani cikin fushi don har lokacin ranta yana a bace da Fatima . Nace suna mai kyau haka ai sunan ki nada kyau ki daina haka kin ji ba a son mace tana dabian rashin kunya don wata rana aure zakiyi ke ma kuma ki zama uwa idan an maki haka yaya zakiji. Ki daina kinji banji dadin yadda kikayi ba shiyasa har na taba lafiyan jikin ki batare da nai niyyan yin hakan ba . Uwar tace wallahi ni kin min daidai haka nake so mutum ya nuna maka gaskiya komai dacin ta idan tazo ba wai yai ma aikin fanin ido ba. Yaro na kowa ne ai idan ka yi alheri wa dan wani wata rana kaima baka san wanda zaiwa naka ba haka duniya ya gada dama. Tace don Allah dai doctor kiyi hakkuri da abinda yarinyar nan tai maki insha Allahu ha zata sake ba da yardan Allah. Don nasan idan maigidan yaji abinda ya faru ba karamin fitina zamu kwasa ba dashi akan hakan. Murmushi nayi nace indai don wanan ne kada kiji komai ba zai taba jin wanan maganan ba don zanyi warning din duk wani wanda nasan zai iya fada mai zancen. Godiya ta fara yi min duk tausayin ta ya kamani uwa ke nan ance da kuka mai jawa uwar shi jifa, yau shi nake gani diyan ta sun ja mata zubar da aji tana bi tana rokon ai masu hakkuri don Allah sherin shedan ne ba komai ba . Na yiwa kowa kashedi ajan maganan sun ja bakin su sunyi shiru sai wani laddabib ya shigo tsakani na dasu da kowa a gidan. Har daddy ya dawo ba wanda yai mai hiran sabanin da aja samu sai ma zirga zirgan hidimar sallah da ake ra kokarin yi don mu a zaton mu a nan zamuyi sallah sai gashi a cikin dan iankanin lokaci yace ina sam ai gida zamu koma muyi sallah can din. Gashi sallah da kwana biyu ina da wanin aikin da zan yiwa wata mace mai lalarurar matsalan ciwon ciki dake yawan samun ta. Duk na fada mai amma yace ina shi wanan bai shafe shi ba idan baije gida yai sallah da iyayyen shi ba su wa nake son su kula mai da yan tsofin shi a can. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 94 Daddy yaso muyi tafiyan a tare dashi sai dai hakan baiyi ba don ni tare da yara na mukai shirya tafiyan da motana inda sani ne zai jamu har zuwa can. Bayan mun fito ne sai anty tace mu zata bi don ba zaitai tafiyan da za ai fitina akan shi ba. Don haka da ita muka tafi mota uku mukai tafiyan dashi don itama Raliya motar ta yaranta suka shiga. Mun isa lafiya zuwa la,asar kowa ta shiga part dinta tana gyara don kuran da yayi saboda rashin mu a gidan. Gajiye ne da mijin ta zaune a gidan tashigo ta taya mu gyara da girka muna abinda zamuci idan ansha ruwa don tun muna hanya nai mata waya. Kafin magariba mun gyara ko ina sai shirin shan ruwa da mukeyi ina dakina zaune ina lazumi sai ga Amira ta shigo take cewa dani. Suna son su ci abinci nace kira min Aisha kuzo tare sai gasu nace idan abincin yana da yawa ku diba kubawa sauran mutanen gida. Suka fita kamar yadda nace hakan sukayi sun kaiwa kowa abincin don tayi muna shi a wadace kamar yadda nace tayi din. Sauran sun karba amma sai Raliya tace adawo min dashi suma sun girka nasu ai ban dauki hakan komai ba a raina. Tunda safe helen ta tashi ta gyara muna ko ina na part din har zuwa corridors din daya raba nawa da na Anty na na da tai mopping din wurin yadda ya dace. Ban fito ba sai sha daya a falona na samu Sani da ya kawo mu zaune da yara suna kallo. Baysn mun gaisa ne nake tambayan shi zancen tafiyan shi yace dani ai anan zaiyi sallah tare da mu don idan ya koma in mun tashi tafiya kuma fa ? Nace aiko mun gode da hakan don ni ina ga kwana uku zanyi dama mu koma don ina da aiki dana koma da zanyi. Zama nayi inda yaran suka fara baibaye ni kowa da korafin shi nace ina Nasir ya shiga Amira tace ta nagani yana daki a kwance bai tashi ba. Nace Jinior duba min shi ka gani idan yana ciki sai yace naga sun fita saman mashin da wanan yaton matar can . Gabana yai mugun faduwa sosai don sam bana son halakarshi da wannan yaron ko kadan don yaron bai min ba gaskiya. Ba wai naki yaron bane don yana dan kishiyana a, a don dai tarbiyan shi ne bana son kasancewar su a tare don kada na saka ido yazo ya ture min ginan da nai shekaru ina azawa akan yaran. Ina zaune a falon basu dawo ba sai zuwa karafe sha biyu da wani abu yaron shigo gidan. Yashigo yana wani rangajin gajiya don azumi ya kamoshi sosai a lokacin. Yana zama ina fadin Nasir ina kafito ya dan bata rai yace mummy mun shiga gari ne nace kai dawa ? Sai ya dago ido ya kalleni yace dani da Awal muka fita nace dashi waye hakana kuma ? Yaushe ka samu aboki Awal ban sani ba kuma sai yai dariya yace ba wani bane sai yaron amaryan daddy din nan. Nasir kafita da wanan yaton mara tarbiya yaushe ka fara yawo ban sani ba har ka fara hurda da wanda baka sani ba ? Ssi yai shiru fada sosai nai mashi har Sani dake zaune ya saka bakin shi yace gaskiya nima yaron haka nake ganin shi kamar baida kwabo wallahi don bai ganin kowa da daraja ko kadan. Mun dai mai fada yana wani kumbure kumbure shiya tayar min da hankali don ba halin shi bane yin hakan idan an mai fada. Bayan la asar sai ga yaron har part din mu yazo wai Nasir yazo su fita sai Nasir din yace ka tafi kawai ba zan tafi ba. Ina jin shi yana lalashin shi da su fita din amma Nasir din yace ba zai tafi ba ya juya yafice nace kagani ko har ka fara jawo muna shi yana shigo muna nan. Yace cikin wani murya mummy nifa bani na kirashi nan din ba fa nace Nasir ni kakewa magana haka ? Daga haka ban kara magana ba nai shiru na kyale shi shima shiru yayi yaci gaba da kallon film din Annabi musa da akeyi a wani tasha. Ban kula shi ba har wani lokaci na fita batun shi shima yana ta cika yana batsewa Haidar na zuwa kusa dashi ya buge yaron . Hakkuri nabawa yaron najashi a jikina sai dai a raina nasan sabon aiki ya samay ni ke nan kuma kan yaron. Yaushe ne har suka fara wanan halakan da yaron nan ban sani ba ni kuma kowa bai fada min ba sai yau da na gani da idona. Daddy ya shigo part din namu ya samu haidar yana kuka yake tambayan may ya samay shine wai yake kuka ? Nasir ne ya dake shi don kawai an mai fada ya fita yawo da wanan yaron Awal shine yake fushi daga yaron yaje gun shi ya dake shi. Haba Nasir may yai maka kuma ka dake shi kai ina kaje ne har akai ma fada yace daddy kawai mun fitane akan babur din shi muka zagaya gari da abokan shi. To mummy ka tace bata son yawo idan zaka fita ka dinga fada mata zaka fita ina ganin shine bata ji ma dadi ba ka fita ba a san inda ka tafi ba. Nace daddy ni dai yawon shi da yaron ne bai mun ba kawai bana son yana yawo da yaron da bamu san halin shi ba daga sama. May ya faru da yaron da baki son hurdan su ba maza bane namiji sai namiji nace bai mun ba na fada mashi gaskiya idan kuma baiji sai mu gani. Ban gane may kike nufi ba da maganan ki ki barsu suyi hurdan su kawai sai dai kai kabi a sannu kaji abinda mummy ku ta fadi. Bayan haka yake cewa kuyi list din abinda za, a sayo maku za a tafi sayayya yanzu. Nace Atika dauko list din nan da Amira ta rubuta dazun ga yacan gefen tv can taje ta dauko mashi list din ya karba yana dan dubawa. Nan yace da Nasir da yaran kuzo mu tafi ko duk suka mike suka bi mahaifin nasu inda zai tafi. Amira ce bayan fitan su take cewa mummy wallahi kada ki yarda kinga shi daddy fa bai damu ba wai maza mazan may can kuma. Bamu zauna ba kitchen muke muna aikin abincin buda baku sai gasu da kayan amfani an lodo ga ledoji sukai ta shigowa dashi gidan. Jinior ke cewa dani wai mummy kin san da wanan yaton muka tafi kinga yadda yake wani yi kamar ma shine yaron daddy. Duk sai ya bamu dariya aikin ksyan da suka shigo dashi muke faman yi don kada su lalace don gobe ne jajibur udan Allah ya kai mu. Duk yadda na hana yoron na lura yana sullacewa ya na fita da yaron sai na share shi ya shigo ya samu mun baza kayan sallah yan matan ana dubawa yake cewa mummy ina namu yake sai na kyale shi. Ya sake tambaya na mummy ina kayan mu na duba nagani shiru nayi sai Amira tace da shi wata mummy kaida baka jin maganan ta. Yayo cikin ta kamar zai make ta yana fadin wallahi idan kina shiga harka na saina makeki wata rana. Nace dashi Nasir ba tare da na kalle shi ba ka fita a idona wallahi kuma duk ranan da kai gigin taba jikin yar uwarka zan gwada maka kai ba zuciya ka kake dashi ba. Yai fushi ya fita yana cewa ni wallahi an tsanane yanzu ba a so na zan tafi inda ake sona ne wallahi . Ban daiyi magana ba sai bayan ansha ruwa naga bai fito ba na mike zuwa dakin da suke kwana. Yana zaune yana game a hannun shi ya dago yaga nice na shigo sai ya gyara zaman shi yana dan dana abinda ke hannun shi a hankali. Wuri na samu na zauna a bakin gado tare da cewa Nasir ya dago kai ya kalle ni tare da amsawa. Nace kace kai an tsaneka ba a son ka yanzu kai da bakin ka kake fadin wai an tsane ka har kake fafin haka a gaban kowa. Nasir idan zakai min adalci kaiwa kan ka akwai wanda nake so duk gidan nan bayan kai ? Yace mummy ni Amira tana matsamin kuma kina gani baki magana ina ruwanta dani nace kana da hankali kuwa Nasir ? Yar uwarka yarka kake cewa ina ruwanta da kai Amira fa wata rana kamar uwa zata zamay maku ka sani ko nima Allah ya dauki raina na barku yarda Anty ta barmu sau ya dago kai da sauri ya kalle ni. Nace eh ai muna namu ne Allah na nashi akan mu yace mummy ki daina fadin haka mana nace ai haka maganan yake. Mummy ni fa yaron nan fa ba abokina bane amma ku kun dauka ina yawo dashi ne ko wani abu ? Nace baka yawo dashi ina kuke zuwa tare dashi sai yai shiru nan dai nai ta mai fada tare da nasiha sai da yai nadama yace dani kiyi hakkuri mummy ba zan sake bin shi ba na mike ina cewa dashi da dai yafi ma ka fito ka dibi abinci kaci. Daga haka na bar dakin bai jima ba yafito ya debi anbincin Aisha tace mummy tayo bikon dan ta ne mu ai da bai fito ba sai mu cinye har nashi kason. Yace Anty Aisha bamu haka dake fa ? Tace yau naga ai har mummy ansha yaji da ita ne na dauka ai harda mu aka hada cikin fushin. Baidai yi magana ba ya fice dakin ni dai nasan lafiya muka zo amma sai na kula da cewa akwai matsala a gidan. Don sai wani busan iska naga Raliya da yaran ta nayi ranan sallah muka shirya da yaran zuwa kaiwa su mama da hajiyan daddy abinci har gidan su Anty mukai. Gidan su hajiyan daddy muka shiga karshe mun samu su Aisha a gida mun gaisa da kowa hajiyan ce dai sai a hankali wata rana zaki wata rana madaci. Yau ma a madacin muka samay ta don su Aisha na min ba a sukace Allah yasa da da tsaleliyar motar taki kikazo mu gani ? Naceta nawaje da ita nazo kai ako zamu sha kallo don munji labarin motar tun a waya duk na matsu na ganta wallahi inji Aisha. Hajiyan dadi tace da yake gulma ne ba don baku san ciwon ian ku ba wa aka fi aiki balle aiwa mutane rufa ido da sunan aiki ? Duk falon yai shiru sai Aisha ce tace haba dai hajiya wanan magana ai bai dace ba tace da ita to uwata fada min abindaya dace naji. Yar uwarta dake aikin banki may yasa bata saya ba sai ita ce za, a ce wai ta sai wanan motar ni dai nai shiru sai Aishan ne tace hajiya ina zaki hada samun Rahama dana Raliya da aikin su na rikici ai ba a ko hadasu ma. Rahama fa yanzu babban likitace a kasan nan wace ke aiki a maikatar lafiya na kasa baki daya aike surukar ki don dai ba mai rigima bace da kin sani. Tace may kike nufi tace wallahi hajiya ba a taba hada su ai sai tai shiru sukan suka mike zuwa ganin motar tare da Nasir da ya san komai na motar kamar yunwar cikin shi. Sai gasu sun dawo suna yaba kyawon motar kai Rahama kin debe takaici wallahi nace ai ban so sayan ta ba ma wata kawar aikina acan ta matsa min na saya. Kin san mu ma aikata duk movement din mu na kan idon mutane sai ace duk samun ka ina yake shiga ka kasa shiga tsaran ka. Eh hakane amma ian mutum yana samun tallafi ba wanda baida wanda ya rike mai kan maciji ina yaga wurin wasa da bindin shi. Kai hajiya ku dai Raliya ta saye ku da amshi ungo din ta yanzu baku ganin kowa in ba ita ba nikan wallahi duk wani barkadon ta bata gaba na don nasan inda gaskiya yake. Nace hajiya ko baba na nan mu gaidashi mu wuce tace ku shiga yana daga ciki muka aje mata kayan tsaraban da muka zo mata dashi muka mike zuwa gaida Alhajin a falon shi. Naji dadi kamar kullun ya karbe mu da mutunci sai faman saka muna albarka yake shima muka aje mai nashi tsaraban da abin sallah mukai mai sallama. Mun koma mun sallami hajiya da su Aisha muka bargidan sai bayan fitar mune suka bude tsaraban nan hajiya jikin ta yai sanyi abinda muka kawo mata din. Aisha tace hajiya ya kamata ki daina yiwa yarinyar nan haka may ye laifin ta duba kiga yadda yaran nan suka koma fa ko shi ai ya isa ai ta samu sallama a wurin ku. Yanzu ki duba fa yakai kusan dubu dari biyu wurin nan abinda ta kawo maki fa tace a ina fa ? Aish tace gasu a gaban ki kuwa sai suka shiga yi mata lissafi tace nikan da ma kudin ta kawo min da yafi ai. Hajiya wai may zakiyi da kudine haka tace a tambaye ki nema a kan su wa yake karewa ba a wurin ku ba. Kagin mu dawo gida mun dan yi biye biye a hanya har gidan mahaifiyar Zulfa muka tafi a can muka samay ta a gidan nasu batama san da fitowan mu ba. Ta tare mu a cikin mutunci tana faman godiya akan irin zaman da mukeyi da yarta sai fadin takeyi adai ta hakkuri zama sai da hakkuri mun biya duk gidajen yan uwan daddy muka juyo zuwa gida don yamma yayi a lokacin. A harabar gidan naga wasu motoci guda uku nasan cewa munyi baki ne sai da muka karasa shigowa ne naga mata zaune saman fararen roban dake waje da aka aje don shan iska a wurin. Raliyace tare da kawayen ta wasu irin tantiran mata ne da ganin su ba sai an fada ma ba ko su waye su din don yanayin shigarsu kawai ya nuna. Gaba dayan su sukayo kaina da kallo har muka fito daga motan tare da duk yaran mun sha kwslliya ba sai na tsaya tsarawa ba don mun tsara da kyau Alhamdullahi. Magana suke a kan mu sai dai saboda nisa baza mu iya jin su ba a lokacin yaran ba wanda ya bi ta kan su ina gaba suka biyo ni dirr a bayana. Dayan tace tarkasa ke kice min yarinyar ta bunkasa ne haka hajiya jummai kin ko ga shigar ta daga ita har yaran kuwa ? Wacce aka kira da hajiya jummai din tace nagani wallahi kayan da muka kasa sayowa matar musa don ne a Dubai fa. Dayar tace wai tsaya itake da yaran nan masu kama da Larabawa ke nan fa ake nufi ? Raliya tace a sanyaye itace mana yan so ke nan a gidan nan ba wasu diya bayan su a gidan nan yanzu ai duk inda zai tafi dasu yake zuwa su biyar kamar kan shi aka fara haihuwar diya maza haka farare. Ke ai dole yaran akwai kyaune wallahi Allah kice dai yarinya ta wuce inda muke tsanmanin ta sai Raliya tace da kike ganin ta a nan shegiya sai bakin wayo kamar ba yar kauye ba. Yarinyar nan da kuke gani a nukurkushe take mulkin gidan nan in anyi magana ace ai duk babu mai hakkurin ta ta mallake komai da kuke ganinta a wurin nan. Duk ta inda na biyo mata kafin nakai shegiya ta sani wallahi takai min ko ina don sauran su bakin kishi ya rufe masu ido ba wayau ne dasu ba. Amma ita yadda kika san diyan wani da wata ko wata tsohuwar yar boko haka take da bakin wayo duk ta rusa min plan dina a gidan nan da kan shi. In ba ita ba babu mace komai zakigan ta dashi kamar mai aljannu dake fada mata. Ai ba sai kin fadi ba duba fa ko kallo bamu ishe ta ba a wurin nan balle tasan Allah yayi ruwan mu ta gaida mu. Dayar tace aiko zama bai ganki ba wallahi Raliya shiga zakiyi ki fita sai kin kifar da ita gaba daya a gidan nan ki nuna mata ira ba kowa bace a zauna lafiya. Nan dai sukai ta bata shawara ga abinda zatayi sunyi zancen motana da shigana da yarana yafi a kirga zuwan Zarah da hajiyan harka ya kara tsunka su don su ma basu tsaya ta kan su ha suka shige ciki a binsu. Nan suma aka shiga nasu gonan akai tayi saida sukayi ya ishesu sukai mata sallama suka tafi tare da bata shawaran banza. Mun dade da su Zarah a ciki muna hira nan hajiyan harka take fada min ko suwaye wa yan nan matan da suke tare da Raliya. Hiran nasu babu dadi nake mamaki ina ta hado dasu haka sai Zarah ke cewa wai ke halan baki san labarin Raliya yar kadagaruwa bane Rahama ? Nace nikan ina zan sani tunda ba mutane nake shiga ba kai tsaye tace aiko ya kamata ace kina da labarin su dai kan wa yan nan tantirai ne fa na karshe. Ni nai mamaki da mijin ku ya aure ta kamar wanda idon shi ya rufe duk matan kwarai dake cikin garin nan amma ya rasa wacce zai aura sai wa yan nan da gari ya gama da su. Munyi hira sosai da su kamar kada mu rabu amma dare yayi dole mukai sallama dasu suka tafi. Washe gari da safe na shiga gun daddy na fada mai zan shiga gun iyayyena nagaida su sai dai ba kwana zan yi ba idan na tafi. A falin yake zaune tare da Raliya sai da na sama yana waya ne nai mamakin ganin ta a falin don dai nasan ba itace da girki ba ranan. Abinda ban matsa wa kaina ke nan muddin ban da girki ban faye shiga wurin shi har na zauna ba idan dai ba shine ya nemay ni ba da wani magana a nan din. Sallama yayi bayan na dan tsaya daga bayan kujera na jingina jikina akai ina jiran ya gama wayan. Sai yace Ragama kun tashi yanzu nake batun aikawa kizo ai don magana aka zo min dashi a kan ki nace to fa ni din nan dai ke nan gashi kuma Allah ya kawo ni yanzu din da ake nema na. Yace yanzu wanan ta samay ni da maganan da banji dadin shi ba sai dai da yake nasan ba halin ki bane hakan ban damu ba sai naji naki hujjan nayin hakan da kikayi . Tace jiya kin dawo da yara tana tare da baki daga ke har yaran kukai masu kallon banza da tsuki kuka wuce ciki ba tare da ko kun gaisa da bakin ba. Ikon Allah nace kafin yaci gaba da maganan shi yace sai kuma tace kin hana Nasir dama duk wasu yara a gidan nan hurda da diyan ta kin ware mata yara a gefe baki bari su shiga gunta. Nace bakin ki uwayena ne ko mai da ban gaidasu ba yai maki zafi ai ban san ranki ya baci ha da sai na aikata fiye da abinda kika ce na aikata din. Nace kin gan ni nan ban maka sheri ko shiga harkan ka amma idan kace kai idona yana kan ka to muka zuba da mai shi sai ankai karshe. Tace naga alama ai don yadda kika kashe Saade har kike kuri da hakan to ki sani wata tafi karfi ki don maye baicin maye sai dai ayi walkabu a mike tare. Nace wata sabuwa kin tabbatar da cewa nina kashe Saade tace waye ma bai sani ba tai maki halarci kin saka mata da sheri. Ba damuwa nace da ita don yana zaune baiyi magana ba na juya wurin shi nace dama na shigo ne na fada ma yau zan leka su Inna sai dai ba kwana zanyi ba yau din zamu dawo insha Allahu. Shiru yayi wurin baiyi magana ba na juya na fara tafiya zan fita yace Rahama nace naam idan kun shirya kizo sai naji tace za a aje ai bakar asirin da aka saba yi a can ke nan ko. Murmushi nayi sai bayan fitana yace kin gama abinda ya kawo ki ko , tace may nagama ai gaskiya na fada ba karya ba. Yace amma kin san tun kan Rahama tazo gidan nan Saade ke fama dz kan ta ke nan itace ta sako mata kafin ta zo din na kyale kine don nasan halin Rahama ba wai shirun banza tai maki ba ko da kikaga ta kyale ki yanzu. Tace tayi abinda zatayi din mana an fadi batayi bane komay waye hai sani ba duk garin nan yace ok kawai ya kayale ta ta fice tana fada cikin son fitina Yadda daddy ya kyale bai yi magana ba ya kara tunzura zuciya na har naje na dawo raina a bace yake ranan tun da safe kuma na shirya da yara already dama na fadawa Sani zancen tafiyan mu tunda safe nake son tafiya. Duk wanda ya tashi ya sama babu gidan mun bar garin daga ni har yaran daddy ya kira waya na daidai ma mun kusa shiga Abuja yake tambaya na kuna ina ne wai naga part din ku a rufe. Nace gamu zamu shiga Abuja insha Allahu ko ka manta na fada ma yau ina da wacce zanwa aiki da karfe goma sha daya. Sai yai shiru nima na kashe wayan yara kawai muka sauke nace da Sani mu fita muna barin gidan nace sani kaini kotu mugani ko sun dawo yace sun ma dawo ai yau aka koma aiki ko ina. Ina zuwa nai karan Raliya tare dz kunna oudio din da tai magana da duk ta fada min take aka buga mata sanmaci na bayar da kudin zuwa kano kai mata sanmacin alkali yace da goma na safe ake bukatan ta kotu gobe. Dan sakon da yakai sako ya samu wani sabin tashin hankali a gidan don Awal dan ta yayi shaye shaye yazo yace sai ya bankawa gidan daddy wuta baki daya. Sai kuma ga dan sako ya sallama yace daga Abuja yake kotun magistre ake neman mai suna Raliya nan kuma aka koma kan shi. Idan hankalin daddy yakai dubu ranan ya tashi sosai yace Rahama tai kara ko may ? Tunda zan shiga theater na kashe waya na ban kunna ba sai dare sosai na kunna wayan ban dade da kunnawa ba kiran Zulfa ya shigo min a wayan. Tace Rahama may ke faruwa ne kika wuce ban sani ba sai kuma ga sanmacin an turowa Raliya tace yau aike dai bari maganan ki ya tabbata don matar nan taga jaiba a gidan nan. Nan take fada min abinda ya faru da dan ta sai kuma ga sanmaci an turo mata ana neman ta kotu yanzu dai suna nan tafe tace yau har Alhajin babba saida yazo gidan nan. Don daddy yace ita data fada taje ta kare kan ta bai zuwa ko ina ta ishe shi a rayuwa don ba wani kwanciyan hankalin da ya samu kan ta. Nace ya samu kan Anty a gaban shi fa ta fada min magana yana zaune bai ce komai ba kin sanni da record din magana don mantuwa va su san na danna ba ne. Tace aiko tashiga uku nace zata dai shiga barta dani take wasa wallahi ko daddy yazo ba zan jaye karan nan ba Anty. Ta shiga zugani ni dai ina jin ta ban ce komai ba har tayi tagama abinda zata fada mukai sallama nace kai kishiya a raina. Zakace a Abuja suka kwana don uban samakon da suka bugo sai dai duk samakon su basu samay ni a gida ba lokacin gashi anzo da mutane. Har asibiti suka samay ni sai akace dasu ina cikin theater room ina aiki sai zuwa sha daya zan fito yadda ma tagani asibitin yasa ta fahinci ko wacece ni a wurin . Ganin zasu bata lokaci suka wuce zuwa amsa kiran mai sharia don kada suyi laifi kuma again kan rashin zuwa da wuri. Aiko suna zuwa Alkali yace a saya ta bayan kanta sai gobe zai yi sharian mu nan hankali ya tashi bayan an saya tane sai ga sun dawo wurina asibitin daidai na fito ina cikin office dina ina wanke hannu. Suka shigo office din nai masu sannu da zuwa tare da nuna masu wirin zama da zasu zauna Bashir yace kai kaunata kin samu cikin wani hali wallahi. Nace an dai sani nida akaiwa batanci a gaban ku baku dauku mataki ba yace ba wanan ba yanzu dai gamu munzo wanan yaya ne ga Raliya wanan kuma dan uwanta ne sai maigidan naku. Don haka munzo ne don Allah Rahama kiyi hakkuri ki janye karan nan don yanzu haka tana can a rufe banji dadi ba a raina amma a fili nace dashi don Allah ku bari na daukawa kaina yanci don wanan kazafin idan ba anyi iyaka dashi ba ban san ina zai tsaya ba haka. Mun dai ji don Allah ku bari a sasanta a gida a fahinci juna tsakani ba sai an kai ga hukuma ba zancen kishi ne ai bai kai haka ba. Nace hakane fa zancen kishine da kazafin kashin kai yanzu sai a bari alkali yai huluncin shi ai muji in wanan magana ya shafi kishi. Dama alkalin muna tare da yar shi Fatima kawa na don haka na samu daurin gidi Fatima ta zuga shi aiwa Raliya ladabi ta shiga hankalin ta. Aikuwa da kyat suka ci saata na fito muka tafi kotun mun samu ance alkali yai tafiya zuwa Nasarawa state duba wasu case a can sai ya dawo. Don haka dole sukai hakkuri muka dawo gida sai alkali ya dawo da yamma zamu koma ira dai tana can a tsare. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 95 Daddy bai min magana ba nima haka nasan dai zaiyi zai gama ai tunda agaban shi mukai komai yai zaune kamar ba namiji ba. Nasan haka rayuwan shi yake abune mai wuya idan ana sa,in sa a gaban shi yai magana iya maganan shi shine ya isheni haka fa ko zan bata maku rai shine maganan shi shi. Alkali bai dawo ba sai dare don haka zata kwana a ciki hankalin su yai matukar tashi sosai dole ya aje girman kan shi ina daki sai gashi ta shigo dakin sallah na idar a lokacin. Ban ko iya gaida shi ba sai yace dani ke Rahama ki sa a sako Raliya haka na don ba zan yarda ta kwana can ba ko yanzu dai ai ta horu don haka ki sa a sake ta da daren na ba sai ta kwana ba. Banyi magana ba har ya fita daga dakin na daga waya na kira Fatima nake fada mata yadda mukayi da shi tace ba matsala bari ta kira tace idan sunzo a basu bellin ta. An kira an bada belin ta din baban na fatima ke fadin Fatima na dai gane har da kishi ga alamarin naku. Tace baba so muke ai muna maganin ta tasan mu ba sa, an yin ta bane da zata dinga shiga gonan mu bamu damu da su ba sun saka mu s gaba. Anje anbada belin ta cikin dare ta dawo gidan kamar bata ciki shiru kake ji ba wani motsi a wurin ta. Da safe na shirya zan fita sai gashi saye da kayan barcin ajikin shi yake cewa ina son yau kuje ku jaye karan nan. Da sauri na dago ina kallon fuskan shi da mamaki nai karfin halin cewa a gaban ka fa tai min mumunan kazafi kana ji baka dauki mataki ba yanzu kuma zan daukawa kaina kace na jaye ? Indan na jaye ya zama gaskiya ke nan maganan ta ya tabbata gaskiya ke nan ya zama dole na kwatarwa kaina yanci wanan karon . Ina fadin haka na juya na bashi baya naci gaba da abinda nakeyi yace ke nan ban isa nace maki ga abinda zakiyi kiyi din. Sai nai shiru bance dashi komai ba ya juya ya fice daga dakin sun tafi kotu alkali ke fada masu nace a janye karan amma su sai sun daukawa mai hakki hakkin ta. Don kazafin kashe mutum ba karamin kazafi bane sai ga Raliya na kuka tana roko alkali yace ko taba da taran dubu dari biyar ko taje gidan wakafi na wata uku. Daddy yace dama ya fada masu kwandalan shi ba zaiyi ciwon kaiba ga zancen ko zuwan da yayi akan tursasawan mahaifan shi ne yazo. Nan fa kudi ya gagara a gunta sai waya take bugawa a turo mata babu kudin, karshe dai shidi ya biya kudin ta dawo gida tsurutsuru da ita. Sauran sun iso daga kano nan aka hada mu falo ranan dukkan mu munga bacin ranshi yai rantsuwa tafi a kirga akan duk wacce ta sake jawo fitina ita kadai zata tafi. An dai sulhunta a zauna lafiya sai kuma zancen yaron ta da ya fara kawo wani harkan banza a gidan yace sai ta mayar dashi gidan uban shi. Nan ma taita magiya tana roko ba kunya tace don Allah Rahama kusa baki mana ku bashi hakkuri. Sai kowa yai shiru zulfa tace gaskiya bazamu bada hakkuri ba ya fara haka ranan da maigidan bai gari fa ya dauko muna magana yaya ake so muyi. Hindatu tace garin kwashe kwashe an dauko muna fitina a cikin gida muna zaune zaman zaman mu. A, a ku dakata a gaskiya tarbiyan shi idan ta mayar dashi inda bata kusa akwai matsala gara dai yana kusa da ita dai. Tace ka taya ni tsawata mashi a tarbiyan shi amma idan aka mayar dashi abin kuma lalacewa zaiyi azo kuma ana da an sani. Ya juya gunta yace kin gani ba kin gani yanzu kin dai ji abinda ta fadi kuma gaskiya ta fada idan ya koma can din sai yafi haka lalacewa. Amma kin rufe ido kina mata yankar kauna ido rufe don wasu banzan kawayen ki da basu da amfani a gunki. Nan kika shiga matsala aka rasa wacce zata ara maki ko kwandala a cikin su karshe sai ni kika sa nai hasaran kudina gun belin ki. Yace kuma sai kinyi hakkuri don shi tarbiyan yaro ba wai kai kadai da ka haife shine nauyin haka ke kan ka ba kowane da ake tare hakan ya shafa. Hindatu tace niko nasan haka don hakan yai min dadi don nagani kan ihisan yanzu dan mannewa yaran nan da takeyi ina hanata sai gashi naga faidar abin a rayuwana. Wanan zuwan kano da mukayi Nunu taje kauyen su itace na samu take muna komai har muka dawo nan. Yace yanzu ke bakiji kunyar fadin wanan maganan ba da bakin ki kike fadin Rahama na bautar da yaran nan ne kawai ba rikon arziki take masu ba. Kai ko dear akwaika da tashin tashin wallahi sai abu ya wuce ka dinga tuna shi ana zaune kalau kuma yace Allah yasa a zauna kalau din dayafi maku alheri a rayuwan ku. Nan dai akai ta mayar da maganan abinda ya dace ina zaune ina sauraren su dama nasan bawai zai kori yaton bane a gidan shi barazanane kawai na maza a gaban matan su. Dakina na koma na samu wuri na kwanta don han son damuwa hutu nake nema kawai a wanan lokacin. Ban sake fitowa ba sai da safe da yake morning duty nakeyi kafin kowa ya fito nabar gidan ko a lokacin. A wurin aiki Fatima take kara labarta min yadda aka kwashe a kotu tace ashe ita duk barazanar banza ne ko mai ma bata dashi dan kudin da zata belli kanta ma ya bowaye ta. Murmushi nayi nace ni fatima kin san ba don ke da kika bani karfin gwiwa ba da taci bulus tace da gaba wanda zatai maki sai yafi wanan da tayi din. ********* ********* ********* Nasha zagi da gori wurin hajiyan su daddy kan karan Raliya da nayi kotu tace abin nawa yayi yawa sai gashi ta bugo min waya tai min tasa ni dai sai hakkuri nake bata kawai. Har tayi ta gama ban daice da ita uffan ba har cewa take na fake ga kula da yara ina cutar su yadda na cuci uwar su na aure mata miji. To komai tsiya na dai ba zan taba zama ni kadai ba yadda nake so a gidan daddy dole in bude ido inga wasu tunda ba don ni kadai akayi shi ba. Nace na sani hajiya kiyi hakkuri don Allah ba za a sake ba insha Allahu tace don dai ma shi ya zama mai naci ne ni inba jaraba ba irin na maza na rasa may yaron nan kewa wanan rawan kai haka a kanki kamar kin fi sauran matan nashi ne. Ta kashe wayan nabi wayan da kallo tare da sake murmushi una sauke ajiyan zuciya na mayar da kaina saman filo tare da lumshe idanuwa nace Allah gani gare ka. Kowa dai Rahama dai Rahama dai may nayiwa mutanen ne haka basu sona basu kauna har uwar miji a kishin mu. Wani hira akayi dani kan matsalolin mata dake yawa yanzu inda nice akaiwa interview din kan abinda ke haifar masu da wanan matsalan a yanzu. Na dinga jero abubuwan da ada can baya iyayye da kakanni sukeyi wanda mu matan yanzu saboda wayewa kai duk mun watsar dasu. Misali mace zata haihu bazata tsaya tayi jego yadda iyayyen mu a baya sukayi ba bazata sha kayan yaji ba wanda mun dauka kamar kauyanci ne a yanzu. Nace idan aka duba yanayin wa yanda muke kwakwayo ba yanayin kiran mu da halittan mu daya dasu ba. Da ace matan yanzu zasu dage da abinda aka koyar damu a baya da duk yawan matsololin nan dake samun su a mahaifa da sauran su bamu samay shi ba. Sosai nai bayani yadda ya dace a fahince ni Aisha tana gani ta bugawa hajiyan su waya tace ta kai NTA ana hira da sarakuwarta a tv jikina na rawa takai taga yadda nake magana a cikin harshen turanci da kuma wayewa ta doka uban tsuki. Tace amma Aisha anyi shashan yarinya na dauka ma watace tasani kaiwa jikina min ciri haka ashe wanan yar kauyen ne da bata iya samun maiba a tv. Wanan hiran yasa mutane da dama sun san koni wacece don da dama basu san cewa nakai wanan matsayin ba haka sai wanan hiran da akayi dani. Daddy ma yana zaune falon shi yana kallo yaga an nuno ni ana hira dani ba inda ban rufe ba ajikina duk da kayan aikine a jikina a lokacin. Hindatu na zaune gefe tayi tagumi tana kallon abinda mukeyi kamar an jefo Raliya falon itama ta tsaya tana kallo program din. Daddy ya kira yaran shi suzo suga mama su ana hira da ita a tv sai hindatu taja wani uban tsoki tace to shine may kuma kamar yau aka fara hira da likitoci a rv muna gani. Yace amma dai ba ta gidana ba ko ke yanzu wanan ba abin alfahari bane a gareki ace an nuno matsayin abokiyar zaman ki a duniya. Tace daya yake kai baka san kishi ba ko a nuno matar mutun duniya na gani har kake jun dadin hakana a ran ka ? Yace kambun ya motsa ke ban kuma yanzu ko Allah ya kaimu a nuno min ke wata rana ana hira dake mu gani. Tace a, a ni a suwa kuma an dai nuno wanda kake son haskawa duniya asan matar kace dama don ita kai niyar bawa ilimi ai. Mu da aka zube a gida kara zube wa yasan damu balle har a haskami duniya tasan muna nan. Ko ta manta da yaran na wurin ne sai da Raliya tai mata nuni da akwai fa yara a wurin taja bakin ta tai shiru ta kyale karshe ma shigewa tayi ciki tabar falon. Sai da yaran suka dawo ne suke mayar min da abinda ya faru nace kai maman ihisan ke nan dai da wani zance. Ilimin nan ba wanda aka hana fita neman shi fa sai kuma ta buge da wanan irin maganan a gaban ku haka. Mummy halan ta iya karatu ne wai nifa ko karatu ban taba ganin tanayi ba nace kai haba dai Amira. Har fa Diploma tayi maman ku dayan kuma tayi NCE basu dai ra, ayin karatu ne su kawai shiyasa kikaga basu damu ba. Mutane suna bugo min waya suna cewa hiran yayi kyau sosai wasu kuma na fadin na tabo inda ya dace a fadakar da matan mu na yanzu. ********* ********* ********* Jamb ya fito yaran sun samu sosai zasu iya zuwa duk inda suke so yin karatu a cikin kasan nan idan sun so. Dukkan su anan cikin Abuja zasuyi karatun su inda akawa Amira Chemistry da physic ita da Atika na, ita kuma ihisan zata karanta bio chemistry. Sojana kuma computer engynearing zai computer science ke nan zai yi yaso bijere muna amma naki biye mashi dole ya yarda zaiyi din ba don yaso ba. Sun fara zuwa schools sin so wai uban ya saya masu mota nice na hana nace sai sun kai two hundred level ko three lokacin sun kara hankali ke nan. Aisha ma na sama mata nursing school na zata jona don karatun da tayo da muka fita da ita na sama mata certifcate a nan da muka dawo ta yi Neco. An dai yiwa yaran sayayyan duk abinda suke so an masu registration har sun fara shiga makaranta ko tun basu saba ba har na daina jin korafin su kuma. Sai gidan ya koma min tsit idan sun fita daga ni sai helen ke zama idan ina gida su sai six suke dawowa gida ko yaushe. Jinior ma yanzu yakai secondary schoool ya dan fara wayo sai dai kinjin shi yana nan bai gushe ba har yanzu don shi haka Allah yayi shi dama. Duk yara na sun fara karatu yanzu sai abin ya dan zo min da sauki nice ke zuwa na kwaso su daga school din mu dawo gida tare. Ban san inda yaran Raliya ke karatu ba nima ban tambaya ba don ba shiga harkan su nakeyi ba ina gudun rashin mutuncin su. Zamu iya daukan kwanaki bamu ga juna ba wani lokaci ma sai dai mu hadu a waje idan wani zai fita ko wani ya dawo a cikin mu. Abin arziki ya sauka a gidan mu don hindatu tana da ciki mun ga abu a kan wanan cikin don ni dama ban san yaya take cikin ta ba. Don tun shigowa na wurin su bata taba koda bari ba balle ciki na gani kullun cikin hanyan asibiti suke ita da maigidan. Na dawo daga wurin aiki na hadu da su zasu fita ya tallabo ta ta wani narkewa a jikin shi yana kokarin bude mata mota. Na fito da sauri na karasa wurin su ina fadin lafiya dai ko nagan ku haka yace tun safe take ta zuba amai shine zamu koma asibiti. Nace Allah sarki Allah ya sauwaka sai kun dawo ina mata sannu har suka wuce na juya na shiga gida. Ina mamakin wanan rawan kafan da daddy keyi haka akan cikin hindatu da wani ne yake hakan da yanzu tai mashi suna ko a gidan. Amma da yake itace shiru kake ji abu yazo ga masuyi ina shiga Zulfa ke cewa kin dawo ashe nace eh yaya gidan tace lafiya. Kin hadu da mutanen ki zasu asibiti nace na hadu dasu yanzu daga gun su ma nake ai sai da suka tafi na shigo gida. Tace da ace watace a cikin mu ke wanan ciwon da yanzu an muna suna ko nace kai ina ruwan maman ihisan kin san ta dade bata haihu ba abin ya zamo mata sabo yanzu. Ke dai samun wuri kona ihisan fa haka taitayi a gidan nan mun ga abu a lokacin ai ko yaushe uwarta na gidan. Nace ashe ko yanzu mu gan su ke nan tunda abin nema ya samu tace zakiko ce kin ce indai sune a nan zasu tare muna. Bayan sun dawo ne muka tafi gaida ita da jiki sai wani basar da mu takeyi daga kwance ni dai na juya nafito na bar dakin. A falon su muka hade sa Raliya nace da ita an dawo tace eh kada ta zargi may ya kawo mu nace munzo duba maman ihisan ce ba lafiya yanzu suka dawo asibiti. Tace ta samu wurin an kama mata ne ai sai taitayi kullun mutum a kwance yaya zaka gane lafiyan jikin ka. Ban dai tsaya ba na wuce abina ina mamakin irin wanan zaman nasu kullun cikin rashin jittuwa suke a tsakanin su. Wani abinda ke damuna ban fadawa kowa ba sai dare yayi fever ya rufe ni da naga abin yai min yawa nace bari dai ne test nagani ina aunawa ya nuna min possitive. Ga lissafina ma nawa yana gaban na hindatu da kusan wata biyu naha bakina nai shiru a tsaye naita rama da renon cikina dama na iya. A gajiye na dawo da ciwon kai da zazzabi a falon mu ma na kwanta na kasa karasawa dakina rage kayan jikina ina son kai din ya dan lafa min. Hayaniyar da ake da fada da tsawa yasa ni mikewa zaune daga part din su Hindatu ne ake wanan fadan sai ga Zulfa ta fito tana fadin yau kuma an tayar ke nan. Ita ce ta tafi sai ma na karajin hayaniyar yai yawa na mike na tafi daidai lokacin da hindatu ke fadin ba yau ba na sani sarai cikin nan ya tsonewa kowa a gidan nan ido ana bakin ciki da samun shi. Ciki ne dai na sama ba ruwa za, a zuba min na fadi ya zube ba komay zakuyi Allah ya riga ya dasa min shi sai na haife shi da yardan Allah ya taka yarda kowa ke takawa a gidan nan. Da an debe tsanmanin sake samu a gare ni yanzu anga na samu sai bakin ciki nake gani iri iri ana nuna min. Zulfa tace akan ciki ake nuna maki bakin cikin gaba daya gidan nan ko may ina kowa na dashi banga abin bakin ciki ba ai. Don Allah malama rufe min baki kinji may ye ban sani ba har dan kaini asibitin da akeyi sai da akai bakin cikin shi gidan nan ko an dauka ban sani bane wai. Ban yi bakin ciki da dan kowa ba nawa tun yana ciki har an fara nuna bakin ciki dashi to ta Allah bata mutum ba dai. Cikine Allah ya kawo shi inda yake so in mutum ya isa ya kwace mu gani ko yayi in yi banza ne. Tsuki na ja na juya kawai don sai naga kamar ta samu tabin hankali ne ma ciki da yake ciwo don hauka wai take kadagi dashi. Na koma na kwanta inda na tashi tare da lumshe idanuwa sai ga Zulfa tace Rahama kin gani ko waiko hindatu na da hankali kuwa. Na bude ido nai murmushi nace da hankalin ta mana tsaba iskanci ne kawai da rashin imani ke damunta. Shi dai cikin kamar akwai wanda bai taba yi shi ba acikin mu zata tsaya wanan haukan haka ? Zulfa tace ni dama ba yauba na kula da ita ko abu ka bata bata ci ko zuwa nan yanzu baki ga ta daina ba. Kin san ance wanzan baya so a jikin shi kin manta da abinda ta taba yi min ne akan cikin baby ? Nace kai wanan ai rashin imani ne tace to shi take ganin kowa ma zai iya a halaka mata cikin nata. Nace Allah sarki tai ta kanta kowa ma nashi ya ishe shi balle yaje daukowa kan shi wani nauyi da hakki. Tun ina ciwo a tsaye har na kai kwance lokaci guda na ramay nafada ban iya cin komai ba wanda ya kawo cikine dani in dai anyi magana sai nace dasu ulcer ke damuna kawai. Ga seminar yazo min zan tafi india haka na daure nai tafiyan na dai jene amma ban iya tabuka wani abin kirki ba a can. Na dawo duk na fada na ramay sai da doctor fati tazo har gida ta daura min ruwa don ido rufe na dawo gida. Lokacin ne daddy ya gane cikine dani da yaji muna magana da ita ciki har yakai wata hudu a jikina lokacin. Bayan tafiyan ta ya dawo dakin fuskan shi babu annuri ya samu wuri ya zauna idanuwa na suna a lumshe yake cewa dani. Rahama cikin kika sake boye min bayan kin an yadda mukayi dake a baya kan cikin Haidar nace akan may zan boye ma daddy. Ba yau daine mukai test ba muka gane cikine dani amma ni may zai sa na boye maka idan na sani. Sai naji ya furzo da iska daga bakin shi yace may kike so a saya maki ko zaki iya ci yanzu ? Nace bana son komai faten wake dai nace helen ta dafa min shi kawai nake son na sha ko za dan ji dadin bakina. Ba zaki ci kaza mai zafi ba a sayo maki ko zai gyara maki bakin naki nace bana son komai faten dai ne ya biyo min a rai kawai. Ya juya ya fita yana fadin Allah ya sauwaka yana fita zulfa ta shigo tana min sannu daidai kawo min faten wake da helen tayi. Na mike da kyat na shiga bayi na wanke bakina nace da ita don Allah mu hada hannu ko zan samu na dan sha da yawa. Waiko Rahama anya kuwa ba kani jinior ya samu ba dama yace wa hindatu shima ai maman su zata haihu. Murmushi kawai nai mata na dan fara diban faten ina sha a hankali sai da na samj nasha sosai sai ko ga amai ya taso min. Da sauri na mike na shiga bayi tana min ba a tana fadin aiyya abin yazo muna nan ashe akwai magana kuwa. Mai kurin ciki yau ta samu kishiya sai yaya ke nan yanzu za, a yi cikin da akace damu kwalelen mu gashi an samu. Ban yi aman da yawa ba na fito na fada saman gado ina nishi da kyat nace kai ni wanan abin ma kamar sabo ya koma min wallahi ko. Tace har yaushe Rahama aike abin naki na da kyau tunda baki jimawa kike samun ciki wanan ne kika jima shiyasa. Tace ni kinga cikin Hanif wani likita ya ban magani sai ko gashi Allah ya kawo min cikin da wuri ban ko dade da fara sha ba ma. Nace ko yanzu idan kina sha sai na gwada rubuta maki ki saya ki sha tace da sauri wallahi ina so gaskiya da zan samu. Nace bari na rubuta maki ida na tashi yanzu kan sai a hankali gaskiya tace kai dana gode wallahi gorin da shegiyar nan tai min yana ci min rai sosai tun ranan. Nace cikin lumshe idona ni wallahi bani ma son ta sani sai dai ta ganni dashi kawai daga sama yafi tace haka za ayi ai kuwa. Da safe daba danji sauki sai gata rana min tunin maganin na rubuta mata ranan ta tafi ta sayo takawo ta nuna min nace mata sune nan na fada mata yadda zata sha. Nace ni kan wallahi da nasan lokacin da cikin nan zai shiga ai da ban bari ba don ni yaran na ma dana samu na godewa Allah haka na. Tace na raba ki ba irin guda nan ake wanan magana ba kin dai ji abinda aka fada muna ai gara taga kowa dashi tasan ba ita kadai bace mace a gidan data iya daukan ciki. Ni dai murmushi nai mata kawai na koma na kwanta don banda aiki sai kwanciya yanzu shine nakeyi na da ji dadi a rai na wani lokaci. Don Allah ina mai kara baku hakkuri dani da fatan zaku fahinci yanayin da nake ciki don wasu na ganin kamar da gangan nake kin rubutawa a kullun, . Bayan sun sa ba haka nakeyi ba ko na dade ban daukan lokaci mai tsawo haka ban rubuta ba. Matsalar waya ce wayan taki min rubutu yanzu yadda nake so shiyasa bakujina ko da yaushe. Sai ida na da samu aro nake rubutawa na turo maku don Allah kuyi hakkuri dani yan uwa. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 96 Sannu Sannu komai yake tafiya a gidan mahaifiyar Hindatu tazo itace take kula da ita wai bata jin dadi a lokacin. Na dawo daga aiki na samu ta iso na shiga gaida ita da zuwa a wullakance take amsawa cikin wani basarwa. Ban tsaya ba na fito bayan mun gaisa da ita irin yadda naga ta sha min toka a fuskan ta. Ban sake komawa gaida ita ba nima nawa ya isheni lokacin karfin hali kawai nake nima don ban jin lakka a jikina. Washe gari na fita gin aikina ban ko bi ta kan bakuwar gidan ba nace naje gaida ita da kwana don naga alaman akwai magana gare ta. Na isa wurin aiki ban zauna ba na shiga duba marasa lafiyan da naiwa aiki suna kwance. Bayan na gama round ne na dawo office na fara duba masu zuwa ganin likita nakai wani lokaci ina dubasu na gaji na huta. Doctor Fati ce ta shigo wurina muka zauna muna hira da ita take tambayana hindatu na dan maide baki nace jiya koda na koma na samu mahaifiyar ta tashigo garin dubata ai. Mamaki ne ya kamata sosai tace kamar dai shine haihuwan fari gareta da sai mahaifiyarta tazo dubata. Idan ba don alamarin kishi ba minti nawa zaki duba abinda ke damun ta ki sani shine zata tsaya wahal da mutane haka ko yaushe ? Nace cikin murmushi ni fa kishiyace kin sani kuma ko han dubata ba nasani matsala ce ta ciki nima shike damuna yanzu haka amma na daure ina normal activities dina lafiya. Yadda nake ji din nan kuwa nasan da itace da wata kila sai an bata gado ta kwanta ma. Kin san ance kowa ya samu rana yai shayen sa wuri ta samu da tace kai yace sannu da tace kafa yana wayyo Allah na. Sai ta bushe da dariya tace anya doctor ba kishi a ciki zamcen ki kuwa nace ba dole nai kishi ba tunda abinda take fama dashi shine nima nake fama dashi yanzu haka. Ta sake bushewa da dariya tace to ai bashi ba doctor kece kika tsaya kina wani muku muku da naki cikin kamata yayi ace tasan kina dashi zakiga ta shiga hankalin ta ta daina duk wani sallo da yangan da take maku a gidan wai ita mai ciki. Naja tsuki tare da cewa ai baki san halin ta bane ita fa kanta kawai ta sani a duniya bayan haka bata san komai ba haka rayuwan ta yake ko yaushe. Mun dan dauki lokaci muna hira daga karshe muka juya kan maganan zuwa wani buki da zamuyi washe gari na auren diyar wata shugabar mu data gaiyyace mu. Na biya na dauko yara daga school muka dawo gida a gajiye na iso ban tsaya ba na shiga wanka na fito daidai Aisha ta shigo ita ma a gidan. Nan ta zauna ina shiryawa muna hira da ita tana bani labarin wai taga Raliya a hanya amma bata tsaya ta dauke taba. Nace ina mikewa tsaye Aisha to may ye abin damu ba gaki kin dawo gidan ba zafin ki yake ji na sani ba yau ba duk wani wanda ke tare dani matar nan bata kaunar shi na ciki na ciki ne da ita. Mun fito falo mun zauna sai fa Zulfa tafito tace ashe kun dawo ina barci daga barci kallo ya dauke ni a wurin . Nai murmushi nace da ita ai dole ki dinga barci maganin da kike shane haka zai ta saki jin kasala kafin ya bi jikin ki da kyau. Tace haba ni kan ai na manta cewa zai iya bani wani yanayi irin haka har nake ta mamakin may ke sa ina jin irin haka ne wai ko da yaushe yanzu ? Abinci zamuci ta zauna take bani labarin wai dazun tunda safe an kwasa da maigidan da mahaifiyar hindatu a gidan. Nace subbahanallahi may kuma ya faru haka ne wai take cewa dani nuna mai tayi kamar bai kula da yarta yadda ya dace shine shi kuma yau yai fushi ya fada mata magana son ran shi. Ni tunda ma tashige ban sake gani giccinta ba tun safe nasan amsa daya bata ne bai mata dadi ba don ita kamar yar nata take kin sani. Murmushi nayi kawai ban ce uffan ba a fili sai dai a cikin raina ina mamakin wanan irin rayuwa haka ace yarka ta dade gidan miji amma kullun kana mayar da ita karamar yarinya wai kaine may taya ta kishi. A can kuma dakin hindatu uwar ce tsaye tana magana da cewa yanzu na kara tabbatar da cewa wanan yar kauyen yarinya ta dauki kanta wata tsiya. Don tun zuwa na datazo tai min sannu da zuwa bata dawo ba gaida ni bance ke ma ki mutunta wani nata don itace ta fara. Mammy haka Rahama take fa ke tama yaba da ke da har tazo tai maki sannu da zuwa har nan isan dai ba wani dalili mai kwari ba zaku iya shekara ma a gidan nan baku hadu da ita ba. Don ko yaushe ita busy take har nan gida yanzu da aka gane ta biyota zakiga mata nayi da mazajen su tana duba su. Tace kuko wawaye kuna zaune baku baki baku fari har yar kauye tazo ta fiku sanin kan ta duk cikin matan gidan nan ita zaka kalla ka san tana zaune a cikin daula da jin dadi ta bar ku jan gadin gida da haukan son miji a baki. Kai haba mammy keda kan ki ke dadin wanan magana kuma har may Rahama tafini dashi da zaki fadi haka. Tace tafi ku wayo da sani kai mana nayi nayi dake ki nemi aiki amma son jiki da kai ya hanaki nema kun kwanmace ku zauna a gida kuna kallon kishiyoyi suna fita nemawa kan su abin dogaro har yaushe ta shigo gidan da tai nisa haka ta haku tazara. Kin san dai yau idan mijin ku ya fadi ya mutum wanan yar da kuke gani sai tafi kowan kason abin da ya bari. Tace mama duk mun san da hakan ai bashiyasa kikaga ina son nima in tara ba Allah dai yasa namijin zan haifa nima. Tace bakije an gwada ki ba ne ko may har yanzu? Tace ranan nayi mashi magana yace min shi baya son wanan maganan ko may Allah ya bashi ai karuwa ne ba a rainawa. Uwar tace ai dole ya fadi haka an cika mai gida da diya maza yana kallo yanzu bai damu da wai sai wani ya haifa mai su ba tunda ya riga da ya samu ko. Kin san ance wai su yan kauyen nan akwai abinda suke sha wai don su haifi diya maza saboda su gaje gida ko suyi ta samun masu taimaka masu da noma. Mammy wai da gaske ? Uwar tace ke haki taba sanin haka bane ko may ? Ai kibar bakauye inda kika gan su kin ga kishi da bakauye da bafillatana akwai wahala sosai a rayuwa. Sai hindatu tace kin ko ga ita Rahama dama zubi biyu ne ita don wurin uwa bafillatana ce ai duk su ta kwaso don uwar ta sai mutuwar Saade ta taba zuwa gidan mu har muka gan ta. Kice naku ya samay ku ashe ni ban ma taba sanin wanan maganan ba sai yau haba shiyasa muke aiki kullun kamar bamayi . Nan dai sukaita suratan su har uwar nacewa ai sun hadu damu kin san su fa yaro bai zuwa aure haka kara zube sai sun shirya yaran su tsab. Tace shiyasa dama nace a daurewa shegiya mahaifa kada ta kara haihuwa a gidan haka ya isa kowa ma ya samu tunda ba ita kadai bace mai cikin haihuwa. Sun kai wani lokaci suna zancen su na shirka a tsakanin su inda suka sha alwashi cewa ba zan sake haihuwa ba agidan na tara yara maza bulbul dasu kamar kiyon agric a gida duk wanda ya gan su sai yaji sha awar su. ********* ********* ********* Washegari Jumma,ane daddy ya fita da yaran maza zuwa sallah kamar yadda a ko wani jumma, a yake fita dasu Sun dawo akan idon mahaifiyar hindatu don sai ya zaga ko wani part dasu sun gaida kowa a gidan kafin su dawo inda muke. Bayan fitan su ne mahaifiyar nata take cewa kin ga abinda nake fada maki kullyn ko ganin irin wanan ai takaici ne a gidan nan ba kunya yake fifita diyan shi maza akan kowa. Jifa yadda ya tasa su a gaba ya fita dasu kamar mai nunawa duniya su ko shaddan jikin su iri daya da nasa kin ko san dai an sha kudi a wurin nan kan . Yar tace ai tare yake masu dinkuna dashi lokaci da dama haka zai shigo da kaya yace wai nasu ne tare ya dinka masu dashi. Da yamma muka shirya ni da yara zuwa wurin buki duk wanda yaga shigar mu sai ya kyasa muna a lokacin har mazan ban bari a gida ba tare zamu tafi dasu wurin dinner din. Mun fito ashe hindatu da uwar ta na wajen gida a zaune suna shan iska suna hira fitowan mu yai daidai da shigowan Raliya gidan da yaranta itama. Duk kallo suka bimu dashi nice nake cewa da Raliya kun dawo tace eh fita zakuyi ne haka tafi da gidan ka ke nan kuma yau zakuyi. Nace eh zamu gun dinner ne ba dadewa zamuyi ba ai da yamma yayi zamu dawo don ban son tukin dare sosai. Adawo lafiya tai muna ta shige don haka muka koma a fili zakace kalau ake zaune sai dai kowa na ciki na ciki kishin barki. Ihisan ce ta na ganin mu take cewa mummy yau ina zaku nace inshan dinner zamu banganki ba tun dazu na dauka kina barci ne ai. Tace mummy zan tafi sai kakan dake muna wani kallon sama da kasa, tace da jikan nata waya kasa dake balle ya kwashe. Tace ni sai na tafi tace bazaki ba na fada maki sai yarinyar ta juya ta tafi nace Ihisan ki zauna ki bari wata rana mu tafi tare. Ina ta shige ta tafi shiryawa nace da yara su shiga mota kafin ta fito aiko kakar na ganin haka ta mike ta shige ciki tabi bayan yarinyar murmushi nayi daga ina nake zaune a gaban motan. Can ta samay ta ta hauta da fada tana cewa ai ga yacan mun shiga mota zamu tafi dama maganin ta ke nan ai. Yarinyar tace mummy ba zata wuce ta barni ba tunda tasan na shigo na shirya don ni bats taba saba min alkawari ba irin mamana. Rankwashi kakar takai mata akai tace da ita mara hankali da wayo kawai uwar wasu kike fifitawa akan naki don wayo bai ishe ki ba an riga da an shanye ki ko ? Taci gaba da shirin ta kakar nata zagin ta har ta shirya tabiyo ta a baya tana fadin su kan ai yanzu sun kai inda zasu tafi ko don tun shigar ki gida suka shiga mota. Sai dai suna fitowa tagan mu zaune a mota muna jiran fitowan ta daga ciki ina ganin ta fito na tayar da mota muka kama hanyan fita. Nan muka barsu nasan dai zagine kwando kwando sai na sha shi gun mahaifiyar hindatu din don mace ce da bata iya boye kishin ta ita. Mun samu wurin ya cika makil da Jamma, a na ja yarana muka dan tsaya daga baya na kira Fati take cewa na karaso daga ciki ga wuri ta aje muna. Ciki muka karasa idon jamma, a a kan mu kamar dai yadda ake akowani buki idan kaga abinda zaka kalla. Sai da naga duk yaran nawa sun zauna na zauna nima sai ga Fati tazo take cewa dani muje mu gaisa da mai bukin don tana cewa dama ba zan zo ba ai don tasan ni bana shiga jama, a sosai. A can wani gun muka samay ta da yan uwan ta tana ganina ta taso ta rugumay ni tana fadin lalai yau sunana arziki tunda har kikazo wanan dinner din. Tun a wurin tacewa yan uwan ta a ware muna gift din mu daban suke tambayana munawa nai murmushi nace ni tafi da gidan ka nayo don ban bar kowa ba a gida. Antyn namu taji dadi sosai tace a samu abu a zuba mun da yawa naje na rabawa har abokan zamana nai godiya tare da bata envelop mai dauke da kudi a cikin sa muka fito muka dawo mazaunin mu. Bayan fitan mune yan uwan ta suka bude envelope din suka shiga kirga kudin kamar yadda akeyi a kowani buki dayar tace anty 200 ne fa cif ta sako maki a ciki tace ai Rahama tafi da nan in dai itace. Yarinyar nada kirki kwarai wallahi gashi bata da hayaniya baka sanin matan mai akwai ne sai wanda ya sani. Buki ya kai buki aka shiga gudanar da event din bukin sai ga ta har table din mu tace ai muna photo da ita. Nan mutane suka fahinci muma duk inda muka fito ba baya ba don manya basu hurdan banza haka da mutum a fili. Sai tara na dare na kwaso yarana muka dawo gida tu fitar mu nabawa ihisan abin bukin ta ta wuce dashi part din su mun shiga mun samu daddy ya dawo gida a lokacin. Yake cewa yau kan mummy da yaran ta tafi da gidan ka akayi ne nace na kai su ne suma suga gari sai Zulfa ke cewa shine kika fita da yar gwal zuwan mama biyu nan tana tambayan ku ai. Nace tunda dai tagaban dawo da nawa yaran ba ai tasan muna tare ke nan dama tun fitan mu ai bata so ba ita. Daddy yace ina ruwa ta da harkan iyalina nifa bana son abin raba daya biyun nan da ake son kawo min a gida idan bata biki ba ita wurta dawa take hurda balle ta san duniya. Ni dai na shige abina ashe dattijuwar bata hakkura ba da safe yaje gaida sune take cewa dashi jiya ai na tafi neman ka baka dawo ba. Yace lafiya dai ko mama ? Tace a, a dama matarka ce ta fita da ihisan naga har dare basu dawo ba shine hankalina ya daga yace akan may hankalinki zai daga mama ? Ita wacce ta fita dasu ba tare suke ba data dawo ai itama dole zakuga ta dawo gidan banga abin tayar da hankali ba tun da tare suka fita da uwarsu ai. To amma ace an fita har dare ai ha dadi ko ? Yace mama gidana ne fa kuma iyalina ne nasan halin ko waccen su Rahama ba zata kai su wurin banza ba tunda ba halin banza gare ta ba. Shiru dakin yayi ya mike yana cewa shi ya tafi sai hindatun tace dashi wai daren jiya batai barci ba da dadi tana son ya kaita asibiti. Hindatu nifa na fara gajiya da zancen asibitin nan cikin nan fa va kya kadai keda shi ba a gida nan yar uwar ki ni ko paracetamol bata taba min complain din shi ba kuma in ma wahala ne tafiki wahala da ciki amma take tsaye. Kwance take amma sai da ta mike zaune da karfi tace ciki a gidan nan baya nawa wacece mai ciki gidan nan kuma ? Yace ki lalaba ki gani ni dai na fada maki ya isheni hakana har ya juya ya fara tafiya sai ya juyo yace na manta mama ta shirya gobe zata koma gida munyi waya da Alhajin ku jiya. Au korata ma kake a gidan ka ke nan to ni ba zaman kowa nazo yi ba yata nazo fakewa don halin da take ciki. Ba koran ki nake ba gani nayi duk sauran na ciki amma suke iya kula da kan su haka na may ye amfanin mai aikin dake gareta da bata iya kula da ita sai wani yazo dubata ? Shi Alhajin da aka bari a gida shi kadai ai yafi bukatan kulawa shida ba lafiya ya ishi jikin shiba ai. Mamaki yabar uwar dashi takecewa bayan fitar shi daga dakin baby mijin ki fa yanzu ya fara baki dama baida kunya amma yanzu rashin kunyar nashi karuwa yayi don tun zuwa na gidan nan baiyi naam dani ba ina lura dashi. Mama kema kin faye yawan magana ne kamar kece matar gidan ina ruwan ki da zancen wai ihisan tabi Rahama wurin buki da ta dawo da abin arziki ba tare kuka raba da ita ba kuma kin kai karanta gun ubanta. Abu dai shirmay zalla haka suke gudanar da rayuwan nasu ba wani zancen tarbiya a cikin sa ko kwabo. Ya barsu suna hasashen daga cikin mu wacece mai cikin da yake magana akai din sun rasa ganewa don kowan mu a tsaye take kyam ba mai alaman lolayi tare da ita balle su gane. Hindatu tace kin san halin shi aiko don kada ya kaini zai iya fadan hakana don a zauna lafiya a gidan. Munadukai ne kuma fa da naci abu kanza ko wacece yar bakin cikin da zatai ciki yanzu lokacin da sukai nasu ina kallo wani irin bakin ciki ne ban hadiya ba a lokacin. Kedai yanzu a saka ido da kyau a gani ko za, a gane mai cikin sai mu san ta inda zamu bullo mata da shirin mu ba dai wata ta haihu ba a gida nan yanzu kuma don lokacina ne Allah ya gani. Bata so wuce ba amma da yamma da ya dawo sai gashi ya hado mata tsaraba dole ta fara shirin komawa da safe don ba wasa ko jin kunya ga alamarin shi. Ban san may ake shiryawa ba agidan na dai aikawa hindatun da sauran da abinda muka samo wurin dinner da muka tafi ne sai ga Amira ta dawo tana fada min taga hajiyan na shiri tana ganin zata koma ne. Nace ruwa ya raka taki gona don nasan idan tana gidan nan na tsawon lokaci sai an kwasa da wani da ita. Bamu fita ba ranan duk muna gida don weekend ne ina dakina kwance don ba abinda zan fito yi waje . A bakin Zulfa ne da natashi nake jin wai ta tafi amma tana ta fada wai ta gane munafunci aka kulla yasa maigidan cewa ta koma gida to ga hindatu nan da ciki tabarta a hannun Allah ya tsare mata ita. Nace kafin ta barta mu iyayyen mu da basu zo ba suka bari amana ai ba ita da ta kasa hakkuri tabar ma Allah alamarin shi ba. Tun tafiyan ta komai na gidan ya koma normal don wani lokaci hindatun kan fito ta zauna a danyi hira da ita ranan har bugun cikin zulfa tayi don taji wake da ciki a gidan tace bayan ke akwai wata mai ciki ne kuma ? Sai dai idan kina fatan ki samu mai tayaki daukan nauyi ne kuyi tare shine dai amma banga alaman ciki ga wata ba ita dai Raliya ban masa rai ga samun ciki gare ta don barikin ta bai bari tai ciki yanzu ai kuma. Wanan maganan da sukayi ne ya kwantar mata da hankali har ta daina hasashen zancen ciki ga wata a gidan. Bata san Allàh yayi ikon shi ba ko kowa kumshe yake da nauyin shi ya ja bakin shi ya kyale sai lokacin da aka gani. Cikin jikin Raliya ta fara ganewa don irin tane mai raki itama don haka muna kallon su suna ta haukan su a tare. Sai habaici da gori ake zubawa iri iri mu dai namu ido bukin kaunar Zarah ya tashi don haka yai min daidai da samun Leave din da nayi har na tsawon sati hudu zanyi. Muna shiri itama Zulfa ta kirkiro zuwa kano wai zata gaida hajiyan ta bata jin dadin jikin ta dole a tare muka tafi sai dai banzo da su Amira da Nasir da Atika suna da last exam da zasuyi suzo su samay ni a can. Baya baida kadan don ranan da muka wuce ranan ne Hajiyan daddy ta sauka Abuja ita kuma sai bayan mun taso ne take cewa dashi gata hanya zata zo a dubata don jikin ta ta rasa gane mai. Lokacin da suka iso gidan yaran suka fito da murna taron su tazo ita da Faridan mama Laraba dake zawarci a gidan hajiyan don zamanta yaki a gidan minin ta data aura gashi har sun haifi da daya dashi. An daukar masu kaya sai hajiyan ke cewa da yaran gun Amaryan baban ku Raliya zaku kai min kayana a can zan sauka wurin ta sai Amira tace mu dama mummyn mu da maman baby basu nan sun . Yaran suka nufi can da kayan nata suna shiga tana ganin kayan tace kayan waye kuma haka kuka kwaso min zuwa nan . Sukace hajiya ce tazo tace mu kawo mata kayan ta nan wurin ki tace ku aje a can ta ja tsaki ta mike da kyat zuwa taron su fuskan ta babu walwala a cikin sa. Da yamma bayan mun isa ne yaran suka kirani suke fada min yadda hajiyan tace nace ku sa masu ido idan dai gari ya waye kuje ku gaida ita da kwana don Allah kada naji wani abu ya fito daga gare ku. Munyi sallama dasu na kashe waya Zulfa ke tambaya na nake fada mata don muna zaune muna cin abinci a lokacin. Ko da daddy ya dawo yana tambaya hajiyan akace tana part din Raliya baiyi mamaki ba do yasan yadda suke da ita hajiya bata ganin kowa da daraja a gidan sai Raliya don da abinda take bata ya kuma san baikai wanda mu muke bata din ba ma hali dai ne kawai irin na hajiya nashi. Muna kano an fara shagalin buki da mu don dama haka nakeso ai komai dani don Zarah ta zamay min yar uwa yanzu mun wuce ma aminai da ita. A can Abuja kuwa washe gari da Raliya ta fita va a kawowa hajiya abin karyawa ba sai sha daya saura ta karya. Da rana ma sai kusan karfe hudu ta ci abinci kuma shine na dare gashi Raliyan ma bata zauna ba balle su gane kan ta. Da daddy yake cewa ga Rahama bata gari balle ta kaiki a dubaki sai cewa tayi ko tana gari fa ai ba wurin ta nazo ba idan kai baka iya kaini sai Raliya ta kai ni ai tunda ita tasan gari. Raliya tace hajiya ai banda lokacin hakan don aikin mu tun safe muke wucewa nan dai ta tsamay kanta daga zancen. Zuwan su asibiti sau biyu amma basu samu ganin likita ba a lokacin dole maganin da take sha taci gaba da dauka hakana a gida. Yaran sunzo sun samay ni suke min hira wai hajiya nacan tace yunwa ma zai kasheta a gidan abinci sai rana ya take za, abawa mutum ya karya haka ma na rana da dare. Nace ku barsu can a nan zan yi hutuna sai mun huta zamu koma bayan mun gama buki ne na buga mai zan shiga kauye na duba su don ance maigari baya jin dadi. Yace na dauka ai da an gama buki ne zaki dawo nace ba yanzu ba gaskiya don ina son in dan zagaya dangi na dade ban gan su ba. Lafiya lau mukai hutun mu a kano naje gida satina daya a ca naiwa yan uwa da abokan arziki alheri sosai tare da mama Altine na dawo zamu wuce da ita Abuja ta zauna a wurina har na haihu. Kiran waya da daddy ke muna yasa na bar garin ban shirya ita kan Zulfa taki dawowa tace sai ta kara kwana biyu ta huta zata dawo tunda yara suna hutu. Mu muka dawo ni da yaran da mama Altine mun iso da wuri don haka muka shiga gyara wuri don dan kuran da yayi. Nai wanka na saka dogon riga shiya sa duk wanda zai ganni zai ga cikina da yafito yai min girma sosai a lokacin. Hajiya dake zaune a falin su hindatu sai hindatu dake kwance ita da Farida suna kallo. Na shigo da sallama na na gaidasu na samu wuri na zauna nake cewa sai mukai ban hannu da ku kuma ashe kuna tafe. ? Hajiya tace ai zuwan mu bai sa kun fasa tafiyan da kukayi tunda kun san muna nan kuka samu wuri kukai zaman ku. Sai Ihisan tace hajiya ko ta dawo may zatai maki tunda kince bakyason ta dubaki ko tai maki hanya tunda bata fiki sanin mutane ba. Dakuwa taiwa Ihisan din tace ke kan hindatu sam yarki bata da kwabo ko kadan wallahi sai dan banzan son jikin tsiya. Aisha ce tashi go dauke da abincin da suka girka da muka dawo ta gaida ita tace hajiya ga abinci nan. Ta ce aje a gun a yatsune sai Farida dake kwance tun shigowa batai wani tarona ba ta mike zaune tana bude abincin tace hajiya tuwone fa da miyar ganye a wullakance take magana. Sai naji hajiyan tace kai amma yar nan Allah yai maku albarka yaushe rabona da tuwo tun da na baro dakina sai wani abincin yamay yamay yake dura muna sai dai muci don kada mu mutu da yunwa kawai. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 97 Bayan nayi wanka na huta ne na shiga na gaida hajiya dake part din su hindatu din. Dogon rigar dake jikina yana iya baiyanar da cikina na dan wata shidda da yai mugun girma da nauyi. Na shiga da sallama suna zaune a falo hajiya da farida da hindatu na zaune suna cin abincin da Aisha ta kawo masu daga wurina din. Nai masu sallama na karaso dakin sai dana samu wuri na zauna da kyat hajiyan idon ta a kaina take cewa to ashe ku duk gidan a koshe kuke kowa yai nauyi ke nan a gun zulai nake ji wai itama Zulfa dan matashin ciki ne da ita. Yanzu ke kuma gashi nagan ki haka a niki dake kamar wacce ma ta kusa haihuwa da alama dai. Loman tuwon da hindatu zata kai a baki bata san lokacin da ya fado mata a zani ba, ta dago kai tana min wani irin kallon kurulla da sauri. Na sauke wani dan gajeren murmushin ka saita nace da hajiyan sannun ku da zuwa tace mukan ai har mun huta kune da sannu ai yanzu. Nace yaya kufan jikin naki ta dauki kofin ruwa takai a bakin ta sai da tasha ta koshi tace dani jiki Alhamdullahi naji sauki don na samu manyan likita sun bani magani ai. Allah ya kara sauki nace da ita na juya gun Farida da ko kallo ban isheta ba sai abincin ta take ci nace da ita hajiya Farida ya kwana biyu tace a tambayeku ku manyan gari. Nasan gatse taimin don har gobe duk inda ta zauna fadi take wai sabodani daddy yaki auren ta nai wa daddy asiri na aure shi. Na mike da kyat tsaye nace da ita ni zan koma hajiya a huta gajiya Allah ya bamu alheri. Bayan fitana Hindatu tace amma hajiya Rahama takai babban munafuka a duniya ida ba yau da kika fadi zancen cikin ta ba, ban taba jin kuma wani yai maganan ba a gidan nan. Hajiya kikace harda Zulfa nada ciki ko mayne don ni maganan mamakine ma yake bani wallahi kai lalai akwai makiran mata a gidan nan ashe. Bata zauna ba ta mike tabar falon zuwa bugawa mahaifiyarta waya ta sanar da ita abinda taji a gun hajiya yanzu. Binta sukayi da kallo hajiyatace ita ke nan sarkin son kai bata taba son kowa da karuwa a duniya sai kan ta. Ban koma daki ba wurin mama Altine na shiga tana zaune ta mike kafafuwan ta da tasbaha a hannin ta tana ja a hankali. Na gaida ita tare da tambayanta mama kinci abinci kuwa ? Nakai idona ga kulan dake aje a gefen da take zaune ta ce na dan tsakura Rahama yanzu na gama tunane duniya ta addabi zuciyana. Sai yanzu nake ganin hikimar marigayiya na yin abinda ta aiwatar a baya gamay dake. Yau da ace baki gida nan Rahama ina naga kafan shigowa cikin wanan daulan duniyan haka ? Ai watakila dako yan jikokin nawa ma bazan gan su ba balle labarin su amma kinga yanzu yau gani zaune a gidan cikin mutunci kamar yar tawa na da rayuwa. Sai kawai ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi nima dai kukan na saka amma haka nake lalashinta ina share nawa hawayen. Ina fadin haba mama yanzu ke kina wanan kukan idan yaran suka gani abin zai dawo masu sabo a rai don ko yaushe a cikin wanan radadin suke suna dai shanyewa ne don irin kulawan da suke samu a gun mahaifin su. Ta share hawaye tace a gunki dai Rahama shi namiji ai bashine mai alhakin kula da yara ba sai mace uwar goyon su dake gida ko yaushe. Rahama ba don Allah ya hada yaran nan da ke ina zasu iya zama a gidan nan cikin wa yan nan matan uban nasu haka. Murmushi nayi nace aiko a haka zasu zauna din dasu dole tunda uban baida wasa wurin harkan iyalin shi. Tace dani Rahama Allah dai ya jikan Saade nace amin mama tace anya yaran nan kuwa zasu iya biyo halin uwarsu a dunitan nan yarinya da abinta bai rufe mata ido ba ga son zumunci da sanin darajan dan adam. Nace ai anty ta dabance wallahi samun mai hali irin nata sai an tona don ba kowa zai iya abinda takeyi ba sai wanda Allah ya ba irin rayuwan. Mun dauki lokaci muna hira da ita na marigayiyan har akai kiran sallah magariba sai muka tashi don yin sallah. Da dare daddy ya shigo gaida zuwa sun dan dade suna hira da ita ya mike ya yai mata sallama ya fito ya dan tsaya wurin yaran suna hira dashi. Ina daki zaune ya shigo da zaifita yana cewa yaya dai ko duk gajiyan ne haka dama kyale ki nayi ki tafi ki dandana ai. Yadda kike haka har kice zaki tafi wani buki a hakan dake rukuruku kamar wani abin dole can. Na dago kaina nai murmushi nace daddy bukin Zarah ce fa ida banje ba tunda ina iya zuwa ai ban kyauta ba kafa san yadda zarah take da kokari itama. Rashin zuwa na zaisa bataji dadi ba a ranta sai dai baza ta iya fada min bane don haka gara kawai dana daure na tafi ai. Yace ai yanzu gaki kina mukurkusa ke kadsi a daki, nace ai nz huta har barci saida nayi da muka iso ban wani wahala sosai ba ai. Nace ga mama nan munzo da ita ta dan huta kwana biyu tare da mu ta dabe muna kewa. Yace aiko kin kyauta wallahi dama tana cikin raina sosai don bai kamata mu kyale ta ba haka a can sai taga don yarta bata raye ne muka fita batun ta. Don Allah nasan ba sai na fadi ba ma abata kula yadda ya dace kada taga don yarta bata nan taga banbanci koda yake kema ai uwar ki ce ita din. Nace daddy indon wanan ne kada kaji komai a ran ka don mama banda abinda zan saka masu dashi a duniya nan don sune sillan zamana haka a rayuwana. Murmushi yayi ya juya ya fice daga dakin na kwalawa Aisha kira tazo ta bani wani abu don tashi aikine gare ni wasan dadi. ********* ********* ********* Washegari da kaina na shiga kitchen ina shiryawa su hajiya da mama abinci don nasan idan na barwa yaran bai wuce su yi tea da irish da kwai kawai su tashi. Miya nake hadawa don har na gama dafa abinci hankalina yana gun abinda nakeyi don haka banji shigowan shi ba sai muryan shi da naji daga bayana yana fadin. Wai may kike yi haka a kitchen da kan ki na dan juyo gare shi cikin dan murmushi ina fadin barka da fitowa ina kwana daddy. Ya karaso yana fadin yaya gajiyan tafiya koda yake naga alaman baki gaji ai tunda ga ki a kitchen da safen nan. Nace wai abinci nake kokarin hadawa su hajiya mai dan nauyi don nasan yaran nan idan na barsu shirmay zasu yi min kawai. Ban san cewa ya karaso har inda nake tsaye ba sai jin shi nayi ya rungumoni ta bayana tare da sauke hannayen shi a saman cikina yana dan tabawa a hankali. Ajiyan zuciya na sauke a hankali nace daddy baka gudun wani ya shigo ya samay mu a hakan nan yanzu. Yace and so what, ? Idan wani ya shigo din wata na rike ba matana ba, ban rike ki ne kike a haka murmushi na karayi na ce kai daddy dai. Hannun shi ya kara saukewa a saman wuyana ban san lokacin da na sauke wani irin ajiyan zuciya ba a hankali. Nace daddy kada fa wata daga cikin matan ka su shigo nan kasan bani ce dakai ba yau gaahi kuma kazo kana rike ni haka ? Yace matsalan ku ke nan wallahi kishi to na sake ki matsoraciya kawai na dan sake murmushi nace yafi min sauki ai. Ya dan ja baya daga inda nake ina rage gudun gas din da nake amfani dashi din sai jaji yana cewa yaya zamuyi ne da zancen hajiya don bamu samu ganin wani babban likita ba. Don ganin su yayi muna wuya andai bata magani shi take amfani dashi har ta danji dama sai kuma gashi daren jiya kuma abin ya dawo mata. Nace yaya take jine wai ? Yace tace wani abu ke tsaya mata a ciki kamar da yana mata ciwo wani lokaci kuma har yakan ma hana ta tafiya. Murmushi nayi nace at this age da take take jin wanan gaskiya ina fa sai an mata aikin shi zaifi don ko tasha magani ya bari watarana zai iya dawo mata da karfi yai barazana a gare ta. Yace wai Rahama may zai hana ki dubata a nan gida ki gani ko zaki fahinci abinda kyau ? Nace da sauri wa ni daddy? Kana ganin ma hajiya zata yarda da aikina har ta bari na dubata gara kawai kuje asibitin a dubata a can nima zaifi min sauki wallahi. May zai hana ta bari a dubata yadda take fama da jiki haka kawai ki gama zanzo mu shiga gunta sai ki dan fara dubata don Allah. Daddy banki ba amma dubawa a gida kamar sabawa doka ne kaga ba wani abin gwaji da zai nuna ga ainihin abinda ke damun ta din. Yace nace ki dai duba min ita bashi ke nan ba ban son mu tsaya muna gardama haka don Allah nace shike nan bari na gama zuba abinci nazo. Daga wurina wurin hajiyan nashi ya koma yake sanar da ita cewa zan shigo na dubats yanzu idan na gama aiki don haka ta shirya. Da sauri ta dago daga kwance tace wa ni nice Rahama zata zo duba har wacce Rahama din yau she ta zama wata likita can da tai ilimin gane ciwo na. Raliya dake hada mata tea tace ai shine gara dai aje aga babban likita zai fi yadda take ji din nan. Fada mashi dai ke yar albarka amma haka kawai ka dauko min wata matar ka can kace wai ta dubani yo Allah na tuba kai da ka dauke ta wata tsiya sai kaje ta dubaka yadda ta saba amma bani hauwa ba kan. Sai Raliya ta sake fadin ga dai likitoci manya da suka san aiki ko bayani kai masu sai sun fada ma matsalarka. Ke rufa min bakin ki banson raini noses kawai ke kin san abinda ta sani ne ko aikin ki ne hakan kada na sake jin bakin ki a cikin maganan nan. Tace Allah ya baka hakkuri daga fadar gaskiya sai a lake min kuma, yace rike gaskiyar taki na fada maki. Ke yi shiru gaskiya ne bai son a fadi ranan littani ki shirya ki kaini asibitin kin ji tunda shi ya nuna ya gaji da zuwa. Yace haba hajiya akan may za gaji da alamarin ki tace baga shiba kuwa kazo min da wani zance watau ni gani gidahuma ko na zauna matar ka tai min shirmay ta kashe ni. Yace haba hajiya aikin nan fa aikin ta ne kin sani sai dai idan wani manufa ne zai hanaki bari ta duba ki din don dai nasan Rahama har case din da yafi naki ta na dubawa don yanzu haka ma har naji ta fadi maysalan ki ko da komai. Taceina ruwan gobe da nisa ta zama yar magori ke nan ashe tun ba a ga mai ciwo ba har an san matsalan shi. Bai yi magana ba ya mike ya bar dskin tabishi da harara tace ka zauna yarinya karama tana juya ka yadda taso har ta kawo gare ni don raini. Sai lokacin Farida tai magana tace wai ma hajiya har wata Rahama ne can zata tsaya dubaki wai yaushe har tai wani karatun kwarai banda galihun da yai mata. Raliya tace ashe kema kin gane ni fa nasan komai kallon su kar nake kawai ana muna barazana wai ga likita a gida. Ko aikin ma ai sai anga daman fita ake fita yin shi likitan kwarai ne zai ta zama a gida ba shiga gun aiki to ire iren su sunyi yawa a wirin yan galihu. Amira ce ta shigo da sallama tana cewa a, a hajiya ashe dai sauki yazo ga shayi naga zaki tausa da bread. To ga abin karyawa inji mummy mu tace na kawo maki saura ki lashe kwanon tace cikin tabe baki har wani abincin zan lashe kwanon akai abincin naku da maggi da mai ke yawa cikin sa. Sai su Farida da Raliya suka kwashe da dariya kyeta hajiyan tace may kuka dafa ne wai nasa bai wuce shayi da kwai dai shine cimar naku ai. Amira tace wa ai mummy mu tafi da nan bude kigani mana nasan sai kin ci ko may ye ma tace ja,ira nice zan bude bude dai naga shirmay naku. Ta fara bude kulan tueon semo sai kular shinkafa da miya da kaya ganishing a cikin sa sai kular miyan yauki da wani na cow leg sai kulan miyan kaji naman yanka manya manya. Tace ja,ira ashe kin san may kukayi kike min shakiyanci dama kamar kun san shayin nan ya ishe ni wallahi tace mummy mu cefa tai maki shi da kanta keda hajiyan maman mu. Tace shine tai barnan nama haka daga inda Raliya take zaune tace ai kin san nama a gidan nan ba matsala bane da yakare kawo masu wani za, ayi . Sai hajiyan tace dole ma tunda baida aiki sai na zuba masu dadi suna ci Amira tace cikin tsiwa kowa ma ai yana zuba mai tunda ba fridge din gidan nan da babu nama irin namu a cikin sa don tare ake sayowa kowa lokaci daya tana fadin haka ta mike tabar su tace cikin daga hannu bye bye aci lafiya ko. Ni dai banga yazo ba ni kuma banyi magana ba sai dana gama komai na shirya na shiga gaida ita ban dade ba na fito don na samu tana cin nama Farida kuma yadda naga ta daure fuska ban ko bi ta kan ta ba ma gaisawa mukayi sama sama na fito abina. ********* ********* ********* Ranan monday ban samu fita ba ina gida Raliya ta kwashe ta zuwa asibitin bayan daddy ya basu kudin komai yadda zai ishe su don ya tafi lagos aiki. Sun tafi sun ga likita bayan tayi bayanin komai ne sai likitan ke cewa zan tura ku wurin doctor Rahama Abdullahi ta duba ku don wanan fannin ta ne kuma itace zata tsaya tai maku yadda ya dace da kyau. Ya kira massinger shi ya kai min file din su office dina yace ku bishi zuwa office din ta suna zuwa ake cewa dasu yau bata fito ba wai bata jin dadi suka koma gun mutumin da sukafito. Yace da zakuyi hakkuri har tazo da zaifi akwai masu iya duba ku ba wai babu ba amma ita tana da experices kan wanan matsala na mahaifa so sai don a germany tai karatun shi. Kallon juna sukayi da yai maganan sai kuma sukaji yana cewa ina ga matsalan cikine don tana da tsohon ciki idan ba zaku gaji ba zaku iya dawowa zuwa gobe nasan zatafito don tana da aiki da zatayi gobe. Sai dai ku fito da wuri don ku ganta kafin ta shiga aiki gani ta yai maku wuya. Likita yanzu kana nufin ba wani da zamu gani bayan ita din tunda bata nan ya da bugi table yace akwaisu da yawa ma sosai kuwa. Bari na tura ku wurin wata ita naga tashigo dazun sai dai zaifi kyau kuga ita wanan likita din dana fada maku ne. Ya tura su wurin doctor Lami tana tare da wata take cewa at dis age wannan case a gare ta da dai suga doctor Rahama Abdullahi naga zaifi kyau. Kara kallon juna sukayi sai ita doctor din da sukazo gunta tace mama matsalan ki fa aiki za ai maki don samun lafiyan ki. Aiko ta mike tashiga fada ta cewa Raliya su tafi don tana ganin kamsr basu san aikin su ba ma a nan. Tun a hanya daddy ya kira Raliya yana tambayan ta sun tafi asibitin ne take cewa eh gamu hanya ma dawowa gida yake cewa da ita kun ga likitan ko sai tai shiru can kuma tace dashi eh mun gan shi . To may sukace daku ne akan ciwon nata tace gadai hajiya din sai ta mikawa Hajiyan nashi wayan ta kara a kunnen ta. Ya gaisa da ita tare da tambayanta yaya jikin jata take cewa dashi da sauki yace may likita yace daku ? Tace wa yan nan mashiririta may suka sani asibiti kamar wanan wai ace muga Rahama itake da masaniyan irin matsala na fiye da kowa. Yace ban gane ba hajiya tace ba zaka ko gane ba kaidai don wata yar banzan yarinya ma cewa tayi wai aiki zasuyi min. Nan yace dama ko Rahama ta fada min haka na tace sai sunyi maki aiki don samun lafiyan ki. Tace bakaji ba dama ai nasan bakin su daya hadin baki sukayi da ita wai ace dole sai na gan ta don ta nuna min ita din takai ta isa. Yace hajiya yanzun dai zan dawo yau sai a san abin yi tunda abin na matsa maki haka zan zo muje aji ko may ye hakana. Allah ya dawo dakai lafiya tace dashi sukai sallama ya kashe wayan shi yana mamakin wanan wani irin kiyayyane haka har da lafiyan mutum zai hada ? May ya hada Rahama da hajiyane haka wai wanan abin yai yawa Raliya yace a ranshi don ba Raliyan ba kowa yanzu bata gani in ba Rahama din ba. Sai dai kuma ko ita Raliyan ai bata tsira ba tunda tace tana barin ta da yunwa ta fita ko kuma a bata abinci ba dadi. Yace kai hajiya ho Allah dai ta bar min ke naita ganin ki ko yaushe muna kwasan wanan draman naki. Ya dawo da yamma rana daya suka dawo da zulfa sai dai ta riga shi isowa garin ita don har ta manta tayi tafiya ko. Muna zaune da ita ya shigo falon mu muka shiga gaida shi yace da zulfa din ke kinga daman dawowa ai na dauka can zaki zauna kuma. Tace kai kaji yaya in zauna gadin gida ko may ka kwaso mata ka gaba daya da yara ni zaman may zanyi can yace wa sanan maki nace ai dole daddy yai fushi anty daga zuwa kin samu wuri kin zauna in ya bude ido ba uwar gida ran gida a gidan. Tace kaji Rahama dai da wani zance can muna dai uwargida ko ga amaren gida wake ta wata uwargida can kuma. Mu dai raka ko a hakan mu samu dai a laba mu muci arzikin ku kawai tace su mama na gaida ku yace kin barsu lafiya dai ko tace eh. Ashe hajiya suna nan har yanzu jikin ya kiya kuma sai jiya dana shiga ne Alhaji ke cewa dani ta samu wuri tai zaman ta nan nasan ba su dawo ba ashe. Yace kai Alhaji koni ai ya kirani yana fada wai nazo na rike mai mata naki turota ta dawo an barshi daga shi sai yara a gida. Nace ba a ga likitan bane har yanzu wai Alhaji ai yana da gaskiyan shi tunda ya tsufa dole yana son mai taimaka mashi kusa dashi ai. Ya dan ja tsuki yace wani likita ba sun tafi dazun ba ance su ganki wanan algunguman Raliya nasan ita ce ke zugata ai. Zulfa tace ashe suna ta ke nan kaima ka fara sani halin makirci na ta ke nan dai. Ta maka mata harara yace dani ke taso ki hada min ruwa na watsa ko zanji dadi don nice da girki a ranan da ya dawo. Sai da ya dan jima da fita na mike nabi bayan shi don hada mai ruwan wankan ca ya rike ni ban fito ba sai da nazo cewa yara su rufe kofa na koma. Da safe na tafi wurin aiki ina office zaune ina tsaka ga aiki file din hajiya yazo table dina sam ban kawo cewa ita bace don ban san zananen sunan ta ba ma ni. Nace su shigo sai gasu da Farida don tare suka zo dashi amma shi ya tsaya waya lokacin yace su shigo gashi tafe don dare jiya abin ya matsa mata sosai. Kaina a duke yake lokacin ina rubutu sai da naji tace to babban likita gamu mun shigo sai a duba mu na dago da sauri na kalle su tare da mikewa tsaye. Nace hajiya kune ashe dama ba a ga likitan bane ko may da aka turo file din ki nan wurina ban san kece mai sunan ba dana ce ki bari na dubaki ma a gida ai. Sai ga daddy ya shigo office din yace ok sun shigo may aka ciki sai nai shiru can na dago kai nace hajiya yaya kike jin jikin naki ne ? Yace ki fada mata komai don kinga na shi na karshe cikin mutum ukun da aka tura mu mu gani. Na jawo takarda ta na fara rubutu akai sai farida ne ke min bayani cikin rashin fahinta amma ni na fahinci komai. Na shiga jefo mata tambaya tana bani amsan abinda nake son ji na rubuta komai na dago na cire glass din dake idona nace gaskiya daddu sai mun cire mata mahaifa don idan ba haka sai na dan sasauta murya na kasa nace zai haifar mata da zuban jini da zai iya sanadin ta. Tace a hasale tare da min dakuwa Rahama karbi nan tun baki isa saka dan kanfaiba rabona da jinin al,ada kinji. Abin ya bani dariya amma sai na daure nace hajiya shi wanan din ba jinin al, ada bane jini ne na ciwo zai haifar maki ya koma cancer na mahaifa don haka don Allah hajiya ki daure ai maki aikin na tun kan matsala ta shigo. Sai jikin ta yai sanyi tace na shiga uku ni hauwa,u yanzu ba wani maganin da zan sha ba sai an taba ni ba yar nan. Nace hajiya haka shine sauki ba wai sai yaran mata kanana ke samun wanan matsakan ba harda tsofin da wanan matsalan ya sama ta faruwa dasu haka. Nace hajiya kada ki ji komai wa yanda za suyi maki aikin kwararun likitoci ne don sun san aikin su cikin yan kwanakin da baikai sati ba zaki mike insha Allahu. Jikin ta yai sanyi sosai ta juya gun shi tace yanzu yaya za, ayi yace hajiya aikinji abinda ta fada kiyi hakkuri a rabaki da wanan abin don Allah. Nace hajiya taso ki hau gadon can mu gani ta mike da kyat jiki ba karfi ta hau gadon na sake labule na dauko abin awo ina dan duba maran ta daga kasa kadsn har nakai inda ciwon yake mata nace na ne yake tokare maki ko tace na ne kedai. Nace idan ya gama zaiyi ruwa shine zai jawo maki wanan zuba jinin nan gaba kadan tun da har ya fara yi maki hakan. Na kamata ta sauko muka dawo inda suke nace dashi daddy aiki zamuyu mata insha Allahu abin zaizo da sauki don haka zan bari har a aje magana sai a saka ranan da za ai mata aikin ko ? ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , 98 Ba don hajiya taso ba aka tsayar da ranan da za ai mata aiki don gaskiya ya fara son sako mata jini ya koma servicer cancer mata. Take hankali ya tashi don har ta koma Kano sai gata an kwaso ta ragai ragai an dawo da ita ba dadi ba bata lokaci nai setting din yi mata aiki a take. Da safe zamu shiga da ita don haka da daren nan muka bata gado a asibitin mu inda za ai aikin. Fatima da Aisha sun zo tare da ita don Farida dama tana nan wurin Raliya ta tsaya bata koma ba tana taya ta kishi. A taya kishi mana don ko ga maciji batayi da mu ko wani nawa sai kule kule da makircin da suke yi ko yaushe a gidan. Don ni har ya kai nai mata kashedi a kan dukan min diya da takeyi da zaran yaro ya fita yanzu zai dawo da kuka yace gwago Farida ce kamar yadda muka koya masu kiran ta. Ranan ta daki Abdul har bakin shi ya fashe ga shedan mari da taiwa yaron yai kukan wahala har yai barci don wahala. Koda na dawo na samay shi a falo yana barci jikin shi yayi zafi nake tambayan may ya samay shi ne ? Sai Amira tai shiru na sake tambayan su ina a tsaye nace ba tambayan ku nake yi bane kun kyale ni haka ? Sai Aisha ce tace dani wallahi gwagon shi ce ta dake shi har da mari sai da ya fadi bakin shi kuma ya fashe takuma hana yin shi kuka. Take naji raina ya baci na juya zuwa part din nasu tana zaune ta tsefewa yar wurin Raliya kai na shiga da sallama na. Suka amsa min ciki ciki na ce cikin rashin damuwa yau kuma Farida may ya hada ki da dan ki haka kikai mai wanan irin dokan haka ? Tace a tsiwace ko kinzo ki rama mashi ne don naga kamar kinzo a fusace ko banda hurumin duka dan kine kike nufi don suna diyan gwal ko ? Nace wani irin magana kike min haka dukan ne dai irin haka bai min dadi ba kawai tace to na dake shi ba kuma zan fada maki dalili ba sai naji shaka da makura. Nace to ki sani kiyi na farko kiyi na karshe tunda abin naki da niyya ne kika yi mai wanan irin dukan haka har may Abdul ya sani da zaki dakan min shi haka ? Tace dama bamu san asalin kolo bane da sai yace muna ai shi daga masar yafito har kewa da zakiyi min iyakan dukan dan dan uwa na. Nace da ita dan uwa dan uwa fa kikace sai dai ni bana jin lissafin ki daga cikin yan uwan nashi kinga kuwa ban sani ba ke nan ashe ? Kaji banza waike kina ganin kin zama wata tsiya yanzu ko kada ki manta ni Farida na san yadda kika shigo gidan nan da yan tsumakaran ki kina rabe rabe kafin kiyi wayau ki cin amana ki kwacewa mata miji. Nace wanan kuma karya ne ki tambaya kiji ni Rahama ban da ragga balle tsunma a tare dani ko da nazo gidan nan don ni ba mai kashin tsiya bace kin kuma gani kin sani. In ma har cin amana nayi aure na da daddy ai kafin nayi kece kika so yi keda har yau son auren shi kikeyi keda ke zuwa wurin mata tai maki goma na arziki. Don ki aure shi kika kashe auren ki gaki nan har yau kin ki aure kina zaman jiran tsanmani don hauka duk da kuwa yar uwarki na cikin gidan amma kin rufe ido don kwadayin abin duniya sai shi. Tace ke akwai wanda yakai ki kwadai ne daga ganin sarkin fawa sai miya yai zaki ina sai faman haihuwa kike ke a dole ki cika gida da shegun yayan ki masu kama da diyan kwara. Wama yasani ko wanan farin ba surki kikaiwa mutane ba kina labawa da wasu diyan kwara can a gefe. Nace ban da wani shakka a nan don dani dake ansan wacce ta rike darajan ta har gidan mijin ta diya kuma yanzu na fara haifosu a gidan nan sai nai dozen. Mara mutunci kawai wacce bata san ciwon kan ta ba sai kwadayi da makirci don son abin duniya da kika sakawa kan ki ke da daddy kuma sai a lahira idan ana aure in kina da rabo ya aure ki can din ban sani ba. Ina fadin haka na juya na barta tana jefo min zagi ina jin ta ina shiga hayaniyar mu ya tayar da zulfa dake barci take cewa dani wai yaya akayi ne raina ya baci ban iya magana ba a lokacin. Nace ba komai kawai na juya sai Aisha ce naji tana fada mata abinda ya faru ta nufi yaron tana taba jikin shi tare da cewa nifa naji kukan shi a cikin barci na dauka ko dashi da yan uwan shi ne ai. A daki ta samay ni na fito wanka lokacin na dan ji sanyi a raina nake mayar mata da irin bakaken maganan da muka fadawa junan mu. Tace a, a abin na farida hauka ne ko rashin wayo yaya zaka doki yaro har da mari irin haka yaro ma kamar Abdul don Allah dai ? Nace ai in halin tane gobe ta kara dukan min yaro ta gani bayau ba tun zuwan ta gidan nan abinda takewa yaran ke nan wallahi ina dai hakuri ina shanyewa ne kawai don na fahinci da manufa take duka su tunda basu kadai bane ai yara a gidan. In don ta nice da daddy ba zaiji maganan ba gaskiya tunda ta fada min na fada mata an wuce wurin ke nan. Amma yana dawowa da dare Zulfa ta samay shi da maganan duk yadda mukayi ta kwashe ta fada mai ya taso zuwa part din dina ya samay ni zaune na rugumay yaron a jikina na shafa mashi metholater a wurin ina bashi magani. Su Aisha na ganin shi suka fita daga dakin yace may yaiwa Farida tai mai duka haka ba tausayawa nace ban sani ba ni dai na dawo na samay shi a haka nai magana kuma tace ban isa ba. Yace shine har da bakin ta zata zargan min diya wallahi duk yadda nake da mutum bana daukan irin raini haka a gabana ya daga waya ya kira mama laraba yana fada mata duk yadda mukayi. Mama tace dama na sani sai da na fadawa yaya may yasa ta barta can don nasan ba a kwashewa lafiya da ita in dai Farida ce . Tursasata sai ta fada ma dawa diya ka sukai kama don in ma wani taji ya fada a sani yarinyar banza kawai mara hankali da tunane. Bai yi magana ba ya juya ya na fadin ku samay ni falo yanzu ina jiran ku ashe bamu kadai bane a falon duk kowa ya kira a cikin mu. Na shigo falon fuska ba annuri ina saye cikin dogon riga dinkin yan ethopian duk suna zaune a falon sunyi shiru gaba dayan su na shigo. Wuri na samu na zauna nima ina sauraren abinda zai wakana a wurin can yai gyaran murya tare da cewa na dawo gida yanzu Zulfa ta samay ni da maganan abinda ke faruwa a gidan kan Abdul tsakanin uwar shi dake Farida. Sai kowa yai shiru can naji muryan Farida tana cewa wai fa yaya don kawai na daki dan ta kowa yake da suna ma oho ? Sai kawai tana dawowa ta samay ni da cin mutunci tana cewa wai na bar dakar mata yara akan may Rahama zata ce wai kada mm a tsawata wa yaran ta ita waye ? Sai yace ita matata ce kuma dan tane kema kin fada yanzu da bakin ki cewa don kawai kin dakar mata da. Yace ke Raliya ina son ki fada min may ya faru tun daga farko abinda ya faru. Sai tace wa ni nikan ina ruwana da zancen su tunda ba dani akayi ba balle na saka kaina a cikin maganan su. Yace tambayan ki nayi ba wai jawabi nake son ji daga gare ki ba, sai tai shiru ta na murmushi kawai yace uhumm ke fa nake saurare kada ki bata muna lokaci a nan. Ganin ba wasa a fuskan shi yasa ta cewa a, a muna zaune ne sai yaran ke wasan ball a baya sai suka daki window side din mu. Shine ita farida tai masu fada tace kada wanda ya sake wasan ball din to ban san yaya akayi ba shi Abdul din ya buga ball din. Sai naga ta fita zuwa wurin su can naji kukan yaron ita kuma ta dawo take cewa wai yaron nan na Rahama karami ne ya sake buga ball din shine ta dake shi. Hindatu tayi mata magana akan don may zata dake shi a nan suke wasa kullun kuma window din ba mai saurin fashewa bane. Sun dai danyi maganan su suka bari sai ga ita Rahama da tadawo daga gun aiki ta shigo tana mata magana sai sukai ta cacan baki anan. Daga karshe dai bayan sun fadawa juna magana sai Rahama din ta wuce zuwa shiyan ta ta bar mu a nan, don har ita Rahaman nacewa kada ta sake dokar mata diyan ta. Jin haka na dago kai da sauri na kalli Raliya din don na fahinci ta fadi hakane don daddy ya fusata yace don may zan hana yar uwarshi yiwa diyan shi fada. Yace ai gaskiya ne don ban taba jin Rahama tayi fada ba akan yaran ta a gidan nan sai yau don ko abin yayi muni mari Farida kewa ya mareki ga kuma bakin yaro yaro ya fashe har ya kumbura haka ? Gaskiya Farida ina ganin gara ita Rahama ta iya kawaici a kan yaran ta ni gaskiya ban iya ba ko kadan don yaran nan amana suke a wurin mu. Ana raba yaro da wasa ne ko may shin idan ma basuyi wasa a gidan uban su ba sun sakata sun wala a gidan wa ake son su fita suyi wasa. Ko mata na gasu nan dukkan su hudu nan ko uwar yaro ne kuwa bata isa ta hana min da yara wasa a gidan nan ba don kuwa don su na gina gidana Idan basuyi wasa a nan ba sai a makwabtane zasu tafi suyi ko may ? Uwar yaro ma bata isa ta dokar min yaro ba balle wani can daban sai ta dago kai ta kalli dan uwan nata sai kuma ta dukar da kan nata a kasa. Yaci gaba da cewa ni bama wanan ba a cikin musayan harshen da kukayi naji ance kin ce yaran Rahams suna da surki wai diyan wani kwara ne ko may ?. Ko zaki fada min dalikin ki na fadin haka ? Kuma ki sani wallahi wallahi idan baki da hujja ga fadin haka sai na dauki mataki mumuna a kan ki kuma ki sani kowa ma ya sani. Rahama da kike gani amatsayin bazawara na aure ta sai dai abinda na sani a kanta duniya ba su san shi don haka yau ki sani kuma ki sheda nine mutum na farki da nasan Rahama a matsayin diya mace a duniya don bata taba taraiya da wani na miji ba sai a kaina. Gaba daya suka kallo shi a lokaci daya yace wallahi Rahama bata taba taraiyya da tsohon mijin ta ba don tun kaita gidan shi ta samu baida lafiyya haka ma duk zaman ta kasancewa tana kaaratu da hurda a cikin maza Allah bai nufi shedan ya rude taba a rayuwan ta. Don haka har ina wanan zsncen zai fito haka na yarda da wanan cin zarafi ki sheganta min yarana don kawai wani banzan kiyayya irin naki. Wanan irin maganan ma ai bai taso ba ga dan uwan ka yaran nan farin fatan uwarsu kawai suka kwaso amma komai na mahaifin su ke garesu ai balle irin kaman da suke da Nasir da Jinior da hanifa duk wanda ya gansu yasan jini daya ne su. Kamar yadda Amira da su ihisan suke da kama duk ai yaran gidan nan kamar su daya sai dai launin fatan uwayen su da suke kwasowa ne kawai. Zulface ke wanan zancen sai hindatu tace wanan maganan ma ai bai koyi dadi ba dan uwan ka zaka shegan ta don wani akidar banza naga mu ban duka ai zaman mutum daya mukeyi. Ba wai sai ka goyi bayan wani ba can don asan in da kake nijan wallahi duk wanda ya shegan ta min diya sai inda karfina ya kare dani da mashi. Ai ba Rahama taiwa sheri ba shi dai ta tozarta kuko haka ba kyau fa a goyi bayan mutum daya a bar daya ba gaskiya bane. Sai lokacin da naji Raliya ta fadi haka nai magana nace ba mamaki don kin fadi haka akan wanan macijiyan da bata da ramin kan ta sai na wani. Nasan kimai Farida keyi a gida nan bakin ku daya to ku sani idan tayi taji dadi tajira nata sakamakon ni dai nasan diyana diyan halak ne basu da surki ko daya. Don ko makaho ya lalaba yasan gaskiya ba komai yasa ta fasin wanan maganan ba sai abu biyu na farko ta fadi ne don ke Raliya kiji dadi sai na biyu dan hassadan dake tsakanina da ita wanda yau da bakin ta ta fadi na samu gida ina zuba diya don nafi kowa kwasan kaso. Farida ki sani kaso baya raina nafi bukatan ganin mijina a raye da ya mutu ya bar muna kaso muyi murnan kwasa a bayan shi. Wa yan nan diyan gaba daya da kike gani ba nawa ba kawai nakowa ma ina ma masu fatan a koyaushe ubangiji ya azurta su fiye dana mahaifin su. Basai sun jira gado suyi arziki ko suci ba shi kuma haihuwa Allah ne mai badashi a duk inda yaso ba don kafi wani ko wata a gare shi ba. Don haka ni dangin miji ko kishiya ko wani mai dauka kin azawa bai taba damuwa na a raina ba don hassada dama taki ne the more ake hassadan the more ubanguji ke kara ma karuwa idan har kai tawakkali. Daddy ne gashi nan Farida yau dai in fada maki gaskiya baima san haukan son shi da kikeyi ba har kike ganin nice na hana shi ya aure ki don ya aure ni. Ban taba soyayya da daddy amma Allah yayi rabon aure a tsakanin mu harda samun zuria a ciki masu albarka idan yau daddy yace Farida zan aura baki taba jin Rahama ta ce kanzil a kan zancen idan ha a aure ni aka auro ni. Don may ni da Allah yai wa wanan baiwar zan tsaya ina fada akan abinda Allah yai min fada a kan shi don haka daga yau ina rokonki da ki sakar min mara ki fita hanyan diyana da kika saka min su a gaba tun basu fahinci may kike nufi dasu ba daga baya. Ina fadin haka na mike na bar falon raina a bace ya juya gareta yana fadin haukan da kuke tayi ke nan a tsakanin ku shekara da shekaru ashe ban sani ba? Da ina jin wai wai na dauka shirmay ne na mutane ashe kekin saka a ranki hakan ne koda Zulfa bata gida na Farida kada ki taba tunanen wanan haukan na cewa zan aure ki a rayuwana don idan akwai abinda na tsana shine auren gida don bai taba bari a zauna lafiya tsakani. Ba kunya tace dashi idan Allah ya nufa Zulfa ko wata bazata taba hana ni ba da ba ayi ai itama da ba a aureta ba ita Rahaman dake fadin haka ai auren ta ne ta hana ka aure ni din. Wani tsawa ya buga mata yace ke Farida ashe rashin kunyan da ake fadi naki har ya kai haka ban sani ba to ki kama kan ki daga yau na fada maki kada ki kara gigin dukan min diya, kuma kinji nayi ran tsuwa tunda baki da hujjan sheganta min diya da kikayi ki shirya gobe goben nan ki bar min gida na nai maki kashedi da zuwa min cikin iyalina kina kokarin bata min kan gida na. Tace yanzu yaya akan wanan magana kake fadin na bar maka gidan ka, don nayi fada da wanan matar taka da kowa take son rabaka dashi har zaka koreni gidan ka. Ta ce ba komai zan bar maka gidan ka amma ka sani daga kai har ita sai kunyi nadamar yin hakan da kukai min saboda mace zaka rufe ido ka manta da zumuncin dake tsakanin mu. Akan mace har ka manta da irin halarcin da mshaifiya ta tai maka don yanzu mutum na ganin ya fi mu shine zai mayar da mu banza. Wani tsawa ya daka mata kamar zai mare ta tai saurin mikewa tabar falon da hanzarin yace da ki tsaya kiga rashin kunya yanzu mahaukaciyar banza da wofi kawai. Ya juya wurin Raliya yana cewa da ita ke kuma ki sani duk wani makircin da kuke kullawa da ita na sani ba yau ba ido kawai ba saka maku har takai ga maki zaki gane kuren ki indai wanan mara hankalin ne. Tace cikin wani irin murya tare da dafe kirjin ta tana cewa wa ni ni yanzu may ye nawa a ciki kuma da za, a saka dani? Yace koma may ye ai kin sani saura ke yanzu idan kinga taiwa wata kinji dadi har kina fadin wai ana backing din on side an bar dayan. Nan hajiya bataso barin taba kika marairaice wai ke a bar maki ita ta dan kwana biyu dama nasan makirci ne kuka kulla gayin hakan. Yau ba don Farida diyar mama Laraba bace wallahi da ko ciki daya muka fito da ita da nayi karanra kan shega ta min diya da tayi . Ita ma Rahaman nasan don albarkacin mama din ta kyale ta da sun kwasa da ita akan wanan kazafin da tai mata sai dai ita wawiyar bata san ana mata ragowa bane don hakan. Ashe ita Raliya abin duniya ya damay ta jin da tayi Farida na son daddy ne da safe na kwanta na huta sai gata har dakina tashigo. Nai mamakin ganin ta dakin nawa take cewa dani ko barci kikeyi ne na tada ke komay ? Sai da na dan juya a hankali nake cewa da ita shidin nake son yi dai kan sai dai ban fara ba ne. Tace dama magana ne ya kawo ni gun ki ta zauna daga bakin gadona a hankali don yanayin da take ciki sai a hankali yanzu. Bayan ta zauna tace ina fatan ba zaki min mumunan fahinta ba ga abinda ya kawo din dama ba wai magana bane sai zancen Farida. Don Allah wai da gaske son daer take yi kodai fada ne yasa kika fadi hakan ko da yake itama naji ta fada ai da bakin ta. Abin tun jiya ya daure min kaina ne Rahama don ta yaudare ni duk zaman da muke da ita ashe ita da wata manufa take tare dani. Zataci gaba da magana nace Raliya ni fa wannan maganan ya wuce a raina don taci albarkancin mahaifiyar ta saboda irin mutuncin da take min sosai. Don haka don Allah abar wanan zancen don ni ba ma so daddy yasan da wanan zancen ba tunda munyi a tsakanin mu da ita. Murmushi naji tayi take cewa dama nasan da wuya ki fada min komai yadda zan gane don kun barni a duhu ni. Nace don Allah mu bar wanan zancen don ni Farida bata tsare min komai ba kuma ba an so ace a sanadina ba ta samu matsala da dan uwan ta. Tagane bata fahintar komai don haka ta mike ta fice daga dakin naja tsuki na gyara kwanciyana kawai ina tunanen ta. Shine sai ga hajiya anzo da ita da yamna ragsi ragai ba lafiya dole na shirya muka shiga asibiti tare da su. Taoe na gudanar da komai da za aimata ranan a cikin dare aka shiga da hajiya din da ni akai komai amma za, a fara aiki sai nace suci gaba na fito daga dakin ban tsaya wurin ba. Daddy suna ganin na fito yake tambaya na yaya may ya faru kika fito kuma ? Nace za, a fara aikin ne yasa na fito na riga da nayi setting din komai ko ai shiyasa na fito ya zaro ido yana fadin don may zaki fito sai na dan kada kaina a hankali nace a, a ba zan tsaya ba ciki idan sun gama dai zan shiga na gani. Ba daddy ba duk wanda ke wurin ya gane manufana ba zan tsaya na ga aina ma sarakuwana aiki bane a gabana kawai. Wani daga ciki ya leko da sauri yana kirana sai gaba daya daddy dasu Aisha suka mike a rikice don duk sun tsorace sosai a lokacin. Na shiga suka dan yi min bayani akan aikin mu baya mun dan tatauna dasu nz fito a tsaye na samay su a rikici ina isowa suke ce min may nene wai nake cewa dasu ba komai bane tambayana sukayi kawai na fada masu ancire mata mahaifan nata ko wani ciwo ne kuma suka gani suke min magana aka shi. Tare dani muka kaita dakin da aka kwantar da ita din sai da ta fara farfadowa lokacin dare yayi sosai amma duk da halin da nake ciki ina tare dasu sai sannu suke min ina murmushi. Sai tara nace zan tafi gida don har ta farfado ko sai dai ta koma barci kuma a lokacin na kwantar masu da hankali na tafi. Ina zuwa wanka nayi na fito na dan karya sama sama na samu wuri na dan kwanta na huta. Hajiya taga gata wurin abokan aikina abinci da su lemo da su ayyaba apple da sauran abin dubiya haka suka dinga kawo mata. Ni da kaina na ke dubata inayi ina dan taba aiki kulawan da ta samu sosai da gata yasa tai saurin helling da wuri ni na bata sallama don ward din mu ne na yan ghany. Na dauko ta zuwa gida zamu nufi part din Raliya da ita sai tace a, a kaini wurin ki Rahama a can zan sauka wanan karon. Ni dai naga su Aisha suna dariya ban fahinci may ya saka su yin dariyan ba muka kaita dakin da mama take na sa a kara gyarawa na ta zauna. Su kuma su Aisha na kaisu dakina can muke tare da su sosai nake bata kulawa don sai jikin ya kara mata sauki zasu koma da ita kano. Yadda nake bata kulawa mutum zai dauka tankar itace ta haife ni don sai abinda ran ta ke so za, a dafa mata. Tai kyau ta murje ba zakace aiki akai mata ba na kula da take take Raliya gamay da zaman hajiya a wurina, ranan dai naji hajiyan nata fada tana fadin haka kawai da aikina zanje na zauna yunwa ya kashe ni a banza. A wurin su Aisha nake jin wai wancan zuwan da tayi ba karamin kwasa sukayi ba ashe da Raliyan da ita, , , , ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , 99 Nidai naji yace dani zasu shiga asibiti da yar wurin Raliya ba kawo komai a raina ba yace ina zasu ga likitan yara da ya kware nai mashi kwantace suka tafi. Sai da yamma ne na shirya na shiga tare da Aisha da Amira da mama mun samay ta zaune a falo suna ganin mu naga ana rufe jikin yarinyar. Munyi masu barka suma sukai muna an dawo lafiya na mika mata abin da zan basu bamu zauna ba muka fito. Muna shiga wurin mu mamake cewa dani anya Rahama yar nan da aka haifa kuwa tana da lafiya don naga kamar ba lafiyayya bace dai. Amira kewa mama dariya tace ke yaushe har kika ganta yar dake rufe tace na ko ganta sai dai gaskiya ban zaton tana da lafiya. Zulfa ta shigo take cewa naga kun shiga gun Raliya sai kukaga ya wata halitta kuma can ko ? Da sauri nace ai bamu ga yar ha ma tace aiba lafiya tazo bama wanda yasa ai zata rayu haka nan dai take fada muna wai yar kamar aljjanna take idanuwan ta a kafe sun firfito ke bata dai da dadin gani wallahi yar sau daya naganta ban sake ba ai. Addua mukai mata tace itama hindatu yarinyar ai har yanzu sai a hankali don haka take kamar wata kala can. Bayan fitan ta ne mama kecewa yaran yanzu dai kan wai ace kina da ciki amma kike gulman wasu bata ko tsoro ita. A wurin daddy nake jin abinda Raliya din ta haifa yarinyar dai ba lafiya gaskiya ina fadawa mama tace wa ya sani mako wurin shige shige ta rokota haka don dai kawai ta haihu itama a gidan. Ai haka mata ke tabka irin wanan shirmay wurin neman haihuwa ba a tsayawa a dogara ga Allah a gani. Take bamu labarin wai wasu idan sun tafi gun maimagani rokon haihuwa sukance su dai a roka masu ko wani iri ne su dai su haihu din kawai. Dole Raliya ta shirya zata tafi kano don neman maganin gargajiya akan yar nata zulfa tace za, a je dai nema wa miji a fake ga yarinya kawai. Daddy yayi kudi sosai ya bun kasa yanzu Aisha ta samu wani dan Zaria shi zata aura haka ma Amira wani dan bauchi ne ke neman ta likita ne shi a wurina ya ganta ranan da muka shiga asibiti da ita. Ban dade da dawowa ba na samu takardan zuwa karin karatu a india na wata shidda don haka nake zullumin zuwa na bar yaran a gida. Don babu wata wacce zata zauna min da su a cikin kishiyoyina da zuciya daya hakana dole Attu da mama ne zasu zauna min da yaran har na dawo inda zan tafi da Aisha da helen can. Wata daya na juya na koma abinda zai fitar dani don da na dawo zan samu na zama conzaltor na lafiya ke nan. Mun tafi bamu dade babe ranan muna waya da Zulfa take fada min dan wurin Raliya yanzu ya zama masu kaya a gidan don ya taushe hanif yana son lalata rayuwan yaron. Hankalina yai matukar dagawa dole na bar abinda nakeyi nazo na kwashe yara na zuwa gida na dake quarter's har na dawo shine min kwanciyan hankalina. Daddy ya yai fadan haka na bashi hakkuri tare da fada mai hujjana nayin hakan ya yarda ba don yaso ba. Ban tsaya ba na juya na koma bayan komai ya kammala anan na barsu suna cin kansu na tafi yadda nayi bai masu dadi ba babu yadda zasuyi dani. Sai da na kai wata tara a can na dawo dawowana aka hada min waliman murna dawowana da ci gabana daddy yai min kokari sosai. Haka ya jawo tashin hankali gun iyalin shi wai shi ne ya kashe min duk abinda akayi ga waliman don irin yadda sukaga ya tsaru . Wanda nina san ba komai bane sai hassadan ci gaban da suka ga na samu kawai ne ya jawo hakan a gare su. Ni banda abin cewa sai dai na godewa Allah ga irin rayuwan ci gaban dana samu wanda ban taba zaton shi ba a rayuwana. Na dawo da wata biyu Allah yaiwa Alhaji mahaifin daddy rasuwa muka kwasa sai kano bani ba ko yarana kagani abin sha, awane su Jinior sun girma sosai yanzu. A kano zama muke a wurin makokin na kowa da kungiyar shi kowa jin kan ta takeyi har lokavin yar Raliya na cikin halin da take sai dai bata shiga da ita cikin mutane ne kawai. Sadaka nazo dashi mai yawa da nake bawa mutane irin buta da tasbaha masu kyau da tsada sai carpet din sallah. Sai kuma ga shi ana gulma wai na mayar da abin bidia sai da wata malama take cewa duk abinda tabada ai na amfani ne don duk wanda yai amfani dashi lada zai shafi mamacin ne ai sukai shiru. A gava su daddy yake min godiyan abinda akayi nan ita Raliya ke fadin kana nufin mu da mukazo muka zauna baka gode ba ke nan ko ? Yace wanan kuma maganan ki ne ai ni dai sadakan da ta bayar na abin amfani yakai ga mahaifina nakewa magana yanzu. Ta bayar ko ka bayar sau ka fadawa wanda bai san komai ba anan duk banbancin da kake gwadawa sai kai tayi tunda bazaka iya bari ba ya zama ma hali. Ba yau na na sani duk abinda zai haska Rahama a udon duniya muko muyi baki shine gurin ka ko yaushe. Hindatu tace niko a nan banga wani abin fitina ba don ya fadi haka don kowa yasan halin kowa a cikin mu ba wanda aka hana yi sai dai in ba kaso ba. Ko yanzu ai bai baci ba zaki iya kaiwa massalatai a bada ai tunda itama da ta raba ba ita da hannun ta take bawa mutane ba kuma kin gani da idon ki ai. Hindatu idan ina magana bana son ana min saurin katsewa tace may ye na katsewa a nan tunda nima zancen ki ya shafe ni ai. Fada ya kaure masu a wurin sai gori ya tashi tace ni nasan rayuwa na kike nema Raliya tunda kika iya sani haihuwa dole a zaton ki cikin zai zube ban haifa ba ko ? Tace wanzan ai don anmaki ranawa ne don kema haka kokaiwa wata ai ko kina nufin ban san yadda kikaiwa zulfa ba a baya. Daddy yace lalai abin naku akwai samun wuri sosai don kunyi ban dauki mataki ba har kukewa junan ku fade haka. Hindatu tace ita Zulfan ra fada maki hakan zulfa tace ai gata idan mun taba wani zance makamancin haka May ma zai kaini wana magana tunda ta hannun damarki ne sai Raliya take cewa baki fada min may ba munafuka ko Rahaman da kuke tare kin barta ne halan. Ina nan kwanaki kike cewa ta baki maganin daukan ciki don kyeta kika bata na haihuwa diya mace. Murmushi nayi daga inda nake zaune sai dai ban yi magana ba don nasan ba wanda yasan zancen na bata magani ko shi maigidan. Tace munafuka bake kika kawo zancen wai maza take haihuwa shiyasa yaya ke son ta ba haka nace anya ba hakana bane itama tana son diya mace sosai gashi ni dake son namiji da tavan magani sai na haifi mace. Daddy yace yanzu dai na gane komai a nan ita Rahama dai itace mai hakkuri a cikin ku don har yau ba a wanan zaman kaji ance ga zancen Rahama ga dayan ku. Haka kuma lalurar ku zai zo tayi tsaye akai yana cikin fadin maganan ne aka shigowa Raliya da yar nata da take muna boyen ta kada mu ganta. Kanta yai kato ga idanuwan ta a waje saboda nauyin kan ta daya rinjayi jikin ta da komai. Fada take tana kokarin bawa yarta nono tana boye ta na mike daga inda nake zaune zuwa wurin ta tsam na dauki yar daga hannun ta na shiga dubata a hankali. Sai duk suka bini da kallo auna girman kan nakeyi na duba yarinyar da kyau nace surgyry za aiwa kan yarinyar nan daddy. Yace kina ganin haka zai yuyu kuwa nace may zai hana tace aiga uwarta nan idan ta amince sai take cewa wallahi bazan yarda ba wa zakiwa bakin ciki don kinji zai fita damu waje zaki kawo wanan issue din yanzu. Nace to Allah ya baki hakkuri ni kinga tafiya na ma na juya inda sauran suke nace na barku lafiya Allah ya sauwaka. Sai naji daddy yace na dama kin amince don wanan abar ba inda zan kaiku na fada maki. Nan sukai ta jidali kuma yace ai tunda ga sauki ya samu har gida tace bata so sai waje to ki zauna da ita hakana kina kallo. Sunyi fada sosai washe gari nikan na shirya na bar garin don zan tafi sokoto wani aiki a can da mun koma. Wasa wasa sai da suka share sati uku suka dawo duk lokacin ina sokoto kebbi zamfara muna aiki dasu. Na dawo garin a jike dan irin wanan fitan ba karamin alheri muke dawowa dashi ba idan munyi shi. Tsaraba sosai nazo masu dashi naba kowa dake gidan ban bari na dauki loiaci ba dama ina shayar dasu yan biyu na don sunyi saurin samun kafa sosai yara sun taso gwanin ban sha, awa dasu. Daki na shige nai barci sai biyar na yamma na tashi nai wanka nai sallah dana gama na dauko abinci don naci. Ranan nice zan yi girki har su Aisha sun kammala min komai ko gyaran wurin daddy nayi da yan wasu aiyuka. Na fito daga part din ina zama falona yara suka rufe ni kowa da irin korafin da yazo dashi ina biye masu nan daddy ya samay ni dasu yake min sannu da zuwa. Mun gaisa ne yake tambayana sokoto nan nake bashi labarin yanayin wurin da yadda aiki ya kaya muna a can da muka tafi. Amira ce take fadin wai idan zan koma tana son ta bini taga yabayin garin itama nake cewa zafi ko zai kusa karki ai don weather su akwai zafi sosai . Nan nake fada masu in two weeks zan tafi ibadan akwai wani seminer da zamuyi a can na kwana ukku ne kawai zamuyi. Daddy yake cewa shifa gaskiya wanan yawon nawa ya fara isar shi a rayuwa nace nima va da son raina ai nake barin yarana haka ba na tafi aikine ya zo da haka . Da sannu komai ke tafiya har tafiyan nawa yazo na samay shi don na tuna mai da zancen sai ga Raliya tashigo falon taji yaja fada akan tafiyan nawa. Aikin kan tunda kana auren likita mace ai sai kai hakkuri don mijin likita dama da hakkuri aka san shi ai tunda aikin su ba tsarin addini a cikin sa. Allah ko hakane ashe kike daukana ban san addini ba shiyasa nagan ki malama ai ke Raliya ban son shigan tsugula ke take aure ko ni da zaki zo min da wanan magana haka ke naki aikin tsari gare shi kullun cikin rikici ga yaudara ba gunma wanan na taimakon al, umma ba da irin aikin ku. Jin amsan da daddy ya bata yasa na yi shiru na barshi yai mata tas yana fadin shi bai son abin musgunawa mutum ina ruwan ta da zancen mu Nai tafiya na tare da Aisha da yara na daga can muka shiga lagos nai masu sayayya sosai na aure muka dawo gida. Washegarin dawowan mu ne muna falo zaune da yara sai ga helen ta shigo tana kuka nake tambayan da ke lafiya may ya faru ne wai ? Ta ce mummy wanan yaron ne ina shanya kaya ya rungumay ni haka ma ranan ya taba min nono na nace wake nan da karfi tace Ahmad. Mikewa nayi tana gaba ina bayan ta har inda yake zaune daga shi sai singlet a jikin shi da gani ma shaye shayen shi yayi a lokacin. Ina zuwa ban tsaya jiran komai ba na kwashe shi da mari zaiyi magana na sake azamai wani marin a tsakiyan fuskan shi yace akan wana yar kafiran zaki mare ni. Nace ashe kasan kafira ce kake son kyeta mata hadi to bari kaji akan wannan matsalan sai nasa an daure min kai a garin nan idan halinka ne kuma ka sake yin hakan. Na juya na barshi a wurin tsaye yana mamakina ban dade da zama ba sai ga uwarshi ta shigo har part dina da fada akan kafira zan mara mata da ita bazata yarda da wannan ba. Raliya ban taba sanin ke kamar dabba kike ba ashe sai yau keda zaki tayani mu yake shi a kan wanan dabiar banzan zaki zo har kina fada akan na dauki mataki kan shi. To ki sani helen zaman amana take a wurina ke koba helen ma yaiwa haka ba naji irin matakin da zan dauka ga dan banza ke nan mara tarbiya. Ashe kece mai daure mai yana lalata yaran mutane tunda har kika iya zuwa fadan na mare shi yanzu. Idan kuma kika kawo min rashin hankali yanzu zanyi maganin shi a gidan nan ha sai anjima ba ma. Fada sosai mukayi da ita ranan abinda ban taba tsayawa yi da wata ba a gidan ke nan irin haka bayan fitan ta ne daddy ya dawo tun a waje Nasir ya tare shi yana fada mai abinda ya faru tsakanin mu. A hasale ya shigo gidan wurina ya nufo yana fadin may ya kawo fitina a gidan nan ? Shiru nayi don har lokacin raina a bace yake yace bake nake tambaya ba ne kin kyale ni da kyat na bude bakina nake cewa dashi. A kan Ahmad ne yake son ketawa helen shine ya kawo fadan don uwar shi ta nuna bata yarda da matakin dana daukarwa dan taba tunda ba gida na bane haka kuma ba gidan uban helen bane. Yana jin haka ya juya a fusace sai part din Raliya tana zaune falonta tare da yaran ta shi ko Ahmad yana zaune daga shi sai singlet a jikin shi a haka ya wuni tun rana kamar wani dan iska uwar bata kwabe shi ba da zama hakan. Ya juya a wurin yaron yace kai gobe idan Allah ya kaimu ka shirya ka koma gidan uban ka ba zan zauna da kai haka a gidana ba fitinar yau daban na gobe daban. Har ta fara tafiya ya juyo tare da cewa kaji na fada ma gobe kada na samay ka a gidan nan zan fadawa masu gadi da kada su bari ka shigo min gida again. Ya fara tafiya Raliya ke cewa ai wanan ba adalci bane ka dawo an fada ma karya da gaskiya sai ka hauka zauna a kai. Yace may kike son na bincika cin mutuncin da kikaiwa matana akan dan ki da baida tarbiya ko may kike son naji ? Ai dama nasan karya da gaskiya zata fada ma don kawai tana bakin ciki da zaman yara nan a gidan nan kawai. Yace cikin mata wani irin kallo amma baki da adalci ko a kan ki tunda kuke abun ku kin taba jin Rahama tai magana akan diyan ki gidan nan. Ko yanzu ma daya tabo ta ai bata fada min sai yaran da akayi a gaban sune suke fasa min ita bata ce dani komai ba. Ya juya yana jin tana fadin ba inda zaitafi tun da ba a gurin uban shi yake ba inda nake nan zai zauna. Yaron yace ni mama ban san may yasa wanan mijin naki yake min haka ba nifa zan ma daina gaidashi ne wallahi. Tace rufa min baki mara kunya kawai ai duk kaika jawo wanan tsiyar ka sani sarai daga shi har Rahama ba su da wasa a kan yaran su. May ya kaika ga yaran ta kasan yadda ta zamawa kowa kamar ciwon ido daga ita har yaran ta a gidan nan. Mama kan yar kahiran nan ne fa ta mareni for god sake wallahi wallahi idan ta sake sai nayi maganin ta a gidan nan . Kada ka soma wallahi don Rahama da kake ganin ta nan tafika bura uba wallahi sannan kuma kana ganin ta nan tasan kanta fiye da tsanmanin ka. Aikin ta yasa tasan mutane fiye da yadda kake zato don dai bata da yawan hayaniya ne sai idan an tabe ta. Smma tafi min wa yan nan munafukan ko dazun na daiyi fada ne kawai amma ba wai gaskiya ne da kaiba ko nice haka zan ma. Ya mike yana gunaguni yabar falon ran shi a bace a lokacin da safe naji suna rikici sosai kan barin yaron gidan. Ban so saka masu baki ba sai dai sam bana son a samu matsala a saboda ni tare muka shiga da su Zulfa da kyat muka samu daddy ya hakkura da zancen. Sai dai ban fadawa kowa manufa na ba naja bakina nai shiru haka rayuwan yaci gaba kowa na harkan gaban shi ba mai yarda da wani kowa tashi ta fisheshi akeyi. Bayan kamar wata uku da case din mu da Raliya sai ga wani sabon rikici kuma wai yaron ya shiga wurin yar aikin hindatu kuma again. Wanan karon kan tsaye daddy yayi sai da yaga yaron ya kwashe ya bar gidan haka ya kawo tashin hankali sosai a tsakanin su da uwarshi. Har yakai daddy ya furta ya saki Raliya ba karamin tashin hankali ta shiga ba don a zaton ta irin asirin da takeyi ba zai iya taba furta kalma haka ba a gare ta. Barin ta gidan ya dan kawo kwanciyan hankali don baka jin wani hayaniya ya auku kuma kowa na kokarin hade kishin shi a tsakanin mu. Haka yasa har yaran suka dan fara samun kwanciyan hankali ranan aka aiko yar wurin Raliya din ta rasu ba wanda yaje mata gaisuwa daga cikin mu. Ni ban ma da lokaci don haka ban damu da abinda akeyi a gidan ba hindatuce taso tayar da halinta itama daddy yasa mata waigi dole ta daina ta zauna lafiya da kowa. Sallah muka tafi kano gaba dayan mu can ma mun samu anyi muna gyaran gida yadda ya dace gyaran yayi kyau sosai. Na roki daddy don ya barni nayi sati daya a kauyen mu amma ya hana kwana uku kacal ya bani haka naje nayisu na dawo kwanan mu shida kano muka dawo Abuja ni da yara don Nasir zai zana jerabawa shi na karshe a jamia. Ga zancen auren Aisha dake gabatowa duk abin ya rikice min akaina yanzu duk da nasan cewa banda wani matsala sosai don dai sai dai nace Alhamdullahi don Allah ya buda min sosai yanzu. Ban san yaya akayi gulma ya shiga tsakanin zulfa da hindatu kan auren da zanwa Aisha har suka samu daddy don jin idan shi yayi kayan dakin da naiwa Aisha din. Bai basu amsa ba sai da yai wani tafiya ya dawone ya tara mu yake cewa dama don tafiyan dake a gabana yasa ban baku amsa ba a kwana ki. Falon yai shiru muna saurarwn shi yace Zulfa da hindatu kunzo kun samay ni da zancen akan kaya dakin da kuke ganin Rahama na wa yar uwarta. Da sauri na dago kaina ina mamaki yace gata zaune a gaban ku sai kuji idan na bata wani gudun mawa akan bukin nan ko. Yace zargin ku akan wanan yarinyar yai yawa wallahi ina son ku sani yanzu Rahama ba yadda kuke daukan ta take ba. Ko da can baya ba damuwa tayi da kawo min korafin ta ba wai nai mata. Balle yanzu da take amsan daruruwan kudi duk wata a matsayin albashi a gare ta bata rasa komai ba a gidana na biyan bukata. Kuna gani yadda sauran ma,aikata suke fifita kan su a gidajen su da sauran abokan zaman su. Amma ni ina mamakin ku yadda duk hankalin ku ya gushe ajan abu daya ko yaushe ni dai a sanina Rahama ba mace bace dake zama tana min korafi a kan ku duk da tasa cewa ina taimaka maku lokuta da dama takuma sani amma batai min korafin yin hakan gare ku. May yasa ku baku daurewa ne daganin tana abu baku zargini ba ko ita alhalin kun san tana da hanya yiwa kan ta abu a rayuwan ta. Yadda take da hali ai muma muna dashi ba sai ka tara mu kai muna tozarci ba inji hindatu ita ko Zulfa cewa tayi. Magana mukai maka ba don komai ba sai don bi namu hakkin akan hakan don muma muna da yan uwa ai. Yace wani ya hana ku jawo su a jikin ku yadda ita take jawo nata take zama dasu har suke samun karuwa irin haka don duk yaron da ya zauna a wurina dole ne yana karkashina na taimaka mai idan harkan shi ya tashi balle Aisha data kwashi shekaru a wuri na bata da gajiya da dawainiya damu ba. Take dai dawainiya da wacce take wurin ta ko inji hindatu yace idan tayi da yarana kamar dani tayi ai. Daddy don Allah abar wanan zancen haka ba zargi sukeyi ba to abarwa Allah don shi yasan komai don haka ni ban da lokacin irin wanan maganan haka. Mikewa nayi daddy yace dani koma ki zauna na koma ba mussu na zauna ina sauraren shi yake cewa damu. Wanan halin ya isheni haka wai ku yaushe ne zaku san kun girma ku dai na haka a tsakanin ku kullun hali daya. Yau ma ace nine ke wannan abin may ye na damuwa a cikin sa balle in dai Rahama ce bata da rayuwan yawan roko na ko yi min ko yaushe na fada maku. Ana zaton girma yazo maku zaku daina abubuwa amma abu sai karuwa yake maku haka to ku sani hakan ya isheni kada ku mai dani karamin mutum ko yaushe. Duk wacce ta karamin wanan halin ta kuka da kan ta don ni ban son yawan zargi nan yana bata min rai sosai wallahi. Zulfa ce ta iya cewa dashi anyi kuskure za a gyara nake cewa dashi Allah ya kyauta namike na basu wuri raina a bace. Watau ita dai kishiya ba yarda ko amana a tsakani ke nan ji Zulfa da wasu abubuwa ta sani ba wai bata sani ba amma kuma ta lalaba ta je yi min haka. Da badon shi halin shi ke nan fafin magana a gaban maishi ba da ba zan taba jun tana min zagon kasa ba haka. Ina mamaki kasan halin mutum amma kuma sun kasa daina wanan rayuwan na zargi kullun. Mama Altine da nadawo raina a bace nake fada mata tai murmushi take cewa haba Rahama ai ba kan ki ne farau din haka ba dama duk gidan da ake zaune da mace tafi daya in daya tafi samun yalwa sai zargi irin na hassada ya shigo . Kedai kibi kowa da zuciya daya don Allah ya tsare ki da ga duk wani sherin da za ayi kokarin kulla maki. Amma da ace kin biye masu kema kina wanan halin da duk kun zama daya sai gidan har yaran ku su tashi babu tarbiya a cikin ku su ma kowa yana bakin ciki da hassadan dan uwa shi. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 100 Sosai nake ba hajiya kulawa akan rashin lafiyan ta, duk abinda take son shi take ci a wuri na har ma da wanda bata ce ba din. Na kan fita dasu Aisha da Fatima su zaga gari nakan masu sayyana abubuwan da suka gani suke bukata. Haka yasa suka samu daman tara kaya masu yawa daga wurina wanda hakan yai masu dadi sosai. Suna zaune a dakin da hajiyan suke da mama sai shirin kayan su sukeyi don zasu koma saboda jikin hajiya da yai sauki sosai yanzu satin su uku a tare da mu Alhajin daddy ya matsa sai su dawo gida hakana ta karasa jinya a can dakin ta. Hajiya ta kalli kayan tare da mamakin yadda suka saye su haka su da sukazo suna kukan basu da kudi a hannun su, amma sai taga sai kaya suke ta faman shiryawa haka a gaban ta. Tace dasu wai wanan kayan fa haka duk a ina kuka samay shi ne wai haka da yawa kuda kuke kukan baku da kudi muna fukakai kawai ? Lah hajiya wanan kayan fa bada kudin mu muka saya ba duk Rahamace ta saya muna su kin gan su. Ku dai fadi gaskiya dai amma duk wanan kayan haka ace wai saya maku shi akayi don kun mayar dani bi can ko ? Wallahi Allah hajiya duk fitan da muke Rahama ce take saya muna su haka kin ga ma wanan da zan hada yanzu naki ne ai. Nawa fa ta tambaya a cikin mamaki take cewa kai wanan yarinyar ashe haka take dama rashin sani ne ya saka ashe nake mata wani fahinta. Daga inda mama Altine take zaune tace ai Rahama halin ta sai hamdalla don yarinya ce da tasan darajan dan uwa da gujewa bacin ra duk wani wanda suke a tare dashi. Haka dai nake gani yanzu dan zaman nan da nayi da ita don ko da ace yar da na haifa ne da cikina take a wannan matsayin to iya abinda zata min a rayuwana ke nan. Suna kan maganan na shigo dauke da tire din da nai masu miyar bindin shanu a cikin sa sai bread dana hado masu dashi suci dashi. Da kyat na aje tire din abincin na kai zaune hajitab ke fadin may kuma aka kawo muna bayan wanda muka karya dashi dazun kuma ? Aisha ce ta kai hannu tana bude kulan a take sai kamshi ta gauraye dakin tace baki dai gajiya yar nan wai kullan a cikin dawai niya haka. Nace hajiya iyakata dafawa mai sayowa ne ai da dawai niyar don shi bai wasa da kayan abincin a gidan shi. Allah sarki yar nan haka nake son ji idan mutum nayi a sani ba kamar wancan zaman da mukayi ba kwanaki yunwa yaso kashe ni ban ma san abinda ya zaunar da yar banzan yarinyar nan Farida ba a gunta ni na dawo rakiyan wanan yar Raliya ai tuni. Sai Aisha tace yau kuma hajiya tace bari yarinyar nan taso halakani wallahi wai shine har take fushi yanzu don naki zama a gunta sai Aisha din tace ashe kin fahince ta hajiya bakiga ko shigowa batayi dubaki ba sai taga dama. Ni Zulfa ce ma ta ban sha, awa inji Fatima yadda ta gane gaskiya suke zaman su lafiya haka gwanin ban sha, awa. Yadai fi mata ai may ye amfanin zama cikin bakin kishi da fitina ko yaushe tunda ba wanda ya aje wani. Dama gaskiya ne basu so ai inji mama Altine tace mutum ya zauna ya dinga bata dan uwan shi gaun mutane don shi yai farin jini kawai sun manta cewa haline ke nuna ka shi a zahiri. Gashi ko ai gaskiyan tayi halin ta tunda dai su bazasu iya wanan kulawan da ita Rahama keyi ba ai. Ai ke dai bari wallahi tun wancan zuwan na rege halin su don na fahinci son kai na tsiya a gun Raliya sai dai kiga yaranta nacin abu muko ta saka yan aikin ta suyi muna kwababen miya muci cikin mu ya burkuce muna. Dariya suka saka ma hajiyan tace don haku san irin halin da na shiga bane a zamana dasu wancan karo ita wanan hindatun ma aiko kallo ba isheta ba don bata da kunya idan an kawo muna kuma ta zauna ta cinye. Mikewa nayi don jinior dake ta kwada min kira ina fita muka ci karo da daddy a falon mu ya shigo wurin mu yana ganin na fa jinior na fadin mummy abamu abinci muci wanan da kikaiwa su hajiya yanzu zamuci Duk yan uwanka bazasu zubama ba sai ta zuba ma da kan ta baka ganin tana fama da nauyin dan uwanka ne a jikin ta. Da sauri yaron ya dago kai yana kallona sai dai ya kasa fahintar maganan uban nashi yace Daddy ai Abdul da su Haidar duk suna can suna kallo tare ma zamuci dasu. Uban yace mummy bata sanar da kai zuwan sabon babyn din ku bane nace kai daddy wanan fallasan kuma fa haka ? Shi Jinior may zai gane ga yaron a tsaye ya tsura min ido yace mummy wai da gaske muma za mu samu baby ga ihisan ko yaushe tana muna sallo wai in mummy ta ta haihu bazamu dauki kanin ta ba itama. Kyaleta kafin ta dauki nasu kai zaka fara daukan naku kaji kai zakai mata sallon ai ba ita ba. Ni dai naja kafana da kyat na barsu a wurin suna shirmay su na fito dauke da tire din dana zubo miya a plate's nace yaron ya karba yakaiwa yan uwan shi ta dawo na basu bread. Aiko yana shiga sai gashi da yan uwan shi da murnan su wai mummy kema zaki haihu harda Nasir a bayan su nace ku tambayi daddy shi daya fada mashi ai. Da ido ya nunawa Nasir ne sai ko yaran suka dauki ihu murmushi nayi nace kai daddy baka barin dai a zauna lafiya yanzu na shiga ukku da damuwar Jinior wallahi. Yai murmushi yana cewa wayon da kikai min a baya kikai min surprise kike son yiwa yara ki ma yanzu ko ? Daddy wayon may kuma can dan Allah dai ? Kafin ya magana sai ga Zulfa dake barci ta fito tana cewa wai ihun may yaran nan keyi haka ne wai ? Nace su da daddy sune suka abin su jinior yace da ita daddy ya fada muna mummy mu zata haifa muna babby muma. Kallon daddy tayi tace har kuma da yara ake irin wanan maganan kuma yake cewa wani irin magana ke nan fa ? Tace Allah dai ya taimaka kowa na dashi da mutum ya ga takaici take ranshi ya haci yace da ita may kuma ya kawo wanan magana haka ? Fadawa yaran shine kuma abin bacin rai ko may da har zaki fadi hakan ? Tace nikan kada ka lake min barni naji da abinda ke damuna yace ashe keda na fadawa su baby ranan haushi nags kinji ba dadi ba ? Wai may yasa ku baku kunyan fadin magana akan kishi tace kajika kuma zaka wani daure ni daga agana nace don Allah dai ku bar wanan zancen haka ba kyau mana a gaban yara kuma ? Mikewa yayi ya shiga dakin su hajiya ya barmu a wurin nima ban tsaya ba na shiga dakina kwantawa nayi don na huta barci ya fara dauka na sai gata tashigo dakin . Take cewa dani kin kwanta ne ashe nace eh batare dana dago ba ta samu wuri ta zauna daga gefe na tana fadin. Watau na miji dan hadin fada ne Rahama daga fadin magana sai ya juya min magana na kawai nace humm m anty don Allah dai mu bar zancen jan don babu yaro a cikin mu ai. Abinda dama nake son magana ke nan don naga ranki ya baci sai lokacin na dago ina cewa da ita raina ya baci kan wanan maganan da ba yau aka fara irin shi ba a gidan nan. Ni dai nasan da zuciya daya nake zaune da kowan ku a gidan nan bance ban kishi ba amma dai ba irin wanda kuke gwada min ba haka wanan maganan banga abin kishi a cikin sa ba don kowa na dauke da wannan abin a jikin shi. Allah na tuba ma ciki har abin tsayawa wani kishine a kansa ayan kayan wahalan dake ajikin mutum kawai. Tace to don Allah kiyi hakkuri ni dai bada wani manufa na fadi magana ta ba don dai naga yara ne kawai nace nifa ban dauke shi wani abu ba can anty. Tace na sani amma dai naga ai ranki ya baci ga maganan nace dole ne don bana jin dadin irin yadda ake gwada min tun dai ke anty duk fa zaman abu daya muke gaba daya a gidan nan. Halin maza kuma kowan mu ya san yadda yake yau a kan kane gobe ga wata to may ye abin jin haushi a cikin sa kuma. Aisha data shigo ta samay mu take cewa kai kuna nan ashe har dakin ki nake ai bakya ciki sai yara dake kallo kawai. Mun zauna da Aisha sai ga Fatima hira mukayi dasu sosai har muka manta da halin da muke a ciki nan cikin hiran nake fahintar wasu magana akan Zulfa din a baya gata ashe gwanace sosai wurin shan kayan mata yadda suke hira da Aisha suna kyalkyalan dariya. ********* ********* ********* Waahegari su hajiya da yaran ta suka shirya komawa gida nan dan yai mata sha tara na arziki inda shi da kan shine zai mayar da uwar har gida harda mota sabuwa ya saya masu ita da mahaifin shi. Sun tafi a cikin dadin rai duk muna tsaye a kofa munyi masu rakiya gaba dayan mu gidan in ka debe yaran Raliya da suka ki fitowa raka su kawai. Suna dagawa sai Raliya tace munafunci dai baiyi ba wallahi ra juya zata fara tafiya sai Zulfa tace waye muna fukin yanzu a nan ke nan ? Ta juyo tana cewa da ita wanda duk ya damu dashi nakeyi aiko nan fada ya barke a tsakanin su Hindatu tace da ita wanan maganan da kikayi ai dole ne a tambaye ki ko. Tace kai nifa duk wanda ya saya na sayar mashi waye ba munafukin ba ko waye bai san munafuncin da akayi ba anan. Duk dai tsiyan mutum sai ya ganni a gidan nan kuma na aje yadda kowa ya aje nashi sai dai a mutu da haushin kura. Don ta Allah bata mutum ba an dauka ko mutum juya ne duk bakin ciki da hassadan da ake min kallon kowa nake wallahi. Yanzu ai sai kiyi da wanda kika gani Juya a cikin mu ko don Allah ya raba gardaman shi ko a nan saukin abin yaba kowa ba maiwa wani gori kuma . Kai fadan nasu yai tsanani har takai zasu fara dangwaran junan su nace haba haba maman Ihisan kin manta da halin da kike cikine kada kiyi soma motsa jikin ki haka zaki iya samun matala yanzu kuwa. Da sauri hindatun ta dan juyo ta kalle ni tace kedai fa dama ko yakai wa kowa ko ina zan biyewa wanan yar kakagidan mu lalace tare ta baya taji an shako mata wuya sai ko kokuwa ya kaure tsakanin su sosai ikon Allah. Ni da nafisu watan ni ne na samu na raba fadan aiko sai ga jini ya balle wa hindatun take a wurin nan kuma muka shiga wani sabon fitina. Yadda nake da haka na gigice nasa su Amira suka kama min ita zuwa mota don ita Raliya ma bata tsaya kan ta ba mun isa asibiti da ita duk wani abinda ya dace muke mata. Da kyat da sudin goshi na samu cikin ya tsaya amma mun yanke cewa idan bai tsaya ba zamu cire mata baby din don anyi scaning mace ce a cikin ta. Ina kan ta har garin Allah ya waye har isowar daddy da iyayyen ta muka dora da su daga karshe dai dole zamu cire cikin don lafiyan shi da nata ita uwar. Nai mata aiki na fitar da yar baby da bata kosa ba muka kaita dakin adana irin su don kulawa tasha matukar wuya sosai a lokacin. Uwarta sai bina take duk ta rude tana fadin don Allah Rahama a taimaka yarinyar nan ta rayu kada ta mutu nace da ita. Mama duk abinda na sani shi mukeyi idan Allah yayi zata rayu zata rayu din don haka Allah ya rubuto mata wanan matsalan. Cikin yardan ubanginji uwar taji sauki itama yar babyn na samun kulawa sosai tana dan murmurewa a hankali Sati uku ban huta ba gashi watana na tara na batun tsaya min haka ga bakin kano na tashigowa duba jikin hindatun don an sallamota sai dai baby din dake asibiti har lokacin. Ranan ina kwance na dan samu hutu sai ga mahaifiyar hindatu har dakina take cewa nazo don Allah wai babyn nan kamar bata da lafiya da sukaje bata nono haka na daure na mike muka nufi asibitin lafiyan yarinyar kalau bayan an dubata nace mama ku kwantar da hankalin ku idan an shiga sati mai zuwa za a bamu ita mu dawo da ita gida insha Allahu. Daddy ma ya iso don an buga mai waya yake cewa don may baza a bar ni muyi aikin mu ba ba a ganin nima halin da nake ciki ne ya kamata su tausaya min hakana mana dai. Ni kaina wanan fitinan ya fara isata haka wanan haukan yai yawa a gidan nan na yau daban na gobe da ban wai kuma duk a kan kishin mutum daya ake wanan abin haka. Ina son yin transfer na koma kano da aikina na barsu nan amma basu yarda ba wai sai dai lagos ko portherqut zan iya komawa ba arewa a ciki inda zan iya komawa din yanzu. Fitinan ya isheni haka ko da yaushe a cikin tashi hankali harda batun salwantar da rayuka gashi kan wanan zancen har yau daddy baiyi wani magana ba akan zancen. Tun kowa na jiran matakin da zai dauka har akaji shi shiru ba wani magana kuma ga Raliya na girkin ta daidai da kowa lafiya lau ba wani fitina. Da haihuwa yazo min a satin da duk aka dawowa Hindatu da yarta gida satin naji haihuwa yazo min daga Amira sai Aisha da sai mama Altine na dauka muka nufi asibiti da su. Don daddy ya tafi kano duba jikin hajiyan shiko da na bar gidan duk suna barci ba wanda yasan fitina da asuba. Tara na safe na haihu lafiya sai dai nima haihuwan yazo min a bazata don dama ina zargin hakan a gare ni. Macen ta fara fitowa sai namijin da ya dan dauki lokaci ya biyo baya ta duk kan su kuma a cikin koshin lafiya sukazo duniya. Sai da komai ya kammala na kirashi ina sheda mai na haihu daddy yace what ko dai kin fadi ne nace gasu kaji kukan su ai. Yace may kike nufi nace tau ga su dai ai kaji su ko yace Rahama tagwaye kika haifa murmushi nayi kawai ban ce uffa ba dai. Tare da doctor Fati muka dawo gida nan kowa yake mamaki da haihuwan sai dai duk wacce taji biyu na haifa sai fuska ya sauya a wurin. Ba wacce bata sauya fuska ba daga cikin su ranan daddy ya dawo garin shi da mama Laraba suka shigo tare. Da farin cikin shi ya karaso dakin don gani kyautan da ubangiji yai mashi a kwance suke saman gado yayin da mama Altine take zaune bakin gadon ta mimike kafafuwan ta duka biyu ina ban daki fitowa na yai daidai da zuwan su. Sannu da zuwa nake masu amma hankalin su na kan yaran dake barci nade a cikin towel suna saboda sanyin da akeyi a lokacin. Idon daddy kyam a kaina ya kalle ni ya dubi yaran yace dani so da gaske kike Rahama tagawaye ne dauke a cikin ki ashe baki fada ba. Nace na shiga uku daddy wallahi nima ban tabbatar ba sai yau don ban taba zuwa scaning ba don in ga may zan haifa sai dai ga yana yin zaman su nakan yi hasashen hakan dama amma kuma naga ba wacce ta taba haifa ma su sai nake ganin baku da kwansu a gidan nan ai. Mama laraba tace waya fada maki shi Alhajin mahaifin shi ai haka suka fito mace da na miji ne macen ta rasu gun haihuwa ne shiyasa. Sai mama laraba tace kunga ita ma din ai ai ubanta tagwaye yake biwa maza kuma duk suna nan da ran su a akauyen su. A hankali daddy ya karasa bakin gadon ya dauki daya daga cikin su yana fadin wanan macen ne ko na mijin sai mama tace dashi namijin ne ka dauka ga macen can ai yanzu nake wa uwar sheri duk tabi ta makale mata kasan mu mata da son diya mace. Mama Laraba tace ai nima sai da na fadi nace yau yar nan ta fado a inda ake son ta Rahama da son diya mace. Addua yake baiyi magana ba sai da ya gama ya mikawa mama yaron ya dauko yarinyar yana binta da kallo. Mama Laraba tace yaran nan ai sun yankewa mahaifin su kauna ana cewa Abdul yafi kwaso uban ga wanda suka kwaso shi da tushe har da dan bakin tabon dake hannu shi sai da yaran nan suka dauko. Yana addua yana murmushi ya karasa ya rugumay yarinyar yana fadin Allah ya raya muna su a tafarkin musullunci ya sa masu albarka a rayuwan su duniya da lahira. Yace ina yaran suka shiga ne mama tace ai suna school basu dawo ba har yanzu sai sun dawo muga hauka yau kan. Hajiyan daddy ce ta kirani a waya na dauka ina saka kaya a jikina muna waya da ita take cewa sannu yar nan ashe an sauka lafiya ga Alhaji na gaida ke yace kin zama maman shi kuma yau. Murmushi nayi na kara gyara kwanciya na ina fadin hajiya a gaida min dasu Aisha munyi sallama da ita mama ke cewa dani naga kin kwanta ai da ki tashi ki dan ci wani abu hakana Rahama tun dazu fa ban da tea ban ga kin sha komai ba fa. Mama Laraba tace haka take haihuwan Haidar ai mun sha fama da Attu da ita nace kai Attu ta faye fada komai tace mutum sai ya ci shiyasa wanan karon na dauko mama bakina alaikum balle tana fama da tsufanta yanzu wani moriya zatai min kuma. Daddy da zai fita yace dani Hamza zai zo da ita ai don ban tsaya daukan ta ba amma na bar sako yazo da su. Abinda yabawa daddy mamaki shine har ya kwana ba matar da tai mai barka a cikin matan shi har ya fita yaje muna shopping ya dawo. Yana zaune da yaran shi a falon shine Zulfa ta shigo wurin su tana tambayan shi wai kayan da aka shigo dasu rabawa za, a yi ne ? Kamar yaya rabawa zakuyi har yaushe na sayowa kowa kayan amfani wanan baki ga na mai lalura bane ga tada jama, a a tare da ita. Tace dashi gani nayi har abinda babu a namu ka sayo ai yasa na tambaya yace Zulfa na sayo nafa fahince ki a harkan nan. Ke batulu ce ta karshe idan har kika bari Rahama ta fahinci ba da zuciya daya kuke zaune ba zakiji kunya ke kan ki kin sani. Tace ban gane ba yace zaki gane ai idan har kishi ya jaki kika gane cewa duk abinda kikeyi Rahama na sane dake. Amma kana bani mamaki wallahi Rahama rayuwana ne ko may ko uwata ce ko ubana yace da ita kada ki kawo min diban albarka a nan yanzu ran ki ya baci maki. Don iskancin ku ya soma isata haka na kaya dai ne nace na mai haihuwa ne ku gunta nace Sani ya kai su. Tace to shine may idan an hana muna kayan ai ba yau aka saba yi muna haka ba a gidan nan. Take ran shi ya baci yace sai ta fada mai lokacin da ya taba ba wata wani abu ita bai bata ba a gidan. Zata wuce yace dawo ai ba tafiya zakiyi ba tace gara na natafi don naga dama a jirace kake dani ai. Yace kina tafiya wallahi yau baki kwana a gidan nan ido ta fitar tana mamakin shi nan yai mata tas sai da ya gaji ya kyale ta. Barci nake a cikin barci nake jin muryan shi yana fadawa su mama zai mayar da ita kano ne dama idan yaje yana bukata wata acan don haka ra shirya ta koma kano da zaran an gama suna. Mama Laraba fada take sosai tace shine matsalan Zulfa bata da wayo wallahi na lura ko dakin nan sau daya naga ta shigo shi ashe ita da manufa take hakan. Ina jin su ban motsa ba don ni ba bakon abu bane a guna bayan fitan shi ne na tashi na kira Aisha da Amira da suke gida nace ta taimaka a gyara kayan su kai komai inda ya dace su aje. Yan barka na shigowa harda ma wanda ban zata ba sun shigo gidan ganin yaran don fari jini irin na tagwaye. Banyi mamakin rashin shigowan yaran Raliya ba don ko ita uwar sau daya ta shigo inda muke har gashi ana zancen suna yan kano sun fara cika muna gida ko. Yaran sunci sunayen Saade da daddy kowa yai mamaki kara saka sunan shi da yayi yace a haka suka zo dama naja bakina nai shiru nan sabon gulma ya tashi kuma again. Sunan yayi kyau sosai don har walima su Fati suka hada anyi rabon abubuwan daya dace sosai a wurin. Naga kishi a gun matan daddy kamar cikin nan ba kowa keda shi ba a gidan ni Zulfa tafi ban mamaki wai a haka shiri akeyi sai tazo taga abinda akayi zata koma gefe tana magana kuma. Yan uwa na sunzo min sosai don haka na kebe dasu nace mama zata zauna dani wanan karon don Attu bata zo ba. Da zasu tafi kamar yadda ya saba yi masu alheri ko yaushe wanan karon ma haka yai masu ya ba kuma Suwaiba da Rukaiyya alheri su samu sanaar yi idan sun koma gidajen su. Gida ya rage daga mu sai su mama dake zama damu din tun mama Laure na shan jinin ta har tazo ta sake jiki don komai sai ince uwata nima fa uwata a tare dani. Munyi arbain ya shirya su mama suka koma gida suma da tarin alherin su mama Altine ce dai ya hana komawa tace a nan zata zauna da mu. Sati na biyu da arban sai gashi da visaza zamu tafi umurah har yaran nawa gaba daya wanan abin ya dan kawo rikici a gidan sosai. Ba fashi muka shirya din an shiga dogon zango na hutun makaranta muka wuce ba saudiya muka fara zuwa ba sai da muka tafi Egypt don jinior ya matsa yana son zuwa yaga gawan firauna da ta gani a waya. Satin mu daya muka juyo saudiya nan muka samu wani gida mukai masauki zaka ce don mu akai gidan dama sai bayan zuwan mune na fahinci akwai aikin da shi kan shi maigidan yazo yi acan dama don baya zama a garin yana shiga wurare da dama a can don business din shi. Wasa wasa sai da muka kai wata biyu a can waya kan da fitina daddy ya sha su a gun matan shi amma ko a jikin shi bai damu ba da komai da zasu fada muna can Raliya ta haihu na dauka zamu dawo ne sai da muka share sati hudu bayan haihuwan ta muka fara shitin dawowa gida a lokacin. Dagani har yaran duk mun canza munyi kyau don itin daulan da muke a cikin sa mun dawo gida mun samu anyi wa gidan gyara na sosai don ashe bayan mu suma sai da suka koma kano a kai gyaran wuri yanzu part dina daban na Zulfa daban haka ma sauran suke. Kwanan mu biyu a kasan bamu damu da muje mu yi wa Raliya barka ba don har yaran ban tsanmani sun tafi ba. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 101 Tun daga wannan rikicin da mukayi na kara fahintar alamarin kishiya dai abin tsoro ne duk dadin ki da kishiya ki tabbatar da kin boye sirin ki na yan uwan ki dana kawayen ta a gare ki. Don da ace ni irin rayuwan Zulfa da ta shige min jiki kamar aminiyar gaskiya ke gare ni na yawa sake maganan duk wanda yazo mata a rai ba yan uwan ta ba ba iyayyen ta ba kawaye ba da miji. Da na sha matukar wahalan zama da ita don nasan dan abu kada ne zai hada mu tafito tsakar gida tai min gori a gaban wanda nai maganan shi da ita ko ta samay shi gefe tace ai Rahama tace da kai abu kaza. Amma sai Allah ya taimake ni duk zaman mu na kama bakina a gare ta bana zama ina sakin maganar kowa kamar yadda ita take zaman yi mun. Ban yi ba ma tana koma gefe tace nayi din inaga nayi mata da yawa bani ba nasan muna samun irin wanan matsalan ga irin su da son shigewa mutum a jiki kamar da gaske son ka suke tsakani da Allah. Don Allah mata mu kula kafin mu yi sauri yarda da mutum mu auna halin shi mu gane irin kalar mutumin da muke zama dashi don wata zata dade tana cuta maka amma bazaka san cewa ita bace ke cuta maka don irin su Allah ne ga baki fir,auna ga zuciya suke. Ba wata kishiya a zamanin nan da zata ce tana kaunar ka da zuciya daya dole na ciki na ciki a zuciyar ta da kai. Nima bawai bana kishin kishiyoyina bane ina yi sai dai ba can ba irin yadda su suke min din don har yarana sai na fahinci akwai hassada da bakin ciki a tsakanin su da su. Tun dai yar Sa,adene da take karama na dauki son duniya ni da uban ta mun kwallafa ma yarinyar kamar yadda fita goma zanyi sai na sayo mata wani abin don shi abin yara mata avalable ne ko yau she zaka ga lates din abin kwalliya na diya mace haka uban ma yake da yarinyar yana kiran ta da sweeting shi mu kuma muna kiran yarinyar da sweet anty. Haka yasa sai ya sayo mata abu idan anyi magana zaice saaden shi ce fa baida kamarta a duniya tare a gansu Allah ne ya hada su kuma ya raba su ba wai sun so hakan ba. Zai dauki yarinyar ya fita da ita suje yawo tare idan zasu dawo da tsarabanta yake shigo muna sai dai yaran su rufeta suna karba a gurin ta. Wata rana sun dawo shi da ita da Yusuf da wani lokaci ake labawa aje dashi idan zasi fita din tare. Yarinyar tayi barci a hanyan su na dawowa don haka suna isowa gida ya dauko ta ga kafadan shi sai dayan hannun da ya kwaso ledojin da yai masu sayayya a a cikin sa hussaini mai sunan shi yana bin su a bawa da nashi kayan wasan da aka sayo masu. A kofa sukai kicibis da zulfa da hindatu dake tsaye suna magana caaa suka bisu da idanuwa sai ita zulf ce take cewa dasu a, a anyi barci ne a hanyar yar baba ? Yar so ne ai dole ne suyi abinda suka ga dama tunda sune diyan gaban goshi kowa ba da bane a gidan nan idan ba su ba. Wani kallo ya bisu dashi sai hindatun ta sake cewa, dashi ana dai fakewa ga son matattaciya ana nuna banbanci kawai idan anyi magana ace wai wata Saade can da ta mutu babu dadin rai a tsakani. Sai yanzu ne don cin amana za a fake ga yara ana wai kiran Saade da Yusuf can don kawai a nunawa mutane banbanci a kan su. Su wa yanda ba a so din sai a kaisu a watsar inda ake watsar da yaran da ba a so mu gani shi zaifi sauki bai masu magana sai dan goga su da yayi ya wuce har ledan da ya dauko yana tokaran jikin hindatu din. Zulfa tace ai ba zai kulaki ba an riga da an shanye shi tun farko baya ganin kowa a gidan nan sai su da uwar su kawai a idon shi da zuciyar shi. Saman kujera ya shimfede yarinyar ya zauna a kusa da ita nan sauran suka rufe su ya dinga mikawa kowa ledan shi ya bada na yar wurin hindatu da bata shiga mutane yarinyar yace a mika mata nata. Sai ga Jinior ya dawo da ledan yana fadin maman ihisan tace waina dawo dashi. Daddy yace ka mayar kace nace ba nata bane na hussuna ne yaron ya juya da sauri ya koma sai da ya dan dade ya dawo yana zuwa yake cewa daddy har tace nace hussuna bata so sai kuma tace na kawo. Bai yi magana ba ya mike ya bar yaran yafita ashe gun ta ya tafi tana zaune daidai tana cin cake din da ya sayowa yarinyar yace ke may ye hujjan ki na cewa a dawo min da abinda nabawa yarinyana. Tace a cikin tsiwa ai ba ita ka sayowa ba nagani shiyasa nace a maida a bawa wanda ka sayowa din su kara. Yace you are stupid by saying that mara godiyan Allah yau din kawai da ban fita da itaba har kika tsayar dani hanya kija fada min magana haka ? Na kyale ki ne kawai don bana son yawan hayaniya a gaban yara amma duk ranan da kika kara min magana makamancin hakan zaki gane kuren ki a gidan nan ko na aikowa yaro da abu ki tsaya min iyayin tsiya zamu hadu dake a gidan nan. Ya juya a hasale ya fice daga part din ta bishi da harara kawai batare da ta kara furta wani abuba. ********** ********* ********** Tun da na dawo gidan don aikin safe nayi nake kwance ina barci ina tashi wanka na fada na fito sai ga Aisha tashigo tana cewa dani daddy ne ya aiko da kankana na gyara mashi. Nace ta bari na shirya na zo na gyara da kaina na fito na gyara na samu plate na saka tare da rufewa nakai mashi. Zaune yake falon shi yayi dadaya yana aiki na shigo da sallamana falon dauke da fruit din a plate. Ya dan dago kai yana kallona tare da amsa min sallaman nawa na samu wuri na zaune ina mashi barka da wuni. Yace likita har angama ganin hanjin an dawo gida ashe murmushi nayi tare da gyara zama na daga gefen shi inda nake nace haba daddy bamu da aiki kullun sai fanin hanji kuma ? To maye aikin naku ta fada tare da ture takardun dake gefen shi yana kokarin bude plate din dana aje mai a gaban shi na fruits din. Yace masha Allahu mai kyaune ashe mai yashi kuke kiran shi komay naji ina son irin wannan kankanan sosai wallahi. Ya dauki fork tare da yin bissimillah ya fara shan kankanan tare dace min bissimillah mana kisha mana na mika hannu tare da daukan daya nakai a bakina. Yace dama ko ina son muyi yar magana dake sai gaki nace tau tare da dan tsagaitawa ina sauraren shi inji abinda zai fada min din. Yace zancen daya da biyu ne ai na farko akan auren Aisha ne don har yau banji kince dani komai ba akan maganan kuma. Na dan rausaya kaina nake cewa dashi to daddy ni may zance dakai kuma ? To amma dai kin san nike da alhakin yiwa yarinyar nan kayan daki kamar yar dana haifa ko don yanzu haka kayan da na oda akawo masu ita da Amira inaga sati mai zuwa insha Allahu zasu shigo sai zancen bukin ban san ko maigari zai yarde min da na aurar da ita nan guri na ba kamar yata dana haifa. Nace to daddy idan haka kake bukata ai ba matsala sai na fada mai don nasan ba zai hana hakan ba ai. Yace to shike nan yanzu ina son sauran list din komai nasu don ko ita Amira din ina son komai nata ya kammala don bazata kai wani azumi ba a gidan nan gaba dayan su. Nace ubangiji ya cika muna guri na alheri yace amin tare da kara kai kankana a bakin shi yace to sai kuma magana ta biyu dana ke son nayi dake. Shine ina son wancan part din na Raliya wata zata maye gurbin dakin nan bada dadewa ba insha Allahu. Da kyat na iya karasa tauna kankanan da nakai a bakina na hade amma a fili sai na daure nace masha Allahu Allah yasa da alheri a cikin yin hakan da za ayi. Yace cikin farin ciki na gode da jin hakan daga bakin ki don har an gama komai budurwa ce yar sokoto ce kuma bana nai karo da ita. Tana jami,a a nan abujane bana zata gama sai dai ina ga a nan gidan nawa zata karasa karatun na ta insha Allahu nace Allah ya nufa daddy na sake daukan kankanan kamar ba komai a raina na kai bakina sai da muka shanye kankanan ban nuna mai komai ba nayi mashi sallama na bar falon tare da kwashe kayan da mukai amfani dashi. Ina shiga dakina na fada saman gadona tare da dafe kirjina dake wani irin harbawa nake cewa a fili ya subbahanallahi. Yar sokoto kuma ai kuma tsugunne bai kare ba ke nan gare mu ya Allah ka hau dani kan ko wacece daddy kuma zai dauko muna a cikin mu da sunan abokiyar zama. Wayana na jawo na fara lalubar nombar zarah don na sanar da ita abinda ke shirin faruwa damu kuma a gidan. Tana dauka tace doctor Rahaman yusuf rano nace rufa min asiri don Allah da wanan kirarin naki daddy kan ai ya zama abinda ya zama Zarah. Yanzu ma kiranki nayi na sheda maki wata sabuwar zancen da yazo min dashi da yamman nan ke dai. Zarah wai daddy aure zai kara kuma , . Tace au may Rahama ? Sai da nai murmushi nace wallahi aure ke dai zarah yanzu yake fada min with ful confidence ya fada min zarah. Tace ke may kikace dashi to ? Nace may zance kuwa Zarah sai addua kawai don ni abin kinga yazo min ta bazata wallahi. Na dai kwashe yadda mukayi dashi nake fada mata take cewa dani yadda kika nuna mai ba komai din a ranki yayi kyau sai dai gaskiya sai kin kara jajircewa don ko yanzu tsugunne bai kare maku ba gaskiya. Wai nima Rahama may daddy ke jin sha, awa ga tara mata haka da yakeyi a gida gashi shi ba zaman lafiya ma ke gidan nashi ba amma bai sa ya daddara ba hakana. Nace ke dai Zarah abin nashi ya zama hali irin na malam baushe a da can baya aita tara mata a gida kamar za a kaisu kurmi sayarwa. Mun dade muna magana daga karshe take cewa amma dai sauran basu da labari ko ? Nace ina ganin dani ya fara zancen don da sunji da yanzu zulfa tashigo min da maganan ai don bata kwana dashi dataji. Tace ni dai shawarana shine kiyi hakkuri don Allah Rahama kada ki yarda ki tayar da hankalin ki ko kadan akan wannan maganan please. Nace to Zarah idan banyi hakkuri ba yaya zanyi tunda ban sakawa ban hanawa tayar da hankali kuma akan may zan wahal da kaina. Ni dai fatana Allah ya hada hankulan mu dama ko wacece za a kawo muna ya hauda mu kan duk wani kaidi dake cikin zancen nan. Tace shine kawai mafita Rahama sa mai ido hakkuri baibar komai ba insha Allahu ai may gaskiya yana tare da Allah. Yo Allah na tuba ma koda tashigo ko diya goma zata haifa a gidan dole dai naku ne a gaban nata aiko. Nace yo Zarah may yai ruwa na da wani haihuwa a gidan daddy yanzu kafin na shigofa na samay shi da diyan shi dama haka kuma nima Alhamdullahi na samu nawa da Allah ya bani to har wani da za a haifa nan gaba hankalina ya tashi kuma ? To ce to ai shine nima nagani Rahama nidai ina kara baki hakkuri daki daure ki cije duk abinda za a yi naki kawai ido a gidan. Da haka har muka kai karshen maganan mu da ita na kashe wayan tare da sauke ajiyan zuciya da dan karfi ina fadin Allah gamu gareka. ********* ********* ********* Banji kowa yai maganan ba don haka tun ina daridari da zancen har na gaji na watsar da maganan na ci gaba da harkokina dake gabana na auren Aisha da ya gaba to min. Sam ban yi tunanen cewa nashi auren ya gaba to haka ba da wuri sai ranan da ya tara mu yake fada muna wai sati biyu masu zuwa ne za, a daura mashi auren shi. Ranan naga fitina a wurin matan gidan da rashin hankali ni dai ina zaune ban samu cewa uffan ba. Sai faman sake bakaken magana sukeyi a cikin bacin rai ina zaune nayi tagumi da yatsun hannuna ina sauraren su tare da binsu da kallo daya bayan daya. Sai kuma haushina ya kama su inda zulfa ke cewa dani haba dai Rahama waban maganan fa ya shafe mu baki daya amma kin ja baki kinyi shiru kina sauraren mu kuma ? Nace anty ni may zance fadan da yafi karfin mutum ai sai ido ko tunda wanan maganan da kukeyi bashi zai sa ya fasa abinda yai niyar yi a rayuwan shi ba dai. Ni magana na nan shi ne na farko ko wacece zata shigo cikin mu Allah ya bamu hakkuri da zaman lafiya a tsakanin mu. Sai magana na biyu shine ga daddy ni a ganina in har za kai irin haka daddy tunda dai Allah ya hore maka ba wai baka dashi bane balle naki fadan abinda ke raina. To gani nayi ya kamata ace ka samu wani hanya na kara kyautatawa na gida bance wai baka yi bane daddy kanayi amma kasan yadda suke fama da sana,arsu sai naga ya kamata ace ka fadada ma kowa abinda takeyi ba azo a samu mutum cikin karamin karfi ba ai batun raina mashi hankali kamar kullun. Sai duk sukai shiru suna kallona yana saurarena shi gogan yana dan kada kafan shi da tun farko haka yake yana sauraren kowan mu dama. Zulfa tace kaji magana kan yace cikin murmushi yanzu kika gane hakan da ita dake da wayo ta fada ko don naga bakin kishin tsiyar ku ya hanaku hango haka din. Sai hindatu tace dashi ba wai bakin kishi bane ai sai gaskiya ai dole ne mutum yai fada ace mutum baida aiki sai kwaso mata kala kala koda yaushe yana cika gida dasu haka. Yace wana sauke a kanki dana cika gidan ko wanace ki tayani riko daga cikin su dana dauko nace adaiyi hakkuri a tsaya a fahinci juna don maganan haka ba shine mafita ba gare mu. Yace to yanzu kun yarda da zancen da ita din ta gabatar ko kuwa don ni dai aure ba fashi a gare ni kunji na fada maku sai kowa yai shiru. Nace ai ba wanda yaki karuwa a rayuwan shi zaman lafiya dai akajawa ba adawo ko yaushe ana yar tsure ba kamar baya. Zulfa tace da kuma fake gaskiya don irin wancan zaman na zamanin Raliya ai baiyi dadi ba ga abin magana amma ba dama a maganta din. Yace to naji yanzi ina sauraren ku kowa ta fadi irin sana ar da zatayi naji ko zan iya don nasan ta inda zan fara dashi. Hindatu tafara cewa nikai ya wuce na fara shiga Dubai ina debo kaya zuwa nan kasan da sauri yace bako a gidana ba. Sai Zulfa tace aiko mutum bai fita ba yanzu akwai hanyoyin yin sana a da dama amma gaskiya nikan zaman haka ya ishe ni gaskiya. Yace cikin murmushin da a lokacin takaici yake ba kowa don gani muke ya raina muna da wayo sosai a yadda yake muna din yake nuna muna ko a jikin shi. Hindatu tace abamu mana ai mu mun san abinda zamuyi idan anbamu tunda ba zama haka zamuyi ba. Yace in har na bayar din zai kawo min kwanciyan hankali ai ba matsala don bana son yawan fitinan nan ko yaushe da kukeyi. Wanan din ma ai yatinya ce don duk kan ku kun girmay mata ga shekaru don budurwace bata taba aure ba ma. Yanzu kuma can aka koma inji hindatu yace da ita dama ina nake tace ni na sani ne tunda baka da alkibla dama kai. Murmushi yayi yace to can na koma sai zulfa tace in dai ba akwaso uwar budurai ba ai angode. Yace balle bakin ku ba zai kama mu ba don yar shar ce da ita bakin ku ya sari dutse kowan su yaja tsuki. Yace yanzu dai ku bani nan da kwana biyu zan nemay ku kuji shawaran da na yanke ga bukatan ku don yanzu kwanaki basufi goma ba a daura aure har tarewan ta gidan. Shiru falon yayi kowa da irin nazarin da take a zuciyar ta kan zancen don kowan mu ya kai wuya ko saukin mu dan bukatan da na gabatar kuma ya yarda dashi din. Jin shirun yai yawa yasa nace dashi an gama ke nan muna iya tafiya ko yake cewa dani idan babu komai zaku iya tafiya ai. Wuf namike na bar falon ina shiga ban zauna da yara ba na shiga wanka ina fitowa sai gashi part din nawa. Ina dago kai don naga waya shigo min daki haka sai mukai ido biyu dashi yana saye da wando fari da riga polo fara mai dan rubutu a gaba daidai wurin aljihun rigar. Yace wanka akafito ashe nace eh naso fita ne zuwa kwaso yara daga islamiya dama yace bar su zan kwasosu idan zan dawo yanzu zan dan fita nace ok nama huta ke nan ashe. Sai dai daddy naso shiga gida kano kafin aure nan naka don kaga sati biyu ne tsakanin ka dana Aisha don nakaita tai sallama da mutane. Yace No ba yanzu ba babu wacce zata tafi ko ina a yanzu ita Aishan ba sai a hada ta da driver ya kaita ba idan ta gama hamza ya ddawo da ita. Cikin rshin damuwa nace Allah ya kaimu idan ta shirya zan fada ma sai a kaita din yace is ok. Ya juya ya fice daga dakin dakin na bishi da kallon mamaki a raina na fahinci wani abu kodai daddy yana zargin zuwa na gida zai iya haifar da wani abune ga auren shi din ? Shima a bangaren shi ya fita yana mamakin irin saukin kai nawa haka don yasan da watace ya hana wanan tafiyan cikin irin wanan yanayin ba karamin fitina za ayi ba yau dashi. Amma sai yaji sabanin hakan ban kuma nuna wani damuwa ba ko a raina ga kuma mamakin kan karuwan yan uwan zama da na gabatar mai wanda su haukan su bai bari sukai ga wanan irin tunanen ba a kan su. Duk da yasan wai ba nayi haka bane don wani bukatana ko wani abu a gareshi na daiyi ne don nasu karuwan kawai. Bayan kwana biyu kamar yadda yace sai gashi ya tara mu ya ba kowan mu envlop dauke da check din kudin har miliyan daya da rabi ko wan mu. Nace ni harda ni nima yace ke dabance a cikin su nace ba hakana bane gani nayi dai ni ina da abinyi ai sune suke da bukata fiye dani. Sai Hindatu take cewa dani ai yasan kina dashi ya kara maki ra ayin shine yin hakan da yayi kawai. Mukai godiya na ce zan je nabawa baba magani don baya jin dadi kada yai barci na barsu a nan ashe baya na an kwasa dashi kan don may zai kara min karfi baya ya barni ina aiki yace ya fahinta ya kara masu ya cika masu bibiyu. Ina dawo daki nake fadawa Aisha zancen tafiya tace dani a, a anty yaya zan tafi na barki a cikin wanan yanayin haka ina nan sai amaryan ta tare ida ma zan tafi din. Sai bayan kwana biyu na kira maigari ina bashi hakkuri kan rashin zuwan mu da mukai alkawarin zamu zo bamu zo ba din. Yace ai shi maigidan naki ya bugo yana sanar damu zancen auren har munyi mashi alkawrin zuwa daurin aure can sokoto idan lokaci yayi. Ko ba komai naji dadin jin hakan daga iyayyena don sun nuna mashi halarci ga hakan da zasuyi mashi din. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABUIDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 102 Zan iya cewa mu a wurin mu bamu san wainar da ake soyawa ba sai dai labari mukaji a kano anyi buki sosai don jama, a sun tafi da yawa wurin daurin aure; a sokoto. Don can aka fara kai amarya suka kwana hudu da sati daya akace za suyi sai gasu da kwana hudu sun shigo Abuja kuma dama already an gyara part din ta don masu decoration ya dauko sukai gyaran ko ina na gidan. Ina zaune da yara muna hutu don nayi up ranan da suka shigo tun monday shi na fara fita night duty na dare. Muna zaune yaran sun dsmay ni da korafi akan daddy su ko waya baya bugo masu jinior keda wanan nan korafin ita ko antyna sai dai tayi zaune tai shiru ko abinci sai da kyat take ci dama abinda nakewa gudu ke nan da sabon da yaran sukayi dashi. Hindatu ce ta shigo falon nawa take cewa dani hussunah ta damay ni wallahi sai kiran kai take yi shine nakawota ki duba min ita. Nai murmushi tare da dan kamo hannun yarinyar nace da ita daddy ne ko hussuna sai na nuna mata Anty dake zaune tayi wani irin zama na ban tausayi a saman kujera. Hindatun ke cewa dani aini sam ban dan abinda sukewa ke nan ba na dai dauka haka din ne kanta ke ciwo din take cewa dadi kan nace ta dan karasa inda Anty take zaune tana fadin yarinya ubanki yayi aure ya debe takaici nai. Daga inda nake zaune nace ya dai kara takaicin shi tunda ya karo wa kansa wani ssbon tention kuma again. Don ita ma aida nata kalar korafin zata shigo mai kamar yadda muke nan kowa da irin halin rayuwan shi itama a hakan zata shigo ya dagwara a inda ya tsaya. Kamar hafin jaki sai ga zulfa ta shigo tana goye da yar ta a bayan ta tace da hindatu ashe kina nan ne sai hindatun ke fadin ina nan ke dai na kawo wannan ne tana nuna yar ta take cewa na dauka bata da lafiya ne ashe ita wai kewar uban ta takeyi haka kin gan su can tana nuna inda anty take zaune. Dariya tayi tare da dan sake habaici tace a, a ke hussuna ashe ba anty kawai ke tare da ubanta ba duk kune gashi ko kullun cikin ganin bai damu da ke ba ashe kema anayi bamu sani ba tunda har kewan shi zai hana ki shakat . Ta lakuto hancin yarinyar tana fadin ai sai kuyi tunda baba ya bar ku nan yana can yana cire takaicin shi a gun yar amaryan shi yar shila. Murmushi nayi na dan gyara rike daddy da yazo guna ya fada a jikina sai hindatu ta ce wai ke may yasa baki sanin abin fadawa mutum wani lokaci may ya kawo wanan maganan kuma yanzu ga yarinya kuma, ? Haba dai ba shi ke gaban ku ba don Allah ya kamata ace zuwa yanzu an daina wanan halin a gidan nan idan ba haka ba itama wacce zata shigo din sai ta shigo muna da raini a gare mu. Bai kamata ace duk mace zata shigo ta dinga samun ana wanan irin batakan ba a tsakanin mu sai raini yai saurin shiga a tsakanin da ita. Amma idan ta shigo ta samu kai yana hade yara ma haka sai ki ga ta rasa madafa a gidan wata idan mai hankali ne dole tabi wa yanda ta sama a zauna lafiya. Idan kuma mai rawan kaine sai tace nata dokan zata kafa dole abita sai idan tayi taga babu kafa a gare ta zata shiga hankalinta. Idan har wanan matar kuma ta shigo ta samu muna wanan halin na kishi haka a junan mu wallahi a take raini zai fara daga wurin ta bazata taba daukan mu da daraja ba don itama zatace zata gwada nata sa,an a gare mu da maigidan sai kiga tazo ta mallakr gidan a cikin dan lokaci . Mata da yawa wanan barakan suke samu a gidajen su sai kiga matar baya tazo ta na son raina hankalin matar da ta samu a gidan . Don ta samu ba hadin kai ko kuma kishiya da miji babu fahintar juna a tsakanin su shi har zata samu daman kokarin kafa nata gwaunatin a gidan. To kunga idan har karamar yarinya zata shigo cikin mu ta samay mu a haka kamar kowan mu na jirace da dan uwa muna yawan fitina yaran mu ba hadin kai a tsakani may kuke ganin zai iya faruwa ? Don Allah don Allah ku daina wanan halin na gwatsale juna a tsakani ana fadawa juna maganan da zai sosawa dan uwa rai. Miji dai mun gani ba mijin mace daya bane ko biyu ko uku mijine na mata hudu Allah ya hada mu dashi idan mun zauna lafiya sai abin yai muna dadi a tsakani. Don mun tsaya muna cin junan mu a kasan shi fa daddy babu ruwan shi duk mun sani a nan kowa da daukan da yake mata a gidan nan kuma a haka yake zaman dadin rai damu yana bamu duk wani hakkin mu da Allah ya dora mai a kan shi. Mune dai har yau mun kasa zama mu fahinci junan mu da daya ta gusa mun shiga gulmanta ke nan a tsakanin mu. Idan kuma dayan tazo a zauna da ita a zagi wacce bata kusa kunga hakan bai muna ba gaskiya ko yaran mu dake sauraren mu kullun zasu fara zargin mu muna fukaine ko su ma su koyi zama irin na annaminanci a rayuwan su. Don haka don Allah mu sahircewa junan mu mu kama mutuncin kan mu mu zauna lafiya a tsakanin mu zama na amana son juna da karuwa sai kuga komay ya tafi sannu a hankali a tsakanin mu. Amma fa ni shawara ne nake baku ba wai nace lalai sai hakan ya gudana ba don kowa da ra, ayinshi a tare dashi. Hmmm maganan ki ai gaskiyace Rahama don baki fadi karya ba ga zancen ki tundai ni da za a kaiwa amaryan part dina mu zauna tare aiko kunga akwai matsala ke nan. Babu wani matsala ga hakan idan kin iya kama kanki da bakin ki gare ta kika ja girman ki sai kiga kinyi power a wurin ta. Hmm ai na yarda da ake cewa ba wayewa bane wayo dan kauye da kuke ganin su sun fimu tashin birni wayon tsiya. Na dago ina dariya nace abin kuma sheri ne haka anty daga shawara kuma. Tace wallahi Rahama duk sunan mun girmay ki ne kawai amma wallahi duk Rahama kin fimu wayo Allah ko. Ki duba shawaran bada kudin nan da yai muna in badon ke ba ni ina zanyi wanan tunanen ma yanzu kuma gashi kinzo mina da wani babban shawara wanda duk maganar ki gaskiya ce a cikin sa. Sai bango ya tsage kadangare ke shiga kafarsa ai idan muna kama kan mu, muna abin mu in matuarity wa zai kawo muna raini a gidan nan. Mun dauki lokaci muna hiran mu duk dai akan matsalan rayuwan zaman gidan daddy ne da yadda za a dora dashi. Kwasan ba zato sai ganin daddy mukayi a falon kowan mu ya baje sai kwasan dariya muke yi a falon. Kallon mamaki, muka bishi dashi har ya kataso cikin falon shima sai bin mu yake da kallo yana mamakin kasancewar mu a wuri daya haka. Sannu da zuwa muke mashi hankalin shi na kan yan yaran dake zaune a gefen mu suna shan lollipop ko kallon shi Antyna bata yi ba zakace ko wata babbace ita irin yadda ta share uban nata. Ya karasa gunta yana fadin yau kuma wani sabon sallo kuka dauko ne a gidan haka yakai hannu ya dan taba yar wirin hindatu yana kiran sunanta sai ya juya gun ta zulfa ya lakaci fuskan ta ya dauki anty yana kiran sunan ta tare da ce beta yana fadin my Saade ke nan . Sai yarinyar takama bultsewa tana son ya sauke ta tana fadin umm, umm ummm yace da ita kai my Saade badai kema kin iya fushi ba ko ? Ba wanda yai mashi magana bayan gaisuwa sai da yaga yarinyar bata yarda ne ya direta tare da cewa ai ke zaki biyo ni sai Zulfa tace tunda an saba bin bayan ka ba. Dama ai kunfi kusa ta hannun damarka ce din da sauri hundatu tace da ita haba dai kuma. Yana sauke yarinyar yake cewa ina sauran yaran ne suke bashi amsa da suna school basu dawo ba tukun. Ya juya zai fara tafiya sai naji hindatu na cewa dashi amaryan fa tana can ne ya dan juyo yana cewa tana part din ta mana. To sundundun ke nan haka ashigo kamar munafuka kuma ba ko sallama asan da zuwan ta gidan shiru nayi nasa dama mai hali baya barin halinsa ai. Abu ne mai wuya su bar hslin nan don ya zama masu jiki ko don kowa da kalar nata kishin a rayuwan ta. Bai dade da fita ba suma suka watse kowa ya koma part din shi da zama don dama zaman na ranan ne kawai aka dan yi shi . Ni dai ban sake bin ta kan shi ba dama akwai gajiya a jikina tare da yarana muka kwashi barcin mu na rana sallah kawai na tashi nayi na koma na kwanta abina sai shidda da yaran suka dawo gida na tashi. Mun dan zauna dasu har bayan magariba ina idar da sallah na fara shirin fita don zuwa duty Aisha na tsaye tare dani tana fada min cewa jiya ma da kyat ta samu daddy yai barci nake cewa sai yayi hakkuri uwarshi ba mai zaman gida bace anytime. Daddy ya shigo dakin a daidai lokacin da nake magana ina saka rigan aikina daya tsaya min daidai saman kayan dake jikina. Sannu yaran suka fara mai ban juyo inda yake ba saida na gama na juyo yana duke rike da hannun daddy karami suna magana. May ke faruwa ne kuma Rahama naga kowa ya shiga gun amarya ke baki shiga ganin ta ba mana tun dazun. Wani kallo na jefa mai daga inda nake tsaye tare da cewa wa ni daddy wani komawa baya kuma zai kama ni da tazo ta sama a gida bata nemay ni ba sai nice zan je gunta haba dai abin nawa bai kai can ba ai. Murmushi yayi yana dan girgiza kan shi tare da fadin bakuwar ku ce fa shine kuma wani matsala can daban. Nace bakuwar ka dai daddy may ye hadina da ita ni kuma da zata zama bakuwa don Allah dai abar ma zancen. Yace hmmm Rahama Rahama wani lokaci sai kiyi wani abin takar ba ke ba wallahi may ye na komawa baya don kinje kun gaisa kawai da ita. Nace to yar gidan sarakai ko to talaucin nawa ni baikai can ba tukun na kai hannu na dauki hand bag dina yake fadin wai ina zakine kuma ? Nace wurin aiki night duty na shiga week din nan na fara ok abin yakai har ki fara baki fada min ba ban sani ba kuma. Nake cewa kamar ya ban fada ma ba tunda kasan dai aikina ne hakan banda choice akan wani abu kuma. Na dago alaman zan fara tafiya yake cewa dani Rahama sai na dakata shiru yayi tare da kura min idanuwan shi a kaina. Nima din kallon nasa nakeyi sai dai ba zan iya jurewa ba na dukar da kaina yace kada ki bullo min da wani sabon halin da ban sanki da shi ba a baya akan kawai na kara aure. Naga dai ba wannan ne karo na farko dana kawo maki kishiya ba a gidan nan ko yarinyar dabaki ko santa ba, baki san waye ita ba kike son ki kirkiro wani fitina a kan ta kuma. Nace fita akan kayi aure zanyi fitina ko may niba mata na sama a gida ba ni har ina da bakin magana ni da akai maka dole a kaina ba da son ran ka ba. Yace ok haka kikace ko nace dashi ai haka din ne ni har wani kadari ne dani gare ka dama matar cushe ba wani power ne da ita ba sai hakkuri don haka duk matan ka ni ba wacce nake kishi ina dai zaman abinda aka dauko ni yi ne kawai . Kuma ina fatan Allah ya bani ikon cinye nawa kalar jerabawan na rikon marayun da ya hau kaina da karantana. Yace haka kika ce dai ko ? Dama ai hakan ne daddy yace no warder naga baki taba kishina ai a rayuwan ki sai dai masu kaunana suyi. Nai murmushin dole duk da raina a bace yake nace, Daddy nayi kishin hauka na zama wa a gurin ka aiko dana ji kunya kishin mijin da yake na mamajo kullun aure. Wani sabon suna na samu ke nan kuma a gidan dama tun dawona dana samay ku haka a wuri daya nasha jinin jikina kan akwai abinda ake kulla min a wurin kuma. Gashi kuma yanzu na gani da idanuwa na tun ba a kwana ba kin nuna a zahiri don ban sanki da saurin sarewa ba irin haka ? Ban iya magana ba sai duban time din da nayi alaman zai sa na makara ya fara tafiya yana fadin dama mata ba a shedan ku ai na gaskanta hakan yanzu. Indai akan kishiya ce har kai min mumunar fassara ba damu inda saniyar gaba tasha ruwa kona baya a nan zata sha itama. Bai juyo ba ya sa kai ya fice daga dakin na sauke ajiyan zuciya nabi bayan shi tare da yara da sukai min rakiya kamar wacce zatai tafiya ba duty zan tafi ba a lokacin. Ban yafi ba sai da nai masu abinda na saba gaba dayan su har manyan nabawa kowa abinda ya sauwaka a hannuna daga can na hango daddy yana fitowa daga part din amarya da sauri na kawar da kaina daga ganin shi na tayar da mota na bar gidan. Ashe bayan tafiyana yake tambayan yaran na tafi ne suka ce yanzu na fice daga gidan ai. Bai tsaya ba ya barsu ya shige wurin shi kai tsaye tare da turo kofan shi ya rufe suma shigewa sukayi wurin mu tare da rufo kofan part din. ********* ********* ********* Washegari a gajiye na shigo gidan ban daki na fada nai wanka tare da cire kayan aikin da na dawo dasu na aje a inda muke tara kaysn wanki na na kullun. Abinci Amira ta kawo min ta zauna tana zuba min ni kuma ina shiryawa hira muke da ita a kan Jinior muna kwasan dariya sai ga Aisha ta shigo dakin. Tace mummy dazun ai naga amaryan daddy a waje tayiwa kawayen ta rakiya mummy baki ganta bane fa wata, , , , Haba Aisha don Allah rabani da zancen ban haushi ko ma yaya take ai haka yaga abinshi ya dauko ko wa kan sa namiji ina ruwan shi da wani siffa idan ya tashi son mace. Wai ni mummy may yasa daddy yin aure ne kuma sai fa da Za,id yai min magana kan auren nan da daddy ya kara ranan, cewa da wanda zata aura din. Nace may kikace dashi ke tace cewa nayi dashi ina ruwan sa bana son yana mun irin wanan maganan again don ba abinda ya shafi rayuwan mu bane. Nace kinyi daidai Amira don da da haja sai yakai ga fada maki maganan da rayuwan ki zai kai ga baci . Tace ai ban daukan wanan raini ne mace ta dinga bari mijin ta ko saurinta na zancen yan gidan su a gaban ta tana kyaleshi watarana abinda zai fada sai yafi wanda ya fara fada mata da farko. Nace kai ashe yar tawa tayi girma da wayone haka lalai daddy nada gaskiyan shi dayace aure zai maki . Tace kai mummy auren may can kuma don shi yana son aure shine ni zai ce ai min nifa masters nake son na yi fa idan ma na gama. Ke rufawa kanki asiri da wani karatu can kya karasa a dakin mijin ki idan kunyi aure in kuma kin haihu to shike nan kuma sai a zauna raino. Da sauri ta fado min a jiki tana rufe min baki tana cewa kai haba haba mummy tana dan jijiga min jikina. Uban ne ya shigo muryan shi mukaji yana cewa ke ke ya haka kuma uwar taki ce kuma kikewa haka kuma ku ba kwa girma ne wai ? Da sauri ta daga min a jiki tana dan turo baki tace daddy mummy ce fa nice nai magana da cewa mutum bai awasa da dan shi ne ni haka nake da diyana. Ke fice min da wanan shirmayn banzan naku don Allah zanga maman ki ne da sauri suka fice daga dakin. Ya karaso inda nake zaune bakin gado yana kokatin tungumoni a jikin shi da sauri na dago ina kallon shi cikin mamaki nace amma dai kasan hakan bai dace ba don bani ce dakai ba. Sai akace don ba ke ce dani ba kada na taba ki kuma ko ? Kara kai hannun shi yayi yana kokarin lalabana da sauri na kauce tare da mikewa tsaye ina fadin mutum da amarya tsaleliya ya dawo yana taba tsohuwa kuma ? Sai naji yaja tsuki tare da juyawa zuwa bakin mirrro dina ya tsaya yana fadin ina son mu hadu idan anyi sallah a falo na Allah ya kaimu nace dashi kawai. Ya fara tafiya ina bin shi da kallon yadda duk mood din shi ya canza daga yin magana kan amaryan ta shi. Sai na fahinci da akwai matsala duk yadda akayi bisama idan anyi la, akari da yadda suka dawo batare da sunyi sati dayan da sukace zasuyi ba a kano. Wanda nasan sun zauna can ne dama don ya samu hutu da yar amaryan shi kada ya dawo nan a damay su sai kuma gasu ba sukai satin ba sun shigo. Yana fita na dan leka yaran na dawo na samu wuri na kwanta sai barci ban falka ba sai da Amira ta shigo ta tayar dani. A Lokacin har karfe uku saura da sauri namike nai sallah na gyara jikina sai ga wayan daddy ya shigo min ina dauka yake cewa dani wai may kike jira har yanzu muna ta jiran ki. Nace gani tafe ai tsab na shirya sai kamshi nake na nufi falon nashi inda na samu duk suna zaune a falon nice kawai ban shigo ba. Nashiga da sallamana abinda ya fara tarona shine yarinyar da na hango zaune gap da daddy a saman kujera daya dashi wanda ba kasa fai muke irin wanan zaman ba indai za ai irin wanan zaman. Maimakon na zauna saman kujera sai na koma daga bayan kujera naja na tsaya tare da cewa gani naji kace kana nema na ? Yace zauna mana baki ganin kowa a zaune ne nace dashi eh to na dai gan su a zaune sai dai zaman ne naga kamar babu tsari yau gare shi don kasan ba haka muka saba zama ba ai. Ya dan yi murmushi tare da daukan remote ya rage vollume din tv dake aiki a looacin ya ce da yarinyar ke Ni,ima koma wurin yan uwanki ki zauna. Sai taunan chewgun take yi kas kas ta dago kai da sauri ta dan kalli inda nake tsaye kamar zatai magana sai ta mike ta nufo gefen da zulfa take ta zauna. Na samu dayan kujeran na zauna a kai may karatu kada kiga laifina nayi hakane don saurin yankewa fitsaran da naga yarinyar tana shirin muna shine dalilin danai amfani da wannan hikimar na fahintar dashi yakuma gane bazan zauna ba a yadda suke zaune din nan. Yace damu ok dama na kiraku ne don na gabatar maku da Ni,ima a matsayin sabuwar abokiyar zaman ku a gidan nan. Ya juya gunta yana fadin Ni,ima ga mata na da nake aure nake kuma tare dasu kuma uwayen diyana a gidan nan. Wanan itace zulfa itace ta maye gurbin uwargidana da Allah yaiwa rasuwa sai kuma ta biyun itace hindatu ya nuna ta yace wanan kuma itace kike biwa watau Rahama ke nan. Sai ta dago kai tana min wani irin kallo tana tauna chewagun tare da wani mayde bakin ta a yatsune fuska. Ya juya gare mu yana cewa wanan itace Ni,ima da na auro na kara a acikin ku da fatan zan samu zaman lafiya a tsakanin ku. Babba ya rike girman shi haka ma karami ya rike nashi a matsayin karami Ni,ima da fatan zaki zamo mai biyayya a garesu a zauna lafiya. Sai may muryan yarinyar naji tana cewa idan sun so a zauna lafiya may zai hana sai dai bazan yarda da saka ido ko shishigi ba a rayuwana. Na dago ina kallon yadda take magana tana wani har da idanuwan ta baki na magana hanci na magana ido yana magana nace tau, , , , Tana fadin haka sai ta mike ta bar falon yana kiranta ko juyowa batayi ba ta shige abinta. Gaba daya muka bishi da kallo don kowa yaga abinda ya dauko wanan karon a gidan kuma a zahiri watau fitsara ya shigo muna kuma again. Zulface ta kawar da shirun da falon yayi da fadin tau dada yanzu sai yaya kuma ka daiga abinda ka kwaso kuma wannan karon. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 103 Ba shi ba da ya dauko ko mi dake wurin munji kunyan abinda yarinyar tayi mashi a gaban mu don mijinka daraja ke gare shi a idon ka da kima. Amma sai ga wata a gaban mu ta zubar da wanan darajan nasa da kima da mutunci da muke gani a gaban mu. Hindatu ne tai karfin halin karawa da cewa eh gaskiya yau kuwa mun gaskanta yarinya ka dauko wa kan ka don nishadi tunda mun ga irin kalanta ta tun yanzu. Mikewa nayi tsaye tare da cewa da su Allah ya bamu alheri na barsu a zaune har lokacin bai iya cewa uffan ba. Ina shiga na zauna falo don duk yaran suna zaune a falo hira suke jana dashi amma na kasa basu amsa sosai sai Amira ce ta dan maida hankalinta a gareni tana cewa mummy halan anyi wani abune kuma da aka kiraku falo naga ranki a bace ? Murmushi na dan kakaro a fuskana mai kama da yake nake cewa da ita bari ke dai Amira wanan amaryan ta daddy tana da rashin kunya da ranshin mutunci a tare da ita. Don yanzu ta nuna muna halinta a gaban kowan mu tai mashi rashin mutunci har mu din daya tara don magana. Mummy ke taiwa rashin mutunci ko daddy din nace da ita shi damu duk daga magana ta sake muna bakar magana ta tashi ta fice yana kiranta ko juyowa batayi ba ta tafi abinta. Au da shi ta shigo gidan ke nan ashe zata ko hadu damu wallahi don bazatai maku mu kyale ta ba nace da ita babu ruwanku a wanan zancen kada ma ki fara . Batai min magana ba naga ta turo baki kawai tana zunbura bakin ta gaba Aisha tace ni dama ina ganin ta nasan bata da mutunci baki ga ksyan dana ga ta saka bane a jikin nata. Tun wanan zaman ban sake bin ta kan koshi daddy din ba balle wata amarya can dake gidan. Zan fita da dare night duty idan na dawo zan ta barci na sai yamma na tashi in dan zauna da yara muyi hiran mu dasu. Ga bukinn dake gabana ya gabato min haka ya kara sa banda lokacin komai ma a gidan yanzu sai na abinda ke gabana kawai. Buki saura sati daya muka tafi aka gyarawa Aisha gidan ta tare mukaje dasu zulfa da hindatu da kawayena uku. Mun dawo gida da yamna lis don kowan mu ya gaji sosai a lokacin nan waje muka samu amarya da kawayen ta da wasu maza biyu sai kwasan dariya suke yi a wurin. A motana muke don haka nice ke jan mu gaba dayan su suka yo kan mu da kallo kowan mu takai don babu wacce za, a gani a raina a cikin mu. Sun rigani fita daga motan don haka nice ta karshen fitowa daga motar ina daga bayan su nake jin abinda suke fadi. Kai Ni,ima wannan sune kishiyon ki fa kikace amma dai kan akwai magana a wurin nan sai naji tace aff maganar may fa da sannu duk zanyi maganin su ko nai waje da yan iska don ban shigo masu ba sai da na shirya masu sosai. Juyowa nayi ina kallon su don na nuna masu naji zancen su dasuke fadi dayan tace da ita wanan kan akwai jin aji dafanin su duba fa ko kallon inda muke basuyi ba balle su san da tsayin mu su gaida mu. Tace da sannu ai duk zasu shigo hannu ne sai kace mu ba ya sokoto ba a kofa na hade da Aisha da Amira zasu fita fadan fitan dare nake masu suke cewa dani ba nisa zasu ba yanzu zasu dawo ai. Nashige yaran na fita nan Amira ta fara sheda dayan su don ta sansu a school sai ga Nasir ya biyo Aisha da wayan ta data manta dashi ciki don an kirata a bayan su. Shima daya daga cikin samarin ya san shi a school din su, kallon kallo sukeyiwa junan si don har amarya ta san Nasir din . May kuka shigo yi gidan mu yake tambayan yaron yace munzo gaida amarya gidan na ne gata na ya nuna mata Ni,ima din dake tsaye tare dasu. Wani iri yaron yaji a ran shi ya juya batare da yai magana ba ya nufi inda su Aisha suke suma wayan ya mika mata ya juyo abinshi. Yaro nan ke fadin baba na ne gidan ku dama ashe ? Yace dashi a kausashe nan ne mana gidan mu yaya akayi ne wai ? Part din mu yanufo tun daga nesa yake kwala min kira nace kai lafiya wanan kiran haka ina aje cup din ruwa da nake sha a hannu na. Mummy dama wanan yarinyar ce daddy ya aura ashe budurwar Yasir ne fa abokina a school kuma fa mummy tantiriyar yar bariki ce sosai. Haba nasir koma yaya take ai yanzu matar baban kace don haka ka fitar da idon ka a kan ta please . Wani iska ya furzo daga bakin shi yakai zaune tare da dafe kan shi ya dade zaune a wurin bai iya magana ba da kowa. Hakama su Amira da suka dawo da wanan korafin suka samay ni nace da su sai dai kuyi hakkuri tunda har ta shigo gidan ai. Daddy baya gari sai bayan ya dawo ne har ya shigo mun gaisa dashi ya fita da yamma sai gashi ya dawo ina zaune da yaran a falo muna shan Apple. Wuri ya samu ya zauna yake cewa dani Rahama ina son kiwa yaran ki magana don Allah su daina yiwa baki a gidan nan wullakanci. Nace wullakanci kuma daddy wani yaro ne har yaiwa wani wullakanci a gidan nan kuma ? Yai dan shiru yace Ni,ima ce take fada min yanzu wai abokan ta sunzo sun wullakan ta su jiya nace dashi ita kuma da shi ta shigo muna. To ka fada mata bazan dauka ba ko kadan ta tsaya a matsayin ta su ma su tsaya a nasu don tana tunanen cewa sun san komai a kanta shine tai saurin fada maka sheri a kan su. Yace may suka sani a kanta nace budurwar abokin Nasir ne yasan ta tasan shi yanzu kuma matar ka take. Humm yace a wanan kuma kuka fito ke da yaran naki kuna ganin maganar taku zaiyi tasiri ne a kunne ko may ? Ba don ka yarda ko kai wani abuba na fada ma don kawai sherin da ita take son hada ka dasu kawai ta iya kanta ka fada mata don mu bamu da lokacin ta a gidan nan. Kada ki saka min yara a cikin zancen kishin ku don ba zan dauki hakan ba ko kare na dauko a gidan nan a matsayin zamana dole ne yarana su mutuntashi a idon su. Balle macen dake zamana a cikin gidan nan koda shi ne ya nemay ta ba abokin shi ba yanzu wanan ya wuce a wurin shi. Daddy ba sai ka fada ba ai dama yara yaran ka ne banawa don haka ba sai duniya sunji zancen wai bani na haife su ba. Idan kuma ta turoka ne kazo kai min cin mutunci don ta nuna min ta isa ka fada mata ni da ita da babu duk uwar su daya a wurina a cikin gidan nan. Don naga take taken ta na rashin mutuncin ta nason ya kawo kaina tun yanzu to ta kama kan ta dani wallahi dama duk wani yaro na don ba zan dauki raini ba ni. Yace kin dai ji abinda na fada maki kada su bari ta kara kawo min karan su akan irin wanan matsala. Nace don kawai basu gaida bakin ta ba ko may yace don ne ko banga laifin ki ba ai don kune kuka fara har yaran suka gani ai. Nace yanzu naji magana kan kafito fili kace dani Rahama may yasa baki duka kin gaida bakin amaryana ba ba kace wai yara sun ki gaida bakin ta ba. Wanan kuma zancen ki ne ban dago kai na sake ksllon shi ba har yai maganan shi yabar part din. Yana fita ashe Amira na jin mu tace ashe akwai abukazan uba a gidan nan kuwa ita wacece da zatace mu gaida bakin ta wallahi zamu hadu da ita ai. Ban san yaya akayi ba don nafita zancen yaran kuma shima bai kara maganan ba tun lokacin don ba ma wani haduwa mukeyi ba sosai. ********* ********* ********* Bakina sun fara zuwa don halartan bukin don haka na zama busy sosai da jama, a a gidan ban da lokacin komai yanzu. Yaran ne sun dawo da kawayen su daga wurin gyaran kai da suka tafi nake jin suna ta surfa zagi daga inda suke zaune. May ke faruwa ne daku dawa ke fada nake tambayan su sai suke cewa dani wanan yar iskance mana muna shigowa ta tare muna wuri da motar ta munyi magana take son fadawa mutane maganan banza kuma. Wacece ke nan na tambaya cikin son jin ko dawa suke fada haka amaryan daddy mana nan dai suke fada min yadda suka kwasa da ita a wajen. Da yamma kuwa daddy ya kirani na samay shi falo, da su Amira bamu dauki lokaci ba muka shiga falon nan muka samay shi zaune yana cin abinci ita kuma tana zaune akusa dashi. Saye take cikin wasu english wear duk sun matse ta ga gashin dokin data kara ya zubo mata a goshin ta da bayan ta. Ta koma kamar wata yar arniya da ita sai wani yauki takeyi a gaban shi nai sallama muka karasa shiga tare da yaran. Daddy gamu nace dashi ya nuna muna wuri mu zauna mina zama ya jawo kwano wanke hannu ya fara wankewa. Sai da ya gama ya juyo gare mu fuskan shi a daure yace Amira may ya hada ku da wannan dazun kuka zage ta ne ? Wake nan daddy Amira ta tambaya yace da ita Niima Niima Amirah ta sake maimaita sunan yace eh gata nan zaune. Tace ba komai daddy motar ta ta aje a gurin da nake aje motana shine nace ta jaye sai kawai ta kai min zagi sai kawai mukaji tace . Na zage ki ke wacece da zakice sai na jaye wallahi ko kina so ko bakya so dai da uban ki nake kwana na tashi dashi. Da sauri nace subbahanallahi wanan kuma wani irin zance ne haka ba dadin ji kuma ? Sai naji Amira tace idan kin kwana da ubana nima ai mace ce sai naje na auri ubanki na kwana dashi kinga anyi daidai ke nan. Ba sai kin fada muna kina kwana da daddy ba tunda ba shine na farkon kwana da ke ba su Yasir ma suna kwana dake ai a baya. Innalillahi nace tare da mikewa tsaye nace to yanzu an kai ga yadda ake so a gidan sai cewa daddy keyi ke Amira Amirah a gabana kike fadin wanan magana haka ? Daddy wallahi ba zan tsaya wanan ballagazar ta fada min magana ba ko kina nufin cewa bamu san yadda kika mannewa daddy har kika aure shi ba ne. Nace ke Amira tashi mu tafi sai sauran yaran suka mike Ihisan tace wallahi daddy wanan idan bata fita idon mu zamuyi maganin ta a gidan nan ka fada mata. Nace ku fice nace daku sai suka fice daga falon na juyo tare da nuna su da yatsa nace ke na fahinci da rashin mutunci kika shigo ko wata bakiyi ba kina son haddasa matsala tsakanin shi da yaran shi haka. To ki natsu ki kama kan ki don ba zan dauki wanan ba idan kin shigo ne dasu a zuciyar ki ki sauke. Tace ni yara basu ne a gabana ba don ba sune sa,oin yina ba ni dake zanyi keda kike kishiya na dama ina da labarin ki kuma ban shigo ba sai da na shirya zama daku mussan man ma kedin da kike jin kan ki wata tsiya ga kowa. Dariya nayi nace to kaji da kunnuwan ka don kada ka zarge ni daga baya don ta shigo dani a rai ni kuma ba zama zanyi kalkon ta ba. Tace dama haka nake so dan da ke wata tsiyace a wurin shi da ba zai dauko ni ha ko ya kalli wata mace bayan ke da sunan aure. Sai naji yace ke, ke Niima dama haka mukayi dake ko alkawarin da kika daukar min ke nan na wanzuwar zaman lafiya a cikin iyalina ? Ban fada maki zaman lafiya nake da iyalina ba ban fada maki ba zan lamunci a wullakanta min matana da kika sama ba a gidan ? Tace ai wanan dama ba alkawari nai maka ba a mayar dani banza a gidan ka don kawai na auri mijin su ai miji yanzu na kowa ne kowa tashi tafishe shi a gidan. Ina tsaye na harde hannaye na cikin murmushi nace da ita hakane fa yan mata miji fa na kowa kowa ta kada rawan ta ai da na dauka da lalama kika shigo muna amma yanzu muje zuwa na juya na fita daga falon. Bayan fitana kaca kaca daddy yai mata bai raga mata ba sai data raina kan ta yace ta fice may daga falo kada ki dauke ni mutumin banza kizo ki kawo min fitsara a gidana. Da taga da gaske yake dole ta natsu yace cikin tsawa fice min daga nan mara mutunci kawai kafin ki zuba da iyalina ni zan zuba dake ai. Ko maganan da yaran nan ke fadi yanzu a zaton ki ban sani bane ni kyale ki nayi naga iya gudun ki. Watsatsa mara mutunci kin gaba bayar da kanki ga kananan yara kizo min nan kina son watse min kan iyalina duk wani bakin cushe cushen dakike kina dauka ban san dashi bane ko may. Na tsani macen dake wanan bakin dabiar na cushe cushen banza a gaban ta don mata ba dabiar su ke nan ba su. Don Allah honey kayi hakkuri sherin shedan ne kawai amma ba zan sake ba insha Allahu yace inma halin kine wanan matsalarki ce don ke zaki sha wuya a cikin su . Yarana zakizo ki saka a gaba don kinga ina daga maki kafa nina san dalilina nayin haka amna yanzu kin karasa zube min a idanuwa na gaba daya. Taji matukar nauyi da kunyan maganan da yake fada mata don ita a zaton ta tana ganin a budurcin ta yake daukan ta gashi hudubar abikan banza ya ja mata rasgin mutunci irin haka a gaban kowa. Buki yayi buki ban kara ganin taba ban bi kuma ta kanta ba balle na san halin da take ciki a lokacin. Sai dai zancen ta yana a raina so sai ina tuna kalamin ta a kaina na wai dani rasgigo tazo tayi maganina ne a gidan dama. ********* ********** ********* Da kanta ganin ana shagalin buki tana gefe ba wanda ya bi ta kanta gadhi kuma tana son nunawa kawayen ta ita wata tsiyace yanzu. Ta samay shi tare da kwantar da kai tana cewa dashi honey ban san may yasa ni ba a fada min yau za, a yi dina ba na tafi naga kowa na shiri. Yace da ita dole taki fada maki tunda baki da mutunci kin gwada mata koke wacece tace don Allah a barzancen ta gane kuren ta ai yanzu. Yace zai min magana inajin kiran shi nasan cewa da magana duk jama, an dana tara na mike na samay shi a falin shi yana zaune ya tasa laptop a gaba shi yana aiki dashi. Nai sallama na shigo da Anty a hannuna data lake min taki yarda da kowa tasha ado itama yarinyar a jikin ta. Ya dago yana murmushi yake cewa dani har kun shirya ke nan ko may nake cewa dashi ina zama wanan taki barinama aina shirya don fitina taki yarda da kowa yau a gidan. Yace yau uwarta na aure bata da lokacin ta kuma da ta yarda da Aishan ai don bata da lokaci ne yau. Daddy gani kace nazo yace eh yana dago kai baki fadawa wanan yarinyar zancen zuwa dinner bane yanzu ta samay ni tace baki fada mata komai ba wai akan bukin. Nace ya salam wai daddy may yarinyar nan keso danine a gidan nan please akwai fa dalilin da yasa nake daga mata kafa fa.. Na sanu Rahama amma tunda ita da bakin ta tai magana kiyi hakkuri ki fada mata nace wallahi bazan fada mata ba ita wacece da sai naje na fada mata. Oho tana son zuwa ta nunawa duniya ko ita wacece a wurin ko ta bata min taro da rashin tarbiyan da ta iya komay. Bazan fada mata ba kuma ban gaiyace taba ga sha, anina idan kuma tai gigin zuwa duk abinda ya faru da ita a gurin ita tajawa kan ta. Yace tunda kince baki gaiyyace taba ai shike nan amma ki sani wanan halin ba zan dauke shi ba don naga kuna so kawo min matsala a gida na. Nace dashi take dai son kawo maka matsala amma ba ni ba da ina da matsala ai da kai kafi kowa sanin haka a baya. Tace ita bata da kunya ta ta zauna taci rashin kunyar nata mu gani mana idan shine maganan ni zan tafi do mutane na jirana aiki mukeyi. Yace is ok kutafi za ce ta zauna ba sai taje ba shike nan ko nace dayafi mata ai bataso hakan ba da tabi da mutunci da wanan ba komai bane. Amma ban sanin halin mutum na bari ya shanmace ni kuma na dauki diyata muka bar mashi falon ban dade da fita ba sai gata ta dawo wurin shi kamar manya tana cewa wai ya fada min yace ke ki bar zancen nan kawai ki zauna. Za tai magana yace ai kinji abinda na fada maki koma may ye aikece kika soma da kinzo da mutunci daba hakan ba ai a tsakanin ku. Bataji dadi ba na samu su Zarah ina fada masu hajiyan harka tace may kikace ke sai nake fada masu Zarah da Fati sukace kinyi daidai wallahi. Bata zuwa yar iska mara mutunci kawai gasa mata kwakwanta ga hannu sai ta raina kan ta a gidan nan. Wai harda fadin da ke tashigo tana ganin tagama dashi take zaton harda ke sai ta juya ki. Aisha da fatiman sister din shi dake gefe don isowan su ke nan garin suna cin abinci sukace karya take ko a can ma kwasa sukayi dashi bakuga sun dawo maku a bazata ba daga shan amarcin da ya gudu nan yayi a kano. Aisha tace wallahi ina ga watsatsar yarinya yai karo da ita don mun je gidan mun samu suna fitina dashi da alama dai amarya fanko ce sai dai maneji kawai. Ai kaji abinda akewa gudu inji Fati yanzu tazo zataiwa mutane rawan kai a gida ita a dole ga yar iska ko? Wuri ta samu ai daya gwada mata ita ba komai bane bata da kima da daraja da ta shiga hankalin ta da kowa. Ai kinsan mazan yanzu ba kowa ya damu da wanan ba sai kiga sun share har ma su so fifita ta banza akan na kwarai akan ta sai su rufe idanuwan su duk da sun san watsatsace. Basu san maganan Allah baya tashi ba akan zina ko tai haifa masu ko a samu jika hakana sai anyi daya biyun a garesu. Nace ai yasani don data shiga gonar Amira ta fada mai a gaban shi sukai yi . Da Amiran Aishan shi ke tambaya nace da ita fa cewa yarinyar tayi tafi karfin ta don da ubanta take kwana ta tashi ita. Sai dakin ya dauki salati hajiyan harka tace dama ido ya bude sai fatiman daddy tace wani amsa aka bata to nace Amira kuma cewa tayi ko ita ai mace ce sai taje ta auri ubanta ta zauna kishi da uwarta ba komai bane. Dariya suka sa kai yaran yanzu sai kace koya masu magana akeyi nace wallahi ni kaina sai da naji kunya a wurin ai. Amira bataji nauyin uban ba tace da ita kuma don kin kwana da daddy nina sa ba bakon abu bane a wuein ki tunda da abokan Nasir yara kanana kike kwana kafin daddy din. Dakin ya kara kwashewa da szbon dariya bandani sai Aisha tace don Allah ji wanan irin magana zata sa yara su fitsare muna a gaban mu. Hajiyan harka tace ai yaron yau ka barshi kawai inda ka gan shi kinga ta karbewa uwarta fada ke nan ya zama nata don kin san dai ita Rahama bazata iya fadin hakan ba a gaban shi. Shiyasa ake cewa kasada ne shiga gidan dake da yara yan mata in har zaka shiga to shigo da salama a zauna lafiya amma in har kace zaka taba masu uwa kaiko naka ya samay ka a gidan. Kai shi da yara kayi da uwar su nace ai ni Amira ta ban mamaki data rufe ido ta gasa mata zance haka ko Nasir don ina mai tsawa ne shima nasan da yanzu sun kwasa dashi ko tuni tunda rawan kan ta har ga yaran kullun cikin kai karan su take a gaban shi. Aisha tace takama ka ta in dai kan yaran shi ne don yanzu na sabanta yake mata nan gaba sai ta rena kan ta gareshi indai yaya ne. Mikewa nayi tsaye ina cewa nifa sam bata gabana yanzu ko kadan don na fahinci kurciya na diban ta. In bashi ba zata kalli idona tace wai dani ta shigo da badon tsoron Allah ba ai tun ranan zata zama bazawara. Hajiyan harka tace na rabaki in ke baki mayar da ita ba indai yaran yanzu ne ita zata mayar dake don yaron yau baijin kunya tubbuke icce har sayen shi a gida. Daga uwar har diyan ta jefa tsanar su a gurin maigida komai sai its ta zama mai juya gida yadda suke so. Nace wanan dai tana da niya yadda na gan ta da halayen ta don fitsaran ta yayi yawa sosai wallahi. Fita nayi daga dakin na barsu suna ci gaba da zancen ina shigowa dauke da wani tire na zubo sayyayen nama a ciki naji Fati na fadin . Kin sai ai yaran sokoto nan suna kadagi da iya iskanci haka suke dama su da kishin hauka kan kishi sai su kashe mutum kishin da uwa da diya ake yin sa da yan uwan ta baki daya. Ai da a garin sune da kunga abu wallahi don zakuga inda kishin hauka yake ba sanayya ko kadan koda kuwa yan uwa ne. Nace dako sun raina kan su wallahi da na gwada masu waye Rahama sun sanni ke kyalewa fa mutum yake ba wai tsoro ba. Zarah tace kaiyya Rahama na rabaki kishin da ake hadawa da asiri shine kishin balai bakiji tace saida ta shirya maku ta shigo ba tasan abinda ta takane inkiji hakan ai. Nace indai hakane muje zuwa ni ga Allah na dogara ba da mutum ba sai mu zuba ta gani ai ni da kaina zan zauna na kai karan ta ga Allah. Ba sai naje gun wani ba don abinda zanyi shi wanda taje wurin shi zaiyi Allah zan fadawa yai muna maganin ta.. Nace da mutane kuci nama don Allah bari a kawo maku abin sha ku dan sha kafin ku shirya don lokacin tafiya holl ya kusa. Aisha tace yanzu kin hana min amarya zuwa ta taka nata rawan kafin nabada amsa Zarah tace ba inda zata wallahi bafa komai bane take son zuwa don kawai ansan itama matar gidan ne yanzu. Shine fa kawai in bashiba may ye na nacewa da sai ta tafi ance ba ayi dakai kace kai sai anyi dole ta tsaya gareshi shi da ya dauko ta tayi. Ashe maganan bai kare ba don ta fadawa iyayyen ta suka kirashi akan maganan don may ana buki a gidan ita zamu ware ta a gefe. Wanan ai an nuna mata kiyayya ne da tsana tunda itama matar gida ce dole a dama da ita ina shiri a dakin mama Altine sai gashi har dakin ya biyoni kin san namiji wani lokaci kamar baida wayo yake. Sun gaisa da mama yake cewa dani zarah na zaune don Allah Rahama kubar yarinyar nan ta tafi bana son yawan korafi wallahi. Caraf Zarah tace wallahi idan taje muko sai mun muzanta ta don bamu gaiyyace taba a harkan mu kawai taje muna da rawan kai ko ta saka muna fitina ta watsa muna taro tunda bata da hankali. Yace haba tunda tana so ku barta mana ta tafi ba shike nan na juyo nace ba dai harkana ba kan ta bari idan nata ya tashi idan ta ganni duk abinda taga dama tai min. Mama tace kai itama dai yar nan ance ba ayi dakai dole ne yaran nan nada gaskiyan su fa fitina ne ba a so tayi da yara balle su da take ganin sa,oin tane tunda ta shigo da rawan kai haka ba kama kai kagama ganin gudun mutanen da ka sama. Ai ba a mulki da karfin dole sai an lalaba akanci gari bada karfin tsiya ba yadda tazo masu. Yace to shike nan ya fice ta sake samun shi wai ra shirya ya bata motar da zata da ita nata yai karama a wurin. Yace ke sunce basu bukatan zuwan ki zuwan dole ne ko lahira ake rabo a wuein mai abu yace baya bukatar ka wurin ba sai kayi hakkuri ba. Aiko nan ta tubure mashi har da son zagin shi wai dama ashe shi mijin tace ne bai iya gidan shi ba ya dauko ta ashe mace tafi karfin shi bata sani ba. Suna cikin wanan rikicin ne sai ga Zulfa take tambayan may ya faru itace ke fada mata sai Zulfa tace da ita kama kanki da Rahama wallahi. Ba irin su akewa a zauna lafiya da ace kin iya bita da kinfi kowa jin dadin ta amma yanzu tunda kikaga haka kama kan ki kawai da ita don duk abinda kike ji Rahama da kike gani tafiki iya shi wallahi. Nan fa ta shiga fada wallahi ita danine mu zuba in karatu nake takama itama tana dashi dariya Zulfa tayi tace a hakan kama kanki wallahi Rahama tafiki iskan ci shiru shirun mutum mugu ne. Ke ma in ba hauka ba may ya kaiki shiga harkan Rahama ki zauna lafiya ai kun kulan da kikace ke nan a gida nan da ita. Hindatu tashigo ta gan su tana sake magana tai mata wani kallon banza tace wanan kuma fa haka ? Shi dai yana zaune bai bar abinda yakeyi ba bai kuma bita kan su ba nice na shigo karshe da yarana har Nasir munyi kyau sosai damu. Jin muryan Anty yasa ahi dago kai yana dariya yace kai kai kai my princess kece haka yau ta haye jikin uban nata sauran duk suka rufe shi ko kallon inda take zaune banyi ba tana zaune sai harara take waysa muna nace ke ba yar iska bace a raina. Daddy banga ka shirya ba ko kai zamu bari gadin gidan ne da dukiyoyin mu don har su mama da kowa watsewa zamuyi mu. Yace nikan ina nan sai Zulfa tace da yar amarya shi ba tare zasu zauna ke nan a gidan tunda bata zuwa ai. Hindatu tace da zulfa din kai maman hanif taje ina kuma don Allah ki bar wanan zancen mana haka wanan ai rashin fahinta ne. Sai yarinyar tace tunda ni ba mutum bace ba ko in dai bukine ai ba yau nake zuwa ba balle ace za ai min maganan banza a kan wanan din wani irin bukine ban gani ba a rayuwana. Eh kin gani kan wuein bin yara kanana asha gara ba dai don matsayi ba wanan kan ba irin ku ke zuwan shi ba. Kafin tai magana nace oya ku karbi kudin ku mu tafi kada mu makara sai ranan ashe ta fara ganin yarana a gidan don su ba su ma san da ita ba a gidan. Hankalinta na kan abinda uban keyi da yaran sai ga yan matan suma sun shigo amsan kudin kari ihisan tace daddy mukan sai dubu dubu ko ? Nan suka baibaye shi suna abinda yasaba dasu yama fita batun mu a wirin tsoki ta buga ta fice daga falon sai kowa ya kwashe da dariya ta juyo tana fadin dariyan ku zai koma kuka soon mu zuba daku a gidan nan. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , 104 Buki yayi buki don an cika an min kara sosai a wurin zakace ko Aisha yar cikina ne nake bukinta. Anci ansha an raba gift don angon yayi kokari shima sosai zan iya cewa a gaskiya Aisha tayi dace da mijin aure mai mutunci ga addini a tare dashi. Mun dawo gida a gajiye kowa ya nufi wurin kwanciyar sa masu yin wanka da sallah suka je yi. A falona muka baza kolin mu nan muka dasa wani sabon hira a wurin sai biyu da wani abu kowan mu ya samu wurin kwanciya don an gaji. Washe gari kuma da aiki muka tashi gidan don akwai walima ga daurin aure ranan kan yan uwan mu sunzo maza da mata sai da suka tuna min da rayuwar kauye. Ayi dauri aure a massalacin uguwar mu bayan an fito sallah azahar anci an sha karfe hudu aka fara shirin walima daga shi za, a kai amarya dakin ta. Biyar da rabi aka tashi walima sai ga daddy ya shigo har part dina yace ina Aisha amarya nace dashi tana ciki. Ki shirya ta yanzu zamu kaita gidan ta ni da mama Altine da matar maigari nace dashi da sauri daddy yanzu yace an daura aure may zata zauna maki yi a gida nabaku minti goma ku fito min da ita yanzu. Dole haka muka shirya ta tana kuka nima kukan nakeyi mama Altine ta rike suka fice zuwa part din daddy din inda daga can zasu wuce da ita gidan mijin ta. Ina zaune aka aiko wai nazo na samu harsu hindatu da zulfa a falon na samu wuri na rakube a kasa bashir na min ba, a ban amsa shi ba sai murmushi raina ba daddi ko kadan sabo da rabuwa akwai daci gare shi duk da a gari daya muke dai. Ya soma da addua bayan ya gama yace to Aisha yau dai zaki fada a sabon rayuwa duk da yake dai banda wani shakku akan rayuwan ki sai dai ki sani zaman gida ba daya yake da gidan miji ba. Yi nayi bari na bari da kika ji ana fada to shine aure aure wani bangare ne maigirma cikin bautar ubangijin mu. Don haka ki zama mai biyayya da sanin ya kamata ki gina rayuwan gidan ki da zurian da zaki samu idan Allah ya kawo su. Da zaki yi koyi da rayuwan yarki da kika zauna da ita zan iya cewa zaki iya zama da kowa a duniyan nan . Don kin dai ganni da yar uwar ki duk zaman ki a gidan nan damu bazaki ce ga rana daya da kikaji wani sabanin daya taba shiga tsakanina da ita. Kinga ashe idan kiyi kwatan kwacin halaiyar ta zance zaki zamo MARICIN KAN DUTSE fitar ka sai an daure. Dariya suka saka a falon Bashir yace sunan kaunar tawa ke nan ashe daddy yace sunan ta ke na a gare ni. Anyi baki anyi fari a gidan nan sai idan ka jefota a ciki take saka kan ta abinda bai shafeta ba koda ta gani bata taba saka kanta a cikin sa. Ga abokan zaman ta nan a gidan nan idan akwai ranan da tazo min da wani korafi a kan su dukkan su. Don haka yanzu kema zaki dora a inda ta tsaya don muna fatan har ki dara ta ga naki halaiyar da zakiyi a gidan mijin naki. Kuka take sharba a hankali shi kuma yaci gaba da magana yana fadin Zulfa da hindatu ga Aisha zata tafi gidan mijin ta yau ina fatan idan akwai laifin data taba maku zaku yafe mata. Sai ya juya gun Aisha din yana fadin Aisha ga yannen ki nan da kika zauna dasu ki toke su gafara bisa kan zama ko akwai wani sabanin da ya shiga tsakanin ki dasu su yafe maki. Zulfa ne tace Aisha kan ai mu fuka ba Rahama ba zamuyi missing din ta a gidan nan don Aisha ai yarinyar zamace gaskiya. Idan tana wuri dan ka baida matsala zaka iya fita hankalin ka a kwance ba wani damuwa gareka ko aikine ka saka ta baka taba jin bacin rai a wurin ta. Mama Altine tace haka ake son dama ka zauna wuri ranan barin ka aji bakin ciki ba ana Allah Allah dakai ka tafi. Aisha ta mike har gaban Zulfa tace anty don Allah ki yafe min idan akwai abinda nai maki a zamana daku a gidan nan. Tace Aisha nikan baki min komai ba in ma kin min na yafe maki har ga Allah taje gun Hindatu itama tace ta yafe mata itama din tace ta yafe mata. Zata koma ta zauna yace ga yarki nan baki roke taba sai ta nufoni tana zuwa tafada a jikina a take ita kuka nima kukan nakeyi. Cikin kuka take fadin Anty don Allah ki yafe min nace Aisha ni baki mun komai ba na yafe maki. Sai ta nufi daddy daidai kafan shi ta duka tana rusa kuka tare da rokon shi gafara cikin dauri yace Aisha na yafe maki Allah yabada zaman lafiya. Sai ku tashi mu tafi mama yace wa su mama Altine da mama Abu kishiyar Inna ta. Nan suka fita suka bar mu shi da bashir a gaba suna baya zaune su sai gidan mijin ta. Aisha yau ta tafi ta barni nida yara da kewan ta don zan iya cewa duk haihuwan da nakeyi Aisha ce tafini sanin zafin wahalan dawainiya da yaran iyakana dasu shan nono ko wani abin can na daban. Nasan ba niba har yaran sai suji kewar rashin ta a tare damu a gidan haka na mike na barsu nan zaune a na hira na nufi part dina. Kowan mu yayi kewar rabuwa da junan shi da dan uwa a ranan don duk abinda nakeyi ina dai yine kawai a ranan har dare. Washe gari baki suka fara tafiya garuruwan su da sannu duk gida ya watse aka bar mu mu kaida yadda muke. Amira raguwa ce don haka yanzu kusan Atika ce takoma jan ragaman part din nawa don ni kaina bana son ma na matsawa yar marainiyar Allah da damuwa kada Allah ya kamani da laifi. ********* ********* ********* Saida na huta na koma girki na sai dai abinda na kula dashi shine Niima bata taran ranan girkin ta koda yaushe idan daddy yana gida tana manne a falon wurin shi koda kuwa aiki yake shi. Na dawo aiki sai da nai wanka na shirya tare da daukan abincin daddy na kai falon na jera na koma ciki don na tsawata wa yaran da kada suyi fada kin san yara ba a raba su da fada a tsakanin su. Ban jima ba na dawo falon tun kan na karasa na hango kafanta kwance a saman dogon kujera shi kuma yana zaune a kasa yana dubar wayan shi. Mamakine ya kama ni haka dai na daure na shiga gun shi don dama bayan gani da ido naji sauran na korafin hakan da ita. Ban zauna ba sai na shige bedroom har na gama abinda nake a ciki na kwanta daddy bai shigo dakin ba kuma ina jin muryan ta. Can har na fara barci naji shigowan shi dakin yana fadin kwanciya kikayi ashe ban tankashi ba naji ya shiga bathroom don yai wanka. Tsam na mike zaune na hado komai nawa na bar mashi part din na koma wurina na saka sakata na rufe har dakina saida na saka sakata a cikin shi na kwanta a gefen diyana dake kwance. Da safe ina shafa mai sai gashi ya shigo dakin yana saye daga shi sai jallabiya a jikin shi. Fuskan shi babu walwala a cikin sa yake cewa dani a wani dalili jiya kika bar wueina kika dawo nan bada sani na ba ? Nace au tambayana ma kakeyi daddy ai na ga banice dakai ba shiyasa nabarwa mai girki wuri taci gaba da aikin ta. Yake cewa dani wanan wani irin magana ce haka kuma wacece mai girkin ban sani ba ? Nace wacce tazo debe ma kewa kasan ni ban iya ba wallahi daddy in dai don ka muzantani akan wanan yarinyar ne ba zan kara lamunta ba a gidan nan anyi na farko anyi na karshe. Bana shiga hakkin kowa daga cikin matan ka don haka bana son wata ta shiga min itama. Yo itama ta san yin hakan waye ba zai ita ba idan yaso don haka ta kama kan ta dani tun kan mu karasa saka kafan wando daya da ita a gidan nan. Yace yanzu dan zaman da tayi shine matsala kuma bata fada kowa da zai debe mata kewa tare da ita shiyasa take shigowa guna. Auto hakane ashe to shike nan ba hira ba har kwanan ma ku dinga yi a tare indai don ta Rahama ne na yafe aje akarata can. Dama na dade da sanin cewa baki damu dani ba Rahama ba sai kin fada ba ai nace ban damu ba kuma ba zan taba damuwa da abinda bai damu da nawa damuwan ba. Yanzu dai muje ki hada min ruwan wanka nace ai sai dai ita data fini muhinmanci ta karasa wanan duty din amma ba dai ni Rahama ba kuma wallahi. Yace kina son ki zarga min sheri ne ko may Rahama kike shirin yi ga maganar ki ? Wallahi ba sheri ga wanan maganan ni ba zan dauki a wullakan tani a kan wata ba tunda ban wa kowa haka ba ina iya kokarina wurin tsare doka ga kowa a gidan nan. Don may zaka zauna karamar yarinya tana son juya ka ka fada ga halaka da saboda tana takama ta iya yin kissa da kisisina watake zaton bai iya hakan ba ne. Don haka kaje dana zauna ka dinga wullakantani a gabanta gara na yafe na san ban jiba ban gani ba ku karata can kaida ita yafi mun sauki. Kara dan step yayi daga inda yake tare da fadin hummm sam ni ban dauki wanan abin a wani abuba a rayuwa na amma kowan ku yai min wanan korafin kan hakan . Duk macen da tasan darajan kan ta ai zata gujewa shiga hakkin wanj kada itama ai mata hakan watarana. Ba komai bane ka nuna mata cewa ita din tafimu daraja da kima a gunka shiyasa take ganin tafi kowa ne a gidan nan. Da sauri ya dan kallo inda nake ranshi ya baci yace Niimar ce tafiku daraja da kima a gurina komay ? Tafimu mana tunda a gabana kuma gaban ta ka shanya ni a daki kana zaune tare da ita kada ka taso ranta ya baci. Murmushi yayi yace kaiyya ita din har ita waye da zata ce tafiku a guna nace ita matar ka mana kuma amaryan da kake diban karfin kurciya a gare ta. Tsuki yaja ya juya rai a bace yana fadin wanan maganan ke kika san shi ni nasan abinda nakeyi kada ki maidani wani wanda bai san abinda yakeyi ba mana. Bishin nayi da kallon haushi naci gaba da shirina har na gama na fice tare da yara da nake kaisu wani nursery mai kyau da tsada. Ban dawo ba sai uku na rana naje gidan Fati na dauko yaran muka tsaya hanya nai masu sayayya su da yan uwansu na doso gida. Tun a haraban gidan nasa daddy yana gida ban tsaya bin ta nasu ba na kwaso kayan tare da kamo hannun yara na zamu shiga gida. Sai gashi fitowa daga ciki bin mu yayi da kallo don bai masan yaran sun fara zuwa makaranta ba sai ranan. Don duk yan uwansu ba a saka su ba tukun niko don fita aiki gashi Aisha bata nan yanzu yasa nakaisu karatu da wuri. Yaran suka nufe shi nai mai sannu na shige da ledojin dana shigo dasu a hannuna zuwa part dina. Ina daki naji shigowan shi da yaran wurina wanka nake son shiga don har na fara tubewa suka shigo. Yaushe ne yaran nan suka fara zuwa makaranta ban sani ba Rahama ? Yanzu kece mai bugun gaban kan ki a gidan nan kike nufi ko may don ban san may kike son dauka na ba. Ba wai makaranta na saka su ba saboda Aisha tayi aure isan na fita kuma kada su shiga damuwa yasa nake kaisu day care na wata yar shuwa data bude wurin ana bada kulawa ga yara sosai. Alright don banda hakki yasa ba a fada min ba aka kai min yara can ko nace dashi kayi hakkuri kawai batare da na sake wani magana ba kuma. Amma dai kin san yin haka zai kawowa sauran iyayyen yaran zargi ko wani abu ko ? Nace daddy yanzu shike nan kuma banda right din yiwa yara na komai sai na hada da na wasu komay ? Nifa wanan irin matsalolin sun fara isata daddy kowa yasan ina aiki yaran kuma suna son kula shiyasa na daure nakaisu can don su samu kulawa a wurin. Sai yaron yake ja mai hannu yana fadin daddy mun yi karatu alifun ba un da kuma cake muka ci. Yana fadi yana jan hannun uban nashi ya dan kai kallon shi ga yaron sai yaja su suka fita daga dakin . Wankana na shiga na fito na tayar da sallah ina gamawa na shirya na fito falo abinci na nema don ina jin yunwa a lokacin. Na zauna na fara ci ke nan yaran suka dawo sai dai su biyu suka shigo wanan karon. Zasu zauna nace su bari nai masu wanka don manyan basu dawo ba a lokacin mama ce kawai muke bari a gida helen ta koma kauyen zatai aure itama. Wanka nai masu na shirya su muka zauna cin abincin tare da su na dan fahinci tun bayan bukin Aisha akwai dan matsala agida namu don kowa yaja baya da dan uwan shi. Hakan bai wani damuna ba don dama na saba zama a hakan don shirin dama na iya baki ne kawai akeyin sa baikai zuciya ba . Muna gap da gama cin abincin ne daddy ya shigo falon ya sauya tufafin jikin shi wanan karon duk wanan sintiin da yake na fahince shi na lalashine kawai kan matsalan dake tsakanin mu dashi. Ban sake fuska ba sai naji yace dani may ye na ganki kuma rai a bace haka dake ? Nace batare da na dago ba may kuwa zai bata min rai yace har yanzu a kan wanan maganan kikewa fushi haka ko may ? Wani takaici naji a raina watau shi bai dauki maganan a bakin komai ba ke nan a gunshi. Takaici duk ya kamani nace fushin may zanyi aini nagama magana ta don na sallama mata kai kuje kuyi tayi can. Murmushi yayi yace dani Rahama dago kai ki kalleni mu gani idan kin salama wa watani da gaske ? Ban dago ba ya sake cewa dani dago kanki mana mu hada ido idan da gaske kike zan gani ai. Kin dagowa nayi don ma ba zan iya ba din don nauyi da kunya ba zai barni ba naji ya sake cewa dani maganan taki iya baki ne ke nan. Nace don Allah daddy mu bar wanan zancen tunda munyi shi tun safe mun gama banga dalilin dawo da zancen ba kuma. Shiru yayi nasan kallona yake a lokacin ya dan sauke ajiyan zuciya tare da kara takowa zuwa inda nake naji yace dani Rahama ina son ki sani daga yau bana son irin wanan maganan daga bakin ki a gidan nan. Laifi akai maki kuma kin fada ya wuce don haka ki tabbatar da zancen ya wuce ke nan ke ma wurin ki. Bana son ki na bari wani na fahintar halinda muke ciki don a kulun so ake aga wani dan baraka a tsakanin mu. Nace nasan da hakan amma dole ne na kwaci yancina a gare ka don ina gudun ai mun dariya zai sa na ki fadar ra, ayina ko may ? Tsaye yayi yana min kallon mamaki na dago kai muka hada ido ya sakar min murmushi na shuumanci. Nunani yayi da yatsa yana fadin ban taba sanin son da ake min ya kai haka ba sai yau din nan. Na dan kara kallon shi nace so fa so fa kace yace cikin daga giran shi yes so mana gashi kinga akan yarinya karama kina wanan haukan haka . Nace ba wai hauka bane ai yarinyar ne da son wuce wuri na fahinci bata da wayo tare da ita ban so shiga shirginta ba amma naga tana son ja danine a gidan nan. Yace amma shine ke zaki biye mata ku zama daya ko yaushe nace aida ace na biye mata da tuni ta raina kan ta ko a gidan nan. To naji bani son dai kiyi abinda zai kai ga zubar da mutuncin ki akan ta ki barni da ita ni da na dauko ta ni nasan halin kowan ku kuma. Don haka wanan maganan abarshi nace an barshi ya wuce sai dai idan an sake baza ai mai kyau ba kan . Yai min sai ya dawo ya fice sai da yara suka dawo na samu kaina na nufi part din daddy din ina tsaka ga aiki kamar ance na leka window sai na hango zulfa da Niima a tsaye suna ta faman magana a tsigar munafunci murmushi nayi tare da fadin kaico a fili. Tun wanan ranan na kara kama kaina da wani hafin kai na kishiya bana shiga harkan kowa a gidan nima na kuma lura da cewa ita Niima ta daina wanan tsagerancin da takeyi yanzu ko tanayi ba dai ranan girkina ba kan. Duk wani kumbiya kumbiyar su na gaiyar tsiya bai damuna don hassada ga mai rabo taki ne gareshi. Hindatuce nake ga kamar ba a gama sakata cikin shirin ba sosai don itama ta mayar da kan ta gun sana,ar ta. Wanan halin ba wani bakon alamari bane a gidajen mu tun fil, azal haka ake a gidajen hausawa masu tara mata. Da zaran anga kamar namiji ya doshi wani wuri ko yana dan tausayawa wata sai kiga saura suna hafin kan karya wanda ko su a tsakanin su ba wani son juna. Sai a ware dayan ace tunda miji na kulata ko tafi samu a rayuwa a barta a gefe daya wai ala dole sai ta zama borar gida da karfi da yaji. Sai dai abinda bamu sani ba warw ta a gefe dayan ne zai kara mata kwarjini da fada gun miji. Nikan a wuri na sai ma hakan yafi mun sauki don babu komai ga wanan irin hadin kan sai makirci da gulma kawai. Fahintar hakan yasa na gane ni din ke nan wata abune a gidan don haka maganan daddy gaskiya ne bari wasu su fahinci matsalan mu babban jin dadin kowan su ne. Haka yasa banda lokacin kowan su idan mun hadu dai sai a gaisa a wasance a wurin a wuce . Mun kai har zamuyi kwanaki mai dan tsawo bamu hadu ba a tsakanin mu sai ma zaman hakan ya fi mun dadi yanzu. Ranan daddy ya kirani a waya na samay shi a falon shi da safe na saka dogon riga tare da dan gyara fuskana na nufi wurin shi. Yana zaune ya baza wasu takardu a gaban shi nai mai sannu da aiki ya amsa ba tare da ya dago kan shi ba. Zama nayi daga gefen shi a kasa bayan na zauna ne ya miko min wasu takardu da akai banding a wuri daya. Na fara bin takardun da kallo sai na lura takarda ne na shedan wasu aiyuka a ciki. Sai naji yace ki duba da kyau ki gani takardun yaran kine na gadon su da uwarsu ta bar masu an juya su har sukai haka shine naga ya kamata yanzu na sanar dasu su san komai a kai. Kwandala ban taba tabawa ba daga ciki tun uwarsu na a raye har zuwa yanzu. Zan so naji ra, ayin su idan za, a rabane tun yanzu don ita Amira dake shirin aure idan kuma za, a barshi a hakane aita juta masu har nan gaba idan sun kara tasawa gashi nan dai. Kara bin takardun nayi da kallo na fahinci ba karamin kudi bane a ciki da kaddarori na yaran da suka gada a wurin mahaifiyar su. Nace Allahu akbar Allah mai hikima da basira buwayi gagara musali Allah mai yin yadda yaso da bayin shi. Ar, razaku mai azurta bayinsa a yadda yaso ga dukiya haka ga yaran nan amma kuma ya dauke mahaifiyan su a tare dasu. Ya Allah kabamu ikon tsayawa akan gadkitan ka mu gudanar da rayuwan mu a cikin sauki da kamala kowa da tashi irin kaddaran rayuwa da yake zuwa mashi. Samun mutum mai gaskiya da adalci irin ka daddy sai an tona a wanan zamanin wanan ba karamin baiwa bane mutum ya rike amana irin haka da wuyan samu a wanan zamanin. Yace Rahama ba zan taba mantawa da Saade ba a rayuwa don saade mutum ce ta fada a duniya a sanadin ta na samu abubuwan alheri da dama a rayuwana. Saade ta tafi ne amma tabar min alherin ta a duniya wanda ke kan ki kina daga cikin wanan alherin da ta bar mun. Dole ne na tausayawa yaranta na kuma godewa Allah da ya rufa min asiri ya hada ni dake kika rike mun su amana tanakar kece mahaifiyar su kika hana su su san maraicin uwa a tare da su. Rahama yadda kika tausa zuciyar ki ka rike min yara nan shine dalilin da har gobe bana kaunar naji ko naga na sabawa rayuwan ki don kin min abinda ba kowame zai iya wanan ba. Ban taba ganin banbanci riko ba tsakanin su da diyan ki saima nace kin fi kaunarsu akan diyan ki in ba zuwan su yan biyu ba wanda suma nasan son Saaden ne dani ya jawo kike masu shi. Don haka banda ma bakin godiya a gareki bani kaidai nai yaki ga hakan ba harda ke da kike bani gudun mawar kan yadda naga kina rikon su haka. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , 105 Ban san irin bakin da zanyi magana dashi ba kan wanan abin da daddy yai muna yai muna mana don kamar ni yaiwa hakan. Ya zama dole na samu daya daga cikin shakikan su na dangin mahaifiyar su bayan mama Altine na fada mata komai sai naga ya kamata kuma na samu wasu don su sani . Matsala daya ne yanzu shine yan uwan na marigayi tun rasuwan mahaifin nasu kan gidan ya karasa watse masu kowa tashi ta fishe shi suke. Ko sisi baka sayen su yanzu duk sun wullakanta dan abinda aka bar masu na gado a wurin su. Karshe dai naga Sadiya ya dace na gani don ita tana da dama mijin ta kuma na da dan abin hannun shi ai. Tunda ba wai dukiyan za a danka maasu a hannun su ba kawai dai su sani ne cewa ga halin da ake ciki da dukiytan yaran don fita daga zargi. Labarin dukiyan da sauran matan daddy sukaji ya tayar masu da hankali don sunce basu yarda ba da zancen shi dai wani hadin kaine mukayi a tsakanin mu da daddy don a fitar da wani kaso daga dukiyan shi a inganta rayuwan yaran su kadai don ni na riga da na inhanta na yarana ba sai sun jira want gadon mahaifin su can ba. Tun Ana kumbiya kumbiya maganar har zancen ya Kai kunnen daddy yaji don yar rashin kunyar matarshi ce to fito mai da zancen gaban shi. Abin yai matukar bata mashi rai sosai har yakai ya tara mu a gaban shi ni dai ina falona don ina up a wurin aiki ban fita ko ina sai gashi tunda safe daddy ya kirani a waya na samay shi a falon shi. Ban kawo komai ba a raina na shirya dama a shirye nake dan gyarawa kawai nayi. Duk kan su suna falon kowacen su ta hakkince a zaune cikin nata kalar shigan sai shi may gidan da alama ya nuna ko wankan shirin fita baiyi ba a lokacin. Da mamaki na karasa cikin falon tare da sallama da fargaban may kuma ya faru haka son ruwa baya tsami banza a hakan. Ina shigowa ya dago kai tare da sauke idanuwan shi a kaina yana mai amsa sallamana. Na samu wuri na zauna can daga karshe nace gani daddy lafiya dai ko ? Da hannu ya nuna min na zauna na karasa kaiwa zaune din ina mai kura mai idanuwa na don ban bi ta kan kowa ba dake falon a lokacin. Shiru falon yayi can ya dan nisa tare da shafo fuskan shi yace na kiraku ne don wani magana da naji daga bakin wanan yarinyar ya nuna inda Niima take zaune da fuskan shi. Sai kowan mu ya gyara zaman shi don jin may ya faru kuma haka yaci gaba da fadin daren jiyane ta fuskance ni da wani zancen da ya kona min rai a gidan nan akan yaran nan marayu da Saade ta bar min ko nace ta bar mu dasu. Daga inda nake zaune nace tau fa ? Yace eh tazo min da zancen wai ita bazata yarda ba sai itama na bata kudi kamar yadda nake bawa kowa a gidan nan don har su Amira da Nasir na ware ma makuddan kudi daka jikina na basu a matsayin kyauta don tallafawa rayiwan su. Kuma ba kowa yasani yin haka ba sai Rahama don tana bakin ciki na mutu a raba gado kowa ya samu yasa ta bani wanan shawaran Take naji raina ya yi mugun baci nace a hasale wai wanan matar may kike so danine a gidan nan wai ? Yace dani dakata hakana magana nake yi sai nai shiru tare da komawa na zauna da kyau. Yace maganan ya bani matukar mamaki don ban san ina ta samo wanan zancen nata ba haka ? Ya juya gunta yace Niima jiya da kike min wannan magana kikaga na yi shiru akwai abinda nake tunane ne bawai na kyale ki bane hakana sai kuma kyale kin da nayi ya bani daman karasa sauraren abinda ni ban sani ba a gidan nan. Kafan ta take kadawa a hankali yayin da tai tagumi da hannun ta daya tana mashi wani irin kallo mai kama da tsanane ko haushi ? Yanzu ina son ji daga bakinki a ina wanan maganan yafito maki haka na ki fada muna ke muke saurare. Sai tai shiru tunda naji Zulfa tace da ita ke Niima may yakaiki yin wanan maganan don Allah nasan akwai wata a kasa in baki manta ba mai karatu Anty marigayiya tasha fada min cewa nai hankali sosai da Zulfa don munafukace ta gaske amma a zatona ta daina halin nata ne yanzu girma yazo mata . Muryan daddy yadawo dani daga tunanen da nakeyi naji yace ke muke saurare fa kada ki shanya mu anan ? Shiru tayi sai ya dan gyara zaman shi da kyau yace saurara kiji wallahi kinji na rantse maki ko ki fada min ko yanzu ki raina kanki ga hukuncin da zan yanke a kan ki. Don duk wanda har yake jiran ka mutu yaci gadon ka to kuwa zai iya kashe ka ya kaiga manufan shi a tare da kai. Tace nima ai fada min akayi gadon ka kuma ai ba ni kadai ke jiran ci ba don duk wacce ke tare dakai shi suke jira suma. Ko don an fini wayon iya gilibibi yasa nawa kawai za a gani don nai magana kawai. Hindatu tace ke ki iya bakin ki don mu ba mayunwata bane irin ki sai ta watsa ma hindatun harara tace shi kan shi ya sani ai . Badon cin gadon akace Rahama na haihuwa akai akai don tafi kowa kaso ba a gidan dariya maganan ta ya bani ban iya magana ba don ya kwabe ni da farko nasan ko yanzu ba zai bari na sake wani maganan ba ma. Yace ai saiki fada muna wanda ya fada maki tace akan may zan fada don an raina min za ace don nai magana da kai za a zo a tsureni gaban kowa nai magana. Da suke siri dakai tsuresu kakeyi ko may dani za ai min hakan don raini. Wani uban tsawa ya daka mata sai data dan razana yace zaki fada ko yanzu na zartan da hukuncin da nai niyya a kan ki don ba zan iya zama da macen da ta iya fitar min da zuciyar ta damanufanta ba haka a fili. Jin abinda ya fada yasa tace a dai muna hukunci da wacce ta fada min don nima daga bakin uwar gidan ka na samu labari. Da sauri zulfa tace ke kada ki fara ki min sheri wallahi ko don yanzu za a jimu dake a gidan nan. Tace sherin may zan maki bake kika fada min ba kikace duk yadda zanyi na kawar da Rahama a gidan nan nayi ko bata fita ba ta koma ita da babu duk daya. Daddy yace kinji Zulfa kinji yanzu abinda ta sake fada ko Niiman tace ai ba kazafi nai mata ba. Kince kudin shi Rahama ke komai dashi tana labewa ga aiki take samu sai abinda tace ake kuna kallo a gidan daku da yaran ku kamar babu ku a wurin shi. Daga inda nake zaune nace Allah na gode ma da baiwar da kai min ka rabani da hassada a rayuwa na. Nace Zulfa ai kun riga da kunyi sake diyar zakanyya ta girma sai hakkuri yanzu don haka munafuncin ki da hassada zai sa ki tabbata a boran ki har abada don babu mai iya sauya ma wani hali shi sai Allah. Don da zaki daina munafunci a bayan ido zama dani dayasa kin daina ko tuntuni may yafi nan kunya ki zauna da yarinya karama kina gulma irin haka don hassada kawai da bakin ciki. May na rage ki dashi na mutuntawa a rayuwan zaman mu dake ba yau ba na sani akwai wanan ranan yana tafe gun munafuki ai. Kada ki kara kirana da munafuka Rahama karya ne may Saade din ta bari da za, ace wai gadon yaran tane wanan kudin da ake fada. Tace dakata gaskiya dai ya baiyyana yanzu kundai yi maganan da Niima ke nan a gidan nan ko ? Tace munyi sai dai ba yadda ta fada ba aiko hindatu ta sani da sauri hindatu tace da kukazo min da maganan may na fada maku ni ? Ba cewa nayi yanzu na gaji da wanan halin ba abinda ke gabana ya isheni kuma ke Zulfa na fada maki Rahama bada tsiya take nufar mu ba kibi a hankali koba haka mukayi dake ba. Tace yanzu ko da maganan ya zama haka amma aiko ke da cewa kike don tafi kowa kaso take haihuwa akai akai haka a gidan nan bake kika fara fada ba. Tun fara cacan baki a wurin ya dafe kan shi baiyi magana sai da yaga abin bana karewa bane yake cewa damu. Kai ya isheni haka na yanzu na gane inda maganan nan ya fito don haka dake da kika fada min da ita data fada maki duk hukuncin da zan yanke ya hau ka ku. Zulfa ba zanyi duban irin zumuncin dake tsakanina dake ga don na fahinci duk wani tsegumi na gidan nan daga gareki yake fitowa don haka dake da Niima ku saurara da kyau kuji. Kudi dai banawa bane bana Rahama bane dukiyan yara ne da nake juyawa na uwar su tun tana a raye kamar yadda ta dauki amana tabani haka na rike wanan amanan har shekara goma sha tara ina rike dasu a hannuna. Sune yanzu ganin yaran sun kawo hankali na fara gabatar masu da dukiyar su don su san dashi a gare ni. Rahama ga tanan a matsayin ta na mata na dake rike mun yaran ita na fara gabatawa dukiyan yaran. Sai Allah ya taimake ni ta bani shawaran da ya dace akan na kafa hujja da yan uwana da kuma yan uwan mahaifiyan su. Nasan kuma zaman da mukayi da su a kano har yasa kuka samu wanan labarin yazo gare ku. Amma da yake baku da tsoron Allah a tare daku ita da ta taimaka min ta bani mafita kuka dauki sheri da zargi kuka saka mata dashi. Mai son abinka har rayuwan ka yana so idan ya samu don haka bazan taba iya zama da irin mutanem nan ba a rayuwa na . Ya fadin haka ya mike daga inda yake zaune yace ku bani wuri don Allah zan shirya ni. Nice ta farkon mikewa a nan zabbar kunya na barsu su uku suna cacan baki a tsakanin su ina shiga wurina wani kuka mai sosa zuciya yazo min a lokaci daya. Ban fito ba sai da lokacin zuwa dauko yarana makaranta yayi naiwa mama Sallama na fita daga gidan gidan yai shiru ba motsin kowa ko irin kidan da kakeji yana tashi a part din Niima yau babu shi a gidan ko kadan. Haka na fita daga gidan naje na dauko yaran muka juyo zuwa gida muna shiga ne na hadu da wata kawar Niima zata fita tabini da kallo ban kula taba na shige abina. Naiwa yaran wanka muna zaune ina basu abinci sai ga daddy ya shigo wirin mu nai mashi sannu da dawowa yake cewa da shi. Yaran har sun dawo ashe nace eh yanzu na dauko su yake cewa zan tafi lagos yanzun nan tafiyan ya kamani sai dai kafin na dawo na fadawa Zulfa da Niima su bar min gida don haka ina fada maki ne babu ruwanki da zancen su kuma. May hakan ke nufi da subar maka gidan ka dakace dasu yace maganin kiyayya nace rabuwa. Yace dani to na rabu dasu duk su biyun ba zan iya zama da masu son rayuwana ba, don ni dukiyana na nemawa iyalina rufin asiri ne banga abinda na rage wata daga cikin ku dashi ba da har suke jiran mutuwa don na bar masu dukiyata suci. Ita Zulfa yanzu zataci na diyan ta idan na mutu din ita ko Niima ta tafi da abinda ta samu a wurina a yanzu. Daddy don Allah kayi hakkuri da wanan zancen haka na kowa da halin sa ake zama dashi ai. Yace naki ra, ayin ke nan nikan ba zan iya zama da masu son rayuwana ba. Yana fadan haka ya fice daga part din nawa da kyat na bude bakina daga kalkon mamakin da nake mai nai mashi Allah ya tsare hanya. ********* ********* ********* Zulfa kan bai dawo ya samay ta a gidan ba don ta tafi kano tun washegari sai Niima ce taki tafiya kamar yadda yaba da umurni. Ya dawo ya samayta a gidan yai mata cin mutunci badon taso ba dole ta bar gidan kamar yadda yace din. Da dare ina gurin shi yana cin abinci sai ga wayan hajitan shi ya ahigo mai suka gaisa suna gama gaisuwa da ita take tambayan shi dalilin turo Zulfa gida dayayi don gata sun samay ta da uwarta. Yace eh hajiya nina sallamay ta don ba zan iya zama da ita ba haka laifi sukai min kuma na riga da na yanke hukuncin duk wanda ke da hannu a wanan maganan zan dauki mataki gare shi ko wanene tunda ba son Allah da Annabi suke min ba. Kai Alhaji ka saurareni da kyau babu abinda zaka boye min yanzu kai bakiji kunya ba akan wata bare can zaka sallami yar uwarka ta jini. Yace hajiya wacece baren da na sallamay ta akan ta tace maku ? Waye banda Rahama da ta gama da kai baka ganin kowa da gashi in ba ita ba da diyan ta a gidan ka. Wayan na a handfree don haka na mike tsam don na bar falon yai min nuni da hannu don na dawo na zauna. Banki ba duk da ban so ba kada naji abinda raina zai baci gareshi naji yace amma hajiya yanzu in ga halarci ai Rahama ta wuce bare a wurin mu tunda na haihu da ita har diya biyar. Dama shine gurin ta ta mallake ka da gida ka shiyasa taita haihuwa kamar bera nida naga sugar mai iyali ana nuna min zazagan hanji. Yai murmushi yace hajiya sai dai ayi hakkuri na riga da na yanke hukuncina a kan su ba abinda ya saura yanzu. Tace baka isa ba aiba kai ka kawo kanka duniya ba zan dawo da Zulfa idan ka isa ka dawo min da ita nan mu gani. Yace hajiya gidana ai gidan ta ne tazo ta zauna idan zata iya ga gidan nan gata. Daga haka sukai sallama ta kashe wayan tana ta fada dashi sai lokacin na nisa nace dama nasan duk laifin a kaina zai dawo ai. Yace hado min passport din ki dana yara yanzu ki fadawa hindatu kuma ina neman ta shiru nayi sai naji yace dani badake nake bane. Na mike na tafi hado mai passport din dayace daga can na tura akira mashi hindatun daya yace don mu biyu muka saura a gidan. Kamar yadda ya fada min haka ya fada mata nakawo yasani daukan permision a wurin aikina ba kakautawa suka bani. Kwana uku yazo ya ce mu shirya zamu tafi London da yara ita kuma hindatu zasu tafi italy da yaran ta. Hakan akayi muka tafi hutun dole ga Zulfan ta dawo da yan uwanta da da suka rakota nan muka barsu a gidan muka tafi. Wanan abin yai matukar bata masu rai sun kwana biyu suna zaton zamu dawo maigadi ke fada masu cewa ai bamu ma kasan gaba dayan mu gidan mun fita waje. Haushine ya kama hajiyan ta tace su dawo kano har mu dawo maigadi ya rufe gidan bayan tafiya su. Wasa wasa sai gashi mun kwashe wata uku a can hakan ya bani dama yin couses di da nake son yi. Allah ya taimake ni a wanan tafitan kuma gurin Nasir ya cika ya samu gurbin zuwa yin ilimin na sojoji a can don dama shine burin mu a kullun da mun dawo zai shirya ya koma tunda sun kammala karatun su. Airen Amira da ya taso ne ya dawo damu gida duk da ba a kasa daya muke ba kusan a lokaci daya muka shigo su hindatu sun dawo da kwana uku muma muka iso kasan shine bai samu dawowa ba a tare da mu. Mun dawo da Sati biyu muka kwasa sai kano don a can zamuyi bukin Amirah saboda yan uwa gana mahaifinta dana mahaifiyan ta kowa nason ganin auren ta. Kwanan biyu muka shiga gidan su daddy gaida hajiyan shi fuska a daure take amsa muna gaisuwan mu. Hakan bai damay ni ba don ba bakon alamari bane yin haka a gareta sai bayan mun gaisa ne ta mayar da hankalinta ga jikokin ta ta share ni nima ban dade ba namike ina gyara gyalen dake jikina ina fadin zamu tafi tace dani yaran ma bazaki barsu mu gaisa ba dasu zaki kwashe su ki tafi. Ki sani dai yara jinane ko kinki ko kin so dole dai a kira su da jikokina idan kuma rabasu dani zakiyi don kin iya raba anta da jin shi ke sai mu gani. Nace hajiya ayi hakkuri idan zasu zauna sai na barsu don ni akwai inda zan tafi dama nai mata sallama natafi tana bina da bakaken magana. Gidan Zarah na nufa mun dade muna hira da ita wayan gajiye ne ya isheni na dauka take ce min ga yara an dawo dasu daga gidan hajiya tun dazu suna kuka. Nai murmushi don dama nasan bazasu zauna ba ai son fitina ne irin na hajiya kawai dani yasa tace nabar mata su. Nadawo ne jinior ke fada min irin zagin dataita masu wai sn biyo mugun hali irin na uwarsu shiyasa basu san kowa ba a dangin su ko sunki ko sun so ita dai ce kakar su don ita ta haifi uban su. Nai dariya nace ai tana da gaskiyan ta watarana ma acan zai kaiku ku kwana wurin ta jinior yace wallahi basu zuwa nace yaro dole ku tafi ai. Niji dadin zama kano da mukayi kwana biyu don muna ta ziyaran yan uwa da abokan arziki wurin raba kayin buki. Daddy bai shigo kano ba sai ana gobe kamun Amira ya shigo garin da dare don haka da safe ya shiga gaida mahaifan shi. Har gidan su Zulfa ya tafi wurin mahaifiyar ta kamar yadda ya saba nan ta tutsiye shi tana fada wai yana wa yar uwarshi wulakanci saboda bare. Murmushi kawai yai mata ya mike tare da aje mata abindaya saba aje masu ida yazo gaidasu. Yaran shi yaja suka fita sun dauka zasu dawo sai gida ya nufa dasu don sai daya biya wurin hajiyan shi suka gaisa itama din dai fadan tai mashi bata gane komai ba a gareshi. Muna nan sai gashi ya shigo da yaran gidan part dina ya nufo dasu yana fadin ga karin baki kin samu kuma. Na dago don naga bakin sai naga yaran Zulfa ne ya shigo dasu gabana yai mugun faduwa amma a fili na nuna farin cikina ga ganin su. Nan muka zauna da yaran suna ta jin dadin ganin yan uwan su har dare naga bai ce yaran su fito ya mayar dasu ba gida. Ban yi magana ba sai gashi ya shigo da dare yake cewa wanan ta bugo maki waya ne na tambaye shi wa ke nan fa ? Yace Zulfa mana nace wayan ma baya hannu na ai yana ciki yana charge wata kila ta kira ban sani ba dai. Yace yanzu hajiya ta kirani take tambayana yaran nasan sun tafi gunta ne da tsegumin su da suka iya. Yara ne kuma ba zan maida mata su ba sun dawo gida ke nan don ba zan barsu a can ba su lalace da mugun hali. Yana gama magana kiran wayan ta na shigowa gare shi again ya dauka ba ko sallama yake cewa da ita lafiya wai ? Idan kirana kikayi akan yara ina son ki cire su a ran ki don ni na karbi yarana daga hannun ki daga yau. Bai jira a binda zata fadi ba ya kashe wayan shi yace dani ki basu wiei su kwanta nan da yan uwan su ba dama nai magana amma duk da haka sai da nace to amma daddy, , , Katse ni yayi dacewa ko ba zaki iya rike min su bane na sani shiru nayi ban tanka shi ba yace idan baki iya rike min su zan kwashe su na kaiwa Fatima ko Aisha su zauna a wurin su. Nace akan may daddy ba zan iya rike ma jinin ka ba koda kuwa sun fi nan yawa ne kawai dai gani nayi kamata yayi kayi hakkuri uwarsu ta dawo hakana ta zauna dakin ta. Kada yin hakan ya jawo maku matsala irin na zumunci a tsakani ai yanzu ta gane kuren ta ko. Rahama ina warning din ki a kan zancen nan tun farko don haka ki iya kan ki daga shiga zancen. Allah ya baka hakkuri bai ce uffan ba ya juya ya fice daga dakin ran shi a bace nabi bayan shi da kallo har ya bace min na juya ina kallon yaran dake barci tare da sauke ajiyan zuciya. Don nasan cewa wani sabon aiki da rikici ya samay ni kuma ke nan in ba son dora min laifi may zai hana shi shiryawa da uwarsu ta dawo ta rike yaran ta da kan ta . Mikewa nayi na gyarawa yaran kwanciyan su tare da sauran yaran na samu wuri na kwanta nima don da safe nasan ban da wani sauran time din kai bakine zasu fara shigo muna ta ko ina. Tun da safe Zulfa ce da mahaifiyar ta tare da su mama hanne autan su hajiyan daddy sukai muns sallama a gidan. A lokacin yaran sunyi wanka suna zaune suna karyawa koma su nuna sun ga iyayyen su a gidan basu nuna hakan ba sam. Mun gaisa da su sama sama don fuskan su babu annuri a cikin sa ko kadan a lokacin sai wani daurewa da suke min kawai. Bayan mun gaisa ne mama hanne take cewa dani ko may gidan ya fito ai muna iso gun shi nace da Jinior ya fadawa baban su ga su mama sunzo . Bayan fitan yaron ne mama zulai mahaifiyar zulfa ta dan nisa tare da fadin ikon Allah ke kuma naki sallon yaidaran ke nan ki kore iyayyen yara ki sa miji ya dauko maki su a wurin ki don wani manufa na sheri. Murmushi nayi nace ni kaina ai ba daban nake ba a gidan balle na saka shi yin abinda zai cuta mai ko wata a gidan nan mama. Nima mace ce mai haihuwa idan na saka shi yin haka watarana nima haka za ai min a kan diyana ai . Ga Zulfa nan idan tayi fada dani ko wani abu da har yasa na jawo barin gidan mijin ta da yaran ta ta fadi yanzu a ji. Idan ma laifine ni akaiwa laifi amma hakan da sukai min bai damay ni ba a rayuwa na don ba shine farko ba a tsakanin mu da ita. Wanan dadin bakin ne kike cin mijin naku dashi ai ko yaushe bai iya fahintar komai akanki idan bake ba baya ganin kowa da gashi a idon shi. Yara dai ne yau sai na tafi dasu in ma tarbiya ne ban dashi a gida na da har yaje ya dauko su yakawo maki ke uwar iya tarbiya ba zan dauki wanan rainin ba ni. Mama kada kiga laifin Rahama a cikin zancen nan don ba ita ta dauko yara ba ni mai abu na dauko su na kawo mata su da kaina ba don ta so ba ita ma. Mara kunya kai yanzu bakajin kunyan kare wanan mayaudariyar da ta gama da kai da matan ka yara dai ne yau da su zan tafi ba zan bar gidan nan ba sai da jikokina tunda kai ka zama sallamamay namiji sai abinda ta saka kakeyi a rayiwan ka. Kana ganin don ka wullakanta yar uwar ka kamar kayi abin kwarai ke nan ko may kake ganin kayi zama da kai a gare ta ai bai zama dole ba ko ? Haba mama don Allah ki bari abi zancen nan yadda ya dace shiyasa nace kada ma ki zo kika nace da sai kin zo din. Yara dai ba ita ta haifa ba ta tsaya a iya wa yanda ta haifa ma tayi iko dasu ba wanda bata haifa ba ta bari idan ta kashe uwar su sai ka kwaso ka kawo mata din amma ba yanzu ba. Mama nifa ban yi fada da Rahama ba don da abin ta na ta tun ranan da abin baikai hakan ba ma da kuma ina bin shawaran ta na kama kaina duk wanan abin da bai faru ba dani. Ke dallah rufa wa mutane baki wawiya mara wayo kawai kishiya ce har zaki tsaya kina wani yabo haka don rashin sanin ciwon kai. Mama don Allah ki bari abin zancen nan yadda ya dace a fahinci juna ba wai hakan da kike yi ba mana don Allah dai. Mama gaskiya Zulfa ke fadi gyara ya kamata ayi ba wai hakan yadda kikeyi din ba don shi babba gyara aka san shi dashi ko ina. Ban iya gyaran ba sarki iyayi da munafunci ki mun shiru ko yanzu naki ya samay ki a wurin nan don ke yar kauye dake kin yi kadan ki fada min abinda ya dace nayi kiyi da wa yanda basu san ciwon kan su ba ga sunanan a gaban ki. Daddy yai murmushi tare da kaiwa zaune yana cewa to yanzu kin gani ai zaki kama kan ki na fada maki tun farko ki barni da yan uwa na kuma matatace ni na san mafita da sauki ga kaina. Amma akan zancen nan na zulfa da zan biye maki da yanzu mun samu matsala dake akan damuwana da kike yi ta dawo dakin ta a hakan ne mutum yai laifi ba a tsawata mai ba ake son wai na mayar da ita gidana. Nan gaba idan ta tashi min wani kullin kuma sai yafi wanda sukai min ke nan a baya ni da diyana dana haifa kafin su kashe ni su kwashi ganima ni zan fara ganin nasu bayan tukun. Sai mahaifiyar nata tace Allah bai yarda kaga bayan diyata sai dai taga nata nan dai taita sake bakaken magana inda take shiga ba nan take fita ba shi kuma ya kafe akan ba zai ba da yaran ba ya dauko su ke nan gidan shi. Text ne ya shigo min a waya ina dubawa naga Zulfa ce take cewa dani na bawa maigidan hakuri na tura mata cewa mu bada tare yanzu a gaban kowa a wuce wurin. Itace ta fara mikewa zuwa gaban shi ta tsugun na sai nima na mike na yi kamar yadda tayi tare da fadin don Allah don annabi duk abinda zulfa tayi a yafe mata kaddara ne insha Allahu ba zata sake ba da yardan Allah. Kuka sosai zulfa din keyi itama tana rokon shi da ya yafe mata don Allah mama hanne ne tai magana yadda mukayi hakan itama tayi takai kasa tana fadin don Allah Alhaji karami ka yi hakkuri ka mayar da zulfa dakin ta ta zauna da iyalin ta. Shiru ya dan yi tare da sadda kan shi a kasa ya rasa abinda zai fadi a wurin ita ko mama Zulai sai jikin ta ya mutu ta kasa ci gaba da fadan da takeyi. Mama Hanne ta ce Rahama ko ba komai ni dai yau kin fitar da duk wani zargi a zuciya dama zulfa ta fada muna komai yadda kikai masu shawara da su kama kan su da wanan shedaniyar yarinyar da ta shigo cikin ku amna tai biris taki daukan shawaran naki Yanzu may gari ya waya wa aka bari a cikin maganan ba ita ba da take fama da dacin rai akwai abinda yafi zafi da kunya ace ka dawo gidan ku da zama ka kashe auren ka bada son ran ka ba. Mama zulai ta bani mamaki da naji tace Alhaji karami kayi hakkuri bacin raine dama ya kaini ga hakan yadda ka rufe ido kaiwa yar uwar ka sai nake ganin ba don kowa kai hakan ba sai don Rahama don muna ganin burin ta ne na ta zauna ita kadai ya kai kai masu hakan da kayi. Har lokacin baiyi magana ba da kowa yana duke da kan shi yayi shiru kamar mai nazari sai mama hanne ta sake cewa ni wanan abin ma da yaya tayi kunya ya bani don a tsakanin mu bai kamata haka ya kasance ba kan diyan mu. Ga zahiri mun gani zulfa bata da gaskiya a cikin maganan nan amma kuma zafin rai ta hana mu ganewa kai babba ne kuka kai keda ragamar aure a hannun ka don haka don Allah kayi hakkuri da yar uwar ka ku zauna lafiya. Ai yanzu in kunne yaji gagan jiki ma ya dauka don ta zauna gidan nasu taji abinda ke cikin sa in har wani abu ke rudin ta dama da take hakan. Iska ya furzo tare da dago kan shi idanuwan shi sun kade sunyi ja jawur dasu yace da mama hanne din. Mama a matsayin ku na uwayena da banda wasu bayan ku idan nace ban hakkura ba a yanzu ban kyauta maku ba. Amma a gaskiya irin yadda mama zulai tazo min koda borin da zatai min yafi hakane na riga da na yankeyank yanke shawara zulfa ba zata dawo gida na ba da sunan aure. Da sauri mama zulai din tace kada kai muna haka don Allah nima ai na fahinci itace bata da kan gado yanzu. Yace yanzu ai tunda ta fada da bakin ta komai ya wuce zata iya dawowa dakin ta ta zauna sai dai ba zan tafi da ita Abuja ba kuma. Dama ga ta nan ya nuna ni da hannun shi inda nake tsugun ne a gefan shi kamar mai neman gafara, yace itace ta matse ni akan sai na tafi da ita can ni kuma na riga da na san halinta kamar yunwar cikina kan sari ka noke. Duk wanan dadewan da kukaga tayi can don ita Rahamar ba mai tafiya da magana bane inda ta fada nan zata bar shi. Shiyasa zaman nasu har yai dadi amma data amu irin ta kinga ta zauna ta zubar da kanta gun karamar yarinya ga banza. A daiyi hakkuri yanzun ai tasan ta duniya kishiya ko wacce ka san tane sosai ina kake daukan yarda gaba daya ka bata balle wacce ta san ta shigo maka a bakuwa. Ya mike yana fadin shi zai fita adai ja mata kunne ta yi hankali don idan ta sakw zasu hadu fiye da hakan. Nan ya fice ya barni tare dasu sai kuma aka koma bani magana ana wai idan naga tayi abinda ba daidai ba na dan rika saka ta a hanya. Nace mama ai a bar zancen girma a wurin miji a girmay ta girmay ni sosai ma ba kusa ba ita bata lurar dani ba sai nice zan lurar da ita ta dai gyara halin ta kawai shi yafi. Munyi sallama dasu akan da dare zasu dawo da ita dakin ta ayi buki da ita nai masu rakiya suka tafi zar kunya dasu. Koda daddy ya dawo lokacin baki sun dan cika gidan na samay shi a dakin shi zaune saman gado na gaidashi da dawowa ya amsa min. Yana cewa ashe har gida ya fara cika hakan ne da baki don naje shiga naga mutane sun cika wurin. Nace hakane sai dai ai gidan baya cika idan matan gidan basu kammalu ba baki daya don Allah daddy tunda kayi hakkuri da Zulfa ta dawo itama Niima ai mata hakkuri ta dawo haka ai yanzu sun horu ko sosai. Wani irin kallon yai min tare da fadin wai ke rahama wata irin yarinya ce mara zuciya haka duk abinda matan nan sukai maki baki gani ba sai wani rawan kai kike wai su dawo dakin su. Halin su na nan ba wai sun canza bane don haka ita zulfa zan yi dubaiyya akan zumuncin da diyan dake tsakanina da ita ne kawai amma ita wanan da kike magana yanzi fada min riban da na samu a cikin auren ta dana yi. Dama kaddaran aure ne kawai dake tsakanina da ita yanzu kuma Allah ya kawo min saukin bacin ran da nake zaman yi da zama da ita. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE, , , , 106 Kafin wani lokaci gidan ya fara cika da jama, a masu zuwa buki don haka banda wani lokacin kaina don yawan jamaan da suka taru. Daddy bai shigo ba tun fitan da yayi da safe muna tare da su zulfa sai ga hindatu ta shigo tana fadin waiko kin san Zulfa zata dawo gidan nan kuwa? Don ga ya can naga an bude part din ta ana ta gyara tundazun kinga namiji ko munafuki dubi yadda yake tayar da jijiyoyin wuyan shi a baya amma ashe har sun shirya ba wanda ya sani. A raina nace gaji kishiya ko nice ma haka zatai bakin ciki da dawowa na gidan sai dai a fili murmushi nayi nace da ita kin sai ai tsakanin miji da mata dama sai Allah. Balle su da suke yan uwa kin san dama ai da wuya su rabu ko ba iyali a tsakanin su balle ga iyali a tsakiya. Tace ke dai dama munafuncin maza ba karewa yake ba shiyasa na dawo daga rakiyan namiji yanzu indai bai shiga gona naba yaje can yai tayi balle na miji irin namu mai son tara iyali haka da yawa in bashi ba mu biyun nan ma bamu isheshi ba don Allah dai ? Mamaki ta sake bani nace da ita kai maman ihisan ke nan da wani zance a tare fa muka samay su duk dake da ita ba wani tsaraiyya a tsakanin ku. Amma nikan ko ajikina idan ma wasu zai karo basu zasu dawo ba duk daya a gare ni tai min kallon mamaki don jin abinda na fada mata. Tace haka dama zaki ce ai na sani don ke kin iya boye abu a zuciyar ki ba irin mu bane masu fitarwa duniya ta sani. Dariya ta bani nace to yanzu da ace na saka a raina wa aka bari a cikin zancen don haka kinga ai gara dai mutum ya tsaya a matsayin sa kamar yadda kika ce yanzu. Nifa ban sa akai balle nauyin zancen ya damay ni a zuciya tace ai kin huta wa ran ki wallahi yanzu haka zata dawo babu ko kunya a idon ta. Mamaki tabani nace a raina lallai manya sunyi gaskiya laifi tudune ka take naka ka hangi na wani ke nan ita ta manta da lokacin nata harda sakin ? Ta mike har ta fara tafiya ta juyo tana fadin yanzu kuma nasan ita ma wanan fitsararar itama dawowa zatayi ke nan ko ? Ai dai yanzu mai daki shiyasan inda ruwa ke mai yoyo don shi ke da kayan shi ba wani ba in dai mutum ya shiga gonar ka shine ba zaka kyale ba. Tace ke ai zaki iya sai ankai inta,ha zaki tankawa mutum amma nikan gaskiya yanzu da sake sosai a wurina wallahi. Allah dai ya sauwaka nace da ita ina murmushi bata fahinci komai daga wuri na ba ta fice tana bakar magana da akan mijinta da matan shi. Daddy bai iya shigowa wurin na ba don jama, a da sukai yawa a gidan don haka na shirya mai dan abin tabawa na samay shi dashi a wurin shi. Kamar kullun yana zaune yana fama da laptop a gaban shi na shigo da sallama dauke da kayan abinci na dire a kasa gaban shi sai dana aje na samu wuri nai mashi sannu da zuwa. Ya dago kai ya dan kalle ni yana fadin ashe kin san na shigo nace dashi yara ke fada min don dazun na tambaye su suka ce dani baka dawo ba. Gidan naku ne naga ya cika da jama, a ko ba zan iya shiga wurin ku ba nace aikuwa mata ne dam a gidan namu. Dama ku ai buki ne harkan ku a taru ana gulman kayan jikin ko wace da ta saka ba wani abin yi sai wanan din. Dariya nayi na gyara zamana ina fadin ga abin tabawa nan ka dan taba ko kadan ne baiki ba naga ya ture kayan da yake aiki dasu a gefe daya. Ya sauko don ya fara cin abincin dana kawo mashi din ganin haka yasa nai saurin saukowa daga kujeran na fara zuba mai a plate. Ina gap da gama zuba mai ne naji yana cewa naga wurin Zulfa a bude mana ko yau ne zata dawo din ? Murmushi nayi nace yallabai ai kai zan tanbaya wanan don kai ne mai yuka a hannu a gidan. Don nima a wurin hindatu nake ji wai taga ana gyaran wurin Zulfa din yai murmushi yana cewa daidai yana daukan spoon a hannun shi. Ashe shiyasa naga tana shan toka a fuskan ta da na shigo gidan wanan ne dalilin nata ashe ? Murmushi nayi kawai ya fara cin abinci nace dashi ita Niima fa daddy yaushe zata dawo gidan don yakamata ai mata hakkuri itama. Dakatawa yayi daga kai abincin da ya diba zai kai bakin shi tare da watso min Wani irin kallo yana fadin waike Rahama wani irin zuciya ne gare ki haka ? To kiji bana son jin zancen yarinyar nan daga yau a gidan nan don nike zama da ita ba wani ba, har yakai spoon din kamar zai dibi abincin ya sake cewa dani wai ke yanzu don rashin zuciya irin naki har zaki ce wai yarinyar nan ta dawo gidan nan da zama ? Wai kin san ko wacece Niiman da kike magana a kanta ni nasan irin hakkurin da nayi da zama da yarinyar nan a gidan nan don bana son mutum mai zalama da yawan korafi. Ya debi abincin ya kai bakin shi tare da kada kan shi yace hakkuri nayi dama don bana son wani abinda zai hada ta da wani har yakai mu ga samun sabani da ita. Kinga hakkurina yaci akan diyana zata iya kallon idona tace wai na fifita su da ita ita har yaushe ta shigo gidan da zata iya fada min hakan. Ko ku dake gidan yau akwai wacce ta isa tace don may zanwa yarana gata da nai niyar yi ita kuma wanan munafukar har da biye mata su zauna suna wanan irin maganan haka ? Ko ita taci albarkacin iyayye da diyan ta ne a gare ni da duk wani makircin ku na bani hakkuri haka ba zai taba tasiri a kaina ba. Nace cikin marairai cewa daddy mu mata sai hakkuri yanzu ai ta gane kuren ta ba dadi ne ace anyi aure ko shekara ba a kaiba an rabu. Yace ke za a zaga ko ni Rahama zama da wanan yarinyar mai jiran cin gado na nagama shi don dama ni nasan abinda nake zama dashi ba wani ba. A daiyi hakkuri daddyn mu ai mata afuwan hakana har ta sake bai tankani ba yaci gaba da cin abincin shi ba tare da yai wani magana ba kuma. Can ina dai zaune shiru naji yace dani mutanen gidan su Saade sun shigo kuwa gidan nan don naji suna korafi wai ba akai masu Amira din ba wurin su. Nace suna da gaskiya ai daddy shiyasa nace dakai tun zuwan mu a bari taje ta dan kwana masu biyu can su gan ta. Sai daya kurba ruwan dake aje a gefen shi cikin cup yace dani, wurin wa kike ganin zan iya turata cikin su ? Mutanen da suka nuna basu ma san da zaman yaran ba a duniya wa kika taba gani ya wanko kafan shi yazo gidan nan da sunan yazo duba su cikin su. Nace wanan kuma ruwan su ai tunda sune sukai watsi da zumunci don basu san falalan shi ba su da basu bar diyan yar uwar su data bari a duniya ba sun yi watsi dasu don wata manufa dake gare su. Yace wani manufa ina dai kan su rike ita Amira din ne nikuma sun san ba yarda zanyi da hakan ba itace ma dai ba yar goyo ba. Don ba don ke ba waye zai iya rike ta irin yadda taso mayar da kan ta a baya abin ya damay ni sosai a lokacin ban da yadda zanyi ne kawai idan nagan ta a lokacin. Ba laifin ta bane nace dashi akwai kurciya da kuma zugi ana fada mata maganganun da ba zasu fisheta ba ita a ganin ta ta dauka so ne. Yanzu ai ta gane gaskiya ita da bakinta ranan naji suna hira da mama Altine irin maganganun da sukai ta fada mata ba don Allah ya gyara ba ai lalata suka so yi kawai. Amma shi yaro ina yasan wanan irin raayin da sukai ta koya mata kan taki ubanta da yan uwan ta. Nifa shiyasa Nasir da jinior har gobe nake son rayuwan su don tun uwar su na raye basu taba nuna min ko diyana wani banbanci ba dama shi da namiji haka rayuwan shi yake sai kalilan ne ake samu da wani halin na daban. Bar ni dasu ai zasu sha mamakina don koda ita marigayiyar take a raye may suka mayar da ita a cikin su in ba suna son abin hannun ta ba zasu zagayo ta. Daddy ba zamu bi ta nasu ba azama daya zan kaita anjima idan an gama kamu sai ta kwana a wurin su zuwa gobe ko jibi ta dawo kaga ai an dai wuce wurin ba shike nan ba. Yace idan kinga hakan ba matsala shike nan amma ni naso ne kawai a share su, nace kada ku zama daya dasu daddy bari dai kawai nakaita da dare gidan anty Amina sai gobe kuma na tura taje can babban gidan ta wuni masu. Yace yayi idan ba zai kawo matsala ba nace insha Allahu ba komai shigowan hindatu falon ya dan katse hiran da mukeyi taje cewa ashe kina nan ne nace da ita eh kawai. Na fara tattara kayan da yaci abincin don na basu wuri sai naji tace ashe yau zulfa zata dawo gidan shine ba a fada muna ba. Hindatu kina da hankali kuwa ko kuwa raini ne ya kawo hakan tsakanin mu matana don zata dawo zaki ce wai sai na fada maki ke lokacin da kika tafi wana fadawa cewa zaki dawo gidan. Ko akwai wace ta biya min sadakin wata a cikin ku ne fice min daga falin yar rainin wayon banza kawai. Ni dai ficewa nayi ina jin yadda yake zagin ta a raina nace wanan kuma ta daukowa kan ta wani sabon fitina a zaune kalau. Na koma na samu wasu bakin sun shigo gidan nan muka baje ana hira su Zarah na ta faman shirin buki da za ayi da karfe biyar na yamma ranan. Mun kai wani lokaci sai ga su anty Amina da anty maryam sun shigo nan muka tare su a cikin mutunci na sa Gajiye ta kawo masu abin tabawa. Barshi inji maryam ta fada cikin rashin damuwa nace a dai kawo masu su taba anty Amina yau fa a gidan ki Amira zata kwana nace da ita. Tace cikin ya tsune fuska ai mu darajan mu bai kai ace za a kawo muna yar mu gare mu ba don yanzu kin fi iko da ita ai. Nace haba anty nina isa don dai kawai bamu kusa ne kin san aikina ba lokaci ke gare shi ba ita kuma Amiran tana karatune kun sani. Yanzu dai bashi ba mun zo ne muji abinda ake ciki tunda mu matsayin mu baikai na anemay mu ba mu san komai akai. Mun ga idan mun kyale ki zakiyi muna rufarufa ba zurfine ki rubda ciki ga komai don kina ganin kin fi kowa wayau. Nace haba dai anty may yai zafi haka kuma ai abin baikai can ba duk abinda ake ciki ina kiran anty Asamau na fada mata komai balle ni ai komai shiya saya da kan shi ya kuma tura a gyara mata dakin ta can bauchi. Bakaji ba ina ruwan an haifa maki jari ashe har jere kin saka ai mata bamu sani ba mu inji anty maryam ? Tace anty ai saiki tashi mu tafi don wanan ta riga da ta mamaye komai ba komai zamu gane ba sai dai shi may gidan ya kamata mu gani. Sai dai ki sani duk cin amanan da kikewa yaran nan a kunnuwar mu yake in zalunci abinyi ne sai ki hau ki zauna ga yaran nan kinwa uwar su ma data kafaki balle mu din. Wasu hawaye ne suka zubo min nace cikin kuka haba anty maryam ban taba zaton irin wanan sakamakon a gareku ba wallahi. Muryan Zarah ne naji tana fadin may ye na kuka a nan doctor da har zaki tsaya kina zubar da hawayen ki ga banza diyan da aka bari ai ba a ke kadai aka bari ba. Wa ya nuna nashine har yasan da zaman su a gun ki sai yanzu ne da ake ganin sun zama mutane aka san dasu ko may da za a zo ana fadawa mutane wani magana can mara tushe. Ke kuma a suwa wai wakike a cikin maganan ko karan kada miya baki kai ba ga zancen nan don haka ki ja bakin ki kiyi shiru ga maganan nan. Aikuwa nan fada ya tashi a tsakani sai ga suwaiba ta fito daga daki itama ta saka baki aja su aja su anty Amina din fada suke sosai da gori a tsakanin su. Sai ga Amira ta fito da abokan ta don jin hayaniyar da yai yawa tana ganin ina kuka ta nufe ni bata nufe su ba tana fadin. Mummy may ya samay ki may my ya faru hakane kuma ina dazun nan kike cewa zan tafi gidan su na kwana. Sai nace ba komai Amira ina share hawayen dake fuskana ba komai kamar ya uwayen ki ne sukazo suna zargin ta wai ta kakace komai ta hana su shiga har kan bukin ki inji suwaibana take fadin hakana a hasale. Kamar ya ta daga kai tana kallon inda suke tsaye suna fada take cewa dama wa ake son yai min wani abu bayan mummy ina da wata uwace data fi min mummy ne yanzu. Nifa yanzu ba zan yarda ba don yanzu ba irin da bane da ake fadawa mutum magana yana yarda amma may mummy ta rage mu dashi a duniya ni da yan uwa na ? Ke rufa muna baki shanyayun banza kawai daku da uban naku duk an shanye ku baku dana fadi a kan ku. Duk dukiyar uwar ku da ta bar mai an handamay wama ya sani ko yanzu babu komai da ya saura gare ku. Haba mama Amina wanan bai dace ba gaskiya kudin dama kuke magana ai ba a hannun ta yake ba kuje ku samu daddy mana shi da komai ke gurin shi amma za a zo a saka mum a gaba da wanan magana haka ? Kai kai wai may ke faruwa haka ne a nan anyi taron arziki za a kawo muna fitina kuma ana zaune kalau wai may ke faruwa ne wai ? Gasu nan gara dai da ka shigo don wannan abin baiyi ba gaskiya yarinya tana iya kokarin ta da yara amma babu kunya kuzo muna da zancen wai dukiyan yara idan an baku dukiyan may zakuyi dashi baku za a yi ku rike ko may ? Mama Altine ne da ranta ya baci take fadin wanan maganan cikin bacin rai da damuwa daddy ya juya gun su yace dukiya wani dukiya kuma ? Maryam tace na yaran mana da mukaji ance wai an fitar masu kwanaki shine muke son ji idan wanan mai wawason bata wawaahe masu ba ? Ke kuma tsohuwar munafuka Altine da kike wanan magana don an shan ye ki an gama daku ana baki na goro idon ki ya rufe har kike wai ana zaune kalau. Kai ku dakata don Allah ba wacce zata shigo min har cikin gidana tazo taba son ciwa iyalina mutunci a zauna kalau. Dama ai na fada maki keda kike daukan su wasu tsiya ko yar uwar nasu dake da rai yaya ta kare dasu sai yanzu ne kuka san ta bar baya a duniya ? Wa ya taba zuwa da sunan yazo gidan nan don ya ga yaran da ta bari sai yanzu to bari kuji na fada maku. Idan ba girma da arziki ne zai kawo ku wurin wanan sha a nin ba na rokeku da ku zauna a gidajen ku daga yau idan yaran suna so zasu tafi inda kuke amma ba a gidana ba . Ku fice min gida idan fitina ya kawo ku ai akwai hukuma sai kukai karana a can ina jiran sanmacin ku. Ya nuna masu hanya da su fice mai a gida nan suka fara sake mai bakaken maganganu suka fice daga gidan a fusace. Suna fita hajiyan harka tana shigowa nan take samun labarin abinda ke faruwa a gidan tace kayya ai dama ace tana gidan haka ya faru da sun ji magana. Wa ya hanavzaman lafiya a tsakanin marigayiya da Rahama ba su ba ta kasa gane va son ta suke tsakani da Allah ba a kullun cikin zuga ta suke da tai rashin mutunci a dakin ta don suna hassada da bakin ciki da samun ta cikin su. Ina kafin ta mutu ta gane gaskiya nan ta mutu ba kunya suka wawashe abin da ta bari a dakin ta yanzu kuma sun dawo dan abinda ya saura ga yaran su kuma wawashe shi a tsakanin su. Nace wallahi hajiya ni ban taba kai zuciyana a irin wanan abin ba a rayuwana duk abinda zanwa yaran tsakanina da Allah nake masu don ina kwadayin samun lada a kan su balle Allah na tuba har anty zata bar baya na ce ni Rahama wai na gaji dasu ko na watsar dasu don ina butulu ko may. Kuma duk abinda zanyi fa tare da sanin anty Asamau nakeyin shi gidan nan don kafa sheda irin haka dama. Ko ba sheda fa Rahama sai makiyin Allah zai ce ga sherin ki akan yaran nan a gidan nan wallahi. Sai da lokacin fita yayi aka sasauta maganan daidai lokacin kuma hajiyan daddy ta shigo gidan kan maganan ita ma tace zata tafi har gida ta samay su tai masu tas yara dai nasu ne su da yar uwar su ta mutu suka kasa rikewa har suna da bakin zuwa yin wani magana yanzu don basu da kunya ko may ? An dai bata hakkuri na hada mata duk wani abinda za a raba gun kamun a ka kai mata a mota suka tafi. Ko ba komai dai naji dadi don dani kadai suka sama ba wani abin da zan iya yi a lokaci sai kuka don takaici amma Allah ya rufa min asiri a gaban mutane suka zo min kuma sunji magana sosai ranan. Anyi kamu anci ansha komai yayi kyau yadda ya dace ayi an tafi da dadin rai a gidan an barmu yan gida muna ta kawar da kayan da aka fitar. Da dare misalin karfe tara sai ga su anty Asmau sun shigo gidan sunzo bada hakkurin abinda ya faru don ashe daddy ta tafi wurin wani kanin mahaifin su ya fada mai. Shine ya kira su daya bayan daya yana masu kashedi akan gida daddy tare da fada masu abinda su anty Amina suka zo sukayi. Sun bani hakkuri nace babu komai ai zama tare ne ya kawo hakan take cewa don Allah abawa daddy hakkuri don tana ma jin nauyin shi da kunya su hada ido don basu da bakin magana akan zancen din an riga da an bata zance ko. Da haka dai da zasu tafi suke cewa sunji ance za a taimaka akai masu amarya ta kwana don Allah kada abi ta zancen nasu. Na aika aka kira Amira tazo sai dai tana zuwa ta nuna bazata tafi ba da lalashi da komai ta shirya suka tafi da ita. Su suwaiba na fadin wai don may zan bari a tafi da ita yin haka kamar na nuna jin tsoron su ne ai, nace haba hakan ai ba komai bane diyar suce fa a barta ta san iyayen ta ta san darajan su tun yanzu don yan uwan uwa ba wasa bane. Dama sune suka watsar da yaran har haka yakai ga faruwa amma ai tasan anty Asamau don idan muna waya tana kusa nakan bata su gaisa da ita ta dan tambaye ta wasu abu gamay da rayuwan su . Sai gashi kuma bayan tafiyab su da yarinyar washegari daddy ya samay ni da nashi fadan don may zan tura Amiira wurin su tunda basu da mutunci. Hakkuri na fara bashi nace daddy yar su ce fa dole ne ko yaya ne su san su don jinin su ne yaran, yace dani cikin bacin rai ke dakata Rahama. Sai nai shiru ido rufe ya hauni da fada akan naje na dawo mai da yar shi kafin raina ya baci inda yake shiga ba nan yake fita ba sai da mama Altine ta bashi hakkuri tare da fadin bari ta tafi ta dauko Amira din tin da safe. Abubuwa duk sun taru sun min yawa a kaina ta ko ina babu dadi a gareni kan wanan magana don daddy ya rufe idanuwan shi yai min tas akan yan uwan anty Saade. Yadda mama ta fada hakan akayi don tunda safe ta shirya nasa driver ya kaisu ita da mama Abu matar maigari da gwagon daddy da take zuwa gun mu akai akai idan muna kano. Sai da aka kwasa dasu don gidan anty Amina suka fara zuwa tace vaza su ba da ita ba sai gobe zasu dawo da ita din. Amma mama ta fada masu cewa idan har basu ba yarda yarinyar ba komai ma zai iya faruwa akan maganan. Haka dai dole suka ce yarinyar tana gidan maryam daga gidan maryam aka kira masu Asmau itace ta bada Amira din suka dawo da ita gida tare da su. Har lokacin raina ba dadi ga jama, a da suka taru don ni a gidan zakace ko yar cikina ne akewa aure a lokacin irin yadda yan uwa na sukai min kara a bukin. Sai dai yan uwan marigayiya sun kawo min cikas a rayuwana kan zargin da suke min na wai nayi rub da ciki da dukiyan yaran yar uwan nasu. Kamar yadda daddy ya dauki zafi nima haka na dauka dashi don ban kara bin ta kan shi ba, tun wanan lokacin. Ban san may ya gani ba da dare ya aiko kirana ina zaune tare da su mama Suwaiba na ta ta faman hada kayan da za a kai hidan iyayyen mijin Amira na gara a cikin manyan robobi don da safe zasu tafi da kayan bauchi. Mutum biyar aka zaba da zasu tafi Aisha Sister din daddy da fatiman shi sai Asamau sister din anty don ita kadai tace zata tafi sai Zarah yanzu ga Suwaiba tace zata tafi itama don mota biyu zasuyi amfani dashi. Sai da na dan bata lokaci na mike na tafi inda na samay shi tare da Zulfa a zaune tare da shi. Sallama nai masu tare da gaida daddy din sai Zulfan take tambayana yaya naji da jama, a dazun ta shiga ance mun dan fita bana ciki. Na dan bata rai na nakai zaune ina fadin wallahi fa mun tafi wurin mai aikin cicin ne tana son kawo muna cikas ga aikin bayan munyi da ita a yau muke son mu kammala komai gobe za a tafi dasu. Take cewa dani ai haka mutane suke wani lokaci basu da alkawari nace ai tayi muna don har ta aiko dashi ko tun dazun yanzu ma hada kayan mukeyi aka kirani. Tace wai gashi har kin wani fada kin ramay ki na ko samun cin abinci kuwa doctor ? Murmushi nayi nace da ita ina naga ta zama naci abinci idan banga an kamala komai ba tace ai shine ance rana baya karya sai dai uwar diya tai kunya inji manya. Wanan uwar diyan kan a tsaye take don tun da safe ban ga kin zauna ba ga jama, a sun taru haka abin tubarkallah wallahi. Nace gaskiya mutane sunyi kokari sosai wallahi don hakane kawai za ai wa mutum a nuna mai so da kauna yasan cewa shi din da dangi ne ta ko ina. Mun dai dan taba hira akan bukin da ita t yana ta faman aikin shi bai tanka mu ba sai can naji yace damu. Naga, har su suwaiban ki ai sun shigo da wuri haka abin ya ban mamaki nace ai dole ne suzo daddy wanake dashi bayan su. Ranan wuya akace sai naka inji zulfa sai Daddy yace ga wanda yasan da hakan ko naga wasu na jikina ne amma suna ja baya ga bukin . Sai duk mukai shiru saboda mun fahinci inda maganan shi ya dosa a lokacin da zulfa yake wanan magana din. Yace dama na kiraki ne naji su waye zasu tafi gobe sai kuma jibi din idab za a kaita da suwa za ai tafiyan kuma ? Na dan ya mutsa fuskana da babu saki a cikin sa nace tau dama dai ga goben sai na lissafo mai masu tafiyan kai kayan . Nace jibi din dai ne ban san masu zuwa ba don kowa na son zuwa yaga dakin nata a can yace ba gaskiya bane kin san dai ba za, a kwasa akai masu dawainiya ba can kuma da yawa. Nace ai yanzu sai ka fada kowa yaji yace ba manya ne zasu tafi ba idan za a je din nace ai yadda kace haka ne za ayi. Amma maganan yana hannun Aisha da Fatima don sune masu gudanar da komai na gani yanzu don ni ba zan iya ba saboda kowa abinda ya kawo shi ke nan. Yace to ji nan kada a wuce mutim goma dai kuma a tabbatar da an tafi da mama Laraba da mama Altine idan za a kaita din don hankalina yafi kwanciya dasu a ciki. Nacd zan fadawa Aisha din don yanzu ta fita ta tafi aurin matar da zasu dauka don gyaran Amira din. Yace gyara wani irin gyara kuma ni dai murmushi nayi sai Zulfa ne tace dashi kai dama ka dauka haka ake dunkula mace akaita gidan mijin ta kai tsaye ba wani dan kwaskwarima tare da ita. Balle wanan Amaryan yar gata duk kawayen uwar ta madu ido a bude sun san komai ko su da kan su zasu iya mata komai ai. Nace kai haba dai abin ya zama sheri kuma ai anty gyara kan Amira ta sha shi sai dai muce Allah ya bada zaman lafiya kawai. Nace a kasalance shike nan ni zan tafi don aiki muke a can aka kirani yanzu din. Yace tunda kika ji na kiraki aikin san magana zanyi da ke ko nace na dauka wanan maganan ne kawai ai. Yace to bashi bane zauna kijirani ina zuwa sai yaci gaba da aikin shi kawai. Dan lokaci kadan Zulfa ta mike tana fadin bari naje na duba yaran nan don yanzu nasan suna can sun min kaca kaca da shiya na. Ta mike ta fice ta barni dashi zaune a wurin tana fita yake cewa dani komai dai ya kammala ke nan ko don banji kince dani komai ba again ? Nace dashi ina ganin ba komai ai da nayi magana cikin daure fuska ya dan dago yana ksllona don jin yanayin da nai maganan. Wai ke may kuma ke faruwane haka kike wani shan kamshi dake haka tun dazu nake lura dake a hakan. Nace may fa kawai dai daurowa ne yace ba gaskiya bane wanan maganan ko dan maganan da akayi dazun ne kikewa wanan cikan kina batsewa haka ? Nace dan magana fa kace daddy fisabillilahi yanzu ni may ye laifina a cikin wanan zancen haka da har ka rufe idon ka kai min haka don kawai na tura Amira wurin dangin uwar ta. Kuma na ga dai wanan maganan ai munyi shi dakai ranan ko yace amma kuma ai daga baya da sukai min rashin mutunci na fada kada a kaita. Nace yanzu sunzo sun bada hakkuri ai na dauka komai ya wuce ne ko idan kuma na hanata zuwa yadda suka bukata sai kuma nai wani sabin laifi ga hakan. Yace ba dai kin tura ta ta tafi din ba ina shike nan nace kasan da hakan kuma ka rufe ido ka nunawa mutane ni ba kowa bane ga yaran da maganan. Yai murmushi tare da ture takardun dake gaban shi yace dani yanzu dai in waban ne laifina ayi hakkuri ina shike nan ko ? Nace ai hakkuri ya zama dole gare ni tunda haka Allah ya doro min wanan nauyin a kaina dole duk yadda yazo min na rungumay shi da hannu biyu. Yace haka ake son musulmi dama da hakkuri amma kin daure haka aiko jama an dake tare dake bazasuji dadin ki ba don haka a washe don Allah. Don Allah wanda na bata wa rai yayi hakkuri dani yanayi ne idan anyi la akari da yadda ake samun novel din a baya da kuma yadda yanzu yake delaiy gurin samun shi. Ayi hakkuri dani please ba haka naso ba nima da fatan an sha ruwa lafiya yan uwa Allah ya sada mu da rahamarsa da gafaran sa albarkacin wanan watan mai albarka da muke ciki ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE ONLINE NOVEL NE NA KUDI, , , , , 107 Washegari tunda safe masu zuwa bauchi suka shirya tafiyan don su samu su dawo a lokaci. Bayan tafiyan su anyi wasu event da ya shafi yan matan bukin na Amira wanda akasarin su sunzo ne daga Abuja don taya ta murnan bukin nata. Sai yamma lis su Zarah suka dawo garin a gajiye suna ta faman yabawa irin taron da akai masu a can da kuma irin namijin kokarin da mukaiwa Amira din a dakin ta. Don duk wani kayan kitchen da uwa zataiwa yar ta nice na sayawa Amira su da komai da ya dace na nauyin uwa a gare ni. Haka uban nata ba a cewa komai don ya gwadawa yarsa gata sosai yadda ya dace duk wani uban da ya dace yaiwa yarsa don nuna hali. Sun yaba sosai ga abinda idanuwan su ya gano masu a gidan na Amira da aka gyara mata shi. Mutane nan suka shiga magana kan irin wannan gatan da aka gwadawa Amira din wanda itace ya ta farko da ya aurar ta jikin shi. Haka yasa kowa ke son zuwa ya ganewa idanuwan shi abubuwan da ake fadi da akwai a gidan na Amira a can bauchi. Mun tashi da aiki washegari don tun karfe hudu muka falka aka shiga yin abubuwan abinda ya dace na sha,anin bukin. Koda gari zai waye an gudanar da komai a yadda ya dace, ayi shi don haka muka samu sararin da muka samu hutu da kimtsa kan mu sai taron jamma, a da muke muna kuma ciyar dasu da abinda ya sauwaka na bukin da muka tanada. Daga hakan ne aka daura aure aka shiga shirin wucewa da amarya sai daga bayane nake jin ai shi daddy da kansa ne zasu kaita shi da Bashir aminin shi. Kamar yadda yayi da za akai Aisha wannan ma haka akayi akan amira din don sai da muka gurji kukan mu a wurin kafin mama laraba da anty Asmau suka ja hannun ta suka fice da ita a falon tana kuka ina kuka har suka bacewa gani na. Haka na wuni cikin rashin walwala a tare dani haka nai ta gudanar da harkan buki har mutane suka watse aka barni da bakin da suka zo min daga wasu garuruwan wurin bukin. Bayan bukin kwana biyu kawai na yi a kano na kwasa sai Abuja don akwai aiki a gabana banda wani lokaci na hutu a gare ni. Nan na bar Hindatu a kano wai bata gama abinda takeyi ba a garin ni dai na kwasa da yarana muka bar garin. A na samo wata yar aiki sai dai ba yarinya bace ita ta dan manyanta hajiyan harka ce ta sama min ita don haka da ita muka dawo garin. Nazo da yar wurin Suwaibana daga can da zata zauna dani sai kanina Audi daya biyo ni don zai fara karatu shima yanzu saboda sun kiyi a can sun tsaya shiririta wai neman kudi. Saukina ma shine daga Aisha har Amira duk a Abuja muke zaune dasu ko ba kullun ba dai zan dan dinga ganin su a gidan wani lokaci. Sannu a hankali na ke koyar da Tani mai aiki dana dauko babu wani tsangwama ko takurawa a gare ta don nima tai muna tsakani da Allah yadda muke mata din. Ban samu matsala da ita ba don tana da hakkuri sosai matan saboda zama da yara dole sai da hakkuri tare dasu. Tafiyan Nasir ya taso sai faman shiri muke yi na tafiyan nashi tare zamu tafi dashi mukai shi mu dawo ni da daddy sai ga wani tafiya zuwa India ya taso min daga wurin aiki inda zanyi wata uku a can don wani nazari da aka tura mu mu uku . Wanan dalilin ne ya hana tafiyan dani a lokacin don haka na shirya ma yaron komai daya dace tare da mashi alkawarin zamuzo muyi mai hutu acan U,S din insha Allahu in na samu lokaci. Na riga su barin kasan inda nai tafiya da kananan yarana sai Maryam dana dauko don su Aisha na karatu a lokacin. Inna ta da mama Altine ne zasu zauna da yarana a gidan sai dai kafin ta yarda da hakan sai da akakai rana da ita daddy da kansa yaje ya dauko min ita acan kauyen mu. Su na bari da yaran a gida su zauna min dasu don kula yadda ya dace na tafi wanan tafiyan idan nayi shi akwai alheri sosai gare ni cikin sa ba don hakan ba ba zan bar Nasir ya tafi badani ba irin yadda yaron ya nuna damuwan shi ga rashin zuwa dani a lokacin. Gida ne aka kama muna kowan mu mai dakuna biyu da falo sai kitchen don haka na samu wani makaranta a kusa na saka yaran a nan. Haka yasa banda matsalan komai na ci gaba da abinda ya kawo ni kasan nakan kira yara muyi waya dasu dasu inna mu gaisa dasu sai ranan muna waya ne Aisha take fada min cewa anty daddy fa yayi aure bayan ki. Duk da maganan ya barna min rai amma sai nake cewa cikin dakewa ashe har yayi auren ko ? Tace anty dama kin san da zancen auren ke nan ashe, nace da ita na sani mana tunda ba fasawa zaiyi ba ai. Tace sukan maman Ihisan fada sukayi da daddy sosai sai da mamanta tazo garin baki ga matar ba wata lukekiya da ita wai yar kasuwa ce irin shi Dubai take zuwa nace kuma dai. Tazo satin ta daya ta wuce bata dawo ba yun lokacin nan dai taita bani labarin yadda zuwan matan aka kwashe da daddy har yake cewa inda Rahama ce ba zata taba nuna tashin hankali haka ba ga duk auren da nakeyi amma ke sai ankai ruwa rana dake ko yaushe baki girma. Yabon banza nace da ita shi dai ya sani yaje yai tayi ai watarana yana gani zai bar matan wanan wani irin rayuwane ma daddy kamar wanda keda bakin uwa akan sa. Mun yi sallama da ita ta barni da wanan damuwar a raina ni kadai a kasan mutane daga karshe na tattara na watsar da zancen don ba zan yarda na saka wanan zancen ya ja min matsala ba. Sai dai ina jiran shi ya fada min da kan shi kancewa yayi auren wanan karon nayi alkawarin zai jini sosai ba dadi don abin ya ishe ni hakana wallahi. Har ina batun dawowa bai fada min ba nima ban mai magana ba akai sai gashi ranan na kira su Inna muna waya dasu nake fada masu karshen wata zamu dawo insha Allahu. Sai bayan mun gama hiran mu nace tabawa yaran sai naji tace dani Yarinya dama ina son muyi wani magana dake kafin ki dawo nace to Inna ta. Tace ba wani abu bane nasan a gurin ki don kin saba da hakan daga mijin ku don ya kara aure a bayan ki don haka kada ki yarda naji wani abinda bai dace ba ya fito daga gare ki kan wanan maganan kamar yadda ya uwan zaman ki sukai mashi. Shiru nayi sai naji tace kina ko jina yarinya nace ina jinki inna ta ba ruwana da zancen auren shi ni matsala na daya shine idan ya tabbatar da lafiyan matan da yake aure ai shike nan . Duk da dai nasan ba zai yarda yana aure haka ido a rufe ba don yana da wayen wan shi akai amma ni mace ba a kaina zata zauna ba ai shi da ya dauko shiyasan abin shi can. Tace haka nake so ji dama a gare ki don Allah ki taushi zuciyar ki irin yadda kika saba don shima ya fadi hakan da bakin shi a gurin sulhun da akai masu da ita wanan hindatun kishiyar ki. Nace kai maman Ihisan ma dai da wani abu take wallahi mata nawa yake daukowa agidan a yaya ake karewa dasu irin su daddy ai sai ido kawai don abin nashi kamar mai bakin uwa akai. Inna tace min ai ba kama bane don ance uwar ce tace dashi a lokacin marigayiya na da rai da zai auri su Zulfa take cewa da ita indai kishi ne sai dai taitayi mata hudu sai ya zauna dasu a gidan tana gani ba fashi. Nai dariya tare da fadin Allah sarki ita Allah bai nufa tagani ba amma su gashi ai suna gani da ran su shiyasa ba a son uwaye nawa diya furci ko yayane cikin bacin rai . Inna tace hakane sai dai ai bamu ganewa ne kawai odan ran mu ya baci a lokacin komai mutum zai iya furtawa yanzu dai kinga bako a kan shi bane ta furta amma da yake abin ya shafe shi kinga shi da yake nata a gunshi furcin ya sauka ai. Inna Allah dai ya kuauta amma abin na daddy ai sai addua kawai don ni na rasa may yake ganewa ga wanan yawan auren da yake yi har nakan yi tunanen nace ko dai mune din baya jin dadin zama damu yasa yake hasashen wasu a waje. Tace ummm, umm yarinya ba haka bane fa abune da ubangiji ya halasta masuyin shi shi kuma kinga yana da halin shi da zai yi wanda ma baida hali yayi wanan kokarin haka rabu da namijin baushe idan yasa rai ga yin abu bawai gazawan ku bane ko wani abu haka dai Allah ya doro mai wanan rayuwan kuma. In bashi ba ai masu hali ma basu faye yawan aure hakan ba nagani ku dai sai kuyi ta hakkuri dashi kawai tunda haka Allah ya nufe ku da gani. Nace nagode inna tace may ye na godiya ki dai godewa Allah da bai aza maki zafin kishi irin na hauka ba akai duk da kinayi amma ai ba irin na wasu ba har a wuce wuri akai. Munyi sallama inna ta barni da tunanen irin matakin da naso daukawar wa daddy kan wanan aure sai naga ai duk maganan inna gaskiyane ba karyaba. Babu abinda na rasa a rayuwana yanzu duk da ina da hanyan samu ai shi bai rage min komai ba na hakkin na daya rataya a wuyan shi don haka may zai sa na tsaya batawa kaina lokaci kan wanan shirmayn nabaya ma da yayi iba suka kai balle wai wata matafiya kuma can. Matsala dai daya ne sai na saurara na sa ido naga ita kuma damay ta shigo gidan idan har bata shiga da sunana ba irin na Raliya da Niima may zai damay ni kuma da ita. Bata zama bana zama banga abin damuwa ba akai kowa tashi ta fishe shi don miji mai aure aure ai ba dan goyo bane na ma godewa Allah da baiyo ni mai rawan kai ba akan miji da zan tsaya nuna ni watace a wurin shi ko wani abu. Don wanan matsalar ne ke damun hindatu take wanan zafin kishin haka akan shi ya kamata ace tasan waye mijin mu wa muke aure muke zama dashi. Shi fa mutum ne irin mazajen da basu da gwana a wurin su amma har yanzu basu gane hakan ba sam. Mutimin da dan matsala kadan zai iya rufe ido a gaban kowa yai maka tas bai dauke shi komai ba ina wata wai mowa a wurin shi ko bora. Gashi iya gwargwado yana kokarin shi wurin baiwa kowa hakkin ta a tsakanin zamantakewar mu , sai dai da yake mu matane bamu ganin wanan kokarin da yake a kan mu. Don a kullun gani muke ai ya karkata a wani bangaren yabar sauran mata ke nan ba a iyamu duk kokarin namiji a kan mu sai mukai zuciyar mu akan abokiyar zaman mu maga may take dashi may suke da miji wanda shine wahalan mu a yau. Mun gama abinda ya kaimu india na dawo da sakamako mai kyau akan course din da muka je inda da mun dawo zan zama consalta da zan iya shiga ko wani asibiti na kasan mu nai aiki mai amfani a cikin sa. Ranan jumma, a da dare muka sauka lagos Nigeria ni da yarana da sauran abokan aikina wanda zamu dan tsaya lagos din muyi dan kwanaki don yin wasu cleares din wasu takardun mu a can. Duk wanan abin maigidan bai masan mun dawo Naija ba yana can tare da amaryan shi sun tafi kaduna wai wani aiki ya kai shi can daga can zasu shiga kano da ita Zaune yake a bakin gadon dakin hotel din da suka sauka shi da ita ya dauki waya yana hira da bashir nan dai yake wa daddy da sherin kadai san kaunata ta kusa dawowa daga course din ta gashi ina ga baka fada mata zancen auren ka ba ko ? Ya dan shafo fuskan shi kadan yana sauke ajiyan zuciya yace hakane Bashir sai dai kuma ina ga ai ba zata rasa jin wanan nan labarin ba ko hindatu da zulfa zasu iya fada mata duk da nayi warning din su ga hakan. Bayan gama wayan su da Bashir din a lokacin itama amaryan na gefe ta na kishingide tana waya da wata kawar ta na shakiyanci sai kwasan dariya suke yi ta wayan. Gyara kwanciyar shi yake shirin yi yayin da yaji muryan amaryan nasa hajiya Samira tana fadin waini wanan matar taka da kowa ke magana a kanta tana ina ne wai ? Da sauri ya dan juyo gare ta yake cewa mata wacce matar daga cikin matan nawa kike magana ne ? Ta dan tabe baki tare da jawo room fresh tana dan fesawa a ko ina na dakin daga kwance tana fadin ita dai wacce ake cewa wai likita ko may ? Murmushi yayi kawai yace a zuciyar shi anzo wurin indai Rahama ne ai zaki san ta ko sai dai a fili nuna mata yayi da cewa matatace mana ko wani abin ne sai tai shiru don ta fahinci irin yadda yai mata magana din. Sunyi haka washe gari da safe ya shiga wanka na bugo nombar wayan shi baya kusa yana ban daki sai tai caraf ta daga wayan. Muryana ne ya daki kunnuwan ta ina fadin hello daddy an tashi lafiya ya aiki ya iyali da sauran jama, an gidan ? Ke ko wacece ta daina kiran wayan mijina da safe haka don bazan dauki wanan halin ba ga kowace mace. Murmushi nayi nace ke kuma wacece karuwansa ne ko dadiron sa ko kuma wata yar aikin hotel ce. Ki kama kan ki ga daukan wayan mijin wasu kina yadda kika ga dama dashi, idan kina son kafa doka gina raminki da kan ki sai ki zauna a ciki amma ba ramin da wata ko wasu suka gina ba kizo kice zaki shige ki mamaye. Idan kina son ki san ko ni wacece tambayan shi kice dashi uwar diyan shi takwas ne ta kira layin shi don haka kibawa kan ki amsa dani dake wake da mijin yanzu ? Ina fadin haka nai sauri na katse layin nawa ban staya sauraren abinda zata fadi ba a lokacin don kada ta jefo min mai zafin da yafin da yafi wanda na fada mata din. Sai dai tana cikin kunduma zagi daddy din yafito daga ban dakin yana goge ruwa a kansa tambaya ta yake tare da kai idanuwan shi aka wayan shi dake hannun ta yana fadin keda waye haka ? Take cewa wata banza ce ta bugo layin ka shine nake fada mata kada ta kara kiran layinka a wannan lokaci sai kawai ta kai min zagi , Ko wacece zamu hadu da ita don bata san wace ta zaga ba ke nan dan ni bana ba da bashi ko kadan,. Bata ma san ya kawo bakin gadon ba sai ji tayi ya wafci wayan shi a hannun ta da karfi yana duba wanda ya kira layin nasa sai yaga ai nombana ne na nan gida Nigeria na kira shi dashi. Watau ke nan da Rahama wanan take cin mutunci haka ko, sai dai gaskiya bata kyauta mai ba don ba haka yaso ba da zancen don shi so yayi sai na dawo muyi maganan. Batare da ya damu da tana gurin ba, ya kira layin nawa kamar kada na dauka dai na dauka yake cewa kina ina ne naga nomban nigeria kika kirani dashi ? Nace ina lagos yau six days kenan da dawowan mu gobe zan iso Abuja insha Allahu sai dai nakira ka wata yar iska naji ta dauki waya har tana min barazana wai wayan mijin tane wanan na daina kiran ka a wanan lokacin haka . Ita din wacece daddy kardai nace kana hurda da matan banza ne kuma abinda ban san ka dashi ba a baya ? Yace bar wanan zancen idan kin iso zamuyi magana akan sa ina yaran suke ne mu gaisa nace dashi yanzu suka fita da doctor Hauwa zuwa cikin gari. Mukai sallama dashi ya kashe wayan tare da sauke ajiyan zuciya tana furzo iska daga bakin shi ya lumshe idanuwan shi a hankali don bai san ta ina zai fito min da zancen ba. Muryan tane yaji tana fadin wai wata yar iskace a cikin matan naka har zatace dani wai na gina ramin kaina wanan ramin ba nawa bane naje gaba ? A hasale yace da ita matar nawa zaki zaga da yar iska a gabana ita bata zage ki ba sai kece mai zagin ta a gabana matar da nake da zuria da ita fiye da kowa a duniya matar da, , , , , Haba malam ya isa haka ko ba a fada ba nasan wanan yar iskan likitar matar takace da ake fadin kana ji da ita don naga alama tunda gashi ka rufe ido a kanta kana son ci min mutunci. Yace idan kika sake maimaita zagin da kikai mata a gabana yanzu ranki zai baci dani a wurin nan. Ki shirya yau Abuja zamu koma don Rahama ta iso Nigeria gobe zata shigo Abuja din ita da yaran da ta tafi. Yana fadin haka bai tsaya bin ta nata ba ya fara shirya kayan shi nan ya barta da mamakin wanan irin rawan kafan da kaduwa da yayi akan matar shi . Wai wacece wanan da yake wa rawan kafa haka ita dai taga matan nashi ba wani abin kai gida a kan su balle ace wai wata tafita a cikin su. Shiryawa yayi ya fita daga dakin yana fadin zai je ya dawo kafin ya dawo ta shirya yana fita taja uban tsuki wayan ta ta jawo tana fadin ni za a kawowa iskanci akan wata banza can wai Rahama ? Kawarta ta kira take fada mata komai har take cewa ba inda zata don kano yace zasu tafi amma yanzu ya canza saboda wata wai su koma Abuja. Kawar tace wallahi Samira kibi a hankali kin dai san ko shekara nawa muka kwasa wurin samun hankalin shi kafin ya yarde muna don haka ki rufawa kan ki asiri kibishi ku tafi. Baki ko san yaya matar take ba balle har kikai ga daukan mataki a kan ta sai idan kin ganta ne ai zaki dauki mataki a kan ta. Take cewa hakane kuma fa bari na shirya naje ko ganin yar iska nayi naga nata kalar wanka wata kila ma wata cus ce can ilimin ne kawai a kai. Sai suka kwashe da dariya a lokaci daya kawar tace koke fa mutumiyar aiba haka kai tsaye ake kama makashi ba sai da kwana kwana. Nan ta mike ta shiga shiryawa sai dai ranta abace don gani take duk ajin ta da kima ace akan wata zata rushe plain din ta da tayi na zuwa kano ziyarar dangin shi a karo na farko ? Da yamma suka shiga Abuja kai tsaye part din maigidan ta sauka don nuna isa da gadara ga matan gidan ta nuna ita ta isa ga kowa don hamshakiyace. Amma sai ya karya mata takon da cewa akan may zata zo nan bayan ga gurin ta can takoma can don a cikin iyalin shi ya shigo. Duk da ranta ya baci amma dole ne tabi shawarar kawar ta ta lalaba shi taga gudun su tukun. Haka ta mike a likacin hindatu tashigo suka hade a falon kowa yabi dan uwa da harara da hassada a fili na kishi. Nan ta fice tabar hindatun na kallon yanayin shi ta fahinci akwai bacin rai a ciki sannu da zuwa tai mashi don har lokacin ba dadi a tsakanin su. Washegari da safe sai shirin zuwa taron mu akeyi don na bugo waya muna iya port a lokacin da zamu taso daga lagos din. Tsayawa fadin irin shirin da nayi bata lokaci ne dagani har yaran munyi kyau sosai don zama indiya ba wasa ba gaskiya. Ban kawo komai ba a raina na cewa zamu hadu da wai wata amaryan shi ni dai daukina kawai shinenaga yarana dana share tsawon watan ni bama tare da su. Mun kai wani dan lokaci kafin mu tashi don haka sai sha biyu muka sauka a Abuja inda shi da yaran ne suka zo taron mu da hindatu. Da murna na rungumay yarana ban ko bi ta kan sgi muka kuma rugumay juna da hindatu din sai yaran da suka rugumay mahaifin su don murnan ganin shi. Jinior yana lake a jikina na dago kai muka hada ido dashi alaman radhin gaskiya irin na maza karara a gareshi nace yallabai mun samay ku lafiya ? Ya dan murmusa yace lafiya kalau ya karatu da zaman india nace sai hamdala na dauki yar wurin hindatu dake murnan ganin mu. Mun dan dauki lokaci muka kwasa sai gida ina tare da yarana har muka kawo gida ina maijin dadin ganin yadda yaran ke a cikin walwalan su babu wani mairaicin rashina da suka yi. Wani abin sai uwa dama abinda nake so ke nan na dage akan sai Inna tazo ta zauna min da yaran duk da kunyan da take nunawa na rashin son nuwa duniya itace mahaifiya na a matsayina na yar fari a gurin ta. Muna shiga gida na hango wata mace a tafe tana bun kasa a kasa da waya a hannun ta bayan na bude motan kafana kawai na sako a kasa ba tare da na fito ba muka tsaya magana da yaran dake fadan daukar jakana na hannu. Sai da na raba gardaman na karasa fitowa daga motar gaba daya hankalinta na a gurin mu yayin dana karasa fitowa daga cikin motar gaba daya sandarewa tayi a tsaye inda take tana rayawa a ranta ta ina zata fara dani. Ga dai Ilimi ga kuma uwa uba kyau da tsari da ta hango muraran a wurina ga wani kwarjini da nai mata a idanuwanta a lokaci daya. Ban ko koma ta kanta ba na ja yarana muka fara hawa steps din shiga gidan hankalina a kwance. Sai naji shi yana fadin Samira ga docter ta dawo fa daga india ita da yaran ta yadda tai min wani irin kallo nima haka na juyo nai mata tare da fadin wacece kuma Samira ? Kafin yai magana sai naji tace wace kike gani a gaban ki nice amaryan maigidan da fatan zaki gane ni daga yau. Wani kallo nai mata tare da sake shuumin murmushi nake cewa amarya amarya fa ko dai uwar gidan wanan ai ba a kiran ta da amarya don ta haife mu ko ? Ai sai dai mu bata kambun uwargidan cin gidan gaba daya shi zai fi sauki na fadi haka ne don irin yadda ta mayar min da magana itama. Murmushi daddy tayi daga inda yake tsaye yake cewa shiga dai ki huta kafin muyi magana ko nace magana kuma may ya saura tunda ka gabatar da mu ga junar mu na juya muka shige da yaran ina jin tana fadin. Duniya na haifa ba ku ba sai ki tsaya ga wanda ya aje ki in kina takama da kurciyane ai ya ganki a gaban shi ya dauko ni. Ban tsaya ba don nasan su Inna na gidan muka shige ciki nan muka tari junar mu da murna ban sake bi ta kan shi ba ga yarana sun baibaye ni. Ban samu kaina dasu ba sai da akai kiran sallah na kora su suje sallah na samu na shiga dakina sai dai zuciyana fam yake da tunanen wanan matar. Bayan nai wanka na sauya kayan jikina sai ga Atika tashigo dakin da murnan ta don bata gida da muka iso tana school muna cikin hira da ita ne daddy ya shigo dakin ya samay mu. Wani kallo na tsana na watsa mashi yayin da Atika ta gaidashi tafice daga dakin yake cewa dani basu dai barki kin huta ba ke nan. Nace ba kadai barni na huta ba kai da ka kara jajibo muna wani wahala a gidan kuma. Wahala kuma Rahama aureb nawa shine wahala nace a lalace aure ina aure a nan ka kwaso muna uwar mata wai kishiya wanan ai a gidan dabe ya dace a ganta ba a gidan ka ba. Mace haka babu fasali a tare da ita daganin ta ma irin matan nan ne yan safara ba abin kwarai bane don tanayin ta yai kama da yan kano jidda. Dariya yayi min cikin shuumanci yace duk ita kadai nace ni na rasa gane wanan irin rayuwan for god sake may ye ka rasa daddy a gurin mu da baka da aiki sai auren barnan suna ko yaushe. Wanan ce zan zauna da ita a cikin gidan nan haka ga yara a haka yara zasu tashi da irin tarbiyan da muke so a garesu. Ko yaushe suna ganin nauin mata lalatattu iri iri gaskiya ya zama dole a gare ni wanan karon na nisance ka kaje duk abinda kake nema a gun mata kaita nema amma wanan tanbadar badani Rahama ba gaskiya. Ysi yar dariya yace dake kuwa zaku zauna a gidan nan ba wani gida ba auren da nake may nake rage ku dashi dakuke wanan kishin haka wai ? Nace kishi kishin wa zanyi wanan ai uwatace ba kishiya ba ni bata a gabana gani nayi kawai a tsaye take tana daukan kanta hamshakiya . Ya kai zaune tare da kai hannun shi a saman cinyana nai saurin kabe hannun nashi ina fadin kada ka soma don nagaji da wanan halin naka daddy a yau nayi nadamar auren ka da samun zuria da kai a duniyan nan. Da sauri ya katse ni yana fadin Rahama ni keke fadawa kinyi nadaman aure na da kikayi nace na fada don abin ya isheni haka. Bai yi magana ba sai naga ya mike ya fice daga dakin ran shi a bace nima na raka shi da haraea tare da tsuki na haye gadona don daukan shi ma nake bai san ciwon kan shi ba kuma. Mutum ya koma na mamajo haka baida aiki sai aure may ya rasa a gun matan shi da yake muna wanan hakin auren kuma ko yaushe kamar ba aure na kai sake ba idan yayi. Kai da zakaga matan sai kaji nauyi da kunya don basu dace da ajin shi ba abu dai gashi bai faduwa ga mutum. Abinda mu ba musani ba shine ashe idan namiji ba mazinaci bane haka wani lokaci yakan kasance dashi ga matan yanzu basu tunkaran namiji sai sun shirya mashi da saddabaru da dan sihiri shi ke saka idan namiji ya yi wani abin kaji wani iri a ran ka. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU Kuyi hakkuri masu fadin wai novel din ya dau lokaci anayin sa ba laifina bane yadda labarin yazo ne idan kuma na katse shi yadda na katse tarko nasan bazaku ji dadina ba zan ta samun korafi ne kuyi hakkuri saura kadan mu karasa da yardan ubangiji Na gode da fatan zaku fahince ni yan uwa kuma kuyi hakkuri dani please rashin waya ya kaimu har wanan lokacin haka. IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE, DON BA A YAFE BA ONLINE NOVEL NE, , , , , 108 Daga wanan fitan bai kara kulani ba nima haka inda na shiga harkokina da yara da abokan arziki masu zuwa yi min sannu da zuwa . Ba wai share junan da mukayi baya damuna bane a a na dai yi niyar daukarwa kaina matakin da ya dace ne don abin nashi ya fara bada tsoro a zuciya na. Tafiyan wata uku kacal sai aure a bayana daga mutuwan anty yai auren Raliya, Raliya tana fita ba a dade ba ya dauko Niima itama ta debi rabonta tai gaba. Nisawa nayi a fili nace mijin bahausa ke nan ke mace baki da tabbas zama da mata daya ko biyu zuwa uku sai ranan da rayuwa ya kare wa bawa. Mun koma bakin aikin mu bayan sati daya ga Inna sai shirin komawa take kano don zaman nan ya kai mata ko ina don bata saba ba zaman dole takeyi. Ranan da na fara fita na dawo a gajiye don yan aiyukan da nayi a office wanka nayi na shirya nafito zuwa dakin da su inna da mama suke na gaidasu. Suna zaune hiran su suke na shigo da sallama na dakin tare da masu barka da gida suka amsa min cikin kulawa da kauna. Na samu wuri na zauna tare da kallon kwanon abincin da aka aje a gefen su basu ci ba har lokacin nake cewa dasu sai naga kamar baku taba abincin ba mana ? Mamace tace dani Rahama in ba so kike mu fashe ba da wanan irin dadin da kuke bamu haka Allah dai ya baku hakkuri zama da mijin ku. Inna tace ai mai kuli wanan mutumin ba abin da za, ace dashi sai fatan alheri ku dai ta hakkuri kowa da halinsa ake zama dashi duniya balle ni banga wani abin gazawa a gare shi ba akan ku. Baida maraina akan iyalin shi ko kadan tunda duk wani nauyi da hakkin daga matan har yaran shi yana saukewa kai bama iyalin shi ba har masu aikin dake karkashin shi bai barsu a baya ba dubi gajiye yadda ta koma matar mai gadi fa kawai ba wani ba can. Kin kai nisa ai inji mama ninan fa yar uwar matarshi ce amma ji yadda yake min tankar mahaifiyan shi ce ke a gidan sau goma zai shigo sai ya shigo nan ya duba ni tare da tambayar banda matsala dai ko ? May yafi wanan dadi Asiya a duniya ai irin mazan nan ko wace mace na fatan samun iri su a duniya. Murmushi kawai nayi na gyara zama na araina nace wanan kuka sani ku may yafi bacin rai kullun namiji sunan kuna zaune kalau amma baida aiki sai na kadin aure. Kamar wanda bai samun jin dadi gun iyalin shi irin wanan ma ai sai duniya ta zagi mutum don baza mu fita sai ace mune bamu gamsar dashi ga wanda bai san halin shi da raayin shi ba. Sai naji Inna tace kinga ta nan tun dawowan ta na fahinci ba dadi tsakanin ta da shi don ko yawan shigowan da take dubamu ya rage. A, a haba dai Rahama may kuma kike so a duniya yanzu ilimi da daukaka Allah ya baki ga miji na gwadawa tsara kin samu ga zuria dayyaba Allah yabaku a tsakani may kuma kike nema Rahama ? In dai don wanan auren da yake yawan yi ne sai ku barshi da halin shi tunda auren nasa bawai yana takura maku bane ko wani abu. Gaskiya in har hakane abinda uwarki ta fada baki ko kyauta ba don banga abin damuwa ba ga wanan dai. Bafa a kan ku matan ke zama ba ke ku godewa Allah ma da ba irin mazan nan bane da idan sun dauko wata a gida ke ra gida dake da babu duk daya kuke a wurin shi. Iya hakkuri bawan Allah nan yana dashi a gare ku iyalin shi ki duba irin tsiyar da yaran nan hindatu da zulfa ke shuka mai amma yana hakkuri yana takewa yana kuma zaune dasu lafiya. Duk masu shigowan nan ni a ganina kaddaran aure ne a tsakanin shi dasu inba ita wanan daya aura mara tarbiyan ba bayan mutuwan diyana waya haihu dashi ? Balle ita wanan uwar guzumar daya kwaso yanzu ai ba batun haihuwa a gare ta ma mufa a zamanin mu bamu kishin komai inba na haihuwa ba ki zuba in zuba kowa ya cika gida kuma babu wani abindake ga namiji in dai ba wanan din ba. Nace mama ni ba wai auren shi bane ko wani abu ke damuna yanzu fa ba irin da can baya ne aure haka a zamanin nan abun tsoro ne ga namiji don zamani ya canza lafiyan mutum akewa tsoro. Haba yar nan har ke kin fishi sanin hakan ko kin kaishi sanin abinda duniya ke cikine wai inna tace fada mata dai mai kuli yarinyar nan bata ji ne tun bata dawo kasan nan ba mukai wanan maganan da ita. Ashe ita da manufa a zuciyar ta yanzu kinji inda ta bullo wai ita malamar lafiya dariya inna tabani nace inna ba haka bane ku baku ganewa ne shiyasa. Bafa ganin mutum yanzu haka lafiyyaye shine lafiya ba ciwon ba a goshi ake ganin shi ba nan dai nai masu bayan komai kan irin cutar da nake gudu gare shi ga yawan auren da yakeyi. Na kara da fadin yanzu fa ki duba waban matar da ganin ta irin yan duniyan matan nan ne dake zaman kasu a wani kasan bama a na kasan ba kawai. Nan nake fada masu yadda mukayi da ita ranan da muka dawo garin mama tace yo ga yar iska ita kuma dashi ta shigo watse gida ko may ? Nan dai suke min nasiha da kuma fadakar dani irin halakan da nake daukawa kaina na wanan zaman doya da manjan da mukeyi dashi a gidan. Maganan su ba wai ya shigeni bane sosai don ina a kan bakana na sai naga takardan gwajin da sukayi da ita kafin auren su dashi. Baya gari da ya dawo ya shigo gaida su nan yake magana akan tafiyan inna da zatayi ga jibi sai inna take cewa dashi Alhaji mun gode kwarai da kokarin ka a gare mu ko yaushe don Allah adai ta hakkuri da iyali. Murmushi yayi yace Inna ai hakkuri ya zama dole tun da an zama daya yanzu suna dauka na ban san may nakeyi bane shi ya kawo haka kawai. Hakkuri za ayi don mu mata dama sai hakkuri balle ga wanda ya aje mace fiye da daya ko biyu a gidan sa. Ya mike yana fadin barsu ai mun saba in dai halin su ne komai zai wuce ne insha Allahu. Da dare na shiga falin nashi don na fada mai ina sin ni da kaina zan mayar da inna gida idan zata tafi do ina son zuwa na duba jikin mahaifina. Ya dago kai yana cewa dani ashe ina da darajan da za a nemi wani alfarma a guna nace ni ba wana ya kawo ni ba yanzu. Yace ban amince ba in dai nike da wanan dokar a hannuna nace ba matsala Allah ya bashi lafiya don ban tsaya jan maganan ba . Namike zan wuce yake cewa dani kina ganin wannan matakin da kika dauka a gare ki shine daidai ko kina min daukan mara hankali ne wai ? Nace namay kuma nifa auren ka ba wai ya damay ni bane kawai dai magana ta daya ne a nan shine naga takardan ku na gwaji da kukayi da wanan yar duniyar matar tunda abin bana kai sake bane nake gani. Ko makaho ai sai ya lalaba yake taka wuri ba wai tafiya yake babu lalabe ba mutum tun yana dauko abinda duniya ke iya dan kallo har ya koma dauko abinda za ai mai dariya don bakin jaraba kawai. Na sa kai zan bar falon naji yace dani Rahama nine yau kuma jarabbabe ko may ? Nace ai haka din ne don in ba jaraba ba banga abin gani gun wanan curarar matar daka dauko ba a gidan nan ban da magana babu abin ganewa a nan. Yace a ganin ki ba ni abin dake min na dauko kune baku ganewa kawai nace sai kuje kuyi ta ganewa kai da ita ku da jaraba ya dama a rai. Ina fadin haka na juya na fice daga falin dakina na nufa kai tsaye na fada saman gado siffan wanan matar dana gani mai kiba wai amarya nake tunane da yace shi yana gane abin sa. Nace a raina to may daddy ya gani har yace mune wai bamu ganewa a nan dayake fadi ni dai banga wani tsiya ba a gunta in banda muni sai ko launin jikin ta da ya nuna mai take shafawa na zamani. Shima na barshi can yana tunanen magana na abin ashe ya bata mai rai yace watau ke nan ina nufin baida hankali ko may da zai afkawa mace irin haka kai tsaye shiko Niima da ya aura a budurwa bata shigo gidan shi ba sai da sukai gwaji da ita. Balle wanan dashi kan sa yasan zaman barikin da tayi a waje dama nan kasan don ba diyar kowa bace ita irin matan nan ne kawai masu sai sunyi kudi da karfin tsiya ko ta wani hanya. Shi kan shi wani lokaci yakan yi mamakin yadda ya aure ta ba dai tsari takai ko wace mace dake gare shi a gida ba balle auren dai ne yazo masu don ta dade tana bin shi amma sai gashi haduwan su da ita a kaduna yaji yana balain sha awanta shiko ba zina ya iya ba don haka tana gabatar mai da zancen aure yaji ya amince mata da suyi din ba adauki lokaci mai tsawo ba aka daura auren. Abinda bai sani ba sai da tai mai zaman kashi na shekaru tana aiki a kan sa duk wani shige da ficen shi ta sani a kasan shiyasa bata sha wani wahala ba wurin samo kan sa. Namiji baida wuyan kamawa gun mace ta wanan fannin sai idan Allah ya kare shi kawai daga kaidin ta gashi ma ita kan ta da ganin Rahama hankalin ta yai balain tashi sosai don yanzu haka a cikin rikici suke da ita. Don ya tsura ta taja waya tana fadin itafa hankalin ta ya tashi ga matar don ko diyan ta fa cewa tayi takwas dashi kawar da ita kawai zanyi don ina ganin ita ce aka fada muna dama bazan iya da ita ba a gidan a kawar min da ita kawai kowa ma ya huta. Bai san may ake fada mata ba a wayan dago kan da zatayi sai kawai ta gan shi tsaye a bayan ta nan ta shiga kamay kamay tana fadin ai na fada maki wanan hadizan yar iskace ni maganin ta zanyi idan bata dawo min da kudi na ba. Ta kashe wayan tana wani fadan borin kunya sai taji yace da ita a gidan nawa nake da hadizan data ci maki kudi har kike son a kawar da ita a duniya ko may ? Tace dashi tunda ba kunya gare ta ba a gidan ka kamar ya kasan da wace nake waya ne balle kace wai a gidan ka ? Yace ke dakata kiji duk abinda ya samu daya daga cikin iyalina kema ya samay ki don duk abinda kike fadi tun dazun a kunne na yake gaki ga matan nawa sai ki kashe ta tun yau mu gani. Ya juya ya fita ya barta tana fadan borin kunya don duk jikin ta yai sanyi har ta tafi basu shirya ba do ta rasa gane kan shi abu ya taru yai mashi yawa a zuciya sai kuma. Wanan shigowan nawa yanzu ya fahinci inda na dosa da zaman mu dashi da muke yar tsama tun dawowa na. Ya nisa tare da furzo da iska daga bakin shi yanisa yace halin mace ta waye ke nan ai su wa yan nan basu ko kai zuciyar ga wanan maganan da nayi ba sai fadan kishi da ya damay su kawai. Ban sake magana akan bin Inna ba zuwa duba mahaifina da yan uwana a gida sai da safe ina daukan waya naga text din shi yana fadin na shirya nakai ina gida tafiya ya kama shi baya samun zuwa ya maidata. Kamar nace na fasa amma kuma sai naga wanan ne lokacin da nake dashi a yanzu kuma ko banza mahaifiya tace zan kai ba wata ba. Don haka a gurguje na shirya tafiyan sai gashi ya shigo yi wa inna din sallama ya kawo sako envelop biyu ya bata daya takaiwa maigari dayan na mahaifina nane. Godiya sossi inna ta shiga mashi ba laifi a gurguje nake ta shiri ya shigo dakin ya samay ni a hakan nai mashi ina kwana ya amsa ba sakin fuska kudi ya bani masu yawa akan tafiyan da zanyi din na ansa da godiya. Nan yake fada min zancen tafiyan shi da zauyi zuwa kasan Kuwait inda zai kwana biyu a can don wani harkan mai da suke son yi a can din. Zuwa wani kasa shi da wasu da suka hada hannu dasu nai mashi fatan alheri tare da rokon Allah ya bada saa ga tafiyan. Bayan na gama maganan ne sai dan shiru ya biyo bayan va wanda yai magana a cikin mu can naji yana cewa dani yanzu haka zaki barni na tafi babu ko tausayawa ? Nace kamar ta kuma aini na gama zance akai ko don na fada ma matsala kuma na zauna inda Allah ya aje ni ko. A ina aka aje ki nace matar da bata da wani biyan bukata aji dadin ta sai na waje da ake hangowa a gare su ne hutu yake da jin dadi ko. Wanan kuma maganan ki ne abin siri ne mai daki shi yasan inda ruwa ke yoyo ai ba wani ne yasan cikin zuciyana ba. Auren da nake kuma kaddaran ubangiji nane wanan don haka Allah ya kaddaro min a rayuwana nace da sauri kuma da niyyan yin hakan ba. Yace haka dai kika ce amma ai ko duniya tasan banda macen da tafi min Rahama a yanzu, in ma yin auren da nakeyi ne ai kina da kamisho a cikin sa tunda kulawan da nake samu da a wurin ki yanzu aikin ki ya hanani samun shi kamar baya. Kin mayar da rayuwan ki akan aikin ki fiyye da bani irin kulawan da kika saba bani a baya. Yaya kike son na zauna a gida ni kadai kulun kamar maraya babu mai bani kulawa yadda nake so ai min. Nace ta nan kuma za a bullo min yanzu su matan dake gida ba mata bane ko ni kadai ne mace a gidan wanan maganan ma kada ka bari wani yajita don Allah don sai ai maka wani fahinta na daban can. Mutum mai mata uku a gida zai tsaya yana fadin irin wanan maganan haka ai abin kunyane a gare ka aji hakan daga bakin ka. Yace ga wanda baisan mai aure yake nufi ba zai min wanan fasaran ko amma wanda yasan aure da kulawan shi ai ba zai ce wani abu ba kan magana na. Nace ni dai ban ja ba kawai takardan gwaji nake son gani shine karshen magana na dakai yace kina min dan kan mai ciwo ke nan yanzu ko kuma wani wanda bai san kan sa ba can ko ? Nace wanan wani magana ce mara evidence kake son fadi don ni magana daya na kawo idan naga amsa sai komai ya wuce a guna amma bani gani mace haka yar duniya ta gama karade duniya da tun da kurciyar ta yanzu ta dawo nan ta cuta muna don hainci kawai. Ya girgiza kan shi tare da fadin Rahama ban san may kika masheni ba yanzu har abin yakai ga ban san zafin kaina ba da zan fadawa halaka don idona ya rufe da aure ko may ? In ma wani abune na fada maki kece mai babban kamishi ga yin haka a gare ni nace da yake ita Raliya daka aure ta lokacin ina aikine ko ? Yace au baki aiki ko ya murmusa yana fadin ni zan tafi don ina ga daga can zan wuce nace Allah ya sauke lafiya yace to ba kaji ba rakiyar ma itama yanzu bana samun ta dai ke nan nace ai wanan ba matsala bane idan ka gama sai ka kirani na fito. Nace mun kuma gode da alherin da akaiwa iyayye Allah saka da alheri yace ba don ki nayi ba albarka nake nema don banga dalilin da zanyi don ki ba nace ko a hakan ma mun gode ai. Yace tare da dan juyo ya nufo inda nake zaune da sauri na mike tsaye dariya ma nabashi yace ashe abin naki da gaske ne nace ka dauka wasa nake ashe. Wanan uwar guzumar da ka kwaso ku karanta can da ita don ba zan yarda ta kwashe min current din na ba ta karawa tsufarta . Dariya sosai yake ya fice yana fadin ni kinga tafiyana sai na dawo da sauri na bi bayan shi ina fadin Allah ya tsare a tare muka fito daga dakin. Mun fara tafiya nake cewa dama ina son tambaya nadawo kuma naga har yanzu zulfa bata dawo garin ba bai takan ni ba sai rike hannun Anty da yayi suna magana da yaran kasa kasa ban majin abin da suke fadi ba. Mun fita tare har haraban gidan inda na samu har wanda zai kaishi yazo yana jiran shi nan muka taru har yaran muna mashi a dawo lafiya. Ya tafi yana daga muna hannu muka juya muka shige gidan tare muna hiran ko ina amaryan tashi ta shiga kwana biyu hindatu take cewa wata kila ta tafi balaguron ta. Allah dai ya kyauta nace da ita tare da jan hannun anty muka shige ciki na bar yaran maza suna wasa a haraban gidan sai na dan juyo ina fadin yau fa kano zamu zanje na maida Inna gida insha Allahu. Tace ashe gidan zai koma mu kadai ke nan a yau din nace gaskiya kan don zamu kwasa gida yayi kira yau din nan insha Allah kano zamu dira. Ban wani dade ba nagama shiri na muka kama hanyan kano ni da iyalina idan sai biyar muka sauka garin don haka nan Gajiye ta shiga dawainiya damu. Zulfa ta shigo ta tare mu munyi yaya bayan rabo da ita muka dan taba hira ta barmu mu huta na shiga da wainiya da yarana. Sai washegari tun da safe Inna ta sakani a gaba don tana ganin kamar zance da ita ta kara kwana a kano saboda hankalinta ya koma gida sosai. Da kyat na samu ta amince min na dan shiga kasuwa don sayo tsaraban da zamu tafi dashi saboda a can ban samu sayen komai ba na tsaraban da zan kaiwa yan uwa na. Sai bayan munyi sallah a zahar muka kama hanyan kauyen mu nida yaeana baki dayan mu don zamu dan kwana biyu a can kamar yadda nake son idan da hali. Mun isa a lokacin yan ma ta danyi kadan bayan la,asar mun samu taro kamar yadda muka saba samu idan muzo a cikin karamci. Wanan karon ban sauka dakin kowa ba dakin mahaifiyata muka sauka daga ni har yaran inda da kaina na shiga gyaran dakin ina fitar da duk wani abinda bai dace ba a dakin. Inna tana faman fada amma nasa aka fice dasu nan mutanen gidan suka shiga tsintar abinda suke bukata daga ciki sai da naga dakin ya koma yadda nake so na shiga wanka ina fitiwa ne wayana yai kuka masu motar kayan dake bayan mu sun iso nan na fita da kaina na bada umurni da su shigo da kayan komai na dakin sabo aka saka ba mama ba har abokan zama nata sai dai na mama din yafi nasu tsada ne sosai. Nan gida ya shiga murna kowa aikin nasa ake yi don da masu haka kayan akazo kafin wani lokaci har sun gama aikin su ko nan na sallamay su suka tafi komai har kayan kallo sai da a saka masu do yanzu mun samu wuta a kauye da safe za a kira min mai wearing yazo yai masu. Zuwa washe gari komai ya kammalu yadda nake so a raina ban samu shiga wurin mahaifina ba don aikin da muka sha yasa na dan gaji sosai. A nan gidan Inna ta Suwaiba ta samay ni duk cikin yan uwa namu yafi zuwa daya da ita sosai nan ta taya ni fitarwa yan uwan mu da abokan arziki tsaraban da mukazo masu dashi. Sai yamma ta shirya zuwa gida inda na yafa muka fita tare da ita a kafa muke tafe muna hira tana bani Labarin sabon bazawarin da Rukaiyya ta samu wai zata aura. Nake cewa da ita ta dai bi a sannu ga yaran ta kanana ne gun wa zata barsu don tasan halin maza yanzu ba son dan wani suke ba tsakani da Allah. Indai ba dan abinda aka bar masu bane yake hasashe yake son ya aure ta idan ya cinye ya gudu ya barta da wahala kuma ga yara kanana. Tace ai kafin yaci mama ta cinye rabi don kullun sune zuwa gidan boka da malam wai tana son su mallake komai da Jatau din ya bari iya wasu. Nace kai haba har yanzu ita mama bata daina irin wanan halin na bawa boka da malamai amana ba duk wanan wayewan kai da malamsi ke bamu haske akai. Tace mama kan bata da ranan barin wanan halin don ko ciwon kai taji yanzu zata yafa ta je gun bokan ta tace wani ne yai mata asiri. Nisawa nayi tare da fadin Allah ya kyauta ya ganar damu hanya madaidaiciya tace amin yar uwa. Mun rabu da ita akan da safe zata shigo mu zagaya garin mu gaida yan uwa da abokan arziki da aka kwana biyu ba a gana ba. A dakin mama Abu na yada zangon muka dan taba hira da ita sai da akai kiran sallah nabar dakin nata. Washegari Suwaiba koda ta shigo ta samu har na shirya muka garzaya sai gidan mahaifin mu mun samay shi a gida don yanzu babu inda yake zuwa saboda sugar da yasa shi gaba. A kofan gida muka samay shi tare da yarana muka zo gidan namu ya nuna farin cikin ganin mu nan yayi yayi da yarana akan suzo gun shi amma sai suka ki. Na ce dasu a cikin tsawa kuje gun grandpa sai suka tafi ya rugumay su a jikin shi yana dan hira dasu na tambaye shi lafiyan jikin yace dani Alhamdullahi. Ai abin yazo min da sauki tunda ina samun kulawa daga gare ku keda mijin ki Allah dai ya saka maku da alheri. Nai murmishi tare da fadin amin baba ya juya gun Suwaiba yana cewa ashe kina gunta haka nake son ganin ku da baku biyewa wanan uwar taku da har yanzu bata san Annabi ya faku ba hassadan ta a kullun kamar karuwa yake a zuciyar ta . Na rasa ko wata irin mutum ce Laure da bata girma kullun jiya iyau take Suwaiba tace baba ni yanzu ai ba zan taba yarda mama ta hadani da kowa ba tunda na gane halinta bana kai mutum ga alheri bane ko yaushe. Nace tashi mu shiga mu gaida su mama mu wuce zuwa sauran gidajen sai dai kafin na shiga saida muka leka mama Altine bata nan ta fita zuwa unguwa. Kamar kullun yadda mama Laure ta saba tarona babu yabo ba fallasa hakan ne ma yau a fuskan ta don tunda tace a, a mutanen birni ne yau a gidan namu bata sake bi ta kan mu ba sai Suwaiba ce ta shiga ta dauko tabarma ta shimfida muna a waje cikin yar rufar dake daga kofan ta da akayi. Amaryan baba tafito da murna tana muna sannu da zuwa na karbi danta dake goye a bayan ta take cewa jiya mukaji labarin kin shigo kin dawo da yaya a wurin mai kuli. Nace mun shigo mama aiki ne ya dan yi min yawa da mutanen dake shigowa yasa bamu samu shigowa wurin ku ba a jiya din. Tace to yaya hanya andawo lafiya Allah yasa abinda akaje nema ya amfana ga kowa ai kina da kokari wallahi duk da baki kasan amma aike ko yaushe baya katsewa a gare mu. Nace kai mama ai hakan ya zama dole nayi mata gaisuwan mahaifinta da na samu labarin ya rasu bana kasan . Dama haka ake so ai a dinga bin masu hannu da maiko idan sun shigo kamar za a fadi ana ladabin shegu gare su. Na dauka ma dani take sai naji amarya na cewa bakin halin wasu kuma bai bari hassada ya sa suci arziki ai gara nabu naci arziki dana zauna hassada ya kashe ni a daki. An girma ba a san an girma ba har yanzu mugun hali ya hana a tuba a koma ga Allah sai yawon bin boka da malam a ka iya. Nace da yarana su mike mu tafi na mika masu tsaraba da bazo masu dashi harda yaran amaryan babana sai kuma mama ta hau fada wai har yanzu ina nuna mata kiyayya a fili. Ita may yasa ban ban ta wani abu ba kari akan wanda nabata amma na uya sakowa kannena har da agolan gida tsaraba. Allah sarki dadi inji barawon takanda an daiji kunya wallahi ai sai ki bari diyan ki da kika hana su nuna yara jinin su ne amma ba wacce hassadan ki ya zamawa taki ba a duniya. Don rashin ta ido wai yau har kina fada kan tsaraban hajiya ina nan a bayan ta babu irin zagin da bakiyi mata har fadi kike wai ta magance kowa a gidan mijin sai abinda ta ga dama take masu a gida. Kin ce ita da uwarta ne ai sukai wa yaran ki asiri suka lalace babu mai mayar da sufe wuta yanzu kuma abinda taiwa yan uwan ta ya tsone maki ido Albarka take nema shiyasa kike ganin ta ko yaushe a haka don babu hassada a zuciyar ta ita da uwarta. ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE DON ONLINE NOVEL NE BA A YAFE BA, , , , , 109 Naji dadin dan lokacin da na samu kwana biyu na zauna a gida tare da yan uwa na da iyayyena don naga matsalolin su na taimaka wa wanda zan iya taimakawa a nan kafin na koma na sake shiri a kai. Suma hakan don sunji dadin kasancewa da mu a lokacin don sun nuna muna so da kauna iya a dadin saboda yadda daga ni har yaran mun sake jiki sosai da kowa a cikin su. Sai da na share sati biyu cur a gida muka shirya dawowa Abuja don aikin da ake nemana akan shi idan ba haka ba yadda daddy baya kasan da sai na share kusan wata daya a gida tare da yan uwa da iyayyena. Sai da na kwana uku a kano nagama komai da nake bukatan yi na bar garin da dare muka shiga abuja don haka kowan mu a gajiye yake a lokacin. Wanka sukayi yaran suka kwanta ni da su Atika muka dan yi abin da ya kamata muka kwanta muma. Washe gari monday haka da gajiya na shiga wurin aiki don meeting din da muke da shi a ranan wanda ya zama min dole da sai na halarce shi dole. Bamu fito ba sai karfe uku na rana don haka ban tsaya ba na nufo gida kai tsaye don nai wanka da sallah na samu dan abinda zanci a gidan. Wanda nayi sa, a an gama abincin wanka na fada nafito na tayar da sallah a gurguje don na makara sosai da sallah da ban samu nayi ba a cikin lokacin sa. Sai da na idar da sallah na shirya na fito falon wurin su mama da yara na zauna nan kowa ya fara kawo min korafin shi na baida abu kaza na komawa school. Shigowan maman ihisan yasa yaran dan tsagaita min da damuwada suka sakani gaba dashi wanda bai hanani cin abincina ba a tsanake. Mun gaisa da ita take tambayana mutanen gida nace da ita duk suna lafiya tace dani kun sha gida wanan karon kan ? Nace wallahi kamar kada mu dawo da sauri tace dani kauye din kike cewa kamar kada ki dawo maman Haidar ? Da sauri na dan kallota nace inane asalina maman ihisan ai kowa yabar gida gida ya barshi da kauye da birni in dai da wadata ai duk daya ne ga bawa. Tace hakane aini nayi dana sanin rashin tafiyana da kuka tafi kuka barni don wanan mara mutuncin matar tashibhaka tazo min da wasu irin tika tikan mata a gidan nan wai suna meeting a wurin ta bakiga iya shegen da sukai muna ba a gidan nan wallahi . Dariya ne ya subuce min nace da ita ashe kun sha kallo tace kallon takaici ko may abu tun sha biyun rana suke abu daya har muka kwanta ni dai ban san watsewan su ba ranan. Nace wata sabuwa ke nan kuma yazo muna gidan ke nan gara da bana nan nasan da nawa ya samay ni don dani kowan su zata shigo gidan ranan. Tunda ni suka saka a gaba tace ko kina nan ai bazaki kula su ba don babu wasu itin kilakan mata ne dasu. Nace ko ajikina tunda ba a guna suke alamarin su ba sai dai wacce duk ta kulani shine zasu jini kin san ai saniya bata sani ana son ta kauce sai an tokari bayan ta ko ? Kai kema dai wallahi kawai dai don baki gari ne kawai nace ai gani sai su kara dawowa in don ni dama sukai taron su gani. Tace dani aini ranan naga ikon Allah zakice gidan nan ko wani wurin sai da motane don irin yadda suka baje motocin su ke da ganin su babu mutanen arziki a cikin su wallahi. Nace ai in mutum bai mutum ba bai gama ganin duniya ba mu kuma irin namu kaddaran ke nan da muke gani ko wace da nata irin sallon da take zuwa muna. Tace bari maman haidar wallahi ni har mamakin wanan mutumin nake ji irin wanan rayuwan haka ga yara mu na tasowa suna bude ido da abubuwan barkata a gida suna gani. Don duk wacce zata shigo da nata irin sallon iskancin da zata zo muna dashi a gidan gida ya koma muna kamar gidan yan iska. Nace da sauri ga wanda ya damu da abinda suke ciki ba nifa ban damu da kowa ba balle lalurar mutum ya damay ni. Tace zulfa fa suna lafiya nake cewa da ita suna lafiya ina ga karshen sati mai zuwa zasu dawo nan din itama yadda mukayi da ita. Tace dani kuma again nan din ita ma zata sake dawowa da zama nace ba anan din take ba dama may ye amfanin zamata a can da takeyi ita kadai ai gara ta dawo a hade yafi. Allah ya kyauta tace dani tare da mikewa tsaye tabar falon ran ta babu dadi a raina nace kishi kumalon mata ke nan koni ai ba taki na bar gidan ba ta zauna ita kadai kamar yadda ko wace mace ke bukatan ganin ta ita kadai a gidan mijin ta. Amma ni may zaisa na wahal da kaina ga haka ni da na shiga cikin mata uku na zo a ta hudu shine zan sakawa raina wani kishin banza can. Wai ma akan wani mijin zan zauna ina kishi mijin da ko yaushe baya nuna an mashi daidai a cikin kwashe kwashen mata yake da yawan aure a gidan. Na ja tsuki tare da kiran Hadiza tazo ta kwashe kayan abincin da naci a gabana tare da mike kafafuwana a saman dan stoll din dake a gabana na dafe kaina da hannu daya ina tunanen maganan da hindatu ta fada min nace a raina Allah ya kara hadani dasu wata rana zasu san allura ma karfe ne ba abin banza bane shi. ********* ********* ********* Kamar yadda muka barar da zulfa hakan ne kuwa a karshen satin ta dawo Abuja sai dai tun dawowan ta ban samu zama ba don yara na dake damuna suna fama da lolayin ciki kowan su. Idan na gama da wanan wanan zata kirani da nata korafin kuma haka suka raba min hankali ga aikin da ya taso min a gabana kuma ban da hutu ta ko ina a kaina. Ranan jumma,a maigidan zai dawo kasan don haka a bangaren kowan mu sai shirin taron maigidan akeyi kowa na nuna nata bajin ta akan dawowan shi kamar yadda ko wani gida haka mata keyi idan miji ya dan yi nisan balaguro da gida na kwana biyu. Ashe mu duk shirmay mukeyi a bangaren mu bamu sani ba sai ranan ds zai dawo yai waya zasu iso da karfe sha biyun rana yakuma ce ba sai mun je taron shi ba da yan aikin su yake tare. Ina dakina ina shiri Atika ta shigo tana ce wa dani ga Anty Amira da Aisha sunzo na ce kai sunzo min da matsalan su ke nan daga mai miyau sai amai a cikin su dariya tayi ta fita daga dakin. Sai gasu sun shigo tun daga kofa suke kwala min kira da mummy mummy nace ya salam wanan kiran fa na tashin hankali haka fa for god sake ? Suka fada min a jiki da murnan su muka shiga gaisawa dasu nan Amira take cewa dani mummy wani buki kukeyi ne a gidan yau naga gidan ya cika da motoci mana haka barkatai. Cikin mamaki nace motoci kuma a ina na mike tare da leka window dakina aiko matane na hango suna shige da fice a bangaren amaryan daddy din. Nace kun san mun samu yan bidi,a a gidan yanzu kila wani abin sukeyi kuma a nan ashe ni ban sani ba wai duk dawowan daddy akewa wanan shirin haka . Sai isowan shi gidan ne mukajiyo hayaniya ta ko ina a gidan da shewa wai suna mai sannu da zuwa. Sai dai kamar hadin baki don babu ko mutum daya daga cikin mu mamaki wanan abin ya bashi don haka yayi zaune a cikin mota yaki fitowa daga ciki. Suna tsaye sai iskanci suke zubawa irin na manyan mata yan duniya suna wani girgije girgijen jikin su. Waya ya daga ya kira mu dashi yana fada wai ban mu san ya iso bane kuma wani haukane haka mata suka taru muna a gida haka suna wanan iya shegen haka ? Nace a gidan nan to banda ma saniya a kan su amma ganinan fitowa yanzu ai. A tare mu uku muka dinga fitowa daga part din mu nice ta karshe tare da yarana gaba dayan su muka fito shigan mu ma kawai ya isa mutum ya tsaya kallon mu don kowan mu ya kure a dakan sa sosai rike nake da hannun anty da daddy da suka sha irin nasu adon nan kuma kallo ya koma a kan mu duk wanan iya shegen da suke zubawa a wurin. Motar har lokacin yana rufe haka muka ratsa su har bakin motar daidai lokacin ne ya bude motan tare da sako kafar shi daya waje. Sai na karasa bude motar tare da rankwafawa gare shi na dan kamo shi da saurin ta ta karaso bakin motar tana bangaje yaran dake murnan ganin mahaifin su har anty na buga bakin ta a kofar motar wai tana kamo shi. Wani tsawa ya daka mata tare da karasa fitowa daga cikin motar gaba daya yana kama yarinyar yake fadin kina haukane haka komay da zaki ture min yarinya kina gani. Jaye min daga nan please ya juya gun matan da suka dandazo a gaban mu yana fadin wa yan nan fa kuma daga ina haka suke su ya busu da wani irin matsiyacin kallo na takaici hindatu ta fada jikin shi ya rugumay ta haka ma zulfa tai mashi ban tafi ba shi da kan shi ya jawoni izuwa jikin shi ya kama hannun su jinior muka shiga cikin gidan yana rungumay dani a jikin shi . Nan muka barsu tsaye cikin takaici da mamakin wannan irin cin fuskan da daddy nuna masu a fili gava kowa don su suna ganin duk a inda yar wanan kungiyar take dole tana da razara da matan da ta samu a gidan don zaman su hamshakan mata a gari masu kafafen kungiya na kan su. Wata da take itace hanshakiya a cikin su ce ta fara magana da cewa asha samira banji dadin ganin haka daga gare ki ba ashe kin san baki shirya ba kika taramu a nan don ganin wanan bakin cikin haka ? Yanzu wanan cin fuskan da mijin nan naku yai muna kinga kin kyauta muna ke nan ko may da har zai dubemu haka a wullakance yaja iyalin shi ya barmu kamar wasu marasa galihu a gurin. Daga haka bata sake magana ba ta nufi motar ta sauran ma ganin shugaban kungiya ta nufi hanyan fita suka fara sake magana suna fita daga gidan daya bayan daya cikin kunar rai wai an masu wullakanci an nakasa su. Hankalin Samira yai matukar tashi sosai daga ita sai kawaywn ta biyu aka watse aka barsu a wurin nan suka shiga magana a kaina. Na yarda da cewan da malam baushe keyi da neman tsari na jiki idan bana sheri bane yana da amfani sosai ga mutum watarana. Ga yadda irin zamani ya koma a yanzu duk da malamai na fadakarwa amma zuciyan wasu sai kara bushewa yake wurin aikata aikin kaucewa Allah. Don dai kawai wani buri ko bukata na duniya akan su irin haka ne ga wanan matan don su a nasu ganin kamar duk wata mace a duniya zasu iya shiga da fice su takata yadda ransu ke so a gidan miji idan sun samay ta. Don koda mijin da baida mata daya su ta aura haka mai shi zai tabbata a duniya ba wata mace sai su haka kuma idan kishiya ko kishiyoyi suka samu ba zasu dauki lokaci a gidan basu watsi da wanan macen ko matar da suka tarar a gidan ba. Sai dai duk da haka ba wai kullun ne suke nasara akan ko wace mace da suka sama a gida ba akwai wa yanda kan dan fi karfin su a zauna aita fafatawa dasu a gidan Allah ya tsare mu daga sherin irin wa yan nan mata masu mugun hali na rashin tsoron Allah. Nasan ba komai daddy yakewa wanan rawan kafa haka ba sai yadda zai ga komai ya daidaita a tsakanina dashi wanan karon. Yayin da su kuma sauran kishiyoyina suke ganin ai asiri ne nai mashi tare kuma da ilimi da kyau din dake gare ni yake min wanan rayuwan haka. Wanda nina san ba haka bane alamarine na Allah, sai farko idan ka samu daukaka gun Allah sai ya tsare ka ga komai. Ke dai yar uwa maida al, amarin ki a gun ubangiji a koda yaushe sai Allah ya tsare ki daga duk wani abin ki a gare ki. Duk wanda ya nufe ki da sheri Allah yana tare da ke sai ya koma a kan mai shi duk wanan aikin dake gabana bai hana ni kullun tsaida dare abokin hirana ba wurin mika koke na ga ubangijina akoda yaushe. Rana ce kawai nakan dan samu lokacin aiwatar da rayuwana na duniya a cikin sa don shi tashin dare wani alamari ne dake tafiya da sabo da saka abin a zuciyar bawa. Fitina ce sosai a tsakanin Samira da maigidan yayin da mu kuma sauran iyalin nashi muke a cikin farin ciki da dawowan shi don mun godewa Allah yadda taso taga mun nakasa a kan shi hakan bai samu ba a gare ta don bai shiga guntaba ma balle ta aiwatar da duk wani shiri nata akan shi balle abin yai tasiri gareshi yadda take so. Don ba karamin gagarumin shiri tayi ba kamar yadda mata da yawa suke wanan irin shirin ga maigida idan ya kwana biyu baya cikin iyalin shi. Wanan baiwan ne daga Allah don badon Allah yaba tsare bayin sa ba da wata irin shirin da kishiya take a kanta ko daga kai miji baya iya yi ya kalle ka da suna wai abokiyar zaman ta. Amma da yake abin daga Allah sai kaga ubangiji yana kare bayin sa masu dogaro a kan shi suna yawan kai kukan su a gareshi ko da yaushe. A nan Allah ya taimakeni a kan Samira don haushin ba nawa bane ni kadai don ya shafi kowan mu saboda ta shiga wurin shi ta samay shi tare da zulfa suna soyewan su washegari da ta koma kuma ta sake samun shi tare da hindatu . Sai haushin nawa ya rage ya koma a kan su take cewa da kawarta dama hakane ana zaton wuta a makera sai a samayta a masaka. Don haka tai muna bugun dan kade gaba dayan mu tace mune mukai mata wani sihiri miji ke ganin bakin ta haka daga dawowan shi. Ranan da girki ya dawo a kaina ne muka kwasa da daddy din don har lokacin ina a kan bakana na rashin yarda dashi da banayi. Ya kirani a waya yake fadin nazo na samay shi ya dawo nan na shirya na samay shi a falon wuri na samu na zauna daga nesa kada dashi tare da gaida shi da dawowan shi. Ya amsa min ba tare da ya dago kan shi ba yace maman Jinior ke nan wai ni ban fahinta ba ya fadi yana kokarin rufe takardan dake a hannun shi. Ya dago yana mai kallona cikin mamaki nake cewa dashi na may fa ke nan daddy don da zaran ya kirani da wanan sunan na maman jinior nasan da akwai magana ke nan daya taso a kaina. Yace wai har yanzu kina nan akan bakarki ne na kina guduna ina da cuta ko may ? Nace ni bance kana da cuta ba daddy kawai dai don na fahinta da irin auren nan da kake a yanzu ko a kai tsaye ne ko da binciki gama yadda duniyar nan ta mu ta koma a yanzu. Murmushi yayi yace dani yayi shine har yakai bana samun kulawan da aka saba bani ko kadan kamar baya. Nace ba haka bane wanan kawai dai dorowa ne don ni ban ma san ka dawo ba gidan ai. Yace dani karbi wanan na mika hannuna na karba a cikin ladabi tare da budewa sai naga ai form ne na wani makaran ta a kasan saudiya dake garin madina. Ga kuma sunayen yarana a jere a ciki su hudu a form din na gani da dan wurin zulfa guda, da sauri na dago kai cikin mamaki ina kallon shi tare da son jin na may ye wanan form din kuma daddy ? Yace dani kin karan ta aiko ? Nace na karanta sai dai ban fahinta ba yace ok yaran nan nake son akai su can suyi karatu dukkan su. Nace dukkan su daddy yace ko baki ra, ayin hakan ne ke nace a, a ni may zance abinda ka zartan ai shine nawa. Yace good ina da raayin yarana su fahinci addini sosai a rayuwan su tunda Ubangiji ya hore min abinda zan iya daukan nauyin su a hakan dashi. Masha Allahu nace dashi yace na gama komai akai saura tafiyan su idan lokaci yayi Allah ya kaimu nace tare da fatan Alheri ga wanan tsarin. Yace haka nake son ji wanan halin naki yasa nake kara son ki a raina ko yaushe Rahama don biyayyan ki a gare ni sai dai kuma gashi ana yabon ki ga sallah kina son kasa yin salati kuma. Nai murmushi nace ni din kuma daddy may kuma nayi baiyi magana ba ya miko min wani takarda dake gefen shi again yace karan ta wanan mu gani kuma. Na karba na bude sai naga takardane na test da aikai masu shida Samira din wata shidda da suka wuce a baya. Hakan na nufin ayi test din ne kafin su daura auren su dashi kuma a sibitin mu ne akai masu wanan gwaji din da nake son gani. Ina kai karshen takardan na sauke ajiyan zuciya tare da dago kaina na dan kalle shi ina kokarin mika mai takardan. Ya karba tare da fadin kin gansu da haja yanzu ko akwai sauran wani abinda kike son ji kuma don naga kina daukana ban san abin da nakeyi ba ne ko ? To ki sani ni jarabar tawa bata kaini ga har na dinga yin abu a ido rufe ba haka yadda kike nufi nakeyi din. Na dan musguta zamana kadan cikin jin nauyi da kunya ina cewa dashi ni abinda doka ya tabadar nake magana a kai, bawai nace kakai ga hakan bane ai. Ya ware hannaye shi tare da fadin what ever d case dai yanzu kin gani a zahiri dama na kyale kine naga iya gudun ki. Murmushin yake nayi tare da dan dagawa na kara mika mai takardan nace abinci fa akawo yanzu ne ko sai anjima. Yace idan an tausaya min abani don tun karyawan safe danayi ne a cikin nan nawa har yanzu. Mikewa nayi da nufin zuwa dauko mai abincin nasa sai naji yace dani ki turo min zulfa tazo idan kin tafi na ansa da to na fice falon. Sai da na shiga guri ta na nufi nawa bangaren inda na fara hada mai kayan abincin da na shirya mai da kaina. Koda na koma na samay su baram baram da ita tace bata yarda da zancen zuwa danta wani kasa ba naji tana cewa ita ba yaran ke gunta da yawa ba da za, a dauke mata dan ta daya akai wata kasa wai karatu. Ban tanka su ba na shiga shirin abinda nake a gaban shi tare da sauraren maganganun su din. A cikin fushi ta bar falon sai lokacin nace dashi tunda kaga hankalinta bai kwanta ba don Allah daddy a bar zancen yaron kawai. A harzuke yake cewa dani akan may itakeda iko dashi ko ni da zance ga abinda nake so har ta tsaya musanta min ga hakan. Ni naja bakina na shiru daga hakan shima din shirun yayi na dan wani lokaci kada na juya gare shi tare da fadin bisimillah ga abincin nan. Komai ya koma muna normal a tsakanin mu dashi ba sauran fitina sai dana fita girki Samira ta karba wanda nake gani a ranan ne ma ta dawo gari. Mu dai da asuba muke jin kururuwan fitina a gidan wanda tun lokacin ban kara biyewa akan su ba. Ban kuma sake jin duriyar Samira din ba ma a gidan da sannu loiacin tafiya yara na yayi sai naga ashe ba da dan wurin zulfa za ayi ba ashe. Sai da na kai su kano sukai sallama da iyayyen mu mukai tafiyan da hajiyan daddy da za a kai asibiti saudiya sai ihisan da muka tafi da ita da Atika. Makaran ta ba laifi a wurin tsaruwa kuma yaro baya dawowa sai idan ya sauka yayi hadda za, a bari yazo gida ya kwana biyu idan yana da bukatan ci gaba da karatu sai ta koma yaci gaba dayi wasu littafai da kuma fannin boko watau secondary di su har digree. Abin yai matukar bani shaawa sosai don nasan insha Allahu idan Allah ya raya min su nan gaba kadan zanyi alfahari da su, bani ba har da kasata baki daya da yan uwa. Bayan mun barsu ne mun dawo masauki nakewa daddy godiya da kuma fatan alheri ga yin hakan da yayi. Akwai kewa amma da yake karuwa ne ga kowa daurewa nayi ga abin na fitar dasu a raina baki daya. Bayan mun dawo ne nake samun labarin wai ashe ba karanin fitina akayi da zulfa dashi ba har takai gun iyayye yasa ya janye maganan tafiyan yaron nata. Ga kuma labarin Samira da tazo har gida tai masu tas har tana ikirarin wai sai mun gani da baki dayan mu abinda zatai muna kamar yadda mukai mata. Amira da Aisha suka haifi diya su duka maza muka sha buki sosai na suna Nasir ya gama karatun shi shima yafito da aninin shi na su na soja. Zama dai ne na hakkuri har lokacin a tsakanin mu don ba wai an daina zaman kishin bane a tsakanin mu. Shekara takwas yarana maza sun zama hazifai na addini tako wani fanni sun zo gida kowan su ya girma sosai. Ida na kalle su sai naga tankar ba nice na haife su ba da cikina mahaifin su ya zama don sosai yanzu kafan shi ya kama kasa ga arziki ga kuma yara sun girma. Haka yasa ya bukaci da na aje aikin gwaunatin da nake na zauna gida a cikin iyalina ban yi mashi mussun hakan ba na aje kamar yadda ya bukata na zauna gida ina dan duba asibitin daya bude a kano duk da haka ida aiki ya taso muna zaga jahohi muna aiki da gwaunati din don kwarewar mu ga aikin . Hajiyan daddy ta rasu don haka muka kwasa sai kano a lokacin yarana duk suna gida baki dayan su kowa ya gan mu sai ya yaba muna. Mun dawo daga gidan hajiya ta gan mu yaba tsaye tare da wasu mutane a kofan gida suna magana mu gaidasu zamu shiga naji mutumin na fadin yanzu kana nufin duk ita kadai ke da wanan yaran haka tubarkallah masha Allahu. Mun gaida mutumin naji daddy yace dashi ka gan ta nan kyautar Allah ce a gare ni don ga sadaukar da rayuwa Allah ya ba ita takuma zamau min marucin kan dutse a rayuwana yanzu, , , , , Alhamdullahi yan uwa wace nabatawa akan wanan novel din ta yafe min don Allah don dan matsalar da aka samu akan tsaikon da mukai ta samu dashi. Don Allah kuyi hakkuri da zainabun ku yan uwa uwayena da yayyena da kannina sai idan Allah ya nufa mun sake haduwa a cikin wani sabon novel din namu nan gaba kuma don Allah kuyi hakkuri ku yafe min yan uwa, , , , , ZAINAB IDRIS MAKAWA SEENABU