. . . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣1❣ *©Mymounerh Basheer* *®NWA* *littattafan marubuciyar* *soyayya gamon Jini* *Raheena* *kishiyoyina* *habibullah* *noor ala noor* *Na Aminta dake* *gimbiya maimunatu* *Akan kaskon suya* *Zeenatu* *Ashe haka so yake* *Queenmeemi.WordPress.com* *************** BISMILLAHIR RAHMANIR RAHEEM *_k'aramar hukumar bunkure,dake jihar kano_* Babban titin dake garin bunkure wanda ya cika da d'aukacin jama'a kowanne ka kalli fuskar sa arazane yake wasu kuma gudu suke ci,ga wasu a kwance dai-dai kusa da wata Babbar mota na gano yarinya Yarinyar da bazata wuce shekara 3 aduniyaba a zaune kusa da wata mota sai ihu take,Jikinta sai karkarwa yake kukan natan Sam baya fitowa sabili da taci kukan harta k'oshi. Daamm!!! k'ara ce ta kuma tashi, take mutane suka hau guje-guje yarinyar da Bacci ya fara d'ibanta ta tashi firgigit ta k'wala k'ara ba wanda yasan tanayi gudu ta hauyi irin Na yara bawanda ke Kula taa kowa ta kansa yake ,ke sai kiran momy take da dady ,wata mota ta gano gurin tayi aguje taje aguje tana bubbugawa dady! dady! neman iyayenta take Amma ko alamarsu Babu ga wajen ya hargitse kowa takansa yake Saboda tashin bomb din da akaji wanda yazamo tamkar wata jaraba gun wani mutumi ta yi ta baya da gudu tayi wajensa tana dady. juyowa yayi a tsorace yayi arba da ita , yana shirin magana k'arar bindiga ce tafara tashi tas! tas! tas! tas! kakeji nan da nan waje ya kuma hark'ewa hayak'i ko ta ina. yarinyar da duk Jikinta yajike da fitsari ga bakinta Na jini ,mutumin nan ya falfala yafara gudu ,yarinyar tabiyoshi dady! dady! sojojine suka tawo aguje suna harbi nan da nan mutumin yai wata kwana yarinyar tabishi tana ihu inda ya b'uya taje ta tsaya ta dafa shi "dady momma" hankad'eta yayi yace "Yau naga jaraba ke ina iyayenki? ana wann nan tashin hankalin don sakaci", tureta yayi yace ta bar wajen, tafiya tayi da gudu tayi wani waje tai kwana tana sangal-tangal saboda ciwo dataji a k'afa wani yaro ne ya arto yana haki yai ciki da ita ta fad'i k'asa d'agowar da Zatai akai harbi Allah ya taimaketa ba aharbeta ba Amma tsoro yasa ta suma ganin hakan tausayi yakama mutumin ya fito Daga mab'uyar sa ,yazo ya d'auketa ya runtuma aguje yana gudu seda yayi nisa yaje motar sa dake ajiye ya ajiye ta agaban mortar dayake motar d'aukan kayace yara su hud'u ya ganni a bayan motar sai ihu suke ya kallesu yace " ina iyayenku"? D'aya ne mai wayo yace "nan mukazo muka b'uya",Sauran kwa ba wanda yayi magana sai kuka duk jikinsu k'ura da d'an Jini-jini ajikin su,jin- jina kai yayi kawai ya shiga motar. ************ *K'auyen mangalu* Jan motar yayi ya fafara aguje nan yiyi hanyar k'auyensu tafiyar awa d'aya da rabi ya kaishi k'auyen mangalu wanda yake a k'ark'ashin k'aramar hukumar bunkuren, Bayan yaje k'auyen nasu su, take bai zarce ko ina ba sai tasha,ya bud'e motar ya fita yaran yad'ebo, ya sauke su gaban motar yaje don d'auko yarinyar wayam ya nemi yarinyar ya rasa neman duniya yayi bega yarinyar ba mamaki k'arara afuskarsa "kode aljana ce tsuka yaja inajin Aljana ce sede ko sauka tayi",nan yayi ta dubawa bai ganta ba Sarkin kasuwa ne yazo aguje "Malam lado me nakeji ne agari wai cikin gari bomb ya tashi da Gaske ne kuwa"? "Tabbas! hakane Sarkin kasuwa Ni kaina wallahi abun yaban tsoro, lodi fa nake zan kai kaya kasuwa kawai mukaji k'arar tashin bomb ai Wallahi munga tashin hankali don an mutu agun ,dak'yar Na sha,kaga kuwa abin tausayi harda wata yarinya dana gani agun sai karakaina take tana neman iyayenta kawai sai yarinya ta dinga bina tausayinta yasa Na d'auketa abin mamaki munzo nan Daga sauka din na sauke yaran can na duba bangan taba". "Allahu Akbar Allah ya k'ara kiyayewa" sarkin kasuwa yafad'a Yaran nan su hud'u malan lado ya mik'awa Sarkin kasuwa da bashi dubu d'aya kan akaisu Police station da ke cikin garin bunkuren ko za asamu iyayensu , sarkin kasuwa yace wa wani d'ahiru ya rik'e yaran ya basu abinci shida MLM lado suka hau dube-duben neman yarinyar nan ,Amma basu ganta ba ,nan suka dawo lokacin yaran Sunci Sun sha MLM lado ya deb'e su sarkin kasuwama ya shiga motar . Sun fita titi caraf idon sarkin kasuwa ya gano masa yarinyar nan gefen titi da Rabin bread a hannu tana ci tana kuka,yace "hala dai ita ce waccan"? Malam lado yace "ita ce" direct motar ta tsaya suka fita abin tausayi jikinta zafi zau suka d'auketa,sunje police station suka bada yaran kan b'atansu a dalilin tashin bomb d'in ,sunayensu a ka d'auka da hotuna,da yake gidan sarkin kasuwa anan yake yasa aka bar yaran a gidan nasa,su kuma 'yan sanda suka hau sanarwar neman iyayensu. malam lado ma ya tafi kan duk yanda akai Skasuwa ya Sanar mai. *by Queen meemi* . . January 2017 Queen meemi ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣2❣ *©Mymouner Basheer* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* wajen yamma MLM lado ya je gida a gajiye shigar sa gida ya Tarar da gwamma na tsinkar zogale d'agowa tayi tace ''MLM Yau kayi nisa da yawa" ,ruwa ya d'ebo a randa ya sha San nan ya zauna atabar mar da gwamma ke kai,yace "ai Yau munsha da k'yar nan ya labar ta Mata dafe k'irji tayi "kai Amma ka auna arziki' ,dama naji labarin birni bai shiga ta Dad'i, gashi yazo garin nan yanzu" alamar jimami ne fuskar sa,yace "ai kede bari gwamma Allah ya kyau ta dai" kallonta ya kumayi "wai Ni ina jummai ne"? tab'e baki gwamma tayi "ai kasan ayawoma ce Sam bata zama agidan nan muddin kasa k'afa ka fice".murmushi yayi don inda sabo ya Saba da halayen gwamma wajen yiwa jummai sharri,sallamar jummai ce ta katse musu hirar da harara gwamma ta sauki jummai da murmushi d'auke a fuskar jummai ta tsugunna tace "malam Barka da dawowa ,naje gidan kaka ne gaida ita Batada lafiya" nan yace bakomi jummai nasan da dalili ai " gwamma tace "tab! Lalle malam ka sakarwa jummai da yawa ace Mata ta fita bada izininka ba, Amma bazakai Mata fad'a ba,ita ga matar so" tashi jummai tayi ta d'auko kwanon abincin malam ta aje mai da ruwa daya ke itace da girki Yau, nan ya hau ci dama yunwa ce ke cinsa. *BAYAN SATI D'AYA* MLM lado na zaune a soro yana jin radio domin tun lokacin da bomb ya tashi bai koma cikin gari lodin kaya ba, don yaji labarin wajen ansa masu tsaro , kuma gashi saboda tsoron karyaje tsautsayi ya afka dashi, sallamar sarkin kasuwa ce ta katse mai jin radio d'in da yake da fara'a ya zauna suka gaisa mudi D'an MLM lado mai kimanin shekara goma ya kawo mai ruwa,sarkin kasuwa yace "wato MLM lado yaran nan cikin ikon Allah duk anga iyayen su biyu a asibiti akaga nasu iyayen sauran kuma duk yan uwan su ne suka karbe su duk ta dalilin faruwan tashin bomb dinne yara suka bata ,kuma duk Daga wani garin suke,wani hanzari ba gudu ba ,yarinyar nan Sam! ko alamar wanda ya Santa ba agani ba balle su zo",gaban MLM lado ne ya fad'i cike da tausayi yace "ikon Allah yanzu ya za ai ke nan sarkin kasuwa yace ai police sunce mu rik'eta agunmu zasu cigaba da dubawa gashi Ni kuma zan tafi garin gabas jibi" ,mlm lado yace "to ai ba matsala ka kawota gurina muga yanda Allah ya yi ,haka sukai sallama ya tafi. *WASHEGARI* wajen k'arfe goma sha d'aya saiga sarkin kasuwa nan da yarinyar suna tsaye sai ga Shi ya fito musabaha sukai da Shi nan yace "to MLM lado gata nan godia malam lado yayi mai ya tafi Shi kuma ya d'auketa suka shige ciki. gwamma na hura ice jummai kuma na tankad'e MLM lado ya shiga kallo suka bishi da shi ,murmushi ne Akan fuskar sa gwamma tace "malam wan nan yarinyar fa"? ,kallonta yayi yace "Dad'i na dake wutar ciki, to 'ya na samu" nan ya kwashe duk yanda abun ya faru ya gaya musu jummai harda kuka saboda tausayin yarinyar gwamma kuwa tace "to rik'eta zakai kenan"! MLM lado yace "to ya zanyi Allah ne ya had'ani da ita" nan ya kalli jummai yace "ga 'ya na kawo miki ki na Kula da ita, kafin Aga iyayenta,da murna ta karb'eta dama bata da yaro tun lokacin da yarta hansai ta mutu har yanzu bata K'ara haihuwa ba,kallon yarinyar tayi tace "ya sunan ki ,batai magana ba sai D'an motsa baki da tayi,malam yace "kinga jummai kisa Mata suna na wucin gadi sai ana kiranta dashi kan Aga iyayenata". "MLM zan ce Mata hansai sunan marigayiya",gwamma tace "Amma ke kan jummai anyi solob'iyo ayi dai mu gani Daga ganin sarkin fawa sai miya tayi zak'i" MLM lado yace" kinga gwamma ban San neman magana tunda bake na bawa ba baruwan ki" tab'e baki tayi ay ba tun Yau nasan kafisan jummai dani ba ,me zanyi da tsintacciyar mage, nan ta buga cinya ke kuma jummai dani kike zancen"....... *By Queen meemi* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣3❣ *Jan 2017* *©Mymouner Basheer* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* haka jummai ta d'auki hansai ta shigar da ita d'aki ta fito ta D'ora Mata ruwan zafi tayi Mata wanka San nan ta wanke kayan ta ta shanya, d'akin nata dake d'auke da azara ta shiga da hansai ta ajeta, tana na zaune tayi zuru nan ta d'aura Mata zani ta bata abinci ta ci,gwamma ce ta shiga d'akin "to gulmamma sai ki fito ki tuk'a tuwon da miyar" jummai ta d'ago "to yaya gani nan" madafar taje ta duba kayan kad'I bata ga kuka ba, nan ta fito tace "yaya ina mudi yazo ya sayo kuka" gwamma tace "ke bazafa ki ta kurawa yarona da aike-aike ba,yanda kika Saba fita sai kije" haka jummai ta d' au mayafi ta shiga Mak'ota siyaowa bayan fitar ta, gwamma ta shiga d'akin jummai, hansai na tsugunne tana rawar d'ari tsayuwa tai ta k'ura Mata Ido "oh malam da kwashe -kwashe ko ina ya kwaso wan nan yarinyar oh" d'aga kai hansai ta kalle ta gwamma tace "ke Maida idon ki k'asa wa yasani ma ko mayya ce ke" wani kwano ta dauka ta fita dai-dai lokacin jummai ta dawo nan ta D'ora girkin ta shirya hansai. *MALAM LADO* malam lado asalin sa d'an nan garin bunkuren ne yana zaune anan mangalu d'in ne tun iyaye da kakan ni ,su uku ne agun iyayen su, Daga Shi sai k'anin sa sai k'anwar su wanda duk suna garin suma da iyalansu,yana sana'ar tuk'in mota yana lodin kaya zuwa gari- gari,gwmma itace matar sa ta tafari haladu shine d'ansa na farko da ita Amma Allah yayi masa rasuwa sai mudi da aka haifa bayan haihuwar sa da shekara uku ya auro jummai, zaman lafiya suke yi farkon kawo jummai Amma bayan samun cikin jumman, sai gwamma ta uzzura Mata ta tsangwameta ,Allah yayi gwamma da fad'a ga San girma da son komi ace itace a kai ga k'yashi ,batak'i ace jummai tana mata biyayya ba don ma malam tsayyye ne shiisa take D'an ragawa jummai bayan haihuwar jummai shekarar 'yar ta hansai d'aya aduniya tace ga garinku, tun Daga time d'in bata kuma samin ciki ba. wan nan dalilin ne yasa gwamma ke shuka Mata tsiya Musamman wajen aike sai dai taje da kanta badai ta aiki mudi ba, hakan yasa take lullub'i ta tafi da kanta ,inkwa aka samu mudi yaje aiken to sai ta bashi kud'i wan nan ke nan. *bayan wata d'aya* *karfe 8:00 da safe* hansai ce tsaye bakin famfo jummai na k'ok'arin dafa Mata ruwan zafi saboda sanyin da ake ga kuma koko da take San damawa gwamma ce ta fito ta bud'e tukunyar ta kamfaci ruwan jummai ta d'ago "yaya fa ruwan wankaan hansai ne fa ,kuma Dana koko". gwamma ta juyo da harara Akan fuskar ta, "na d'iba d'in mudi ne ke San wanka Yau kwanan sa hud'u bai ga ruwa ba, don zakiwa wan nan figaggiyar yar shine zaki magana kan na d'ibarwa D'an gida,koko kuwa dole ki dama" tsaki tayi afujajan ta yi hanyar band'aki. jummai bata ce komai ba sai ma d'aukan hansai tayi ta Goya ta ,malam dake fitowa da buzu ahannunsa zai je soro ya tsaya yace "kaga jummai da yar ta" murmushi tayi tace "wallah MLM gata da hak'uri sai dai tana yawan cewa wai mamma da dady" ,alamar tausayi ne a idon malam yace "Allah sarki, wallahi kullum naga yarinyar nan sai naji k'walla a idona saboda nasan duk inda iyayen ta suke basa hayyacin su" ,jummai tace "Allah dai ya sa agansu. MLM yace "ameen" nan ya fita ,sai wajen 11 hansai ta samu wanka. lokuta sunja haka watanni Yau kimanin watan hansai shida, Babu amo ba labarin iyayen hansai haka malam yace yaji ya Gani zai rik'e ta amana son yarinyar yake kamar me komai ya samu itace nan ta koma cemai dady duk ganin sa take shine ba banta haka jummai tamkar 'yar cikin ta nan tace tana ce Mata inna sosai - sosai yarinyarta ware,ganin irin kulawar data ke samu nan gwamma ta kuma tsanar hansai ko gunta bata San zuwa da taje zata kwad'eta tace tafi can tsintacciyar mage mudi kuwa cin zalinta yake shiisa bata zuwa inda yake. haka dai rayuwa taci gaba da tafiya da k'alubale da dama Yau ga hansai nada shekara bakwai ahanun goma a hannun malam lado wanda in aka had'a da shekaukun ta shekarar ta goma kenan,hansai ta zamo yar da suke so kullum tashin duniya MLM ya kalleta sayya ji kamar yayi k'walla, (haka ake San bawa mai yawan tausayi) wanda ta zamo jinin jikin jumai da mlm. Sallama hansai tayi ta shigo da Allo ahannunta ta dawo Daga makarantar Allo ta dawo ta yamma. Nan taci karo da mudi take ya kai Mata mari wasu wuta ta Gani nan ta durk'ushe tana kuka gwamma dake b'arar gyad'a tana watsawa abaki tace "kayi min dai- dai ita ba Mara kunya ba, wai waccen munafukan marik'iyar taki itace ke zugaki har Kina had'a hanya da mudi" ,jummai tace "Haba yaya yanzu ai bai Dace ba kamar mudi yayi Mata wan nan Marin,saboda ai kwarin su d'aya ba", gwamma tace rufen baki mai rik'on wahala tashi tayii ta janyo hansai ta mik'ar da ita, had'a Ido sukai da gwamma nan ta yiwa hansai dak'uwa, "daina kallona da Ido kamar gujjiya". d'aki suka shige jummai tace "hansai ki hak'r kinji mamanki gwamma ba wai sanki ne batai ba, kawai haka take" ,hansai ta jin-jina kai "ai inna na sani" Amma azuciyarta Sam tarasa mesa gwamma ta tsane ta. Zama tayi tana tilawar karatun ta, jummai ce ta shigo rik'e da rubutun tsari tabawa hansai ta shanye wanda kullum sai an bata ko Tai Mata tofi aruwa ta sha ,yanzu izifin hansai arba'in, domin malam ma yana da sani dai de gwargwado yana koya Mata. Akwai wata makarantar boko a bayan gari ita hansai ke tafiya tana aji d'aya 2 na fimamare duk da yaran garin basa zuwa karatun, a ajin nasu basu fi su goma ba domin wataran ma a bakin bishiya suke zama ahakan hansai ke dagewa domin wataran malam shike takawa da k'afar sa ya kaita San nan ya dawo ,yana so tayi karatu koda secondary ne daya ke malam nada wayewar ilmi sabili da yawan tafiyar sa ,mudi kuwa Sam baya San karantun shiisa inaga shekara d'aya kawai yayi yana zuwa ya daina Shi isa MLM ya turashi gona da yake malam yanzu baya tuk'in motar shiisa ya koma gonar. hansai kuwa duk lokacin da jummai Keda girki to tare suke yi, tana koya Mata shiisa jummai bata da damuwa kokad'an, ga tsafta sabili da jummai na da tsafta shiisa hansai ma ta tashi cikin tsaftar Sam bazaka ganta futu-futu irin sauran yaran kauyen ba,sai ka d'dauka sune asalin iyayen ta saboda kulawa. ganin hakan yasa gwamma ta bud'e huta kan sai hansai ta dawo hannunta, jummai bata iya fad'a ba, Amma aranar tace Sam bazata bawa gwamma ba ,malam dake shiga gidan ya shiga yace "Haba gwamma yada haka bakya tunanin lalurar dake jikin ki" nan ta fasa kuka ,"ai MLM dama nasan kafi San jummai shiisa ganin hakan yasa ta samu damar yimin habaici,wai tana da yar huce takaici lo bata haihuwa" don na rok'eta kan hansai ta dawo hannuna saboda cikin dake gareni yanzu ban iya komai shine ta bud'e min wuta" . jummai kuwa in Banda kuka ba abinda take saboda tasan k'arya ta Mata. MLM yace "duk hakan bata taso ba, naga hansai ko agunwa take, wata zata iya sata Aiki, to meye abin tashin hankali" gwamma tace "nikam malam ka bani hansai kawai idan ana San zama lafiya ta dawo guna kawai" . Malam yace "Haba gwamma ki zama mai adalci mana sai da kika ga yar ta fara zama mutum San nan kizo kice a baki? bayan ga wanda taci kashin ta". gwamma ta shige d'aki tana kuka jummai tace "malam na yarda ta koma tunda nasan ba rabuwa Mukai ba", k'ank'ameta hansai tayi ni inna nafi San gunki". MLM yace hansai 'yata ki koma gun ta kinji kan ta haihu Kinga k'ani zaki samu", saida jummai ta lallasheta San nan ta yarda. da gudu taje soro tana kuka innar ta kawai take so Sam bata san gwamma Amma ba yanda zatayi dole ta koma tunda ma suna tare. *BY Queen meemi* . [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣4❣ *©Mymouner Basheer* *®NWA* *Queenmeemi.wordpress.com* _Salamu Alaikum fans masoya littafina ina mik'o gaisuwa gunku,na gode da kulawarku_ *Sati biyu da komawar hansai dakin gwamma* komawar hansai d'akin nan gwamma ta shiga takura Mata da tsangwama. kullum cikin aiki ada hansai Sam bata zuwa rafi Ko yo itace domin jummai bata saka ta koda deb'o ruwa ne Amma gwamma da gayya zata aiketa deb'o ruwa Ko ita cen sabili da malam baya so. yau ma da ake rura uban sanyi wajen k'arfe takwas na safe,hansai na kwance tana barci gwamma ta d'akawa hansai duka tare da kai Mata hauri ,firgigit ta tashi tana zare Ido, da k'arfi ta fad'a "inna" jummai dake zaune tana gyra ta mik'e ta fito tsakar gidan a tsaye ta tarda hansai,na rawar d'ari da botiki a hannu,gwamma ta fito "ke hansai tafi rafi" jummai tace "haba yaya ina hansai ina zuwa rafi" . tsaki gwamma tayi "to munafun- fun yara nawa suke zuwa rafin, su dama suke "yan gida balle ita tsintacciyar mage daba galihu gareta ba" ,tsawa tayiwa hansai tace "shige muje Ke Kuma," haka suka yi hanyar soro gwamma tace saura ki Dad'e ga su tsahare can za su je". nan ta dawo ciki har lokacin jummai na tsaye nan ta kalli gwamma tace. "Amma yaya kin San dai hansai tafi k'arfin tsintacciyar mage Wlh hansai agarin nan bata da maraici, malam da zai tafi rano sai daya jaddada kar a Aiki hansai rafi Amma kikayi sabili da kinsan gurin ba tsaro". "lalle jummai wuyanki ya isa yanka, ina fad'a Kina fad'a Ko? ,to kisani yanzu hansai ba a hannunki take ba sai yanda na yi da ita Wallahi". jummai tace "yaya hansai 'ya tace domin jinta nake har b'argo na don haka ina nan bazan bari ta cutu ba, domin Amana ce awurin mu . tsaki gwamma tayi tace "JUYA Kawai"littafin Feenaat ja afar) San nan ta shige daki jummai da rai sakato ta juya cike da jin haushi sa b'acin rai na kalmar juya data kira ta. *Hansai* tun fitar hansai take kuka nan taja birki kusa da wata bishiya ta zauna ba yaran data ga ya fita iyan zu sai ita, saboda yanda ake sanyin nan, ga rafin da nisa tashi tayi ta hau gudu cak! ta tsaya ganin cakau sunan wata akuya ce mai tunkuyi a garin k'ahonta cako- cako data ga yara Mata zata bisu tana tunkuyi, jikin hansai bai Dena b'ari ba gudu tasa akuyar ta hau binta. Muntari dake tawo wa ya tsaya cak! take ya kori akuyar ya kalli hansai yayi murmushi "kema tsoron cakau kike"? "Eh wallahi agaba na ran nan ta fasawa d'ahiru hannu" murmushi yayi keba k'anwar mudi bace"? "eh nice" ta fad'a a tsorace . "Ina zaki" "rafi zani d'ebo ruwa"d'aga kai yayi yace "kai da sanyin safiyar nan, duk yaran ma ban ga kowa ba ana sanyi fa. muje na rakaki"haka suka je ya d'ebo ruwan ya d'auko mata suka juyo yana rik'e da botikin har ya kaita k'ofar gidan su ,San nan ya koma. tana kai ruwan ta koma ta fara hura wuta gwamma nadaga d'aki tana Shan koko yunwa duk ta ishi hansai sai data gama San nan ta bata koko da k'osai biyu tasha ,gyangyadi ne ya kama gwamma nan hansai ta sulala tayi d'akin jummai(inna) tana zuwa ta kwanta kusa da ita suna ta hira ta K'ara Mata abincin taci. ji tayi an kai Mata shuri gwamma ce tsaye tace "Ke hansai wancen wankin nawa wazai miki ehe"? idon hansai ya kawo ruwa tace "mama gwamma bazan iyaba sunyimin nauyi" dundu ta kai mata "Dan gidanku a banza zamu na baki abinci ina lefin rik'on da ake mike, tashi kona masge ki" hansai dake shiga rud'ani duk lokacin da gwamma tace Mata rik'on ta suke, Ko tace Mata tsintacciyar mage,sai taita tunanin kodan tsanar da rai Mata ne yasa take Mata hakan, tashi tayi tana matse hawaye, jummai ce tace "yaya kawo wankin nayi saboda hansai bazata ita ba" . "oho can ta matse miki jummai nidai Naga kaya awanke dan me nace ta dawo d'aki na" . wani uban wanki ne ta tulo jummai ta jin-jija kai tace azuciyan ta, ran nan inaji mudi yace bazai Mata wankin ba ,Amma da zalunci yarinya k'arama ace ita zatayi wan nan uban wanki, haka tayi wankin nan tayi ta shanya . *Washegari*. washegari malam ya dawo,sunyi murar dawowar sa yayi farin cikin ganin hansai da dare yana zaune suna hira ya fito da wani takalmi me kyau irin na roba me ado ya bawa hansai yace "ga tsarabar ki" nan gwamma tace "ina na mudi" kallonta yayi "haba gwamma ya kike haka ne? inaga mudi saurayi ne mai zan bashi in Shi bai bani ba? hansai kwa yarinya ce" tabe baki tayi tace "ayi dai mu gani" tunda malam ya dawo ta daina aiken hansai rafi sai de aikin gida duk ta fige ta rame ran nan malam ya shiga gidan yaga hansai na wanke kayan gwamma kwalla kiran gwamma yayi ta fito yace "yanzu don rashin imani har hansan nawa take da zata wanke manyan kayanki, ina mudi ai shi ya kamata yayi" gwamma tace "ita nayi niya haba! sai kace 'yar gwal ba dangin iya ba na baba". malam yace d'a de ai na kowa ne hansai de 'ya tace ina k'aunar hansai har raina kamar yanda nake son mudi, don haka karki Kuma sata Aiki me wahala . k'walla kiran hansai yayi yace taje gun jummai ta zauna Ko taje waje tai wasa da tsahare. Ahankali ta fita taje can waje ta zauna tana ..kubiyoni. *by Queen meemi* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣5❣ *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* _*sadaukarwa ce ga Bashir usman family's*_ _sis Marwa Phart bb ,Anty maijidda ,Nazifa Ngd Ngd sosai da kaunar book nawa,San nan 'yan group Dina na QUEEN MEEMI FANS ina godia da kaunarku agareni sosai kuna nunan kauna nagode Nima ina sonku luv u_ ***** tana zauna tana kuka Muntari dake tawo wa Daga can ya ganota yazo kusa da ita yace "hansai meya sameki"? da sauri ta share hawayen daya zubo Mata Babu komi ta fad'a juyar Dakai yayi tabbas yasan da matsala can k'asan zuciyar sa yana tausayin hansai Ko acikin yara bata da kuzari ,"kina jina? kiyi hakr kinji yanzu ya makaranta?" ya tambayeta bata bashi amsa ba sai ma d'agowa da tayi ,yace "Ko bakya zuwa kema? kin zama su tsaharen?" da sauri tace "Aa ina zuwa ajina 4 a firamare Yawwa hansai ki dage Kinga Matan garin nan basu damu da zuwa ba, har mazan ma, ki dage kina zuwa ki zama gwania acikin su," tace "to" yace "San nan kullum kina zuwa gun sahura (kanwar sa) ina koya muku karatu," Dad'i ne ya kashe ta tace "to" mangwaron dake ledar hannun sa ,ya zaro ya bata ta amsa tana mai murmushi. Muntari D'ane agurin mai garin ,garin mangalu a gidan su shine d'a na uku a ciki yayansa duk Mata ne sai maza kannen sa da Autar su mace,matashin saurayin k'auye ne D'an shekara goma sha takwas Allah yayo Shi da San karatu duk gidan su Shi kad'ai Ke zuwa, har ya kammala firamaren sa ,ya shiga secondary ta maza yana aji biyar ,duk k'auyen Ko acikin Samarin ya fisu ilmi ga kirki,tun ganin sa da hansai yake jin tausayin ta haka kawai ba don komi ba, hakan shine farkon alak'ar su da hansai. Bayan kwana biyu a tsakani yau ma MLM ya fita gona gwamma ta aiketa rafi wajen k'arfe hud'u na yamma ta d'au botikin ta tafi ,da d'an nisa sosai haka taje zuwan ta rafin taga yara birjik.Daga gefe ta tsaya tana d'iban nata ruwan ,wata Daga cikin su tazo taja kan hansai "Ke waya baki izinin d'iba,? bayan Kinga ana fad'a" hansai tace "to ni meye ruwana daku" fitsararriyar yarinyar tace "to duk nan na Riga kowa zuwa Kuma ba wanda zai d'iba sai ni" ,hansai tace "tabdi" kande tace "hansai sahura fa yar gidan mai gari ce fa!". hansai bata saurare su ba ta d'iba ta juya, jitai an jefar da botikin juyowarta, taga sahura na huci hansai zatayi magana sahura ta kamata da fad'a ,da yake sahura tafi hansai k'arfi ta jefar da ita a k'asa ,santsin k'asar gun taja ta tajita cikin rafi ,tinjim! kake ji k'arar fad'awar ta,Yaran gun duk suka saka ihu idanuwa sahura suka Rena fata,hansai kuwa sai ihu take duk tasha ruwa dai-dai lokacin Muntari ya taho yana zuwa yace "Ke sahura haryanzu aikenne? ga inna can na nemanki,"ganin suna kuka ya tambaya dije tace "sahura ce ta wulla hansai rafi" a kid'ime ya yi wajen ya ganta har ta daina motsi cikin ruwan ya shiga ya d'auko ta, ya fito da ita gefe yaran duk suka zagayeshi ya danna cikin hansai ruwa sai fitowa yake Amma duk da hakan bata farfad'o ba. haka ya d'auketa yaran suka bishi abaya duuuu. malam dake zaune sai fad'a yake "bana ce adaina aiken hansai rafi ba,? haba gwamma mai sa bakyaji ?gwamma dake zaune ta had'e rai "haba mlm "wai duk yaran garin nan tafi su ne? da za'ace bazata ba",mlm yace "eh tafi su ,ace tun k'arfe hud'u har yanzu shida dai- dai Babu alamar ta" ,jummai tace "malam Nima hankalina bai bani lafiyaya ba" . Sallama aka doka mlm ya amsa Muntari ya shigo da hansai a hannu jummai tace "la haula ,mai ya sameta Muntari ? yace "ai fad'a wai sukai a bakin rafin itada sahura, shine ta fad'a rafi" kuka jummai tasa ta k'ank'ame hansai, mlm yace "Muntari na gode sosai" bayan fitar sa ya dawo kan gwamma "Kinga ABINDA AKE GUDU (littafin batul mamman) ko, gashi kin gani dai Ko"! d'aki ya shinga ya fito da magani yasa a raunin hanun ta da k'afar nan yasa jummai ta D'an gasa jikin hansai ,haka dai sukayi ta treatment d'inta sai wajen k'arfe Tara ta farfad'o tana kuka yau a d'akin jummai ta kwana. Washegari dak'yar ta taka, saboda yanda k'afarta Ke ciwo ,sai da aka gasata da ruwan zafi San nan ta samu sa'ida ,muntari ne ya shiga shida sahura da leda a hanun yayi ya jikin hansai, San nan ya umarci sahura data bawa hansai hak'r badon Taso ba, suka tafi. yau 3 kwana kenan, kullum Muntari sayya zo duba hansai Kuma yazo ya jata da hira shak'uwa ce sosai ta shiga tsakanin su sosai bayan warkewar ta sai Muntari Ke zuwa yana biya Mata karatu irin su hadisi sira ,kawa'idi,alkurani,da tauhidi. (da yake da da yake D'an karami Dan shkear goma ankai Shi makarantar almajirai yayi shekara daya sai aka dawo dashi ya shiga boko Kuma daya dawon ya cigaba da d'aukan karatu gun malamin makarantar Allon su hansai). haka ya fara koya Mata da amincewar mlm, ba haka gwamma taso ba, don yamma k'arfe 4 yake zuwa asoron gidan su hansan,yana da k'wak'walwa sosai haka ya Farai Mata harda na bokon, kullum Kuma sayya zo da kayan k'walam ya bata .Daga baya ma sai sahura tazo shima ya had'asu yana koyawa,haka dai rayuwar hansai ta kasance yau fari gobe baki,cikin wata safiyar laraba gwamma ta haihu ta samu mace tunda ta haihu bayan anyi suna yarinya taci suna khadija suna kiranta dije, sai ya za mana duk wani Aiki hansai akeyi wanda ma yafi k'arfin ta ga yawan dukanta da mudi keyi yayi tai Mata wasan banza sai de inta ganshi ta gudu d'akin jummai. *BAYAN SHEKARA HUDU* wani busa Ke tashi a tsakanin duwatsun dake wajen hansai Ke busa Shi tana murmushi taci irin kwalliyar su ta k'auye Masha Allah hansai ta K'ara girma kyanta ya dad'a fitowa duk da ban tab'a suffanta muku ita ba . hansai 'yar farar yarinya ita ba irin gau d'in nan bace, ita Kuma ba za a kirata bak'a ba tsaka -tsaki ce'yar lawai-lawai bata da kib'a sosai sai de Allah ya horema ta kuturi(hips tun ma bata K'ara girma ba Ke nan ,shiisa jummai take bata hijab tasa domin tasan tana da baiwar da daukacin Mata Ke so,Kuma hakan shine ya kamace ta duk da yaran k'auyen kamar ta wasu basa yawo da mayafi. Sam hansai in ka ganta bazaka ce zatayi k'arfi ba komai a sanyaye ta keyi, siriryar fuskarta wadda Allah ya wadata ta da Dan dogon hanci siriri da bakinta madaidaici sai gashin Ido da suke gazar -gazar dogwaye tamkar tasa eye lashes ,idan ka kalli jikinta duk gashi ne ajiki sai de bata dayawan gashi kai tana da de na fakin Amma gaban goshin ta cike yake da gashi a kwance luf-luf hansai Ke nan😉 Muntari dake saman bishiya yana murmushi Shi kad'ai ya d'ago da idon sa, "Anya hansai duk k'auyen nan A kwai me kyanki kuwa"? dariya tayi "haba dai ka dad'a bincika yace to ni dai masoyiya ta tafi kyau,tun bayan shekara d'aya kenan suka fara soyayya shida hansai wanda kowa ya sani agarin, kullum nan ne wajen hirar su cigaba tayi da busa usur d'in .D'an dogo wa tayi ta kalli saman bishiyar lokacin muntari ya juya, kallon Muntari tayi azuciyar ta tana sonsa, domin ya taimaketa arayuwa, ya Sanar da ita ilmi da yawa ya taimake ta sosai, magana yayi firgigit ta dawo Daga duniyar data tafi tare da jin kunya da gudu tayi hanyar gida ....... *By Queen meemi* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣6❣ *JAN 2017* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usaman family's_* *ABUJA* A fafare Zuby ta shigo da motar ta ta faka a tafkeken filin gidan su. Ruby dake bayan motar ta fito a zafafe suna hararar juna kowacce d'auke da jaka sukai ainihin cikin gidan wanda Ke d'auke ta kafcecen falo, wanda Ke d'auke da K'ofar shiga part guda hud'u falon dake tsakiya wanda yake a circle ga manya manyan kujeru na leda masu D'an karan kyau, d'aukacin falon an kewaye Shi da labulaye masu kyau, ga wani site dake yamma da falon an k'awata gun tafkekeiyar plasma ce awajen tana ta aiki,ga wani kuku na k'alk'ale tile d'in falon. Shigar su Zuby da Zuby kowacce tayi part nasu .Ko wacce ka shiga part d'in nasu wani falo ne shima again d'auke da kujeru lintsuma- lintsuma ga decoration me kyau a falon, sai plasma tv da dining area da kitchen San nan jerin d'akuna guda uku,kowanne part haka yake duk gidan,d'akin mama. Tashiga ( hajiya khadija) tana zaune bakin tamkeken gadon ta, wanda ya malaye Babban d'akin ta zauna kusa da ita ,Mama tace "zuby har kun dawo"? "eh wallahi Mama gashi yunwa nakeji, sai de Kuma raina a b'ace yake" tayi tsaki ,"wallahi Mama wataran saina fasa bakin Ruby" Mama tace "haba Ke Bakya rabo da fad'a, Ruby ai kin San bada fad'a, dama Sumy kika ce ne da saina yarda". "Mama wai akan driving yarinyar nan zata min rashin kunya, dan taga itace babba,Allah ni banso dady ya had'ani mota da ita ba" ,dai-dai lokacin Sady ta shigo tana rawa mama tace "har abada dai Sady bakya rabo da shirme" sady tace "mama wallahi wak'ar ce da dad'i ,nan ta kalli Zuby tace "ya zuby mai naji kina cewa ne? inde zan cen mota ne wallahi mu had'u muje ga dady Kowa a sai mai dai -dai, ta yaya za ace kamar mu Kowa sai ace su biyu ne a mota d'aya. jiya fa haka sai da Sumy ta lalato motar ta, bayan na hau tace ni na lalata har sai da umma tayi min fad'a" Zubi tayi tsaki "gaiskiya Ya Ruma ta huta ita kad'ai da motar ta" ,mama tace "to sai kuyi hakr, ai ruma dai yayar kuce dole abata girmanta". D'an fita zuby tayi ta tafi Babban falo ta zauna tana kallo Rabia ce ta fito Daga nata falon itama ta zauna, Zuby tace "Anty Rabia ina gajia" batai mamakin jin yadda Rabia ta gaisheta ba tamkar ba matar baban su ba, "lafiya tace" ,da dai- dai da d'ai-d'ai Matan gidan da 'ya'yan suka fito sukai birjik a falon, gidan Alhaji tanko kenan. . Alhaji tanko Babban Dan siyaya ne, da yayi shura yana zaune a garin Abuja,yana zauna A maitama yana da kud'i na fitar hankali ,yana d'auke da muk'amin minister na kudi ,yanzu hakan yana da matan aure guda uku Hajia khadija itace matar sa ta farko ,tana da 'ya'ya da Shi Rumasa'u (Ruma) itace babba sai Zubaida (zuby) San nan Sadiya(sady). Wan nan sune na b'angaren ta San nan Hajiya Karima itace matar sa ta biyu, itama tana da 'ya'ya da Shi Rubayya(ruby) itace babba awajen ta sai sumayya (sumy) itace Ke binta wan nan sune iya 'ya 'yanta, sai Amaryar sa daya auro shekara 5 kenan tana da 'ya'ya da Shi khalili shine babba sai Mubarak, duk a gidan Ruma ce babba mai shekara 25, sai Ruby mai 23 San nan Zuby mai 22 sai sumy da sady sa'annine suna 20 sumy ta bawa sady wata biyu,sai khalil Dan 4 yrs San nan mubarak Dan 2 'yan gata ne sosai suna jin d'ad'in su San ransu ga gadara *MANGALU* Shigar Hansai gida yasa gwamma ta kwad'o mata murfn kwano a k'afa take ta dafe gun tana kuka gwamma tace "wallahi Hansai zamusa k'afar wando d'aya dake, kin gansame agari ba mai aurenki, duk sa aninin ki an aurar ,hatta ita tsaharen ankaita d'akinta bara Amma Ke. Kina nan shekara goma sha hud'u god'ai god'ia dake duk ba sa aninnki sai wanda kika girma,kullum sai aukin sa hijab tamkar matar liman,Ke ga malam ya tsaya miki wai sekin gama makarantar gaba da furamare ake cewa kome, to ayi Dai mu gani duk ran da aka fara saka ki A wak'a ai maji,ni b'acen da gani kar na ballaki ki,na k'arashe k'afar, je ki min wanki",tana d'ingishi ta tafi jummai ta fito lokacin itama Allah ya bata ciki ta kusa haihuwa tace "haba yaya hansai fa tana k'ok'ari miji Kuma ai lokaci ne Kuma ai D,an gidan mai gari ne Ke Santa, kin ga kuwa ai lokaci muke jira" gwamma tace "ayi Dai mu gani ba" dije ce ta shigo 'yar shekara hud'u gwamma ta kamo ta tace 'yar lele ina kika je ?tace "rafi kamo kifi" ,da sauri ta rufe bakin ta jin muryar malam dake k'ok'arin ya shigo ,tace "Ke yi shiru kin san malam baya so yi maza shige d'aki. Hansai da kafar ta keta jini wajen da gwamma ta wulla Mata murfi,Daga gefe sai kuka take ga wunya dake d'ibar ta tace "mama gwamma zan d'auraye k'afata jini" tace "Dan k'aniyar ki sai da kikaga malam zaki ce haka to bazaki wanke ba gulmammiya kawai" jummai dake kusa da ita tace hansai zo na d'auraye miki sai kici abincin," da gudu gwamma ta taso "Ke karki tab'a ta domin Salam munafinci",Malam dake shigowa yace "Aa meye haka nan kukayi cirko -cirko. *by Queen meemi* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . . . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣7❣ *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* *_sadaukarwa ce ga Basheer usman family's_* _happy birthday *MIEMIE BEE 👄*Wish u more years ahead ,GOD bless u🎉_ **** Sun tsaya cirko-cirko Malam ya k'araso yana tambaya da sauri gwamma tace "Aa magana muke kawai" hansai da kanta na sunkuye gwamma na harar ta MLM yace "Ke Kuma meye kike d'ingishi"? jummai tace "ai bigewa tayi" yanki ya d'auko ya bata ta d'aure gun yace ta koma gefe ta tafi tana d'ingishi,gwamma haushi tamkar ya kasheta ga wankin da bata k'arasa ba kenan, domin tasan malam bazai K'ara fita ba tun daya shigo, haka ta duk'ufa tana K'ara sawa. Washegari da jummai ta fita asibitin cikin gari Malam ya fita gona sai hansai da gwamma kawai ganin,hansai da uniform gwamma tace "Ke bazafa ki je ba, kizo ki d'eban ruwa"hansai tace baba gwamma yunwa nake ji" "baza ki ciba ki fita kawai wallahi" haka ta aje jakar buhun dake hannun ta,ta d'au botikin ta fita sai sauri take har taje rafin, ba kowa agun sai wasu mitsi-mitsin yara acan gefe suna wanki d'iban ruwan tayi ta d'ago kenan ta ci karo da lawandi k'irjinta ya bada dam! tayi gefe, bin ta yayi yace "Ke hansai"! taki tsayawa sai sauri take fit! taji ya ja hijab d'inta nan ta tsaya yace "Ke hansai don baki da rabo ina maki magana Amma bakiji don ina sonki kikemin wulak'anci. tace "kayi hkr inada masoyi" yace k'arya kike da kina da Shi bazaki zauna Ke kad'ai a gari ba duk kamar Ke an aurar sai kace mai bak'in jini, koda yake wa zai auri yar tsintuwa" da sauri ta juyo "kadaina jifana da munanan kalamai saboda da iyayena dariya".yasa dariya "tafi can ki farka tun dare bai miki ba" ,don ma zam taimakeki duk kyan nan naki ace ba mashinshini" tace "wallahi karya ne da iyayena malam da inna dariya yayi "kinsan dai ni abokin mudi ne, don haka ya gayan Kuma nasan bazai miki k'arya ba" fuu ta juya ya zata tafi ya cafko ta nan tahau ihu yace "bari na kwashi rabona tunda kince baki sona" k'ok'arin cire Mata hijab yake ta k'walla ihu dama kowa yasan lawandi a k'auyen bashi da mutunci shammatar ta yayi ya fisge hijab d'in ,kuka take sosai "kayi hk'r na tuba" jinjina kai yayi ya turza k'afafuwan sa a k'asa "gaki da kyan jiki Amma kullum arufe" hannun sa ya kai jikinta yaji an mauje hannun, Muntari ne Ke huci ya nuna lawandi "ka shiga taitayinka iskancin ka bai tsaya ba har akan budurwata, to wallahi duk k'auyen nan za'a jimu Kanmu" mazga ya kaiwa lawandi take shima ya rama suka nan suka hau naushe -naushe da gudu hansai ta juya ta yi hanyar gida tana kuka shigarta gidan ta tarar da jummai na tsintar shinkafa,lokacin bata Dad'e da dawo wa ba sai ta shige d'akin jummai tana kuka, cike da jimami jummai tajata tace "meya faru hansai"? nan ta fad'a Mata abinda lawandi yace da ita ,hankalin jummai ya tashi ta tuno lokacin da Malam Ke shaida Mata karta bari hansai ta San basu ne suka haifeta ba to waya gayama lawandi nan tayi ta lallashin hansai tace zata gayawa Malam . Makarantar daba taje ba kenan ,gwamma ta shiga d'akin jummai tana masifa "bafa zan d'au asara ba dole a biyani botiki na" ,hansai tace "kiyi hk'r tsautsayi ne yasa ya fad'i ,fizgo ta tayi ta fito da ita waje ta hau jibga hansai na ihu jummai ta janye ta tana haki "wallahi karki Kuma dukanta gwamma don Kinga Banda lafiya shiiisa kwanan nan kike dukan ta" ,gwamma tace "jummai dani kike zancen wallahi sai kun gane kalata ta kwanan" nan tayi k'wafa ta fita. jummai ta kamo hansai suka shiga d'aki tana bata hkr. Muntari da Lawandi kuwa sai da suka ji jiki San nan suka rabu lawandi yace saiya ga bayan Muntari inde akan hansai ne. Hatsaniya sosai sukayi har wajen mai gari ina waje d'aya ya Tara su lawandi da muntari na agaban maigari yace "kaga kai D'ana ne Muntari, kai Kuma lawandi kai Nike jagorantar ka meya had'a ku"? . Lawandi ya furzar da huci yace "yarinyar dana keso wai ita yake so" maigari yace "wake nan"? Lawandi yace "Hansai ta gidan Malam". Maigari yace "ayyo na gane" nan ya juya gun Muntari yace "haba Muntari na san ka da hankali ya da fada akan yarinya"? Muntari yace "baba wallahi tin hansai na shekara goma muke tare, atambayi Malam ma da ita Hansai d'in. nan maigari yace aje akirawo malam , yana gona akaje kiran sa ya tawo suka gaisa a soron gidan maigari d'in, yagan su nan maigari yace "Malam ya maganar 'yar wajen ka hansai"? cikin lawandi da Muntari wake Sonta malam yace "Allah ya gafarta Malam ai Muntari na sani tun da dad'ewa". "To kai kaji lawandi cewar maigari sai kayi hkr, karna K'ara jin wani tashin tashina anan" .Lawandi dake tsuke baki ya tashi ya fita yana mai k'wafar kota Halin k'ak'a sayya samu Hansai *ABUJA GIDAN ALHAJI TANKO* Sady ce da Sumy sukayi shawarar zuwa gun dady .yana wangamemen falon sa mai d'auke da kayan K'awa ,Anty Rabia taci uwar kwalliya tana gefe tana had'a mai tea zuby ta zauna daga gefe haka Sumy ma suka gaidashi " dady dama muna da complain akan mota wallahi yakamata ace kowa nashi dai-dai aka sai mai ,sady ta cafe "eh wallahi dady kullum baama jin Dad'i da sake wa ga frnds" har dariya suke mana A school" dariya dady yayi "har kun manta, Amma kafin na sai muku wan nan motoicin ai da kowa tasa yake hawa yawan yawonku ne yasa na had'a ku mutum 2 a daya". Sumy da alamar zaak'uwa tace "dady pls wallah zamu gyara ,kamar mu big girls a School Ace muna had'akar motor" Anty rabi ta kalle su lalle su Sady sai na ga hakan yafi dacewa" Sumy tace ni fa bansan sa ido don dai ba su khalil aka ce bane Shi isa mutum zai sako eyes" tsawa dady ya daka musu Dan baisan atab'o mai rabi saboda sonda yake Mata yace "inde rashin kunya zakuyi to ba wacce za a canjawa" Sady tace sorry Anty tab'e baki Rabia tayi ta fice nan suka bashi hkr yayi musu alk'awarin kowa d'ai- d'ai sabbi . da gudu suka fice direct public room d'insu dake Babban falon gidan ,inda nan suke zama da rana ,da rawar shoki Sady ta shiga Ruma da Ruby suna Aiki kan computer Zuby na checking phone d'inta, Sumy tace "yau sharr muke dady yayi alk'awarin new car kowa dai-dai take kowacce ta how murna. Zuby tace "wallahi saina rainawa su ramla hankali inde nayi sabuwar mota don aranar da dadyn ta ya bata new car har wani d'agan head take" "Allah yasa masu zafi zai bamu" inji Sady, Sumy tace "ai uploadin zan yi a Instr su gani na basu surprise" tsaki Ruma tayi tace "ku yaran nan abinda ya dame ku kenan ko"? Ruby tace "barsu 3 month fa da canjamana mota Amma sun koma don tsabar k'arya" dariya suka sa dukan su. *by Queen MEEM* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣8❣ *_Sadaukarwa ce ga Basheer usman family's_* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* ******* Misalin k'arfe goma na safe.Hansai na gefe a zaune tana dafe da cikinta dake k'ugi kallon d'akin jummai tayi taganshi da kwad'o don tasan ta tafi Asibiti. gwamma ce Ke can gefe tana wak'e -wak'e sallama akayi delu ce Daga bakin k'ofa tace "gafaranku dai" .Gwamma ta washe hak'ora "dele ce yau agari!.Gaskiya kinyi nisan kiwo",delu tace "wallahi sai jiya na dawo daga D'an lasan," zama tayi kan tabarmar suna hira ,d'umamen tuwo ne sai tururi yake ta Matso Mata dashi. kuka Hansai tasa,gwamma ta juyo tace "au barin aikin kikaii"? sunkwi dakai tayi,nan suka cigaba da cin d'umamen da ita da k'awarta delu suna ci suna shewa hansai ta tashi tace "mama gwamma cikina murd'awa yake yunwa nakeji". Delu tace "tab lalle 'yar nan kin samu sake ,gwamma ai Naga saka cinki " "to ya zanyi bayan malam shike tsaya Mata" tulun wanke-wanken ta nuna Mata "jeki wanke min banza gansama mai bak'in jini" kuka tasa "au bazakiyi sauri ba! ,Salan malam ya dawo ya hau fad'a" cigaba da shewar su sukayi. haka ta hau wanke wanken ,cikinta na hautsina sai Misalin12 ta gama lokacin ta gama galabaita ,San nan ta bata ragowar tuwon nasu. Delu tace "wai ni har yanzu ba Aga iyayen ta bane"?,gwamma ta tab'e baki gata nan, waya sani ma ko bata da iyayen". Delu tace "kede ki tashi tsaye don yanda Naga take taken sa sayya iya bata gado tun bai mutu ba, ai kina ban mamaki gwamma,duk kin sakwarkwace". Loma biyu hansai tayi duk tana jiyo su.Amai ne ya biyo baya haka taita kwarara amai gwamma tazo ta tsaya kanta "munafuka kawai ,kima tsiyayar da kayan hanjinki, ni bai shallen ba,shaidaniya ai wallahi ko zan yawo tsirara sai kin bar gidan nan, har akanki malam bai damu da dije ba,da mudi"dundu mai rai tayi Mata hansai ta durk'ushe.Delu tazo zata fita tace "gwamma sai na jiki". Wajen azahar jummai ta dawo.Hansai na gefen d'akinta a kwance tana kuka tana ganin ta ,ta rungume ta tace "inna ku gayan so biyu Ke nan Ana cemun Banda iyaye. don Allah ku sanar dani ,kuka ne ya kubcewa jummai ta bud'e d'akinta suka shiga . Zazzabi ne ya rufeta ta kwanta, sai bacci sai wajen la 'asar ta tashi tayi sallah ta fito tsakar gidan, taga Malam na Jan carbi da alama Sallah ya idar, da kuka taje ta sameshi "baba don Allah wai dagaske ba kune iyayena ba? kuka take saosai, jummai ta fito "Malam na rasa Inda hansai taji" ,hansai tace "mama gwamma ce Kuma ba yanzu ba, tun da dadewa,lawandi ma sai daya gayan,don Allah ku gayan ko na samu saida" ..Malam da idon sa yayi jajawur alamar bacin rai ya d'ago idon sa cike da tausayi ya kalli hansai,"tabbas bamu ne iyayen ki ba" tana zaune ta kwanta,nan ya cigaba bomb shine Sanadin rabuwar ki da iyenki "nan ya labar ta Mata duk abinda ya faru, luuu hansai ta fad'i alamar ta suma. Nan suka yayyaafa Mata ruwa, ta farfad'o tana kuka ta rungume jummai tace "baba har Ababa kaine babana Gaskiya samun irinku sai an tona, baba ka nunan k'auna kaida inna insha Allahu zan cigaba da yi maku biyayya ,Wan nan rayuwar danayi daku itace dama wadda Allah ya shirya min,nikam banyi maraici ba. Amma tabbas Nagd wa Allah daya wad'o dani cikin ku nagode inna da baba" cike da tausayi baba yace "hansai Allah yayi miki Albarka "jummai ce taja ta suka tafi dakin ta. fakam- fakam gwamma ta shigo gidan malam ya dakatar da ita,yace "ki koma Inda kika fito gwamma tunda kin zamo mai karya Alkawari ,kin b'atan rai kije sai na neme ki,".Salati ta hau "yanzu akan yar tsintuwa shine zaka ce naje gida to ai shike nan zan dawo ai",nan ta d'aga murya" jummai wallahi kin tab'o gwamma sai na yi miki rashin mutunci,nasan Ke kika had'a gurmi". *BAYAN WATA UKU* Bayan wata 3 dangin gidan su Muntari suka zo aka tsaida auren Muntari da hansai zo kuga murna gun hansai da muntarin duk tsiya hankalinta ya kwanta dalilin gwamma bata gidan. kuma gashi ta cigaba da zuwa makarantar ta,yanzu tana aji biyu na secondary dake cikin garin bunkure ,acan take zuwa ta dawo duk nisan ga muntari na k'arfafa Mata gwiwa. kwatsama cikin daren ranar juma'a jummai ta haihu ta samu d'a namji zo kuga murna gun hansai ranar suna aka samai suna Abdullahi ,suna kiran sa d'an jummaii,lokaci yana ta tafiya. Har jummai tayi arbarin hansai Ke Kula dashi tana jin k'aunar sa. Washegarin Arba'in d'in jummai sai ga gwamma ta dawo inda da k'yar da sid'in goshi malam ya maido ta. Ganin yanda hansai tayi kyau abinta ya bak'anta ran gwamma, dama taji labarin auren su da Muntari nan ko ta d'au damarar yak'i da hakan muje zuwa. *BAYAN KWANA 2* *da yamma* Tafiya hansai keyi tana sauri zata gidan sahura k'anwar Muntari ,lawandi ta gani agaban ta ,da sauri ta kauce lawandi yace "ki tsaya mana!, da gudu ta arta ya bita Allah ya ci da ita taga wasu mutane akan jakai take lawandi yayi baya hamdala tayi ta tafi. *k'arfe goman safe* washegari mudi na zauna a d'akin gwamma se yau ya ya shigo,satin sa d'aya bai lek'o suba ,gwamma tace "ai ni yanzu burina wan nan yarinyar tabar gidan nan",mudi yace "Yawwa ni akwai wani abokina lawandi yana Santa,kwanaki ai har fad'a sukai da muntarin" ai da hankali na bazan bari ta auri muntari ba,haka kawai saboda banso ta samu rayuwa mai kyau, kace gobe lawandi yazo" mudi yace "ba matsala". da yamma hansai na soro itada munatari yana Mata K'arin karatu gwamma ta fito da botiki ,cike da ruwa ta kwarawa Muntari tace "kai kam anyi Mara rabo, shikam dayake tsaye jiki na d'igar ruwa ,hansai kuma na gefe jikinta na rawa ta kalleta, tace "wuce muje 'yar banza" nan ta bita da dundu ,ta dawo kan Muntari tace "to kai yanzu karasa wa zaka aura sai 'yar tsintuwa 'yar daba asan iyayenta ba"?. "Amma ka bani mamaki ,kasan dalilin dayasa tak'i auruwa kuwa? to cikin shege tayo aka rufe a bun" idanuwan Muntari kam sunyi ja yace "haba mama gwamma yada jifanta da irin kalaman nan Sam ban yarda ba" "to baka yar daba kenan? to wallahi da gaske nake" kansa ne yaji ya fara juyawa ya dafe shi yana waswasi. *by Queenmeemi* *Queenmeemi.WordPress.com* [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣9❣ *JAN 2016* *Queenmeemi.WordPress.com* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_* Nagode da bibiya @* *ummu yusra*, *Amiener* *Ngileruma ,Maryam* *Shettima,Ummie* *Maryama Niger* *khadija lagos &Ashnur tnks* ❤ Muntari baice komai ba sai ma waje daya yi gwamma "tace tafi can wallahi sai na rabaku". komawa ciki tayi tahau wak'e- wak'e . Mudi kam Bayan ya gayawa lawandi sak'on gwamma baiyi wata -wata ba sai gashi da sassafe .Bayan malam yafita yazo gwamma ta fito soro suka gaisa tace wa lawandi "ka ce kana son Hansai ko"? yace "eh to karka samu damuwa Amma kafin nan sai na saka ka Aiki. kuma kayi a k'arshe zaka ga yanda komai zai tafi dai- dai lawandi yace "ai ko ba so tsakani zan iyayi miki" nan tace "so nake ka d'auke Hansai kaje can wani wajen ka b'oye ta,kana jina"? murmushi yayi lallai fad'uwa tazo dai de da zama, ya d'ago yace "to yanzu yaushe za ai,? tace "ko yau ma, kaide wajen uku kabi hanyar rafi zan ai keta yo jida". Sallama sukayi ya tafi Misalin k'arfe uku gwamma tace wa hansai tazo tana zaune a bakin d,akin jummai ,goye da D'an jummai, gwamma tace "Ke jeki sauke wan nan bushashen yaron," Hansai taje ta sauke Shi ta Koma wani k'aton buhu ta bata, "gashi so nake kije ki yo mini jida a gonar Malam kalla".Jummai na d'aki ta fito "haba gwamma kinsan wajen da nisa, kuma jida har me zata samo Bayan duk an gama", gwamma tace "bari kiji ko jiya saida lantana 'yar wajen larai taje yo kalen Dan baki ga gyad'ar data samo ba ,don haka dole Hansai tayo mini jida ,wallahi ko na kileta". Jummai tace bafa "zata je ba, gwamma tace "dani dake aga wa zai bi wani" wawuro ice tayi tabi Hansai aguje tayi waje da buhu a hannu . Haka Hansai ta santali hanya tiryan- tiryan, tana tafiya hawaye na bin kuncin ta,sai wajen hud'u da rabi taje ta hau kale Babu komi da k'yar ta samo kad'an tayi kwana tana sauri saboda gajiyar da tai ,ji tayi kawai an sure ta K'ara ta k'walla buhun ya fad'i ,wani dutse ta d'auka ta kwad'awa lawandi, tace "Amma kai kayi asara, ka rabu dani nace," binta yayi ta hau gudu ita da zatai hanyar rafi sai tayi wata hanyar da k'yar takai wani gida ta tsaya tana haki,ji tayi an rufe bakin ta' an d'aga ta sama sai ihu take Amma baya fitowa ,Mari lawandi ya faska Mata sai data ga wuta d'if ta some nan lawandi ya tafi da ita. K'arfe bakwai dai de malam da jummai ne tsaye suna neman hansai, ba inda ba a duba ba. Amma ba alamar ta .Jummai kam kuka take hankalin malam idan yayi dubu ya tashi ,komawa gida yayi yace da gwamma "mai yasa ne kika aiketa kale? haba sai kace bamu da abin sawa abaka" malam sai hak'uri, Nima tun d'azu hankalina atashe yake" . Wajen takwas na dare sai ga Muntari ya zo zance ya gun hansai da wata leda a hannun sa, zuwan sa k'ofar gidan, ya tarar da malam a tsaye nan suka gaisa malam yace "D'ana Muntari ko kaga Hansai"? a fargaba ya d'ago "Aa malam miya same ta", malam yace "ai tun k'arfe 3 ta fita wai kale har yanzu shiru ba labari" da jimami Muntari yake magana a gigice, "ina zuwa" malam ya sanar da Muntari ya shiga ciki shiga ciki . gwamma dake lab'e ta fita soron tace "amma kwa Muntarii anyi sahorami, yanzu ba kaji abinda na gaya ma jiya ba ko? ka d'auka k'arya ne ko"? Muntari yace "Ni ai ko ma mene Hansai tayi koda ta da wani batare da aure ba ita nakeso kuma zan aura kuma haka nake santa ko da duk kowa zai ce baya sonta".Gwamma tace "ka rabu da hansai Muntar", "mama gwamma hansai fa kamar 'yar ki take kina yi Mata zaton Alheri" "lalle Muntari ka fitsare ko girmana baka duba ba ,kake gayan wanga magana ,dani kake zancen dole ka rabu da ita" muntari da ya share zufa duk sanyin da ake alokacin Amma gumi yake saboda zafin da gwamma ta had'a mai yace*_"rabuwa da Hansai ,tabbas zai iya zame min matsala,haka Sanadin Rabuwa da ita zai jefami a mawuyacin hali wallahi Ita nake k'auna _* gwamma tace "tab! anya kana da kai, lalle dole ne na Ke gidanku" .da sauri ta fice don jin da yayi kansa na juyawa. Ledar da ya shigo da ita ,ta d'auka ta duba taga soyayyan kifi, "hmm da wan nan cimar zan k'yale Hansai ta aure ka ,inaji ina gani Hansai ta auri d'an maigari ta shiga daula ,ai dole na tashi tsaye ,ai idan yasan wata bai san wata ba.Juyawa gidan tayi ta shiga d'akin ta suka ci ita da dije. . haka Muntari yayi ta yawo baiga inda take ba ba inda baije ba, har wajen 9 na dare yana yawon nema harda k'walla don yanda yake jin Hansai a ransa. ****** Al amarin hansai kuwa, bayan da lawandi ya sace ta bai zame ko ina ba sai wani gida wanda ba kowa a ciki sai wata tsohuwa ,aje ta yayi a d'akin tsohuwar ya d'ago yace "kaka ga ajiyata nan" dafe kirji tayi!" kai D'an nan yau ma jafa'in ka jawo? har ka fara satar bil adama". Lawandi yace "kede kaka ba ruwanki ki sa Ido kawai" fit ya fice daga gidan. Bayan fitar sa ,Hansai ta farfad'o ta hau kalle- kalle kuka ta kuma sawa, "na shiga uku wayyo baba, wayyo inna" ,tsohuwa tace "yarinya mai ya had'aki da lawandi"? Hanai ta kalleta "wallahi iya ,ya nace yana sona Alhalin an saka min rana da wani ,in dai zan fita sayya biyo ni, yau ma tsautsayi yasa naje jida ,shine ya d'auko ni don Allah kaka ki taimakan". tsohuwa tace karki samu inaga Allahu gobe zan bud'e ki tafi,ina kike" ta tambaye ta ,Hansai tace a mangalu"tsohuwa tace "ai bamu da nisa ma" dadi taji tsohuwa tace ta tashi tayi Alwala haka tayi ta dawo ta zauna.Tai tsuru-tsuru tana jimami. tsohuwa tace "ai lawandi kwai tak'adari wallahi tunb yana shekara goma nake fama, jika nane ni na haifi baban sa,babar sa tazo haihuwa ta mutu baban sa kuma ciwo yayi ya rasu, sai rikonsa ya dawo guna neman fada doke doke ba irin wanda bai ba daya fara girma ya tsiri dauke -dauke, har ya girma bai nutsu ba sai ma janyo fada wanda ya sha kwana gun masu kayan sarki('yan sanda) har yanzu sai adda'a domin kullum sayya yi wani abun rashin da'a,tun da nace ya samo Mata nai mai aure kowa nutsu ,shine ya satoki ko? kiyi hak'uri gobe- goben nan, zan saki a hanya ki Koma mangalu" Hansai tace "iya dama cikin gari ya kawo ni"? iya tace "ai nan cikin garin bunkure ne".kuka hansai tasa kaka na bata hak'uri. *By Queen meemi* . [12:02am, 15/01/2017] ‪+234 903 281 0350‬: . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣10❣ *JAN 2017* *Queenmeemi.wordpress.com* *dedicated this page to sis marwa &sis Ameener* _jinjina gareku, *Anty maijdda* *Anty sis,Anty sadyjegal* *LubieD*, *Hapsert NM, Kursiyya* *yusha'u ,Aneesaty*, *respectable* *& Princess Amra*da sauran wanda ban fad'o ba duk kuna raina_ Washegari da sassafe sai ga lawandi nan tunda dama ba kwana yake a gidan ba ,kokon da kaka take sha ya d'auke ya d'ad'd'aka. Hansai kuwa rakub'ewa tayi a gefe ya kalleta .Hansai gani gaki sai yanda nayi dake zaki raina kanki keda ba gata gareki ba ,kaka tace" kai lawandi tsiyar ka da rashin da'arka ya kaini bango wallahi zan sab'a maka" lawandi yace "to kaka bake kika ce na samo aure ba, don haka ga Mata na samu" harara Hansai ta galla mai tashi yayi ya fita.ya rufe k'o far ta baya . Hansai tace "kaka yanzu zan tafi "kaka tace "bakya ganin ya rufe", kuka tasaka ta tashi ta fita tsakar gidan ta ta zaune shikwa Lawandi yana waje ya kasa ya tsare don yasan dole hansai zata nemi guduwa. Acan gida kuwa hankulan malam da jummai atashe yake ganin har safiya ba labariin Hansai yanzu ma da suke zaune jummai kamar Mara lafiya tace "yanzu shike nan 'yar da na k'wallafa rai akanta ta bata"? .Malam yace "ki daina kuka ai na sanar da Maigari yanzu anjima za naje ,kuma ina addua sabida tamkar amana ce Allah ya bani" gwamma dake d'aki tayi tsaki "kwayi kwa gama ai, kunyi bankwana da hansai ". Wajen k'arfe 11 Malam ya fita gona, sai da ya fara biyawa ta gidan Maigari ya kumai mai tini kan maganar San nan ya suce gonar. Al a' amarin Muntari kuwa yana d'aki yak'i fita sai matsaar k'walla yake, Maman sa ladidi sai karakaina take don ya karya don tun jiya takula bashida kuzari da abinci jiyan ma baici ba,da k'yar yaci ya fita nai man hansai har gun su da suka Saba zama yaje bai ganta ba ya Dade a gun San nan ya kuma nausa neman ta. Hansai kam durfafar k'ofar fita tayi ta sakace ganin ba lawandi agun ta kalli gabas da arewa nan tayi gabas tafara tafiya kenan ta k'unshe hannunta a cikin hajib sai ga lawandi yasha gaban, ta yace "Ke hansai koma"! tace bazan Koma ba", nan yace ai kinshigo kenan dole ki soni, kuma sati mai zuwa za a d'aura aure".Wallahi bana sonka muntari nake so shine jarimina" hannu yakai zai damk'o ta tace "karka k'ara tab'ani! domin Naga kai baka San dokar musulunci ba",wata siririyar wuk'a ya d'auko a gefen wandon sa ya nuna ta da ita ki Koma ,konai miki kwale a fuska ,duk kyan nannaki ya b'aci" hawaye ta fara ganin ya nufota ta juwa ta shige gidan, kaka na zaune tace "Ahh! ya kika dawo?...Hansai tace "ya k'i bari na na wuce har wuk'a ya nunan" kaka tace "barshi sai na nuna mai b'acin raina". *Bayan kwana 5* Maigari ankai report guron 'yan sanda dake cikin garin bunkure ,saboda ganin yau kwanan hansai shida ba labari,jummai har zazzab'i tayi saboda sabo akace Turken wawa Shi kansa Malam d'in daure wa yake haka akaita nemanta. *RANA DUBU* _*(Hausawa na cewa rana dubu ta b'arowo rana d'aya ta mai kaya)*_ yau lawandi wajen 12 ya fita don zuwa wani waje kaka tana sane ta kirawo hansai tace "yauwa hansai ga naira D'ari ki tafi kiyi sauri kan ya dawo ko ya rufe k'ofar ki jijjiga ta " godia tayiwa kaka ta fita.Allah da ikon sa sai gashi k'ofar abud'e saboda ya sakankance hansai ba zata gudu ba, da sauri Hansai ta fita tana kalle- kalle gudu ta hauhi,ganin wasu mutane taje gunsu tace "don Allah wane ina zanyi ya kaini titi "nan suka nuna Mata wata hanya haka ta yi ta gudu har taje , nan tana tsaye kan titin taga wucewar lawandi ai sai ta b'oye don kar ya ganta, wata mota ce Ke shiga mangalu duk sati taji Ana ambatar mangalu! mangalu! ai da gudu ta shiga akaja,cikin ikon Allah wajen k'arfe 1, sai ga hansai a mangalu godia tayiwa Allah,ta yi hanyar gidansu. Gwamma na tankade tana wakar _ahayye yaraye_ hansai tayi sallama tashi gwamma tayi tana tafa hannu "Ke 'yar nan sai yau kika dawo daga yawon tambad'ar? oh ni! gwamma duk k'auyen nan ace Ke kad'ai ce ba aure duk sai k'annen ki ai dole ki yawo"�����~|�f�(Q��E�3<�J�)���JH��Dw�j��/���BJ�����*G`K��JbW����3@P>-N+�\L���]E� �\ qO�5�߸c��R,i�.���Z:�2J�H9DuI����3@{��lӴI�| �aҰ#�G�D�[��ߪ i �3fx�t���o���)x�,"�9S8�a�������ҁ�jC�*��X�n �R� �Ř�\hp5���{�7��7�?�2p( R)���� UK&V��g�`�Ά�bewŪĥMA�\|��H�Ҹ `;r� �h�\�� ~�]�xF���z�`�b�zn�*LgK�#B���9� P;� *�+��`��y��QP2%j~�H�'{�S��+vuhe:�� "�tg�#�d�ʳ��[��N��W�W`�iߥס��x՟6��Ȥ��h� �n J��J����T�:+�f� �K}�k��|�O�QEј�a�PF������+�}�b��b�,y���^�..`|����pkS�]#Aٟ�M��,���Kz�0⯝˝N�m�B|��`>\�bv����W�]�f�H|��S���X�� ��� ���� 4�_��D������E��������| WKZ����yuœҪ��� 9t���i)��j���V�7���WwS�o��i�)� 7��|� ����؇��Y�� ���G���!G������*Z�������T�Dj��f��oQ8�?`�-�_� 1BJ7]_��1X���+� ���?(�8�E�hfo������Rx��,��j��]�/�6Ɋ�Y�xf*�����n�X黧�Z �nz�R,bUoc�������;]��tt\�.&�ux���z �����;���A� �T`�������5������{�l�E��t˵�g����&��z�4�Rm��Q�v5�ƺȊn�����]l�zk����)�8������W��?Y�c*w��fV�V?�}vux��������(�oM2T�m akai .Washegari aka sanar musu dama sosai suke da case da lawandi nan suka hau neman sa. Zo kuga yadda gwamma ta tashi hankalinta domin lokacin da malam ya Koma yana ta fad'a agabanta yake maganar an sanar da 'yan sanda nan ta shiga rud'ani ta San dole asirin ta zai tonu,haka taita kaikawo tana habaice -habaice "haba ko dije a ka d'auke ai Malam bai ci kai wan nan gigicewar ba, Amma kan 'yar tsintuwa duk ka d'imauce" ,haka taita surutan ta. Cikin sa'a aka kamo Lawandi sai da suka zo gun maigari .Maigari yace "kai yanzu lawandi abinda kayi yadace ne? haba! ai nayi maku tsakani da Hansai ko to kuma har da d'auketa ko"? ,lawandi ya tsuke baki ranka ya Dad'e nasan ina son Hansai, Amma banyi niyar saceta ba, sani akai".Maigari yace "waye ya saka? yace "gwamma matar malam". Malam dake durk'ushe ya d'ago tabbas matar nan ta rainani , duk sai yaji kunya ta kamashi. Maigari yace "ai sai Malam kai ne zaka hukun ta ta, kai kuma lawandi sai atafi da kai". haka kuwa akai masu kayan sarki suka tafi da lawandi . Afusace malam ya shiga gidan, gwamma ya k'wallawa kira saida hanjin cikin ta suka bada k'uuuuu !ta fito "Malam gani tace "yada wan nan kira haka"? yace "kin tozarta ni, kin badani acikin wanda Ke ganin mutuncina, gwamma kin addabeni kije ni a yanzu bazan ce ki je gida bako wani Abu kawai na datse alak'a ta dake ba ruwanki da hansai ko jummai, nima karki shiga tawa ki zauna agidan nan Amma saina waiwayeki ,abinci kawai na baki izinin ci shima sammaki zan" kuka tasa "yanzu Malam duk sosyyyar dake tsakanina dakai akan hansai kake min haka"? ,afusace ya juyo yace "Ke ko akuya Kikaiwa haka saina hukunta ki Ballan tana Mutum" dije ta fito tana zumbure baki jin anawa gwamma fad'! duk gwamma tana koya Mata halayen ta Malam yace "Ke dije je ki d'auro d'ankwali zunb'uro baki tayi tak'i tafiya, malam yace "kinga halayenki ko! gwamma gashi kin koyawa yarinya,Allah ya shirya" .gwamma sai fatar hanci take tana kuka ,Jan dijen tayi suka shige d'aki.... Muntari kuwa dad'i ne ya kashe Shi ganin hansai ta dawo ,cikin gari ya shiga ya sayowa hansai hijab guda 2 yazo gidan su hansai ta fito sunkuye da kai harda d'an murmushin ta na ganin muntari zama sukayi yayi ta tambayar ta tana bashi amsa duk yanayin data shiga a sacewar da lawandi yayi Mata.Muntari yace "hansai tabbas kin fita da yaran kauyen nan shiisa nake sonki kina da nutsuwa dad'in dad'awa kullum jikin ki arufe sab'anin sauran yaran dake yawo gandak'ai.Murmushi tayi "innace tace na dunga sawa, ai yanzu ni na sabama" mik'a Mata leda yayi to ga wasu a K'ara sakawa" haka sukai ta hira yanai Mata K'arin karatu wan nan Ke nan..kubiyoni *By Queen meemi👑* . [7:43pm, 15/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣11❣ *JAN 2017* *Queenmeemi.WordPress.com* *_Sadaukarwa ce ga basheer usman family's_* _dole na miki Gaisuwa gunku, *Miss hafcy ,Mamu,Anty Ybk,zahra,mum's gurl,Autarhajiya,Futha besty, chuchu Ammani,waheeda* San nan 'yan group d'in *qasaitattu Mata*_ *Bayan sati daya* Duniya tayiwa Gwamma zafi sosai abubuwa sunyi Mata yawa ta rasa yarda zatai ga Malam ya kafa mata Doka.Abinci sai Jummai tayi ake yafa Mata ga Malam ya daina kulata baya shiga Dakinta. Yau ma data Ke kaikawo don neman mufita Abu yaci tura ga d'aci da ranta keyi, sabili da ganin Malam da Jummai a zaune suns Hira. Malam na bata Labarin wata tafiya daya yi da dad'ewa da irin Gwagwar mayar da suka sha sai dariya take. Da sauri ta d'au Buta ta shiga band'aki ta fito ta Koma d'aki gashi tana San fita Amma ba dama ta zauna Ke nan taji Malam nace wa: "Ai Hansai so nake ace ta gama Makaranta. Amma Allah baiyi zata gama ba, tunda bikin saura wata Hudu." Jummai tace "tabbas haka ne Malam" . kiran Hansai yayi datake d'aki ta fito ita da Dije 'yar Gwamma .kallon Hansai yayi yace "aji nawa kike.? Sunkwi dakai tayi tace "ajina Uku". Hamdala yayi yace "ko a hakan kika tsaya ai kin samu . Jummai tace "Malam ai se a saka Dije ma tunda kaga tayi Girma". Malam yace "anya ba'a bari ta kai goma ba ,ko bakwai." Da gudu Gwamma ta fito "wallahi kar wanda yakaimun yarinya makaranta".Malam ya d'aga Mata hannu "waya saka dake ehe?,meye naki aciki? nayi maki tsakani damu don haka Ke 'yar kallo ce, idan kinga bazaki iya ba,ga k'ofa nan abud'e take". Jiki a sanyaye ta Koma.Haka dai rayuwar ta kasance a yanzu hankalin Jummai da Hansai ya kwanta, har k'iba sukayi. Hansai kuwa soyayyar su ta dad'a ninkuwa itada muntari domin bala'in son Junan su, suke d'aya baya son rabuwa da d'aya ,arana sai muntari yazo gun Hansai so uku ga Shi komi yagani sayya sayo mata ,duk da shima ba sana 'a yake ba. Amma yana zuwa gona,tun Bayan gama Secondary d'in sa yana son cigaba .Amma tunda baiji Maigari yayi magana ba shiisa yayi shiru . Hansai kuwa ta b'angaren iLimi sai nace Masha Allah ,duk k'auyen ayaran Mata,domin ta dage kullum Malam na k'arfafa Mata Gwiwa Musamman na Addini sai san barka. Sam bazaka ce Hansai daga K'auye take ba,tun Bayan da malam ya dakatar da Gwamma sai ya ce Dije ta Koma gun Jummai haka Dije ta fara nutsuwa ,gashi Hansai Ke koya Mata karatu Sun saba sosai ,sab'anin da sai de ta tsaya k'ofar d'akin su tana hararar Hansai duk da yarinya ce mai Shekara Hudu. Gwamma kam tana gani ba damar magana don Malam yace duk randa takarya doka inta bar Gidan to har abada bazata dawo ba. shiisa tai shiru saboda tana k'aunar zaman Gidan domin tabbs tasan Malam yana da kyautatawa da yawa. Matan k'auyen na surfe sukam Malam bai bari suyi gashi har kud'in kashewa yake basu ,wad'an nan dalilan su suka sa Gwamma tayi lamfa.haka dai rayuwa tayi ta tafiya har su Hansai suka zana Jarabawar Junior Secondary school,ayanzu Hutu suke. BAYAN WATA UKU Bikin hansai da Muntari yana ta k'aratowa ayanzu saura wata d'aya,nan gari ya d'auka saboda an Dad'e ba ai biki gidan maigari ba ga kuma Hansai da ake ganin ta dad'e.San nan gashi soyayyr su mai Asali wadda ta kaisu ga Shekara hud'u da rabi kenan shiisa kowa Ke zumud'in Bikin. (Bari mu waiwayi Lawandi muga wane waina aka toya tun lokacin shigar sa gun 'yan Sanda). Bayan da suka tafi dashi dama suna da case dashi sai direct suka kaishi cell saboda dama andad'e Ana neman sa, bisa dalilin satar da sukayi wa wani D'anfulani ,sai lefin nasa ya zama biyu gana satar yarinya gana kayan D'an fillo ,kawai sai aka sashi cell na wata uku ba beli . To ayanzu wata ukun ya cika ya samu ya fito . Zuwan sa gun kaka lokacin tayi fishi dashi tace ya bar Mata gidan ya Koma gun Dangin Maman sa kaka sai kuka take hakan yasa ta d'akko wata Jikarta suke zama tare Shi kuma Lawandi ya had'a kayan sa ya cale Lagos neman kud'i ,acewar sa sai kaka ta neme Shi . kaka tace "nikam nayi nan kayi can .Allah ya bada sa a can yayi tafiyar sa. Al amuran Gwamma kuwa tayi ladaf din k'arya don har ciwon karya tayi domin ta jigata matuka. Malam na zaune tazo ta zauna sai matsalar k'walla take "Malam kayafeni na tuba bazan K'ara ba na jigata tamkar a Kurku ku nake ,ka taimake ni ba donni ba. Malam ya kalleta "Ashe har kin horu" Gwamma tace "na horu Malam." "To kije na janye. Amma idan sab'anin hakan ya kuma faruwa zanyi mai gabad'aya." "Malam aina saduda". Tashi yayi ya fita domin Shi kam yasan tuban muzuru Gwamma tayi. *Bayan sati daya* Kud'in da Malam Ke tarawa dama na bikin da wasu awakan sa daya sayar ya had'a jumulla dubu d'ari dashi za yiwa Hansai siyayyr kayan d'aki. Wajen k'arfe 9 na dare ya shiga d'akin Jummai lokacin ta na zaune ,ya zauna gefen tabarmar ya kalleta. "Jummai kinsan dai bikin Hansai ya matso yau,saura sati daya ko! to shine Allah da ikon sa ga kud'in da za'a sai Mata kaya, yanzu sai kuje keda iro har kano sayo Mata duk abinda ya samu." Godia Jummai tayi itama ta d'auko nata ajiyar, nan duk suka had'a, Hansai na kwance tana bacci d'an tashin datai taji suna maganar, kuka takeyi A hankali tabbas babu wani sarki sai Allah mai had'a bayin sa duk inda yaso, gashin ya had'ata da Mutane masu kyautayi, tana daga kwancen ta rok'i Allah ya bata abinda zata rama d'umbin Alherin da sukai Mata. Duk maganar Kud'in da sukai akunnen Gwamma nan hankalin ta ya tashi ta kasa tsugun komawa d'aki tayi ta rafka tagumi. "Lalle nayi sake D'an zaki ya girma ,dole na san abinyi kud'in ma ba za asadani ba lalle dole na tashi tsaye" ,haka taita Sumbatu tana jira safiya tayi ta San abinyi.tooohhh muje zuwa dai..... *By Queen meemi* . [4:00pm, 17/01/2017] 👑Meemi🔸: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣12❣ *JAN 2017* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* *Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's* _TUNATARWA_ _Ya 'yar uwa ko d'an uwa, ka/ki kiyaye harshen ka/ki, domin shine wakilin Zuciyar ka/ki.Kuma shine hallakarka/ki take jikin sa, karka/ki rik'a sakin sa,sai akan Alkhairi ko abinda Zai Amfaneka/ki_ ********** Haka kuwa akayi washe gari da sassafe kuwa Jummai da iro suka tafi can kano don siyayyr kayan d'akin. Misalin k'arfe 11 Gwamma kuwa Bayan fitar Malam itama ta fita, dama ba tambayar sa take ba,bata zarce ko ina ba sai Gidan Maigari . Da Sallama ta shiga, Ladidi tana zaune tana hira da bak'uwa tacee "Ah! lale da Gwamma" dariya Gwamma tayi tace "wallahi kuwa" nuna Mata waje tayi suka kuma gaisawa, haka sukai sallama da bak'uwar ta tafi, nan ta juyo gun Gwamma tace "yasu Dije da Jummai" ta amsa da Alhamdlh gyara zama tayi "Ladidi dama magana nazo da ita kan Hansai. Ladidi tace "Eyyya ya shirye- shirye?" tab'e baki tayi batace komai ba, d'an juyowa tayi ta fuskanci Ladidi tace "wato ranar wanka ba a b'oyen cibi dole idan kaga za acuci Mutum ka sanar." Ladidi tace "ban gane maganar da kike ba,"tace "ai In gaya miki Hansai de ba 'yar gidan mu nan bace." "Asalin ta tsintar ta malam yayi, ba asan iyayen ta ba ,to ku kam kwaso had'a iri da ita.? Ladidi tace "haba dai Gwamma idan kikaji wani na maganar nan ai seki kwab'eshi ,nasan Hansai ai 'yar k'anin Malam ce". Gwamma tace "wa din? to wallahi aga bana ya shigo da ita,kinsan badai zan miki k'arya ba." Shiru Ladidi tayi tace "tabdi Amma wan nan magana da mamaki! zan sanar da Maigari nan Gwamma tace karde kice nice na fad'a don Allah" Ladidi tace "haba dai sai kace wata yarinyaa." "Yawwa bari na tafi." Haka Gwamma ta tafi,tana tafiya tana maijin dad'i. Da misalin k'arfe Hud'u Maigari ya shiga gida Bayan ya huta Ladidi ta zo mai da maganar da Gwamma rltazo da ita, Murmushi yayi "wan nan ai magan- ganun Mutane ne" ita wan nan Matar dama bata son Yarinyar ,don haka abar Maganar kar ma kowa yaji." Haka Ladidi ta hak'ura tabar maganar Amma abin na ranta. k'arfe shida su Jummai suka dawo ba laifi sun sayo kaya da yawa, k'aramar motar d'aukan kaya da gado aciki na katako duk k'auyen Hansai ce Malam ya fara yiwa, duk a wanda akaiwa aure ba masu irin sa duk da wan nan d'in ma bamai tsada bane can,lalle ta cika yar gata littafin( Miemei bee) Malam yayi farinciki ganin kayan . Gwamma kuwa sai dariyar Mugunta take ganin ta had'a gurmi, haka dai sukai ta shirye- shiryen su. Bayan sati d'aya Gwamma taji shiru ba alamun cewa an fasa auren, sai ma shiri data ga anayi a irgen da tayi yau saura Sati Uku bikin,hankalin ta ya tashi. Yau ma da takasan ce ranar Laraba Gwamma na zaune ta rafka ta gumi zumbur ta mik'e cike da wani tunani, ta yafa mayafi ta fice bata zame ko ina ba sai Gidan Delu,ta shiga Delu na zaune tana cin Zogale ta taso tace "lalle daga ganinki ta ciyoki." Gwamma tace "sosai ma ai mufita nake nema."Delu tace "ai Labarin Bikin Hansai ya karad'e K'auyen nan ,ina zaune a nan nace kinyi sake". Gwamma tace "yo ai lokaci bai k'ure ba." Delu tace "tabbas yanzu kawaii kizo muje Gidan Boka na gaban K'auyen nan, da Zafi-Zafi akan bigi K'arfe. Gwamma tace "yo ai matsalar ta Kud'i ce." Delu tace "ai ba damuwa kije ki had'a su Kud'ad'en ki ,sai muje. Gwamma tayi shewa "shiisa nake sonki Delu haka kawai yarinya ta zame min sai kace 'yar kishiya"! haka suka gama Gwamma ta tafi. Fafutukar samo Kud'in Gwamma tashiga yi ,kurd'a- kurd'a, kullum tana yawon rancen Kud'i har wata Akuyarta, ta sayar nan ta had'a dubu Goma ,ta shiga kuma neman cuko dak'yar da Sid'in Goshi ta had'a Kud'in a sati d'aya ,hakan yayi dai- dai da Sauran Bikin Hansai sati Biyu. Da sas safe Bayan Malam ya fita ta fita ,dama bata tambayar sa unguwa, ba bata zame ko ina ba sai gidan Delu tana zuwa suka tafi Gidan Boka. Sunyi tafiyar Awa d'aya San nan suka hau Mota ta aje su adede Dajin da zai kaisu Gidan Bokan, Surk'uk'in Daji ne gun. Amma haka suka Shiga. Sallama sukai boka ya daka tsawa yace "ba ai masa Sallama( saboda tsabagen tab'ewa irin ta Boka) haka suka shiga Gwamma tace "Boka dama akwai wata Yarinya ce da mijina ya tsinta tunda tazo na shiga Matsala ayanzu hakan D.an Maigari zata Aura ,ni kuma ban so ,dalilan daya sa nazo ne akan a rusa Auren karya yiwu ,San nan Kishiya ta sai abinda nace Mata, shima Mijina ayi min abinda kome nayi bazai ga laifi na ba." Dariya ya kwarara "tabbas kina da sa a azzaluma mai son kanta, wan nan Aiki Sam bashida wahala,Amma fa kin cika muguwa ki tuba" dariya ya kurma yayi surkulle nan Hayak'i ya fuuuu ! ya d'auko wani Garin Magani yace "gashi ki yi abinci kitabbatar Kishiyarki da Mijinki sun ci . San nan kuma Aiki akan auren can Zanyi shi .Godiya sukai ya kwarara ihu "ba aimun Godiya tab'ab'b'u kawai, ni ai na gama shiga ha'ula'I gashi kuma kun biyo Layi ,dariya ya saka .(meemi tace sakarkaru kawai Allah dai ya kiyashe mu tab'ewa ya shiryi masu hali irin na Gwamma).Aje Kud'in sukayi suka tafi... .kubiyoni *By Queen meemi* . [3:58pm, 18/01/2017] 👑Meemi🔸: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣13❣ *JAN 2017* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* _*Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's*_ . _TUNATARWA_ _Ya 'yan uwa ,Mu yawaita neman gafara awajen Allah domin Allah gafururr Raheeem ne.Mu yawaita tasbihi domin samun kusanci ga Allah_ ************ Tun komawar Gwamma gida sai ta tsiri faran-faran da Jummai Malam kuwa har wani canja Ladabi tayi mai da yake itace da girki bata sha wahalar bad'a Maganin ba. D'aki ta koma tana Murmushi "sai ni Gwamma mai Mugunta ba dalili" can sai ta yatsine fuska "haka kawai ai sai inda mai na ya k'are." Washegari kuwa Gidan Maigari Ladidi ta damu da Maganar can k'asan ranta taji bata k'aunar Auren (Da alama Bokan Gwamma yayi tsiya)sai kai-kawo take tasa aka kira Mata Muntari Lokacin yana can Gidan da zasu Zauna da Amaryar sa yana Gyarawa,haka nan yazo Ladidi ta tareshi. "Muntari nikam wai kai bakasan Hansai ba 'yar Gidan nan bace?" Gabansa ne ya fad'i yace "haba Gwaggo kidena damuwa da jita- jita." "Kai Muntari ba wani Jita- Jita sai Gaskiya. Dai -dai Lokacin Maigari ya shigo ya tarar da su a tsaye nan ya tambayi ba'asi Gwoggo tace "Malam nikam ayi bincike kan auren nan nifa Gaskiya ina juya maganar Gwamma ,shiru yayi baice komi ba can yayi gyaran murya yace "nima kawai ji nake bansan Auren gabana har fad'uwa yake. Amma yau zan samu shi Malam d'in akan Maganar. *Bayan Awa Hud'u* Malam ne tsaye Shida Maigari suna Magana, idan ka kalli fuskar Malam tsab zaka Zakulo razanar dake kai .Amma sayya dake yace "wato ranka ya Dad'e Maganar Gaskiya Hansai ba 'yata bace nan ya gaya mai Asalin Had'uwar su San nan yace "Kaga kuwa mai Asalice Rabuwa ce kawai Sanadin daya sa bata tare dasu iyayen nata, idan akai duba da yanda abun ya faru, ayanzu nine matsayin uban ta." Maigari yace "Lalle Abin tausayi ce .Amma zan gayawa ita Mahaifiyar yaron aji ta bakinta. "Toh! toh! ba damuwa" inji Malam.Jikin sa asanyaye ya shiga gida . Shikam Maigari yajewa da Gwogg Maganar nan tayi tsalle ta dire kan D'anta bazai Auri wanda ba asan iyayenta ba, shima Maigari d'in baya so Amma kunyar Mutane yake ji, nan suka k'ark'are kawai Afasa Auren.Turk'ashi! wata Sabuwa kenan inji 'yan caca. Washegari kamar k'arfe Goma na Safe Malam na shirin tafiya Gona akai sallama dashi ya fita, Yaron Maigari yagani saida K'irjin sa ya buga, nan Yaron ya gaidashi sa'an nan yace da Malam Maigari na neman sa, tare suka jera nan sukaje Maigari na Zaune kan tabarma Asoron Gidan sa, ya shiga suka gaisa . Sai da yayi tsai San nan ya tashi ya Zauna yayi Gyaran Murya yace "wato Malam komai dama Muk'addari ne daga Allah, Matar Mutum Kabarin sa, kayi Hak'uri Auren nan abarshi, tunda uwar Yaron tace bataso, haka 'yan Uwa da Azo daga baya Ana kace nace! .Gwanda A Hak'ura. Dumm!! Malam yaji akansa Idon sa yayi ja "yace bakomi dama Matar Mutun kabarin sa, Allah ya had'a kowa da rabon sa". Maigari yace "Amin ,Amma aimin afuwa" Malam yace "Haba de wanda baisan k'addara ba shine zai damu" . Haka ya fita yana tafiya a Hanya yana Magana har yaje tsakar gidan sa, Gwamma na gefe tana shara Jumma na d'aki kawai sai ya zauna bakin Bishiya ya dafe kai. Gwamma ta taso "Aa Malam ya na gan ka haka?" Shikan Malam yace "An fasa Auren nan, Maigari yace ba zasu Aura wadda bata da Asali ba". D'ora Hannu tayi a ka kamar zata kurma ihu Malam yace "Aa meye haka? sai kace wanda akai Mutuwa". Gwamma data juya ta yi dariya ganin hak'an ta ya cimma ruwa tace "Allah sarki Hansai . Nan Jummai ta fito tana Malam Lafiya haka?" Gaya yayi take ta hau kuka, "shike nan na shiga uku yanzu abinda Zasuyi mana kenan! yau saura kwana takwas wayyo Allah" . Hansai dake shigowa Gidan da leda A Hannu ta aje da sauri ta tari Jummai tace "Inna Mayya faru?". Jummai tace "an fasa Aurenki da Muntari". Hansai taji kanta na yuuu saboda Mamaki. Luuu tayi k'as Asume. Da sauri sukayi kanta Gwamma kam D'aki ta Shige tana rawa, yay yafawa Hansai ruwa sukayi take ta Farfad'o da kuka, nan Jummai ta shige da ita D'akin ta, ta kwanta tana Mata nasiha ita kam Hansai son Muntari ne taji ya nunku kuka ta fasa. Can kwa Gidan Maigari Muntari shima Kukan yake saboda tsananin son da yakewa Hansai da shak'uwar da ke tsakanin su, Shekara biyar kenan daya k'wallafa ransa akan ta ,haka sukai ta lallashi shikam yace haka yake sonta koda bata da kowa d'aki ya shige ya kulle ,suka bishi suna bugawa Amma yak'i ya bud'e. Haka dai wad'an nan rayukan masu tsananin son juna ,suka rayu a kwana biyun nan cikin k'unar Rai ga gari ya d'auka ai Hansai bata da iyaye an fasa Auren ta, ko ina Maganar abuga k'auye. "Jummai inaga zanyi huce Haushi kawai domin duk Lokacin Dana sa Auren baza a fasa ba, sai a d'aura da Mudi". Fit Gwamma ta fito "Aikuwa badai a Gidan nan ba, wai abada Auren D'ana da wan nan abar, to sai de ko Bayan Raina". Malam yace "to sai de Muga ni dake Waye yafi iko da shi." Buga k'afa tayi "Ai wallahi sai de wani Amma ba Mudi ba,don kaga Yarinya ank'i Aurar ta, shine zaka Lak'abawa Mudi, haka kawai yo dama Mutum mai Hankali ina zai yadda D'ansa, ya Auri Hansai ba asali,gashi d'ai-d'ai shekarar ta goma sha biyar ace ba Aure" Malam yace "ya ishe ki haka Gwamma! domin zan huce akanki wallahi,kisani Hansai babu K'ashin tsiya agareta kawai haka Allah ya shirya,kuma in banda ke da bak'in cikin ki,Abinni Akwai Mata 'yan talatin 30 basi Auren fari ba Amma dan anan Anayi Masu aure da wuri shine zaki takurawa yarinya ,to wallahi gwamma ahir d'inki Aure ne sai anyi da Mudi ki fad'i ki Mutu shashashar banza" Afusace ya fita. Gwamma tace wallahi ba zan yardaba" ta kalli Jummai tace "Almunafum-fum kawai " ta juya ta shige band'aki Ita kanta Jummai bata son had'in domin tasan Mudi basu dace da kamilalliyar yarinyar irin Hansai ba, cutar ta kawai zaiyi . Duk wan nan budirin da ake Hansai na d'aki tana sharar Hawaye domin son datakewa Muntari jitake kamar yana k'aruwa gashi taji Ana zancen had'ata da Mudi. Malam da kan sa ya shiga dakin Jummai Bayan da ya sake shiga gidan,ya zauna kusa da Hansai yace "kiyi hak'uri 'yata komi Muk'addarii ne daga Allah ,dama Allah haka ya shirya ,kiyi hak'uri kinji sai de bansa ni ba idan na miki katsalan dan Arayuwa wadda nake ganin shine kad'ai zai sa na Huce haushi na had'aki da Muntari, duk da nasan bakya son sa." Dumm!! taji k'irjinta ya buga ta d'ago tace "tabbas Baba basai nayi tunani ba, ni ai ikon ka ce kayi duk abinda ya dace dani ka cancanci hakan Insha Allahu zanyi Biyayya agareka". Dad'i ne ya kashe shi ,yace "Allah yayi miki Albarka Hansai, ya Baku zama lafiya, tashi yayi ya fita Ita kam Hansai ji take Numfashin ta na gudu tana kamo Shi....... Auren nan zai yiwu kuwa?? ya Rayuwar Hansai zata cigaba da kasancewa? Anya Hansai da muntari zasu Hakura da juna kuwa?. Gwamma fa !!kudai cigaba da bin Queen meemi da sannu za muje inda muke San kaiwa. *By Queen meemi* . [1:04pm, 19/01/2017] 👑Meemi🔸: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣14❣ *JAN 2017* *®NWA* *Queenmeemi.WordPress.com* _*Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's*_ _Ban kanta daku ba *Nana* *fiddy, Husy, Maryam* *Ahmad,Neesah,Maman Ramlat ,Maman Rahma,Feedoh 'yar ficika*_ *********** Haka Nunfashinta yayi ta neman kufcewa ta Kwanta Ahankali ta Sami nutsuwa har bacci ya kwace mata. A b'angaren Muntari kuwa tunda ya rufe d'akin ya Kwanta kamar Matacce sai tunanin Rayuwar su da Hansai yake Zumbur ya mik'e lokacin karfe 9 na safe ya fita . Gwoggo na ganin sa tace Muntari ,bai waiwayo ba sai ma K'ara Sauri da yayi bai zame ko ina ba sai bayan Dutsen da suka Saba had'uwa da Hansai nan ya k'urawa wani gun da Hansai ke zaama. "Yace tabbas bazan iya rayuwa babu ke ba Hansai" kamar wani k'aramin yaro yana Magana "ya za'aimin haka! maisa sai dana sa rai dake, za a hanani ke, wallahi ina sonki" haka yayi ta Magana kamar zautacce. Mudi kuwa wajen 1O ya shiga Gidan da sauri Gwamma ta tareshi "Zonan d'an Gwamma" nan ya bita d'aki suka zauna tace "abinda zan gaya maka ka saurareni, kasan kuwa Malam yace zai had'aka Aure da Hansai"?. A mik'e ya tashi "kamar ni ace zan Auri Hansai bazata sab'uba." Gwamma tace "yawwa haka nake sanka ,ina zaka iya da ita ,yarinya da ba asan Usuli ba, ko da Malam ya maka Maganar kace baka son ta." Ganin wuce war Hansai Mudi ya bita da kallo shikam yasan Hansai nada kyau ga jikinta na birgeshi, wani tunani ya canja ya juyo "to Mama ki bari kawai na Auretan mana"! ai ba damuwa. Gwamma ta d'aga kai "Lalle kacika shashasha "to wallahi sai nayi maka baki akan hakan, kai me zakai da Yarinyar da ta gama tambad'a" . Mudi yace "to Mama ba damuwa nima dama ba wani sonta nake ba kawai don Naga baba yace dole ne." Tashi yayi ya fita suka had'u da Hansai Asoro yace "ke zo nan!" Zuwa tayi ya Nuna ta da Yatsa "kifa gane ni ba sa anki bane nai miki zarra, me zan dake Gwanda ma kicewa Baba bakya Sona ,don in ba haka ba wallahi zaki gane kurenki." Hansai tace "idan ba biyayya ba nima me zan dakai, wallahi darajar Baba kaci zan Aureka ne kuma wallahi bazan tab'a cewa bana son Auren ba." Kai Mata hauri yayi tayi baya tana kuka,dama da Hijab d'inta ,kawai se ta zarce Bayan dutsen su tana zuwa ta zauna da abin busa d'inta, tanayi idon ta na b'ulb'ulo da hawaye ,domin ta tuno Muntarin ta, kamar Amafarki yaji sauti . Firgigit ya mik'e daga baccin daya kwashe shi,tsai ya ganota durowa yayi daga kan Bishiyar ya je kusa da ita ya tsaya, yace "Hansai an rabamu ko? Da sauri ta juyo suka had'a Ido tace "Muntari yanzu shikenan Mafarkin mu ya zama ba Gaskiya ba?". Muntari yace "nikam bazan iya babu ke ba". Hansai itama tace "nima haka Muntari .Amma ba yanda muka iya". Kuka ne ya kubce Mata da gudu tayi baya ya bita, suka tsaya yace "har abada Hanasi kece Masoyiyata, ina Sonki Sona Gaskiya dama zasu Amince da Auren namu". Tace "Muntari mu fawwalawa Allah shine zai iyar mana" haka sukai ta hira. Suka rabu cike da k'unar Rai. ******** Bayan kwana 2 anyi rigingimu a Gidan inda Gwamma ta kek'ashe baba ma ya kafe . Yauma da take tsaye tana tunani "yo wai ni ko Maganin da boka ya ban baya Aiki ne? Naga Malam baya yarda da Magana ta" nan Taje ta duba kwanan ajiyarta,Mamaki ne ya cika ta Ganin Maganin da Bokan ya bata ,tace "kodai bashi na zuba ba!". "Lalle dole mana Malam yana min musu" da sauri ta d'auka Mayafinta,ta fita Gidan Delu, zuwanta ta Sanar da ita, Shine Delu tace "yanzu Shikenan kin b'ata Aikin ki da kanki". Gwamma tace "to ni yazanyi ,yanzu?" Delu tace "ki kawo wani Kud'in na koma ya had'a wani Gwamma tace nikam wallahi ban da kud'i sai dai ki ran ta Min". Tace "ba Matsala zan baki" nan suka K'ark'are zata je anjima haka ta tafi tana Surutai A hanya. Wajen k'arfe 8 na dare sai ga Delu har taje gun bokan. Gwamma suka kule ad'aki tace "gashi Boka yace ki tabbatar ayau da daddare kin amfani dashi Hayak'i Zakiyi kamar turare, inde suka shak'a kin samu kansu." Da rawar Jiki Gwamma ta boye a zanin ta,sukai Sallama da Delu ta tafi. Bayan Dan Lokaci ta turara Hayakin duk suka shak'a . Washegari kuwa Malam ya tsare Mudi yace "kaga yau saura kwana 2 D'aurin Aurenka." Mudi ya kada baki yace "Baba ni bana son Auren nan". Gwamma dake d'aki tace "yawwa". Baba ya sunkwi da kai "yanzu kai bakaji kunyar gayan Maganar nan ba na ko?! ai shike nan dama ai babarka tace bata so kuma nasan ita ta kitsa ma. Amma komi Mutun yayi Shi za ayi mai. Mudi kam wata jakar bagkoy ya d'auko, ya tsaya "ni na tafi Lagos neman kud'i baba dama yau na tsara tafiyar". Gwamma ta fito "Yawwa mudi yau ka biyani". Baba yace "ni kam ina Umartar ka A matsayina na Mahaifinka kar kaje duk da nasan ba ka Maidani komai ba." Gwamma tace "wallahi Sayyaje". Mudi ya d'uri jaka yace acan zan hadu da Lawandi ya fice. Gwamma tayi shewa "Ahayye yaraye nanaye" Kuka hansai keyi saboda tausayin Baba, tace "Baba kayi hak'ur. Baba yace "bakomi Hansai ina Alfahri dake Allah ya baki miji na gari" ya tashi ya fita. Haka Malam duk ya sanar an fasa auren nan nan gari ya hau tsogwami anata Gulmace- Gulamace ko fita Hansai tayi sai a fara ga Hansai mai bak'in Jini "da kuka take dawo wa, sai da Malam yaje yayiwa tufkar hanci ,San nan aka sakar Mata Mara. K'anin Maigari ne dake zaune a kano yazo mai suna Alhaji Salisu, Shi ya tashi a hannun k'anin Babar su Maigari to ita abirni take Aure shiisa ta d'auke Shi ya tashi yayi Boko ,yanzu hakan yana aiki A NNPC Manager ne, yana da 'ya'ya da Mata Biyu. Zuwansa Gidan ya tarar Ana tak'addama akan Muntari kan ya kafe bazai Auri wata Lantana da Gwoggo ta kawo ya Aura yace tunda anraba Shi da Hansai ba 'yar da zai Aura, to ganin hakan Alhaji Salis yace zai tafi dashi can Birni ya cigaba da karatu ,Jin an ambaci karatu yasa ya Amince zai bishi. bankwana .. . *BY QUEEN MEEMI* . [12:55pm, 21/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣15❣ *JAN 2017* *Queenmeemi.WordPress.com* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman Family's_* _TUNATARWA_ _'yan uwa muna hak'uri da rayuwa aduk yanda tazo mana,hak'uri maganin zaman duniya ne ,komai ya sameka mujarrabi ne daga Allah_ ****** *Misalin k'arfe 9 na safe* Shirin sa yayi tsaf ya had'a Jakarsa tunani yayi dole yayi bankwana da Hansai, hakan ya tashi ya tafi gidan su, ikon Allah adai-dai Lokacin Hansai ta fito, turus tayi suka K'urawa Juna Ido nan yace "zo muje bayan Dutse." Haka kuwa akai ta bishi a baya har suka je ,nan ya zauna yace "Hansai birni zan tafi" dafe kirji! tayi ta Mik'e "na shiga uku." Muntari yace "gwanda na tafi Idan na zauna ina ganinki Zuciyata zata iya bugawa." Saboda nasan an raba mu soyayyarki tana nan a Araina kece ta Farko Dana keso." Hansai tace Rabuwa da kai Shine Sanadin cin Fuskar da na ke fuskanta daga gun Mutane da Ammana Aure da hankalina kwance,ba wanda zai min." Kuka ta kuma fashewa "Wallahi bazan so kowa ba sai kai" Shima da k'walla ya fito mai yana jin Zuciyarsa kamar zata fashe. "Hansai da inada dama da sai na gudu muyi Aure. Amma ba dama San nan nama fasa tafiya Birnin ma, Zan Zauna na Jajirce har su yar da subani ke ko." Hansai ta mik'e tsaye Muntari karkayi hakan ka tafi kawai. "Allah ya k'addara Saduwarmu." Kollonta Yayi da Siraran Hawaye suka Zubo yace "Idan da rai da rabo.Hansai inde da rabo a tsakanin mu gaba zami Aure." Murmushi tayi "Allah yasa" Nan suka tafi a tare sun zo kwanar su yaga Maigar da Alhaji Salisu an saka Jakar sa a Mota kuka ne ya Kubcewa Hansai. Maigari ya kwad'o Mai kira tafiya yayi yana waiwayon Hansai .Maigari yace Au gurin "Yarinyar can kaje? Iyayen naci ai gwanda ka tafi Birnin kowama ya wuta Soyayya ba Alkunya." Dariya Alhji salisu yayi yace "Zamani ne ai, Amma mai yasa Baku basi Auren ba.? Maigari yace "Yarinyar ce ba usuli . Dai-dai Lokacin Muntari ya K'araso Maigari yace "tafiya zakuyi." Idon sa yayi ja yace "baba na fasa" Maigari yace "saboda kaga 'yar Gwal ko? to dole ka tafi" sharshar hawaye ke sauka ya tashi ya Shiga gida don sallama da Gwoggo. Wata Takarda ya d'auko da wata Leda , bayan sun sallama da Gwoggon. D'ahiru kanin sa ya bawa ya kaima Hansai. Tana nan tsaye inda ya barta can ta tusa Hijab Baki tana Kuka saida ya tsaya ya k'ura Mata Ido ya share Hawaye ya shige Motar ,Maigari yace "Allah ya kiyaye ya bada sa' a ". Ganin an tada Motar Hansai ta durk'ushe agun tana gurshek'en kuka. Tamkar ance Baba ya Mutu Muntari, yana ganota ji yake kamar yayi tsalle ya kamota, D'ahiru zuwa yayi ya mik'a Mata "gashi inji yaya" da sauri ta karb'a sai da taga tafiyar su San nan ta tashi kamar wadda k'wai ya fashewa a ciki ta shiga gida. Gwamma na d'umamen tuwo tace "ke zo nan.? ko kallonta batai ba ta Shige d'akin Jummai. Zazzabi Mai zafi ya rufeta. Allah sarki Soyayya. Saida Hansai tayi kwana 2 tana ciwon love Hankulan su Malam atashe. Allah da ikon sa ta samu sauk'i . Hakanan Gwamma ta bud'e shafin Cusgunawa Jummai da Hansai. tunda yanzu ta Shanye Malam baya iya katab'us a gidan, koya ga Abu baiyi ba ,da yayi Magana zata hayayyak'o mai. Hansai kuma ad'an Lokacin nan ta gane shayi ruwa ne don azabtuwa da take domin Gwamma ta bud'e Mata huta. Yauma data tasheta tana bacci "k!e ke! tashi kizo ki min talllan zogale." Mutsitstsike I'do tayi. Gwamma tace banza Gansai ni tashi ki tafi." Hansai tace "talla kuma! ni aiban iya ba." Gwamma ta kai Mata duka yaran gari dake yi finsu kikai? Tashi Jummai tayi ta Shiga d'akin "Haba Yaya wane talla kuma? ai kinsan ba'ai agidan nan." Gwamma tace "to kan Hansaai za a fara, haka ta taso ta agaba wata Jibgegiyar Langa ce ta d'ora mata. Malam ne ya fito Jummai tace "Saboda Allah Malam ace kamar Hansai za a aiketa Talla?. Malam yace "haba dai ai baidace ayi ba Gwamma tace "wallahi bazan asara ba dole taje" Malam yace "to shike nan. Hansai Allah ya kiyaye kiyi hakuri ya fita Jummai na Mamakin canjawar Malam kwanakin nan Sam kamar tsoron Gwamma yake baya tanka mata. Haka dai rayuwa tayi ta tafiya yau Fari gobe Baki Acikin hakan ba irin taskun da Hansai bata shiga ba, saboda Malam yanzu bai fiya Magana ba ,hakuri ne yazamo tushen Rayuwar Hansai. BAYAN SHEKARA DAYA kudakace ni fans ga wan nan ba yawa saboda Banda caji. *By Queen Meemi* [12:31pm, 22/01/2017] 👑Meemi🔸: . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣16❣ *JAN 2017* *®NWA* _*Queenmeemi.WordPress.com_* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman Family's_* _TUNATARWA_ _Cikakkiyar Nutsuwar Ruhi ta tabbata ga Mutuncin da Tunanin Laifukan sa ya hanashi hangen laifin wani ,'yan uwa mu daina aibata 'yan uwan mu, mu guji yi da wani da aibata Shi, batare da hak'k'in sa ba._ *Abuja* Sumy ce tsaye tana jijjiga "ke kandala" ta k'wala kiranta a karo na 2 Jikinta na rawa ta tawo "gani Anty Sumy" tsaki taja "wato na baki wanki baki ba, ina kika tsaya?" "Mopin nayiwa Antyn mubrk" Sumy tace "awajenta kike ko gun Umma?" "Aa gun umma" "To kar na k'ara ganinki acan, gashin can kije ki wanken Under Wears d'ina a Washing Machine" Jiki da b'ari ta tafi ita kam Sumy side d'in Anty Rabi taje, tana zaune tana karanta Novel ta tsaya "Anty sako daga Umma tace adaina arar Mata 'yar Aiki, course ba ke kika d'auka ba, Anty Rabi ta had'e rai to mara kunya naji". Sumy ta fita tana k'unk'uni "inbanda Shima Dady da aure- aure Anty Rabi ai sa'ar Ruby ce" mtwss taja tsaki tayi side nasu. Anty rabi kuwa inda sabo ta saba nan ta k'uduri Aniyar Dady na dawowa zata sanar mai itama zata d'au 'yar Aikin. Haka kuwa akai A round 6 :pm tajiyo dirin motar Dady data guards din sa ,Zuwa tayi ta fesa wanka da kwalliya San nan ta tafi. Mama da Umma ta gani kowacce a Hakim ce agefen sa Murumushi ya sakar mata "mum's Boys y gida" zama tayi tace "fine Dadn Boys". Mama tace Alhaji kenan idan an girma ai a sani tashi Sukayi suka fita, dayake girkin Rabia ne Hug ya bata, nan ta fara hidima da shi bayan ya kimtsa tace "Dady dama inason nai samu 'yar Aiki Saboda Shiru Side D'ina kuma gashi kowacce nasa sai a ce ba aso ka kira. "Mum's boys ba damuwa ki nema" Dad'i ne ya kashe ta tace tana zuwa. After Some Minutes Rabia tayi dialing layin Maman ta ,bugu d'aya aka d'auka nan tace "Mama dama ina son Mai Aiki ne" daga can Mama tace "ba damuwa zan baki Nomber din Lami ki kirata, bari na turo miki" cike da jun dad'i ta kashe kirr sai ga Msg ya shigo. Nan ta buga Layin din Lami daga can ta d'auka suka gaisa tace "Rabia ce 'yar Maman kano" Lami ta washe baki "ranki ya Dad'e" nan suka gaisa tace tana son mai Aiki. Amma me D'an girma ba k'arama can ba." Lami tace babu damuwa Insha Allahu za asamu nan suka kashe. *********** Bayan kwana 2 lami ta tafi gidan k'awarta shiga da sallama ta amsa "Aa Rai kanga Rai" nan suka b'arke da hira Lami tace to nikam Ana neman mai Aiki kin San ni k'anana nake kaiwa 'yan 11 zuwa 12 to tace 'yar me girma nake so" Delu tace tooo Zan Bincika miki ba damuwa." Bayan tafiyar Lami Delu tayi tunanin kawai taje Gidan Gwamma. Bayan kwana d'aya da Maganar. Delu taje Gidan Gwamma .nan hira ta b'arke na yaushe Gari zance har ya kai kan Hansai nan Delu tace : "Hmm haba da Sake ta yaya za'ace ki Zauna da katuwar Budurwa bakya Morarta. Kibani ita Mutafi Abuja ta nemar miki kud'i ko Samira kya sai mata, sai kace ba Inna Gwamma ba mai Mugunta ba Dalili" .Ta bata hannu suka tafa tareda shewa "Waima ina Hansai en take ne"? Delu ta tambaya. "Na aiketa rafi d'ebo tafasa cewar Gwamma Dede lokacin Hansai tashigo ta tsaya tsaye "Gashi Mama". Gwamma ta kalleta "ke Hansai baki ga Delu bane? kin tsaya gansai ba gaisauwa. Mai suffar Munafukai waima waya baki izinin dad'ewa? Jummai ta fito daga d'aki "ni nace tabiya ta sayo kuka" Gwamma tace na gaji da Gulmarki Jummla tam".Ke kuma Hansai Algunguma Nagaji da Zamanki haka tafiya Dole ce ki nemar mun kud'in hidimar Bikin Dije inya tashi ehe. Saura naji kingayawa Malam nida kene tayi k'wafa Shige ki ban Guri." ta shige sum -sum tai Daki Delu k'awar Gwamma tace "Kai Mutuniiyata ,wan nan baza Umarni haka?" tafawa sukai "ke to ni ta wasa ce ai barni da Munafukai sun isheni nafisu na fiso dagani sai 'ya 'ya na.... Tana shiga D'aki tasaki kuka tana Surutai tana cewa narasa mena tsarewa Inna Gwamma wannan tsana haka tayimin yayi yawa dame zanji ya Allah ka kawomin D'auki takwanta akan karauni tabarmar dake D'aki Dakin kamar kurkuku babu daban kasa Saman sa sai A zara ga cinnaka ba k'warin dababu aciki ga Shirgi,duk wan nan Gwamma ce tayi bayan ta zama mai fada aji agidan tasa Hansai ta koma d'akin shirgin. ***** Acan tsakar Gidan kuwa Bayan tafiyar Delu ,sun gama K'ark'are Maganar Gobe za a kai Hansai Aiki Taa baje A K'ark'ashin Bishiya ana ta yiwa Jummala Habaici inda Sabo Jummala tasaba jin wannan dan haka tak'i kulata taci gaba Aikinta na had'a Danbu A Zuciyar tana cewa Allah ya shiryata Mata kamar Shed'an bata da Magana sai ta sharri bayan ta gama taraba ta bayar aka kaiwa Malam Gona ta. Jummai ta faki ido ta shiga D'akin Hansai ta tarar da ita tana ta kuka abun tausayi Ta tasheta tace "haba Hansai meye abin kuka? sai kace saban abu kullum fa kinsan sai Anyi haka a Gidan nan tashi kici Abinci miyi Magana dak'yar ta tashi kan ta nasara Mata Kamarya tsage tafara ci Hannu baka Hunnu baka Hannu k'warya tas ta cinye Rabanta da Abinci tin na safe Gashi yanzu kusan La'asar bayan tagama tasha ruwa tadawo D'akin Jummala tace "Abinda zan gaya miki. Kinga tunda wannan Matar tafara wannan Maganar ta kaiki aiki to sai tayi ki tsare mutuncinki. Yadda Matar nan takeso taga wani abin kunya yasameki ki kula Da Sallah da Addua Allah ya tsare ki da ina da iko da na hana Amma ko Malam bai isaba bareni zan dinga yimiki Addu'a Allah yakare. Suna cikin Magana sukaji Ihun Dije nacewa "Mama suna ta Zaginki ." nan Gwamma tayin kukan kura ta tashi tace "barni da Shegu yau zasuga tijara agidan nan ta Dauko ittace taiyo,D'akin a fusace tana zuwa tad'aga ice zata Makamusu Malam yayi Sallama da Gudu ya zo ya kwace ice yace "haba Gwamma kullum kebaki da Aiki sai fad'a kishiyar da Yarinya." Tace "dalla can "Malam matsa kabani guri sahurami kuma wallhi sai na suburbud'i Hansai a Gidan nan ko tai bacci Zatasan sunhad'u suna zagina." Jummai tace "wallhi ba Zaginta Mukeba". Allah sarki Hansai tini tarude sai Rawar Jiki take saboda tasan Gwamma da Mugunta Dije sai Gwalo take mata . Malam yace "baki isa kidake taba ba wallhi babbar banza Mara Girma saina Jiki." Gwamma tana kad'a jiki Malam yace jummai kama Hansai kuje d'akinki". Gwamma tace Malam "Gobe Hansai zan kaita Aiki har min Magana da Lami za akaita Abuja." Cak! Malam ya tsaya baice komai ba Yace "Naga yanda za ai taje Allah ya kaimu goben." *By Queen meemi* . [7:08am, 23/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣17❣ *JAN 2017* *NWA* *Queenmeemi.wordpress.com* *_This page Dedicated to Anty Maijidda Musa Tnz A a lot_* _TUNATARWA_ _yawai ta istigfari Awurun Allah ,yana saukaka Samun biyan bukata_ ****** Washegari kuwa da Asubayin fari Gwamma ta fito da Hansai ko gama wartsakewa batai ba ta tulo Mata wankin ta tace tai maata na k'arshe kan Rana ta gama fitowa, ga sanyi hakan tayi sai 7 ta gama. K'arfe Goma Hansai ta gama Shiri sai kuka take Malam ya fito "Gwamma nadai gaya Miki Yarinyar nan baza taje ba, wallahi in taje ranki sai ya b'aci." Gwamma tace sai de ya b'acin ,haka kawai Ga hanyar samu sai na zauna tunda ita ba Aure dole ta nemar mun kud'I. Don baka ga Laran Gidan Toka ba sai busha sha Suke da Kudin Aikin nata." Malam yace "to ki kai Dije ,Amma ba Hansai ba tunda ba ' yarki bace, Hansai Jeki maida kayan nan." Cike da D'oki da Jin Dad'i ta koma D'akin ,Shi kuma ya Fita Gona." Bai dad'e da tafiya bada ,sai ga Delu ta Shiga gidan. Da Zumud'i Gwamma ta tare ta,nan taje ta fito da Hansai "fito Algunguma komai Malam zaiyi saide yayi sai kinje." Jikin Jummai a sanyaye ta kalli Hansai tacea "Hansai ki Rik'e Allah ki kiyaye Mutuncin ki ki Zauna Lafiya dakowa, Allah ya karemin ke" Rungume Jummai tayi "Inna banason tafiya" "Fito ko na zo na makeki da duka" cewar Gwamma Jummai tace "Amma dai Malam ai ya hana. Gwamma tace "tafi can wayake take" nan ta kalli Hansai "ke kuma d'auki kayan nan ki D'ora akai, wallahi idan kiyaje bakya Aiki sosai sai kinci na Jaki. Delu tace sai kizo mu tafi" kuka Hansai take tamakar taci babu da k'yar ta tafi, Jummai ma kuka suna fita Gwamma Tai shewa "wayyo Ina daga zaune kud'i suna zuwar min." Delu kuwa suna tafiya sai hantarar Hansai take har sukaje Gidan Lami dama Jiran su ake yara ne su biyu Hansai ta uku .Amma duk ta fisu Girma Lami na ganin Hansai tace "Yawwa kinga wan nan zata dace da Alama zatai tsafta". D'ari biyar ta kawo ta bawa Delu "ga Ladanki" nan sukai Sallama har ta tafi ta dawo "Yawwa Lami kinga Hansai sai kin Jamata kunne domin bataji.". Lami tace "yo ai dama duk 'yan Aiki sai na Jamusu kunne" sai wajen k'arfe Goma Shabiyu suka tafi,in Banda kuka ba abinda Hansai keyi. Malam kuwa yana komawa Gida yaga Jummai na kuka ya tambaya tace "Ai antafi da Hansai." zama yayi yace "Amma Gwamma Allah sayya yimin sakayya duk abinda kike Allah zai saka mana" Jummai muyiwa Hansai Addua, Allah yasa hakan Shine mafi Alheri agareta ,Allah ya bata kwanciyar hankali" Jummai tace "Amin." Sunje tashar mota suka shiga fuuu Mota taja sai kano ta Dabo Tunbin Giwa kodame kazo Anfika ,sai la' asar sukaje nan Lami taje duk Gidan dake bukatar Yaran takai musu ta k'arbi Kud'in sallama Dana kowo su.Hansai ce ta k'arshe ta kaita Gun Maman Rabia dake kanon tamfatsetsen Gidan suka shiga Hansai nata Raba Ido shigar su Falo yayi dai-dai da fitowar Mama tace "Aa Lami kece da Yamman nan!" Lami tace "wallahi." Au! har an Sami 'yar Aikin Lalle Lami agaishe ki" nan ta zauna tacii Abinci San nan tai shirin tafiya nan ma mama ta bata Kud'in kawo wa ta fita Idan Hansai ne suka kawo ruwa Lami ta kirata tace "ke hansai wallahi karnaji karna gani Banda sata da k'azanta zan zo d'aukanki Ganin gida in kikai watanni "nan tayi tafiyar ta. Mama kam Umartar Hansai tayi data yi wanka hakan kuwa akai ta kirawo iya mai Aikinta tace ta duba kan Hansai nan ta tsefe mata wajen 8 na dare aka wanke kan tayi wanka sosai ta ci Abinci tayi Sallah ta kwanta bacci. *washegari* Da safe Hansai ta karya da breakfast mai Dad'i nan iya tayi Mata kitso Mama na kan kujera Rabia ta bugo waya tace "an samu! Mama tace "gata nan kuwa Masha Allah, an samu" yanzu sai ki turo driver yazo ya d'auke ta, Rabia tace "to Mama Amma sai gobe, saboda yau yana da uzuri" Mama tace "ba matsala" nan ta kashe . Ta kalli Hansai tace "ni meye Sunanki na Gaskiya ne? Hansai tace "Hansai Shine na Gaskiya" iya tayi Dariya "Hansai ai ba Sunan Gaskiya bane" Mama tace "A toh". Amma kinayin Makarantar Allo Acan? Hansai tace "Eh ina Makarantar Allo, Nayi Izifi Arbain" Mama tace "Masha Allah.Boko fa" iya tace ai kinsan k'auye basu damu da boko ba,Na Addinin Ma wasu ko ansasu basa yi" Hansai tace "Nayi boko Ajina uku a Secondary" Mama tace Lalle ki Godewa Allah. Bayan an agamai Mata kitson Mama ta kuma sata tayi wanka nan tace kinga Abuja za'a kaiki kina tsafta ,duk da naga balaifi." Hansai tace "to" Hansai kuwa duk bidirin nan zuciyar ta na kukan tuno inna da baba haka tayi yinin nan har ta dad'a fes ba Tsangwamar Gwamma. Washegari kuwa wajen 12 sai ga Ashiru driver bayan yaci Abinci nan Hansai tasaka kayanta bayan motar suka d'au Hanya sai Birnin Tarayyya. Bari na D'an huta kan su Hansan su sauka. Sister's kuyi Hkr ba kullum zakuna jina ba saboda matsalar ba wuta ngd. *By Queen Meemi* [9:52am, 26/01/2017] 👑Meemi🔸: . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣18❣ *JAN 2017* *Queenmeemi.WordPress.com* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_* _Sakon ku ya iso gareni masoyana na gode da kulawa❤_ ***** Sai wajen k'arfe 6 dai -de su Hansai sukaje Lokacin taci bacci ta k'oshi Hon din da Ashiru nayiwa Maigadi ne ya tashe ta ta bud'e Ido tayi tozali da k'awataccen Gida juya baya tayi taga duk Layin da suka shigo kusan hakan Gidajen su ke .Maidadi ne ya tashi ya bud'e zirif Ashiru Driver ya shiga yayi parking a gurin adana Motoci ne Reras a ajiye, ahankali ta fita Ashiru ya fito Mata da kayanta daga bayan Motar, nan tayi Duru- Duru sai kallon gidan take wanda ada tana ganin na Maman Kano mai kyau ,sai taga ko Rabin kyan wan nan be kaiba da Girma da k'watuwa. Ashiru ne yayi gaba tabishi suka danna door bell da dad'ewa wani Namiji yazo ya bud'e ya basu Hanya suka Shiga ya cigaba da goge -gogen sa y Mamaki k'arara akan fuskar Hansai,Masha Allah ta kira azuciyar ta Sakamakon Tozali datayi da had'ad'd'en falon wanda dukan sa acircle yake Ashiru ne ya tsaya can sai ga Anty Rabi ta fito daga Part nata da D'an saurin ta d'auke da Murmushi saman fuskar ta ,tace "Aa Sannu Ashiru kunsha Hanya!" Alamar russuna Mata yayi yace "eh Wallahi Maman tace agaishe ki" nan ya juya ya fita Rabia ta kalli Hansai "muje ko" zungi zungwi ta bita sai kallon waje -waje take tana Mamakin tsaruwar Gidan Ahankali ta furta "Aljannar Duniya" Jikake ta guum! ta k'ume da k'ofar Shiga paty d'in Anty Rabia da Hanzari Anty ta jiyo "Aa kiyi ahankali fa" nan suka shiga b'angaren Antyn baki sakin baki Hansai tayi ganin wani falon wanda yafi kyau ,nan tayi ta k'auyancin ta zama tayi gefen kujera ta kafawa Tv Ido tana kallon film d'in da ake ga sanyin Ac na hurowa had'e da sanyayan turaren wuta zo kuga yanda Hansai ta langwab'ar da kai gefen kujera kamar tai bacci. Anty Rabia kam dawowa tayi d'auke da Khalil a Hannu ta zauna tace "ya Sunanki ne?" Hansai ta sunkwi da kai Sunana Hansai . Anty tace "Madallah Garinku fa?" Tace "Bunkure". kina Makarnta tace "eh Ajina Uku a secondary" (oh su Hansai Ana ji da Aji ukun din nan da akai)Anty tace "Madallah, tom kinga yanzu Aiki kikazo na Farko banason k'azanta na Biyu Banson Gulma kinga da 'yan Aiki wajen biyu A Gidan nan Kamar ki da tsohuwa ga Namji mai Goge -Gogen Babbann falo, ki Kame kanki,Banda shiga inda ba hurumin ki ba, Zakina min Renen boys D'ina Mubarakh da khalil ,San nan Zakina Wanke- Wanke da Gyaran kitchen, nan falon Zakina Shareshi da Goge kujera ,zakina Goge kayansu Tv vedio ,center Table su Dining Teble duk kiyi sai ki Moping tile d'in da D'an abinda baka rasa ba. Shine kad'ai iya Aikin ki, Maganar kud'in Aikin ki Kuma dama Munyi Maganar da Lami." Dadi ne ya kama Hansai Jin Aikin bame yawa ba don ak'auye wanda take ya ninka wannan ,nan ta d'ago "Insha Allahu Anty zanyi abinda kika ce finsa Ma" Anty Rabia tace "yawwa yanzu kije zan nuna Miki toilet kiyi wanka duk da ba anan Zakina kwana ba akwai Shashin Masu Aiki" Hansai tace "tam Anty." Dai-dai Time d'in aka kira Sallah nan ta tashi tayi gaba ta bita suka fita Daga part d'in suka koma Ainihin Big Falon, San nan sukayi wani dan sako daga Arewa nan suka Shiga wani korido San nan suka shiga wangamemen daki da Madaidaitun katifu Guda Hud'u aciki,Gefe ga wasu akwatin Katako Babba Doguwa kayan su ne aciki. Kande ce da Karime suna Alwala a Band'akin dake Cikin D'akin Anty tayi Magana nan suka fito duk suka Zube. Anty tace "ina kuke kwance? wacce katifa ce Empty Kande tace "waccen ta Lokon e babu ,wan nan ta Tsakiyar nice akai sai ta Gefen Karime waccen kuma ta iya Abu ce sai ta Lokane ba kowa." Anty tace "ok naji ke Hansai kije waccen nan zakina kwana ki aje kayanki Acikin Wan nan doguwar Kwatin tunda nasan akwai inda babu komai aciki, Bayan haka yanzu ki fara wanka kan ki sallar tunda ba a tayar ba." Idan kinyi Sallaar kizo side Dina." Hansai tace "to" nan ta fita zuwa kuwa tayi ta aje kayan nata Acikin akwatin ta zauna kan Luntsumar katifar San nan ta tashi tashiga band'akin tayo Wankan ta fito . Lokacin su kande na zaune sai hira suke ta canja kaya tayi Sallah San nan ta kalli su Karime tace "Sanunku" sukace "yawwa" suka D'an tab'a hira San nan ta tashi ta fita. Sai hanyar ta kauce Mata ta Manta part din Anty tarasa ina yake sai zagaye falon take duk girman Shi, take nan tayi part din Dake Gabanta b'angaren Hagu Alhalin ita Anty tana side na Dama shiga tayi a hankali ta Danyi sallama ta shiga Zuby ce ta d'ago "waye?. Hansai tace "nice" sai Lokacin ta gane ba gun bane Zuby tace "ke daga ina?". Hansai tace "nayi Makuwa ne!! gun Anty Rabia zani." Zuby tace "oya get out ,ba nan bane." Haka ta juya sai Lokacin ta gano gun ta shiga da Sallama Anty na Sallah ta d'au Khalil tana mai Wasa sai Dariya yake bayan gama Sallar Anty tace "Jeki kitchen akwai abinci ki d'auka" ta nuna mata. Tashi tayi tabi ta Gefen Dining ta yi kitchens d'in sakin baki tayi tana kallo nan ma kamar ba Kitchen ba ga had'uwa ga Girma sai kalle -kalle take San nan tadauka ta fita, tace Anty na d'auko" Anty tace "ok." Hanyar fita tayi tace "dawo ki Zauna anan kici nan ta zauna tana ci Dad'i ya cika kunnen Hansai sai Hamdala take ,nan ta tuno Inna da Malam tad'an Share hawayen da suke neman zubo Mata,tas ta cinye takai kwanon Kitchen. Ta fito tace "Anty ina Omo zan wanke kwanukan" Anty tace "habade! kije kawai ki kwanta ki huta." "Hansai tace Anty bari nayi kawai" nan ta shiga ta nuna Mata sinck ta nuna Mata inda zata matsu Ruwan San nan ta fita . Cikin Mintuna ta wanke komai ta kife ta fita ta tsugunna tace Anty "na gama" Anty tace "to Hansai ki je ki Huta." Nan ta fita bata b'ata ba Saboda ta Gane gun yanzu sai Hira su Karime, suke nan ta Zauna Lokacin Iya ta shigo Iya tace "Aa Kande kuce Sabuwa Muka Samu?" Hansai tayi Dariya ta Zauna Iya tace "to Sannu da zuwa 'yata Hansai" tace "yawwa" Nan da nan tabi su Karime sai hira suke kamar sun dad'e da Sabo dama 'yan aiki in sunga Juna akwai Saurin Sabo wan nan ke nan. kubiyo ni *By Queen meemi* [12:16pm, 27/01/2017] 👑Meemi🔸: . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣19❣ *JAN 2017* ®NWA *_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_* _My fecebook fans ina miko gaisuwa gunku nagode da kulawa_ ******** Yau kwanan Hansai uku haryanzu agajiye take yauma sai wajen 9 Hansai ta tashi taga d'akin wayam duk basu Kande da Sauri ta tashi tayi waje Part dinsu tayi tana shiga taga Anty na breakfast tsugunnawa tayi "Anty kiyi hakr na Makara." Da Murmushi Anty ta juyo "Ai nasan baccin gajiya ne ,yanzu sai kiyi" da sauri ta mik'e tai kitchen ta fara Aiki sai wajen 11 ta gama San nan tayi break tafita nan taga iyalan gidan a big falo nan Gabanta ya bada Ras! tazo zata wuce Umma ta kirata taje duk suka zubo Mata ido, tace "ke 'yar Aikin Anty ce? tace eh Mama tace Gata kwa kyakkyawa Sumy ta tab'e baki ta kafa uban d'auri da alama school zata "yauwa ke ya sunanki? ta fad'a Sumy tace "biyoni" salo -salo ta bita ta Shiga d'akin su ta dauko mata under wears da bra ta wanke ta kalleta "kifa wanke tas bansan Almundaha na" tace "to Anty" k'was- k'was ta fita Hansai ta mik'e tayi part d'in Anty tana zaune tana bawa khalil tea ta tsugunna "kinga Anty d'aya daga cikin 'yann Gidan nan tace na wanke Mata" tsaki Anty tayi "oh wad'an nan yara ba kunya Bra ma din sai an wanke musu duk gayun tsaki tayi, ni sun hanani Kula nasu Amma bakomi je kiyi." Nan ta tashi taje can D'akin su ta tarar da karime na ninke kayan ta tace karime don Allah ina ake wanki karime tace acan bayan D'akin nan ne bari na Nuna miki nan ta tashi ta fita ta bita ta zagaya da ita ta nuna Mata hakan ta zauna tad'au wani boket ta zuba tana wankewa tas ta wanke ta shanya. Ta koma D'akin su tayi wanka Bayan awa uku Sumy ta fako motar ta ta shigo dai de Sady ma ta fako Tata ta shigo Hansai Lokacin na zaune a kusa da flowers Sumy tace "ke d'ebon kayan" shaf ta manta da gudu ta tashi tayi bayan nan taga duk sun fad'i k'asa sun b'aci tsaki tayi ta d'auka takuma wankewa. San nan ta koma ta shiga d'akin nasu birjik kowacce daga ita sai shimi tace Anty na wanke Amma na koma kayan duk sun b'aci ran Sumy ya baciallema 'yar Aikin nan! ni zaki b'atawa kaya" ji kake kauu ta kai Mata Mari Ruma tace kai Sumy me tai miki kin fiya zalinci" Murgud'a baki tayi Aiki nasa ta ta b'atan." Nan ta kalleta "Get out kona Mauje ki Stupit kawai" kuka Hansai take tafita gaanin Anty Rabia zaune a big falo yasa ta D'an kawar da fuskar ta nan kwa ta ganta "tace zo nan" taje ta tsugunna meya sameki nan ta gaya Mata cikin b'acin Rai Anty taja Hannun Hansai suka tafi d'akin ta shiga tace "ke Sumy me yarinyar nan ta miki?. Sumy tace "Aiki nasa ta." Anty tace "ke tsaya kiji karma wanda ta kuma sata Aiki tunda Baku kuka d'auke ta ba." Sady ta turo lips "Dady ne ai ke biyan Albashin ta, don haka dole musaka ta." Anty tace "Nadai gaya muku" ta fita afusace Dariya Sumy Sady da Zubo suka saka "Lalle Matar nan zamusa k'afar wando d'aya da ita." Ruby tace "ni bakuga bana shiga harkar ta ba don gani nake sa'ata ce." Zuby tace "yar Aikin nan munafuka kullum tana Sanye da Hijab sai kace Matar Liman." Sumy tayi tsaki "zan San ya zan ,dole a bamu 'yar Aiki d'aya kuma wan nan yarinyar muke so tana mana wankin k'ana nan kaya, inga Anty sai ta mutu" Sady tace "Good idea tawan." Yaya Babba Ruma tace 'kukam Anyi banzaye ace har sai me Aiki ta wanke muku su bra Anji kunya" ,Ruby tace "haba Anty Ruma Lokacin Abu ayishi." *Bayan wata d'aya* Hansai tad'an Saba da Gidan har D'an K'iba tayi Skin colour d'in ta yafara fitowa sai tayi kyau dama wahalar Gwamma ce ta dafar da ita ,tana zaune agefen kujerar falon Anty tana kallon wani Film BARAUNIYA sai Dariya hansai ke ga Mubarak agefe shima yana taya ta kallon tunda ba School yau weekend. Anty ta fito cikin Shiri oya Hansai tashi Mutafi Hjab dinta ta saka ta dau khalil suka fita.Mubrk na Dan tsalle- tsallen sa don zasu Unguwa ba kowa a Big falo duk suna d'aki bacci. Nan su Anty suka fita harabar Gidan inda d'aukacin Motocin Gidan ke suka doshi motar Anty duk suka shiga ta bata wuta suka fita daga Gidan tun zuwan Hansai sai yau ta Lek'o wajen wata d'aya kenan sai kalle- kalle take ganin yanda garin yayi Mata kyau . Wani Supermarket suka je zuu suka tsaya a harabar kantin suka fito Anty tace "Hansai fito Mana" nan ta fito suka shiga nan k'auyancin Hansai ya Motsa sai Duru-Duru take Anty tace "kifaa nutsu Hansai." kayan aka jidarwa Hansai irin yan kantin nan masu iri d'aya masu siket manya San nan aka d'ibar Mata atamph,da bra su pant da body spray wajen biyar masu kyau akai counting Anty ta biya suka fito nik'i nik'i da kaya. Direct wurin wani tailor d'inta taje ta bada a d'inkawa Hansai nan ya Gwada ta yace 1 week zai gama sai wajen 1 suka dawo gida a gajiye saboda gajiya Anty tace Ashiru ya gyara Mata parking d'in Motar suka shiga. Sumy ce da Sady sai tirk'ar Shoki suke a tsakiyar falon suna kwaikwayar yanda na tv d'in keyi kowacce da jins da tsht , domin vedio din suka saka. Anty ta tab'e baki sukai side dinta. Hansai kuwa d'aya daga cikin kayan da Anty ta sayo mata ne Anty tace ta saka ta daina sa wadanda tazo dasu daga k'auye zo kuga yanda sukai dab'as ajikin Hansai dayake Allah ya wadata ta da hips me d'aukan hankali Anty tace "dole kinasa hijab kici gaba da sawa shine dai-de." Hansai tace "to" nan ta d'auko mata wani k'aramin Hijab d'inta tace duk ta daina sa wad,ancan kan a d'inko Mata Sabbi .Hawayen Dad'i ne suka zubo Mata tace "Anty na gode" tace "no ke Amana ce agareni." Da zumudi ta tashi ta tafi b'angaren su, kande da karime nata hira ta zauna "kuuu! zo kuga kayan da Anty ta sai min" ta yaye musu Hijab tace kunga d'aya ta bud'e Leda tarik'a zaro su wajen kala biyar, San tace kuma akwai d'inkin wasu." Kande tace" Lalle kin cab'a dama nice gun Anty" karime tace "hmm mu kam ba wacce ta tab'a saimana kaya daga Sallah sai Sallah sai kuma kwancen su Sumy." Hansai tace "kunsan kowa da irin kyautar sa." Karime tace "Hansai kin sanme? Hansai tace sai kin fad'a! tace "ina zuwa" nan ta Lek'a kudu da Arewa bata ga kowaba ta dawo.... *Queenmeemi.WordPress.com* *By Queen meemi👑* . [12:16pm, 28/01/2017] 👑Meemi🔸: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣20❣ _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman family's_ ********* "A 'ya'yan Gidan nan wallahi kinga Sumy wuta ce Saboda sa Aikin ta da fad'an ta, Zuby kuma isah Ruby kuma Zuma ce ga zaki da Harbi Anty Ruma kuma" Shiru tayi ganin yanda Kande ke karkarwa Hansai kuma Tai k'asa da kai ad'arare Ta juya Zuby ce tsaye tana kallon su ta saka wani Material me Blue da Pink fuskar nan sai k'yallin Make up take sai tashin kamshi take tace "Lalle karime kinsamu sake kinji jar miya kin Tara su kina Gulmar mu ko? dole nay punishment dinki next bazaki ba." kuka take "kiyi hkr" tafiya ta fara ta kalli Hansai "ke zo ki min Aiki" Jiki na rawa ta mik'e ita kam tsallan kwad'o tasa karime acan waje, itakam Hansai d'akin baki Zuby ta kaita tace ta dad'a gyara shi ta sa Room fresh haka ta fara ko ina sai data goge ya dawo fes sai wajen 4 ta gama taje d'akin su Zuby tace to "Anjima zan bak'o Idan yazo karki bari nai Magana kije kitchen ki had'o Drink da Cup da Cincin kingane" tace "eh Anty ,zan iya tafiya?" "well zaki iya" fita tayi ta tafi Bangaren Anty . Bari mu leka b'angaren Su Gwamma muga wai nar da suke toyawa *MANGALU* kuka Gwamma keyi tace "Amma kuwa Delu kin badani akan bashi shine zaki taran Mutane!" Delu tace "eh na Tara lokacin da kike so na baki har Gida kikaje don biyan buk'atarki Amma don ke dama taurin bashi gareki yau wata d'aya kenan ina son ki bani kink'i, to wallahi yau sekin bayar". Gwamma ta share Hawaye bazan bayar ba, kinjiko,Delu duk abinda zakiyi kiyi." Nan ta koma gidan ,Delu ta bita suka tsaya tsakar gida tace baza fa ta sab'u ba, ki bani kud'i na, uzuri gareni." Ke kika sani Amma wallahi Delu bazan bada ba sauke Mayafi Delu tayi tasha damara tace "yo kinyi Asiri kin Raba Masoya kin had'a gurmi amfasa Auren shine zaki ce haka ko, da komai ya kammala." Jummai dake d'aki ta dafe kirji dama Gwamma ita ta Raba Hansai da Muntari tashi tayi ta fita lokacin Gwamma da Delu sun kaure da fad'a Jummai tace "Subhanallah! ya da abin yara?" Cizo Gwamma ta akaiwa Delu tace "Lalala kika cijen?" Dayake Delu Jibgegiya ce tafi Gwamma girma ta naka ta da k'asa ta hau kan ruwan cikin ta tana duka sai ihu Gwamma take Dije ta fito tana dukan Delu ta baya nan ta hamb'areta. "ki bani kud'ina Idan ba haka ba wallahi sai kin gane ban da kyau" Gwamma data Jigata sai kitan Malam! Malam!! take . Jumma tace "Delu kiyi hkr" Delu tace "ke yimin shiru wallahi Idan bata ban Kud'in nan ba sai na kaita gun 'yan sanda." Adai-dai time d'in Malam ya shigo "Me zan gani haka nan, Delu ta mik'e Gwamma ta Jigata ko Hannu batta iya d'agawa yace Meye haka nan da Girman ku ba yara ba." Delu tace "kudina zata biya ni bashina" yace "Nawane? tace "dubu Goma" ya jin-jina kai a "yanzu da ake wiyar Rayuwa Gwamma kika ciwo wan nan bashin? to ita ku sai kibiya ta." Gwamma ta tashi ta face Hanci wallahi kin daki Kud'in ki Koni ko ke." Delu tace mu zuba D'an Halak ka fasa Jarababbiya afusace ta fita Gwamma ta shige d'aki tana huci Jummai ta fasa dariya tare da cewa "Allah ya kara" ni meemi bace "Ameen" Ga wan nan ba yawa fans Sakamakon hannu na dake ciwo shiisa banyi da yawa ba. *Queenmeemi.WordPress.com* *By Queen meemi* . . [8:33pm, 30/01/2017] Miemee: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣21❣ *JAN 2017* *®NWA* *_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_* *_Sakon Nuna kulawar ku gareni masoyana duk ya iso mun, Nagode da kulawar ku, kuma na samu saukin hannun nawa nagode_* ********* Wajen k'arfe Biyar bak'on Zuby yazo tana d'aki zaune sai fesa kalolin Perfume take masu dad'in k'amshi Ring d'in wayar ta ce ta hau Ruri nan ta D'anyi Murumshi ta D'aga "Hello habiby" daga can ya amsa da yana D'akin bak'i, Ruby dake kwance Rigingine idon nan yayi JaJawur tana Chatin ta Juwo "wow see u Baby, Amma kin had'u sai ina haka?" Zuby tace "fawwz ne yazo" Ruby tace "ok Ki gaidashi" k'was k'was ta fita kamar mai zuwa Gidan Biki tazo ta wuce Hansai na zaune a Big falo tana yankewa Sady farce ,Zuby tace "ke Hansai ki kawo Drink nan da 2 mints" Sady ta d'agawa Zuby hannu tace sai Zubyn mu irin wan nan wanka haka" Zuby ta farfara Ido ya San ranki Part of my Life yazo ai Dole na Gwangwaje" ta tafi tana juyi. K'ara Sady tasa "Lalala kika yanken Hannu!" Mangari ta kaiwa Hansai Fool Girl kawai, ni ina ganin cikin Kande da Karime kamar kin fisu Dama dama ashe kema hakan ce." Hansai kam Raba Ido take "yi hkr Anty" tsaki Sady tasa ta Maida air piece Kunneta ta tashi ta bar gun Hansai kuwa da bak'in ciki ne ya cikata, ta tashi Jiki a Sanyaye ta shiga kitchen ta had'o Drink a Cup da Cincin tayi hanyar D'akin bak'i da sallama ta Shiga taje ta aje Zuby dake zaune suna hira tace "ke Hansai zo nan wazai zuba mai." Juyowa Tai ta d'au cup ta Murda Juice d'in ta tsaya ta mika mai kallonta yayi "thks" kan ya Amsa ta saki ji kake fas! a kas. Hannu tasa abaki na d'imauta Zuby tace "ke wai baki da hankali ne?" ta kai Mata Mari bar nan aguje ta fita Zuby gun sa "Sorry my Fwwz" nan ta Goge mai yace ba damuwa. fawwz kenan Dan kwalisa sai basar wa yake ita kuma hakan da yake sai yake birgeta. Hansai kuwa gurin Anty taje tai Mata Aikace Aikace San nan ta dawo falo ta d'au khalil da mubrk suka tafi can harabar Gidan taanai musu wasa Sam tama Manta da wasu Zuby k'arfe Shida dai-dai Motar Dady ke shiga harabar Gidan asan nan lokacin kuma saurayin Zuby suka fito zai tafi. Da gudu Mubarak yayi gun sa "Oyoyo Dady" Khalil dake Hannun Hansai sai ihu yake yana San zuwa Alama yayi da Hansai ta kaishi ,da sauri taje bakin Motar Dady ya karb'eshi ya D'an kalleta a fakaice. Jikin Zuby ne ke rawa Ganin Dady da tayi Domin ta San kwanan zan-cen da D'an sauri fwwz yaje ya gaida Dady ba yabo ba fallasa ya amsa ya had'e Rai nan yayi wa Zuby Sallama ya ja Motar sa ya fita daga Gidan da gudu tayi cikin gidan. Cike da b'acin Rai ya mik'awa Hansai yaron ya shiga cikin Gidan duk da Part nasa bata nan ake bi ba Amma so yake ya Sab'arwa Zuby da k'araji ya Shiga "Ke Zubaida! Zubaida! Tana daki Jiki na rawa mama d'ake daki ta fito haka Umma sai Anty daga karshe sun San anyi lefi inde Dady akaji yana kiran nan.Zuby ta fito yace ke" wace irin Yarinya ce? ba na hanakiw tsayawa da wan nan Yaron ba? ko so kike ubansa ya rena ni to wallahi ki shiga taitayinki ba wan nan bama bance ba yarinyar da ta isa ta tsaya da saurayi ba sai kun gama Degree. Nan su Sady ma duk suka fito jiki na rawa yaci gaba bakwa koyi da Rumasa'u abinda nace Shi take yi yanzu ba gashi saura watanni ta gama ba to wallahi zan muku fata- fata yanda nake Babba agarin nan, ba kowa nake so yazo Gunku ba sai D'an wane da wane kuna jina?" Suka "eh" San nan ya kalli Mama da Umma yace Last warning da zaku bar wata Yarinya ta tsaya da Saurayi" ran Mama daya b'aci ta tashi ta bar gun Anty rabia tace "haba Alhaji wan nan da ba" ..D'aga Mata hannu yayi ya fita . Zuby kuwa d'akin Mama ta shiga ta fad'a Jikinta tana kuka "Mama Gaskiya nikam ina son fawwz, shima fa Dad nasa me kud'i ne." Mama tace "Zuby ki bi Komi a sannu ki dakatar da zuwan sa atoh kin San Dad Bai iya fad'a ba agaban kowa yi zai yi idan Ransa ya b'aci". Ruma ta shigo tace "Zuby juyo ki kalleni, kin san dai ni nice babba anan Gidan Amma kina gani ina bin abinda Dad yace ki kiyaye" Sady ta shiga "oh Zuby ke meye yanda kike 'yar Manya ace kina wani son fwwz ,kin san de Baban sa yaron Dad ne nikam sai na zaba" Zuby ta bige bakinta. "Bansa dake ba yi mun shiru" nan ta juya ta cigaba da kuka. AD'akin Umma kuwa Ruby ce ke tsaye tana Jijjiga Umma nifa na Rasa gane Ra'yin Dady duk wanda yace yana sammu sayya ce Bai masa ba, haba" Sumy tace "atoh" Umma tace "kudai kubi a sannu musammm ke Sumy mai rawar kai" tace "kai umma." Anty kuwa dake ta tunani tace tabdi gaskiya Dad yana da daukan dala sai kace wanda zai jika Yaran yasha Sai kace wasu hurul'ain saboda kyau tsaki tayi. lokacin Hansai ta shigo ta mik'o khalil tace "Yawwa zo." Zaunawa tayi tace to "Anty" nan ta zauna tace abinda nake so dake tun lokacin da aka kawo ki Allah ya Doran tausayin ki Iamatsayin kanwa nake d'aukanki yanzu kinga watanki 2 agidan Nan inaso ki dada nutsuwa ki bi duk wata Dokar gidan nan kinga su Sumy ba kunya garesu ba tunda sukaji Dad yace duk wace yar,Aiki zasu iya sata Aiki ina sane nasan Salon yanda suke saku Aiki na fitar hankali Musamman ke tunda suna ganin kina da tsafta kuma kin fi su kande wayewa to ki dada kiyayewa kinji." Hansai tace "to Anty tace Ngd Anty ,bari naje d'aki" tunda ta fita take kuka sakamakon jin dadin Yanda Anty ke kyautata Mata, tuno Malam da inna da tai sai kuma Gwarzon ta Muntari ko ina yake Allahu ya Alam, sai kuma can ta tuno ita fa ba'asan iyayen ta ba, da sauri ta kori wan nan tace Malam da inna sune Murumshi tayi ta shiga side nasu. ji tayi su Kande da Karime na Gulma ta zauna tace "kunga ku daina Gulmar su babu kyau barin ke Karime kin manta wuyar da kika sha ran na." Kande tace "hakane fa" nan sukayi shiru. Hansai kuwa akwatin ta ta bud'e tasa hannun ta nan ta zaro wata Leda ta rasa ta meye Lokacin duk su Karime sun fita wanke -wanken dare jiki na rawa ta bud'e ledar kud'i ne a ninke a ciki sai farar takada da hoto ahankali ta juya Hoton Ganin fuskar Muntari tayi nan tasa Murumshi ta tuno Lokacin da zai tafi birni ya bata tsai ta k'urawa hoton Ido ta tuno Lokacin dayaje Birni ni ya d'auka da Sallah sai Kud'in data irga taga dubu biyu ne Hawaye ne suka subo Mata ta warware wasik'ar tun Lokacin da da k'anin sa ya kawo Mata, sai yau wajeen Shekara D'aya da wata biyar Allah ya nifeta da Bud'ewa nan ta bud'e ta fara karantawa kamar haka: *By Queen meemi*👑 *Queenmeemi.WordPress.com* [3:28pm, 31/01/2017] Miemee: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣22❣ *JAN 2016* *®NWA* _Sadaukarwa ce ga Basher Usman Family's_ ********** Bud'e wasikar tayi tafara karantawa kamar haka: _Hansai soyayyarki bazata taba Gushewa a Raina ba, kin zamo tamkar Jinin Jikina, wallahi Birnin da zani babu wata 'yar Birni da zata Rud'eni na manta dake,ina sonki Muyi hkr da Rabamu da akai domin Rabuwar tamu ta zamo Sanadin tafiya na Birni don Sanun Ilmi,San nan nasan ab'angaren ki ina ji A Jikina kema zaki samu Ilmin komai rintsi Ina tare dake.Karki manta dani ina Ji A Jikina ke tawa ce na d'au wan nan Alk'awarin ,San nan Hansai Masoyiyata ina so ki Jajirce kicigaba da neman Ilmi na Addinin Dana Bokon idan Allah ya sake had'amu dake zanyi Alfahari dake,duk wahalar da Gwamma ke baki ki jure da sannu zata Girbi abinda tayi,Hansai ina sonki sosai d'an digon Hawaye tagani adai-dai gun, nan tashafa gun bisssalam Hansai Allah ya sadamu da Alkairin sa I luv u & miss u so much._ Kuka mai tsuma Zuciya tayi tayi ta sa wasik'ar ahannunta ta duk'un-kune ta maida A kwati, kud'in kuma ta rik'e a Hannu. Iya ta shigo Aa "yata Hansai Meyasa kike kuka?". Nan ta share Iya na tuno su Inna ne, tace Eyya sai hk'r kowa da yanda Rayuwar sa Allah ya tsara sai hk'r ai nan da watanni zaki gansu d'an Murmushi tayi tace Gaskiya ne . Washegari Hansai taje ta kaiwa Anty kud'in tana zaune ta shiga tace "Yawwa Hansai Jeki min blandin kayan miya" da sauri taje tayi ta dawo ta zauna ta mik'awa Anty kud'in tace "Anty gashi ki aje min agunki tun agidane da aka ban na manta sai yau" tace "ba damuwa sai ki sayi kayan Makeup dasu ko?" Hansai tayi dariya Anty wane kwalliya? "Tace haba Aidole kinayi gashi Allah yasa ked'in Kyakkyawa ce" tace to "Anty." kamar ance ta fita taga Sumy zaune kan Kujera ga Kande da Karime duk a durk'ushe Sumy tace "kema zo nan!" Asanyaye taje ta zauna Sumy ta fara Magana inaso ku sani daga yau babu wacce zata saka kayan Gida sai Uniform, kun gane nan ta zaro su guda Uku Riga da Wando Rigar iya gwiwa tace su zasuna sawa kullum ta kalli Hansai "banso ki maka Hijab kin gane Aiki kika zo Iyayi ba,ko me za kalla Jikin ki! atoh kuje ko wacce tasa ina nan kuzo." Haka duk suka d'auka suka tafi Shigar su D'aki Hansai tace nikam kayan sun Birgeni Karime tace "tab! yanzu shikenan Mundena saka kayan mu!? Kande tasa Dariya kide zauna Surutu Cas kayan sukayiwa Hansai kyau gashi sun D'an kamata daga kasa kamar ba ita ba,shape dinta ya fito daram tsakiyan cikin ta ya d'ame ga kirjinta har dan fitowa yayi, dogon wuyanta ya fito ya dace da beautiful face d'in, tsaki tayi "jifa yanda kayan nan sukayi mini? ni kam dama tabarni Nasa Hijab d'ina." Karime tace "kai Hansai duk yafi miki kyau"Kande tace "eh wallahi" Karime tace "duk gayunsu wallahi kin fisu kyau" Kande tace "eh dande tana rufe Jiki ne." Nan suka fita Sumy na zaune tana kad'a k'afa suka zo suka tsaya tayi Dariya "ko kufa yanzu kuka dace da 'yan Aiki Musamm ke Hansai kinga Anty ta tsaya miki har Super Holland kike kwancen ta to Daga yau ta kau, oya kowacce ta tafi nata guri nan suka juya." Bin Hansai da kallo tayi tab! dama haka yarinyar nan take! dole ta rufe Jiki d'an tsaki tayi ta mike. *MANGALU* 'Yan Sanda ne ak'ofar Gidan Malam, Dije da sauri ta shiga ta kaiwa Gwamma tsogwami nan ta shige d'aki ta gark'ame Jiki na rawa Fad'an- Fad'an Delu tazo tace bari na shiga Gidan. Tashiga tana k'wala Sallama Jummai ta fito Delu tace ina wan nan Muguwar ta fito wallahi yau ko ta ban kud'i ko atafi da ita." Daga can d'aki tace "bazan fito ba Wallh" Delu tace "yo ai bafin k'arfin kikaiba nan ta Danna K'ofar nan kwa ta bud'u ta Janyo Gwamma tace "kudi ko tafiya" tace "ki bari Mudi zai yimin aike." "Ban yarda ba." Gwamma tace "ke bafa tsoronki nake ki ba wallahi bazan ma bayar ba" a fusace Delu ta fita ta Sanarwa 'yan Sandan nan suka Shiga soron Gidan sukace Gwamma ta fito dak'yar ta fito tana yafa Mayafi suka tasa k'eyar ta har waje yara ne dam! a tsaye nan ta tsaya tana huci tace "Delu munsa k'afar wando d'aya dake." "Tink'is -Tunk'is aka tafi da ita D'uu yara na binta.Jummai kuwa sai tafa Hannu take "oh! su Gwamma an fara tab'ab'arewa." Malam ya shigo Jin Labari da takaici yake tambayar Jummai ta sanar mai yanda akai yace "Al amarin Gwamma Sam ba Allah aciki, ta wulak'anta Rayuwar ta kuma wallahi ba inda zani Sanda sukai niya sa sako ta." Jummai tace "Allah ya kyauta Malam yace "nikwa yau watan Hansai nawa?" tace "ina Kin Uku Malm" yace "Allah sarki Hansai muna Kewarta" Jummai tace "nima haka." *ABUJA* *Bayan wata d'aya* Yau ya kama Sunday duk 'yan Matan na Gida suna zaune kowacce da abinda take Zuby ta kira hansai da yake Anty ta sai Mata wata Aitle shiisa duk wacce ke da aiki kir zata kira ta. Hansai tazo gani Zuby ta Aiketa ta had'o Mata drink ta tashi ta tafi ta d'auko Jitayi an watso Mata Bra Sady ce ke Jin wak'a tace "Jeki wanken" ta tashi ta tafi sai wash take Saboda tunda ta tashi suke sakata Aiki har ta gaji Allah yaso ma Aikin Anty bame yawa bane, dawuri take gamawa. Tas taje ta wanke ta shanya k'aryar ta ta tashi har sai Sun gama bushewa San nan ta deb'e sai wajen 2 ta dawo rik'e da su,ta shiga wangamemen d'akin nasu duk Sunyi wanka Sun fece Sumy ta kalleta "ke anjima zaki rakani Shopping" Ruma tace "oh no! ku kam wai mesa kuka takurawa yarinyar nan komai ita duk baga su Karime ba." Sady tace tab! wad'an nan k'azaman Ji Uniform din su kullum datti sai Dana sa Iya ta sasu suke wankewa kullum , kinga kuwa ita kullum nata agoge shiisa nafi san Aikin ta Ruby data k'urawa Hansai Ido tace "Gata kuwa so beautiful" Zuby tace "LOL" . Sumy tace "nikam Anty Ruma Dady na nan? tace "eh mana yana garden" tace "nikam kayan make up D'ina ya k'are da perpums gashi duk nayi searchin new a Goggle" Sady tace !tab ai kuwa nima hakan." Sumy tace "Nifa bansan gasa Sady tace k'afata k'afar ki" Sumy ta "kalli Hansai dake tsuggune ta Sunkwi dakai ke ki fa shirya zaki rik'en kaya". Hansai tace "to Anty Amma da wad'an nan kayan zani ? Dariya suka fasa su duka, Sumy tace "to da dame zaki? meye Amfanin ki ba 'yar Aiki bace ke? dole ki bada Alama da hakan." Anty Ruma kam akwai Sauk'in kai tace "no baza ai haka ba, itama fa 'yar Adam ce taje kawai ta saka kaya masu kyau ,ke ba abin kunya bane aagareki ta tafi da uniform na aiki." Sumy tace "kai Anty Ruma!" ta kalli Hansai "oya Jeki wanka kisa kaya me kyau." Hansai tace "to" ta tashi a salub'e ta fita D'an sauri take Ojuku ya tsareta "pls baby Do you love me? Hansai ta harare shi "ni ka matsa meye ruwa na dakai, ka takuramin" Yi hank'uri Baby me kyau" wucewa tayi yabi bayan ta da kallo yana mai wani had'e Ido, cigaba da Goge tiles d'in yayi yana wak'a baby love me ! love me." Sumy da suka fito zasuyi part din Dady ta wullawa Ojuku key "pls ka wanken Motata saboda anjima zani Shopping" yace "Okay Maddam" Look ban. Hanaka cewa Maddam din nan ba?" yace "Sorry Hajiya" tsaki tayi Sady tace "ke komai fad'a" tace "nayi." Part din Dady suka Shiga Sunkai tsakiya sukaga Anty tana magama "pls Dady's boys a D'aukarwa Mubarak me Lesson" yace "ba komi Amaryata" Sady tace "Aikin kenan komai boys, Don taga su Mama sun d'aga Mata legs" Da sallama suka shiga Sady da yake yar gaban Goshin sa ce da saury taje kusa dashi ta zauna "Dadyna" yace "Uwata ya dai?" Sumy tace "Dady kayan Makeup d'ina ya k'are da Perpums" yace "kai Yaran nan bakwa Rabo da kwalliya Last 2 weeks na Baku fa" Sady ta Marairaice Don Allah Dady yace "oke Don worry" ya tashi ya bud'e kit ya curo bandir ya bawa kowa 20k suka had'a baki "Allah ya K'ara Budi Dady." Suka fita nan ya juya yace "Maman Boys Insha Allahu Next week zai fara zuwa tace "Ngd Dadyn kids" K'arfe 5 dai-de Hansai tagama shiryawa tasaka atamph da Mayafinta black da Anty ta bata Sumy ta fito tace "Sady wai ba zaki sayo ba?" Sady tace "ke ni fa dama ina dasu Sumy tace "Amma bakiyi ba shine kikaje kika ragen yawan.samu" dariya tasa D'aukan Jakar ta tayi ta sak'ale a Hannu tasaka after Dress pink Dubai products me adon Blue sai Mayafinta Pink shima me Adon blue ta bazo Gashi gefe tayi linin Mayafin abayar Sumy tayi kyau sosai ga Jakarta blue da flat Shoe blue nan ta fita ta kalli Hansai taga ta zambada Red Jambaki ba Lefi tayi kyau. Tace "ke zo nan! Hansai taje "oya Goge Jambakin nan na bakin ki, Nasa Jambaki kema kinsa" da sauri ta Goge suka fita. Ojuku sai dad'a k'alk'alar Motar yake ya k'urawa Hansai Ido kamar maye Harara ta buga mai ya washe baki nan ta bud'e baya ta zauna. Sumy tace "ke waye driva ki? fito dawo nan, Mtsww komai aka had'a da Villager saiya ci Kara." A hankali ta fito ta bud'e Gaban a d'arare ta zauna Lokacin har Maigadi ya bud'e Get,din da Gudu ta ja Motar suka fita..... *By Queen Meem👑i* *Queenmeemi.WordPress.com* [5:14pm, 01/02/2017] Miemee: . . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣23❣ *JAN 2017* *®NWA* *_Sadaukarwa ce ga Basheer Usman family's_* ********** Cikin mintuna suka je Supermarket d'in Parking Motar tayi suka fita Hansai na binta abaya kanta a sama ta shiga kantin Basket tasa Hansai ta d'auka nan tayi wajen Perfumes ta dunga zab'ar irin Wanda take amfani dasu Hansai sai binta take abayaa tana sakawa a Basket d'in haka b'angaren kayan Makeup shima ta saya sun gama ta juyo Hansai tai Karo da wani Saurayi ta d'aga Manyan idan ta ta kalleshi "ke wane shashanci ne wace iriyar Yarinya ce bakya kallon Gabanki?" "Kayi hkr don Allah" cewar Hansai Sumy ta juyo "Sorry fa 'yar k'auye ce shiisa" Saurayin ya tab'e baki "no wonder." Hansai kam kamar ta kurma ihu haka suka je gurin Counting ta biya suka tafi tun data shiga Motar Sumy ke Mata balai' har sukaje wani D'an wajen Shan iccream sumy ta fita tana waya gani nan fa na shigo" haka ta tsaya tana ta yatsina can sai ga Saurayin ya tawo yaci Swags dama duk Samarin Sumy Swag ne tafi San irin su,acewarta sune manyan yara, ya tawo yace "my Sumy" tace "my Nazi kaga nan yafi safe" suka sauna kan wasu kujeru yace "wai meya sa Dady naku baya barin aje Gidan ku gurin ku?" tace "Dady karatu yake so muyi kuma ba kowane mutum yakeso mukula ba" Nazi yace well Nikam nasan zan samu guri" tace "sosai my nazi" kurb'ar leman dake gabansa yayi "yanda nake Sanki ai bazan iya barin ki har na 2 days ban ganki ba." D'an Murmushi tayi tace "Allah? yace "yeah of course" wayar ta ta d'auka ta kira Hansai "to 'yar k'wama kawon bag d'ina" ta kashe Hansai da tai tsuru- tsuru Amota ta fita D'auke da Jakar Sumyn, tunda ta doshi gun Nazi ke kallonta tayi mai kyau nan Sumy tace "me kake kalla?" Nazi yace "Sorry wan nan fa?" A Lokacin Hansai ta mik'a Mata Jakar, harara ta bata "oya tafi can ki zauna kin wani je Mota kin k'wame" ,ta juyo ta kalli Nazi "yar Aiki ce". Yace "kai Amma fa tana da kyau Sam bata dace da Aiki ba, wan nan in ta samu wanka za ai Hot Baby." Wani kallo tai mai "shut up nazi, ya agabana kana yaban 'yar Aikina haba" "Sorry tawan kin sani ni bana Rufi". Tabbas tasan halin sa ,nan tace "ok Amma karka kuma, ai saika sa ta raina ni." *NAZI* wani Matashin Saurayi ne mai tashen Money baban sa Alhaji wada shahararren D'an siyaysa ne Wanda ake ji dashi har yamafi baban su Sumy Naira ,Nazir su biyu ne a gurin iyayen su daga Shi sai k'anwar sa D'an gata ne nak'in K'ara wa ga Fafa baya 6 Month da mota ake canja mai wata duk abonkasa 'yan Swags ne akwai Shi a Kwai San Mata duk wacce yagani sayya yaba, sun had'u da Sumy ne A Uni Abuja yana Lavel 4 ita tana 2 nan suka d'inke suka fara Soyayya Sanin Dady Bai barin su zance yasa suke bi park -park duk Lokacin da suke san ganin Juna ko su had'u a School wan nan kenan. Hansai kuwa duk ta gaji Manyan yara ne kawai ke giftawa sai binsu da kallo take,ta tuno ak'auye yanda batai aure ba akace tayi girma sai gashi abirni yar yarinya ce akan yan matan birnin,bacci ne ya d'auke ta Jitai an d'aka Mata duka ta mik'e Sumy ce da Nazi tsaye tace "kin share baki kina bacci Useless kawai Hansai taji zafin kalmar don ta San Ma'anarta (dadin karatu kenan) kallo Nazi yabi bayan Hansai dashi yana k'issima abubuwa da dama. Nan sukai Sallama da Sumy ya shiga Motar sa kiran benz ya fita itama suka shigaa suka tafi sai 6:30 sukaje Lokacin har Dady ya dawo ad'arare Sumy ta shiga gidan, Nik'i Nik'i da kaya Hansai ta bita d'akin su ta Shiga ta aje ta fita. Zubewa Sumy tayi a Aininhin d'akin ta tana Murmushi domin tana ganin ta samowa kanta mafita. Itakam Hansai tun shigarta Anty ta tsare ta sai yanzu? Hansai tace wallahi munje wajaje ne". Anty tace Allah ya kyauta wallahi bansan janki yawo da suke don sunga kinada juriya." Wani irin bacci takeji tun karfe 7 na safe take galaulawa nan ta koma side nasu na 'yan aiki, tayi Alwala tayi salllahr magrb da yake an kira kwanciya tayi sai bacci , kamar daga sama taji Ana tashin ta ta Bud'e Ido Sady ce tsaye akanta tace "ke tashi ki dafan indomie, kamar ta kurma ihu ta tashi taje main kitchen din gidan tana had'awa sai Magagin bacci take yi . Ji tayi an cakumeta ta kurma ihu ta juya da sauri Ojuku ne ke ta murmushi "my love sorry na baki soro ko" hararar sa tayi "ni ka tafi kaban waje me kake har yanzu a shashen nan kuma ni ka daina tabani saboda ni addinina yayi hani", Allah idan baka fita ba zan maka ihu dogare Hannu yayi ta bud'e baki zatai K'ara da Sauri yayi baya . Haka ta yanka Attaruhu k'anana da Albasa ta d'ora ruwa tab'are indomie 2 ta zuba magin ciki ta K'ara Rayco daya tasaka curry kad'an da Dan mai ta rufe ta tsaya jiran ta dahu, tunda ta tab'a dafawa Sady indomie taji Dad'i shikenan take Uzzura Mata duk dare sai ta dafa Mata. 9:30 ta gama taje can part din su Sady ta shiga ta tsugunna duk suna falon suna kallo dayake da dare kowa part d'in mahaifiyar sa yake tafiya da yake d'akunan baccin su anan yake, da rana ne suke da wangamen dakin su a big falo to nan suke haduwa 'yan matan gidan. Mik'a mata tayi ta k'arb'a "Weldone" takai Loma har Hansai takai k'ofa Sady tace" ke wai waaya koya miki dafuwar indomie haka"? tace Anty ce ta koyan" Mama ta juyo "lalle kuwa",San nan ta kalli Sady "ke yanzu girkin 'yar Aikin kike ci ke ko, bakya ganin k'azantar da suke?" Sady tace "Banda Hansai tana da tsafta har so biyu take wanka fa shiisa na ke bata wasu abubuwan tana min",Mama ta kalli "Hansai data tsaya "ko wan nan ma Antyn ce tace kina wanka biyun ?" "Eh itace" "Lalle jeki kawai" ahankali ta fita Sady ta kalli Mama tace Mama ya kamata kema kina saka kande tana tsafta kinga ke kika d'auko ta" Mama tace "'Yata ce da zance sai tayi tsafta! nide taimin Aiki wan nan kuma jikinta tunda ba kuwa shashena take ba k'ark'ari taimin moping da wanke -wanke ta fita" Sady tace "Mama bari naje na hau computer inada Assignment" tace "ok" ta fita. *Queen meemi* *Queenmeemi.WordPress.com* . . [2:18pm, 03/02/2017] Nene: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣24❣ *JAN 2017* ®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION _*Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's*_ *Wan nan page naki ne ANTY MAIJIDDA MUSA Tnz 4 d care And support* ************* Hakan rayuwa tayi ta tafiya akwa na Atashi yau watan Hansai Goma agidan ta dad'a kilewa tayi fes Sam bakace itace Hansan Gwamma ba fatar ta tayi kyau da yake tana sa mai masu kyau wan nan kuwa duk Aikin Anty ne don ta d'auketa takmar kanwa,ga kanta ma ya dada tsawo saboda samun gyara da take kai bakace yar aiki bace ta saba da wahalar da su Sumy ke bata,cikin kankanin lokacin ta iya abubuwa da dama. Yau ma da take zaune a bayan d'akin su tana kuka sakamakon tafiyar su Kande duk anzo D'aukar su Amma ita shiru yau satin su d'aya ke nan ji tayi Anty na kiranta ta mik'e ta fita Anty tace "Hansai yau munyi waya da lami tana tafe gobe sai ki shirya" kamar tayi tsintsuwa tace "ngd" Wayyo Dadi nan ta tafi daki da gudu ta duba akwatin ta taga wayar da tasaiwa baba 'yar dubu uku tana nan tun kud'in da Anty ta bata haka ta aje shi gefe d'aya. Wani gefen kuma tana Jimamin tafiya saboda Gwamma. Sha Tara ta Arxiki Anty ta had'a Mata ,da atampha da takalmi dasu shadda. Washegari da sassafe Ashiru ya d'auketa tana kukan missn din Mubrk da khalil Anty dake jadda Mata sati biyu kawai zatayi Hansai tace to Anty nan Motar taja suka dau Hanyar kano tafiya yankin Azaba tun Hansai na kalle -kalle har ta kwanta bacci sai wajen azahar sukaje gidan Mama. Mama ta Rungume Hansai tace "Lalle Hansai Kece haka kamar bake ba?" ta sunkwi dakai "kekam Abuja ta karb'eki" nan Ashiru yaci abinci ya koshi yayi sallah San nan ya koma har Mama ta bashi kayan kadi ya kaiwa Anty Rabi ita kam Hansai bayan tayi sallah ta huta sai bacci don ta san sai La asar Lami zata k'araso ilai kuwa sai la asar d'in tazo. itama ta yaba canjawar Hansai tace "lalle kinyi kyan gani." Mama tace ice dai zaki dawo da ita don nasan halin ku duk 'yar Aikin da zataa tafi bata dawo wa" Hansai tai caraf ai nikam zan dawo Mama".tace aike kam kin zama tamu sai wajen 4 suka tafi da k'arfe shida dede sukaje suka sauka atasha . Lami tace hansai ki d'au Jakar mana" Hansai tace "Aa zan rik'e" Lami tai dariya "Lalle birni ke kam ya karbe ki ,da Dane ai ka zaki dora" suna tafe suna hira sai kallon Hansai ake har sukaje k'ofar gidan su. Malam yana Alwala Hansai tayi magana ya d'ago "Aa Hansai Masha Allah" nan suka shiga ita da Lami Jummai na tuk'in tuwo Hansai ta Rungume ta ta baya ta juyo 'Lalla wa zan gani kai lalle mutan Abuja Hansai kin canja' murmushi tayi tace ina Abdullahi Jummai tace yana can waje dai dai lokacin Malam ya shigo Lami ta zaro dubu ashirin tace ga kidin aikin ta ni na dauki kudin lada na nan da sati 2 zan zo na maidata ta yanzu sauri nake ta fita. Malam yace "Allah abin godia Jummai kalli yanda Hansai ta dawo fes da ita" Jummai tace "wallahi kuwa kamar ba itaba." kudin ya irga yace "wan nan sai a aje maki." Gwamma dake band'caki ta fito da sauri ta fisge kud'in "lalle nayi Mata hanyar Aiki anga kud'i nan ta d'au dubu goma "bashin da ake bina zan kaiwa 'yan sanda" ta soke dubu biyar ta mik'a musu "ga wan nan tace ya isheku" Malam yace "ke kam har yanzu baki saduda ba duk kwanan da kikai a guron 'yan sanda besa kin hankaltaba" "Malam ka k'yale ni haba Yau wajen wata shida Ana kawo min farauta zuwana gun yan sanda uku duk dan bashi yanzu ga kud'i dole nai wadak'a" da sauri ta shige daki Hansai ta tab'e baki suka shiga daki. Da saafe ta fiddo taarabar su ta basu har yar Gwamma Dija ta D'auko wayar baba ta bashi yayi murna tace baba nima kaga tawa Anty ta ban inna kuma inna kuma samu zan saya mata." Gwamma tace lalle hardasu waya tace dole ke ki zauna yanzu Dije ce zata wlh itama ta samon Arzikin bawanda yace Mata komai,haka da yamma taje gidajen da take shiga suka gaisa duk inda taje sai an yaba ta har wajen da suke zama da muntari taje tasha kuma agun san nan ta tafi.taji dad'in zaman domin Gwamma bata kulata da sun hadu sai zagi ita kam Hansai daga gaisauwa bata fita don Jummai tace kar tai abinda zai ja ta dake ta . *Abuja* Acan abuja kuwa tun bayan tafiyar Hansai su Sumy duk wani Abu bassai dama Hansai ke gyara d'akin big falo yanzu kuwa kaca -kaca bra din su nan sun Tara hili sai ta dawo ace warasu ta wanke ga su kande basu dawo ba kullum sai de su fesa wanka asheka uwar makeup atafi schools. B'angaren Anty kuwa kewar Hansai ya dameta ga kullum Mubrk ina Hansai sai de Anty ta lallase shi. Bayan kwana 2 Ruby ke tsaye tana tunani ta dago tace "Ruma agasky idan ku zaki jure nikam bazan iya ba wallahi ba abinda ke burgeni sai aure don bakuga frriend dina last week tayi Aure nikam ko a haliita ina bukatar Aure." Ruma ta d'ago ta zare Glass dake fuskar ta tace "Ruby kina son bata ran Dady ko? ya fiso sai mun gama degree San nan 'ya'yan manya Amma ke fa Naga Nuradden ke San ki tabbas kin San Dady ma yafi Baban sa Naira, hakan Shi Aikin sa ba mai tsoka bane" Ruby tace "nifa ba ruwa na da hakan "ki kalla shekarata 24 ai ina bukata" Ruma tace haka Amma ai na girmeki ko?" Ruby tace "nifa dake ba d'aya ba atoh dole zan gwada sa a ta ko Allah ya sa na dace don Nuradden sona yake da aure. Ruma tace Allah yasa mu dace" Tace Ameen nan tafita tayi wajen Ummin ta don samun mafita. *By Queen meemi* *Queenmeemi.WordPress.com* . [2:18pm, 03/02/2017] Nene: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣25❣ *JAN 2017* ®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION *_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_* *ANTY SIS sakon gaisuwa gareki ,da Masoyan Rabuwa ce Sanadi na Tnz 4 ur love & support* *********** Shigar Ruby d'akin ta tarar da Umma na waya ta zauna umma ta d'ago "wai ina Sumy ne? Ruby tace "ta tafi Birthday d'in frnd nata" Umma tace "Okey Motata tad'auka ko?" Ruby tace "eh" tace na hana ta d'aukar mun, kome ta ta take? zata zo ta samen ne." Ruby tayi Jigum Umma tace "meye fa." Sunkuyar da kai tayi "Umma Nuradeen ne ya damu yana so Magaba ta su shiga cikin maganar mu wai da Aure yake Sona." Umma tace "tab! ke kam kin d'auko Dala ba Gammo kina ganin Ruma Masters take yanzu Amma ke har yanzu ko gama Degree baki ba" tace umma Carry Over nake ta samu fa"! tace 'Allah ya kyuta nikam ba ruwana a zancen sakkowa tayi Mama me zance mai? tace kice ba yanzu zaki Aure ba, tashi tayi ta fita tana Hawaye." Wayar Nuradden ta d'auka tayi mai waya ya d'auka "My life" tace "Naam" yace "ya Maganar mu" tace "Dady baya gida sai ya dawo anjima Zan Maganar yace ok I'm waiting suka akashe a tare. Ruf da ciki tayi ta rufe ido har ta fara sleep kamar 10mints Zuby ta shiga tace "sis kizo inji Dady" tashi tayi tace "ya dawo?" Tace "Eh Man kede kizo" Suka fita can falon sa Sumy na gefen sa da Sady Sumy suka zauna ya D'ago "wato ku bakwa ji ko?" Ya kalli Zuby "ke ran nan na kori wani ko" yanzu Sumy tazo min da Maganar Wanda ke santa to na yarje muku zance Amma sai nayi Screening" Ya Kalli Ruby "ke wake sanki?" tace "Nuradden ne" yace "waye uban sa anan?" tace ba nan yake ba D'an kano ne Aiki de yake Anan Abuja. Kallonta yayi yace "ki rabu dashi meyaci meya baki, duk daular Dana Baku in kinje balalle ki samu ba."kuka tasa wlah Dady yana da kirki" kallon Zuby yayi "yace ke dama na yanke Magana kar yaron nan ya kuma zuwa saboda bama jetuwa da Ubansa, kuma akasa na yake don haka ki Rabu dashi ,sai ke Sumy D'an Alhaji Wada na yarje miki ya dinga zuwa." ya kalli Sady "kefa uwata?" nan tace "ni Dady Banda kowa" yace "to akula da karatu, ku tashi ku tafi" sanyaye suka mik'e. Ruby da Zuby kam kuka suke Zuby ta zube afalo "nikam bazan iya Rabuwa da Fawwz ba, I can do without him." Sumy tace "Sorry sis kiyi ta Addua" Sady tace "nikam har now banga choice d'ina ba" Ruby tace "duk naku mai sauk'i ne nikam Banda tacewa zanbawa Nuradden hkr kawai. Sumy ta dau phone dinta tana latso kiran Nazi ta sanar mai ya fara zuwa ko yaushe. *Mangalu* kwanci tashi ba wuya a wurin Allah Hansai tayi Sati biyu, yau ta tashi sai wankin tafiya take sai yamma ta gama taje ta siyi kayan tsaraba ta dawo. Washegari da safe ta shirya da wuri K'arfe takwas Gwamma ta fito da Dije ta shirya Gwamma tace "ke Hansai fa ba zaki koma ba, wlh Dije ce zata amatsayin ki." Jummai tace "wata Sabuwa haba ke kuwa?" Gwamma tace "ke rufen baki bansa dake ba, k'arfe goma Lami tazo ta tarar da husuma Gwamma tace "Lami da Dije zaki koma Hansai ta zauna." kuka sosai Hansai keyi domin tasan da biyu Gwamma ta ce hakan sallamar Malam ce ta katse hayagagar Gwamma yace "meyafaru?" Jummai ta gaya mai yace "Gwamma hawainiyar ki ta kiyayi rama ta, idan ba haka ba wallah zan d'au Mummunan mataki akanki" ya kalli Lami yace "ki,tafi da ita Allah ya kiyaye hanya" Hansai tace "baba zamuna gaisawa ta waya" yace "Yawwa Hansai ai naji dadin wayar na gaisa da Mutane da muke kasuwanci da." Nan Lami tayi gaba Hansai bi bayan ta.Dije ihu tasa domin k'auyen gasar kai yara aiki ake Malam ya daka Mata tsawa ta shige daki. Yau kwana Hansai 2 da dawo wa Abuja inda ta hau hidima da su Sumy Su kande ma duk sun dawo sati d'aya da dawowar ta Hansai taje Anty a d'aki tace "don Allah Anty taimako nakeso da kudin Aikina inaso zan koma Makarnta dashi sai Ana biya da kudin Aikin. Dariya Anty tasa tace "ai duk Makarantar nan ta kudi ce ovar yanzu idan nace Alhaji ya sakaki wata jarabar ce Amma mai lesson din Mubarak idan yazo zan mai Magana sai tmyana koya miki har kisamu kiyi waec" Dadi ne ya ishi Hansai tace ngd" Anty tace kudin Aikin kuma yana nan da k'arfin jiki ta tashi tana mai godia ga Allah tabbs duk wahalar da su Sumy ke bata tasan zuwan ta ABuja Alkari ne agare ta ko wani Abu dama da sana dinsa. *By Queen meemi* *Queenmeemi.WordPress.com* [4:03pm, 11/02/2017] Nene: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣26❣ *JAN 2017* _Sadaukarwa Ce Ga Basheer Usman Family's_ *_Alhamdlh Masha Allah ,komai yayi Normal Ngd da kulawa Fans ina tare daku akoda yaushe_* Tunda Hansai ta fara zama Lesson din Uncle Abba ya zamana ta dage dalili Mutumin nada kirki farkon fara zuwanta su Sumy suka hana acewarsu Aiki tazo ba karatu ba saida Anty ta bud'awa idonta toka tace "ai ni na d'auko ta, don haka ba ruwan ku, aiba kullum zatanayi ba weekend ne idan yazo yiwa Mubarkh sai tana yi." Saida Umma da Mama suka ce su Zuby su k'yale Maganar san nan suka hak'ura wan nan duk don saboda Dan dafe dafen su ne datake musu da aiki dole sai ta gama suke sakata. Yau ma da yazo suna zaune akan kujera irin fararen nan mai Dining Roba Jibga Jibgan Littafai ne Wanda yasan 'yan SS1 na Amfani dashi yake koya Mata sai an gama da Mubarkh ya dawo kanta dad'in Shi Hansai tana da ganewa Dan ma Turanci na Mata tsiya tunda karatun k'auye Dana Birni ba d'aya ba, hakan yake koya mata har turancin wajen k'arfe 1 ya gama ya tafi Hansai ta.koma gida da Littafai cike da jin dad'i tabbas Burin ta zai cika . D'akin su taje su kande nata kuka ta zauna "wai meye ." Kande tace "nikam na fara gajiya kullum kamar Jakai yanzu wan nan Sadyn ta Samu Aiki don na kuskure ta maren ta had'a har da Karime." Hansai tace "kiyi hkr" karime tace 'wai me ake koya miki ne?" tace karatu kema kina zuwa" kande tace "tab kema ba munga ta yanda aka barki kikaje ba, aike kin sa ar me rik'o wllahi karime" tace "ni fa ban taba zuwa Makarnta ba, sai ta Allo itama d'in in naje yawo nake tafiya shiiisa Babata ta kawo ni Aiki wai na samu na kayan d'aki." Kande tace "ni kuma Matar Babana ne ta kawo ni k'anina kuma Almajiranci aka kaishi." Hansai tace "nikam kunga Babana shiya dage nayi karatu har nakai Aji uku ,nima ta Sanadiyar Matar Baba nazo nan,"haka dai sukai ta hira har iya ta zubo musu Abinci suna ci. Ruby ce A captaria itada Nuradden tana Shan Drink haka shima da Alama ziyara ya kawo Mata School d'in,"Ruby plss karki bari a Rabamu, ina Sonki" "Tace Nuraddn Dady na ya Rantse don karkace Yaudara ne shiisa nake gaya ma." Shiru yayi yace "hakane Allah ya zab'a mafi Alheeri" tace "Ameen" haka yaza me mata sai a School suke zance da Nura bayan ya tafi ta tashi ta tafi Hostle din wata frnd d'inta sai hira suke. Frnd din nata mai suna kubra tace ke "Next week bikin fareee" Ruby tace ymm! "Amma nayi Mata murna ,Amma nayi Mamaakin Yarinyar itada bata san Aure." "Kubra tace ke kinsan 'yar Gombe ce tana karatu Annan ta hudu da wani Sugar Dady barin kud'i kawai yake mata, nan da nan ta Amince ke kinga Motar daya sai Mata! da akai Engaged." Ruby tace "tab! to kema ai yakamata kiyi" kubra "tace niwa tab! ba Aure a lissafina yanzu kayan takaici." Ruby tace "Look nikam ba abinda nakeso inba Shi ba Sbd ina k'waruwa" kubra tace tab! ai seki dage" hakan dai sukai ta hira Ruby ta fito ta shiga Motar ta ta tawo gida. Tana dawo wa ta tarar da fad'an da Sumy ke idonta yayi ja ga Hansai na kuka dafe da kunci Zuby Sady suna zaune kan kujeru tace "yau kuma Uwar masifa dame aka tashi ? Zuby kam Dariya tasa Sady tace "wayyo cikina kinsan meya faru wai Nazi Saurayin Sumy yau 2 weeks kenan tun sanda Dady ya bada izinin zuwan sa to idan yazo Hansai ke kai ruwa shine fa kullum in suna Night call sai ya tambayi Hansai,to shine wai d'azu yace anya ba had'asu zai ya Aura da Hansai ba." Ta kuma fashewa da Laugh Sumy tace "Sady karki bari na yo kanki bar nazi kayan takaici Dirty Girl din nan zai had'ani da ita don yama Raina ni" ta kalli Hansai "Stupid kawai Munafuka wlh kinyi kad'an inma Asiri kikayi ,me zai dake kucaka to ki saurareni wallahi daga yau kar na kuma ganin kin sa kayan nan." Ruby ta wulla Ipon d'inta kan kujera ta zauna tana Dariya tace "OMG! wlh wan nan Girl nada matsala bake kika yo musu Uniform ba, Allah ne yayiwa yarinyar me kyau dole taja Ra ayin Nazi me san Mata aini na san Labarin son Matan sa balle yaga Hansai Ak'alla bazatafi 17 ba." Sumy tace "ya isa Ruby nikam ku barni na Lakad'a Mata na Jaki" Janta can bayan Garden tayi ta sata kamun kunne Hansai kuwa idon nan ya bushe da Hawaye ga Shi ta Hanata Magana sai Addua take Allah ya kawo Anty don sun tafi Osokoro Murnar Haihuwa . Zuby tace ke kam Sumy ki kyale Yarinyar nan sai nake gani kamar ba Laifinta bane da kin barta da Hijab d'inta da Shi yafi Sauk'i Amma ki ga sai Dan kwali kawai ba mayafi haka fa suke yawo nan nan ina ganin Ojuku na yawan kallon ta." Sumy tace "kunsan yanda nake san Nazi kuwa? to wallahi zan iya wulak'anta ta ayau zataga canji Dady tace "ke kika jiwo" haka kowacce tayi d'akinta aka bar Sumy na jijjiga . Anan baya kuwa Hansai ta jike da gumi sai kuka take daga baya ma sai Sumy ta d'auko kujera ta zauna a Garden din ,ga can Kande da Karime kuwa sai zaginta suke suna yi suna kallon baya sai wajen 3 Su Anty suka dawo aykuwa ko zama batai ba Karime taje tana kuka Anty tace "meya faru?" Tace wlh Anty Sumy ce tun wajen 1 ta sa Hansai kamun kunne a Garden sai kuka take kuma bata co abinci ba bayan ta mata duka Anty ta fita a xuciye.... By Queen meemi Queenmeemi.WordPress.com Join My Facebook group #QUEEN MEEMI NOVELS . [4:05pm, 11/02/2017] Nene: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣27❣ *JAN 2017* _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_ ******* Bayan Garden d'in Anty taje ta ga Sumy na waya gefe ga filet da Drink tana sha. A k'ufule tace "ke Hansai tashi" da k'yar ta mik'e ko tsayuwar kasawa tayi ta koma ta zauna Anty ta kamata Sumy data mik'e tana kumburo baki. Anty tace "Amma ke kam kin cika Muguwa wallahi me tayi miki? Sumy tace "Anty abinda tayi min Babba ne" tace "koma dai meye ai ba kya sa ta haka ba, Ai Mutum ce don haka karki K'ara saka ta wani Aiki naki de na kanki na soke inga yanda zaki." Ta kalli Hansai muje." Sumy afusace ta bi ta k'ofar baya tayi gun Ummi tana huci ta zauna Ummy tace "nikam ban tab'a ganin Masifaffiya irinki ba." tace Umma "wai ni yau Anty ta nasha zagi akan Hansai har Aibata ni ta Ringai" Ummi ta tashi zaune "me kikai Mata?" nan ta kwashe komai ta gaya mata. Lallle yanzu tana 'yar aikin? Ruby dake danna waya ta d'ago nikam aganina Sumy ba Hansai ya kamata kiwa ba, Shi Nazi d'in ya kamata saboda shine yace hakan,Alal hakika yarinyar nan bama ta san Shi ba, kuma kom meye kece sila." Sumy tace "ay don ba ke bace" Umma tace hakane ni ban san neman fad'a da har kinsa zan shiga gun Antyn Amma Naga kece silar komi saiki hkr." wayar ta keta Ring taga kiran Nazi taki d'auka kit ma ta kashe wayar . B'angaren Anty kuwa! tambayar Hansai tayi tagaya Mata akan komeye, Anty tace "ita taja ai daga yau kar na kuma ganin kinsa Unform d'in nan Ki koma sa hijab naki Hansai tace to ,sai datayi kwana 2 san nan k'afarta ta saki Tana zaune sai ga wayarta na K'ara da sauri ta d'aga Muryar baba taji nan ta fasa tsalle tace "Baba ya gida? ya inna da Abdullahi? nan duk suka gaisa har da inna taji dad'i sosai . ***** yanzu taka tsan tsan take da Sumy wani tsoronta take wajen yamma Anty tace taje neibour din su don kaimata sako taji dad'in fita wata iska ke ratsa ta dai de Lokacin Nazi ke sako Hancin motar sa cak! ya tsaya ya fita yaci Swag yace "ke Hansai ta jiyo Jikinta ya fara b'ari. Yace "zo nan" ad'arare taje yace kina sona? Dam! taji Gaban ta ya fad'i tsugunnawa tayi "Don Allah kayi hkr ni me Aiki ce idan Anty Sumy taji Duka zata min ka kyale ni don ina da Miji a k'auye." Magana take sai kallon bakinta yake yana Mamakin wai tace yar kauye don shikam baiga Alama ba, yace "ko bakya Sona ni kam ina son ki". Tashi tayi ta shiga Makotan da sauri Aranta tana cewa nikam ba Wanda ma nakeso sai Muntari nan ta knocking door , Matar gidan mai kirki suka gaisa ,Hansai ta dade don bata so ta kuma ganin Nazi sai hira suke da me Aikin Matar sai wajen 6 ta koma tayi Hamdala kanin suna dakin bak'i da Dauri ta shige . tun shigar Nazi yake ban hkr har Sumy ta hakura Amma kasan Ransa yana Mutuwar son Hansai ******* kwanci tashi ba wuya awurin Allah ,Hansai ta samu shekara daya da rabi Agidan Aikinta inda ta fuskanci k'alubale da dama tare da Nasarorin da take ganin ta cimma su,ciki harda k'okarin zana waec d'inta Wanda Uncle Abba yayi Namijin kokarin tare da taimakon Anty Wanda komai A Account din ta ake diba inda tace da na kowa ne dole ta taimakawa Hansai. Zaune Hansai take sai karatu takeyi saboda Jarabawar da zata zama next week. B'angaren su Sumy kuwa Ruma ta gama Masters nata yanzu su Zuby ke fama itada Ruby suna level 4 sai de wani hanzari ba gudu ba Sam Ruby yanzu bata maida hankali kan karatu kullum Carry Ova,Zuby kuwa soyayyar Fawwz ke nuk'urk'usar ta domin har yanzu suna tare Sun kasa Rabuwa kullum cikin damuwa So kenan. Al Amarin Sumy kuwa yanzu Soyayya suke zubawa san ran su ita da Nazi. Sady Kuwa duk Saurayin dayazo gunta to sai ta kore Shi Musamman idan bashi da naira. 11:PM Gidan tsit kowa na bacci Hansai ta mik'e tana ihu jin Ana tab'a ta jin karar Hansan yasa aka fita aguje,nan ta kunna fitila taga Karime da Kande na Sharar bacci Iya kam sai Munshari take,a salube ta koma bacci tana kamo addu'oi. By Queen meemi Queenmeemi.WordPress.com Join my facebook Group# QUEEN MEEMI NOVELS . . [4:19pm, 13/02/2017] Nene: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣28❣ *JAN 2017* NAGARTA WRITER'S ASSOCIASION(NWA) *_Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_* *Sakon Gaisuwa ga Queen Meemi Fans Allah ya bar kauna❤* ************* Tunda ta tashi daga Bacci ta Rasa sukuni bata gayawa kowa ba tai shiru da bakinta. Suna zaune itada Kande suna hira Lokacin Gidan Tsit kowa ya tafi harkar Gabansa ta ce "nikam Kande Jiya kinji motsin shigowa? Kande tace "Aa kinsan ni nauyin Bacci gareni." "Hmm kinsan me wallahi jiya atsorace na kwan domin an Shigo d'akinmu naji Anata tab'ani Baccin da ban ba kenan, Amma na rasa gano abun". Karime ta k'araso ta zauna Kande tace wai kinji Jiya anbud'e D'akin mu?" Karime tace "wlh naji Likimau nayi ai Jikina na rawa" Dariya suka saka Karime tace "nifa ina Ganin Ojuku ne ya shigo kinsan yana Sonki." Da sauri Hansai ta d'ago "tome ze kaishi har Lokacin? bayan kinsan ba a Gidan yake kwana ba." Kande tace "nima na yarda shine sede yau musa Ido" Karime tace "haka za ai." Kuka sosai Zuby keyi tana Rok'an Mama data saka baki kan Maganar ta da Fawwz Mama ta D'ago "Toni mai zance ne? kinsan yace baison Yaron nan ba, Gaba suke da Uban sa." Zuby tace Mama "wai wace irin rashin Jetuwa?" Mama tace "kisan tun kuna k'anana kinsan dai Dady ya Dad'e yana Siyasa to aLokcin da ya tsaya takarar D'an Majalisar Tarayya to shima Baban Fawwz ya tsaya Shi Dadyn ki a Jam'iyar *PRR* Shi kuma Baban Fawwz yana a Jamiyar *KMK* to Alokacin Dadynku yafi Magoya baya da yawa, to Lokacin da akai Primary Election, a zahiri Dadynku yafi samun K'uria sai akai Magud'i wajen Tantancewa aka bawa Dadyn Fawwz to tundaga Lokacin suke 'yar tsama to kunji don haka ki cire komai aranki na gaya miki." Kuka tasa "Mama Don Allah kimai Magana ko za adace."Mama ita kanta a Ranta tanaso ai Maganar Amma yau zata Gwada. *Gidan su fawwz* Yana zaune a Falon babansa Honourable Muktar da Momynsa agefe sai D'an gyara Hula yake Momy tace "Fawwz kaga Kaine Babba ya kamata kai Aure" Hon yayi Dariya "kana da Matar ne? ya Sosa k'eya "Eh Sunan ta Zubaida suna Maitama Okay waye Dadyn ta? Yace "Alhaji Tanko Minister" da sauri ya d'ago kai kaga ka Rasa dawa zaka had'ani suruki sai Wada da yake gaba dani, karka ma soma Domin banson harka dashi ba Party din mu d'aya ba." K'irjinsa ya bada damm! yace "ayi hakuri nan ya tashi ya fita yana mai Jin d'aci Aransa. *********** *Bunkure Mangalu* Gwamma ce ke ta kururwa duk k'auyen Anfito an tsaya gefe ga Mudi k'afa Akarye duk Jikinsa yanka kuka take kurmawa "Wayyo Mudi wallah Magauta ne na sani shiisa akai maka haka. Jummai hk'r take bata tace "kimin shiru kece dama kikai k'ulli ban yafe ba" Malam da kansa ke sunkuye yace "kimin shiru duk halin daya shiga ke kika Jawo kin d'auka zaman da suke A Lagos din na Dad'i ne? to wlh ba hannu na aciki duk balain da ya Janyo kece don haka ki ta k domin nansha Ganin aiken kud'in sa Ana kawo miki,abinda zanyi kawai na kaishi Asibiti." kuka ta saka "Malam dama nasan baka sonmu" da 'ya'yan Jummai ko waccen 'yar tsuntuwar da tuni ka mik'e to wlh bazan yarda ba." Shikam Mudi in Banda nishi ba abinda yakeyi da karfi tace "Mudi kayi Magana wai Meya faru? kaine akaima haka? Wayyo ni Gwamma." Da sauri ta shige Daki. Ganin Dije aciki yasa tace tai Mata wanke- wanke tace "ni fa Inna Nagaji." Au Bazaki ba? tace "wallahi bazan ba." D'an Jummai da ke zaune D'an shekara Hudu yace kawo nayi maki? Gwamma tsawa ta daka mai "kai yimin shiru Dan Magulmaciya" Jummai dataji haushi tace "Atoh da anyiwa Yarinya Tarbiyya me kyau ai da tayi." ta shige d'aki. Dai-dai Lokacin Malam ya shigo da me Taxi aka d'auki Mudi Ranga -Ranga Gwamma sai kuka tana yarfe zani .Bayan su Malam ta bi "bansan ki bini balle ki mana haukan." komawa tayi ta Shige D'aki Jummai kuwa sai Jimami take sai zagaye take tana jiran taji yanda abin ya faru. *Abuja@8:PM* Mama ce zaune tana a gaban Dady yana kwasar Dinner ya d'ago "Nasan da Magana a Bakinki tace "sosai kuwa Dady. Agaskiya ya kamata ace an Kauda Rumasa'u kai har ma Zuby Da Ruby, Saboda kaga fa har Ruma ta gama Masters." Ya d'ago to wake zuwa gunta? Mama cike da ta kaici "ai yanzu ba Wanda ke Zuwa gunta! domin duk Samarin Datai da wasu ma sunyi Aure har da 'ya'ya ,Alhaji bayan kaike koresu ban mantawa Akwai Wanda har Marinsa kayi kan bashida kud'i ya Nace yana kuwa ga Ruma Lokacin tana 18 yrs tai Farinjini ,Amma yanzu d'if kekeji ba Mai zuwa Dande mai hkr ce, Amma tanaso wlh yanzu bamai zuwa gunta ta" ta share Hawaye. Dady yace "naji ni na kore su Amma yanzu zan samo Mata miji Wanda Naga ya dace kuma dama irinsu nake so ba Talakawa ba." Tace "sai kuma Zuby Alhaji yarinyar nan ka kyaleta da yaron can tana son sa, hannu ya d'aga Mata karki fara banson zancen so nake ta samu wani Amma Banda Dan Hon Muktar. ita Ruby Yaron Banyarda da ingancin kudin Ubansa ba mai yaci meya ba." Mama tace "to Allah dai ya kyauta" ta tashi Jiki Asanyayae tanaso tai Biki itama bata tab'aiba duk 'ya'yan k'annenta wasu an musu Aure kuma duk basu kai nata 'ya'yan shekaru ba, itakam ba Ruwanta da sai masu azabebben kud'i ,donma Umma tak'i bata Hadin kaine ta kula itama mai idon cin naira ce, tsaki tayi don kana da kud'i dole sai 'ya'yanka Sun Auri finka a kud'i ni narasa irin wan nan Abu! sai Maganar zuci take har ta koma Side d'inta. *D'ankin su Hansai@10:30 PM* Yau Hansai da su Karime basi bacci ba Sun kunna Fitila sai Raba Ido suke iya ta tashi daga katifar ta tace "ku Yaran nan ki kashen Fitila kunsan bana iya bacci da Fitila" cike da tsoro suka kashe Ganin Goma da Rabi tayi . Can wajen shad'aya dai de duk su Hansai an Lula Duninyar bacci nan sukaji Ana Lalubar su Kande ta juya ALamar Gyara kwanciya Saboda Nauyin.baccin ta. Hansai kuwa jin an Janye Tigar ta ta tashi da saka k'ara nan duk su Karime ma suka mik'e yau basuji fitar ba, sai kuka iya ta tashi kai "Meye?" nan suka k'ank'ame Juna ,tashi tayi ta kunna Fitila duk sanyin Fankar dake kad'awa sai Gumi suke tace "meye?" Hansai tace "wlh kullum sai Mnuji Ana Lalubar mu a Jikinmu yauma Munji" iya tace "tohhh kode Mutam B'oye ne? nan ta zauna kuyi hkr da kunji Motsi ku hau cewa *(Innahu Min Sulaimanu wa Innahu Bisimillahr Rahman Rahemm)* suka ce "toh iya" "Karime tace kuma fa mun Rufe k'ofar" iya tace "Duk Al amarin Aljanu ne" tsuru suka kumai Hansai na kamo Addua suka kwanta. Nima Meemi na aje Biro zuwa Safiya. BY Queen Meemi Queenmeemi.WordPress.com . . [4:04pm, 14/02/2017] Nene: . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣29❣ *JAN 2017* ®NAGARTA WRITER'S ASSOCIASION _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_ . ********** Misalin karfe Goma na safe Motar Hajia Babar Alhaji ta kunno kai a harabar Gidan. Maigadi ya bud'e driver ya faka ya budewa Hajiya ta fito. Mubarkh ne yafara ganin ta da yake yau weekend suna Gida ya Rungume ta yayi yana oyoyo Grandmother tace "jairin yaro ni cikani Mak'alk'aleta yayi suka shiga falon su Sady sukai ta murnar ganinta akwatinta driver ya shigo Mata dashi ta zauna sai hira suke dukkan su sai gaida ita suke . Ta kalli Ruma "oh Rumasau har yanzu Bazaki Aure ba? to wlh wata daya zan Agidan nan dole asan abinyi." Sun san halinta da fada nan aka kaita dakin da ta saba sauka. Wajen 12 Dady ya shigo cike da jin Dadi Hajia ta farai mai fad'an barin yara ba Aure yace ai Hajia basa kawo wanda suka dace" tace "kai rufen baki idan aka biya ta taka bazasi ba don haka ni nasan abinda zanyi." Yau kwanan Hajiya kamar karfe 8 na Dare Dady ya kira Ruma ga Mama da Hajia agefe yace "wato dama akwai Wanda zai fara kuwa gunki Alhaji musa" hajiya tace "ko kaifa" mama kam sunkwi dakai tayi dama tasan k'arshen zencen a had'a ta da aboki, nan ya sallamesu ." Ruma kam ba yabo ba falllasa don tana da hkr ga Biyayya Hajia tace "to Ruby da Zuby fa? Alhaji ya sunkwi dakai. Hajiya "ba su Kara sa Makarantar ba sai sunyi Masters tab'e baki tayi "ka d'au Al adar Bature ka d'orawa kanka yara na kwad'uwa kana Ganin Ruby kasan Aure take so Allah ya kyauta." Yace "Hajiyaki hkr "ta mike ta fita. *Bayan kwana biyu* 10pm Hansai Sun gama shirin kwanciya don kwana 2 Sun saki Jiki ba'a tab'a su,duk Sun hangame baki sai sharar bacci suke. Hansai taji an Rungumeta an matse nan tafasa ihu da sauri su Kande suka mik'e Suma suna ihun, iya ta mik'e ta kunna Fitila dafe kirji sukai don ganin wadda ke tsugunne ihun su karimen ne ya taso 'yan Gidan har Hajia sukayo paty din masu aikin cirko -cirko sukai ga Hansai na kuka. Umma tace "meya faru? ke kuma Ruby me kike a dakin nan? sunkwi dakai tayi iya dake tafa Hannu tace "Abu dama ba a fuska yake ba.". Hajia tace "kai kuyi baya ni" nan Hansai ta karanto tun Lokacin da ake Lalubar su har yau, salati Hajiya tayi "abinda nake gudu kenan" Umma da ta fara Hawaye "Ruby d'abiar da kika koyo ko? duka takai Mata Zuby tace "kiyi hkr" kuka Ruby keyi Anty taja Hannun Hansai tace suje side dinta . Hajia kuwa in banda fad'a ba abinda take Gidan kamar rana Umma kuwa kukaa take tayi a daki tunda ta koma. Mama kuwa dama bacci take. Ruma tace "Haba Ruby ban tab'a sanin kina aikata haka ba, da hankalin ki haramun" Zuby tace "haba Ruby mesa haka? Sumy da Sady dama basu tashi ba Ruma tace "yanzu don Allah dabiar da wasu Matan ke fama da ita har tazo inda muke? Ruby dake ta kuka "ba halina bane ba wallahi kubrace sila kunsan ni Allah ya Sani a Jerin masu san Aure to ina wahala gashi Dady yace Wanda na kawo bai masa ba, nikam ina azabtuwa Ranar nan a School Muna hira da Kubra taga idona yayi ja sai nake tambayar ta idan tana jin shaaawa ya take sai tayi dariya tace "ke yakike? Nace Mata yakwa zanyi hkr zanyi ,sai ta ce "nikam ina da Hanya" nan Nace "ko azumi kike? dariya tasa "haba ba wan nan ba". Nan ta tashi ta d'auko wayarta ta bud'en vedio na 'yan les hankalina ya tashi Nace "yanzu ke kubra wan nan fa Allah ya tsinewa masu yi" Dariya tayi Ai akwai istigfari nikam nace baki san ranar mutuwa ba nide baruwa na." Tace min to zauna nan tashi nayi na tawo gida kwana 2 mukai bamu hadu ba sai Ana uku naje Hostel din su ina shiga dakin su Naga kubra na kissn din wata yarinya ni nasan kubra 'yar Suniya ce akwaita akwai barkatai din k'awaye shiisa suka tsundumata. zan juya ta kamo ni ta hau kissn d'ina shedan ne yarinjayen tun banso har na biye mata tundaga Tanar muke yi da ita to tunda mukai hutu kuma sai nake azabtuwa ba da wanda zan.Shine nake shiga dakin su Hansai musammn Hansai din." Salati Hajiya tasa Sam basu san tadawo falon ba kuka sosai Ruby keyi Zuby tace wa Ruma "nikam dama Sam bansan k'awancen Ruby da kubra domin an gayan Halayenta kawai don nasan kona gaya wa Ruby bazata sauraren ba." Ruma tace Amma kuwa Ruby wan nan abun bamai kyau bane yanzu kinfiso Allah yayi ta tsine miki ?" ni yanzu meye banaji sai de nai ta azumi na karki Kara barin shedan ya rinjayeki. "Nayi Dana sani Wanda nayi ma zanta istigfari don Allah ki tayani da Addua ." Hajia tace "yawwa Allah dai ya karemu don abin yayi yawa a Al ummar nan, kuma duk don anbar koyar war mazon Allah S.A.W ne sai kaga Yarinya k'arama tana Irin harkar nan." "Allah ya karemu" inji Zuby (to gareku iyaye Mata ku dinga bibiyar irin kawayen da 'ya'yan ku keyi ki sa ido a Al amuransu ,san nan kusan abinda suke muradi) Allah ya karemu da karewar sa. . *BY* *Queen meemi* *Queenmeemi.WordPress.com* [4:49pm, 14/02/2017] Nene: ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣30❣ *JAN 2017* _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usaman Family's_ ®NAGARTA WRITER'S ASSOCIASION ********* Washegari kuwa Hajiya rai ab'ace ta fito Ruby kuwa sai Fafautukar Yafiyar Umma take har gun Anty taje ta bada hkr kan abinda taiwa Hansai din. Hansai tace ta yafe .Umma Sam taki Kula Ruby Balli Hajiya ta tashi dashi Tai b'angaren Dady tun da yaga Ranta abace ya sha Jinin Jikinsa tace "Tanko karka bari na saukar da fushi na akanka!" nan tace "wallahi idan baka Aurar da Ruma Ruby da Zuby ba zan Mummmunan Sab'a maka kazo Babban falo na side din Matanka na tarasu can suna jira." Juyawa tayi Dady ya bita Umma Mama Anty ,Ruma Zuby Sady Ruby Sumy kowa tayi tsit tana zama ta k'wala kiran Hansai ta tawo Jikinta na rawa tace kazauna aGidanka Ana ta'asa baka sani ba, to ka Jibge yara k'aramar su itace yar shekara 20 suci me kyau susha me kyau Jiki da jini dole suji b'ukata haba" Takalli Hansai "kalli yarinyar nan Amana ce de aka kawo koda Aikin take 'yarka Ruby ke Bibiyar su cikin dare saboda tsabar sha'awar dake ranta to kayi masu Aure ." Dafe kai Dady yayi Anty tace hansai ta koma ciki wani kallo yayiwa Ruby batai Aune ba taji saukar duka atsawace "irin tarbiyar da na baki kenan ? Mai sa bakwa koyo da Ruma ne? kuka take sosai tana bada hkr Hajia tace "ba wan nan ba yanzu nakeso ka tsaida Ranar da zakai musu Aure" yace Hajia Ruma dama ma had'ata da Alhji musa ita kuma Ruby akwai wani Manager Nnpc sai Zuby D'an Gidan sanata kuma nan da wata 2 ." Hajiya tace "dayafi maka" ba Wanda yafi mama Jin dad'i Hajiya tace suma Sumy da Sady don kar abin yayi yawa ne da har su" haka suka watse kowa yayi side nasa. Da k'yar da sid'n goshi Umma da Dady suka yafewa Ruby suka haramta Mata kawance da kubra,istigfari take tayi. Bayan Sati biyu yau Hansai ke final Exams na Waec tun tana Rubutuwa take kuka saboda murna suna fitowa ta bugawa Baba da murna ta sanar dashi yace "burina ya cika Hansai Allah ya taimaka sai kuma Aure ko" kunya taji batace komai ba suka gaisa da Inna da Dan Jummai. Driver dake d'auko ta ya kaita Sun sha kwana Round about da zai kaisu Hanyar Maitama taga nazi dai- dai inda take sukwi dakai tayi Sun fara tafiya Nazi yasha Gabansu Ashe ya gansu da yake yasan driver din nan ya zaro 2k ya bashi ya bud'e side da Hansai take "ke Baby kince bakya sona ko? to kisa aranki se kin soni kuma sai na Aureki ba Sumy kike tsoroba karki damu." D'agowa tayi "kayi hkr ni fa inada miji agarinmu" dukan gaban Motar yayi "shut up kin maidani sakarai, kin kwa san yanda matan Abuja ke sona kuwa? su sa suke ma Gig Girls." Tace "ni ka k'yaleni wlh bana sonka" Dariya yayi yace "zan baki Mamaki ne ya shige motar sa yaja. itama driver yaja itakam ji take kamar tai tsuntsuwa ta ganta a Mangalu Sam tun lokacin abinda ya faru taji gidan yafita a ranta. *Mangalu* Baba ne a tsaye gefen dakin sa ga Gwamma na huci yace "dama duk abinda kaga wani D'an nayi wasu iyayen ne basi masu kyakkyawar tarbiya ba Ashe tun tafiyar Mudi Lagos suke sata shida Lawandi daya ke akwai Wanda suke kaiwa shine shi Mudi ya ce ya dai na kai musu fad'a ya kaure tsakanin su suka yayyen ke Shi kuma ak'ark'ashin Gada suke kwana a ikkon, Shi Lawandi ne bayan abin ya faru ya gudo dashi shine bayan Sun zo kano dama akwai yaransu anan suka kuma yimai duka suka Jimai Rauni shine kika Ganshi haka." Dama tun tafiyarshi Jikina bai Aminta ba Amma Gwamma kika Nace ai ga irinta nan." Jummai tayi Jimami tace "Allah ya kiyaye Gaba." Gwamma kuwa duk bata yardaba acewarta da sa hannun jummai. Malam yace "dole fa Dije ta Dena tallan nan ta na zuwa Makaranta yanzu Jbi Hansai jiya taimin waya tayi Jarabawar gama Secondary." Gwamma tace "ai dama ba san su kake ba! yace meye banyi ba ran nan Dije har kusan zagin Maalam na Allon su tayi, Allah yagani na basu Tarbiya kin bata,wlh Gwamma kawai kinci darajar wadan nan yaran ne Amma da tuni na sallameki." Hakan Gwamma take jinyar Mudi duk ta kare ga Masifar bashin dake kanta kullm sai anzo an fada akan hakan ga ciwon hannun da take yi duk tayi wujiga- wujiga . By *queen Meemi* *Queenmeemi.WordPress.com* . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣31❣ *JAN 2017* _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_ ®NAGARTA WRITER'S ASSOCIASION *_'YAN GROUP D'IN QASAITATTUN MATA ADAD'E ANAYI SAI GASKIYA. GODIYAR NAKU NE ALLAH YABAR ZUMUCI_*❤ *********** Tunda Dady ya Yanke Hukunci Zuby ta shiga Matsala saboda tsagwaran san datakewa Fawwz kullum suna Manne awaya abinda ya dada sadda da Rashin gamsuwar ta ga Mijin Da aka bata sabili da zuwan da yayi Sam sai taga kamar batai mai ba yana basarwa had'e da nuna isa. Agabanta yayi waya da Budurwar sa wacce yakeso bai wani nuna naam da ita Zuby ba La akari da tai watakil shima dole akai mai tundaga nan Jikinta yayi sanyi kullum kuka inda taje ta Samu Hajiya kan Maganar tace sai de tayi hkr. Bangaren Ruby kuwa ba yabo ba falllasa sun dai-daita kansu Mutumin nada 'ya'ya biyu ba wani Babba ,ne sosai da Alama yayi Mata ,itama tayi mai tunda yaganta d'agwas- d'agwa kaji abin Manya k'warya tabi k'warya . Itakam Ruma nata Suga Dady ne Babba ne yana da manyan yara Baban d'an sa ya Girme mata,itama tayi Naaam don Biyayya inda Shi kuma gani yake ya samu dami akala sai b'arin Naira yake wan nan kenan. Shirye- Shirye ake inda Manya aka saka Ranar 22 ga watan March 2017 inda shine d'aurin Auren. Zuby sai kuka take tana zaune ta D'ora kan ta akan cinyar Mama tace "na shiga uku Mama nifa wulak'anci yake min da Alama ban masa ba, kuma nima bai mun ba ,ki taimakeni." Mama tace "kiyi Biyayya ki hkr" ba yanda ta iya ko waya ya bugo Mata sai de yayi tsaki yace ykk ba yanda ta iya tace Lafiya ahakan har aka suke waya. Yauda suke zaune anata tsara Bikin ita kam Zuby kanta ke ciwo Ga Soyayyar Fawwz dake nuk'urk'usar ta kullum damuwa Sede su had'u dashi a School. Zaune take Adaki taci kuka, bakin ciki ne yayi Mata yawa ta fita wajen Garden tana kuka kiran wayarta ne ya motsa ta dauka daga can Dan Sanata yayi tsaki "idan bazaki Magana ba zan kashee." Haushi ya isheta "ka kashe mana Waya damu da kai ,duk abinda kake tak'ama dashi nima hakan" yace "bana Sonki don haka ki Sanar da Parents naki" kit ya kashe. Tunani ta fara Lokacin da wani kb ke sonta da sukaje Jigawa k'ark'ari ta Dinga cewa bata Sonsa har kuka yayi agabanta ,ta Buda kasa a idonta tace bata Sonsa face to face, sai yanzu taji Ciwon abin ashe haka kb yaji? duk da ita tasan bata san Dan Sanata Amma taji d'acin kalmar na Bai Sonta.hmm Abinda kai Shi za ama. Komawa Gida tayi tace Hansai ta dafa Mata kunun Gyada saboda bata iya cin Abincin. *Bayan Sati 2* Zuby ciwon so ya kwantar da ita itace har Asibiti nan hankalin Mama da Dady ya tashi kai kowa ma na Gidan, direct bayan treatment dinta da Doctor yayi ya kira Dady inda yace "ranka ya Dade 'yarka hawan Jini ke neman kama ta saboda damuwa da yawan tunani ya kamata ta samawa kanta salama." Dady yace "okay ba matsala" yau kwanan ta 3 a Hospital Su Dady shida Mama na zaune Dady "yace yanzu Zuby kan na Rabaku da Fawwz shine Sanadin Sa damuwarki har ta ke nema ki jawa kanki ciwo? Mama tace "Aa yarinyar nan fa D'an D'anata baya Santa koni wani Zuwa da yayi na zo zan fita naji yana gargaya Mata Magana kullum kuma sai tace min ga abinda yace Mata to ga Wanda takeso an Rabasu haka kuma Shi Wanda ake son had'asun yana yimata hakan Dole damuwa tai Mata yawa." Shiru Dady yayi "yace ba Matsala zami Magana da Sanata d'in kan Maganar . Satin Zuby D'aya aka sallamota duk ta fige Dady kuwa sunyi Magana da Sanata ya sanar mai abinda yake faruwa Sanata yace "ay 'ya'yan zamani sai ahankali, yanzu tunda abin yazo da hakan mu Janye had'in kawai, Allah ya had'a kowa da Raban sa, Amma wani hanzari ba gudu ba Minister ya kamata ku dai-dai da Baban Fawwz domin koba komai Gaba ba kyau kodan ka ceci Rayuwar 'yarka ,Amma ni da kaina zanje har can wajen nasa insha Allahu." Dak'yar Dady ya hkr. BAYAN Sati D'aya Da k'yar da sid'in Goshi Baban fawwz ya sakko duk da dama Dady ke Gabar dashi ,ba yanda zai yi haka ya hkr yace Ayi daman shima Fawwz din duk ya rikicemai wan.nan shine Silar shiryawarsu nan akai maganar Auren aka Maida kan Fawwz Nan shirin ya kuma kankama. Zuby ba Wanda yakaita jin Dad'i Auren Masoyi akwai dad'i su Dady an Rikice sai barin Naira ake komai daga waje ya wayar ai order Su ,ya'ya sun Samu irin Mazan da yake so. Sumy anci K'uzun Bikin nan, Mama kuwa Mutanenta kowa Nason zuwan sa haka Umma to Bikin 'ya'ya Uku wasa ne! hansai ba abarsu abaya ba wajen son Zuwan Bikin Wanda Jikinta ke bata tabbas wani Burinta zai cika agun Wanda yayi dai-dai da Saura Wata d'aya cir. Bari na tsagaita Anan . By Queen meemi Queenmeemi.wordpress.com . . . ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣❣ ⚜❣❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ❣ ⚜ ⚜ ❣ ⚜ ⚜❣ ⚜ *❣RABUWA CE SANADI❣* *_⚜BY QUEEN MEEMI_*⚜ ❣32❣ *JAN 2017* ®NAGARTA WRITER'S ASSOCIASION_ _Sadaukarwa ce Ga Basheer Usman Family's_ *********** Gida kowa shirin Biki yake kai hatta su Hansai ba abarsu abaya ba an musu kaya da yawa kowa ne event da za agabatar suma an musu nasu kalar anko da su head din su duk iri d'aya . ABangaren su Sumy Da Dady kuwa ba a cewa komai domin kaya na gani na fada suka dinka duk na event . Amare kuwa ba a cewa komai. Lokaci na tafiya Bikin na dada K'ara sowa Ankawo Lefen kowacce aciki set 24 tamkar had'in baki kaya turmus kamar abude kanti . D'aki d'aya aka ware musu nan aka d'auko 'yar Maiduguri tana Getta su masha Allah kowacce sai kyau suke ,yau da akewa Zuby Sady ta shiga Tace "Anty Ruma ya Za'a ai preparation na frnds event d'inku sa frnds naku?" Zuby tace "no wan nan ai akwai masu yi ki bari kawai" Sumy ta shigo "wow gaskiya dole ai mini nima don na Rikita Nazi." dariya Ruma tasa "tab! nikam keda nazin nan kuna ban Dariya." Sady ta tashi tana waya tafita don karbo dinkin ta hatta gidan sai da aka getta su duk an canja wasu kayan yau ta kama saura sati d'aya Bikin Hajiya ta duro da sauran Dangin Dady ,haka Dangin Maama da Umma suma suka duro. Anty kuwa k'annen ta ne zasu zo Amma sai anfara Event. Nan fa Dida ya kacame Dangi kota ina Dady sai barin Naira yake tunma ba A faraa Bikin ba ,ga Gift da yake karb'a gun Abokanan Siyasan sa. Shi kanshi katin Rabo kala -kala zaka ganshi Amare kuwa ko Giftawa sukai sai kaji kamshi kai gashin kansu ma ba abarsa ba ya ba wan nan kenan. Ranar Talata shine Ranar fara Biki inda za ayi Dinner da dare wajen k'arfe 7 dai- dai aka fara talle Amare cikin wata me makeup ce tazo ta yimasu kwalliya me kyau kamar dawisai haka suka fito A tsadaddun Amare, kowacce taci latest gwan inda wani shegen matrial ne me d'aukan ido da less ajiki abu na manya idonka Shi zai tantance maka yawan k��� y � �Uq��_X:� [kX{��lGm��z=����S�}u@� �� �m�bR�'�=�����i����Y��d��Y����3L�5咹5� >��6����螞Мh(�����7�� x�ⶩ ��ѓ5sbV��<�([ā��$��1P%XP#`��U��D�0����HI�� ���0P�4�LL!�� �Bl@�+q��EϽ97ܭ��WI�?!G������&^�q�/nu����!k�kDk�B��#�~��] ��u���� �M�Tl���׷A"G�sy����@��@R�Rd�S�1�a���X{���6��5�K�F�]�&�Qйx���R��r%x��z�]뼤�jhy�O�C�����V/����ה]�G!G�����J/nm���g�oS_\� -Jܼ�]X��f�3�\)�oe\�}a�O�sr[P��:[#��{V���vC�i�a�{�w���L��#��b�LT�Hߟ�6Ѹ�A,��q���� I��.5TXn�(�Y������~ ���ؐ�g��wn�u/n�i��T���Sþܱ�3��DGDT�@5>, ��Z����u�k3�Ϸ���"��1Moje�� �a�g��o?{��ն� �^�:��p�@ڣGvn. �N�_��X�/��#�۸��!�WWm�G;��C�鲇�>� \�k�0�G\XڎX���i�Ji1 !{۾mT�}��!/b�����yD���Ɠ�% ��������e�+ a�oPay�8�V��A� l\� }�����T��F���s��, �r �#,�oo�u�dޙ�X�eB01 �&, ��� ������x�`�)�!s� ��v�����s�a{B0Z�\���oU~��J-(�I�ǎ&�Qp�z� ��^1E�� ��}��yT����B�e�G������!�=u�K[�rS��2Xg��(�+��N��^"�� {E-`�^K�&'�O}��F��hS�:�w��->��Lp�z/O�wu ����^q�b�����p�3/yku�*�Ñ�:Q-� E���Jv��Agx7�C��`-�J��:�U������� kذG�VUJ��>��iA PAT_��K�6Y����9Ӯ�����1u(f�{}�3��5��z�^�-v&$\ȓ���1��q'����G�W[2�JW�C�Q�V� GI�Z�,`"$T&"d�3#��;ި��j�Y�L��>R�������m<�،lU���Z'H,,N��J0���C�݀uj�F�g�Q�3(������z�Zp�6z��������@J�N�>Cr�zc ���^<�F��8�F0�v���/��G`0���[��4�Day���O�� �gW&�l (+(d��8DaP��+"W'�B�P[��?�'���׻ ��2�悇XU�W��@����ދK��� ��3�H���q�����5�G�c��F#��G0� �\�$]%��ʶ���ѩ|pGMY��b�>yu�������緢<��_c���F��3 ��8�|����j�ʫ��0�F��?#-��7T��٥ T���(˸�˼�R�����O���IC����Fh�w .�\�∐��P*�~쭏 ��$B`���@cHѼ3�"���L��P|x���p�Ҏ�� �vK�$Z��m4c��Mlj϶͚" �NJ�j� Pb6Ϣ��$2� ��g!g�DRs i �`�a�Eg��E��ds�m�I ���� �C�.Ʉ���'��('uML OW�,4' :�Mk Zd�2/uJ��2����&? 84�>� h0�Wk�S���NQ�-7i�$>�3煻�y��I!8�/{3��R#� �+� h�mC�`��$�� 8Y�� ���j�V(da�%�,��q:���0^y�1!���Z�Z�n��gI�H8�: �K$gQ�j�#JFH��)�����E� 6�G_����c c��3�!���.65tP��3�$Ufn%�]*p� T�8��M������uv������U�Q2 ��� c.M]֎h�� �E`�| |`�r��� U<�Ҽ��0�^ �YS��AQ ��4 �B������ø�Yz�|(Ꮣ.��ʝI�:!���$ �\#�<4������cCRzh�9vٹ��(ӏ��W �E#��_��{�M :��Ō��Nh���yĠ5�sX�� z�<��!0�ᒰ��������#���q|�b�V R����btq�����C,j�%� WSᒭ � �k传�U� �F_�R&�����-���3��2tB�Q:ϴ���AȾ2�X!ږQK�EA��[D.����o�z�����Fʸz"�Wmь �F���pᚫ�0d��0�_ �C�$x��2kK|�"�D��]^�֙(�b �u ��}:!{�4���W��~�P"E�'w�p 47���B팢 gF� �D2x�Z�1��F����HՈ���S�JpC���wFyt���p�]6J���\�m�D!G������"Z�q���9r*~n��V1-Ē�W F��F {���5x_��o�w�>�϶�u6j]�WrШ��vG�e�߂qzG�s�ZӘ�����reI�)�|���6KvM%�_�|�M���=��nj(��/7���ŰC�����?� z���6�0���a��cA�w�2` ��x!G���� �)Ru�<�^L�EOB-`K-i����^O8��ƾ&m�h��M'�J�>���|���Y�����:'�&}������л (XS���К<�)�nT���o�"�K�����W7˟k�J�,�˳��z�T�"Ez��T ��X�=�d�XЀf��^����� ����?�T�X5���[`���{����gic���)Xvwޞ��z��et�<[vQA\�ǟ����'ؚ�4�E�OK@V��[��񟰘� ^f}�觓�?F-��x�_���\��xx��V f�3��g�Ċ "Q��ekJ�=Z�Ik:X!W� �;74����Õ)��ۥ��+:���D�ʂ�%+ ���h=6�� ���H�½���r5](b#�K [ �)` Q�8`)�R��<ƈը���-�\�u�M3Vʧ�6_�KȢ�x#3�;Ǘ���H:��\�~��|�BE���<�?��1�[KA0X���iٸ�1��Ed�0�p�⇒�Sby1۸Bx�� �0\}�Ӟ3s �i�� x3z���ԕ��V�0�K�՝����Y;��b������8���1QЧ�C��A��Dy����U u����~WL>�b��,����(U�)W��|YDC`�P�Ѐ �=+�$sxZd�[#d&HОH � ����a���nt��'���-�x�fa>4t���y�C�g���� �d�X�WK�'Ww^unC��"kxq�:� Uٖ��Z��]u��FE�'d������ E��7�G{ ��Llh3I�+BLI���%ޯ�G� �%\�H���+Y�ÊM4�@>Tȏ�Y��o������=bx0���/�x �M4\��ː~6}�&[S���a�}��x�"�PL�� �wV�u�%�:5���5� �A��/B�?�++�dv� _v�Ȕ�� u� �(� � �#�������n%+�`��K���f����$ j�W:�8 ߕ\&� Pd�*�Vo��q���e��v�Ô�i��uR�[ �S+�d�:�Yr�"��Ϯ����-$���4d ���״C���[���0FxG|%�a�,&l����b�A�����@�h�-N6� (�������cq18 �xD;�j� 85<���X1J�b�jD@*� W(n��^� �Q_Ya|)�[��OA�����\�n�BAKA�h��g�w{�|�0�,M8]yU+`FBh����7���S��Fu5�vbC������=��n��P� �[-�Z)zڪ��B8��I~�i��t��F�ؤ� ��,誚:�I�r�|lhQF� ��#`q��q�r�:��b�,�#X�|w�&��� Ѷ��Ʃ ���l�0�� ��ņ���=?��`�ZWFT#�V��(����VJ��F�&��T�s_q :'oPh�nz��9)�q~�pv��GD�Њ#S J���g1p��# �x��>���S����,��Qj�jQb�+�b�����J�;��DY �f��W=���㋨Atafkeken filin Gidan su akai Decoration na Gargajiya su kwarya ,tum-tum,su Ludaya ,Fai-fai da sauran kayan Gargajiyar yayi kyau don masu tsara irin gun aka d'auko ga Masu kid'an k'warya ne da yan Gad'ar su aka dauko nan suka zo, yau duk shigar Gargajiya sukayi inda Amare Suka sa Super Sharaton Babbar Aka d'aura musu Gwaggwaro(head)da Atampar rigar akai Buba suka dora zanin akan Rigar sunsha Makeup sunyi kyau kamar ka D'auke ka gudu Amma yau kowacce da kalar tata Sai d'aukansu Vedio ake idan DJ ya kada sai mai kid'an k'warya tabuga. Su Sady Kamar kai ya tsinke ko ina ka kalla sai walwali yake Ga yan Gada sai yi suke su Mama sai liki suke wa Hajia dake tsakiyar fili da Sauran Dattijai sai rawa suke , ko ina wadace da kayan motsa baki kowanne tebur. Dai de an fara Kamu Ana ta zuba Uban guda wayar Sumy ta buga nan ta d'auka Nazi ne yace yana kofarar Get ta fito zai bata sak'o,tafita sai yauk'i take kugun nan yasha Murjani ,tana zuwa ta tsaya "my Nazi How far?" yace "fine dear ya Biki?" tace "Alhmdlh." Nan ya mik'o Mata Gift Ga "wan nan ki bawa Sisters namu Gudunmawa, Dad'i taji tace 'oh! dear Sun Gode" yace "they diserve more" Murmushi tayi "Jirani na dawo" Juyawa tayi tana Mirgina Ukwu binta yayi da Ido ,kamar ance ya Juya Hansai ta fito daga Mak'ota da wani Makeken flaks akai da sauri ya fito zuciyar sa kamar ta fad'o wani irin Bugawa datayi tayi fat! fat!, "Hansai" taji ankirata cak! ta tsaya juyawa tayi Ya kafa Hula yayi shigar Abuja Boys ,yace "ke ya Biki?" Jiki na rawa tace "Lafiya" Dariya yayi yace "ke bakya sona ko? dara daran idanuwanta ta d'ago ta zuba mai "I can't love you" Shafa gemu yayi "Lol Yarinya kinfara Jin Speak ashe ,Harara ta watsa mai ta tafi ,ya rik'o maya finta, dai de Lokacin Sumy Ta fito rik'e da flaks da kayan take Away. "Tab jar Ubban can!" tsawa ta dakawa Hansai "me kike anan? Jiki na rawa tace bkmi Anty" harara ta kaiwa Nazi yace "Sorry Princess tambayarta nake." Mari ta kaiwa Hansai har da bugu ta dumata Dundu abaya, Durk'ushewa tayi tasa fasa kuka Nazi ya had'e rai "wait Sumy ki daina dukanta." idonta yayi ja saboda kishi tace "ya zaka zo kana nuna Mata so bayan kasan banso wallahi hansai sekin ganekuren ki, in banda son matanka me zakai da hansai ,Ai se Nuhu maigadi, ki sani wild duk randa Na kuma ganin ki dashi sai kin koma kauyen ku." Wani kallon masifa Tayiwa Nazi karma kazo kana ban hkr domin bazan Saurareka ba.A fusace Nazi ya shige Mota da Gudu taje mai take away a gaban motar afusace ya ja nan ta dawo kan Hansai "tashi banza ko yaushe akanki nake samun matsala da Nazi rankwashin ta tayi mai zaiyi dake adauri kashi ko abata Igiya." Motar Suhaima ce ta Danno kai ta yau ba irin ta jiya bace motar hon tayi ganin Gidan cike ba Space yasa ta Dan matsa gaban Gidan tai Parking Motar ta fito Yauma tayi kyau kana ganin ta kasan hutu ya ratsa yau kuma shigaright Purple tayi, tayi Masifar kyau. Sumy ce ta ganota "Oyoyo Sis Suhaima Welcm" idanuwan Suhaima ne suka sauka kan Hansai tayi Murmushi "meya faru yau kuma?" Sumy tace "Rabani da wan nan banzar 'yar Aikin tunda Saurayina ya k'yalla ido ya ganta Raina ke b'aci Agabana yake nuna Mata so bazan iya d'aukan kowane irin Nonsense ba wallahi." Tausayin Hansai ne ya kama Suhaima tace "Sorry Aiba Lefinta bane" Sumy tace ai sena renama Nazi hankali. Kamo hannun Hansai Suhaima tayi Ta d'aga ta ta mik'e nan ta dau flsk din Ta kalli Suhaima "Nagd" Duk yayin da ta kalli Suhaima se gabanta ya fad'i nan suka shige Gidan . Biki yayi Biki gud'a ko ta ina na~ub!��QO�<���׈��B�yf?*���C�b�CO�gF���5�"�13+[���F�fR�B9��gn�^鑚�W�ʼ�.���ߪP?���lu85 �ZPLJh�&NZW��P��b��5HT�e�>�����4*J���)\~_��/�d��6���L1���JGdk �"��N��g<�Pb��ꮜ�ǧ���db4�:��oĕ�L%x�V����;`��y9��+�g�^�#6���f{�/2r,�sT�>R��sP"ҀX���+R�un:�g�6M{ d�SӇw�_ ��4���|'']8d~_���$1�_�F<��/E�j¡�� r�7�c ��F|��������i/������x ��6$�0P����I:���P�_�8�-�� ���' � � ��YQ�34�(������d��{��qw�R5D�=�<>�~�����>"�[ ;p���w:N�*l ~V�� d���:}2/�"�w.s�� Ə�s�r{�] ��X\AE<�V������)ɑ�E_��2�_kF�9�M',�ȅĮ�ZT�bQ\$x� ]C7���� T\W����?`�_(f#q8 ��Wo�踐�,��/ѡ _���ǘ��¹��W�*�s2�����6�c �C �2� Մ�ȧZ"�j�H�W���P��'m��� } �M'��> R��}Z��~ꪁ���oɨ�(��1 ����' ��c.ؙu�b���S8B��G�'�?���7�6'��+8$��%� ��j1�-a�sl< �Z � Zٽ����G��@��C ��Fj���,�B .WF3�<�����+�?�A�CƼ㡟����Q���+�N��H�i�!"�����#��|��w��@mE ��q�<�|Z}�ȜLA�n,'nqk�Hdֶ8�����⸰�@�md L�V(AZbCQ kdA��Eat��� ���?4��9b0��`ɪ�� 0/ �֎�%. �������?�����^p ��Cr+ ��� �O�%F�����N-���}j{tN�����e�'"H���oTm ��K?d�w�v��� I$�o���E��l:��D$/h,��p�Bo �������BY��È3��:Fy�odAPV"R;�V^��� ����*�a�H0��C!;߷z��go�u`�h�=1fViIi�������#_�n��o�L����4�l7���q������!����.Rv7�`� �H|�F�J0LF+��cD�?�Ax��Da��U�؀׈��#��'W� ��|����ՃA^�Eb�zo{r�T�1�9�����cCG�:��^�[�+�&|C/���1@f|� �Qj�P�p��� �H��c������*��#���22�x�U&r2����'�!G�����Q��������P�g~ZHRכ^YTln�[RJ�3� 9 A�E�W�`�;d�u�D�@��'ɘ������ ��gp�&e��sp�0@�wR�`�Rec_C �d�/�o��|�J� J���&X]��[m.\t{����QMf;m�8װ��;-���U�5 ]) S��\\R�R�~|u��U�ww\@E�wQp�P��{{��M��}ݼ�D����j�Vf����ST�,ee6����:�c}�>��U=�� ���$x�D˙��0U�EWsC�����N��²�����s� �+�����>��6K�%Ѩ��FJ��Tg�L�UG�VZ`V��7�V?�p3��)�A�Q���m���|$��)ò3?���=��+M��)΁���o/k:�?clr}9���!p U�9�)M�����R:��h£��Z������ǝQ�T�a�G�Bp�5SZ��uBi殭+34vo��V�"V�x����3 z+��(Q`)���-D�D,�Cs3í�b�P�Y�ӌ(��� z�p�t���|*��7�Ũܭ�)J*%����;�5IQ0�g?��k����̽��b��� /�[{�I�Է���R�W}�ɍZ9�+Cy"(�0FZ�����c�� �P6A,z%{߻��i�^��X#�*�#���i����� ��`1P�H*4{P,��(d��S�Eq{�'ϪfV�Z���T�Ғ:�\-h�W4�[`�&��i��2c���)�Q�}@�kFı }��./�lEO��3A��9TB��2�f"C gk�\G�,���7�c;v��b��è�Z�fzY �x=���<���M£�Hri��Ta�d��Fꕪ&���o��ف��&!�c%Rɘ����h+�h�k!�I�x�ڳ�-���t9�E���q5�y�>�7���}~�IQ �@xX����{�� :��I��`�)]�FJ�:AR�������.�C�0u�;M*���h�[�޶�W�C?�l�� h����v�1]ōp�R<�^i��w'�����:g�zulh1��R�kU)!��M+lD���f���:؀gB� �7qd� P��<�F�Q��t]L�@.F��!��:~�J�RR�C��٪<�j��ߪs3E�36���/�V���K>%(S=)~�����yR��9쭐�O���BZ��,᡹�ރ�A�X(@��qy�$�T���_�*�WX����� ��t ˻�i�qH�@��׈�u @�� *I��J�S�z�P�`_��\;��0��]:A�I�|�Ʉn���D|��}<%~��\�S~ӆ��p�@�-H�V�<�2q6#{�&�_\5ԻM�{��C��'���� ��T��\\s��E] "���r��g�İK��D�,\�b(�JE��:S~@�p����p8�V��A�oġr�1$H�f�|#� ��w�2DD�G&`��A��n{M��'wK:h���L�д�OjĞ�Hٺ{5�t����P֑